Hadari ne ya hade garin sosai baka ganin komai sai walkiya da kara kainan motoci a lokacin wanda suke haskawa don ganin gaban su.
A daidai wanan lokacin ne motoci guda uku da suka karyo titin a jera wanda ke nuna wani mai akwaine tafe a lokacin yadda mutane suke ta kaucewa a titin suna basu wuri.
Wasu daga bakin titi ke fadin yanzun haka ma ba maigidan bane tafe wanan fitsarariyar matan tashine haka da bata ganin kowa da mutunci a idon ta.
Wani gida motocin suka shiga a lokacin gini ne na zamani motan ne suka dan tsaya da alama magana akeyi da wani a cikin gidan.
Ba a dade ba suka wuce zuwa cikin gidan kai tsaye security ne suka fito don bude motar nan naga wata farar mata buzuwa ta fito tasha ado na fada da gani daga saman ta har kasanta kwaliya ne.
Doguwa ce sosai ga fari sai dai idan ka kura mata ido zaka iya gano farin ne kawai ke aki yake rudin mutane don kyau akwai kyau inda bamu matan mu na Nigeria masu kyan asali da dire bayan farin da gashi da kuma tsayi babu abin da suka dara matan Nigeria dashi na fannin kyauwo.
Tana wani tako ta shige ciki zuwa part din ta ta dan jima ciki ta fito tana kwala ma wata mata mai suna Labara kira da karfi .
Da saurin matar ta iso gareta tana dukawa tare da fadin hajiya barka da zuwa an dawo lafiya yaya han, , , ,
Dakata tace wa matar yaya naga witan part din can a kunne ko mara zuciyar nan ta dawo ne kuma ?
Matar ta dago kai a hankali tace wa hajiya babba kike nufi waye hajiya baba ina nufin fatima matar wancan shiyan ta fada a fusace jin an kira uwar gidan nata da hajiya babba taji haushi.
Eh ta dawo laraba tace ai tun ranan da kuka wuce washe gari ta dawo kutawa tayi tare da juyawa da karfi ta shige part din ta a hasale.
Anan tabar laraba da kallon mamaki ta nisa tana fadin ikon Allah mata da mijin ta kinzo kin hana zaman lafiya a tsakanin su haka ?
Ita kuma a daki sai faman huce takeyi ita daya nan ta dauki waya ta kira mijin nasu da suka rabu yau ya tafi waje yin wani aiki.
Duk da tasan dare ne a duk inda yake amma bai hanata kiran shi ba a wanan lokacin saboda tsananin kishin dake damun ta a lokacin.
Kiran farko ya tsunke bata hakkura ba ta sake kira a karo na biyu bai daga ba sai wayan na gap da katsewa ya dauka da alaman barci yake a lokacin .
Murya irin ta masu barci ya daga wayan tare da fadin Nafisa lafiya kira da dare haka yanzu fa kin san dare ne nan sosai a wanan lokacin.
Bata jira ya gama magana ba tace watau munafuntana zakayi ashe kasan matar ka ta dawo shine baka fada min ba tun muna tare sai kawai in dawo in samu ta dawo gidan.
Ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin tadawo fa ni ban san ta dawo ba don basu fada min da cewa zata dawo ba ma kit ta kashe wayan.
Ta wurga a gefen gadon ta tana fadi a fili duk sai nayi maganin shegun tsofin don sai auren nan ya mutu inga ta bakin naci irin nasu.
A daidai lokacin ne kuma aka turo kofan side din nata wata matace cikin dogon riga ta dora hijjab a saman rigan nata.
Fuska da murmshi tace mutanen Abuja ashe kuna tafe yanzu ne an sauka lafiya yaya hanya fuska a daure ta juyo tana fadin eh muna tafe ko idan zan dawo sai na sanar da wani akace ko ma ?
Ke yanzu don baki da zuciya dawowa kikayi duk da maigidan ya nuna baiyi dake saboda rashin zuciya irin naki sai da kika dawo kamar ana zama dole ne.
Matar tadan sake murmushin dabai kai ciki ba tace nake ganin ke nan haka amma ni nasan yana yi dani har gobe ke ce dai ganin ki ke rudin ki ga hakan don ko na bar gidan shi bamu rabuba don ga diya ga zumunci a tsakanin mu.
Fati ke nan zakiko ga abinda ba daidai ba wallahi in dan kin nace sai kin zauna min da miji don sai na rami ya fiki shan iska a gidan nan tunda haka kika zaba wa kanki sannu sugar mai iyali ko tasbi sarkin zumunci shida bakajan da daya bai biyo ka ba .
Murmshi tayi Allah na tare da mai gaskiya dama jin kin dawo ne yasa nazo taron ki da dawowa ba wani abu ya kawo ni ba a huta lafiya bata tsanmanin ta amsa mata ta fice daga dakin .
Zuciyar ta yana ciki da mamakin fitsara irin na Nafisa wanda sam babu kunya a cikin shi ko kadan sai zallah cin fuska da fitsara filli.
Daki ta nufa a daidai lokacin da ruwa ya gauce sosai a garin na kaduna kamar da bakin kwarya da sauri ta isa ta rufe mirrow da sauran abinda baison walkiya a dakin saboda tsaro wanda ba kowa ke wanan ba a wanan lokacin sai masu sani da hakan a baya suka saura rufe irin wa yan nan abubuwan a daki yayin da ruwan sama ke zubuwa daga samaniya don kariya daga fitinan walkiya.
Falo ta dawo ta zauna tare da yaranta dake cin abinci a wanan lokacin ido ta tsurawa yaran biyu sai da ba wai don tana kallon su hankalin ta yana gare ta ba ne tunane takeyi a zuciyar ta na irin rayuwan da ta tsunci kanta a ciki yanzu.
Tun shigowan Nafisa cikin su komai na rayuwan ta da mijin nata ya sauya sallo a lokaci daya ba yadda suka saba gudanar da rayuwan su ba suda yaran su da sauran yan uwa.
Hatta yaran yanzu a matse suke da zama gidan mahaifin nasu sun fison zama a gidan kakanin su da zaman gidan nasu saboda matsin da suke ciki a yanzu.
Ita dai tasan aure ne a tsakanin ta da mijin ta na soyayya tun tana karama soyayyan su ta samu asali don gidajen su basu da nisa da juna shi din abokin yayan ta ne.
Kuma akwai zumunci na makwabtaka da ya koma kaman na jini daya a tsakanin gidajen su tun kakan su zumunci ya kulu a tsakanin gidajen biyu.
Wanda yakai bako ba zai iya banbanta tsakanin su ba sai wanda yasan tushen abin koda ta girma bai daina kulata ba cikin yan uwa haka ya kai har aure ya kullu a tsakanin su.
Tayi haihuwan farko lafiya ga cikin na biyune ya samu aiki kano suka koma can sun koma bada dadewa ba ya hadu da Nafisa yar mutan Niger da suka shigo Nigeria neman kudi da iyayyenta ta lake mai tun bai kula ta har ya soma kulata don suna sayar masu da abinci a bakin ma,iakatar su ne.
Yaron ta ne dayazo inda take zaune tana tunane ya katse da da fadin mama daddyn mu bai dawo bane naga anty ta dawo.
Shafa kan yaron tayi taja sauke ajiyan zuciya tace bai dawo ba Affan da kaga ya shigo nan ai anty ce ta dawo ita kadai.
Yaushe daddy zai dawo mama yaron ya kara jefa mata tambaya kuma tace Affan ban sani ba idan ya dawo ai zaku ganshi.
Bai barta ta huta ba ya sake jefo mata tambaya again yace mama ai anty ce bata bari mu ganshi ko munje wurin shi sai tace mu fito muna damun shi yana hutawa.
Murmushi tayi tace kai Affan ba yana zuwa nan ida muke kuna ganin shi ba to may kuma kake so shiru yaron yayi kamar yana tunane a zuciyar shi.
Sai kuma yace ni mama ban ma son ya dawo saboda may Affan uwar ta tambaye shi yace saboda idan ya dawo sai ki ta kuka mama su kuma suna dariya da anty kuma su fita tare.
Affan ban son yawan surutu fa ka faye surutu ina jin tsoron wanan bakin naka kullu naji ka kara fadawa wani matsalan mu sai na yanke ma kunne daya.
Shiru yaron yayi yana tunanen kada uwar ta yanke mai kune kamar yadda tace din kayan da sukaci abinci ta kawar ta gyara wurin suka shige dakin kwanan su.
Da safe bata fito ba sai da ta gyara part din nata ta nufi kitchen don dafa ma yara abincin zuwa school sai ta samu kitchen din a rufe.
Dakin kwanan laraba mai aiki ta nufa a nan ta samay ta tace yau laraba lafiya naga kitchen a rufe Labara tace aikin hajiya karama ne hakan.
Nima na fito zan gyara tace na barshi taja kofa ta rufe nayi tunanen zaki fito don saboda abincin yara gashi kuma ta kulle kitchen din.
Dan jimm tayi tana tunane a ranta wai may Nafisa take nufi da ita ne haka abinci dai na kowa ne a gidan amma haka take mata idan ta bushi iska sai tace wai ana barnan abinci da yawa gidan.
Bayan abinci ma da take ita daya sai ta ba wasu balle yanzu da ya samu karin girma sosai a wurin aikin shi basu da talaucin komai a rayuwan su.
Muryan Laraba ne ke fadin sai hakkuri hajiya idan mutum ya ci gaban ka sai dai bi wallahi gama tana ganin ta samu miji a hannu sai abinda tace a gidan.
Ba komai Laraba na gode badin tura su can cikin gida wurin hajiya su karba haka ta juya ta wuce zuwa part din ta tabar Laranba a wurin tana jin tausayin ta.
Daki ta koma ta shirya yaran ta fito dasu da kanta ta mika wa kanin mijin su dake zaune dasu a gidan ya kaisu cikin gida wurin hajiya a basu abinci.
Yace yau kun makara ne tace eh salis koda na tashi har gari ya haska sosai wallahi kaga idan nace zan tsaya dafa masu yanzu sai su makara.
Ta koma ciki ya kwashe yaran zuwa gidan su dasu don duk a unguwa daya suke zaune da iyayyen nasu gida uku ne a haka kuma Nafisa ke tsula tsiyar ta a gidan.
Don tafi son zaman kaduna saboda anan kawayen ta suka fi yawa da yan yaren su na buza da suke kara zugata tana iya shegen.
Salis na shiga gidan kafin ya isa part din mahaifiyar mijin nasu da yaran matan gidan suka fara magana a, a su Affan ne haka yau da safe nan.
Salis yace eh maman su ta makara ne yau bata tashi da wuri tayi masu abin karyawa ba shine zasu zo nan su dauka.
Murmushi hajiya kubura tayi tace Fatice zata makara da safe kawai dai yar bakin halin gidan su ta dawo jiya akwai da wata a kasa.
Ba an mayar da Fati bata san tadawo ba shine ta dawo ta samay su bakin halin nata na banza ya tashi yanzu ta soma ke nan har sai ta kure ta ta tanka mata.
Allah dai ya sauwa dayar matar gidan ta fada daga daki tace shi kuma da yazo sai ya biyewa iya shegen nata ba daga daki suke magana.
Sun shiga gun kakan su tana ganin su tace ai na sani ba yar iskan yarinyar nan ance ta dawo jiya ba nan yanzu tsiya zai tashi a gidan wanan karo ko ba zan saurara mata ba wallahi.
Salis yace cewa tayi makara tayi fa bata samu dafa masu abinci ba yau yaya maganan ku yazo daya da na mommy ne ?
Hajiya bata iyayin magana ba sai jan yaran datayi zuwa cikin part din ta ta zuba masu abincin da tayiwa yan marayun jikokin ta da suke hannun ta.
Bayan ta gama sallaman yaran ne ta dauki waya ta kira Fati din tace wai may ke faruwa ne yau a gidan naku cikin fara a ta fara gaida surukar nata da bata ko tsaya gaisawa da ita ba.
Amsawa tayi sama sama dakyat tare da maimaita tambayan ta a gare ta tace hajiya makara nayi tace jinan fati na san komai walahi nasan abinda yar banzan yarinyarin nan zata iya.
A sanyaye fati tace hajiya ba haka bane makara nayi yau din ban samu dafawa ba kashe wayan hajiya tayi badon ta yarda ba.
Kashe wayan nata yayi daidai da shigowan hajiya kubura wurin ta tace sai gasu Affan na ga sun zo karban abinci kuma ?
Bari hajiya Kubura duk da uwarsu ta boye min na san akwai wata a kasa wallahi bai yuyuwa haka kawai taki tanadarwa yara abin zuwa makaranta.
Nan suka zauna suna maganan hajiya kubura tace idan ita fatin bata iya magana mu ba kyalewa zamuyi ba ai ana horo da yuwa ne kuma ?
Kai hajiya ta dafe tace Allah ya kawo muna karshen wanan yarinyar a gidan nan hajiya kubura tace amin tana mikewa tare da fadin bari mu gani zuwa rana idan har sun dawo nan kin ga hasashen mu ya tabbata ke nan ta rufe kitchen din nasu ke nan.
Ta fice ta bar hajiya a cikin bacin rai tana tausaya ma wanan rayuwa da yayan nasu suka tsunci kan su a ciki na bamin auren buzuwa da ya dorawa rayuwan shi yana zaune kalau da matar shi ya jajibo masu wahala haka.
A gidan Fati kuma bata karya ba tun safe ba tunanen kanta takeyi ba a yanzu sai tunanen idan yaran sun dawo may zata basu idomie ne ya fado mata arai ta sayo ta dafa masu suci.
Damay zaki dafa wani zuciya yace mata tsaki taja tana tausaya masu a ransu take tunanen da can baya lokacin tana ita kaida ya fado mata a rai.
Abinci sai wanda ransu ke so zata dafa da ita da yaranta da maigidan ta har sai taba makwatab wani lokaci yau kuma gashi a sanadiyar kishi da buzuwa har horo yakai ga a rufe store da madafar abincin gidan baki daya.
Babu wanda zata kara kai kara gareshi tunda baji mijin nasu keyi ba ko ta fada karshe ma ya dawo ya hauta da masifa gashi ita ba son masifa take ba a rayuwan ta.
Haka ta taso da tsoro sam bata fada ko kadan saboda ruwan ciki irin na matan hausawa da ta taso a cikin shi wanda a cikin tarbiyan diyan hausa yake.
Kamun kaina a diyan hausawa rasgin hayani da fada da mutane barkatai wanda akasarin matan hausawa hake ne ke cutar su a gidan mazaje su da gun kishiyoyin su yan bana bakwai.
Tana tuna yadda Nafisa tazo gidan daga ita sai ghana most go din yan kayan ta a ciki amma yau ta koma kamar wata hamshikiya a gida.
Auren ta da aka dauro ba tare da sanin iyayyen su ba can bariki suka dauro auren su da ita inda ta tare a gidan da yake a lokacin a kano.
Sannu a hankali har ya samu iyayyen shi suka hakkura ta fara shiga cikin su inda take baiyana harin ta na zahiri a hankali.
Da farko ta yaudari mutane inda taja yan uwan miji a jikinta duk suka yarda da ita ta gama jin sirin su kaf kafin daga baya data bunkasa ta fara fitar da kalan ta ga mutane.
Inda yanzu kowa ya gama gane ta wasu masu zuciyar imani sun gujeta masu kwadai kuma har wanan lokacin suna tare da ita duk da abin hannun ta bai ban baruwa wasan dadi sai kayi mata bauta kafin kaci abu daga gare ta.
Don haka take kallon kowa a wullakance sai uan uwanta dakan zo jefi jefi cin arziki wurin ta wanda ba a wuce wata daya basu zo gidan ba.
Tazo da wata yarinya da take cewa wai kaunar tane sai da tafiya yai tafi aka gane cewa yar tace ta cikin ta yarinyar.
Nafisa zata girmay ma Fati ga shekaru haka yasa tafi fati wayo sosai har take jin tsoron ga fin karfi ga sihiri don bata shigo haka kai tsaye ba sai da ta shirya ta shigo gidan .
Shi kan shi maigidan ba a banza ta barshi ko yanzu kuma bawai ta fasa abinda takeyi din bane sai ma abinda yaci gaba a cikin halayen nata.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
MIJIN BUZUWAðŸ§
2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
NOVEL DIN NAN NA KUDI BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAN IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA
Hayaniyar yaran da suka dawo daga makaranta ya dawo da ita ga tunen tace shike nan nawa ta samay ga Affan da dan banzan wayo kawai na shiryasu zuwa cikin gida wurin kakanin su tasan idan sunje can sa samu abinda sukaci a cikin su.
Yaran suna shigowa suka fada mata a jiki suna fadin mama mun dawo yunwa nakeji sosai wallahi karamin ya fada take taji gabanta ya fadi don hakan halin su ne .
Sai subar abinci a cooler makarantarsu su dawo dashi kuma suce yunwa suke ji halin yaro ke nan oya a cire uniform kuje cikin gida wurin su hajiya kwaci abinci a can banson yawan hayaniya yau.
Acan cikin gida kuma dawowan yaran gidan makaranta yasa hajiya ta kasa kunne taji shigowan jikokin nata da take zaman jiran tsamanin su tunda safe.
Ba afi min ashrin ba ta fara tsinkayo hayaniyar su daga kofan shigowa gidan tace a ranta nasan a rina dama tabbas hashe na ya tabbata ke nan wanan yarinyar har takai can.
Yaran suka shigo dakin da murnan su don anan kawai suke samu su sake suyi yadda suke so batare da wani tsangwama ba.
Suna shiga Affan ya cire rigan jikin shi ya rage daga shi sai singlet yana fadin hajiya maman mu tace muzo nan muci abinci a wurin ki wai yau bata son damuwa.
Yar ta Aisha ta kwala wa kira tazo ta basu abinci sai gata ta fito daga daki tana saye da dogon riga a jikin ta tana ganin yaran tace a a su Affan ne yau da rana tsaka anan zakuci abincin rana ke nan ?
Hajiya tace zuba masu Abinci don Allah ki kawo masu nan ta wuce kitchen cika umurnin mahaifiyar nata da sauri sai gata dauke da plate din abinci ta kawo masu.
Hajiya na zaune gefe ta kurawa yaran ido tana kallon yadda suke cin abincin gwanin ban tausayi dasu tunane tayi aranta da yau babu ita fa kamar yadda babu ran kakarsu ta wajen uwa yaya Fatima zatayi da wanan ukuban haka ?
Hajiya kubura da take matse ita tunda rana sai gata ta shigo wurin hajiyan da mamaki a fuskanta tana fadin yaya kin ga hasashen yana son ya tabbata a kan yarinyar nan ko sai ga hajiya karima uwargidan su tashigo a bayan su tace tabbas maganan mu ya zama gaskiya.
Ya tabbata ke nan ta ki bari yarinyar nan ta girka abinda zasuci a gidan abin har ya tashi ga ta hana mai aiki yi masu girki suci ya koma ta hana masu abinci.
Sallama ake daga kofan shigowa dayar yarinyar gidan ta leko daga kofan hajiya karima tana fadin sannu da zuwa yaya Suraj.
Bai amsa mata gaisuwa ba sai tambaya yayi ba kowa a gidan ne ina sallama gidan shiru tace suna dakin hajiya mama ina gani can yanufa dakin don yasan idan sunyi irin wanan taron akwai abinda ke faruwa da ya shafi dayan su ne don don iyayyen nasu nada hadin kao sosai a gidan.
In ka debe ko wanan ya kasance amaryan su Asiya bata gida ne a lokacin da su hudu zasu hade a dakin kofan ya nufa yana saye cikin uniform din shi na sojoji.
Sallama yayi a bakin kofan daga ciki suka amsa mashi mahaifiyar shi hajiya karima tace kamar muryan suraj nake ji a kofa yace nine ummi.
Dakin ya shiga kallo daya yayiwa iyayyen nashi alokaci guda ya gane akwai wani matsalan da suke fuskanta wanda ya shafi hajiya mama a gidan.
Gaida su ya fara yi a cikin ladabi kamar ba soja ya samu wuri ya zauna bayan sun karba mai gaisuwa.
Duban hajiya kubura yayi yace mommy akwai matsalane su Affan dake cin abincin su hankali kwance ta nuna mai tana fadin wanan fitinaniyar matar uban tasu ce kila ta rufe dakin girkin gidan ne yau ko da safe a nan suka dauki abincin zuwa makaranta.
Yanzun kuma kaga uwarsu ta turo su nan su da sauri yace ita Fatin fa may zataci to ya tamnaya yana kallon fuskokin su gason jin amsan su.
Mommy tace ai shi muke tunane a nan dafe kai yayi yace wanan mata ban san abinda take nufi ba a gidan nan tana son mayar muna da dan uwa binan.
Kada kaga laifin ta ai shine mai babban laifi mama ta fadi a hasale sai mummy tace ba yin kanshi bane yaya bar irin shuuman matan nan wallahi.
Suraj ya mike a hasale yana fadin yau sai naci mata mutunci idan haka gaskiya ne wallahi ko a gidan maza ana ma mutum horo da yunwa ne balle gidan brother za a ce anyiwa mutum haka.
Ko maigadin gida ai yana iya kyauta da abinci tunda bai rasa ba balle diyan shi ummi ta kalle shi lokacin da yake shirin fita daga dakin tana fadin ina zaka ?
Kai tsaye yace gidan zanje wallahi idan na samu gaskiya ne yau sai tabar gidan nan wallahi ummi tayi saurin cewa dashi kaifa mahaukaci ne na sani a dai karbe key din ka bude wurin shike nan.
Kasan yadda dan uwanka ke son ta hakan zai iya kawo matsala a tsakanin ku yace wallahi sai dai ya kawo ummi wanan wani irin bakin haline haka ?
Ai haka suke mommy tace mashi abinda ake mai gudu ke jan tun farko bai gane ba basu son kowa sai kan su da yan uwan su kawai wanan halin su ba wai ba.
Mama dai ta rike goshin tada hannun ta sai wanda duk yai magana cikin su ta bishi da ido kawai shine nata yayin da zuciyar ta ke mata soya a ciki tana jin wani irin ba dadi a ranta.
Yana tsaye daga kofa mommy tace bari muje tare dakai zaifi da sauri ummi tace haka zaifi kan don wanan kin san mahaukaci ne ya shawo Alluran shi ja sojoji kar yaje ya sauke wa yar mutane a kai.
Ai da zai sauke din haka zai fi gani take duk ta gama da kowa a gidan babu wanda bata iya takawa shiyasa take abinda taga dama inji mama.
Yanzun dai bari mu tafi idan munje ni zan fara shiga wuri ta inji ba asin yin hakan da tayi sai asan abinyi sukace yayi kyau hakan mikewa tayi zuwa dakin ta ta dauko hijjib din ta ta saka suka fice da suraj din a motar shi suka karasa gidan.
Daidai lokacin Abba ya dawo shi da anty amarya daga asibiti da dan ta da bai da lafiya ganin motar suraj ya gilma ya nufi gidan dan uwan nashi yasa suke mamaki.
Anty amarya ke fadin yau suraj ziyara zaikai gidan Abdul ne haka mahaifin nasu yace kila yazo ya samu Fati ta koma dakin ta ne zai dubuta.
Sai da suka shiga gidan ne suke jin abinda ke faruwa karban key anty Amraya tayi bata shiga dakin taba ta bar yaron wirin uwar gidan nata ta mara masu baya.
Sun samu kofar gidan a rufe wai taba maigadi sallahu cewa kada ya bari kowa ya shigo gidan ya damay ta don yanzu ta dawo da yarta daga makaranta zasu huta.
Da kyat ya bude masu kofa sai da suraj yayi mashi jan ido wanan abin shiya kara harzuka suraj din rashi ya baci sosai kusan a tare suka shiga gidan da anty amarya don samun delay din shiga da sukayi.
Bin gidan Suraj yayi da kallo daga sama har kasa kafin ya karasa fitowa daga motar shi cikin hasala mommy tace ashe kun dawo ke nan take cewa anty amarya tace mun dawo ina shiga ake fada min abinda ke faruwa nace barin biyo ku don ba mutunci ne da ita ba.
Anty tasan ida take rashin mutunci ta ai nika yau idan tayi min wallahi balbalata zanyi in daki banza sai dai mu rufe da mijin ta ai mun saba.
A tare suka shiga gida jin karan bude get din gida ta fito a fusace tana fadin maigadi wani dan bura, uba kabudewa, , , , , ganin su mommy yasa tayi shiru ta juya da saurin tana zaton basu ganta ba suko sun ganta.
Kafin su iso ta wuce part din ta ko da sauri don tasan ba bakin ta bane na Fati ne don ita suke zuwa gidan su .
Tunda ta sallamay sallah la,asar take zaune saman sallaya ta tun tana addua ta koma tunane ga tunanen ya bowayeta don yunwan da ke cin ta.
Sun shiga da sallaman su aka gaisu tace mommy kune tafe ashe mune fati har kasa takai tana kara gaida su cikin mutunci suka amsa mata ta dago tana fadin yaya Suraj marmari daga nesa.
Ke kin ci abinci yau ko baki ci tambayan da ya jefo mata ke nan a lokaci daya tayi murmushi tace kajika da wani magana kuma ba a gida ka samay ni ba zakai min wanan tambaya haka ?
Mommy tace Fati ba tambaya muka zo yi ba don mun san abinda ke wakana a gidan ko yau dai bakici komai ba tunda garin Allah ya waye haka ne ko ba haka ba.
Kai ta sadda kasa tace hakane mommy tace to akan may Fati zaki zauna ana maki horo da yunwa dake da diyan ko haka abincin nan akwaishi ba babuba kuma.
Mommy yau fitina take ji tun jiya data dawo ta samu na dawo gidan ta fada min bakaken magana har tana ikirarin sai na rami ya fini shan iska a gidan nan.
Shine yau da safe zan shiga kitchen na samu ta kulle komai tunda asuba wai kada a dora girki a gidan ta fadawa Laraba ni kuma ban koma ta kanta ba tunda nasan don ni tayi hakana.
Haba Fati sai ki zauna da yunwa ai zaki kashe kanki ne idan kina haka yanzu bari muje mu samay ta muji may take nufi wai.
Suraj bai bisu ba ya dan tsaya ganin Fati din yana kuma tambayan ta may zataci yaje ya sayo mata tace duk abinda ta samu yace kayan tea fa tace suna store acen muke ajewa fita ya yi ya mara masu baya.
Sun shiga da sallama cikin isa ta karba masu sai suka tsaya gaisawa da ita tunda iyayye ne su bayan gama gaisuwan mommy tace munzo ne dama muji dalilin rufe kitchen da tsore din gidan da akayi wa mutanen gidan.
Hajiya nan fa gida na ne ina da daman da zan rufe ko ina nake son don Abdul bai bar abinci da Fati a gidan nan ba tunda bai cata dawo ba ta dowo don haka sai ta jira idan ya dawo ya bata abinci ita da diyan ta suci.
Karya kike yi munafukar Allah kuma baki isa ba wallahi muryan Suraj ne da batayi tsamani ba ya fado dakin yana zazzare mata ido a cikin hasala yake magana yana huci.
Tare da daka mata tsayawa yana fadin ban makulin nan tun ban balbalaki yanzu a wurin nan in kuma sa sojoji suzo su kwashe ki sukaiki barikin mu su daure har ranan da miji ku ya dawo inji shiku idan shiya ai horo da yunwa haka.
Kallo da tayi wa Suraj raga fuskan nan nashi ba imani a cikin sa zai iya aikata abinda yace a kanta tsoran ta Allah tsoran ta soja da sauri ta mike ta shige dakin ta yabi ta da harara.
Yadawo da fuskan shi kan yar ta dake cin abincin da tayo masu take away a hanyan dawowanta gida ya watsa ma yarinyar harara da sauri ta noke kanta kasa ta kasa cin abincin da tun shigowan su dacin abincin ta take yi bata ko gaida su ba.
Da sauri tafito daga dakin dauke da key din a hannun ta tana mika mashi cikin ladabi ya fisge a hannun ta har ya fara tafiya su mommy zasu bishi sai kuma ya juyo yana fadin.
Ina ne kitchen din da tsore suke ki taso muje yau za a yi ta ta kare and idan bayan tafiya ko harara naji kin ma yar uwa wallahi yau ba ubanda zai hanani daureki a garin nan jiki na rawa ta bi bayan shi zuwa tsore din yace ta bude da kanta ta bude.
Laraba da mai masu aikin gida namiji da ta dauko dan kabilar su can garin su wanda ya zama kamar CID din ta ga komi a gidan ko tana nan ko bata nan ya kira.
Komai na tsore din aka fito dashi waje aka kasa uku yace Fati ta kwashi kashi biyu ita da diyan ta kashi daya ta dauka nata ne.
Ga abin magana ba halin yi don tsoron soja da ke zuciyan ta tun da zasu shigo Nigeria sojoji suka latsu a hanya take tsoran soja inda duk ta ganshi.
Yana tsaye a rike kunkurun shi da hannayen shi biyu yake tambayan fati akwai wani tsore da kitchen a gidan tace eh akwaishi a part din ta wanan nata ne ita fatin suke amfani dashi in generar.
Kwashi naki kikai part din ki da sauri taja wani kwali da kyat tana fadin kasiye dauko mun sauran ta matsu tabar wiein wanan dan banzan soja mara hankali dake gabanta.
Dama tun zuwan ta gida da ta fara ganin shi aka nuna mashi ita a matsayin sabuwar matar wan shi bai yi murna da ganin ta ba a fili ya nuna hakan kowa ya gani.
Don shi kyamar irin su yake yi bai dauke su wasu cikakkun mutane ba a idon shi, yafi daukan mayaudara aduk inda ya gasu haka yake kallon su a yatsune.
Shine dan uwan shi ja jini ya auro ya kawo ta cikin zurian su take juya mutane yadda ta ga dama a gidan da takaicin ta ya juya tafi bai shiga gidan nasu ba a lokacin mommy tare da anty Amarya suka koma gida bayan sun yiwa Fati nasiha kadan.
Nan suka tafi suka bar Fati da tsoro a zuciyar ta fam sai dai abinda bata sani ba a halin yanzu Nafisa tafita shiga tashin hankali don tsoranta Allah tsoron ta Suraj soja.
Wanda ta hango mugunta zalla cikin kwanyan idon shi abinda ya fadi tasan karamin aikin soja ne yayi shi ya aiwatar da abinda ya fada din dole ga magana nacin ta da zata fadawa Fati a yau sai dai babu halin yin hakan gare ta dole ta kawo ido ta saka mata a gidan tana jiran dawowan mijin nasu wanda zata sa ya ci fuskan Fati din a gidan.
Ai idan sun san wata basu san wata da makirici zataci galaban su gaba daya don ta gane yan uwan mijin da iyayyen shi duk munafukai ne a kanta.
Can gidan su hajiya sun koma kumshe da dariya a cikin su sai da suka shiga mota suka fara dariyan abinda suraj din yayi wa Nafisa .
Yanzu sun gano takon ta Suraj ne zai dinga mata hukunci irin nasu na sojoji na rashin imani sun shiga gida nan suke bada labarin abinda ya wakana a gidan.
Mama taji dadin har cikin ranta ko banza Suraj ya kwantarwa Fati incin ta yau wanda inba shi din ba, ba wanda ya isa yayi haka a zauna lafiya da ita tunda tayi niya.
Maganan mommy ne ya dakatar da ita da taji abinda Nafisan ke fadi a lokacin shigan su gida da take fadin wai babu rabon su Fati da yayan ta ga abinda maigidan ya bari a gidan.
Lalaima wanan matar tantiriya danta ya dauko mata ba kwai ba donge amma har take ikirarin cewa wai ba abincin su a gidan.
Wani zafi na bakin ciki irin wanda iyayye ke ji a gamay da diyan su idan sun yi abu ba daidai a cikin alumma wanda sai uwa ko mahaifi suka san da irin zafin da mama taji a lokacin.
Haka dai ta shige daki a dadafe bakin ciki da takaicin da matan dan nata ke kumsa mata a zuciyar ta yayi yawa kuma dan nata ya sani amma bai iya daukan wani mataki akan hakan.
Wunin ranan haka suka kare shi da maganan Nafisa wanda hakan ba bakon abu bane agurin anyi sau tari da yawa sai dai na yau din ya banbanta da sauri don ta fito ta nuna masu karfin iko da izan da take dashi a cikin kan dan nasu .
Wanda suka haifa suka tarbiyartar da hannun su kuma ya tashi da tarbiya suke saka ran samun farin ciki a wurin shi kamar yadda duk wasu iyayyen ke fata ga diyan su idan su samu
Amma lokaci guda Nasifa ta shiga rayuwan dan nasu wanda ya watsar da duk wani rayuwan farin ciki da suke hasashen samu daga gare shi.
Gashi a yanzu yana a cikin ganiyan samun duniyan shi wanda bai zauna ba tsaye yake wurin neman na kanshi a rayuwan wanda ba komai yakawo hakan ba sai addun mahaifa da yawaita ta sadaka akan diya yake bibiyan shi a yanzu.
Don a baya in zata iya tunawa bata da aiki sai yawai ta sadaka fiye da kowa a gidan in anyi magana sai tace ba neman duniya nake wa kaina nemawa na baya nake madogara.
Ga yawan taimakon na kasa da ita tundai idan ance yaro maraya ne sai mama tasan yadda takai alherin ta ga yaron ko ta saka yayan ta suyi mai alheri daga abinda suke dashi na jikin su mai kyau wanda zai farauta ran yaron da za a ba abin.
Don Allah iyayye mata mu kula kada muyi sakaci da wanan dama akan marayu da muke gani zaki iya dafa kan yaro maraye zai ji dadin hakan da kikai mai har a cikin ranshi.
Bawai duka maraye bane zai bukaci taimako wasa ma da dariya a gare su sadaka ce dan abinda zai farauta masu rai sadaka ne Allah ya bamu ikon yi ga maratun dake a kusa damu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
MIJIN BUZUWAðŸ§
3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
NOVEL DIN NAN NA KUDI NE BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO 08036959257 ASHA KARATU LAFIYA YAN UWA.
Tsaye take gaban mirrow tana gyara rigar da ta sa a jikin ta na tampha wanda akai mata dogon riga dashi mai wani launi kamar jikin damisa brown colour.
Dinkin mai dan kwala sai da wuyan rigan V neck akayishi wanda yasa gaban ta ya fito dakyau daga cikin rigar kasan rigan ma an bude shi free yadda zata iya walla kafafuwan ta ba cikin matsuwa ba.
Turare ta dauka ta feshe jikin ta dashi ta juya ta dauko gyalen ta dake saman godo gefe ta fesa mashi turare ta mayar a hand bag din ta dan kwali ta dauko ta dan daki lokaci tana daurawa take fuskanta ya fito tsonen a jikin mudubin.
Duk wanan shirin da take yi ranta ba dadi don bata son zancen zuwa kaduna a zuciyar ta tafi son tayi rayuwan ta a gidan ubanta dake a cikin garin Minna.
Inda gidan su yake a kwangila road asalin su su hausawa ne zamane na kakan ni ya kawo su garin minna har suka zama yan ainihin gari baza kace su bakin gari bane yanzu don kowa nasu anan aka haifeshi.
Daga wajen gidan wanda irin ginan da can bayane na siminti wani murya ya kirata da fadin Khadija kina makara fa a cikin irin hausan mutane Niger shiba kananci kuma ba hausa pure ba do ya dan hade da surkin harshe.
Muryan Khadija ne ke fadin mama shiri nakeyi gani fitowa yanzu da sauri ta karasa shirin ta jawo dan trolley din da ta sa tufafin ta a ciki tare da rataya handbag din ta a kafada ta fito waje.
Kallon ta mama tayi wace zance a wurin ta khadija ta debo kyau da na saba kafin in ga mahaifin ta farar mace ce doguwa yar kabilan gwarin may kunkele dake a cikin minna din.
Kallon yar nata tayi tace kin fi son ko yaushe kiyi tafiyan marance mama nina fison in shiga da yamma yafi ba wanda yasan zuwan ka sai dai a ganka.
Maimakon tayi haraman tafiya sai ta ja kujera roban dake gefenta ta zauna kallon ta uwar tayi tare da fadin yaya haka kuma ?
Banbara nake jira na aika a sayo dashi zan tafi bana son in mising din shine idan naje ke dai yanzu na gane baki son zuwa wurin yar uwan naki tunda kika girma kika fara karatun jamia .
Ta dan ya motsa fuska mai kama da sallo ko yanga wanda ba haka bane kusan yanayin yan garin ne haka suke maganan su da kamar sallo da yanga tace ni nafison in yi hutu na a gida.
Amma ita ya Amina kullun sai tace sai mutum tafi wurin ta hutu yanzu kuma ba da bane ban son ina missing din gida sosai murmushi kawai uwar tayi don tasan halin yar nata.
Ba ajima ba mahaifinta ya shigo gidan yana ganin ta yace a Khadija an fito ke nan eh baba zan tafi hannu yasa ya fara laluban aljihun shi sai ya fito da dubu biyu ya cire guda ya miko mata.
Kai ta girgiza mai tace baba ka barshi kawai kudin da anty ta turo min zai ishe ni na gadone a daidai lokacin yaron da ta aika ya sawo mata banbara ya iso da leda a hannun shi yana mika mata da canjin karike canjin tana bude ledan ta debo banbaran ta mika mai ta mike tana gyara jakkan ta yaron ya taima ya fita mata da kaya ida ta tare Napep zuwa Abdulsalam garej .
Tana isa saura mutum daya ta biya suka shiga suka kama hanyan garin kaduna yamma lis suka shiga gari lokacin kuma akai hadarin marancen nan da Nafisa ta dawo ta samu Napep din da zai kaita unguwar da yar uwar nata ke aure wanda kusan rabin zaman ta a baya a nan tayi shi sai data girma ta koma gida karutun da take yi Abuja yanzu shine silar mayar da rayuwan Khadija gida Niger state.
Tun ranan da khadija tazo kaduna bata fita ba tana daga daki sai falo indan ta fito ko kuma ta shiga kitchen tayi masu girki a gidan.
Yau da yamma ya Amina ne ke kwala mata kira tana zaune tana cin banbara da tayi worming din shi kamar yanzu akayi shi bai kwana ba.
Ya Amina gani ta fito tana fadi cikin ranshin kallon fuskanta don Allah zo ki shiga gidan su mommy ki karbo min sako tace yanzu in tura a karbo min.
Fuska khadija ta ya motsa tace ni ban shiga ba tunda nazo banje na gaidasu ba Amina tace wai khadija may ke damun ki ne haka ?
Ke a rayuwan ki sam baki son shiga jamma a ban san inda kike dauko wanan rayuwa naki ba haka cikin bacin rai ta juya dauko gyalen ta kayan da tazo dasu garin ta kara sakawa a jikin ta.
Yaran anty nata biyu ta, ta kira su rakata gidan da aka aike ta din fitowan su bakin get din gidan yayi dai da zuwan wata mota a guje ta watso masu ruwan dake kwance a wani dan rami saman hanya.
Cikin bacin rai Khadija ta dago kai tana fadin you are very stupeid bakya gani ne kika watso ma mutane ruwa haka.
Horn kawai Nafisa tayi masu ba tare da ta tsaya khadija tabi motar da hararan takaici tana dan kakabe riganta da ruwan ya dan taba a lokacin.
Raina yayi matukar baci haka muka doshi gidan mutane ina mita wani saurayi dake tafe a bayan mu naji yace yar iskan buzuwan nan ne haka take tuki kamar mahaukaciya wallahi.
Dan juyawa nayi na kalli mai maganan nace sannu yace yawa bata dai zuba maku ruwan sosai ba ko nace kadan ya taba mu inayi har lokacin ina kakaban ruwa a jikina.
Gidan muka shiga wanda har lokacin raina a bace yake da buzuwar da naji saurayin nan yace min da sallama muka shiga gidan.
Wanda sai kawuce kofan falon gidan kabi wani dan siririn hanya da zai sadaka da cikin gidan da muka shiga wanda babban gida na ba yau bane farkon shigana gidan don duk zuwa nayi sai anty ta aike da gidan ina shiga akai akai yanzu tunda na girma bani shiga idan nazo sai da wani dalili.
Sallama mukayi inda kofan uwargidan ne fara isa sai na mama daga can ciki sai kuma wasu biyu dake kallon nasu din na mommy dana anty Amarya ke facing din su.
Hajiya ummi da yaranta nake jiyo hayaniyar su daga kofan part din ta na dan matsa daga kofan dakin ina gaida su dakyat aka amsa min ban tsaya ba na wuce.
Lekowa akayi daga dakin ummi don ganin mai gaidasu din da bai shigo ba bata gane ni ba alokacin har nakai kofan mama shiyasa ban son shiga wanan gidan don yawan dake garesu kuma sai kabi kowa kagaida shi dole don hadin kai irin na matan gidan.
Koda baka gaida mutum ba wanda kaje wurin shi zaice dakai ka ko gaida mutanen gidan sanin haka danayi yasa na fara binsu daga daga ina gaida su.
Dakin mama ma a kofa naja na tsaya ina fadin ina kwana mama ta amsa min daga ciki tana fadin waye shigo mana ciki.
Dole na shiga daga cikin dakin tare da kara gaida ita inda nakai gwiwana duka biyu a kasa irin gaisuwan mu na mutanen Niger.
Daga kuryan dakin ta aka fadin muryan wa nake ji kamar khadija Adamu da sauri mai maganan ta fito falon ida nake wani irin ihu ta sake a lokaci daya tare da kwalawa binta kira tana fadin ga khadija Adamu ashe tana garin nan mukayi maganan ta jiya.
Murmushi nayi ina dagowa daga gaida mama da nake nan suka shiritar dani nace anty ta aiko ni wurin mommy.
Bayan nagaida amaryan su ne na wuce zuwa dakin mommy ta tareni da fara anta mun dade tana jana da hira wanda ni ban iya sake jiki dasu muyi hiran sosai saboda mutunci da girma da nake gani a idona.
Sakon ta dauko min na fita mukai sallama dasu nan suka rakoni suna dan taka min in baki mantaba mai karatu na fada maki a nan kaduna nayi rabin rayuwa na.
Kamar abin tsokana wanan motar dai ne na dazun ta dawo a guje ta kara yin facali da ruwa a take nace wanan wani irin iskanci ne wai haka ?
Har motar ta wuce sai ta dawo baya a hankali zuwa gare mu a lokacin zainab ke fadin Nafisa ce fa ta dawo zai tai muna cin mutunci kila taji zagin da khadija tayi ne.
Gab damu ta tsaya tare da sauke glass din motar wata farar mata nagani ciki tare da wata zaune a gefen mai zaman banza.
Tace wace yar iska ce cikin ku take zagina shiru naji sunyi suna soke kai kasa nan san lokacin da nace mata kece dai yar iskan da baki san darajan mutane ba kika gudu da mota haka a wulkance cikin gari kamar yar koyo.
Ke tafadi a zafafe tana kokarin bude kofan motan da sauri naji su Binta da zainab na fadin yi hakkuri anty bata san ke bace .
Cikin zafin rai nace ke wacece da zaki watsa ma mutane ruwa kice kada ayi maki magana wallahi ko diyar shugaban kasa kike sai nayi maki magana .
Karasa fitowa tayi daga motan tana fadin ke yar gidan uban waye a garin nan take raina ya kara baci nace kedin yar gidan uban waye da baki da tarbiya fada min naki in fada maki nawa.
Fisgan hannu na Zainab keyi ni kuma ina turjewa don ban ga wani kimar ta da suke gani ba idons a lokacin don sam ban da tsoro akan gaskiya na.
Ke yar waye da zaki tsaya kina fada min magana son ranki nace ni yar gidan ubane ke kuma cewa akai titin na gidan ubanki ne da zaki dinga gudu kina watsa ma mutane kura da ruwan titi.
Yadda taga ina yi sai ta tsaya tana kallo na kafin ta mayar da fadan akan su Binta da zainab din tana fadin zamu hadu da kune wallahi don nasan da sanin ku take min hakan.
Nace wai kun san wanan banzan ce da kuka tsaya tana fada maku maganan banza saman hanya haka ?
A harzuke tace nice banza nace an fada maki idan ba banza kike ba may kike zaki tsaya kina ma mutane son raki ke gaki mai kudi ki takamu ki wuce lafiya kin taki banza ko ?
Zaki gane kurenki wallahi wani kallon banza na watsa mata nace sai dai mu gane kuren mu amfada maki don kina da kudi zanji tsoron ki ne ko may kudin ki bai damay ni ba tunda ban taba zuwa wurin ki neman wani abu ba.
Matar da take cikin mota ne taji abin yayi yawa kuma dukkan mu munki bari ta bude mota ta fito tana jan ta tana fadin haba Nafisa zaki tsaya kan wanan karamar mara kunya kuna raba hali a saman hanya ai sai ta ja maki raini ga jama, a.
Kuta tayi ta watsa min harara na mayar mats ta shiga mota tana fadin zaki san kin shiga hurumi na nace inga alheri .
Fisgan mota tayi sai da yayi wani irin kugi suka nufi hanyan cikin gari zainab tace wai Khadija kin san kowacece ita din ?
Wacece kuwa banda kila matar wani ko wata kusan gwaunati shike nan don muna kasa sai ta rena mu Binta ce ta katse ni da fadin matar yayan mi ne kishiyar anty Fati.
Inda motar yabi nabi da kallo nace yanzu wanan matar matar dan uwan ku ne wallahi na dauka irin matan bariki din nan ne masu zaman kasu nima ban san yaya akayi idona ya rufe haka ba naci mata mutunci.
Nan nake fada masu abinda tayi muna da zamu shiga gidan su yanzu kuma ta sake maimaita muna shiyasa raina ya baci don naga kamar da gaiyya tayi hakan amma kuyi hakkuri don Allah.
Binta tace ai mu yau kin muna daidai wallahi don ba karamin dadi naji ba da kikaci mata mutunci nan a gaban mu.
Mun da jima a tsaye dasu karshe mukai sallama muka shige gidajen mu har lokacin ina da zafin matar nan a raina.
Nafisa ko sai fada take kawar ta na bata hakkuri tana fadin ban son ki biye mata ba tunda kinga kannen mijin ki a wurin may yuyuwa tasan ki ke baki santa ba.
Zanyi maganin ta wallahi sai ta rena kanta zata san ba a taba ni a zauna lafiya ko wacci tuwo dani miya ya sha na san dai ba yar gidan uban kowa bane ita.
Su zainab na shiga gidan su suka fara bada labarin arangaman mu da matar yayan nasu nan mutanen gidan suka fito suna sauraren su.
Mommy tace kai amma wanan yarinyar wallahi ta burge ni sosai yau da haka Fati ke daurewa ta mayar mata da martani da abin nata ya rage.
Anty amarya tace ai ba zata iya ba ne don ta riga tasa mata tsoron ta a zuciya kuna ganin a banza ta bar mutane ne haka da kowa ke shayin ta.
Ummi tace kwarai ai irin su ba a banza suke barin gida ba sai sun kama bakin kowa sun daure yadda ba mai iya motsawa a kan su.
Sai lokacin mama tayi magana tace aini wanan yarinyar ta gama shereni wallahi tayi min daidai yanzu zata san in ta daure bakin wasu bata iya daure na wasu.
Nikan da muka shiga gida ya Amina tana daki mika mata sakon nayi a cikin wani dan leda wanda ban san abinda ke ciki ba dakina nakoma na fara rage kayan jikina.
Na mayar da dan riga mai karamin hannu da bujen body hook dana cire sai hula dana dora a kaina kitchen na nufa don dora abincin dare saboda yamma yayi.
Kafin wani lokaci har na kammala na gyara wurin na mayar da kauan da nayi aiki a inda suke daki na kofa nayi wanka kafin a kira sallah na fito na canza kayan jikina.
Kananan kaya na kara sawa a jikina don idan ina gida sune kayan sawa na wayata na jawo ina duba sakon dana samu daga abokaina da muke karatu dasu.
Lokacin sallah yayi na mike na gabatar da sallah ban daga ba sai da na yi har isha,i na nike abin sallah na fito din in ba yaran anty na abinci.
Anty ce ta fito daga dakin kwanan ta muryan ta naji daga baya na tana fadin har kin fito eh kawai nace mata ba tare da na juya ba ina zuba abincin a plate na mika ma yaran dake zaune suna jirana.
Juyowa nayi inda nake tsanmanin take zaune nace in zuba mata abincin yanzu ne kallo na naga tanayi cikin mamaki tambayan da ta jefo min a lokacin ban zaci ji ba.
Khadija may ya hada ki da buzuwa yau kin ko san waye buzu kin san ko matar waye don Allah ki rufa min asiri tunda nake unguwan nan ban taba fada da wani ko wata ba ina jin tsoron rashin tsoran nan naki wallahi.
Kara daure fuska nayi nace ina ruwa da wata buzuwa ko baturiya take ba zan yarda ta wullakantani ba ga banza don tana takama tana da kudi tunda ba kudin ta nace ta bani ba.
Don Allah dai ki bari ban son irin haka ni na dauka kin bar halin nan naki yanzu da kika girma ashe halin na nan baije ko ina ba.
Mijin ta fa na iya sakawa a kore mu a unguwan nan wallahi don suke fada aji yanzu a garin don Allah dai ki bari.
Kamar zan yi magana sai nayi shiru ranan banci abinci ba saboda haushin buzuwan nan dake ci min rai haka na kwana da tunane kala kala a raina.
Hajiya mama haka ranan itama ta kwana tana tunane a ranta kan yadda zatayi da danta akan buzuwan da ta zama masu fitina da masifa a cikin zuri,an su.
Dan ta ya zubar mata da mutunci da kimar da mutane ge gani nata duk a kan auren wanan matar da bata darajja mutane da halin ta.
Da safe nafito na hada breakfast har na gama ya Amina bata fito ba tana daki na gyara ko ina na gidan sai na koma na shiga wanka na fito na shirya tare da hayewa gado in dan huta.
Sai lokacin na fara jin hayaniyar su a falon gida alaman sun tashi ke nan daga barci hakan baisa na fito ba sai kara lafewa danayi saman gadon barci ne ke son dauka na a lokacin.
Muryan ya Amina naji na bude idona a hankali ina kallan ta daga inda nake kwance nake mata ina kwana murshi tayi ta karaso gare ni tana fadin.
Har kin gama kin kwanta yau barci ne ya dauke ni tana fadi tana kaiwa zaune a saman gadon da nake kwance jin banyi magana sai naji tayi murmushi .
Tace khadija fushi kike yi akan maganan da nayi maki jiya akan buzuwan nan bata da mutunci ne khadija shiyasa kowa ke tsoron shiga tsabganta don mijin ta zai iya keta ma kowa a kanta yadda yake son ta.
Dagowa nayi nace OK shike nan don mijin ta na da kudi ko mulki ba zanyi fada akan dama na na dan adam ba murmushi naji tasake yi tace khadija ina raba ki da shiga tsabgan irin mutanen nan.
Kai na kawar gefe ina hade miyau takaici da yazo min a lokacin haka abin yai ta cina har na gaji na sake na manta da wata can a zuciya.
Jin shiru da su Binta sukayi yasa su ranan biyo ni gida a falo suka samay mu dukkan mu nan muka zauna har anty muna hira suna min korafi wai kullun ina gida kumshe ban fita.
Zainab tace kodai kina tsoron haduwan ki da Nafisa ce nace waye Nafisa kuma tace matar yayan mu mana da kuka kwasa ranan .
Oh kuce mi buzuwa mana ai sai in gane ba Nafisa ashe sunan ta ke nan ni na fi gane ma buzuwa ai Binta tace ai bata son a kira da buzuwa shiya sunan ya mutu a bakin mu.
Ranan da ra kai kara wajen yayan a gidan bakiga irin fadan da yai muna ba ni tun lokacin gidan ya fita raina wallahi.
Ashe ya zama mijin buzuwa ke nan yar sani in fika wai agola da rabon gida ina kika san yar sani in fika ne ai sai kin ga yadda ta mayar da anty Fati a gidan.
Ita da mijin ta yanzu ta koma yar kallo a gidan ko dan aikin gidan yafi ta daraja a gidan kwanan fa sai da ta fito aka maida ita kin san may ?
Da ta koma bata gidan tana dawowa sai cewa tayi wai uban wa yace ta dawo gidan sai ta kama kitchen da komai tarufe na gidan ta hana ma anty Fati da yaranta.
Sai lokacin anty dake gefe ta saka baki a hiran da mukeyi a falon tace amma samun wurin nata yayi yawa wallahi nace wai wace anty fati kuke magana haka ?
Wanan da ta taba haihuwa har mukai fati daku a baya dan tunane nayi nace nagane ta itace mijin ta ya auri wanan matar wallahi itace inji Binta zainab dai sai dakilan wayanta takeyi tana charting.
Anty ce tace yanzun yaya akayi akan abincin nan dai take fada muna yadda suka kwashe da suraj anty ce ke dariya ni banga abin dariya ba tunda ba dukan ta naji yayi ba.
Sun kai wani lokaci suka ce zasu tafi na mike na dan taka masu har bakin get din gidan anty na na dawo ciki.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Yau ta tashi tana ta farin ciki maigida yace zai dawo garin sai abubuwan taron shi akayi ita da kawayen ta a gidan.
Fati bata san abinda ke wakana ba sai dai gani tayi mata da maza suna ta shige da fice a cikin gidan nasu wanda duk girman shi bai hana a jiyo ihun da suke yi ba a lokacin wai duk cikin murna ne hakan.
Hajiya ce ta aiko gidan a tambayi Fati mai ke faruwa ne gidan nasu amce anga mutane na ta shige da fice a gidan.
Fati tace itama ba ta sani ba itama dai haka ta gani suna shiga suna fita kawai a gidan amma bari ta tambayi laraba taji ko ta sani zuwa tayi ta kira Laraba take tambayan ta abinda ke faruwa tace wai maigidan ne zai dawo shine ake shirin taron shi.
Mamaki Fati taji a lokacin tace yanzu dawowan na yaya Abdul shine shine akewa wanan hiddimar haka ikon Allah ikon gaskiya.
Hajiya mama ma da taji fada tai tayi tana zage zage sai da hajiya ummi da mommy suka ce ta sa masu ido ga duk abinda take yi wani abin saboda neman baki take yin shi.
Ran hajiya ya baci sosai daki ta shige saboda bata son yawan surutu abin kunya abin takaici wai dan da ta haifa da cikin ta a gaban idon su tantirai ke wanan wasan a gidan shi.
Yau ina tarbiyan da tai mai a matsayin dan ta na fari a matsayin shi na jikokin malaimai bu sanadin mace ya samu raini a rayuwan shi macen ma shu,umar mace da tafito yawon barki.
Muryan mommy ya katse ma mama tunane tace nazo ne in ji haka zamu kyale Fati ita kadai a cikin tantiran matan nan.
Mama ta nisa tace may zanyi hajiya karima mommy tace ni a gani na yaran nan suje suma su zauna a dakin Fati din kin ga ko suna da niyar mata wani abinda ba daidai ganin idon su zai sa su fasa.
Abinda kuka yi shawara akai sai ayi ni banda abincewa don wanan yaron ya gama bada tako ina mommy tace kada kice haka yaya kowa yasan ba halin shi bane juya shi akayi ya koma haka.
Murmushin takaici mama tayi tace haka dai kuke cewa amma har da raayi kin san shi tun farko da son farar mace ai doguwa.
Shine dai abinda ke rudin dan naki kawai ba wani asiri wallahi yaya mudai bishi sannu har a samu ma fita yaran ta kwala ma kira duk suka hadu nan take fada masu tana son su shirya gobe idan yayan su zai dawo su je su zauna da Fati a part din ta sai ta sake cewa ina ganin zamu biku ni da antyn ku amarya zan buga waya sauran uan uwanku suzo ba zata zamuyi mata kamar yadda tai muna bazata itama bata fada wa kowa da shafe shi ba.
Nan dai suka taru sukai ta shawaran abinda zasu yi bada sanin buzuwa ba don su rama abinda take shirin masu din na iza masu takaici ta nuna masu su ba kowa suke gare shi ba yanzu.
Muna falon antyna zaune karatu muke da yaranta ita kuma tana duba littafinta na islamiya don tana hadda a wata makarantar matan aure dake unguwar su.
Wayan ta ne yai kara tace dan ta dake kusa da wayan ya miko mata jin ta ce hajiya karima mun wuni lafiya yasa na gane da mommy take waya don aminiyar ta ne sosai mama kuma a uwa ta dauke ta a gidan tafi shiri dasu su biyun.
Bandai ji may suke fadi ba bayan gaisuwa da sukayi sai ji nayi antyna tana fadin kwarai kuwa hakan yana da kyau sosai mommy in Allah ya yarda goben zan shigo dani da khadi tunda tana nan sai muzo a cika taro da mu muma.
Dagowa nayi na kalli antyn nawa don jin abinda tace bayan sun gama waya ne take ce min ikon Allah wai dan gidan hajiya mama ne ya samu karin girma bai fadawa yan uwan shi ba sai gani sukayi matar shi tana ta shirin buki ita da kawayen ta.
Haushi naji a raina nace shiya sani mana duk wanda ya wullakanta iyayyen shi ai kan shi yai wa wasu ma suna can suna neman iyayyen ido rufe basu samu ba.
Shi ya samu Allah ya bar mashi nasa a raye shine zai wullakanta su antyna tace ai shi na gani nima wallahi.
Shi fa dama haka yake kamar mai tsoron mutane yake hadewa da buzuwan nan da yayi sai abin ya kara bulakucewa mai.
Yanzu hajiya karima ta kirani ne tana fada min wai gobe tana gayyatan mu zuwa gidan nashi don suma zasuyi nasu taron a part din Fati.
Kai amma suma dai basu da zuciya wallahi akan may ba zasu saka mashi ido suga iya gudun su ba ai mutum baiyi sai da nasa.
Ni dai ba zan je sai kun dawo don babu komai wurin nan sai tarin takaici tace a a don may bazaki ba ba gaiyyatan mu sukayi ba muje mu mara masu baya a cika taro da mu muma.
Ban iya bata amsa ba sai ma cewa da nayi da yaron ta kana jina ko muci gaba da karatun mu dajin wanan abin takaicin.
Duk abinda muke sai na gaza yi sai cewa nayi da ita wai mashi wani irin mutum ne haka wai tace ai zaki ganshi gobe idan munje gidan.
Washe gari ko da wuri anty tasa muyi aiyukan da muka saba a gida muka gama komai akan lokaci.
Tace mu shirya zuwa karfe uku mushiga gidan su mommy din raina bai so ba haka na shirya dole cikin wani buje dariga na atampha da nayi dinki shi a abuja atamphan pink ce don haka shirgan pink colour nayi na ni kaina nasan kayan sun karbe sosai don sun fitar min da sura na fili.
Muka fito muka rufe gidan muka nufi gidan da kafa saboda ba nisa sosai abin mamaki sai samu mukayi duk yan uwa da abokan arziki sun hadu a family house din nasu.
Mun dan shiga dakin mommy ita kirjin abin nikan ganin duk matan aure ne a ciki yasa naja yaran anty muka wuce dakin mama wurin su zainab.
Ba wasu mutane a dakin sosai sai ita da yaran ta kuma da alama kamar wani magana mai muhiamci suke a lokacin sai naji na tsargu ga yadda na gansu din a lokacin saboda kar na takura masu dana gaida su sai na mike zan fice daga dakin.
Muryan mama din naji tana cewa a a dawo abinki ki zauna ai ba wani magana muke yi ba cikin muryana da yake kamar sallo da yanga nace No bari kawai na tafi daga waje ai.
Binta ne ta fito daga cikin daki tace muryan ki naji yasa ni fitowa yanzu wai rangas wanan irin kwalliya haka ai sai ki sa kallo ya koma kan ki.
Guntun murmushi nayi nace da ita silly girl ina zainab ashe tana kusa da mama zaune saboda cika min ido da sukayi ne banganta ba tace gani nan bakiji ina cewa khady ba da kika shigo.
Binta ne tace mu shiga daga ciki mu zauna sai maman tace a a tazo nan ta zauna abinta ki sakata ciki kamar kunshi matsa min take yi wai nazo na zauna a kusa da ita ban hau kujeran ba sai na zauna a kasa kusa da kafafuwan ta.
Ina zama tace da yaranta masu aure mutum biyu kun ganta nan ranan ta burge ni da ta tsaya taci wa yar iskan yarinyar nan mutunci ido rufe akan titi taso ta kawo masu rainin hankali a saman hanya ita ko ta wanke ta tas wallahi.
Anti fauziya tace kin min daidai wallahi dama ai ganin ana daga mata kafa ne yasa takewa mutane iskanci wai ita a dole matar mai kudi.
Nan dai suke ta maganganun su a wurin kamar daga sama muke jiyo haya niya wata ta leko tana fadin ga yaya Abdul nan ya iso kuma nan ya fara shigowa.
Fita suka kama yi a raina nace ashe shiyasa yake maku abinda yaga dama saboda hakan da kuke mai nidai ina zaune a kusa da hajiyan tasu.
Ganin yaran nata sun fita yasa ta mayar da hankalin ta a kaina tana fadin dada dai yanzu khadija gudun mu kikeyi baki ko son shigowa gidan nan in kin zo na dan yi murmushi nace no mama ba haka na bane kawai dai daurowa ne.
Nan take dan jana da hira cikin rashin sakin jiki nake dan bata amsa a hankali ganin dandazon mutane sun nufo dakin nata ne yasa na mike zan bar wurin tace dani koma ki zauna abinki yanzu fita zasuyi idan mun gaisa.
Wani farin mutum ne ya dumfaro kofan zai shigo kamshin turaren shi kawai ya isa ka dago kai kaga ko waye maishi nan dandazon yan uwa suka dare a kofan dashi da wani suka shigo dakin kawai ba wanda ya shigo bayan su sai ni da mama da yaron anty na da muke zaune a dakin a lokacin.
Mayar da hankali na na nayi ga wayana dake hannu na a lokacin ban daga na kallesu ba suka zube kasa suna gaida mama din cikin girmamawa.
Tace dashi bayan sun gaisa ashe kana tafe baka fadawa kowa ba harda samun abin arzikin da kayi bamu kai girman da zaka sanar damu hakan ba a yanzu sai dai muji ga shanun talla ana fadin wai ka samu karin girma a ma aikatar ku.
Yace ba hakkana bane mama bari nayi sai nazo in fada maku dama ashe ma kun riga da kunji abinda ba a ko rantsar dani ba tukun .
Daidai lokacin na dago kai cikin jin haushi na watsa mashi wani irin harara ban sani ba ashe idon shi yana kaina a lokacin cikin rashin sani na nayi saurin dukar da kainanajigina da kujeran da mamake zaune tare da mayar da kaina ga wayana da nake duba.
Wanan wata yarinyace haka miskila har da zata iya hararana da nuna min ko in kula yace a ranshi in dai zaka sake hali wallahi kasake mudin dai mune iyayyen ka ba wasu ba.
Yanzu ka duba fadin gidan nan kaf yan uwa ne da abokan arziki da mommyn ku ta gaiyato suka zo don ka idan ba a zumunci waza ka gani a nan yanzu kai hakan ma da sukai maka bakaji dadin shi ba.
Ace mutum babu nashi wanda ya ja a jiki sai dai yan duniya masu maka rudi da duniya kaina na kada alaman fada mashi dai mama na tabe baki na.
Wayana ne yai kara a lokacin baba nane ya kirani da sauri na dauka cikin kashe murya nace daddy yau kaji ban kiraku ba ka kirani yanzu nake son kiran ka a yanda nake magana da mahaifina cikin sakewa da walwala kamar ina magana da wani sa a na sai mutum ya saurara zai iya jina don kada in damay su in hana su maganan da suke yi din.
Muryan su naji yana fadin mama zan shiga gida in huta don ban isa can ba nan na fara shigowa in gaida ku.
Har lokacin yanayin ta ba dadi Allah ya sauwaka naji ta fada masu tace Yusuf ashe kuna tare yusuf din da ya dukar da kan shi tunda mama ta fara mai fada sai a lokacin yayi magana yace eh mama tun da ya bugo min zai dawo ai naje abujan taron shi.
Mikewa sukayi zasu bar dakin tace kaji an mayar da Fati dakin ta ko hakan yasa shi tsaya yace naji mama.
Wani sabon hararan na dago in aika mai still muka kara hada ido yasha toka a lokacin yace zamu tafi Allah ya tsare ta kara maimaita mai suka fita dakin.
Ajiyan zuciya na sauke bayan fitan su mama din tace kin ga yayan ku ko yau khadija nasan kila baki san shi ba.
Murmushi kawai nayi mata nan sauran diyan suka shigo suna fadin su mommy sun fita ance gidan ya cika da mutanen Nafisa don haka mu zamu wuce can.
Kafin ya gama ganawa da baba su zainab suka fito suka ce in tashi mu tafi Allah ya gani da zasu bar ni in zauna wurin mama da zai fi mun dadi don ban son hayaniya da yawa ga matar gidan da mai gidan da nake kule dasu a raina.
Ganin mota zamu shiga yasa na dauka gidan yana da nisa sosai ashe ma ba wani nisa muna shiga mata yan duniya ne birjit a farfajiyan gidan zazaune saman kujeru farare sai kidan dj dake tashi kamar wani buki akeyi mai muhinmanci a gidan.
A raina nace kudin banza a bazan suke tafiya mommy na gaba ita da anty amarya muna biye da yawan mu a bayan ta muka shige gidan.
Nan naga duniya a cikin gidan sai kace ba a garin kaduna muke ba part din Gatin muka shiga a sama suke dukan su mun samu tayi kwalliyanta ba laifi nikan a nan falon ta na zauna zainab ma da namu yazo daya sai ta zauna a wurin.
Anan wasu suka zauna basu shiga dakin ta ba su anty na kan an shige daki nace magulmata a raina jefi jefi muke hira da zainab muna dan dariya .
Sai gasu sun fito suka ce a sauka kasa a falon kasa zamu jira shi koda muka fito ba kowa a falon sai zuwa can Nafisa da mutanen ta suka fito cikin mamakin ganin yan uwan shi da na Fati wanda bata zaci haka ba yasata daure fuska atake ta nuna kinshin ta karara a wurin.
Gashi kuma har ya iso gida a lokacin nan su mommy suka ja Fatin zuwa taron shi daidai kofan shigowa falon gidan mai dan karen girma da tsaruwa.
Duk abinda su mommy suka ce tayi shi tayi a wurin aka dauki ihu da tafin yan uwa itama tazo da nata tawagan sukayi iskancin su da sowace sowace irin na yan duniyan mata shiko yana wani washe baki yana runguman matan nashi.
Ranan dai naga kishi kara don buzuwa a gaban kowa ta kwace hannun mijin su daga gefen Fati din ta rungumay shi ita kadai.
Juyawa nayi wurin zainab nace wanan tsohuwar may take nufi ne haka wai tsuhuwar da nace yaba sauran yan matan da muke tare dariya duk aka kwashe da dariya.
Ido rufe ta kallo mu tana rugumay dashi a jikin ta kamar wani soko sai lumshe ido yake yi tace kada ku kawo min iskaci a gida na don ban gaiyace ku ba.
Ai ba gaiyyan ki muka zo ba mu wane mu da gaiyan ki kin ga mun yi maki kama da mutanen banza ne duk wurin akayi tsit ana kallon mu .
Wai wanan yarinyar yar gidan uban waye a garin nan nace yar gidan ubanki ne a garin nan tsaye kowa yayi yana kallon mu ta fara fisge fisge wai zata zo ta dake ni a wurin .
Ko dar banji ba na ce da turanci too hell with you wallahi don ba don ki muka zo gida idan kikayi gigin tabani yau sai kin raina kanki wallahi .
Anty Fauziya tazo ta jani da mommy suka hau sama dani shi kuma sai cewa yake ta bari bai son fitina ita fa ta tara mutane tace ba gaiyyaci kowa naka ba don nasan halin su ba sona sukeyi ba.
Saman yabi da kallon mamaki yadda karama dani na iya tsayawa a gaban su nayi wa yar lalai matar shi tas na barta nan tana hargowa.
Anty na duk ta tsure sai fadi take ku bari mu tafi gida khady dama nasan halin ta bata daukan wulakanci tun tana karama.
Kowa a wurin fadin albarkacin baki shi yake yi mun dade a dakin kagin mu fito zuwa gida muka bar wasu anan sai da su Binta sun fito tare damu sai nuna ni abokanta sukeyi da muka fito.
Niko ko a jikina don ban damu ba ban biya gidan su ba gida muka wuce mommy taba anty wani leda dake da kaya a ciki ni har nayi gaba a lokacin har muka kai gida ba wanda yayi magana a cikin mu.
Sai bayan mun yi sallah magariba da ishai muka fito falon har lokacin ban sake ba raina a bace yake da abinda ya faru dani.
Zaman mu shigowan su zainab da Binta da Amira suna shigowa suka saka dariya gaba dayan su anty tace dasu yau ai ni naga abin mamaki gun khady mata da gidan ta ki ce zaki fadan karfin hali.
Nace anty wallahi ko ba yau ba wanan matar tai min ramawa zan yi haka kawai zan tsaya tana zagina akan may wata tafi asali.
Ni dai don Allah ki rufa min asiri a garin mutane khady ki koma gida lafiya wanan abin da may yayi kama Binta tace anty mu ai tayi muna daidai wallahi.
Baba ma da yaji cewa yayi wai waye khadija din nan har cewa yayi a kiraki mukace kin tafi gida.
Anty tace kinji ko wallahi khadija ki rage wanan girman kan naki don ba zai kaiki ko ina ba wallahi tace ai bayan dawowan mu ayin fitina sosai a gidan dasu anty Fauziya da suka tsaya suma sai da akai rashin mutunci dasu yau.
Wuri ta samu mana shiyasa takewa mutane rashin mutunci son ranta inji zainab ai yau naji mamaki da bai biye mata ba da dane ai rama mata zaiyi.
Sai lokacin nayi magana nace ashe na manajo ne yayan naku cabdi dako yau yaji magana wallahi binta tace da zaki iya ramawa nace mai zai hana iyaka dai yasa a kama ni ko zainab tace wane shi.
[10/12, 3:46 PM] Khadeejah🥰: A raina sai mamaki nake wai wanan matashin da nagani wanda bai wuce ace yanzu zaiyi auren farko ba ke da mata har biyu haka.
Buzuwan nan dai da za a zauna a fadi gaskiya tana iya girmay mashi daga shi har matar shi sai idan ance yanayin jikin su kawai da ba a gane hakan.
Ita kuma Fatin baka ce sai dai da zata zauna ta gyara jikin ta banga abinda buzuwan nan zata gwada mata ba sai dai kasshh yanayi irin namu na matan hausawa yana cin rayuwan ta da haka nake hango buzuwa ta kwace mata miji .
Yau da gobe sai Allah dama sati uku zanyi don hutun ba yawa shiyasa ban so zuwa kaduna ba a wanan lokacin amma anty na ta dage sai nazo ita kadai ne a gida mijin ta yayi tafiya.
Ashe kuma da rabon mu kwasa da matar mulki ne a garin ya kawoni don haka shiri nake inda ba komai nake shiryawa sai kayana don ban daukan provition da ga gida sai na tafi can nake saya.
School zan wuce direct sai nakwana biyu zan shigo mina in masu weekend in kwashi abinda na samu in koma bayan kwana biyu don haka nake ta shirin komawa makaranta a lokacin.
Kwatsan da safe muna karyawa saura kwana biyu tafiyana sai ga wayan mommy ta bugo ma anty wai Fati ta dawo gida yanzu haka tana nan gidan su naji anty na fadin o o Allah yanzu matan nan da karfi da yaji sai ta raba wanan auren take nufi.
Banji may mommy ta fada mata ba nadaiji tana fadin gaskiya haka nane idan abu yaki sai ayi hakkuri kada zumunci ya baci idan abin ya sake shi inda rabon komawan ta gidan sai ta koma.
Bayan ta kashe waya tace mummy tace ki shiga kafin ki wuce kada ki tafi baki sallamay su ba nace haba anty may yasa kika fada mata zan wuce ai sai yazama kamar roko idan naje sallaman su.
Kai ta girgiza min tace ba haka halin su yake ba dauka na sukeyi kamar wata ta gida a gurin du duk zuwa kikayi kika wuce sai sunyi min korafin hakan.
Shiru nayi sai tace o Allah sarki wanan buzuwan dai ta hana Fati zama gidan mijin wai yanzu kuma ta kara fitowa tace bazata koma ba.
Dudufa baifi wata da ta koma gidan na yanzun kuma ta kara fitowa jiya wai sai dai na shiga inji may kuma ya hadasu fada yanzu.
Takaici bai barni nayi magana ba sai dai a zuciyana nake bankawa mijin zagi da rana su binta suka shigo gidan mu anan muke jin labari wai tunda ya dawo buzuwa taki bari ya ke be da fati hakan bai isheta taja Fatin da fada har tana fadin sai ta kashe ta.
Shiya ba Fati tsoro tace barin gidan yafi mata nace shike nan ta samu galabanta ai ta kashe ta din idan ta isa mana.
Gaskiya matan nan ta samu wuri da yawa wallahi nace shiko sokon yayan naku fa may yayi a kai tace jiya baban mu ya kirashi sai cewa yayi shi yagaji da halin fati tana bata mashi suna.
Ai wallahi idan da nice tace sai ta kashe ni da na nuna mata hauka ke matsorata ne fa iskancin abaki yake masu kawai Fatin dai ne wallahi she is to slow .
Anty tace khadija baki san aure ba fa shi wanda ake abin a kansa bai nuna wani feeling din shi akan ta gara dai da ta hakkura ta basu wuri.
Zata tafi nace barin bisu daganan in masu mommy sallama tun ranan da mukai fada da buzuwa ban sake shiga sai yau da zan tafi sallaman su da anty ta matsa min.
Tsab na shirya na fito cikin wani dogon riga mai hannu shara shara shara da gyalen shi na yafa akaina sai turaren da na fesa a jikina.
Mun shiga gida inda na fara zuwa dakin mama na gaida ita sai na fito naga anty amarya a waje anan na gaida ita har zan wuce tace khadija ashe haka kike ina ganin ki shuru shiru dake ashe ke ma jaruma ce ban sani ba.
Dan guntun murmushi nayi nayi kasa da kaina kawai dakin mama na nufa ina jin suna maganan a waje da mai masu aiki na shige wurin mama in gaida ita.
Tana zaune a falon ta tana waya haka yasa na samu wuri a kasa gefeta na zauna ta gama wayan ta dago kai cikin fara a tana fadin yau khadija ne gidan nace mama ina kwana.
Ta amsa min fuska a sake nace mama nazo in sallamay ku gobe zan koma school tace a a har hutun ya kare wanan karon nace eh mama.
Ta sake cewa gida zaki ko Abujan zaki wuce aa zan wuce school ne daga nan tace barin baki tsaraban yan makaranta ko nace mama da ki barshi ai ba zan dauki kaya daga nan ba sai naje can saya.
Tace a a wanan kan zaki so dambu ne da akai ma yayan zai tafi dashi kin san yana son dambun nama sosai shine na aikai mashi shima gobe zasu tafi.
Ta mike ta shiga daga ciki sai gata da roba dan madaidaici ta fito da kudi a hannun ta ta miko min nayi godiya namike zan fita ko ba a fada ba yanzu na sheda wanan kamshi ba kowa bane sai dan ta Abdulsamad mijin buzuwa.
Zai shigo ni kuma zan fita ban yi tunanen in kauce mashi ba a lokacin dole suka jaye a hanyan na fita ashe da buzuwa suke tana bayan shi.
Mama ce naji ta kwala min kira sai na dawo wanan karon sai da na bari sun gama shiga na shiga dakin nima na karasa wurin ta gwiwa na biyu a kasa na zube ina fadin mama gani.
Buzuwa ke gaida ita ta tsaya amsawa ta dago tana cewa dan ta gobe ne zaku tafi din ko yace insha Allahu mama yanzu ma mun zo mu sallama ku ne don goben sakko muke son yi dan zan shiga office.
Ta juya gare ni tana fadin gobe sai ki shirya su tafi dake indan zasu wuce gaba na ya ba da damm da sauri nace a a mama ba tafiyan safe zanyi ba ni.
Khadija yayan ku ne fa ki shirya ki bishi yafi shiga motar kasuwa su wuce da ke shidai baiyi magana ba ya rike goshin shin da hannu guda .
Sai buzuwa ne tace motar tamu ai a cike take dayan ni dashi ne sai driver dayan kuma na masu aiki mun ne su larba sai na security din mu .
Naku zata shiga don ita din ba bare bace yar gida ne kaji na fada maka tau mama yace ta shirya da safe din kada ta makara sukuku na mike tare da fadin mama na gode.
Fitana dakin mommy na tafi ina nuna mata abinda hajiya mama ta bani tace ai yaya tafi danan ban fada mata zancen bin mijin buzuwa da tace in yi ba a lokacin itama daki ta shiga sai gata ta fito min da wani bakin dogon riga da takalma cikin na sayarwanta tace ga wanan a samu na sakawa.
Binta ce ta shigo dakin tana dariya mommy tace maynene kuma tace khady nakewa dariya mommy mama tace da yaya gobe su tafi da ita.
Ga buzuwa can tana fada bayan fitar mama daki wai bata yarda ba bata san mama ta jita ba shine mama ta fito tana fadin har ta isa tace ga abinda take so tace ita bata yarda ba yaya ce shi baice ba zata bisu ba ai.
Juyowa mommy tayi ta kalle ni nace nifa ban iya bin su gaskiya don idan tayi min wallahi nima yi mata zanyi gara ko kada in bisu din.
Dariya take min mommy tace akan may kin samu sauki bazaki bisu ba ai shi Abdulsamad baida hakana tunda har yaya tayi mai magana da bai daukan ki tun a nan zaiyi magana balle yanzu da yasan yaya tana hake dashi ai ba zai so ya bata mata rai ba kuma.
Daga cikin dakin mommy anty Fatine ta fito tana saye da wani hijjab har kasa fuskan ta duk ya kode alaman tasha kuka har ta gaji.
Gaida ita nayi ta amsa kasa kasa ta zauna a daya daga cikin kujerun falon mommy tace kin tashi tace eh mommy tace ga mutanen ki can sun shigo sallaman mu zasu koma gobe wai.
Shiru tayi batayi magana ba sai mommy ta kara cewa kin san yaya da son jan magana wai cewa tayi gobe su wuce da khadija da zata koma makaranta goben.
Wai ai ba zata bari ba wallahi bata son kowa ya rabe shi balle wanan da take gani mace haka maikyau kuma gasu da wata a kasa daman.
Aiko banyi niyan binsu ba da amma yanzu sai na bisu tunda abin haka inga yadda zatayi a motan dani idan na shiga.
Murmshi mommy tayi tace ki shirya da wuri don shi da wuri yake tafiyan shi idan zai tafi tashi nayi nayiwa mommy sallama muka fita da binta ta rakani.
Naje gida na nuna ma ya Amina tsaraban da suka bani don da zanfito anty amarya taji zan wuce ta dauko min wani set din turare mai kamshi ummi ce bata ban komai ba a cikin su.
Sai can muna hira nace ya Amina kinsan wai mama cewa tayi in shirya gobe in bi mijin buzuwa da buzuwa idan zasu koma.
Da sauri tace may ne ?
Nace wallahi da banyi niyan binsu ba amma tunda ta nuna bata son haka zan bisu din inga yadda zatayi dani a hanya .
Nidai wanan zuwan wai damay yazo muna haka ne da tarihin buzuwa ko damay yanzu ke binsu din zakiyi, ba zaki hakkura kibi motar kasuwa ba.
Don mama ne kawai zan bisu kada in bata kunya tunda tana sin gwada masu ikon ta ne a kan su da kuma ita buzuwan zantafi.
Da yamma sosai na fito zan shiga gari in karbo dinkina da nakai ina fitowa bakin get sai ga motan shi tundaga nisa na kawar da kaina don ban san wanda ke cikin motar ba sun kawo kusa dani na gane su ne na watsa mai harara na kawar dakai.
Yusuf wacece wanan yarinyar wai da nake gani a gurin mama yarinyar bata da kunya ko yanzu baka ga wanj harara da ta watsa muna ba kullun shi take min fa har a falon mama da muke haduwa.
Dariya Yusuf din yayi yace amma kuma tana da kyau gaskiya koda yake kai yanzu baka ganin kyaun mace gaka da buzuwa a gidan ka.
Wai Yusuf may ya kawo wanan magana haka daga tambayan ka yarinya idan baka santaba kace kawai baka santa ba period.
Dariya Yusuf din yayi yace kai ke nan da anga mace mai kyau kace kada ayi magana wallahi yarinyar ta hadu sosai shiya take da jan aji da yawa.
Nafisa fa tayiwa rashin kunya a gida na ka sani kuma kake wanan magana yace a a suka dai yiwa juna ta zage ta ta rama don uba baifi uba ba.
Matsalan Nafisa tace kowa zata juya don tana takama mijin ta na da kudi kaji dai abinda yarinyar tace mata ai batazo roko wurin ku ba zumunci ya kawo ta.
So tayi ka kama mata kuyi wa yar mutane cin mutunci a banza.
Yace ai don na ganta a wurin mama ne yasa na kyale ta amma da ba zan yarda ta shigo min gida tayi min tujara ba for what ?
Matar ka ce yar cin mutunci ai ya furzo iska daga bakin shi yace matsalan ta ke nan wallahi cikin ina tsawata mata ta bari ke nan ma.
Yanzu dai kun kori Fati kun huta tabar maku gidan yace ta dai kori kanta amma ni ban kore ta ba ai ban san irin Fati ba wallahi .
Bandai san irin ka ba malam buzuwa ta hanaka ka ba Fati da yara hakkin su kai kuma ka biye mata ranan fa a gaban kowa ta banbare hannun Fati a jikin ka kuma ka yarda.
Wallahi idan zakai ma kan ka fada kayi tun baka makara ba kana ganin su Affan idan suka girma sukaga kanawa uwar su haka zakaji dadin su ne.
Kai wa kan ka fada wallahi akan buzuwan nan kada ka tashi ranan lahira da bari shayaye .
Bugu yakai ma abokin nashi yace Allah man abinda akace yana samun masu karkata gin mace daya ke nan na fada ma tun farko ban yarda da ita ba yanzu kaji abinda hajiya ta fada muna ranan.
Nisawa yayi yace ai Fati ta riga da ta hadani dasu har baba fushi yake dani a gidan da sauran yan uwa.
Yusuf yace buzuwan ka kuma tana jin dadi ba ta kori yar masu gida an bar mata gida tana yadda take so ita kadai tayi hankali wallahi da iyayyen nan namu.
Shiru yayi yana nazarin maganan abokin nashi baice komai ba san cen yace kasan hajiya don jan magana cewa tayi gobe da wanan yarinyar zamuyi tafiya.
Ina Yusuf ya tambaya da sauri yace wai Abuja zamu tafi a can take tace nowarder idon ta yake a bude haka bata da tsoro da ganin ta ai.
Na karbo dinki na dawo na shirya kaya na bayan na gama komai na zauna ina tunanen yadda tafiyan mu zai kaya a goben.
Ya Amina ta ban abinda zata bani taja min kunne don Allah kada in kula buzuwa har mu isa nace ni ina ruwana da ita su dai kaini su sauke kawai.
Da safe ya Amina ta tana dani da wuri na shirya jiran kawai nake ace in fito mu tafi ya Amina tace in dauki jakkana da sauran kayana inje dasu gidan su mommy nace ai wanan ya zama tonon asiri haka .
Ni madai su wuce idan haka ne dole ta kyaleni don ba yadda zatayi dani na gama komai har da karyawa ya Amina ta sani yi da safe don tafiyan da zamuyi din.
Can sai ga su Binta sun shigo wai in fito da kayana ga su buzuwa nan sun fito suna ciki suna sallaman su mama zasu biyo nan su dauke ni inji mama.
Tashi nayi na fara fito da kaya na waje suna tayani fitarwa kofan gida sai ko ga motan su ya tsaya suna baya dashi da buzuwa gaba zan zauna dani da driver su.
Ina jin ya Amina tana gaida su binta ta bude min na shiga duk da kamshin turen su amma nawa ya karade motar har na shiga na zauna ban yi masu magana ba ina daga wa su ya Amina hannu muka tafi.
Tsayawa sukayi suna bin motar da kallo Binta tace yau akwai tafiya a wurin nan jifa yadda anty Nafisa ke cika tana batsewa kamar ta fashe.
Zainab tace suna daidai da khady ai ta fita iskanci daidai zasuyi a motar niko saida aka fara tafiya na dan juyo nace dasu ina kwanan ku murya can ciki bai fita.
Ina kokarin cire airpies dina na sa a kunnuwa na tare da sake kira, a a wayan na lumshe idanuwa a hankali ban kara bi ta kansu ba kuma.
Tun ina bi sai dan barci ya dauke ni ina yi ina falkawa na gyara zama tare da dan satan kallon su ta karkashin idanuna na naga yadda suka zauna manne da junan su sai dai aiki yake a laptop din shi.
Ita kuma tana gyangyadi daga zaune da yake lafiyayun motoci ne kafin wani lokacin har mun kusa isa Abuja driver yaiwa magana yatambaye ni ina za a sauke ni .
Ya juyo idanuwa suna lumshe ya dan taba sit din na bude ido tare da cire airpies din dake a kunne na yace yallabai yace a ina za a sauke ki ne ?
A hostel nake zaune na bashi amsa ya juya gun ogan nashi yana fadamai abinda nace mai bai kara magana ba har muka shiga gari.
Ban ankara ba sai naga suna shiga jerin gidajen dake asorock a wani gida motar ta danna kai suka shiga katon gida ne mai wani babban get ginin gidan sai mutum yace a turai yake sai lokacin na cire airpies din kunne na naji buzuwa na fadin ita a ina za a sauke ta banji may mijin ya fada mata ba nidai ban fita motar ba su kuma sun shige ko godiya ban masu ba.
Driver ya shiga masu da kaya ciki ni dai sai bin gidan nake da kallo a raina nace shiyasa yake abinda ya ga dama ashe yasan abinda ya taka,
Ga wasu manyan motoci gudu uku a fake wata katuwar jeep ta dauke min hankali har ina satan kallon ta a wurin motar sai sheki take tana daukan ido da gabin ta sabuwace.
Sai dai ga daular duniya matashi dashi amma ya kasa auren yar kasamu suci arziki a tare sai wata bare ce buzaye ne gidan naga suna fitowa daganin su kasan yan uwan buzuwa ce ba sai an fadi ba nace mijin hausa ke nan inwar giginya na nisa ka more ka.
Driver ne ya fito tare da wani dan saurayi buzu a baya shi yana dauke da tire da drinks yace gashi mai gida yace a kawo maki No na gode na fada tare da juyawa da kaina gefe a can cikin gida kuwa fitina na tsakanin buzuwa da mijin ta.
Wai sai dai in shiga motar haya akaini hostel bata yarda ya wuce su sauke ni ba dole yasa driver yakai ni sai ya dawo ya kai shi office daga baya.
Mun kama hanya driver ke cewa kai matar oga akwai kishi yanzun haka ta rike shine ciki wai bata yarda ya fito atafi kai ki dashi ba.
Murmushi nayi nace mahaukaciyar banza kawai itake nata haukan ni ko a jikina yace nayi mamakin yadda ta yarda aka dauki ai nasan shi take ma fushi har muka zo ba shiri a tsakanin su.
Surutun nashi ya isheni don haka nakawar da kaina gefe kamar ina kallon titi don abokin gulma yake nema da alama ganin na kyale shi shima yaja bakin kishi yai shiru har muka isa gidan da nake ba a cikin hostel sai dai gidane na haya da yan makaranta ke kamawa.
Driver shi ya taimaka min da kayana har zuwa bakin gidan namu ya shiga min dasu sai dai bai shiga ciki ba kudi ya miko min yace gashi oga yace idan na sauke ki in baki.
Dan jimm nayi kamar bazan karba ba sai dai nasa hannu na karba tare da fadin kace nagode sai dai ban faye karban irin kyautar nan ba kallo na yayi ganin na fara jan trolley dina yasa shi wuce yana mamaki na a ran shi.
Dakina na bude wanda mijin ya Amina ne ya kama min hanyan shi dakine ciki da falo da bandaki a cikin sa sai inda mutum zai danyi girki daga waje haka dakunan suka a jere har dari da wani abu.
Dakin yayi kura dan sati biyar din da nayi ban ciki daga kofa na aje kayan da na dawo dashi na fara gyara dakin tukun sai da na sharo ko ina na dakin.
Na mayar da komai yadda nake son shi na fito ba zan iya fita ba haka yasa na kwanta don in sauke gajiyan dake jiki na a lokacin.
Ba wanda yasan na dawo do haka na rufe kofa na kwanta abina sai barci mai nauyi ya dauke ni a cikin barci sai gashi wai muyi mumunan fada da buzuwa mijin kuma na tsaye yana kallon mu baiyi magana ba.
Falkawa nayi don kiran wayana da akeyi na lalubu wayan da kyat saboda barci da yaci idona ya Amina takirani.
Ina dauka naji muryanta tana cewa ina kika shiga ne haka waya nata kara baki dauka ba cikin muryan mai barci nace wallahi barci nakeyi anty.
Tace yaya kuka sauka shine koki kirani hankalina ya kwanta nace wallahi lafiya kalau muka sauka tace badai wani matsala ko ke da buzuwan ki ?
Naja guntun tsaki nace suna can gidan su muka sauke su driver su ya kawo ni hostel ni komai bai hada mu ba a motan bayan gaisuwa.
Tace to barin barki ki huta an jima zan kira son naga yanzu barci yaci karfin ki nace ai na tashi yunwa ma nake ji yanzu tace to ki samu abinda kikaci kin san kina da ulcer nace yanzu zan tashi.
Baki sayo komai ba ma ke nan nace yau na gaji ne anty ba zan iya zuwa ko ina ba sai dai gobe idan na fito lecture.
Allah yakai mu tace muka kashe waya ina jin dadin yar uwa ta sosai saboda kulawan da take bani na musanman shiyasa nima nake mata komai kamar ita ta haife ni.
Mafalkin da nayi ne ya fado min a raina lokaci guda yake dawo min dan dariya nayi nace ikon Allah wanan buzuwar kamar manya ta tsaya min a rai haka ?
Sai a lokacin kudin da driver nan ya bani ya fado min a rai na jawo jakka na daga kwance na kirga kudin ido na zaro ganin har dubu hamsi ya bani nace wanan yasan zafin kudi kuwa ?
ZAINAB IDRIS MAKWA
SEENABU
Bai yi mamaki shigowa ya samu abinda ya gani ba a gidan don ba yau bane farkon yin haka gare ta don a duk lokacin da ta ganshi ya rabi wata mace ba aita ba ko kannen sa da suke uwa daya ko uba daya ba hakan take mashi wannan haukan a gida.
Don sani yadda suka rabu da ita kafin yaje office akan kawai mahaifiyar shi ta bashi umurni ya bi na su rage min hanya zuwa abuja kuma a motar shigan su.
A hankali ya kusa kai cikin falon su na sama ga tarin gajiya a jikin shi daya kwaso yau ga na tafiyan da sukayi ga ya zo ya samu aiki a office.
Hankalinshi yayi matukar tashi saboda ganin yadda tayi kaca kaca da falon komai ta har gitse ta fasa na fasawa ta watsar dana watsarwa a kasa.
Hatta tv bango ta tarwatsashi ga crystal glass da aka aje don decoration din falon a folon a kasa ta tarwatsa duk komai na falon a har gitse kamar ta haukace.
Tsayawa yayi a daga kofa yana bin ko ina da kallon mamaki a ranshi kuma yana mamakin irin zafin kishin Nafisa.
Wanan wani irin kishine haka shi bai da dama ya sake da wata mace a rayuwan shi sai ita duk da tasan neman mata ba halin shi bane.
Wanan wani irin rashin hankali ne ko kishi haukane kinshi Nafisa ba ba bai san yadda zai fasarashi ba don abin baiyi kama dana mai hankali ba.
Shi dai tun farko bai fada mata da ita kade zai zauna ba a rayuwan shi kuma tasan yana da mata tayi ta nacin sai da ya yarda ya aure ta.
Amma kuma shigowan ta ta hana shi zaman lafiya da iyalin shi da mahaifan shi gaba daya halin Nafisa idan ya motsa sai yaji nadaman auren ta dayayi.
Amma kuma idan komai ya wuce sai ta koma kamar ba ita ba shi dai wanan abin yana matukar damun shi wallahi.
Dakin barcin su ya nufa inda ya hangota takure a wuri daya tayi kuka tagaji ta ba kanta hakkuri jin an shigo dakin yasa ta dago kai cikin fushi don taga ko waye ya shigo mata daki.
Daga kofa ya tsaya ya kare mata kallo da kyat ya bude bakin shi yace wanan wani irin rashin hankali ne ko kishi haukani a garin ku ko kwakwalwan ki ya tabo ne da zaki min hassara irin haka don bake ke saye ba ko ?
Ya ka maganan cikin fushi yana hararanta a harzuke ta dago tana huci tana fadin eh hauka nake kuma a kan ka wallahi kadan ka gani duk kace zaka hadani da wata mace a duniyan nan abinda zan ma sai yafi wanan.
Yace oh ashe kina da aiki kuwa don dai ni namiji ne mijin macd hudu so zan iya aure a duk sanda nayi raayin hakan.
Cikin wani murya tace wallahi karya kake baka isa kace zaka hadani da wata kishiya can ba ni ni kadai ne matar ka, ka sani.
Oh dama tunanen ki ke nan amma kafin ki shigo kin samay ni da wata matar ko amma sabods zafin kishi irin naki ki hana mu zauna lafiya da ita.
Kaima kasan abinda ba zai yuyu ba ke nan ka hadani da wata mace may na rage ka dashi a duniyan nan wani irin kulawane baka samu a gare ni da sai ka hango wata a waje.
Cikin mamaki yace wana na hango a yanzu din kuma wa kika gana kula haukan ki dai ke nuna maki hakan mahaukaciyar banza kawai.
Indan kai ba baka hango ba ai mahaifiyar ka ta hango maka ita in bashi ba may ye nace wa sai wata ta biyomu a motar mo inba son hada fitina ba.
Yace Nafisa rashin hankalin naki har yakai ga mahaifiyata haka tanan kika biyo kuma Nafisa kan mahaifana tace in ba haka ba ne may take nufi yasa ta hado mu da ita ?
Yace cikin daka tsawa karki kuskura ki kara fadin wani maganan banza akan haka rakin zai baci sosai a gidan nan daga haka ya juya zaj bar dakin sai kuma ya juyo yace.
Ki tabbatar da kin gyara dakin nan da kan ki kuma ki mai da komai da kika fasa in ba haka ba wallahi zaki ga bacin rai na a yau din nan.
Sannan wani magana guda kada ki kuskura ki kira wani dan aiki yazo ya kwashe wanan barnan da kikayi ke da kan ki nake son ki kwashe shi daga haka ya fice ya shige wani daki a gidan.
Bin shi tayi da kallo don tasan ya hau sosai ga abinda tayi din sai yanzu nadama yazo mata a rai ga abinda ta aikata don tasan gaskiya ya fada mata kuma zuciyar tane kawai ya bata hakan ta hau ta zauna akai.
Gashi ta jawa kanta aiki don abinda ya fada har cikin ranshi ya fada duk dan aikin da takira ya gyara mata tasan abakin aikin maishi yake.
Gashi duk yan uwanta ne na jini babu wanda zata so a kora a cikin su haka yasa ta mike dole a cikin daren nan ta fara gyaran duk inda ta bata din.
Dakin yake yayi wanka ya sauya kayan shi zama yayi tare da dauko laptop din shi ya duba sai dai ya kasa aikin da yake son yi a lokacin tunane halin Nafisa yake yi.
May take nufi dashine ya tun haduwan su na farko da ita a bakin ma aikatasu yazo shigewa ta miko mai hannu tana fadin baba bani kuddi.
Kallon mamaki ya tsaya yana mata tare da waigawa baya ko da wani take magana bashi ba sai yaga babu kowa a wurin sai shi kadai tsakanin shi da mutane akwai nisa ta sake mika hannu tana fadin baba bani kuddi.
Yace kudin may zan baki tayi mashi alama da hannu abinci zataci alhalin su ke sai da abincin dayake shi mai tausayi ne kamar yadda mama ta koyar dasu na taimaka ma nakasa dasu sai ya ciro dari biyar ya mika mata da sauri ta karba har kasa tana mai godiya.
Ta nufi rufan sai da abincin nasu ta mika kudi yana kallo aka bata abinci ta koma gede tana ci a haukace kamar mai yunwa.
Tun wanan ranan idan yazo zai shige zata taso tana fadin baba bani kuddi sai ya mika mata dari biyar taje ta karya dashi.
Har shakuwa ya shiga tsakanin su mai karfi ko bai ganta ba zai aje mata dari biyar din nan kudin karyawanta yakawo mata yace ga kudin abinci nan.
Tsaki yaja ya rufe laptop din tare da kai kafadan shi saman gado ya kwanta rigingine yana ci gaba da tunane shi mutum na farko da ya fara warning din shi akanta shine Yusuf.
Yace kasan fa irin mutanen nan kudi suka fito nema ido rufe da maza ya kamata ka daina bata kudin nan kar mutane suyi zargin ka akanta.
Shiko tausayi take bashi baiga zai iya kin taimaka mata ba don taba bukatan taimako aa lokacin har yakai sun fara kyaabewa da ita.
Alokacin kallon yarinya yake mata don bai dauka ta haihu ba ma sai da yaje da zancen ta gida wurin su mama nason ya taimaka mata.
Mama ta kafe ba zai dauko mata fitina cikin zuri,anta ba anyi anyi da mama tace ba zata yarda ya dauko buzuwa ba yadda take ganin a na kwashewa dasu a gidaje da suke.
Ga fati bata rage shi da komai ba tana mishi biyayya don auren gata akai masu shida ita tun yana karami sosai saboda an ga taso yazo daya da ita aka dauka soyayya suke yi dashi aka hadasu aure tare.
Ido ya runtse a haka barci ya dauke shi cikin barcin ne yaji ta a jikin shi don bata zuciya dashi duk yadda ya iya fushi da ita bata yarda fushin nasu yai nisa.
Tea na tashi na hada don yunwa ke damu na na debo danbun da mama ta bani ina hadawa dashi ina jin kida na tashi a gidan alaman adawo da yawa ke nan hakan bai sa na fito ba don har na rufe kofana a lokacin.
Na gama nayi shirin kwanciya na don kada in makara da safe ina son shiga school tunda safe in gama komai don zan tafi shopping da yamma.
Washe gari bakwai na gama komai na fito don zuwa cikin makaranta ina rufe daki ne makwaciya na ta gani tace ashe kin dawo dama naga haske jiya a dakin ki sai kuma ba sake gani ba nayi zaton idona ne ke gizo kawai.
Nace eh nadawo jiya nan dai na tsaya muka gaisa sama sama da ita don ina sauri a lokacin na samu napep da zai karasa dani cikin school tunda ajike nake da kudi yanzu.
Naje na gama komai har na samu shiga lecture a lokacin sai karfe uku na juyo zuwa gidan mu a hanya na tsaya sai da na sai abinda zanci na wuce zuwa gida.
Sallah na fara yi don lokaci ya shige sosai koda na dawo wanka nayi na dan huta sai na shirya don zuwa sayo abincin da zanyi amfani dashi na wanan time din tunda ina da waddatacen kudi a hannu na saboda wanan tafiyan a saa nayi shi nake gani.
Don ga kudin da ya Amina ta bani wanda dama ita ke sallama na idan zan dawo sai dai kudin bai kan isheni sai na je gida na dan kara roro abinda ke akwai in kara kafin time ya kare.
Sai gashi wanan karon na samu a wurin mama da kuma dan su mijin buzuwa da ya driver ya bani dariya nayi don tuna sun da nayi nace jamgwangwan ke nan.
Ai sune maganin mazan dake ketare matan kasan mu su auro su don kawai ace buzuwa mutum ke aure ko may ko kuwa jaraba ne irin na mazan Nigeria oho ?
Na watsar da maganan su na mike na sabala jakata na rufe kofana na nufi bakin titi don samun abin hauwa a lokacin sahad yana tashe sosai a cikin abuja do haka na yanke shawaran zuwa can in sayo komai da nake so a saukake.
Ban samu wani matsala samun abin hawa ba ni kadai na dauki shata har can bakin sahad mai Napep ya aje ni na karasa shiga ciki.
Ban tsaya wani feleke ba abinda ya kawo ni na fara yi inda na dauki basket na fara zagayawa ban gare su indomie da taliya wanda shine abincin dan makaranta.
Sai shikafa karamin buhu dana dauka da su kayan miya yadda zai kai min time kada yazo ya kare in rasa mai taimaka min.
Bayan na gama da wayan nan sai na nufi bangaren kayan tea madaran Nidor na dauka na gari dan madaidacin gwagwani na juya zan sa a basket din da nake tara kayan a ciki .
Kamshin turaren mijin buzuwa ne ya daki hanci na kaina na kasa ban dago ba sai takalman mutumin da na gani bakake a kafan shi hakaya na dago kai na dan kalle shi.
Mijin buzuwa ne tare da Yusuf suke sayayya a shagon su ma dan daburcewa nayi da ganin su kamar ba zan gaida su ba sai wata zuciya tace min ko dan kudin da ya baki ai kya gaida su.
Sannu ku nace dasu tare da juyawa na fara tura keken kayana Yusuf din ne ya amsa min tare da fadin a a yar garin mu ke ce.
Ummm kawai nace dasu na wuce abina na karasa saura sayayyana na dungura keken zuwa wurin biyan kudi na aje a gaban wanda ke lissafi ina jiran inji ko nawa na kashe a cikin shagon in biya.
Ya gama lissafi kaina yana akan wayana ya dago yace thirtythree thousand five hundred nace OK na bude jakkan dake makale a kafada na zan biya kudin yace ai an biya maki kudin ga canjin ki ma ya rage yana miko min kudin.
Yana kokarin miko min ledojin yaron shagon ya mike da sauri yana karba da mamaki nake kallon shi ina kallon kudin da yake miko min din.
Waya biya nace mai duk da nasan ba wanda ya sani in ba mijin buzuwa da Yusuf dana hadu dasu yanzu ba a ciki.
Yace gasu can suna fita su suka bada kudin sukace indan kin gama sayayya a biya maki suka tafi da sauri nabi bayan su har na samu sun tayar da motan su suna ribas a lokacin.
Ganina Yusuf ya tsaya na dago da zuman fadar wani magana kuma sai na kasa yaya akayi yar garin mu nagan ki a sukwane ko hanya zamu rage maki ne ?
Nace murya a tausashe aa nazo inyi godiya ne mai shago yace kun biya min kudin kayan na mika mai canji nace ga sauran kudin daya rage nan.
Nuna min mijin bazuwa yaya yace bani na biya ba ogana ne ya biya maki albarkacin ki na yar mama mun yasa ya biya maki ban san sanda nace mijin buzuwa na gode ba.
Ido ya waro waje jin abinda na kirashi dashi shiko Yusuf dariya abin ya bashi yace kwarai kuwa mijin buzuwa ne abokiyar fadan ki ko ?
Sai nayi kasa da kai kunya ya kamani nace ga sauran canji ina mikawa Yusuf din kudin kai ya girgiza min yace ai shi bai kyauta ya karba jeki dashi Allah ne ya baki sai a kara ayi provition ko don naga alaman sayayyan yan makaranta kikayi.
Kallon ledan da yaron ke biye dani dasu nayi nadan yi murmushi nace na to gode kai mun godiya wurin mijin buzuwa zai ji yace dani.
Ai da kizo mu sauke ki don naga gaki da kaya dayawa abin hawa zai maki wuyan samu a nan da sauri mijin buzuwa yace amma dai kasan sauri nakeyi ko ?
Haba baka gani marance yayi ina zata samu abin hawa mu sauke ta mana sai mu tafi aiba dadewa zamuyi ba a can ko may kace yana bukatan jin ra ayin shi.
Da sauri nace a a zan hau napep a bakin titi zaku iya tafiya na gode yana kokari bude mota yace a a ai ba zamu bar yar mama a nan na shiga kawai mu sauke ki kada ki fada ma mama mun ganki muki rage maki hanya tayi muna fada.
Ya fito ya bude booth din motan yake magana ban da yadda na iya dole ina kallo yasa mun kayan a booth din su ya bude min bayan hangamaymay jeep din su na shiga sanyi da kamshi kawai ke tashi a cikin motar.
Ya shigo ya tayar da motar muka fara hanya shiko mijin buzuwa ko ta kan mu bai yi ba sai faman aiki yake a sytem din shi saman jukin shi.
A hankali yake tukin motar mun dan bar sahada din Yusuf yace mijin buzuwa sorry fa mun bata maka lokaci ko ?
Ban son iskanci yace a harzuke sai kuma ya juyo gare ni yana fuskanta yace and ke kuma duk na kara jin kin kirani da wanan sunan sai na bata maki rai wallahi.
Da sauri nace ni kada kaga laifi na haka naji kowa na kiran ka da mijin buzuwa bani na fara fada ba ina magana ina jujuya idanuwa na manya.
Dariya Yusuf keyi muna yace a a mijin buzuwa da haka kowa ya sanka a layin mu don ta fada yanzu shine zakaji haushin ta nace ai shi nagani nima.
Yace dakyau yar mama har lokacin wani kallon takaici yake min yaja tsuki ya mayar da kan shi ga abinda yake yi ya fita batun mu da Yusuf din.
Yace yar mama ke may sunan ki sai naji mijin buzuwa yaja wani uban tsuki yace kai malam kafa san aiki nake yi ka samu yarinya kana biye mata don wauta.
Kasa kasa nace wai yarinya yarinyar dai tafi buzuwan matarka yasin ban dauka maganan duk sun jini ba a motan sai gani nayi ya rufe laptop din ya dafe kan shi da hannu daya.
Shiko Yusuf cewa yayi a sosai ma yasani ai gashi yana gani a gaban shi yace kai Yusuf tsaya in fita motar nan don Allah kun isheni wallahi ban son damuwa kasani.
Maimakon ya tsaya kamar yadda yace sai ya kara ma motan wuta ya harba saman titi da sauri shi yana dariya ya sake cewa baki fada min sunan ki ba mana.
Khadija nake yace suna mai kyau a uni ke karatu ko ina nace eh anan nake yace dakyau aji nawa yanzu nace ban dade da farawa ba biyu muka shiga yanzu.
Kai amma kinyi kokari nake ganin ki yarinya ashe yarinyar da kwazon ta yace may kike karantawa anan ?
Ban kai ga bashi amsa ba yace yaushe ne kazama dan jarida haka Yusuf ban sani ba wanan tambaya ai yayi yawa haka yace ai ba zaka san na zama dan jarida ba sai na karasa tambaya na tukun.
Kawar da kai yayi gefen window motar yana kallon titi Yusuf din yace baki bani amsa ba nace bari in ogan ka ya fita bai san ni nafishi rashin son magana ba ma .
Yace aini naga alama shi ne dai kamar bai ga hakan ba ke nan zan bari sai next haduwa mu sai mu dora a ida muka tsaya tunda ku dukan baku son hayaniya jin nayi shiru yasa ya dan juyo yana satan kallo don jin banyi magana niko ina kokarin ciro wayana daga ciki jakkata da ake kirana.
Bayan na dauko naga baba nane ke kira da sauri na dauko ina fadin daddy i miss you ina mama yace gata kusa dani jiya anty ki tace kin dawo makaranta nace eh daddy amma ban zan zo minna yanzu ba sai dai hutu ina gani.
Mun gama watan da naji Yusuf yace ashe ke yar Niger state ne nace eh ni yar minna ce yace a cikin garin minna kuke da zama ?
Ohh god wanan wani irin abune haka for god sake in kana son jin kwab ne basai kuje gidan redio ba kuyi wannan abi damay yai kama don Allah.
Ku ajeni daga nan don Allah zann karasa da napep don ma mun kawo kusa da inda nake ai a haba ke ko baki son muga a inda kike ne don watarna idan za a bamu sako mu baki.
No I no wan wahala ne ji yadda yake ma fada ban son in ja maka matsala gun ogon ka ne don naga kamar bai so dauka na da kayi ba beside nima din ban son shiga mota dashi don takurawa.
Ke yace yana kallo na a zurke yace ka neman min rai ni a wurin wanan yarinyar Yusuf harta kalli idona tace ina takura mata.
Ya kara yana jan tsaki don Allah yaya Yusuf ka tsaya in sauka anan tun bai yi ball dani waje ba don ban daukan irin wanan na karasa fadi a hankali.
Ina zamu bi don mun kawo unguwar Yusuf ya ke tambayana nace wancan layin zaka bi anan gida jen namu suke ya dan gangara kadan sai nace wancan get din zaka tsaya nagode ina kokarin mikewa ya ja ya tsaya get din a wagale yake a lokacin.
Bai bode motar ba sai yace a nan kike da zama ke nan eh kawai na bashi amsa yana sake bin gidan da kallo sai can ya bude mota nima na bude gefen da nake na fito.
Ya fito ya fara fitar min da kayana daga cikin motar ina tsaye gefe har ya gama ya dago yana cewa kona shigar maki dashi ne ciki.
Abinda yasa ni murmushi ke nan har dimple dina ya dan lutsa kadan yace ko maza basu shi nace ko haka na gode Allah ya saka da alheri kai min godiya wurin mijin buzuwa.
Dariya ya kwashe dashi ya shige mota yana dariya ina tsaye a wurin suka ja motar suka wuce na sauke ajiyan zuciya a hankali na duba tarin kayan dake gaba na a lokaci.
Shiko yana shiga motar ya sauke ajiyan zuciya yana fadin kai yarinyar ta hadu wallahi ga kyau ga zakin murya kamar dai ita tai kanta ji idanuwa karmar ita ta tsaya ta halici kanta wallahi.
Tsakiya yaja yace wai yaushe ka koma haka ne don Allah ka koma kamar wani sabon shiga a ganin mace mai kyau.
Wanan din kyaunta na daban ne ai dole ne a yabata wallahi don komai akwai zamzam wanan sai irin gidajen ku ai.
Gidan wa ya juyo da sauri yana fuskantan shi cikin alaman tabaya a fuskan shi yace ban ga laifin Nafisa ba da ta haukace min jiya a gida.
Hauka fa kace yace hauka mana don kawai mama tasa mun rage ma yarinyar nan hanya take ta hauka wai mama na son shirya wani abune akai.
Jiya koda na koma gida gaba daya duk ta hargitsa komai na falon sama da daki wai tana kishin wanan din.
Kaji ba Nafisa tasan abinda ta gani anan ita ke nan ma mace taga inda kyau da fari ke aiki ba farin bane kawai irin nata.
Yace cikin gatse gashi fa in akwai kyau ba gashi may akayi yace kasani ko duk ta hada kai dai ka kwantar da hankalin kasha kallo kawai a nan.
No warnder Nafisa take fadin bata yarda dakai ba ashe tana da gaskiya yau kaine da bakin ka kake fadin inso wata bayan ta ni wata mace kuma zan so yanzu nidake da Nafisa a gida na.
Baki Yusuf ya tabe yace ai ko baka kai namiji ba idan ka buge ga wanan buzuwa ke nan ka zama mijin buzuwa da gaske.
Lumshe ido yayi da Yusuf ya fadi hakan yace yarinyar nan ma ta raina ni wallahi da ganin ta bata da kunya dama don dashi ta tare ni.
Wallahi yarinyar ta hadu ne kai dai kawai ka mace ga son yar buzuwa baka ganin sauran mata da gashi yanzu.
Ina mukayi yace mashi yana kallon shi don son ji yace kaini gida kawai murmushi yayi tare da fadin buzuwa tayi kira ke nan ?
Bai ce dashi komai ba sai lumshe idon da yayi mai kawai yana sauka yace to mijin buzuwa sai gobe ke nan ko don nasan in kashiga ka shige ke nan .
Harara ya watsa mai yana tafiya yana gyara jakkar laptop din shi cikin hasala da abokin mashi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Agidan su kuma Nafisa ne ke waya da kawar ta da ta baro kaduna wace suke kira da madam a cikin su tantiriyace ta kwarai na fada.
Da mijin ta sai dai kamar itace mijin ba mata ba don sai yadda tayi da mijin a gidan idan tace kada ya zauna bai isa ya zauna ba.
Atakaice dai ya zama mijin tace ga madam ko kawayen nata zasu iya aiken shi ya tafi komai nisan wuri koda da kafane sai yatafi yadawo.
Itace Nafisa ta kira tana son fada mata abinda ya faru da ita bayan barin su kaduna ta dauko wayan ta madam ta soma nema a wayan sai dai wayan nata ringing ba a daga wayan ba takaici ne ya kama Nafisa.
Ta ja tsaki ta na fadin yar iskan ko gidan uban wa ta shiga waya nata ringing haka bata dauka ba har ya katse bata dauka ba kin sake kiran layin tayi a lokacin sai taci gaba da tunanen ta tanayi tana kada kafan ta daya dake har de.
Babu abin da take tunawa sai irin shirmay da ta tafka jiya din akan bakin kishin dake damun zuciyar ta akan mijin ta wanda take mashi son daba taba yi ma wani abu ba sai dai kuma a kasan zuciyar ta ba so bane can na har abandan don da zai iya shiga wani halin jarabtan rayuwa a yanzu tsaba zata iya gudun shi ta koma wa mai maski.
Wayan nata aka kira ya hanata karasa muna jin birnin zuciyar sai ta dan sake guntun murmushi tana daukan wayan nata tare da fadin Aloh ina kika shiga nake ta kiranki baki daga waya ba.
Cikin muryan barci madam din tace tana hamma baki hangale bata fasa magana duk da tana hamman tace wallahi barci nakeyi tunda rana.
Tsuki Nafisa taja tare da fadin barci sai kace wata mai ciki ko kasa ni don Allah watseke fuskan ki kiji ni magana nake son muyi dake ki ban shawara.
Madam tace ina jin ki matar manya dadi Nafisa take ji idan su madam na fada mata wanan sunan madam din ne tace ke nake sauraro fa.
Wallahi ke dai madam kin san ko sai da munafukar tsohonwan nan ta hadamu da yarinyar da nake fada maku tace mu rage mata hanya ?
Don Allah ki bari madam ta fada itako tace sosai kuwa ai saida muka dauke ta a mota daya mukai tafiyan.
Tace yaya kika bari haka ya faru don Allah kin ko san iein mijin ki neman su mata keyi ido a rufe nasha fada maki ki nisanta shi daga ko wace mace in ba muraharamin sa bace har kika yarda hakan yafaru dake.
Ke dai bari madam nanu mashi rashin yarda na ga hakan amma ya rufe ido yace shi yace umurnin mahaifiyar shi ce dole ya bi.
Madam tace yaya kukayi a motar injin baki basu daman sakewa da juna ba a motan ?
Tace ai in fada maki ban yarda ko daga kai yayi ya kalle ta ba kuma nima ban sake ayi hakan ba sai dai mun kwashi rikici dashi sosai da muka iso gida wai zai tafi office a sauke shi sai a wuce da ita.
Bude mashi wuta nayi sosai in fada maki sai da mukayi kaca kaca dashi na kuma hana shi fita sai da aka kaita a ka dawo san nan ya tafi.
Da haushi da bakin ciki ya kamani duk na farfasa kayan falon nan gaba daya don in nuna mashi bacin raina don gobe kada ya kara min haka.
Madam tace kash aike kinji matsalan ki ke da zaki bishi da lalama ki nuna mai ba wata mace sai ke a duniya daga baya sai mu sake shirya wa tace.
Madam idona ya rufe a lokacin da kishin ganin wanan yarinyar a kusa dashi amma da ya fahintar dani shi irin su ba su gaban shi shi yanzu wace mace zai kalla ta bashi sha,awa sai naji hankalina ya dan kwanta a lokacin.
Madam tace amma kin so ki bada mu wallahi kai kin ma dai kwafasa wallahi yanzu ke ko irin matan abujan nan ya lalubu maki har ki ta da hankalin ki haka mudake da wuka a hannun mu nama kawai muke jira.
Kawai yanzu idan ya dawo kije ki bashi hakkuri akan abinda kikai mai din don kada ya zarge wani abu a gare ki.
Kin ga zaki ji a bakin shi ko ita wanan yarinyar wacece a garesu kin dai san yadda zaki bugi cikin shi ai muji komai a saukake.
Tace zanyi kamar yadda kika ce din amma ba yanzu ba zan dai saka ido in gani idan suna tare ko basu tare sai musan abinda zamuyi daga baya.
Sun dauki lokaci suna maganan akaina ana ta kulla sheri da tugu akan mazajen su kafin suyi sallama madam tace zata kira zuwa gobe taji indan da wani matsala kuma.
Na gama shiga da komai daki na da taimakon wata yar gidan namu da ta dawo tagan ni da kaya ta tsaya taimaka min.
Kayan jikina na fara cirewa san nan na fara gyara kayan ina aje komai a inda nake bukatan shi na gama na zauna ina tunane a raina.
Bakomai nake tunane ba sai mijin buzuwa da Allah ya jefo a rayuwana a dan lokaci ya taimaka min yau gani da kudi a hannu na wanda yakai dubu dari ta dalilin mijin buxuwa da iyayyen shi duk na samay su.
Waya na dako a cikin handbag dina ina neman layin ya Amina don in fada mata abinda ya faru don komai ya faru dama nakan kirata in fada mata.
Kira uku ta daga wayan ina ji bata kusa da wayan ne a lokacin mun gaisa nake tambayan yaranta tace suna lafiya sun tafi islamiya.
Nace anty kin san wani abu da ya faru yau tace ina zan sani Khady nidake kaduna zaune kina abuja ke.
Nace anty yau na hadu da mijin buzuwa danaje sayayya tace kun sake haduwa kuma again nace wallahi anty wai duk wanan uban kayan da na sawo nazo biya sai ake ce min ai ya biya bayan da suka sauke ni ranan ya ba driver dubu hamsim ya bani.
Kai da gaske khadija nace wallahi anty kuma su suka kaini gida sai dai shi bai so su dauke ni ba sai abukin shi ne yace saboda mama ne suke min haka.
Dariya tayi tace to Allah ya saka da alheri ki dai bi a hankali inda duk kuka hadu don buzuwan nan ba imani ke gare ta tana iya komai akan mijin ta.
Ya Amina ni inama zan kara ganin shi kuma Allah dai ya tsaga rabona daga Aljihun shi wanan karon mutumin da ko yaushe take a cikin hade fuska banda gaisuwa may zai hada ni dashi kuma.
Daga haka muka kawar da zancen shi muka dauko na iyayyen take fada min cewa sunyi waya da baba yana fada mata kudin su na ritaya ya kusa fitowa kwanan nan.
Ihun jin dadi nayi don murnan iyayyen mu zasu fita acikin hali talaucin da suka shiga na ritayan da mahaifin namu yayi muke cikin halin kaka nakayi.
Tace ai zan riga ki ji idan kudin sun sauka don haka sai abinda kika samu daga baya nace ai ni indai daddy zai samu bukata na ya biya ke nan.
Yanzun ma shawara nakeyi inje banki gobe in tura mai kudin da mijin buzuwa ya bani don akwai kudaden da zasu isheni a hannu na tunda ina da abinci waddatace .
Tace haka akeso mutum idan ya samu ya tuna da iyayyen shi dama dako kin kyauta wallahi dama sallaman ki ya hanani tura mashi kudi wanan watan.
Haka dai mukai ta hira da ita daga karshe mukayi sallama na kashe wayan tare da mikewa na jona electric dina don in dafa dan abinda zanci da dare.
Kira, a na saka a wayana ina aiki ina bin kira a don ni gwanace a wurin iya hadda tun ina yar shekara sha hudu na sauke alkurani mai girma na sake maimaitawa yakai kashi uku yanzu don duk wanda yasan yaran minna ya sansu da ibada da kamun kai ga girmama na gaba dasu a duk inda suke.
Da wanan halin namu nake shiga ran mutane farat daya kowa tsakani na dashi gaisuwa ne na mutunci da sani girman wanda ya girmay mun.
Na gama na zuba a plate na dauko ledan ruwa guda cikin wanda na sayo na aje a dakin na zauna don in fara cin abincin sai ga kiran waya ya shigo min.
Binta ce ta kirani a lokacin na dauka kafin wayan ya tsunke hiran mukayi sosai ranan da ita har nake mamakin ko nawa ta sa awayan ta haka don da mun sake wanan hiran take dauko min wani.
Har take fada min yadda akayi ranan da zamu wuto da buzuwar yayan su tace bazata shiga mota dani ba mama ta dage daya zo mata da maganan kan lalai sai sun tafi dani.
Nace kin ko ga tunda muka kama hanya batai min magana ba nima ban masu ba daga ita har mijin ta.
Tace wanan ai dama shi miskili ne magana kamar aiki yake ganin sa a gare shi zai iya zama da kai kuyi awa daya baice uffan ba haka kuma matar shi anty fati itama take shiru shiru bata magana.
Nace aiyanzu sun samu mai magana a tsakanin su haka yasa ta samu daman musguna mata yadda take so ai.
Tace ke kin ko san halin wanan matar shu,uma ce wallahi ta karshi da farko da tazo boye halin ta tayi kamar wata mutumiyar kwarai da ita.
Sai daga bayane ta fitar da kalar ta kowa ya sani bata kaunan ko dan uwan yaya ta ganshi a gidan nan wallahi.
Nace wuri ta samu wallahi ni kar nake kallon ta don banga abin tsoro ba anan ku dai na fahince ku kuna bata girma ne don mijin ta yana da hali a cikin ku.
Tace ga tsiya nace eh mana haka din ne amma in bashi ba ta yaya zaku zauna wanan matar ta dinga raina maku hakali har tace wai idan tana wuri kada ayi dariya .
Tace ina ma kika sani khadija ai sai wani lokaci da mukaje hutu wurin su a abuja ba girma muka dawo gida kwanan mu biyar ko sati bamu kai ba matsi yai muna yawa a gidan.
Muka matsa ma yaya zamu dawo ga yan uwanta nan muna ganin yadda take ji dasu amma mu ko falo ta hana mu fito muka koma kamar wasu bare ba yan uwan maigidan ba.
Dariya nake mata sosai tace Allah ko magana mai karfi wai ba ai mata a gida tace ba kallo ba komai sai zagi da hattara ga anty Fati damu da ita duk muka koma daya.
Bayan mun dawo sai ga anty Fati ma ta dawo wai a kaduna zata zauna bata iya zama da buzuwa a abuja bata bari ko miji ta gani idan yana gida.
Nace ke ki bari don Allah ashe ba karamar shuuma bace tace baki santa bane Khady wanan fa ko kashe mutu tana iyawa fa.
Nace wanda Allah yabata ikon kashewa ba wani kan ai yafi karfin ta wallahi ba abinda zata iya wanda Allah bai tashi yi da bawan shi ba.
Ni don Allah har kin ban haushi da wanan maganan naki don ba a gidan ku nake ba wallahi da taga tsiya a guri na nifa irin matan barikin nan haushi irin su nake ji.
Zako kiji nata don bata da hali mai kyau ko kadan akan mijin ta zata iya yiwa mutum komai musan man ma ce ko waya tayi da wata ranan sai sunyi jidali sosai da ita ke ta zama mai kaya ko shi yanzu bai da yadda zaiyi da ita ne kawai wallahi.
Nace ya dai ga dama ne Binta idan ka ganshi ga mutum har mutum amma baida kuzari gun mace tir yayan ku ya zama mijin hajiya wallahi.
Haushin abinda na fadi taji da fada muka karasa wayan a rana na kashe ina mata dariyan shakiyanci na gama na wanke kayan na samu wuri na kwanta.
Washe gari da wuri na fita don ban yarda in makara in ba wani dalili ya tsayar dani ba mai karfi shi kadai zai sani makara kawai.
Ban da yawan kawaye sai mutum biyu yan department din mu kosu shirin mu dasu don sun ga nafisu kawo wuta sosai a class din shine likewan su dani.
Banda wasa ga abinda ya kaini abujan daga school sai gidan mu sai ko idan wani dalili zai sa na fita a ranan zan fita.
Yau ya dawo a gajiye don daga wurin aiki ya wuce wuri wasan polo da suke yi don dan wasan ni ne sosai wanda yana daya daga cikin abinda ke kawo mashi kudi a lokacin bai dogara ga aikin shi ba yana buga buga irin na maza gida da waje shike sa yana samun mahaukacin kudin da yake riko.
Wanka yayi yana saka kaya a jikin shi ta shigo dakin dan juyawa yayi ya kalle ta ya kawar da kan shi yaci gaba da abinda yake yi.
Karaso wa tayi gare shi tana wani rangaji na daukan hankalin shi ta sake abinda yake so ya sauko mata har mazaunan ta.
Cike da sallo ta iso gare shi sai dai tsiyan shi da ita duk gayun ta bata damu da saka kamshi ba kuma har yanzu ba gwanewa tayi ba da iya kwalliya shine ma yake kokarin wurin gyara mata idan tayi wani kwaliyan zasu fita.
Gata da son karya sai dai ko bokon kasar su bata samu ba kuma babu na Allah a tare da ita abin ya taru yai mata yawa amma hakan bai hana shi son abin shi ba.
Rungumoshi tayi ta bayan shi ya sauke wani ajiyan zuciya yana dan murmushin jin dadin ganin ta tace yau ina ka shige haka ne ta dawo ta gaban shi suna fuskantar juna.
Bai ce komai ba yadan jajeyeta ya dauko turare yana fesa ma jikin shi tace har da daren ma sai an feshe jiki da turare ko fita zakayi ne haka ?
Sai lokacin yayi magana yace sai zan fita ne zan saka kamshi a jiki na ke baki son kamshine ashe yasa baki sakawa .
Taji zafin maganan amma ta daure don in da sabo ta saba da gorin saka kamshin da yake mata din ko yaushe kuma hakan bai sa ta saba da sakawa ba.
Tace muje kaci abinci yace na koshi ta dubeshi da sauri tace tare da fadin ban gane ba yace mun ci abinci da Yusuf kafin in dawo.
Juyawa yayi ya nufi saman gadon su yana jawo laptop din shi tasan idan ya fara dakilan laptop sai ranta ya baci kafin ya gama.
Idan tayi magana kuma yace business yake a ciki shi ko wani abin dariya tayi ya dago yana duban ta na lafiyan ki kalau kuwa ?
Sai yaji tace maganan turaren da kayi ne dai yaban dariya har na tuna da yarinyar da mama ta saka mu dauko ranan.
Bakaji wani irin kamshi tiraren da takeyi ba kamar tayi wanka dashi yace tasan kan ta ne yasa ta saka turaren haka don kada a raina ta.
Tace shi saka turare kuma har wani sanin kai ne dashi wai ma may ye alakan ta da mama ne data nace sai mu dauko ta wai ?
Yana bude laptop din yace sai yanzu kike son jin halakan su da mama da kishi ya rufe maki ido baki tsaya tambayan ta ba da farko.
Tace kayi hakkuri cikin yanayin tausasa harshe tace nasan ban kyauta ba kishin ganin ka kusa da wata mace nakeyi tundai irin wanan yarinyar dake cikin ganuwan kurciyan ta ga kyau kuma da gani tana kuri da ilimin ta.
Ina tsoron ka hango kyawon tane wallahi kazo kace zaka dauko min ita a gidan nan wata rana son ka nake har karshen zuciya ta ka sani.
Ya tsaya yana mata wani irin kallo yace don kina kishina sai ki min hauka mata nawa nake gani a rana da ina raayin mata ne zaki san lokacin da zan nemay su ne.
Har kina fada min cewa mahaifiya ta da biyu ta hadamu tafiya da yarinyar don in so ta kika haukace har kina fashe fashe a gida.
Kwantowa tayi a jikin shi ta dan shafi kan shi tace kai min afuwa don Allah haka ba zai sake faruwa ba a tsakanin mu.
Yaji hakkurin da ta bashi har cikin ranshi yace ki rage kishin nan nake don ni din mijin mace hudu ne watarana.
Da sauri ta rufe mai baki tana fadin don Allah ka daina fadin haka don kana sa zuciya ta tana bugawa da wanan zancen kishiyar da kake min.
Yace idan lokaci yayi ai yi zanyi sai dai ki tausasa zuciyar nan naki bakiga mahaifina matan shi hudu ba kin sani ko in gado shi nima ?
Kuka ta soma mashi tana fitar da hawayen munafunci a idon ta dariya yayi mata yace akan kishiya kike wanan kukan haka fati fa ba kishiyar ki bace kin ga ai ko yanzu kina da ita ke nan.
A bar maganan Fati tace don ni kaina ma kunya nakeji ace wai ita din kishiya ta ce balle kai ace matar ka ce Fati ta sunna.
Ohh kin fison indan zai ne ma yanzu in nemo wace idon ta ya bude sosai don itace ta dace dani tace ba haka nake nufi ba don Allah mu bar zancen kishiyan nan haka na.
Tambayan ka nayi cewa wacece wanan yarinyar ne sai ka dauko min wani dogon zance kuma akan kishiya ?
Yace nima ban san ta ba a gurin mama wanan zuwan da nayi na fara gani ta koma waye dai ita nasan alakar ta da mama mai muhinmaci ne sosai.
Shiru tayi tana nazarin maganan shi daga karshe dai data ga ya fara aikin shi ta kwanta tana ci gaba da tunane kala kala a zuciyar ta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
Bayan mun gama waya da ita naji raina ya baci sai a lokacin na gode ma Allah da ban goge number shi ba a wayana kira nayi har sau biyu bai daga ba sai na tura mashi sako masu zafi na kashe wayan.
Don nasan zai gani da safe in ma kwanciya yayi a lokacin haka yasa na danji zafin da nake ji ya rage min da kyat barci ya dauke ni a ranan.
Har na rufe ido sai nayi wayana yana kara na dauka a zatona shine yaga sakona ya kira wayan sai dai ba number daya kirani daya kira dashi bane.
Nace ummhumm ina jin ka naji ance haka ake karba kiran wanda baka sani ba na sheda muryan Yusuf din nace yayana kaine a na dauka wani ne.
Yace nice injin ruwa bai saki jin zazzabi ba dariya nayi nace ai na watsa ruwan zafi a jikina yace good dama na kiraki ne don mutumin ki ya karbi number ki a hannu na nasan zai iya kiranki kada ki biye ma halinshi don Allah don bansan abinda zai kiraki ya fada maki ba koda yake yace akan maganan hajiya mama zai kiraki yaji don Allah , , ,
Na katse shi da fadin ai ya kirani ko har munyi tsiyan shi ya dauka kowa nema yake a gare shi ko yaushe ni kuma na wanke shi tass.
Da karfi naji yace haba don Allah nace wallahi na kwashe komai na fada mai har text din da na tura mai mai zafi yace amma baki kyauta ba wallahi.
Nace saboda may zai mun hadi yace khadija kin san kuwa kece mukee son kizama weapon din mu wurin yakan buzuwa nan gaba.
Don Allah ki dinga sausautar harshen ki gare shi nace wa ni ni ina ruwa da shi da zan zama muku makami a gare shi da buzuwan shi.
Dariya yayi yace ke ko ke dashi khadija ke da komai da zaki yakar muna buzuwa don kin cancanci yin hakan.
Ni din yayana yace kwarai kuwa kauna na sai dai idan mun hadu zan maki bayani yadda zaki gane nace to shike nan tunda haka ka fada yace bani na fada ba umurni nima aka bani kan hakan .
Yace sai dai idan mun hadu din zan maki bayanin komai nace Allah ya kaimu ina saurarenka da haka muka yi sallama dashi ya barni da tulin tunane a zuciyana.
Da safe zarah ce take buga min kofa jin bugun kofan na tashi na bude daki tana tsaye kofan dakin nawa ganin tana son shigowa na bata hanya ta shiga daga ciki.
Tambaya na tayi ko da safe zan fita nace ai kemakin sani yanzu haka shiri nakeyi kada in makara take cewa dani zata fita amma wai za a kawo mata sako shine take son in karba.
Nace zarah fitan kuma zakiyi yanzu tayi dan guntun tsaki tana fadin eh wani friend dina zaiyi tafiya nake son inje muyi sallama dashi.
Zarah ba zaki wankan ki fada ki zauna ki abinda iyayyenn mu suka kawo mu yi ba wanan dabiar da kika dauko bai da amfani gare ki nan gaba.
Ta dan yi murmushi ta nufi wurin da taga na aje plate din abin ci da tukunya tana bude bayan ta bude ta dago tana dariya tace an fada maki yadda bakin san wayen kai ba haka kowa yake yanzu da anganki kamar may wayayen kai .
Nace in dai irin wanan wayen wane kada Allah ya nufe ni da yin shi ina neman tsarin Allah ga irin wanan dabian naku Allah kuma ya shirye ku ku gane gaskiya.
Ta juya ta debi arish a plate ta zauna ta fara ci ni kuma ina ta shirina nace kiyi ki gama gada ki makarar dani anan don banson in makara.
Tayi murmushi tana kai abinci a bakin ta sai da ta hade tace wanan halin naki na ina kika fito karatu ina zaki karatu sai ke khadija.
Khady look at you me kika rasa ke kanki jarin kanki ne amma kin tsaya kina wahal da kanki haka har kina wani girki tunda safe kamar wata matar aure amma waike nacin karatu sai wahala kike haka.
Wallahi da zaki yarda akwai wanda zan hada ki dashi cikin kwana biyu kiyi clean ke baki daukan misali a kwaina khady da haka nake ?
Amma yanzu gani tunda hanya ya bude min mai na rasa na rayuwa atare da ni amma ke gaki da abin kawo kudi kina ta faman kumshe shi a jikin ki ta fada tana dariyan shakiyanci.
Ni dai ina tsaye ina mata kallon mamaki da huduban shedan da take min har kuryan dakina ta dauka nasihan ta ya na shigana ne ganin yadda na tsaya ina kallon ta.
Tace ina son ki fahimci wani abu tsarin rayuwa yanzu ya canza ki shigo kawai a dama dake yarinya.
Nace cikin murmushi zarah baki fance ni batsarin rayuwa ta daban yake da naki ban sanya ma zuciyana kwadayi ko son jin dadi a ko wani irin yanayi ba don haka kada kiyi tsammanin guntun huduban ki zaiyi tasiri a raina .
Ni da kika ganin nan ina da mutunci na kuma nasan ciwon kaina dana iyayyena kada kiyi tsammanin kananan kwarin da kike bi zasu iya rudana da wani abu.
Shi jin dadi lokaci indan lokaci yayi sai inji amma ba ta hanyar wullakata kai yadda kukeyi din nan ba kema idan da zakiji sharata da kin watsar da wanan rayuwan ki rungumi abinda ya kawo ki Abuja.
Su kansu mazan da kuke bi aida karatun suke amfana yanzu bance maki ban saurayi ko rayuwa ba sai dai in gajarce maki ni indan zanyi mai tsabta da sanin ciwon kai zanyi amma bana kwanan gida irin naku ba.
Baki zarah ta tabe min tana dariya ta saba da nasihana kullun wanda ita a ganin ta ni har yanzu ban waye ba ban san ciwon kaina ba bansan ta kan duniya ba kuma.
Nace keyi dariya amma ni idan zan faso gari ba irin wa yan nan kanana kwari masu gurbata rayuwa zan tsaya dububa ba sai wanda ya san kanshi da mutuncin kanshi.
Ta mike bayan ta gama ci dama ina magana ina kallon agogona ne kada in makara tace ina son ki fahince ni a yanzu ba a samun irin wa yan nan mazan da kike hasashe kinga ko zaki shawa wuya wurin neman su.
A naki ganin ke nan zarah amma muna nan dake zakice na fada maki watarana ta miko min key din ta nace kenan yauma till down zakiyi tace yo may za a fasa kuma.
Ta fita na rufo kofana muka fito tare da ita a titi muka raba hanya tana neman lift ni kuma na nufi cikin makaranta ina mamakin wanan rayuwa da zarah ta daukan ma kanta.
Itama yar minna ce kama na dalilin haduwan mu ke nan da ita don ko a minnan ba unguwa daya muke ba su suna zama a cancaga ne ni kuma muna tsakiyan gari.
Kasancewar mu yan gari daya yasa muka zama kamar yan uwa da ita da farko halin ta mai kyaune kafin idon ta ya bude da bin mazan abuja.
Sai lokacin muka raba hannu da ita amma hakan baisa mun daina kula junan mu ba kamar baya sai dai ban taba yarda naci abinda take samuwa ba daga wurin yawon banzanta ba.
Tun abin na damun ta har yazo ya daina damun ta ta daina ba sai wanan da iyayyen ta suka kulla suka aiko mata yanzun tana ganin tafi karfin shi ita shine ta kawo min inyi amfani dashi.
Tun asuba yake tayar da ita ta tashi tayi sallah amma tana kwance tana barcin ta har yagaji yatayar da ita da karfin tsiya ta zauna tana mustsukan ido alaman barcin bai isheta ba har lokacin yana ganin ta tashine yasa shi fita daga dakin azaton shi zata tashi tayi sallah.
Ya fita zuwa dakin motsa jikin shi da yakeyi duk safe inda kuma yake aje wasu kayan amfanin shi jiya anan yabar wayan shi yana canji ya je ya kwanta yana tunanen rashin son ibadan da batayi.
Ya gama komai na motsa jiki da yakanyi da safe ya wuce zuwa inda wayan shi yake jone ya dauko din ka idan shine sai takwas yake bude waya da safe.
Budan wayan yasa sakon da suka taru mai shigowa ya gane su wanda farko budewa nawa ne ya shigo da farkon.
Mamaki yayi don ba suna sai lamba ga dogon sako kuma da maishi ya turo mashi kamar kada ya karanta tunda baisan mai sakon ba sai kuma wata zuciya tace dashi karanta kaji mana abinda sakon ya kumsa kila mai amfani ne gare ka.
Fara karanta sakon ne yaji ranshi ya baci don ya fahinci inda sakon ya fito don ganin farkon rubutun nawa kamar haka
Mijin buzuwa a zaton ka zaka iya rabani da hajiya mamane ko ka zubar min da mutucina da take gani kayi kuskure wallahi kuma kayi karya don bakina da naka ban fada ma hajiya mama tana gida an mata rasuwa ba.
Ga wanda yasan mutuncinta yasan darajan ta na fadawa shida ya tambaye ni ko ina da labarin su bakai da buzuwa wace bata da daraja da galihu tasa ka zubar da matan ka da yayan ka da kowa naka kana ganin tsohuwar buzuwa tana maka rudi da huduban shedan kullun.
Kai bari ma kaji wallahi wanan buzuwar ta zubar ma da kima da komai naka a idon duniya tunda kiri kiri ta mai dakai mijin hajiya.
Ga mutum har mutum amma baida ta cewa saboda mace macen kuma buzuwa wace bata san Allah how dear you kaida mace bata bari ka zauna dako matar sunnan ka har kake da bakin yi mun hadi a wurin mama, , , ,
Jikin shi har rawa yakeyi da yake karata text din kasa kai kashen rubutun daki ya nufa da sauri da zuman ya shiga yai wanka ya fita ya samu Yusuf shida yaja mashi rene da wullakanci wurin yar karamar yarinya harta iya turo mashi text din banza haka.
Sai yayi magani na a garin sai yasa na raina kaina may nike dashi may nake takama dashi da zan iya yimai cin fuska haka ina aibanta shi shi da matar shi.
Waya ya fada min maganan da sukayi da hajiyan su hajiyan ne zata fada min kowa komai dai may nene sai ya rena min wayo sai na gane banda wayo yau a garin nan duk inda na shige sai ya tononi a cikin garin nan yayi min wulkanci
Sai dai yana shiga dakin su kuma sai bacin ran nashi ya karu ganin Nafisa kwance tana barcin ta hankali kwace rashi ne ya kara baci ya tuna abinda nace a text dina.
Bai san lokacin da ya isa wurin ta yakai mata mugun maka a tsakar bayan ta ba ta mike firgigit tana fadin Samad may nayi maka ?
Tsawa ya daka mata yace wanan abin zai hada ni dake ke sai yaushe ne zaki rike ibada a zuciyar ki ne yaja tsuki ya shige wanka.
Da sauri ya watsa ya fito ranan ya fito bai wani dauki dogon lokaci ba ya shirya ya fita daga gidan koda ta fito ta samu baya gidan.
Tun a mota ya kira Yusuf yana fadin kana inane yanzu?
Gani gidana ya bashi amsa OK kajirani ganin zuwa yanzu gidan yace eh mamaki Yusuf yaji yana tunanen mai zai kawo Samad gidan shi wanan lokacin haka.
Don ka idar shine sai takwas yake fitowa ko takwas da rabi ware hannu yayi alaman shi ya sani ya mike ya shiga wanka kada yai mashi girshi.
Yana shiri ya sake bugo mai waya gashi kofa gidan shi ya fito ya karasa ya fito ya samay shi don ko driver bai fito dashi ba Yusuf din na gani haka ya rufo gidan nashi ya fito ya samay shi.
Anan ya bude mai mota ya shiga yarufe sai ya dauki hanya batare da yasan inda zasu nufa ba sai yaga ya miki mashi wayan shi duban wayan yake da mamaki yake fadin na maye wanan kuma ?
Ka duba mana cewa fuska a daure ya karbi wayan ya fara karantawa a hankali yana sake murmushi ya gaba yana mika mai wayan yace kai amma wanan yarinyar takai jaruma wallahi haduwan zai zama abin shaawa ga mai kallo.
May ne kace yanzun kai baka ga abin jin haushi ba a nan yace ban gani ba sai ma wani abin da na hango na daban tsakanin ka da beauty din.
Yau sai nanu namata ita ba kowa bane a garin nan sai na wullakanta ta a garin nan dariya yayi sosai yace da kaima kan ka wallahi da ka tozarta kan kuwa.
Wai kaiko kaga yadda kukai balain dacewa da yarinyar nan kuwa wallahi ni abin naku burgeni yake yi idan kuna yi har wani dadi nake ji.
May kake nufi ne wai yace abinda idona ya hango min mana a kai saidai fatan alheri amma zancen ka ci mata mutunci bai taso ba ko kaje ka tozartata duk ba wanan a tsakanin ku ko kamanta da hikimar hajiya na hada ka da wanan yarinyar ne ko kana nufin kai baka gane hakan ba.
To bari kaji Khadija itace zata iya fitar dakai daga zargin da ake maka na cewa Nafisa ta gama dakai da cewan da ake saboda ita ka kasa zama da Fati.
Akan wani dalili zata fitar dani ta yaya din zata fitar dani yace muje zuwa nan gaba zaka sani idan lokacin hakan yayi yanzo ina zamu ne kadauko ni tunda safe haka.
Wurin ta zamu in gwada mata ita din ba kowa bace ya kwashe mai da dariya yace ta zama kowan ke nan tunda har zaka iya biye ma shirmay ta na mata.
Bai kara magana ba sai juya kan motar yayi zuwa office din su ya shige bai tsaya jiran Yusuf din ba.
Anan malam musa driver ya tsayar dashi yana fadin yana da magana dashi na siri da yake son suyi a tsakanin su yace da malam sani din wani abu ya faru ne yace eh to sai dai maganan nason siri gaskiya yace dashi babu damuwa kasa may ni a gida da yamma idan mun tashi.
Ga haka suka bar zancen da malam sani din sai dai ya barshi da tunane a zuciyar shi ko akan may yake bukatan kebewa dashi bai sani ba ya san dai abune mai muhinmanci sosai.
Shiko gogan acikin office maganan da sukayi da Yusuf ne yake ta mashi yawo arai wai zata zama mai garkuwa a kan matsalan shi da Fati da Nafisa ta yaya ma haka zai faru .
Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi yana tuna zancen a zuciyar shi.
Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida.
Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina.
Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan makaranta.
Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba.
Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu turo mata da sako ba.
Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta.
Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone .
Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da hannu kawai ta nufi wurin ta dauka.
Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana wai ban rage abinci ba in bata.
Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici abinci bane acan ?
Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau.
Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty.
Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin.
Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya dai saka ido ga alamarin ta kawai.
Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa.
Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai.
Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta.
Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi.
Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman babban titi.
Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin.
Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso.
Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin .
Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin.
Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke yake.
Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai yana tambayan shi ina ne nan kuma ?
Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa Yusuf din.
Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata .
Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi mashi.
Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai.
Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga muje don ki kawai muka biyo nan fa.
Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah ku bani minti biyu in dawo.
0 comments:
Post a Comment