{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
Godiya ta tabbata ga Ubangijinmu daya halicci alk'alami, yasanar da bawa abinda bai saniba.
Salati da aminci da d'aukaka su k'ara tabbata ga farin jakada,babba d'an Abdullah Muhammadu-Sadiqul-amin,da alayenshi da sahabban shi da wad'anda ke kan tafarkinshi har zuwa ranar rarrabe tsak'anin k'arya da gaskiya (Alk'iyama).
Godiya ta musamman ga Umar Dalha.Dakai muka kai ga gaci.
Kima:-
Kimarku muke gani Katsinawan Dukko d'ak'in kara,mun gaisheku gaisuwar kima, musamman Maskawan k'aramar hukumar Funtua da ahalin Muhammadu Me-ruwa dana Tankon Marka anan BCG,dana garin Gadagau.
Dan tunawa da:-
Gwanarmu a duniyar marubuta littafan Hausa.
Marubuciyar 👇
{Dare ga mai rabo...}
Halima Abdullahi (Amma).
My One & Only Aminu A.Baba.
Lovely Sister Badi'atu Ibrahim.
Son Aliyu Yahya Namadi.
Little peerless Ali Yahya Namadi (Malam Garga)
Ubangijinmu ya kyautata makwancinku😭👏
Sadaukarwa:-
Ga d'aukacin Hausawa da Fulani...musamman Ya'yan Ibrahim ako ina kuke a fad'in duniya...😊
...GWAJIN DAFI 💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na d'aya.
A kwance yake cikin damuwa, hawayen da suka cika idanunshi suka fara zubowa ta gefe da gefen fuskar shi suna gangarawa jikin matashin daya d'ora kai,a haka bacci ya d'aukeshi.Da sallama tashiga dak'in,kwanan abincin tabud'e, yananan yadda tazubashi, ALLAH ma yasa ya bud'e ya ga abinda yake ciki,da sanyin jiki tad'ago tana kallanshi,bacci 6arawo kamar yadda ake fad'a,to da alama saceshi yayi,tagirgiza kai cikin tsantsar k'aunarshi da tausayin halin da yake ciki,komai yana nan rad'am kamar yan awannin da suka shud'ene abin yafaru.Tausayin shi yadad'a mamayar zuciyar ta,dak'yar tamik'e daga tsugunan zuwa D'akin-girki tad'ora musu abincin rana.Bata koma dak'in ba sai da aka fara kiraye-kirayen sallar azahar daga mabambantan masallantan unguwa.
"Julaib... Julaib... Julaib...
Cikin natsuwa take kiranshi.Dak'yar yabud'e idanunshi da sukayi jawur saboda damuwa ga kuma bacci me nauyi daya kamasu.Tad'anyi murmushi"yi hak'uri na katse maka bacci lokacin sallah ne yayi.Yabita da kallo kamar bai fahimci abinda tafad'a ba.Tabud'e baki zata sake magana sai kuma tayi shiru tawuce dan sauke nata faralin.
Yana dawowa daga masllaci takawo mishi abinci "Ta kalleshi,barka da dawowa" a zuba maka yanzu ne?"shiruma amsace. Yad'auke kai daga kallan da take mishi.Da sigar rarrashi tazauna agefenshi"Julaib... kayi hak'uri,zama da yunwa ba shine mafita ba,ba shine zai magance damuwar zuciyarka ba,zama da yunwa k'ara dagula maka lissafi kawai zaiyi, Dan ALLAH Julaib kadaure kaci kome k'ank'antar shi zai samar maka da natsuwa, natsuwarce kuma zata ba ka dama na tsayawa kai da fata wajan yawaita addu'a agaresu.Tazuba mishi faten waken dayaji kayan had'i k'amshinshi yagauraye d'akin."Dan ALLAH kadaure kaci, tamik'a mishi farantin amma yak'i kar6a, tabishi da kallo tana murmushi "To abaki zan ba ka? Tad'ibo a cokali indai hakan kake so ni a wajena abune me sauk'in gaske,takai cokalin tsakanin la66anshi na sama dana k'asa"Haaa bud'e bakin ka kaci kayan k'arin lafiya da gina jiki.
Dakata haka malama!
Yajuyo da 6acin rai me yawa a tashi fuskar yana mata wani irin kallo data kasa fassarawa"ni na ce miki inajin yunwane?Ko nasafe ban ciba amma kin sake dafo wani saboda almubazzaranci?Tabud'e baki zatayi magana yayi saurin katseta"Keee! kwashe kayanki ki fita bana san hayaniya.!Yahaye gado kanshi na mishi wani irin matsanancin ciwo kamar ana buga mishi guduma.
Tabishi da kallo cikin mad'aukakin mamaki,tsawon zamansu da duk halin-ko-inkulan dayake mata tana mishi uzuri,akwai damuwa me yawa atare dashi,to amma yau itace rana ta farko daya 6ata mata rai,cikin raunin murya dake shirin fashewa da kuka tace"Julaib... hawaye masu d'umi suka zubo mata sharrr... Julaib...dama na san baka so na,to yau na dad'a tabbatar da hakan,na zama maka matsala ko?Adole kake zaune dani ko? Tasauke numfashi toh, ai ALLAH yanaji yana kuma gani na yi iya iyawata dan kawar da damuwar zuciyarka amma hak'ata bata tadda ruwaba,na sani za fi da rad'ad'in da kakeji bazai ta6a barin zuciyarkaba matuk'ar kana numfashi a doran k'asa, to amma ya kamata ka sassautama ranka,"Shekaru uku ba kwanaki uku bane"A shekara kwanaki d'ari uku da sittin muke dashi,to kwanakinnan sun ninka kansu har sau uku,kaga kwanaki dubu d'aya da tamin,kwanakin da sukayi a mace kenan"kukan mutuwa baya dawo da matacce"kasama ma zuciyar ka salama kayi rayuwa kamar yadda kowani d'an Adam me numfashi a doron k'asa yake yinta.
Julaib...to wai me yasa baka jin tausayina na mace me raunine?Tasake binshi da kallo sai kuma ta gyad'a kai,saboda kawai baka so na?To shikenan amma ina so kasani ni har kwanan gobe ina k'aunarka duk da bana samun irin kulawar data dace,ni na yadda da abu daya,aure bautar Ubangijjne dan haka zan cigaba da dauriya dan nima kamar yadda Abbana yafad'a min"ina kwad'ayin babban rabo a gidan gaskiya(Darul-karamah)ni zan sauke nauyin dake kaina,amma tunda ba ka san ganina,ba ka san abincina,ba ka san hayaniya da duk wata kulawa tawa to ko Insha-ALLAH zan kiyaye, zan killace kaina a d'akina,amma fa k'ofata a bud'e take ina maraba dakai,a duk lokackin dakake da buk'atar tallafina kasanar dani kai tsaye,ni kuma zan baka tallafi irin wacce tadace da buk'atarka, karambani ne dai bazan kuma ba tunda kai ba a maka gwaninta...
Tajuya da gudu zuwa d'akinta, gado tafad'a tana wani irin kuka, kukan data kasayi agabanshi hawayen sharrr...sharrr...suke zubowa, tad'aga hannayen ta sama"Ya ALLAH kataimaki mijinah...kayaye kunci da damuwar zuciyarshi, kamaye hakan da natsuwa...Ya ALLAH Ju..Jul.. Julaib..d'in...sauran kalaman suka mak'ale saboda kukan yaci k'arfinta,takifa fuskarta a jikin matashin hawayen nacigaba da zubowa.
Kalamanta sun sanyaya mishi jiki, yarintse idanunshi da k'arfi yana jin kanshi kamar zai rabe gida biyu,"Wayyo ALLAH nah?!yafad'a a wahalce yasa tafukan hanneyen shi yak'ank'ame kan,jijiyoyin wajan sun fito rad'am kamar shatin bulala suna kuma harbawa da k'arfin gaske. "Wai...Wayyoh ALLAH...!Sai yafara fad'in "Babu tsimi babu dabara sai ta Ubangijjnmu.wucewar wasu dak'ik'u ciwon kan yad'an sarara mishi...sai kuma zuciyarshi tafara tunatar dashi.
"Iyayanta sun maka halacci, sun maka karamci,sun taimakeka a lokacin da kake buk'atar taimakon,lokacin da ba ka da kowa ba ka da komai, lokacin da ba ka san a wace duniyar kakeba.
Ruqayya matarka tana sanka tana k'aunarka,ka ga haka,ka kuma san da haka tun ganin farko daka mata bayan ka bud'e idanunka tsawan kwanaki,makonni da watanni a wata duniya daba zaka bada labarin wani abu guda d'aya na cikin taba,idanunka da ita suka fara yin tozali,haba Julaibib wannan ba halin girma bane,dan halal ai baya manta alheri,sai dai me halin kaji"Ci ka goge baki"abinda yake damunka bai shafe taba,ba ita takar zomo ba bai kamata ta d'auki rataya ba...
Kai musulmi ne kayi imani da k'addara kuma yana daga cikin cikar musulunci, wannan al'amarik'addararrene tun daga lauhul-mahfus.. Zuciyar shi tacigaba da tunatar dashi. Yasauke numfashi da ajiyar zuciya, k'irjinshi ya mishi nauyi yana kuma mishi suya,yahad'iye wani zazzafan abu kamar garwashin wutan da aka bad'e shi da dakakken barkono d'an munci.
Yamik'e zaune dak'yar sannan yaziraro k'afafunshi k'asa zaije ya rarrashi Ruqayya dan yana jiyo sautin kukanta, amma jirin dake shirin kaishi k'asa yasa yakoma yazauna ranshi ba dad'i...Yanzu ace mahaifin Ruqayya yashigo,ya zaiji idan yajiyo kukanta?Tabbasss ko bai nuna ba amma bazaiji dad'iba,gaskiya iyayanta sun maka karamci fa.Yajijjiga kai cikin gamsuwa,sai yamaida tafukan hannayenshi yarufe fuskarshi cikin tunanin rayuwarshi.
➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿
Zonkwa ne shalkwatar (Headquater) k'aramar hukumar Zangon-Kataf d'in kudancin Jahar Kaduna.Babban garine matattarar jama'ar sauran jahohin Nigeria da sauran yankunan nahiyarmu ta Africa,mutanan Zonkwa wayayyun mutane ne saboda masu ilmine,babban abun sha'awar,yadda ake zaune lafiya duk da tarin bambance bambance ta fuskar addini da al'adu,ga kuma k'asar noma me albarka.Manyan yaran wannan yanki guda biyu ne Kaje(Kajawa)amma bayan yak'in Zangon-Kataf sai suka zamanantar da sunan suka koma kiran kansu da Bajju.
Baranzan da matarshi Zamburan sune asalin tushen Kaje,su d'in mafarautane da suka taso daga yankin Bauchi da Jos,ance saboda sunk'i kar6an jihadin D'anfodio.ance kafin su k'araso nan, matarshi Zamburan da wasu daga cikin tawagarshi sun mutu,amma ita Zamburan ta mutune a garin Forest sai sukazo suka kafa sansaninsu a saman dutse suna kiran wajan da Kufai(Kufayi) kamar yadda akasan maguzawa nayi a can bayan gari, amma yanzu gine gine ne masu ban sha'awa awajan na sarkinsu (Agwam Bajju) hausawa masu yawan fatauci suna zuwa harkar cinikayya irin ta da,ta bani gishiri in baka manda a tsakaninsu,ga zaman lafiya, zaman lafiyar da tasa idan sun shigo cikin gari talla sai da kayayyaki kamarsu citta,daddawa,zuma dasauran dangogin su,indai kuna shiri kukace kuna son yarsu ko d'ansu to ko Insha-ALLAH zasu baku sun kuma zama naku har abadan duniya,lokaci zuwa lokaci idan sun shigo cikin gari za suzo suganku, kuma zaku kaisu wajansu lokaci zuwa lokaci.ALLAH Alhakimu sunk'i musulunci,amma sun bama musulmai kyautar mutum sukutum da guda,sun kuma san musulunci da sallar za suyi,sai su taso su girma suna musulmai,d'aya daga cikin k'ananan yaran da suka taso a cikin musulunci yar asalin k'auyan Narom ce...Itace Khadijatul-kubra inda wasu bayin ALLAH mutanan Daura su suka nuna soyayyarsu gareta mahaifanta kuma suka yadda suka bar musu ita,Bintan Daura tazama uwa a wajanta,mijinta Garban K'aura yazama uba a wajanta, tagirma suka mata aure itama ta hayayyafa d'aya daga cikin ya'yan data haifa itace kakarsu Sudaida tawajan uwa,kuma shi Abubakar (Garban K'aura) aikin d'an sanda yakawo shi garin Zonkwa shekaru masu yawa,suka zauna a gidan Amasaye itace kakar,kakarsu Sudaida ta wajan uwa.
Asalin wad'anda aka tarar a k'waryar cikin garin Zonkwa Fulanine masu kiwon shanu,da mutane suka fara yawaita sai suka tashi suka dad'a nausawa cikin daji kamar dai yadda al'adarsu take, dan shanunsu su samu wadatacciyar ciyawa da ruwan sha,ba tare da sun takurama wani ba,shima kuma bai takura musu dasu da shanun suba,Ance adai-dai wajan da aka tarar da Fulani makiyayannan anan wajan aka gina musu k'aton masallacinsu na Juma'a kuma masallaci na farko a garin,kusa dashi aka gina gida da Limamin da masarautar Zazzau ta turo musu dan yadinga musu limanci,yana kuma karantar dasu addini.
Ibrahim Nabarandi asalin Bakatsine ne masu yawan fatauci,bayan tashin Fulanin nan shine yak'afa cikin garin Zonkwa,gidanshi babban gida ne kun dai san zamanin da daba siyan fili a ke yiba kai zaka shaci yadda yamaka kayi gininka, shine yazama Sarkin hausawa,duk wani bak'o a gidanshi yake sauka kafin a bashi muhallin zama.Manyan zauruka(soraye) irin nada sun kai goma anan duk wani bak'o indai namiji ne zaiyi zamanshi,mata kuma akwai d'akuna a cikin gida da aka gina musamman saboda irinsu,suna mishi kirari shi Ibrahim Nabarandi da:
(Naladi bawan bak'o,yan gari kuma bayinka)
Su kuma Kataf(Katafawa)suma bayan yak'in Zangon-Kataf d'in sai suka zamanantar da sunan suka koma kiran kansu da Atyap,Su kuma ana tunanin asalin maguzawan Kano ne suka fito suka kafa sansaninsu a wajan,Masu yawan fatauci musamman Kanawa kowa ai yasan mutanan Kano ba cima zaunan al'umma bane,harkar kasuwanci a jininsu yake tun tale-tale,idan suka zo a nan suke ya da Zango bi ma'ana suke hutawa daga doguwar tafiyar da sukayi,bayan sun huta sai su shiga k'auyuka da sauran garuruwa dan harkar fataucinsu, to dalilin hakan garin yasamu wannan suna na Zangon-Kataf...Shi kuma asalin ma'anar"Zango Ciwon kurkunune"da yake fito ma mutum a k'afa,ko ad'an yatsa sai yakasa tafiya saboda tafiyar k'asa da akeyi a da bana wasa bane,wani zarene yake fitowa a wajan sai yayi kamar zai tsinke yatsa ko k'afar,to a inda mutum yazauna zaman jinyan da zaiyi har sai ya warke zai iya tafiya,to sauran abokan tafiya ba jiran mutum za suyiba,to idan aka had'u da wasu,ko kuma suka koma gida sai afara tambaya"ina wane? Sai abokan tafiyarshi suce ai ya ya da zango.
Akan kasuwa akayi wannan yak'in na Zangon-Kataf,su Katafawa sunce sai dai a tashi daga inda ake cin kasuwar a koma inda su suke so, tak'amarsu ai sune tushen wajan,kowa yazo a bayan sune,dan haka yadda suke so dole haka kowa zaibi,Su kuma Hausawa da Fulanin wajan sukaja tunga ALLAH yakashesu kasuwa baza ta tashi daganan ba...Kaya-kaya-kaya kowa yaja ya kafe nashi ra'ayin za abi... Atakaice kenan.
Sarkin Zazzau na wancan lokacin adalin sarkine,daya samu labarin bayyanar wad'annan mutannan sai ya turo wakilanshi dan su musuluntar dasu, sai dai kash... Wakilan sarki sunci amanar sarki basuyi abinda yakamata ba,sai suka bi yarima suka sha kid'a,suka sasu a k'angin bauta,su kama mata da ya'yansu wacce duk tamusu sumata fyad'e,su kwashe musu katti majiya k'arfi su tafi dasu masarautar Zazzau a matsayin bayi dan haka akwaisu da yawa a masarautar Zazzau,d'aya daga cikin ire-irensu shine Yakowa wanda har gwamnan kaduna yayi kafin ya mutu,shi yasa suke wata wak'a wai (Ba zamu ramaba ALLAH ne zai rama mana🤔)
Suka tafi suka bar baya da k'ura dan da yawan matan da suka ma fyad'e sun samu ciki kuma basu zubar ba sun haihu sun mayar da ya'yan irinsu kaico! kuma da yawansu an turasu Biafara Inda Ojuku shima ya jazama k'abilarshi ta Igbo haramcin yin shugabancin k'asar Nigeria har abadan duniya"garin neman gira an rasa idanu"Bayan yak'i suma sun kwaso ganimar yak'i,duk macen data musu suma sun taho da ita yankinsu dan suma anjaza musu salalan tsiya tunda basu da kowa duk sun mutu a wajan yak'i.
Suna cikin k'unci da damuwar abinda aka musu kuma ba daman ramawa kasancewar su bayi sai ga bayyanar wakilan kiristanci(Missionaries)Su basuyi abinda wakilan Sarkin Zazzau suka yiba,suka taimakesu da duk irin taimak'on dasu kaga ya dace su basu, suka dinga musu wa'azi akan addinin kiristanci (Christianity) shine addinin gaskiya,su kuma sukayi na'am da hakan suka rik'e addinin da hannu biyu,nan da nan suka waye ga kuma bayyanar ilmin boko an gina musu makarantu,asibotoci da duk abinda ake buk'ata,shine sai suka bar zaman kan dutse suka kafa k'auyuka da garuruwa suka warwatsu tunda dama sunada mugun yawa, kamar irinsu:-
Fadiya.
Fadan Kaje
Madauci.
Madakiya.
Katsit.
Kamurun Kaje.
Ladduga.
Zonkwa.
Da sauran su kuma ance wasu daga cikin sunayen Ya'yan uban Bajju d'inne Baranzan aka sama k'auyuka da garuruwan.
Suma Katafawa suka kafa nasu k'auyuka da garuruwan kamar irinsu:-
Asha a wuce.
Bakin gogi.
Dama kasuwa.
Mashan.
Unguwan wakili.
Gora Bafai.
Samarun Kataf.
Zangon Kataf.
Da sauransu da sauransu.Amma duk da haka Kajawa da Katafawa(Bajju da Atyap) masu yawan gaske sun zama musulmai iyaye da kakanni,suna kuma musuluncin da gasken-gaske,d'aya daga cikinsu Maryam Gid'ad'o Idris, inda tazo garinsu Samarun-Kataf tagina asibiti, masallacin juma'a da makarantar addini me suna
(HAYATUDDEEN ISLAMIYYA SAMARUN-KATAF)
Musulman wannan yanki Hausawa da Fulani sun amfana kwarai da gaske da wannan makaranta wanda ta sanadiyyarta suka fara halartar gasar Musabak'ar Alqur'ani me girma ta Jahar Kaduna,dan manyan malamai masu addini tad'auko daga Bauchi da Adamawa,sai wasu daga garin Samarun-Kataf,da Zangon-Kataf da Zonkwa, sune suke koyarwa.
Shekaru masu yawa sun shud'e, an cigaba da mu'amala cikin kwanciyar hankali kowa yana neman kud'inshi lafiya lau.Wannan kenan atakaicen takaitawane.
Doctor Julaibib Abdullahi D'ansarai asalinshi d'an D'ansarai ne,k'auyene dake k'aramar hukumar Malumfashi a Jahar Katsina,suma a wayansu suke saboda ilminsu,shi k'wararran likitan mata da k'ananan yarane,yayi aiki a jahohi biyar daga nan gwannati ta turoshi wannan gari a matsayin babban likitansu,garin yama Doctor Julaibib dad'in zama shida Iyalanshi,yayanshi guda uku suka cigaba da karatunsu,suma sauran yan'uwa na D'ansarai duk wanda yazo dan ziyara sai garin yamishi dad'in zama dan haka sai yanemi canji aiki yadawo nan da iyalanshi suyi zamansu,da haka danginsu na D'an sarai suka dawo Zonkwa gaba d'ayansu aka cigaba da hayayyafa.
bayan ya gama aikin aikin gwannati (retired) Sai bai koma D'ansarai ba,yan'uwa da zai koma ko dansu to suna zaune anan,yagina k'atan gidanshi yacigaba da rayuwarshi a haka har Ya'yanshi suka girma sukayi aure,da matar d'anshi Bishir ta haihu sai Bishir yama Babashi kara yasa sunan mahaifin Doctor Julaibib wato Abdullahi.Ai ko Dr.Julaibib yaji dad'in wannan kara dan haka yad'auki san duniya yad'orama Abdullahi,kome nashi na Datti ne kamar yadda yake kiranshi,Abdullahi ya taso cikin gatan daya zarce na duk sa'anninshi.
zai shiga aji d'aya a secondary ALLAH yama Doctor Julaibib rasuwa mutuwar data dakesu sosai,sannu ahankali kuma zafi da rad'ad'inta yanata raguwa,kafin matarshi tagama idda itama tace ga garinku nan.
Mahaifansu suka cigaba da kula dasu.koda yagama Secondary sai yafad'ama mahaifinshi yafi sha'awar kasuwanci fiye da cigaba da karatun boko,mahaifinshi yayi na'am da hakan duk shi d'an boko ne ma'aikacin gwamnati, yace kowa da abinda yake sha'awa a rayuwarshi, idan aka hana mutum abinda ya keso to an shiga hakkinshi, sai dai idan abinda ya keso d'in shari'a bata yadda dashi bane.Yakawo kud'i masu tsoka yabashi tare da mishi addu'ar ALLAH ya sanyama kasuwancin na shi albarka.Haka rayuwa tacigaba da tafiya kamar yadda tasaba har suma mahaifan nasu suka kwanta dama.
Alhaji Abdullahi dattijon arzik'ine, matarshi ta aure guda d'aya da albarkan ya'ya uku, Karima,Asma'u da kuma autansu Julaibib da suke kira D'ansarai,musamman mahaifinshi.Alhaji Abdullahi yanaji da Julaibib sosai dan bai manta gata da soyayyar da Dr. Julaibib ya mishi ba.
Julaibib ya taso cikin tarbiyyar musulunci,ALLAH sai yatarfama garinsu nono yarone me jin magana,duk yadda iyayan nashi suka d'orashi a haka yataso.Yana gama secondary yasamu gurbin karatu a Kaduna State College Of Education(KSCOE)Gidan-Waya,shida abokinshi kuma d'an uwanshi Musaddiq.Duk wata d'awainiya ta karatun Alhaji Abdullahi ne yayita ba tare da mahaifin Musaddiq kuma Kawu a wajan Julaibib d'in ya bada ko sisin kwabo ba.
Alhaji Ibrahim shine aminin Alhaji Abdullahi tun zamanin k'uruciya abin kuma bai rusheba har girma,Alhaji Abdullahi shi yaga kanwar abokinshi yace yanaso itama ta amince aka d'aura musu aure.
➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿
Ibrahim Me-Lambu shine tushensu Alhaji Ibrahim,dan haka Ya'ya da jikoki da Ya'yan jikokin gidan suna amfani da Me-Lambu a k'arshen sunayen su na makaranta,wasu ma da wane ko wance Me-Lambu suke amfani.Ibrahim Me-Lambu ya samu sunan Me-Lambu ne saboda sana'arshi ta saida kayan lambun kamarsu:-tumatur,tattasai, albasa, alaiyaho,yalo,latas, karas,lafsir da sauransu da sauransu.
Asalinsu yan k'aramar hukumar Tsanyawa ne ta Jahar Kano.Cirani yakawosu garin Zonkwa Iyaye da kakanni,dad'in garin da kuma k'addarar ALLAH inda ya rubuta maka zama to ba makawa anan d'in zaka zauna kome dad'i ko rashin dad'in waje,da suna zuwa ganin gida daga baya suka daina sai kalilan daga cikinsu dan suna da yawan gaske a Zonkwa,wasuma basu da sauran dangi na jini a Tsanyawa,Unguwa gudace dasu k'atuwa ta musamman da ake kira"Lungun Kanawa.Sukayi zamansu a nan suka hayayyafa.
Alhaji Ibrahim matanshi na aure guda biyune,Mama itace uwargida kuma mahaifiyarsu Musaddiq,Khausar,da sauran kanninsu maza da mata.Sai Umma mahaifiyarsu Aminu,Adnan,Sudaida da tarin kaninsu maza da mata.Kan ya'yansu a had'e yake saboda matan sunada fahimtar juna,mijinsu kuma yana musu adalci dai-dai iyawarshi.
➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿
Julaibib yana zaune atsak'ar gidansu yana nazarin wani littafi duk da wancan makon suka samu hutu.Musaddiq yashigo da sallama,yad'an daki kafad'ar Julaibib "Haba malam an samu hutu kaima ya kamata ka hutafa"Julaibib yayi kamar ba dashi yake maganaba.Musaddiq ya jijjiga kai"gaskiya na gaisheka"yawuce dak'in Inna, tana zaune a inda ta idar da sallar walha,sai yasaki labulan"to barinje na dawo anjima".Daga ciki ta amsa"shigo ai na idar.Yazauna suna gaisawa,sai yafara mata hirar Safiyya budurwarshi da sak'on data bashi yakawo mata.
Aminu shima yashigo da sallama yana fad'in shi wai D'ansarai baya gajiya da karatune Inna?Yakama ha6arshi da hannun dama"Tabbb ina ruwan Alhuda-huda,koda yake bazai gajiba tunda yafi sha'awar zaman gida, gaskiyar magana wannan da macece da sai ince ALLAH ya kashe ya ba mijinta kakarshi ta yanke saka wallahi.Inna takalleshi"kamar yaya?Yawaiwaya inda Julaibib yake zaune"o Inna aishi ya huta da fitinar mata tayawan tambayar unguwa, zani gidan wance,anyi haihuwa zan shiga barka, zanje dubiya dan gidan wance an mishi shayi, muna da biki agabas,gobe suna a arewa,jibi tarewar yar gidan wance a yamma, zani, zani, zanin mata ai bata k'arewa.Inna tayi dariya.
Julaibib yakalleshi ba laifinka bane, ka ci bashi zan kuma rama.Aminu yagyad'a kai"Nima zan so haka,ina nan ina jira,yashige D'akin-girki yad'auko kunun tsamiyarshi yafito"Inna yau naci aikine kamar ba gobe,tun daga sallar asubahi sai yanzu zan koma gida.Inna takalkeshi da tausayi "Wayyo sannu,a lallai ka aikatu neman kud'i makahon aiki, ALLAH dai yak'aro masu albarka.Amin Inna nagode barinje in kwanta.To ALLAH huta gajiya.
Kasham...da yaransu na Bajju yana nufin abu me kyau.kuma a zahirin gaskiya wannan suna ya dace da ita dan me kyance, matsakaiciyace a tsawo,me k'irar kalangu,gata da yalwataccen gashi me tsawo da santsi,shi yasa ba kasafai take kitso ba, manyan idanunta masu maik'o(Oil eyes)da d'an k'aramin bakin ta su suka k'ara mata kyau na musamman,wankan tarwad'a ce a yanayin kalar fatar jiki,itama dalibace anan Kaduna State College Of Education(KSCOE) Gidan Waya.Aranar farko a kuma kallan farko data ma Julaibib so da k'aunarshi suka mamaye zuciyar ta ba tare data shirya hakan ba, duk tarin samarin dake mata nacin suyi soyayya sai taji ba wanda yamata nan duniya daya wuce Julaibib,ta so k'warai a ranar suyi magana amma hak'anta bata tadda ruwaba, saboda kwarjinin daya mata lokacin data tunkareshi,ashe gaba da gabanta aljani daya taka wuta.To amma me san d'an tsuntsu shi yake binshi da jifa"naci da shishshiginta yasa suka fara gaisawa duk da idan ba ita ta gaishe shiba ko zasu had'u sau dubu a rana bazai nuna yama ta6a ganin taba.
Duk inda tasan zata ganshi to in dai ba tana da lecture ba to tana wajan,yau da gobe sai ya fahimci tana neman wuce makad'i da rawa sai yadad'a kamewa,amma da Musaddiq sun saba dan suna d'an ta6a hira dan shima yana da miskilanci idan baiga dama ba,amma gangaran d'in miskilai sai "Julaibib Abdullahi D'ansarai ".
Musaddiq yana zaune a capteria yana cin abinci tazo tasa meshi tana fad'a mishi "Wallahi Musaddiq na ka sa danne zuciyata,na ka sa yin yak'i da ita,gaskiyar magana ina san Julaibib zan aureshi".
Cikin tsoro da mamaki yace kina san Julaibib?Yagirgiza kai"to gaskiya ki cigaba dayin yak'in wajan ganin kin cireshi a zuciyarki,baza ki samu abinda kike so...ta tareshi da sauri"me yasa za kace haka? Saboda baki dace dashi ba"wai d'an dambe ya d'auki adda"ni nasan Julaibib farin sani wallahi,kinga kuma addininmu ba d'aya bane. Idanunta suka ciko da k'walla,"wai yau ita ake fad'ama namiji ba zai so taba a yadda take d'in nan me kyau...
Tayi jimmm..na wucewar wasu dak'ik'u "Musaddiq kafad'a mishi "ni Kasham tanuna kanta ina sanshi,ina neman goyon bayan shi ya yadda muyi aure,na mishi alk'awari zanyi abinda yakeyi (Sallah)zanbi addininshi (Musulunci) Abincin da bai gama ciba kenan yamik'e dan zata dame shine kawai.Tabishi da kallo dan ALLAH kafad'a mishi.Ya amsa da To.
Rannan tana zaune a d'akin karatu, nazari da bincike(Library) ta ka sa yin abinda yakaita tunanin Julaibib ne kawai yacika kanta,kamar ance ta d'ago kai sai kawai gashi yashigo dak'in,yaja kujera yazauna.
Ganinshi yak'arasa kashe mata jiki, tanajin wani sabon yanayi daya tsirga ilahirin jiki da zuciyarta,gefe guda kuma tana jin takaicin k'in kar6an tayin soyayyar data keta mishi naci duk da kasancewarta k'wararriya data isa da kanta in dai a fagen hilatar d'a namiji yafad'o tarkon tane,ba wanda ta ta6a d'anama tarko bai fad'aba sai Julaibib,ta rasa me zatayi dan shawo kanshi,dan abinda takeji game dashi ba irin abinda takeji game da sauran maza bane,wani irin abune me sark'ak'iya,me zagaye ilahirin gangar jiki da zuciya,ita kanta bata san ya zata fassara shiba wallahi.Tasake kallanshi rubutu yakeyi cikin natsuwa,takad'a kai.
"Julaibib...you're an enigma".
Ahankali ta furta hakan,sannan tabi d'akin da kallo mutane dayawa sun gama abinda yakaisu sun fita,saita samu k'warin gwiwa koda zai wulak'anta ta bazai mata ciwo dayawa ba tunda mutane kad'anne. Tamatsa gaban kujerar dayake zaune,tasunkuyo tana kallan fuskarshi"Sannu da aiki Julaibib...tafurta hakan da wani salo irin na ta na yanga.Bai d'ago ya kalletaba kamar yadda take fa ta,bai kuma amsaba "shiruma amsace"rubutun shi kawai yakeyi.
Tatsareshi da manyan idanunta masu maik'o,ya mata kyau cikin fararan kayan,yau kanshi ba hula,kwantaccen bak'in gashin kanshi yanata sheki da k'amshin irin mayukan gyaran gashi da yake amfani dasu,jikinta ya gama mutuwa murus,ga k'amshin arabian perfumes d'inshi yadad'a jefata a wani irin yanayi,ta lumshe idanunta wani murmushi ya su6uce mata "ALLAH dai yakai damo ga harawa ko baiciba yayi burgima"taja dogon numfashi tana zuk'e k'amshin,ahankali kuma tafara fesar da iskar tabaki ta hanci sannan tabud'e idanunta tacigaba da mishi kallan k'auna me cike da shauk'i har yagama rubutun,yatattara takaddun daya shigo dasu a gefe, yakwashi wad'anda yad'ibo a d'akin yamayar dasu mazauninsu.
Magana take mishi amma yayi kamar ALLAH baiyi ruwan tsiran taba,ganin haka yasa tayi saurin k'arasawa bakin k'ofar da zai fita ta tare hanya sai yaja yatsaya.
Please...Julaibib...
Magana nake so muyi please...tahad'a tafukan hannayenta alamar magiya."please Julaibib, wallahi with all my heart ina sanka,kana burgeni, me zai hana ka aureni?
Yagirgiza kai"Bazan iyaba.Idanun ta suka ciko da k'walla"wai kai wannan amsar ta "Bazan iyaba"bazata bar bakinka bane D'ansarai? Wai me zan yine da zaka so ni Julaibib?Yakalli agogon dake d'aure a hannunshi nadama tana 6ata mishi lokaci fa.
Ki matsa zan wuce.Tasake kallanshi "Julaibib zanyi sallah fa...yad'ago yana mata rikitaccen kallanshi "Ki bani hanya nace ko? Yafurta hakan da 6acin rai a fuskarshi.
Yamata wani irin kwarjini data kasa aiwatar da k'udurin zuciyarta.Sai tagyad'a kai ta kuma matsawa a kofar"shi kenan zo ka wuce.Ya ra6a ta gefenta kamar wanda akace idan ya ta6ata ya gama amfani a doron duniya.
Tabi bayanshi da kallo har ya6ace ma ganinta...sai tayi d'an yak'e mak'alallun k'wallan cikin idanunta suka samu damar d'igowa a kyakkyawar fuskarta, sai kuma wani sanyi-sanyi data faraji, tsigar jikinta yana tashi alamar zazza7i yana so yakawo mata ziyara.
Harshenka zakinka idan kasa keshi yacin yeka"...
11 Rabi'a Thani 1441
8 December 2019
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2 geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in.
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na biyu.
Musaddiq yashigo da sallama, yad'auki ya zauna yasha,sannanya kalli Julaibib "sak'o aka bani wajanka...sai kuma yaja yayi shiru. Yad'an d'ago ya kalleshi"Uhun ina jinka sak'on me? Yaciro d'an k'aramin kati launin ruwan k'asa yanata kyal-kyali yamik'a mishi "karanta kagani.Kasham ce take gayyatar su party dan murnar zagayowar ranar da aka haifeta(Birthday) ranar talata a Bigard Hotel.
Yad'ago yana mishi wani rikitaccen kallo "nasha fad'a maka yarinyar nan ta daina aiko ka wajena kana zuwa kana fad'amin ko?Ya jijjiga kai"to ba laifi ka cigaba amma abinda zan maka zaka sha mamakinshi wa...bai bari ya k'arasa ba shima yatareshi"ba laifinka bane nawane ainan d'in tace za tazo tasame ka da kanta, ni kuma sanin da nayi baka san hakan yasa nace mata ka tafi Matsirga amma takawo in ajiye maka da...shima Julaibib ya tare da sauri..."na tafi Matsirga,na tafi Matsirga fa kace?To saboda me zaka min k'arya?Ganin ranshi ya 6aci yace"kayi hak'uri D'ansarai.Baice komai ba yakoma yakwanta,duk sukayi shiru,zuwa can Musaddiq yasake kallanshi."Kasham da gaske tana sanka Julaibib, ko zamu d'an lek'a matane ko na rabin awa dan itama taji dad'i yaba kyauta tukwuici.Yagalla mishi harara"idan zakaje to ni ina ruwana?Musaddiq yayi murmushi"D'ansarai autan Inna me duniya.Inje kuma?To ni asuwa?Kare da gudun laiya?Da dai zakaje dana maka kara na rakaka.
Yamik'e ni ga ka tafiya ta wajan Safiyya,yamik'a mishi hannu sukayi musafaha"Ka gaisheta.Musaddiq yad'an zaro idanu dan mamaki "Wuuu yau wace rana Julaibib yaji zanje wajan masoyiyata yace agaisheta? Julaibib yamik'e zaune da sauri,yana k'ok'arin kai mishi naushi yagoce yana dariya, ah ka ga mugu da 6allallan kafad'a kake so inji hirar"uu tambayata kakeyi?To tsaya yanzu zaka gani ya yunk'ura zai mik'e Musaddiq yafito daga d'akin da gudu yana fad'in "mu had'u a gidan Hajiya bayan sallar la'asar".
Agajiye yashigo gidan,dawowar shi kenan daga Kaduna.Yaya Karima ta tareshi "oyoyo barka da dawowa.Yauwa Yaya Karima.Yacire takalman shi masu rufi,sannan ya zauna a tabarmar tsakar gidan suna gaisawa.Inna tafito daga D'akin-girki"lale D'ansarai autan Innar shi"sukayi dariya to gashi,ruwa tabashi a k'aramin kwanan sha.
Yakar6a"nagode Inna.Da bismillah yafara shan ruwan,ruwan randan Inna me dad'in gaske ga wani irin sanyi,kowa kuma ya san ruwan randa sanyin shi baya cutarwa,ga k'amshin saiwoyin da take sawa a ciki da suke k'arama ruwan armashi wajan sha.Kad'an yarage sannan ya ajiye kwanan cikin hamdala ga ALLAH.Yakalle ta"Inna ruwan randarki gard'i da d'and'anonshi har yafi ruwan roba Swan.Sukayi dariya.
Abdullahi babban d'an Yaya Karima yayi sallama ya shigo yana rik'e da hannun k'anwarshi Kamila da take kuka."Mama ga tanan tak'iyin shiru tunda ta dawo daga makaranta,wai me yasa baki bari an taso suba kikayi tahowarki.?Ya k'arasa wajan Kawunshi cikin murna "Kawu sannu da zuwa,sannan ya gaisheshi.Yarik'o hannunshi "Yauwa Abdul yakaratu?Ya d'ibo Inibi to ga tsarabar ka.Abdul yasa hannu biyu yakar6a"nagode Kawu ALLAH amfana.
Karima takalleshi kwana biyu ka daina zumunci sai Musaddiq kad'ai yake sadar da ita."Baban Abdul dai yagaji shine yace in biyo sawu ko mun maka laifine"?Yayi murmushi yana shafa kai"Yaya Karima ba kumun laifi ba,bana samun lokacine amma Insha-ALLAH wannan Juma'ar zan shigo kin san tsarin karatunmu ba d'aya bane.Ta gyad'a kai"hakane Ubangiji yanuna mana Juma'ar.Ya amsa da amin.
Wata magana zamuyi.Sai ya tattara hankalin shi ga sauraran abinda zata fad'a."Julaibib me zai hana kafito da yarinyar da kake so a had'a bikinka dana Musaddiq?Ina sha'awa k'warai ace yadda kuke kome tare to lokacin aure ma ku angwance tare.Yagirgiza kai"ni bani da budurwa ma, ki tayani addu'a ALLAH yakawo tagari.To amin. Amma duk yan matan Gidan-Waya ba wacce ka k'yasa?Yad'anyi tsaki'ni fa ba tsayawa kallansu nake yiba,abinda yarabani daku,yakaini can d'in shi nakeyi (karatu)
Musaddiq yashigo yatarar da zancen, yace tab shi autan Inna sai a hankali kuma gashi da farin jini a wajan yan matan amma kowacce sai yace bata da kamun kai,bayan shi kanshi ya sani a shari'ance ba haramun bane dan mace ta yaba da kai tafurta maka kalmar k'auna.Musaddiq yaja dogon tsaki yana hararar Julaibib saboda tuno abinda yata 6ama yar course d'insu.....
Atikah Aliyu Kagoro.
Jikar Sarkin Kagoro ce tana da hankali da natsuwa kuma k'wak'walwannar dai Ubangiji ya hore mata shi na fahimtar karatu,Malamai ma ji da ita sukeyi bari d'alibai yan karankad'a miya.Tunda taga Julaibib tace nan duniya ba wanda yamata da aure kamarshi.sai dai kashhh...yawatsa mata k'asa a idanu.Atikah Aliyu Kagoro tayi kukan rashin shi.
Rannan tazo wajan Julaibib d'in amma bata same shiba sai Musaddiq shine take fad'a mishi zata bar makarantar saboda ba zata iya cigaba da ganin Julaibib ba bayan yace baya ra'ayinta,ita tanaso yasota da zuciyarshi ne ba yaso ta dan an tursasa shi an mishi dole ba,amma badan haka ba tana kai maganar nan wajan Me Martaba to anyi angama maye ya auri ramammiya, Julaibib zai zama mijinta dan bai isa Sarki yabashi auren jikarshi yace baya so ba"ai wata fuskar ta fi gaban mari har abadan duniya"tad'ibo wasu damin sababbin kud'i tabashi,ya girgiza kai ki barshi kawai.Sai tad'an harereshi "kai karfa ka 6atamin rai dan ka san kai ba Julaibib bane,dogarai zansa su baka na jaki".Sukayi dariya.Yagyad'a kai"wannan gaskiya ne ranki yadad'e.
Ta sake mik'a mishi"To d'an ALLAH ka kar6a.Yasa hannu biyu ya kar6a yamata godiya, sannan ya d'an kalleta"yanzu Atikah kin bar karatunki kenan?Tagirgiza kai"zan koma wajan Mahaifina a Saudi-arabia,dama tun daga yaye zamana ya d'ore anan,bayan na gama Secondary d'ina yaso k'warai in koma can in cigaba da karatu amma nace nafi san nan,ba dan ya so ba yahak'ura,saboda ni tagaban goshin Me Martaba ce,abinda nake so to dole kowa ma yahak'ura yasoshi indai yana neman zaman lafiya dashi.
Da jami'ar Abuja zan tafi amma nace ni nan nake so,ni kaina kuma ban san dalilin dayasa na za6i nan d'in ba,ashe k'addarar had'uwa ta da wannan miskilin d'an uwan na kane zai zama silar koma wata wajan mahaifina wanda dama ba abinda yake so sama da ya ganni kusa dashi,saboda mahaifiyata lokacin da data haifi k'anina ko ganinshi batayi ba ta rasu,da yammacin ranar shima abinda ta haifa yace ga garinku nan,mutuwarta ta dakeshi sosai saboda suna san juna suna zaman lafiya. Yadad'e baiyi wani aure ba,auran da yasa ke ma Me Martaba ne yagaji da ganinshi haka ya aura mishi matar. Saboda ni duk lokacin daya samu sarari yake zuwa Nigeria kasarmu ta gado.
Musaddiq ya kuma jan dogon tsaki fiye dana d'azu ALLAH yashiryeka.Julaibib yayi murmushi"amin shiriyar da ba ta ALLAH ba shirme da shiririta ce kuwa ,amin nagode".
Shi da Inna suna zaune a tsakar gida,yana 6arar gyad'a Inna kuma tana gyaran tsakin masara, jefi -jefi suke magana, saboda shirin da suke sauraro a gidan rediyo.
Assalamu alaikum.
"Inna tana nan...?
Daga zauren gidan suka jiyota.Cikin murmushi suka amsa sallamar.Inna tarage sautin rediyon "maraba da yar gidan Inna,to shigo mana kya tsaya a zaure kamar wata bak'uwa?Tashigo tana yar dariya"Inna na yi laifi na zaci kinyi fushi ne shi yasa naji tsoron shigowa kai tsaye"Dan ALLAH Inna kiyi hak'uri.Tazauna tana kallanshi"barka da warhaka Yaya Julaibib,Ina kwana.Yad'an shafa kai,tare da dauke kai daga kallan da take mishi.
Sudaida...Lafiya lau, ya karatu'?
Alhamdulillahi gashinan muna tayi ba kama hannun yaro.
Tajuya wajan Inna tana gaisheta. ALLAH Inna jiya dakika aiko mantawa nayi da aka tashi daga makarantar allo ban shigo ba.Inna ta girgiza kai"ba kome nima nayi tunanin haka.Tasa hannu ta d'ibo gyad'ar tana tayashi 6arewa,yau za musha fate kenan?Inna tace wai da dambu zanyi. Tad'an k'aryar da kanta gefen dama"kai Inna gwamma dai faten,kin san Hajiya(Kakarsu)tafi san shi,zaifi armashi ma idan Yaya Julaibib yaje yasiyo mana tantak'washi.Yad'ago kai yana kallanta"ni zanje insiyo miki tantak'washi?Tace to ai da Hajiya da Inna za musha.Baice komai ba yamik'e yashiga dak'inshi, bai dad'e ba yafito yanasa hula,yama Inna sallama yafita... Sudaida tad'an d'aga murya karfa ka manta kaji?Yak'arasa ficewa.Shiruma amsace.
Sai bayan sallar azahar suka shigo shida Musaddiq.Tace yauwa na ma huta dama yanzu nake shirin biyoku shago.Musaddiq yakalleta "ta samu kenan,idan kaji gangami da labari.Yabud'e kwanan data ajiye agabansu,tana murmushi"Yaya Musaddiq chips d'in gwaza namuku tunda baku cika san shan fateba"Yad'auki d'aya yakai baki,kai wannan yarinya da iyayi kike wai zuwa kashin rana da fitila.To Yaya Musaddiq chips lallai sai da dankalin turawa?Gobe ma da dankalin hausa zanyi. Julaibib yamik'e"kici lafiya...kai zo mutafi gidan Hajiya baza a rasa abincin arzik'i acan ba.Haushi yakamata"to wannan na tsiya ne?A ah sai dai shima chips d'in bazan ciba.
Inna tasa baki"kai baza a maka gwaninta ba kenan?Ya waiwaya ya kalli Sudaida da wani irin kallo data kasa fassarawa"ni nasa ki? Tagalla mishi harara dan ba k'aramin haushi yaba taba,shiruma amsace ta shige D'akin-girki dan k'arasa abinda takeyi.Taja tsaki"shi wannan D'ansarai autan Innan ALLAH yasawwak'e mishi".
Yana wankin kayanshi tashigo gidan, Asma'u ce ita yake bi.Takalleshi"manya ba a ganinku sai an cike foam,foam d'inma sai wanda ake buga mishi stamp.Yayi murmushi"Yaya Asma'u ban kai nan ba,wa ne kare da hantar kura?Barin dai k'arasa inzo mugaisa.Tawuce d'akin Inna suka gaisa,sai ta mik'e"barin lek'a d'akin autan na ki ko zan samu abun sawa a bakin salati.Tashige ciki tana mishi bincike. Yagama shanya kayan sannan yabita,baiji dad'in abinda ta mishi ba,gaba d'aya ta hargitsa mishi d'akin,har kayan sawanshi na cikin akwati sai da ta bincike.Yazauna yana kallanta cikin zancen zuci "Yaya Asma'u yar sa'ido ce ta gaban kwatance, da shiga sharo ba shanu,kamar wata yar C I D,kaza dai garin tone-tone wata rana zata tono wuk'ar yanka ta.
Takalleshi"kai d'akin na ka ba wani abu da mutum zai kai bakinshi zuwa uwar hanji sai tarin littafai kala-kala?Yana tattara littafan data hargitsa yace"to dama me zaki samu a d'akin talaka kuma d'an makaranta?Aike zaki taimakamin koda da yar dubu goma in k'ara na Hand-out da 'yan wasu abubuwan,kinga kinyi halin girma,ladanki yana wajan ALLAH.Lallai yaran nan ka ci abinci sauranka ruwan sanyin randan Inna.Yanzu duk cikinmu akwai wanda ke cin kud'in Baba kai harma da Innan kamar ka? "Ni?yanuna kanshi da d'an yatsanshi"sharri dai ba kyau Yaya Asma'u.Tad'an harareshi tana dariya" za ka fad'i haka mana.Yagyad'akai"ALLAH Yaya Asma'u tunda ke hajiya ce kamata yayi ace kin d'auko ma Inna yar aiki,kina biyanta duk k'arshen wata,ni jarin nawa baiyi k'wari bane dani zanyi hakan.
Tamishi wani kallo"ALLAH sarki, Inna ce za a d'auko ma yar aiki?To ina abun yake wai maye ya cinye jariri?Tabbb...kai akwai ka da san kashe kud'i na ba gaira ba dalili,amma fa harda dan baka san yadda ake wahala wajan nemo su bane.Na sani mana tunda nima ina sana'a.Ta tareshi da sauri "A ah ban yadda ba sana'ar taka har wata sana'ace da zaka fad'i wahalhalun cikinta?Kuna komawa Gidan-Waya Baba zai cigaba da kula muku da kome, kaga ai yafiku shan wahala daga kai har Musaddiq d'in,ko zirga-zirgan da yake yi tsakanin nan da Kaduna ai bakwayi.Hun Julaibib arzik'i gashin hancine rabuwa dashi ba dad'i,kabari sai ka gama karatun,ka fara sana'a ka'in da na'in sai muyi zancen. Yace to Ubangiji yanuna mana lokacin.
Dama so yake yaji me za tace, amma ai ya riga yasan halinta na rowa,indai maganar kud'ine kuma itace zata bayar tofa sai anyi tata6urza,sa6anin idan itace zata kar6a yanzu mutum zai sha dogon lissafi da sharhi.Tamike" kai ni barinje wajan Inna baza a rasa abun kaiwa bakin salati ba.Yagirgizai kai"yanzu haka da abinda yakawota gidan,kuma abun tirrrr d'in tana da rufin asirinta dai-dai gwargwado dan tafi Yaya Karima ne sa ba kusa ba, amma Yaya Karima ta fita wadatar zuci.
Da safe kafin Inna tafito ya gama had'a karin kumallo,yashare tsakar gidan,ya wanke bayi,tafito tana shi mishi albarka kamar yadda tasaba "Ubangiji yamaka albarka, yarufa maka asiri duniya da lahira.
Yayi murmus"Amin Innar mu ALLAH yabar manake, yad'an kalleta"nifa yar aiki zan d'auko miki Insha-ALLAH kafin mukoma makaranta, ayyukan suna miki yawa,ni kuma a yanzu ina san ganinki cikin jin dad'i da hutu.Tayi yar dariya"to banda abinka Julaibib ina aikin yake da har za a d'auko maiyi?Dagani sai Alhaji,idan kana garine muke mu uku fa.Tagirgiza kai "ni kam nagode,da duk ya'ya haka suke jin tausayi da soyayyar mahaifansu to da al'umma ta kasance cikin tsabta da kwanciyar hankali mara yankewa,nagode maka gaya amma kabar zancen yar aiki,kai baka san 'yan aikace-aikacen ma motsa jiki bane?Na sani Inna"to kibari asamo miki koda wacce zata dinga miki hidimar tsakar gida,ke kuma kicigaba da yin abinci.
Ga kayan motsa jikina nan ba sai ki dinga amfani dasuba.Inna takama ha6a🤔tana dariya"Wuuu rabani da wuyu"kashin k'ota"kayan motsa jiki na zamani ai sai ku,ni ina zan iya da wad'annan k'arafa da na'urori? ALLAH dai yamaka albarka autana.Yayi murmushi yana shafa kwantaccen bak'i gashin kanshi me shek'i da kyallin irin mayukan gyaran gashin da yake amfani dasu. Suna gama karyawa yamata sallama yatafi shagonsu dan neman na halali,dansu an d'orasu a kan dogara da kai a hakan kuma suka taso,ba dogara da kud'in mahaifa ba...
Yana sanye da farar shadda,kanshi da farar hula zita,sai bak'in takalmi sau ciki,kafad'arshi ta dama rataye da dudduma,dawo warshi kenan daga sallar juma'a.A tsaye yake a k'ofar gidan yana tunanin kawun nashi jarumin mutum ne me kamanta adalci a komai nashi,ga shi yanaji da mahaifiyarshi da gasken-gaske,yana mata wata irin k'auna ta ban mamaki,kafin asamu me halinshi sai an tona,dan yafifitata sama da mata da ya'ayanshi,yar gatan tsohuwa kenan data kerema duk tsofaffin k'arninta, kai ita Hajiya ALLAH yamata gyad'ar dogo sama ya'ya,k'asa ya'ya tsakiya ma ya'ya,gaba d'aya ya'yanta takwas babu k'ashin yarwa.
Kai Julaibib ka tsaya awaje kamar wani bak'o me jiran abashi izinin shiga?Hajiyace, yakalleta da murmushi"to ai dama ke nake jira "bismillah muje...Suna tafiya suna hira har suka shiga cikin gidan.Musaddiq yafito daga d'akinshi, kaga ban tsaya jiran kaba, wallahi a sahun makararru natsaya,idan su Baba suka fito suka hangoni a haraban masallaci kasan zan sha fadane.Kamar ba dashi yake magana ba yashige d'akin yad'ebi wasu takaddu zai fita,Musaddiq yakalleshi bari akawo mana abinci mana dama kai nake jira. "Bazanciba" Ah bazaka ciba kamar yaya? "Azumi nakeyi" yabashi amsa atakaice. Azumi yau juma'a? Yagyad'a kai "Eh azumin tsakiyan wata sha uku,sha hud'u,sha biyar,to yau sha uku ga wata.Yagyad'a kai"ALLAH yabada lada"yafara kiran Sudaida,Sudaida,shiru Khausar nan ma shiru sai yamik'e to ina jin basanan barin d'auko da kaina,suka fito tare shi yawuce wajan Hajiya, Musaddiq kuma yatafi D'akin-girki d'auko abincinshi.
Sha d'aya da rabi a sanda hantsi yadubi ludayi na safiyar asabar aka taso su daga makarantar allo, tana sanye da bak'ar abaya da farin hijab,da wasu littafan addini a jakar data rataya a kafad'a,allanta kuma ta rik'e a hannu.Suna zaune a dogon dakalin tazo tawuce kamar bata ganshi ba. Yamik'e da sauri yabita"haba ranki yadad'e Sudaida Sarauniyar Sinan,me yayi zafi haka idanu suke cin wuta?Takalleshi da 6acin rai"wai dan ALLAH kai baka da wajan zamane sai a cikin yan maro (Wiwi)? Zama da mad'aukin kanwa fa yana kawo farin kai. Yagirgiza kai cikin damuwa "Sudaida ba yadda zanyi da sune,ina zaune zaman jiranki suma sukazo suka zauna,wajene na kowa to ya zan musu?Khausar tazo tawucesu da takaicin Sudaida,ta rasa abinda yaja hankalinta wajan soyayyar Sinan.
Bakice kome ba.Sinan yakatse shirun. Tad'an harareshi"ALLAH yaso ka na na huce.Yayi dariya tare da shafa k'irjinshi bangaren da zuciya take.Yauwa ko kefa,kinga yanzu hankalin masoyi ya kwanta.Sukayi hirarsu sannan yataka mata kad'an sukayi sallama,yaso yarakata har k'ofar gida amma tace nan ya isa, dan tasan su Yaya Musaddiq suna wajan da autan Inna,kuma ba tasan wannan rikitaccen kallannashi me ban haushi dan ba magana zai yiba..Taja tsaki"ALLAH yasauwak'e mishi wannan halin...
Nagari ake so ba d'an gariba.
13 Rabi'a Thani 1441
10 December 2019
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD... 2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in.
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin 🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na uku.
Kasham tabaro k'auyansu Madauci da yammacin ranar talata,bayan taji sauk'i daga jinyar da tayi na tsawon awanni ashirin da hud'u.Tashiga cikin makaranta da d'okin ganin Julaibib ta kuma hango shi a inda suke zama.Tak'arasa da saurinta "Barkanku da yammaci"Maimun abokin karatunshi ya amsa"Yauwa barka dai.Tatsare Julaibib da manyan idanunta masu maik'o cikin kallan k'auna me cike da shauk'i "kai bazaka amsaba kenan?Iskar data d'ibo tama bata isheshi kalloba.Tayi jimmm...na wucewar wasu dak'ik'u tana kissima wani abu a zuciyar ta,sai tad'an motsa kafad'a any way...sai anjima. Tajuya tayi tafiyarta tana murmushi.
Julaibib my enigma man...Salonka yana k'ayatar dani wallahi"...
Maimun yakalleshi"Kai nifa bangane ma wannan bita da kulli"dukan kabarin kishiyan ba"Meye had'inka da itane duk inda taganka sai tazo wajan?... Julaibib yafad'a mishi kome.Maimun Yagyad'a kai "to ka yadda mana tunda har ta amince za tayi sallah ba kuma wanine ya tilasta mataba,ai inaga ba wata matsala,kuma kayi jihadi ne,gata kuma Masha-ALLAH kyakkyawace.Yamik'e yana mishi wannan rikitaccen kallan nashi"bazan iyaba.Maimun zai sake magana yad'aga mishi hannu"dakata haka malam, taso mu tafi.Maimun yagirgiza kai "ba d'akin da zan tafi yanzu gwamma in d'anyi shawagina.Yajuya yayi tafiyarshi to shikenan.
Yana shiga d'aki ya ajiye Hand-out, yasa hannu yana 6alle botiren gaban rigarshi tare da lumshe idanunshi a kasalance,yacireta rigar yajefa a saman kujera,ya gaji lik'is ga rashin bacci,dan baiyi wani baccin kirki a daren jiya ba saboda karatu da binciken wasu littafai da yake yi na tafsirin Alqur'ani me girma,idanunshi har wani yaji-yaji sukeyi,a a hankali yafurta"yau da wuri zan kwanta...
"Zanzo tayaka kwana...
Bazato yaji an mishi wata irin runguma ta baya,zuciyarshi tabuga dammm...dan wallahi yaji tsoro...
"Zanzo tayaka kwana tunda Musaddiq baya nan.Tafad'a cikin rad'a
Kasham...zuciyarshi taraya mishi, tabbasss ita d'ince danga k'amshin turaranta nan... Yayi k'ok'arin raba ta da jikinshi amma ya kasa,dan ruk'on kura taga nama ta mishi...
Kanshi yayi wani irin sarawa.
Tafara mishi wani salo da hannayen ta a cikin gargasarshi dake kwance lufff bak'ink'irin da sheki...kar...kar...kar...Jikinshi yad'auki rawa"baah...ba... bahh..banasooo!...dak'yar yafuzgo furucin.Tayi lallausan murmushi tad'ago kanta tana kallan kwantaccen bak'in gashin kanshi...
Meye baka so din...???
Yayi shiru.Tagyad'a kai"tayaka kwannanne baka so ko wannan din?tacigaba da mishi wani salo da hannayenta a dai-dai saitin zuciya... Jikinshi ya mutu murusss...
My enigma say something hun"
Tasake fad'a cikin rad'a da wani irin salo na ta nayanga.Yadaddage ya hankad'eta...tafad'i tabaya akan katifarsu.Hanyar fita yayi sai dai abin mamaki "talaka da mata hud'u har da k'wark'wara me gari gwauro"ta kulle k'ofar dan dama baiji shigowarta ba.
Daga kwancen take kallanshi, yasunkwui da kai,gaba d'aya ya jike sharkaf da zufa kamar wanda yad'auki awanni yana matso jiki.Wata jijiya tafito asaman goshin shi rad'am kamar shatin bulala ranshi in yayi dubu ya 6aci...Amma jikinshi ba k'arfi kona sisin kwabo kamar wanda aka zarema laka.
Sai kuma jikinta yayi sanyi, tasan itace tasashi a damuwa tamik'e tsaye"Kayi hak'uri Julaibib "tahad'a tafukan hannayenta"Dan ALLAH kayi hak'uri ba naso ace ta dalilina kashiga damuwa,danni me k'aunar kace,farincikin ka shi nake so ba damuwa ba.k'walla yacika idanunta... muryarta tafara rawa
Bazaka hak'ura bane D'ansarai?
Yadda tayi furucin a hankali da wani irin salo,yasa yad'ago zai kalleta,itama shi take kallo caraf idanunsu yahad'u,yakauda kai dasauri yanajin wani irin abu yana zagaye ilahirin jiki da zuciyarshi,shi yasa baya san kallan wannan manyan idanun na ta masu maik'o.Kawai sai ta fashe da kuka,tsoro da mamaki suka baibayeshi to me aka mata wai???
"Kasham...
Yafurta sunan dak'yar.Tad'ago da sauri tana kallanshi.Sai kuma yayi shiru kamar me koyan had'a kalmomi da yadda ake furtasu.Idanunshi sun kad'a jawur.
Julaibib kayi hak'uri dan ALLAH".
"Bakomai...Tayi murmushi yau wace rana ya mata wata magana ta daban ba amsar daya saba fad'aba na "Bazan iyaba"saita kalleshi "to za ka aureni?Yayi shiru kanshi ak'asa.Tad'an motsa kafad'a. Tana zuwa kusa da k'ofar ya matsa da sauri kamar zai hantsila.Tayi yar dariya"Matsoraci kawai "ni ba abinda zan maka yanzu amma duk ranar daka shigo nan tanuna tsakiyar tafin hannunta na maka kattt...kisan mummuk'e,sai tayi d'as d'as d'as da yan yatsunta wani murmushi ya su6uce mata. Tamishi wani kallan k'auna me cike da shauk'i...Tabud'e k'ofar tayi tafiyarta.Yasauke gwauran numfashi "wallahi da basu da lecture gobe da sassafe da yau yayi tafiyar shi gida kamar yadda Musaddiq yatafi.Yamaida k'ofar yarufe da sak'ata yasa mukulli sannan ya kwanta cikin wani irin yanayi.
Tana zuwa d'aki tafasa ihu tafad'a gado.Lidiya da suke yan'uwa kuma d'akinsu d'aya sai dai kowa da abinda yake karanta kamar dai Julaibib da Musaddiq tabita da kallo sai juyi take cikin wani irin yanayi,tabar yanka ganyen Ogu da take yi na abincin darensu,tazauna agefen gadan.
"Inzayadami Kasham?(Meyafaru Kasham)
Kasham tacigaba da juye-juyenta cikin wani irin yanayi,zuwa can kuma tamik'e zaune, tajingina kanta ajikin gadan cikin sanyin murya tace " Julaibib ne"
"Jesus Christ! Holy ghost fire!!!
Lidiya tafad'a tare da dafe kirji da duka hannayenta,tabita da kallan takaici taja dogon tsaki, wallahi kinji kunya,wai dan ALLAH me kika ganine ajikinshi daya tafi da hankalinki haka? Dogone k'akk'arfa,kar kuma kimanta Baranzan wanda kukayi alkawarin aure dashi,shima haka yake,ke ya mafi Julaibib tunda shi Sojane training d'in da yakeyi shi ko rabin-rabinshi ba ya yi, sunansu kuma d'aya"Maza"ko akwai wani abu bayan haka?Tayi lallausan murmushi"taja dogon numfashi a hankali take fitar da iskar tabaki ta hanci.Sannan tace"Hummm...Lidiya kenan ai maza kama suka tara amma halinsu ya bambanta. Tagalla mata harara"kin gama asara,ni dai banga abin so a wajen me shegen girman kai ba,shi ba kowan kowa ba dillalin kashi.Sannu wannan dazai amsa miki da yauwa sai yaga dama amma ke kina neman haukacewa saboda shi...kai tirrr...wallahi tayi d'as da yan yantsunta takoma kan girkinta tana mita Rubbish girl...
Kasham tazame takwanta"duk abinda zaki fad'a indai akan san D'ansarai ne bazai ta6a tasiri a zuciyata ba har abadan duniya, ina san shi koda shi aka tarama munanan halayen jama'ar duniya,ni na san ko waye Julaibib,ba shi da wani girman kai"so hana ganin laifi...
Suna zaune a shago jadawalin bikin Musaddiq d'in suke dad'a dubawa,dan saura kwanaki goma sha biyu.Tayi sallama daga waje tana sanye da riga da zani da dankwali na atamfa ruwan goro da ratsin k'ananan filawoyi ruwan madara da Bak'i,tayafa bak'in mayafi takalmanta bak'ak'e abinci takawo musu.
Wa alaikumussalam shigo.Tana shiga idanunsu yahad'u,yad'an saki fuska"yau Baba yayi tafiya sai zuwa yammaci zai dawo, ni kuma ban san irin garar da yake had'a muku ba idan kun kawo abinci"rake zan sha"sai Maths text book da Graph-book da za a sai mana ni da Yaya Khausar.
Banza yar k'auye,tafi kibamu waje, ba dama a tambayeta me take so sai tace"rake"to ba za a sai rakenba.Julaibib yad'aga mishi hannu "a ah malam shan koko fa kwanciyar rai,to me yamaka zafi?Yamaida kallanshi wajanta"koda yakema idan fitsari abin banzane kaza ma tayi mana.Ta sunkwui da kai"kowa yayi zagi a kasuwa ya san da wanda yakeyi,shine ko nama a wasu lokutan baya iyaci duk san shi da nama kamar kura sai gani sai hange idan ciwon hak'orinshi ya motsa.
Me kace? Musaddiq yatambaye shi fuska a yamutse.Abinda kaji na fad'a"ke Sudaida jeki ki...sai kuma yamik'e ina zuwa.Dakanshi yasiyo musu Maths da graph d'in yakuma kar6o musu gasassun kaji guda biyar,d'aya ki kaima Inna,biyu nasu Mama,ku kuma dukkanku kuyi hak'uri ku raba biyun.Tasa hannu biyu takar6i ledojin"mungode Yaya Julaibib".Yakauda kai daga kallan da take mishi.Jeki kinji karki daka ta wannan da hidimar aure tasa kanshi yake shirin yin gobara... mutum bai kar zomo ba sai kiga yana shirin ba shi rataya.Tawaiwaya inda Musaddiq d'in yake,shima su yake kallo.Sai ta toshe bakinta da sauri kar dariyar da take 6oyewa ta su6uce mata tashiga uku,idan yakoma gida da daddare zai iya bata na jaki...tajuya dasauri tabar shagon.Julaibib yabita da kallo fuskarshi da murmushi.
Yauma Musaddiq ya rigashi komawa gida tun ranar laraba yatafi,Maimun ma an aiko mahaifiyarshi bata da lafiya shima yatafi.Yana fitowa daga masallaci yanufi d'akinsu dan yanajin yunwa shi kuma yafi gane yadafa abinda zaici fiye da yaje capteria,yana da miya dan haka yadora farar shinkafa yazauna yana yayyanka kabeji, tumatir albasa da gurji.Tana jingine da bishiyar barankaci tana hangoshi dan abaranda ya zauna saboda cikin akwai zafi kuma ba wuta,tana mishi kallan k'auna me cike da shauk'i,shi ko baima san tanayi ba kunu a mak'ota.Tasauke numfashi tana kiran sunan shi a saman la66anta wani murmushi yasu6uce mata ranar da duk ALLAH yabani sa a akanka?....Hummm tagyad'a kai"d'aurin gwarmai za kasha amma na k'auna... tajuya tafiyarta.
Hajiya tashigo da sallama.Ya amsa cikin murmushi"Sannu da zuwa Hajiyarmu, yashimfid'a mata tabarma.Tace a ah mutanan Gidan-Waya saukar yaushe?Ai tun safe ina garin nan,wajejen k'arfe sha d'aya naje gida ba kyanan.Tagyada kai"Tabbas anyi haka,naje asibiti gaishe da Liman na masallacin juma'a ne.Yace "ALLAHU-AKBAR"ashe har yanzu ba a sallameshi ba?Ubangiji yabashi lafiya,zaman jinyar kuma yasa kaffarace. Ta amsa da amin,amin.Anjima ya kamata kuje kugaishe shi Yagyada kai "Insha-ALLAH.
Kai kadaine agidan?A ah Inna tana wankane"Tamishi kallan nazari"ni wannan zuwan sam baka min kyan ganiba,duk kayi wani firgai-firgai sai kace angon da hidima tasha kanshi kud'ad'en aljihu sun k'are,ko dai bakaji dad'i kwana biyu bane?Cikin yar dariya yace "to da Musaddiq kike wannan gugar zanan.Kai tafi can Musaddiq d'in wa?Shi da za a mishi auran gata,dakai nake yi.Yagirgiza kai"Hajiya ni dai lafiya ta k'alau.Cikin kad'a kai tace"amma dai sanin hali ai yafi sanin kama,idan ta kumbura tafashe tayi wari zamuji.
Bismillahi tamik'e"ni bazan zauna zaman jiran uwarka ba wannan halin nata tun na k'uruciya ashe bata barshi ba,taja tsaki haka takeyi idan tashiga bayi kamar tasamu gadon bacci da daddare,wani lokacin sai na bita da bulala take fitowa,shiga bayi ai lalurace da kake sauri ka kawar da ita kafito.Julaibib yad'an yamutsa fuska"Kai Hajiya"takalleshi saboda uwarkace sai ink'i fad'an halinta?Yagirgiza kai. Tace"to wooo ashe dai kowa yana san wawa haihuwarshi ce ba a so,dama wajanta nazo kwana biyu bangan taba"To kijirata mana.Wa?Ai tunda na mik'e sai dai kuma tabiyoni nawa gidan,tunda na ganka ai shi kenan ko baka gode bane? Aiko nagode miki ba kad'anba Hajiyarmu.Barin taka miki. Suna tafiya a hankali suna hirarsu,har gida yarakata sannan yawuce gidan Yaya Karima.Yaya Karima tadabance wallahi saboda halin dattakonta.
Rana bata k'arya saidai uwar d'iya taji kunya,ranar juma'a aka d'aura auran Musaddiq da Safiyyah,abokan karatunsu sunzo d'aurin auran nan Motoci har hud'u cike tam da jama'a.Maimun yace gaskiya garin Zonkwa yamin ba zata yadda nake tunanin garin ashe yawuce haka.Aminu yagyad'a kai"k'warai kuwa muna yin addininmu da komai namu kamar yadda hausawa,musulmai sukeyi a k'asar Hausa tunda akwai malamai masana addini a fannoni mabambanta,ga makarantu sai wanda kaza6a.
Maimun yakalli Julaibib cikin tsokana "Yah D'ansarai inane k'auyan mutuniyar takane?Na ta6a tambayarta tace min Mabushi ko Madakiya?Ko mene?Ni na manta.Shiruma amsace. Yagyad'a kai "To da alama yan miskilancin sun motsa kenan.Aminu yamik'e"Maimun zo muje muyi shawagi kaji,zama waje d'aya tsautsayi.Suka bar Julaibib a d'akin,sunyi yawo sosai har Fadar Sarkin hausawan garin saida yakai Maimun yakwashi gaisuwa,Sarki me kirki da karamci yayita sa musu albarka yamusu addu'ar sumu ALLAH yabasu mata nagari,sai bayan la'asar suka koma gida dan shirin tafiya wa'azin maza da za ayi agidan Bak'i,bayan sallar magriba aka rufe taro da addu'a abokansu suka dauki hanyar Gidan-Waya, Aminu dai yarik'e Maimun wai dole sai ya kwana.A kwana d'aya da sukayi sunyi sabo naban mamaki kasancewar duk su biyun baki abin magana ne, sukayi sallama da alk'awarin kaima juna ziyara a duk lokacin da suka samu sarari.
Yafito daga cikin dalleliyar motarshi kirar Toyota bak'a wuluk sai walainiya takeyi a cikin hasken rana.Yana sanye da kakin soja,tafiya yakeyi cikin isa da gadara dajin cewa eh ya ne kayi hattara,ka kuma kiyaye ni ko kasha na jaki.Kwan kwan kwan...ahankali yake rank'washin k'ofar kwan kwan kwan...Just come in... yajiyo muryarta daga ciki.Yasa hannu a marik'in k'ofar yamurd'a yashiga.
Yabita da kallo tana kwance ruf da ciki da kayan bacci,dasauri yak'arasa gadon ya d'agota...suka kalli juna na wucewar wasu dak'iku, sai ta kauda kai a maimakon tabashi sumba kamar yadda tasaba.Yajuyo da fuskarta yana k'ok'arin sumbantar ta amma ta fuzge da sauri. Takoma ta kwanta "Beauty...tashi muje asibiti me ke damunki ne haka? Nace maka bani da lafiya ne? Hey don't fool me,idan ba ciwo ba me zai ramar dake haka?Idanun ta suka ciko da kwallah sai kawai tafad'a kirjinshi tafashe da wani irin kuka.
Lidiya tashigo da murnan ta sai kuma tayi saroro tana kallansu,Ya juya yana kallanta. Lidiya me yasamu Beauty haka?Tad'an motsa kafad'a"Ga kai ga k'afa ka tambayi me aka yanka? Ai ita zata fad'i meke damunta.Baranzan yayita rarrashinta dak'yar yasamu tayi shiru.Ya gewaye hannayenshi ajikinta,yana mata magana a hankali "na fa shirya mana party na Birthday d'inki da akayi bana nan.Lidiya tabashi hannu suka tafa. "Good Baranzan a ina za a yi?Yakalli Kasham yana murmushi"Kasham Hotel Kafanchan"Lidiya tayi d'an tsalke tana ihu "Hallelujah".
Tad'an daki kafad'arshi ta hagu,suka kyalkyale da dariya.Tad'auki jakarta"to yah ne? Bani kud'i zanje inyi nail fixes da gyaran gashi.Ya zarosu da yawa baiko tsaya k'irgawa ba ya bata.Tak'arba tare da sara mishi"Yes Sir ta buga kafarta da dama a k'asa"Thank you Sir.Tafita da sauri.Yasaki Kasham ya kunna taba sigari, yamata kyakkyawan zuk'a sannan yafara fesar da hayak'in tabaki ta hanci cikin shakara yana mata wani kallo.
I miss you deadly Beauty...
Yamik'a mata karan taban,tagirgiza kai "No I'm not in the mood"yakalleta nifa gaskiya yunwa nakeji saboda d'okin ganinki ko karyawa ban tsaya na yiba dan nasan zaki dafamin abinci me rai da motsi amma gashi baki da lafiya "Tashi muje in nemi abinda zanci".
Tacanja kayan baccin jikinta da wando legging ruwan zinare da wata shirt checker,tana sa ma6allan gaban rigar shi kuma ya d'auko katon ribbon ruwan zinare ya tattara gashinta daya hargitse yad'aure, yana kallan d'an k'aramin bakinta daya d'an bushe dan bata shafa mishi mai ba"ni fa da yunwan kome na zo, kema kuma kin sani,amma na ga kamar hak'ata bazata tadda ruwa yadda nake so ba ko?Tayi kamar bataji abinda yake fad'aba.Tarik'o hannunshi"dan ALLAH mutafi dan idan nakoma na kwanta wallahi ba inda zani".
Yana sanye da fararan kaya, bak'ar hula da bak'in takalmi sau ciki yayi sharrr dashi,ya rataya bak'ar jaka a kafad'arshi.Daga bayanshi yaji k'arar mota, sai ya kauce gefe.Tasauke gilashin bangaran da take zaune.
"Barka da safiya D'ansarai...
Yayi kamar ba dashi take yiba, yacigaba da tafiyarshi har yasha kwanar lecture hall d'insu ya6ace ma ganinta.Baranzan yaja motar yana tambayarta"waye wannnan ana mishi magana yayi banza da mutane?Tamaida kanta jikin kujerar motar"Ina ga baiji bane dan naga da headphone a kunnuwanshi.Jikinta yayi sanyi bata so yaganta da Baranzan ba wallahi,duk maganar da yake mata tamishi shiru kamar me bacci.
Wannnan party baiyi wani armashi kamar yadda suka saba yin chasu da rawar mak'osa ayi shaye-shaye yadda a kaga dama,dan gaba d'aya bata da walwala banda ma ya takura mata da ba inda zataje, kwananshi uku awajanta sannan yayi shirin komawa Jaji Barrack bakin aiki amma yayita rok'onta idan ta samu sarari tabiyoshi,ta amsa da to,amma tayi alk'awari ba wanda zata sake bi har ta kwana dashi indai ba Julaibib ba.
Ranar talata Musaddiq baije ko ina ba yana zaune a D'akin-shak'atawa yaji ana k'wank'wasa k'ofar,yace shigo dan yasan kila Asma'u ce amma sai ta fad'a mishi dalilin ta na k'inyi sallama,amma me?Kasham yagani a tsaye. Kasham? Yafad'a da mamaki kece?Dama kinsan gidana ne?Takasheshi da lallausan murmushinta "Kabar mamaki,dan matambayi ai baya 6ata.
Naji kayi aure shine nazo tayaka murna, I'm I not wellcome? Bata jira amsar shiba tama kanta mazauni a d'aya daga cikin kujerun d'akin,tad'anbi D'akin-shak'atawar da kallo, sannan takalleshi "To ina amaryar taka?Yamike bari akirata yashige d'aya d'akin sannan ya kullo k'ofa"Safiyya takalleshi lafiya?Yarungume hannayen shi a k'irji lafiya lau,tashi kije ku gaisa wata yar makarantar muce tazo mana ALLAH yasanya alheri.Tamishi kallan tuhuma"Oh wanda tamaka a makaranta bai gamsar da itaba har sai ta biyoka gida?Yayi murmushi"Haba amaryata yaushe akai daren da gari zai waye? Kasham...she mean nothing,ai kece komai na, yafara Istirja'i, shaid'anne yake so yasak'a miki mummuna,kinji amaryata?Tayi murmushi suka fito tare.
Wani Ovation take dubawa tad'ago tana murmushi"Amarya barka da fitowa,tanuna Musaddiq kinga mijin kin nan kirkinshi ragaggene a wajena tunda har zaiyi aure amma bai fad'a minba,ni kuma ai naga abin farin cikine to meye na 6oyewa,?To koma dai yayane ba a gayyace niba amma danaji labari gashi na zo" Musaddiq ina tayaku murnar aure,kuyi hak'uri Ku zauna lafiya for better for worst.Suka mata godiya, tace haba ba komai fa,wata kilama mutumin nakane yace karka fad'amin. Kamar bai gane wanda take nufiba yace"Wa kenan? Tad'an kalleshi "Wa kake dashi a Gidan-Waya daya wuce D'ansarai?Yayi murmushi"au shi kike nufi?To ba ruwanshi,Julaibib bai ta6amin maganar kiba.
ALLAH da gaske!???
Ta tambayeshi cikin mamaki zata cigaba yatari numfashinta"Indai maganar D'ansarai zakiyi tona rok'eki kiyi shiru kawai tunda bashi da wani amfani.Yafad'a miki gaskiya... Takatseshi da sauri "Karkasa jinina ya hau,danni nayi alk'awari ko ana ha maza ha mata sai na auri Julaibib dan ina sanshi,takalli Safiyya" Madam ku taimakeni dan na san za ku iya wallahi,sallah ne dai da banayi yasa kuke k'ok'arin nisantani daku ko?To nace zan iya, ai ko bai kamata a k'wacemin gatarin danace zan iya had'iyaba...
Safiyya ta jijjiga kai kenan a yadda take magiyar nan ta dad'e tana yak'in neman soyayyarshi ALLAH ne kawai yatsare shi daga fad'awatarkonta,tasake kallanta masha-ALLAH tanada kyau najan hankali,d'an k'aramin bakin ta da manyan idanunta masu maik'o su suka k'ara mata kyau na musamman ga ta da yalwan gashin kai,gashi kuma da alama ma'abociyar kwaliyar jan hankalice,dabara tazo mata dan haka ta kalli Musaddiq cikin tashin hankali"Dama baka fad'a mataba?To bari kiji Kasham kike kowa?Ki bud'e kunnnuwanki ki saurareni dakyau"Julaibib yana da matar aure karatu ake jira tagama musha biki kuma kanwata ce,dan haka kitashi kibar min gida.Tamik'e rai a 6ace ta wuce cikin.
Takalli Musaddiq shi kuma yayi saurin kau da kai"Shin da gaske ne abinda tafad'a? Yagyad'a kai "Aishi yasa tun farko nafad'a miki Julaibib bazai aureki ba danna sanshi farin sani.Tamik'e tana sa6a jakarta akafad'a" Shikenan amma ba hakan yana nufin na hak'ura da shi bane,ku ai musulmai mata hud'u kuke iya aura,dan haka ban damu ako tanawa zanzo ba,ni dai burina in mallaki Julaibib a kowani irin hali da yanayi,zanje inyi tunanin abinda zai fishsheni.
Tana fita Safiyya tadawo.Yayi murmushi yana mik'o mata hannayenshi "Amma gaskiyar magana kin burgeni"bata mika nata hannayenba,tagalla mishi harara"Shi me gayyarma ba shiga shirginta yakeyiba sai kai,ba kamar kid'iba sai kayan ganguna? Yafuzgota da k'arfi" Haba Safiyyahhh... Kina ganin wani abu zai shiga tsakanin mune?Kasham bata gabana. Tashagwabe murya"ai ba anan takeba an danne bodari aka,ni dai kawai ko?Tad'ago tana kallanshi.Yagyad'a kai" Uhun ke me? Ni dai kawai maganin kar ayi to tun wuri kar a fara..Yayi yar dariya yana d'an jan karan hancinta"To ranki yadad'e zan kiyaye"Yakamata kuwa hakan.Sai yad'an bata marin soyayya suka k'yalk'yale da dariya.
Kwanakin Julaibib uku a Kaduna sannan yadawo ranar laraba da yammaci,wata yar Seminar sukayi da k'ungiyar"Ansaruddeen"yana rataye da bak'ar jakar matafiya,godiya yakeyi ga ALLAH daya kaishi lafiya yadawo dashi lafiya sannan yashige gidan da sallama.Inna ta amsa sallamar da murnan ganinshi "Maraba da autana "Yazauna agefen tabarmar cikin murmushi,Iyaye dad'in ganine dasu,musamman idan kayi dace da masu ilmi da sanin yakamata. Fatanshi har kullum ALLAH yabashi ikon jiyar dasu dad'in rayuwa kamar yadda suka jiyar dashi,musamman ilmin addini dana boko da tarbiyar Al'Isamiyya da suka bashi.
Yacire takalmanshi masu rufi da safa sannan yagaisheta"Inna ya zafi"?Tagyada kai "Zafi kam akwaishi,sai dai yakusa k'arewa tunda damuna nagab da sauka.Yadi6o ruwan randa yanasha yaji dad'i har ranshi saboda k'amshin saiwoyin datake zubawa aciki dan k'arama ruwan armashi wajan sha yana zancen zuci"Inna duk lokacin da bana gida ruwan randan nan naki nake fara kewa,ya ajiye kofin.To Ubangiji yabamu damuna me albarka.Inna ta amsa da Amin.Yaciro mata tsarabarta sannan yamik'e yasa takalmanshi"barinje gidan Hajiyar mu"To ka gaisheta.
Daga gidan Hajiya yawuce gidan Kawunshi,yaran gidan suna zaune a D'akin-shak'atawa suna kallo,k'ananan suka taso aguje suna murnan ganinshi"oyoyo Yaya Julaibib,oyoyo Yaya Julaibib duk suka mak'alk'aleshi dan D'ansarai indai wajan kyautane to ba daganan ba,sam abin hannunshi baya rufe mishi idanuba, suna ganin ya bud'e jaka suka fara tsalle kowa yana fad'in "Yaya Julaibib bani, a ah ni zaka ba,nima ai na iya rabo Yaya Julaibib....yace a ah bari aba babba Sagir maza kaima Khausar taraba muku, yanunata da yatsa"banda ke a ciki,rabo irin na adalci kawai za kiyi a tsakaninsu.Tayi yar dariya"To shikenan Sagir kawo ledan."waisu Mama basa nan ne? Eh sunje gidan suna. Yajuya shikenan na dawo anjima.
A zaure sukayi kaci6is,taja baya da sauri"Sannu da zuwa"ya amsa da yauwa.Daga ina kike? "Gidansu Nasmat.Ka siyo min tsaraba?Yad'an kalleta "Haba dai, babba dake acin tsaraba?Tayi yar dariya "Yanzu dan ALLAH Yaya D'ansarai wani girmane dani?Ina abin yake wai maye yacinye jariri?Ai duk girmana ban kai Hajiya ba,daga gidansu Nasmat naje gidanta na kuma tarar da ita tana cin tuffa kuma tace tsabarar dama kai matane.
To dake da Hajiya dayane?
Daga baya suka jiyo muryarshi.Tad'an karyar da kai gefen dama"Kai Yaya Aminu yanzu ni banfi Hajiya ba?
Ke dalla tafi kabamu waje, irinki goma baza su kama k'afar Hajiyarmu ba bare su fita,to ke asuwa?Karankad'a miya dake. Julaibib yace"ah to kin daiji ko?Ya tambayi Aminu"akwai ragowar kunun tsamiya a d'akinka? Kaima ka san ba a rasa nono a riga sai dai idan rigar bata Fulani bace.Yace yauwa to kije ki d'auka kiyi farau-farau dashi.Tajuya zata shige gida"ai ni kunu koda d'uminshi ba d'ad'ani da k'asa yayi ba bare ragowa, zanzo har gida in kar6a,sai kaba Innarmu ta ajiyemin koda na zo baka nan...
...Kome na rayuwa naci dana sha an halicceshine dan d'an Adam,shakeru aru-aru tun kafuwar doron duniya,za kuma kaci har kagaji,basa k'arewa sai dai kagama rayuwarka katafi kabarsu...
...Rabo na me rabo ko kura tagani haramiyarta.
15Rabi'a Thani 1441
12 December 2019
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI 💔
Daga alk'alamin 🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na hud'u.
Monday ranar aiki ko nasara na tsoronki.Ranar litini aka koma makarantun boko a zangon karatu na farko.Sudaida da Khausar sunfi kowa farin ciki saboda shigarsu aji d'aya a k'aramar Secondary,kuma a wannan lokacin aka turo yan TP(Teaching Practice) Julaibib na d'aya daga cikin wadanda aka turo makarantar su,to kamar yadda su Sudaida ke murna haka Kasham ma tayi murna dan makarantarsu d'aya.
Dasafe yashiga gidan cikin shigarshi ta fararan kaya.Yagaishe da su Mama, sannan yakalli Sudaida da take karyawa"idan kika bari nafito daga d'akin Kawu baki gamaba to ni tafiyata zanyi.Tamik'e tsaye tana addu'ar gama cin abinci nama gama barin kira Yaya Khausar sai mujiraka a mota.Gaisawa kawai sukayi da Kawun nashi yafito suka tafi.
Kasham tana zaune a farar kujerar roba a inuwar dalbejiya kullum tana ganin irin zirga-zirgan da Sudaida takeyi idan an tashi tara(break) tsak'anin wajan saida kayyakin da wajan da Julaibib yake yawan zama,da alama ita yake aika tasiyo mishi abinda yake buk'ata. Tasauke gwauran numfashi wato dai yana magana,kalli yadda Sudaida take dariya, duk yadda akayi shi yayi furucin daya sata darawa.
Bayan an koma aji yamik'e yashiga d'akin malamai(Staff Room)sai ganinta yayi zaune a tebur d'inshi magana zamuyi tafad'a cikin murmushi.Ranshi a 6ace yama rasa abinda zai fad'a sai kawai yajuya dama alli(chalk)zai d'auka to gwamma yatafi Principal Office yad'auki wani acan.Tabiyoshi da sauri"ji mana Julaibib,ka tsaya kaji abinda zan fad'a maka,idan kuma kaki to ina biye da kai duk inda kasa kafafunka.Bai saurareta ba yayi tafiyar shi,sauri yake yi har yana tuntu6e, abin yabata dariya"To wai shi Julaibib tsoronta yakeji da bayaso ya tsaya kusa da ita ko me?Ta tuno ranar data mamayeshi ta rungumeshi a Gidan-Waya yadda ilahirin jikinshi yakama rawa.Toh ni dai bana gane ma wannan tsoron naka wallahi.
Lidiya tak'araso wajan tana mata kallan takaici nama na jan kare"ai ke dai kin gama a sara Kasham,namiji yana gudunki amma ke kina ta shige mishi sai kace shine mahad'in numfashinki?Taja dogon tsaki"to kidai yi a hankali kafin dalibai su farga,dan kin san ba dad'i zaki jiba idan suka tasaki a gaba da wak'ok'in shak'iyanci.Tagyad'a kai"zan so hakan indai zasu danganta ni da Julaibib a cikin baitocinsu.Ke Lidiya bazaki gane kome ba dan baki fad'a tarkon so ba. Ai ko na fad'a tarkon so bazanyi hauka da wawanci da rashin aji a wajan da nasan ba a maraba dani ba.tawuce tabata waje."Iska dai na wahalar da me kayan kara.
A sanda hantsi ya dubi ludayi na ranar a sabar,yana zaune a shagonsu yana lissafin mutanan da suke bi bashi kuma su kai shiru mak'atau balaguro a lahira"kamar sun sha nonon uwarsu,d'ago kan da zaiyi caraf idanunsu yahad'u.Yafara ambatan ALLAH a zuci.
Tana tsaye a barandar shagon cikin shigar shadda me maik'o ruwan makuba riga da zani bata d'aura d'ankwalin shaddar ba sai ta yafa k'aramin mayafi ruwan madara a saman gyararren gashinta data d'aureshi da k'atan ribbon ruwan makuba jaka da takalmanta ruwan madara,fuskarta,ta d'auki kwalliya,ta rungume hannayenta a k'irji tana k'are mishi kallo,yana sanye cikin yadi ruwan madara kanshi ba hula saisayan dayayima gashin kanshi da k'asumbarshi sun mishi kyau,ya fito sharrr dashi k'amshin arabian perfume d'inshi ya mamaye har inda take tsaye.
Yamaida kallanshi cikin littafin amma ya kasa cigaba da abinda yakeyi. A hankali tafara taku d'ai-d'ai har tashiga shagon.Hucin numfashinta kawai yaji a gefen fuskarshi"Dan Sarai barka da hutun k'arshe mako".
Ke malama na fad'a miki kifita harkata ko ana soyayyah dole ne!?Tamishi fari da idanun ta sannan tafara magana da wani salo irin nata na yanga "Kana ganin ba a soyayyah dole?Tagyad'a kai "To ko ba ayi za a fara hakan akan mu,kaga zamu shiga kund'in tarihin duniya"Julaibib da Kasham"what a perfect match.. Wai kai sai dubu nawa kake so in fad'a maka ina sanka, zanyi sallah koda zan 6ata da kowa nawane sannan za ka yadda dani? Haba Julaibib lokaci fa yayi da zan tunkari iyayena da maganar ka,kabani goyon baya,kaga mun kusa gama karatunmu sai kawai muyi aure hankalin mu zai kwanta"kanwa ta kar tsami k'wannafi ya kwanta.Tayi taku biyu tad'auki ragowar ruwa da yasha,tafara kur6a tana kallan shi danjin abinda zai fad'a,amma har ta shanye baiyi wani motsi ba.
"Jesus christ"!
tafad'a cikin kad'a kai,miskilancin ka yawane dashi wallahi,wanda bai sanka ba zaiyi zatan kai kurma ne awasu lokutan fa.
Bai kalletaba yace nima sau dubu nawa kike so in fad'a miki bazan iya auren kiba kafin ki yadda dani?!
No No No tad'aga mishi hannu ni ba irin wannan banziyar amsar zaka bani ba.
Musaddiq yashigo da fara'arshi ganinta yasa shi d'aure fuska.Suka gaisa a tak'aice tana tambayarshi ya d'aliban makarantar da yake TP?Ya amsa da lafiya lau a tak'aice.Yamik'ama Julaibib hannu sukayi musafaha. suka cigaba da maganganun su zuwa can Musaddiq ya kalleymta"Wai lafiya kuwa? Tamishi wani kallo"Kaima ai kasan tatsuniyar gizo bata wuce k'ok'i "Musaddiq ban sanka da irin wannan halin ba.Yadauke kai daga kallan datake mishi "Eh ai kinsan kamawa takeyi a d'aure me d'aurewa,Zama da mad'aukin kanwa kuma shi ke kawo farin kai.
Musadd...yatareta da sauri "A ah kiyi hak'uri kawai matata tace bata yadda magana tadinga shiga tsakanin muba. Matarka?Ta tamabaye da mamaki Eh haka nace matata.Tad'an ta6e baki"to kenan tsoronta kakaji? A ah Ba tsoronta nake ji ba,sai dai bana san 6acin ranta kona sisin k'wabo.Ahaf,tawatsa hannaye "ba cinya ba k'afar baya.tama Julaibib lallausan murmushin ta"ni zan wuce sai mun had'u ranar litini a makaranta"tajuya tayi tafiyarta.
Ranar litini itace da darasin farko a ajinsu Sudaida tana shiga ta tarar dasu a tsaitsaye suna caccar baki.Tabisu da kallo "Lafiya kuka cika ajin da hayagaga bud'ar kan karya?Linda tafara mata bayani "ranar juma'a Sudaida tana cikin yan weekend-sanitation na wancan makon, amma takama hanya tayi tafiyarta ba tare da tayi kome ba,shine yanzu muke fad'a mata wannan juma'ar dole ta tsaya suyi ita da Dinatu,shine tafara masifa wai ba wanda ya isa yasata tayi sai idan taga damar tsayawa tayine kawai zata tsaya,wancan makon ne take da aiki batayi ba kuma ai yariga ya wuce. Kasham tace"baki kyautaba maimakon ki bada hak'uri kome yawuce shine sai ki rufesu da masifa?Sudaida ta turo baki gaba"to ai bani kad'ai bace Dinatu ma tafito indai gaskiyane abun.Tatsareta da manyan idanunta masu maik'o"Idan kuma karya ne fa?Sudaida tad'an motsa kafad'a"shikenan sai tayi zamanta dama idan aka tsaneka ko ruwa ka fad'a sai ace ka ta da k'ura"tafara k'unk'uni.
Kasham tajijjiga kai"ban ta6a dukan kowa ba tunda nazo makarantar nan,amma yau za kisha na jaki,jeki Staff-Room ki jirani.Yan ajin suka zaro idanu, wasu suka d'ora hannayensu aka"Yau Sudaida zata kad'e har ganyanta a wajan malamai.Har ta kusa fita daga ajin sai kuma takirata"Hey come back"Sudaida tadawo tana kumburi"Kneel down here"takai gwiwoyinta k'asa tana k'unk'uni.Kasham tanunata da yatsa ke"If you dare say something again...I will deal with you.
Takira Dinatu tana tambayarta me yasa baki tsaya an gyara ko in dake ba? Cikin rawar murya"Tace bani da lafiya ina kwance a hostel ranarma ban shigo ajiba". Hakane? Ta tambayi sauran d'aliban suka amsa da eh.sai tadan dafa kafad'rta"Amma yanzu kinji sauk'i?Eh malama naji sauk'i.To jeki zauna ko.Tajuya gaban allo tafara rubutu,tagama rubutawa tajuyo tana fuskantar d'aliban tana musu bayanin sabon darasin da suka shiga.
Sudaida tasake kallan siririn farin agogon fatar dake daure ahannunta na dama,lokacin tama ya kusa k'arewa amma dan wulak'anci ta barta a durk'ushe, gwiwoyinta har sunyi tsami dan rashin tausayi da imani,tabi k'eyarta har zuwan gashin kanta da harara, wannan uban gashin k'aryane ba na ta bane wig ne,ga wani d'inkin rashin mutunci da tayi da atamfar jikinta,koya tayi tasa oho?Taja dogon tsakin dayasa duk yan ajin suka kalleta da mad'aukak'nn mamaki.
Kasham tasake jijjiga kai"ni keki jama tsaki ko?Wallahi yau sai nayi maganin bakin rashin kunya.Tashi kafad'a min abinda yasa kikaki tsayawa ranar juma'a.Taturo baki gaba"to ai Yaya D'ansarai ne yace shi bazai zauna jirana yarasa sallar juma'a ba,ni kuma shine na bishi. Wani lallausan murmushi yasu6uce mata har kyawawan fararan hak'oranta suka bayyana,jin ta ambaci D'ansarai wato dama k'anwarshice wannan? Kawai sai ta rik'o hannunta suka fita.
Ajin yakaure da hayaniya,wasu suna mata ALLAH yak'ara gwamma ayi maganin bakin tsiwan, wasu masu raunin zuciya har idanunsu sun cika da kwalla na tausayin halin da zata tsinci kanta aciki indai tashiga dak'in malamai,musamman kuma da Kasham tayi wannan murmushin sai suke ganin lallai na tanadin wuyane da ALLAH ne kad'ai zai ceci Sudaida.
Sun d'anyi nisa da ajin sannan suka tsaya.Kasham tadafa kafad'arta "Kidaina irin wannan halin bashi dakyau,masoya da mak'iya ba a guzurinsu halinka zai baka su a duk inda kaje"Next time karki sake binshi sai kinyi aikinki kingane ko? Tagyad'a kai.Nima kiyi hak'uri da abinda namiki.Tayi mirmishi "bakome jeki aji ga malamin lissafinku can zai shiga"Always be a good student.
Takoma aji tana wata tafiya irin ta eh yane naci dubu sai ceto.D'aliban suka zaro idanuna suna binta da kallan sama da k'asa alamar"a ah abin mamaki wai Baturiya da suna manga.Dan ba hawaye ba wata alama ta an bata na jaki,amma ba damar tambayarta ya akayi aka haihu a ragaya?Danga Malamin lissafi nan yahad'e girar sama da k'asa,dan shima k'wallan shegene shi yasa ko d'an k'us k'us k'us d'in nan na d'alibai basuyiba sai an tashi tara za a baje kome a fai-fai.Sudaida tamusu fari tana wani lallausan murmushi sannan tazauna awajan zamanta,Suna had'a idanu dashi itama tashiga taitaiyinta.
Suna ciye-ciyensu dasu A'isha a sanda aka buga tara,sauran yan ajin sun zagayesu ana tambayarta an daketa kuwa?ya akayi tabarta tadawo aji da sauri?Sun dauka har a buga tara basu gama horata ba,bulala nawa aka mata?Tawani hura hanci cikin kuri kamar gaske "tama isa ta dakeni ne?Ai wallahi ko kura ta san gidan me babban sanda.Suka kyalkyale da dariya suna ihu;shegiya yar gidan Ibrahim-Mai Lambu, tad'aga musu hannu"a ah kar wasa yayi wasa a tsikari uwar miji fa.Ni yar sunna ce dan haka kar wacce takuma shegan tani ehemmm.
Kasham dasuke zaune a benci ita da wasu malaman suna hirarsu ta k'walamamata kira tayafito ta da hannu.Sudaida tadanja tsaki"nifa wannan malamar tana neman shigarmin hanci da k'udundune. Suka sake kyalkyale da dariya"kila yanzu ne zata hukunta ki a bainan-nasi.Dammm...zuciyarta tabuga tsoro ya baibaye ta, kuma kila hakane,ba mamaki tajuyo maganganun sune tunda dama ba a hankali sakayi taba.Bata kulasuba tamik'e tana Istirja'i.
Ga ni tafad'a cikin ladabi "dole gyad'a tai mai idan tak'i tasha matsa"Kasham tabita da kallo,haka kawai taji tana santa,tunda k'anwar masoyin tane.Lidiya tace"meye haka kuma?Kin kira yarinya kin tasata a gaba da kallo kamar wata magiji.Tasauke gwauran numfashi, tasa hannu a jaka ta zaro kud'in dabata k'irgaba tamik'a mata"ungo kije kisai abinda kike so. Sudaida tabita da kallan tsoro da mamaki kamar yadda sauran malaman sukayi "to da wace hujjar nasara zaiyi hawan k'aho?
"Kar6a mana Sudaida.
Tajuya ba tare data kar6a ba"bar abinki nima ina da nawa.Lidiya tadaka mata tsawa"ke k'aramar mara kunya dawo.Sai kawai tasa gudu.Tayi kwafa zamu had'u dake gobe aji.Kasham tahad'a tafukan hannayenta"Dan ALLAH Lidiya karki daketa dan bata miki kome ba.How dare you Kasham kice bata min kome ba ni sa'ar wasan tace dazan kirata tak'i zuwa?Saboda ita kanwar wancan me shegen girman kan tsiyan?To niba ruwana abu kazan uban ta zanci.Haushi yakama Kasham sai kawai tace"ai ko abu kazan uban ta yafi k'arfinki har abadan duniya.Cikin tafasar zuciya Lidiya tanuna kanta da yatsanta"Kasham ni kikema wannan rashin mutuncin saboda wasu tsinannun hausawa?Ban miki wani rashin mutunci ba, magana kikayi ni kuma na baki amsa.Banda shiga sharo ba shanu ina ruwanki da ita?Ko ke kika kirata? Kome tamin ni naja,idan naga dama in mata hukunci,idan naga dama in k'yaleta bai shafeki ba"wannan sa kai a uku ne takaban siriki.
Suka farar cacar baki malamai suka shiga tsakani daga nan taran yawatse dan an koma aji. Takoma Staff-Room dan bata da darasi a kowani aji har a tashi sai kuma gobe.Tabishi da kallo cikin harara dan kwana biyu taje yajin aiki akanshi, duk yadda takejin san shi ba ta kulashi sai dai tayita kallanshi.Tamaida kanta jikin kujera ta lumshe idanunta tana wata kisima a zuci "Julaibib kyakkyawane"Melanin beauty"tayi nazarin shi dakyau baya san hayani,wani abun ba wulak'anci yake mataba haka halinshi yake bashi da yawan magana,tana so ta aureshi tahaifi yarinya me irin kwantaccen gashinshi, tana san Julaibib ta rasa ya zatayi da rayuwarta"Ciwon so" data san inda zata nemo maganin shi tasha ta warke daga san D'an Sarai ne?
"Oh my God!, ta dunk'ule hannu ta naushi iska"
Dasauri tamik'e zuwa wajanshi D'ansarai takira sunanshi.Yad'ago yakalleta yacigaba da abinda yake yi,sai ta rasa me zatace...Dan ALLAH bani aran correction pen. Yaciroshi a aljihun gaban rigarshi daya soke yamik'a mata.Tashafi hannunshi sannan ta kar6a "nagode idan nagama zan kawo maka.Yagirgiza kai "Kirik'e kawai.To nagode,tasa ajaka dama neman magana ne itama tanada nata fa.
Duk ranar alhamis suke House Assembly, wani ikon ALLAH sai akasa Kasham da Julaibib a house d'aya,Sudaida ma anan take. Kasham a matsayinta na sabuwar malama ita tafara musu bayanin kanta da yar nasiha,sai malamai biyu duk yan TP sai Julaibib cik'on na hud'unsu.Cikin natsuwa yake musu bayani sannan yad'ora da nasiha a kan su dage da karatu ba kawai sai lokacin jarabawa ko za ai wata kaci-kaci da muhawaraba, kullum Ku zama masu nazari da bincike da tambayar duk abinda baku ganeba, da wanda baku saniba da hakane ake samun ilmi me yawa,ita k'wak'walwa d'an Adam ne yake cikata da aiki,idan kuma baiyi hakan ba to ita zata cika mishi da abubuwa na shirme wanda bazai amfaneshi akaran kanshiba,bare har al'umma ta amfana,ina fata zaku dad'a sa k'wazo duk da nasan kunayi amma Ku k'ara, ina kuma fata zaku zama masu amana kamar yadda sunan gidan na ku yake "Amana House.
D'alibai suka d'auki tafi.A'isha da take bayan Sudaida tace"Amma gaskiya ina san Yayanki Sudaida,yanayinshi me sanyine,sukayi murmushi.Mr Julius shugaban house d'in shima yatafa mishi,yau bani da abin fad'a.Yanuna Julaibib da yatsa"This great teacher of ours has said all".Yad'an bubbuga kafad'arshi sukayi murmushi,sannan yakalli d'aliban yad'an motsa kafad'arshi"shikenan you can go back to your classes" duk suka watse.
Maimun yakawo musu ziyarar bazata ranar juma'a da yamma,sun kuma ji dad'in haka sunata ba juna labarin makarantun da aka turasu har Maimun yasako mishi maganar Kasham...Yayi kamar badashi yakeyi ba.Zuwacan kuma yagirgiza kai"ni fa ba zanyi abinda zai zama min matsala ba,aure ba abin wasa bane, ba kuma yin auran ne yadameni ba,a ah samun matar data dace dani me mutunci da mutunta kai.Kasan ALLAH Julaibib Kasham tana sanka,wannan soyayyar da take maka zaisa tamaka biyayya tabi umarninka.Yagirgiza kai"Kyaleta kawai Maimun. Maimun bai kuma maganarba suka cigaba da hirar data shafesu har Musaddiq yafito suka tafi k'wadago neman halali.
Baranzan yajuya yana kallanta"Ke wai meye damuwarki ne?Wani haushin shi takeji gwamma tabar mishi d'akin dan batayi maraba da zuwan shiba,idan tazauna za ayi d'anyan aikine dan shima bashi da mutunci idan yana 6acin rai.A fusace tajuya zata fita,caraf taji yarik'o dantsen hannunta kamar zai k'aryata.
Tarinse idanu dan azaba. Yasunkuya akan fuskarta"sai kin fad'a min da uban wa kika fara soyayya da har kike guduna? Sake min hannu.Yasake rik'eta tamau.Sai fa kin fad'amin da uban wa kika fara soyayyah? Haushinshi yadad'a ninkuwa a zuciyarta Kawai sai tace da"Ubanka...bata gama rufe baki ba taji saukan mari hagu da dama,idanunshi suka kad'a jawur"za kimin rashin mutuncine?Uba na sa'ankine?Yafad'a da karfi cikin tashin hankali da alama allurar soja ta motsa.Uba na ko? Tagyad'a kai duk da a zabar rik'on data keji.Kikace eh? Yashak'eta,manyan idanunta suka fir-firto numfashinta yazo wuya,yasake kifa mata mari hagu da dama,sai da taga wasu k'ananan taurari sun tarwatse, gefen bakinta ya fashe,ji da ganinta suka d'auke na wucin gadi..
Wannene abin so?... A tari fitsari a wanke zawo?
18 Rabi'a Thani 1441
15 December 2019
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin 🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na biyar.
Dak'yar aka 6an6areta a hannunshi bayan tasha wahalar duniya.Yarafff... tafad'a gado tana wani irin tarin wahala tana fuzgo numfashin ta dayake k'ok'arin kufcewa.Shima ya fuzge daga rik'eshin da akayi ana ta bashi hak'uri,yayi kanta,aka sake rik'eshi
Lidiya tashigo da gudunta dan bata san abinda ke faruwa ba yanzu aka kai mata rahoto"haba Baranzan kazama namiji mana, jarumin namiji me kwanan daji irinka me zai sa katsaya fad'a da mace?Kasham fa kwana biyu bata da lafiya ya kamata kamata uzuri.Anki a mata uzurin wa tafad'a ma bata da lafiya? Yabita da kallo tana kwance sambal,gashin kanta a hargitse kuma ta rame ba haka yasan Beauty d'inshi yar gayu ba.To kitashi muje asibiti. Shiruma amsace.Yad'ibo wasu damin kud'i yaba Lidiya wai tarakata asibiti ta tabbata an dubata ankuma bata magani me kyau.Tagyad'a kai tare da sara mishi "Yes sir tabuga k'afar damanta a k'asa.
Tarakashi da adawo lafiya sannan ta rufo k'ofar ta zauna a bakin gadon,tasa hannu tashare mata jinin da yake gefen bakin ta,tabud'e idanunta suka kalli juna.Lidiya tad'an d'age gira"wallahi kashin kare baya taki" Baranzan shine yadace dake ba wancan tsinannan bahaushen ba,danni bazan fasa fad'a miki gaskiya ba,kome naku d'aya da Baranzan"Hun wai saboda wani bare da bai san ALLAH yayi ruwan tsiran kiba kike ga ba dani,indai bani namiki magana ba ke bazaki minba. Tamaida idanunta tarufesu"ita abinda yadami zuciyarta shi d'in ne yadameta"daga ita har Baranzan basu d'ad'ata da k'asaba"kowa da kiwon daya kar6e shi mak'ocin me akuya ya sai kura".
A'isha tabiyo Sudaida dad'an gudunta da aka buga tara"Ke malama jirani"Tatsaya tana kalllanta har ta k'araso"Kefa kika ce ba inda zaki".Aisha tagyad'a kai"Eh nafa sane naga gaba d'aya ajin an watse an barni kamar mayya,me zaki siyane?Ta tambayi Sudaida"Ba abinda zan siya dan bana jin cin kome na makarantar nan yau.Wajan Nasmat zani.Tarik'o hannunta"Dalla shareta zo muje wajan Yayanku tad'an turo baki me zanje in mishi?Ke shifa Yaya D'ansarai ba yaso a dameshi.Ke dai zo muje mana ni wallahi ina sanshi.Sudaida tamata wani kallo sannan ta ta6e baki"Lallai kinji jiki, Yaya Julaibib d'in kike so?.Eh wallahi"Yanayin shi me sanyi ne,baya san hayaniya.
Wa alaikumussalam.Ya amsa sallamar su. A'isha tamata nuni wai su zauna,ita kuma tana nok'e kafad'a.Yad'an d'ago yakalle su,sai yacigaba da nazarin d'aya daga cikin tarin littafan dake gefan shi,hannunshi rik'e da jan biro da alama hannu yake sawa akan aikin daya basu.Yasake d'agowa yakallesu ganin sun zauna sunata kallanshi"yaya wani Abu ne?Aisha tayi tsagal "Yaya Julaibib dama... da... sauran kalaman suka mak'ale saboda wani rikitaccen kallo da yake mata,sai ta mik'e "bakome Sudaida taso mutafi.Har sun jiya Sudaida taji kiranshi.Ta tsaya sannan tajuyo tana kallanshi ya yafitota da hannu.Tak'arasa wajan"Yaya Julaibib gani "Yad'anyi murmushi"hala kud'in taran na ku ba yawane yau?A ah wallahi muna da kud'inmu. Yamik'a mata wasu kud'in"duk da haka sai Ku k'ara,tasa hannu biyu takar6a"Mungode ALLAH yak'ara bud'i.Yad'an bita da kallo yana murmushi.
A'isha taja tsaki kawai anzo wajanka amma saika wulakanta mutane. Sudaida tad'aga mata hannu"a ah wallahi Yaya D'an Sarai bashi da wulakanci, kuma baki ga abinda yakeyi bane?Ai dama nafad'a miki shi fa baya so adameshi...Nasmat tak'araso wajan tatarar da Aisha tana k'unk'uni "Ke da wa kuma?Da Yayanku d'an wulak'ancin can mana tanu mata Julaibib d'in da d'an yatsa.Nasmat ta kyalkyale da dariya miskili kafi mahaukaci ban haushi"to amma shi da baya shiga shirgin mutane to me yahad'o ki dashi? Tawatsa hannu"shareshi kawai suka cigaba da tafiyarsu suna hira.
A sanda hantsi yadubi ludayi na safiyar lahadi suna hirarsu da Inna Khalifa d'an mak'otansu yashigo da gudunshi"Yaya Julaibib ana sallama dakai"To kace ina zuwa. Suka cigaba da hirarsu,ganin bashi da niyyar tashi Inna tace"Tashi katafi mana.Yamik'e To Inna yad'auki rigarshi daya cire yana sawa,a zaure yak'arasa sawa,yana fitowa caraf idanunsu yahad'u,yamata wani irin kallo data kasa fassarawa.Tayi yar dariya"Malam D'ansarai kenan wato ganina yasa ka canjawa kamar kaga me tagayyara rayuwarka har abadan duniya ko?To ni dai nazo gaisheka ne,wancan makon ko sau d'aya ban samu nazo makarantaba dan bani da lafiya kuma a dalilin sanka nashiga halin dana shiga amma ko katambaya"Lafiya kuwa Kasham bata zuwa makaranta?To koma dai yayane Thank God naji sauk'i,ina kuma so kamin jagora zan shiga gaishe da Mama."Bata nan"Yabata amsa a takaice. Takama ha6a🤔D'ansarai wallahi bakayi kama da masu zabga k'arya a kalaman suba,nafa tambayi yaran yacemin tananan,inaso muyi kome cikin mutunci da girmama junane shi yasa ban shigo kai tsaye ba,amma kai naga kamar ba hakama kake so ba,idan natsaya rarrashinka kuma raina ne kawai zai 6aci a banza,tunda har yanzu baka d'aukeni wata tsiya ba,ko albarkacin k'aunar da nake maka ban ta6a ciba.
Koma inda kika fito,tunda ba gayyatoki nayi ba.Tagirgiza kai idan kamin haka tsakani da Allah baka min adalci ba,tanuna mishi Bible d'in hannunta daga majami'a (Church) nake,ana tashi nashigo cikin gari ko gida ban koma na ajiye Bible d'in ba,duk dan d'okin ganinka.Yau d'aya dai kamin adalci a matsayina na yar Adam bama masoyiyar kaba.
Inna tafara jiyo hayaniya."Na rantse da girman ALLAH idan kika tako inda nake sai na 6allaki.Inna tajuyo furucinshi cikin fad'a.Kai dawaye Julaibib?Inna ta tambayeshi bayan tashigo zauren.Cikin tafasar zuciya yajuya yakalli Inna idanunshi jawur"ni da wancan mara kamun kance.Zuciyar ta tabuga Dammm...Kasham wato kwana biyu da bataji d'uriyar taba ta zaci ta hak'urane kamar yadda taita zuwar mata kwanakin baya. Inna dai hakuri take bata tunda maigayyar yace baya so, zuwan ta nak'arshe da Inna tafad'i haka yar dariya kawai tayi tamata sallama tatafi .To yau kuma kwatsam ba zato sai gashi tadawo.
Kasham daga waje tace"Mama kice yabarni in shigo dan ba wajanshi shi kad'ai nazo ba har dake,idan kuma ba haka ba zan mishi abinda har abadan duniya bazai manta dani ba.Wata jijiya tafito rad'am agoshin shi kamar shatin bulala"ni kuma sai dai baki k'araso wajan nan ba amma wallahi sai na 6allaki"ke! yafad'a a tsawace idan kin fasamin abinda bazan mantaba har abadan duniya ke ba...Inna tatareshi"Kai Julaibib dakata! Inna wallahi...tad'aga mishi hannu na dai ce ya isako?Yasunkwui da kai.."haba Julaibib idan rai ya6aci bai kamata hankali ya gushe ba,wai kamanta da sharrin mace har yafi na shaid'an kaifi?.Bai sake magana yasa kai yafita.
Kasham tashigo zauran suna gaisawa,Inna tabita da kallan tausayi"Iska na wahalar da me kayan kara.Takai gwiwoyinta k'asa tahad'a tafukan hannayenta alamar magiya idanunta sun ciko da k'wallah "Mama ki taimakeni mana".
Inna tajijjiga kai"Zanso k'warai Julaibib ya aureki ko dan matsananciyar k'aunar dakike mishi,kuma ya tsamoki daga duhu zuwa haske amma hak'ata bata tadda ruwaba,to kema me zai sa bazaki hak'uraba? Sharrr...hawayen masu d'umi suka zubo a kyakkyawar fuskarta "saboda ina san shi Mama,Julaibib d'an kine na san zaiji maganarki,idan kikace dole ya aureni ai bazai k'i miki biyayya ba.Inna tadafa kafad'arta "Kasham kenan, kasancewar Julaibib d'a na ne ba yana nufin in tilas tashi yin abinda baya so bane,Julaibib yana da hakki akaina, kamar yadda nake da hakki akanshi,shi aure ba abin wasa bane,zaman aure kuma ana yin shine bana wucin gadi ba,a ah zaman din din din ne da ba a san rabuwa sai dai idan k'addarar hakan ta kasance ba yadda za ayi,kinga shi yasa ma ake so mutum yaza6i abokin rayuwar daya kwanta mishi arai, kowa yanajin k'auna da soyayyar d'an uwanshi da gasken-gaske,tayadda idan an samu sa6ani za ayi fad'a, idan an huce za ana juna uzuri,za a yafema juna, amma idan d'aya a dole yake zaune da d'aya to abu kad'an d'in da bai ta ka kara ya karya ba sai rigima ta 6alle wanda daga nan auran zai lalace an rabu, to ina amfanin 6ata goma biyar bata gyaruba?
Suna cikin haka saiga Alhaji Abdullahi yashigo shima da nasiha yabita me ratsa jiki.Tagyad'a kai"Eh tabbas duk abinda suka fad'a gaskiyace wacce daga k'inta sai 6ata. To amma fa ita har kwannan gobe tana san D'an Sarai bata kuma cire rai da auran shiba.
Bayan sun gama cin abincin dare.Alhaji Abdullahi yakalli Julaibib "D'ansarai na san ba abinda ke tsakaninka da wancan yarinyar amma duk da haka sai ka k'ara yin taka tsantsan,dan shaidan baya raina k'ofa,kai kace bazaka aure taba,ita kuma bata hak'ura ta daina bibiyarka ba.Kanemo mata kayi aure dan shine kwanciyar hankalinka damu kanmu,bana so kad'auki wani dogon lokaci ba tare da iyali ba.Yashafa kwantaccen bak'in gashin kanshi "Sannan ya amsa cikin ladabi.Amma cikin zuciyar shi inda kizo ke sak'ar wacece yake jin santa? Dammm...Zuciyar shi tabuga,yayi maza yakawar da tunaninta a,Yasauke gwauran numfashi " Yau ake yin ta wai anyi da mutum ya ji"...
Hajiya takalli Sudaida da 6acin rai"Kai wannan yarinya da kafirin taurin kai take kamar mutanan farko,za ki d'auka kisha ko sai na sa6a miki? Ta turo baki gaba"ni fa wallahi na ji sauk'i"ke tafi can kinji sauk'i amma kwana biyu kina kwance?Ni na ta6a jin inda akayi haka? Baka da lafiya bazaka sha magani ba,baza a maka alluraba?To ko duk tsiyarki gobe sai kin tafi makaranta dan naga abun na ki "Tsiya ne d'inkin ludayi.
Ya shigo da sallama.Tabishi da kallo "Yaya Julaibib ina atilan dana ce kasiyo min"?Yayi kamar ba dashi take magana ba, yazauna a kujera suna gaisawa da Hajiya.Tad'anyi tsaki"ALLAH yasauwak'e maka wannan halin... takauda kai daga kallan da take mishi tafara k'unk'uni saiga Sinan shima ya shigo"Tace yauwa Sinan kamar kasan ina mararin ganinka.Yagaishe da Hajiya tare da tambayar ya akaji da me jiki? A Alhamdulillahi ai taji sauk'i tunda har tana k'in shan magani, shekaran jiya da bata san inda kanta yake ba ai ina bata take kar6a tashanye ba musu ba gaddama.Sudaida ta turo baki gaba ni fa kaina ba inda yatafi yabarni muna tare har a k'abari.
Sinan yamatsa kusa da gadan da take kwance ta lullu6e jikinta da bargon Hajiya fuskarta kawai ta bari a bud'e.Yamata wani kallo"Sannu sarauniyar Sinan" tagyad'a kai cikin murmushi.Yafara mata magana k'asa-k'asa. Takyalkyale da dariya tad'an zaro idanunta"Kaiiii Sinan wallahi ba ruwana.Sai yamik'e tsaye daga sunkuyan da yayi a kusa da ita"Me zan kawo miki anjima"?Tad'an harari Julaibib caraf idanunsu yahad'u tadauke kai,sannan tad'an marairaice "atile"dame kuma?Sai kuma yaba kanshi amsa"da masoyin sarauniyar Sinan rake.Tayi murmushi" Wallahi nagode maka ba kad'an ba Sinan.Tad'aga hannu tana mishi adabo"adawo lafiya.
Filin wajan da malamai suke ajiye mashina da motoci taje,tad'are mashin d'in Shunkut dan yayi saiti da inda Julaibib yazauna a barandar d'akin malamai,tana kare mishi kallo...Tayi murmushi cikin sauke numfashi "Julaibib da ka san matsanan cin son danake maka wata kila daka ceci zuciya ta da take shirin yin gobara.
Holy ghost fire!
Lidiya tafad'a dan Kasham batama san tazo wajan ba.Akan wancan tsinannan bahaushen kina neman zama mahaukaciya"For Christ sake wai me yashiga k'wak'walwarkine? Lidiya kome zaki fad'a min indai akan son wancan bahaushen ne tamata nuni da inda yake zaune, to ina maraba dashi,kin sani tun ganin Julaibib a kuma kallanshi farko so da k'aunarshi suka mamaye zuciya ta,shi kanshi ya fad'a min uncountable times bazai aure niba and I don't know why har yanzu nake jin kaunar shi deep down my heart".
Tadafa kafad'arta ki tayani addu'a duk ranar da ALLAH yabani sa'a yashiga nan ta nuna tsakiyar tafin hannunta,yad'and'ani zak'i da gardin zuma ta,to wallahi na mishi katttt...kisan mummuk'e.Lidiya ta kyalkyale da dariya"gaskiya iska tana wahalar da me kayan kara,malama dame kama ake yin k'ota.Wancan me shegen girman kanne kike tunanin za ki yaudare shi?To yaushe ma yatsayi kulaki bare har hilarki tayi aiki akanshi? Wallahi kinga dai bana san shi amma na jinjina mishi 👍zan kuma iya bada shaidarshi harkar mata baya yinta, dan da yanayi wallahi ko sau d'aya ne tun zuwanshi Gidan-Waya da mun sani,kema ai kin san mune idon gari a makarantar nan,wannan harkar sai sojanki Namamajo,ke dai kawai ALLAH yaganar dake,amma banda 6atan basira mutum yace baya sona to nima banga abinda zai sa ya kuma d'ad'ani da k'asaba tunda shi d'in ai ba mahad'in numfashi na bane,ko yaranmu d'aya dashi zan hak'ura in kyaleshi,bare wani hausawa me girman kan tsiya,shiba kowan kowaba dillalin kashi,kin sani ni nak'i jinin hausawa, ke ba hausawa kad'ai ba duk wani me sallah bana sanshi da inda k'arfin iko na rantse miki da ALLAH ba wasu tsinannun masu sallah dazasu zauna mana a gari.Taja tsaki fuskar nan tarine da 6acin rai ruwan kafircine zallah babu gauraye da haske da tausayi da Imani ko na sisin kwabo, jikar kajawace (Bajju) gaba da baya"bana san ma su sallah.Kuma ba yadda za kiyi dasu "sun zama kuturwar uwa dole a zauna dake.Kasham tabata amsa,sannan tasauko akan mashin d'in tawuce bayan aju-juwa da aka k'awata wajan da shuke-shuken filawowi masu ban sha'awa,tadinga bi tana tsinkosu kaloli mabambanta masu k'amshi tacika hannunta sannan tasa zaran ulu,ruwan hoda tadaure tawuce d'akin malamai zaman jiranshi.Dak'ik'a biyar da buga k'ararrawar canjin darasi sai ga shi yashigo,saida tabari ya zauna a kujerarshi yana hutawa ba ajin dazai kuma shiga sai gobe.Yakwantar da kanshi a jikin kujerar, idanunshi a rufe wani bacci me dad'i yafara shirin saceshi sai kawai yaji an shafa mishi wani abu a daidai hancinshi me wani irin k'amshin dad'i, yabud'e idanunshi da yanayin bacci har sun d'anyi ja.
Tamishi lallausan murmushinta "perceive the natural fragrance of this bounch of flowers.Tafurta hakan da wani salo irin na ta nayanga sannan tacire daga hancinshi ta d'ora mishi a saman tebur.Yakauda kai daga kallan da take mishi kamar kura taga nama.Wallahi yama rasa abinda zai ce mata.
Tayi k'asa da murya ganin wasu malaman sun fara sa musu na mujiya"ai nasan ban kyauta maka ba ko?Kai dai ba a maka gwaninta,d'an motsa kafada tayi "karka damu dani,kar kayi la'akari dacewa nice nakawo maka,tagirgiza kai kayi la'akari kawai da tarin amfanin da k'amshin furen filawa yake dashi ga d'an Adam.How I wish Jualiabib ka bani dama na nuna maka irin kaunar danake maka, tagirgiza kai cikin damuwa "How I wish ka tallafi zuciyata ka magance min damuwar cikinta...sai dai kash!Ban samu hakan ba,saboda baka san illar kaso a k'ikaba,tabbas daka san haka da baza kabari zuciyata tayi gobara ba.Tahad'a tafukan hannayenta alamar magiya "Don't let the love that I have for you to go in vain please...!
Yad'ago yakalle ta,sai yaji wani abu ya tsirga ilahirin jiki da zuciyar shi,har ya bud'e baki zayi magana sai kuma yagirgiza kai"a ah Julaibib daure kawai, maganin kar ayi to tun farko kar a fara"kawai sai yamik'e yabar d'akin.
Shunkut ya sunkuyo a fuskarta yana murmushi"Ke ki hak'ura dashi mana ai ba a soyayyah dole, yanuna kanshi da yatsarshi"ni d'in nan namiji ne duk abinda yake dashi namazan taka nima ina dashi,kiyadda kawai muyi soyayyah.A fusace ta tureshi"you fool! dawa za kayi soyayyah Shunkut?Tayi d'as da yan yatsunta over my dead body.Tagalla mishi harara sannan taja mummunan tsaki"ruwa ai ba sa'an kwando bane"sai yajuya yana tafiya "Amma kuwa za kiyi 6atan 6akatantan...
A gajiye lik'is yashigo,gidan shiru dan Inna tana gidan Hajiya,yazauna yana hutawa, ya6alle botiren gaban farar rigarshi,yamaida kanshi jikin kujera tare da lumshe idanunshi sassanyar iskar bayan la'asar tana ratsashi. Mafarkan da kwana biyu nan yakeyi sun tsaya mishi a rai"Kasham yake gani cikin kyakkyawan kirar kalangunta,sanye da kayan fulani,gashinta yasha gyara ta tufkeshi a baya,amma kuma idan tayi magana muryar Sudaida yakeji"ya rasa kan wannan mafarki.
Hayaniyar shigowarsu Kamila yasashi bud'e idanunshi,aiko suka shigo sunata zuba surutunsu, sunata mishi tambaye- tambaye.Shigowar Musaddiq yasa suka koma tsakar gida suna wasannin su,yadaki kafad'ar shi"kai malam tashi da ALLAH magana nazo muyi. Uhun ina jinka.Musaddiq yabishi da kallo"Julaibib ka nemi A'isha kawarsu Sudaida mana tunda dama ta nuna tana sanka kaine baka bada goyon baya,tana da hankali kuma ko su Baba idan sukaji ita kake so za suji da...yatari numfashinshi a hasale "bata min a matsayin matar aure ba,dan haka akai kasuwa".Yakalle shi da mad'aukakin mamaki"To me yayi zafi da har idanu za suci wuta haka? Tagyada kai "To yayi,indai har A'isha bata maka a matsayin matar aure ba to ashe gulmace da kai,kana kuma kallan mata za kuma ka iya za6a,amma da zarar magana ta tashi sai kace ba sa gabanka,to kuma harsu Baba sai sunji zancen nan.
Yanunashi da yatsa"Idan kai zaka min zaman auran ai sai in aureta.Yamaida idanun shi ya rufe, shi wai ma wacece wata A'isha?Wasu lokutan dai Sudaida tana fad'a mishi"A'isha tace tana gaisuwa"ko kuma A'isha tace kaza da kaza game kai,sai dai bazai iya tuno me take fad'a d'inba, dan ba itace a gaban shiba,shi dai bai san tana sanshi ba,dan ko Sudaida bata ta6a fad'a mishi wai A'isha tana san shiba, kila Musaddiq d'inne kawai yake san had'awa.
Sallar a zahar Julaibib yayi yagama azkar d'inshi sannan yafito daga masallacin makarantar,yau ba ayi wani karatun kirkiba saboda Inter-House ya kusa,ga dalibai nan sunyi rukuni rukuni na irin abinda suke so, suke dad'a yin gwaji (practice)yajingina da bishiyar giginya tare da rungume hannayanshi a kirji yana kallan Sudaida yadda take d'aga mulmulallan bak'in k'arfen discus da yadda take jefashi cikin k'warewa da nishad'i a bokan wasanta suna mata tafi wasu suna mata ihu dan tanayi yadda yakamata.Yayi murmushi yatuna lokacin da yake makaranta yayi wasannin kala kala,wasan kwallo ne bai ta6,a burgeshi ba wannan sai Musaddiq,saboda kwazanshi a fannin wasannin shine yarik'e shugaban wasanni na lokacinsu (Game Prefect) yakalli Khausar sune yan Javelin, Nasmat kuma ana bangaran Long jump. Yabar jikin bishiyar yana tafiyarshi cikin natsuwa har yaje Staff-Quater zai kar6i wasu littafai a wajan Mr Julius.
K'arfe uku tanayi yasake komawa filin wasannin da Nasmat yafara cin karo yace"Ke idan ba zaku tafi gida bane ni kunga tafiyata.Dan ALLAH kajiramu barin kirasu tayi cikin filin da dan gudunta.
A mota suka sameshi ya musu wannann rikitaccen kallan nashi Sudaida tabud'e baki za tayi magana yanu nata da yatsa"kul naji bakinki.Tad'an harareshi ta zauna tana turo baki gaba.Yaja tsaki"kunje kun shagala da wasanni ko sallar azahar ma baku yiba ga la'asar ta kusa,kufa kuna da ka'ida da bambanci tsakanin ku da wad'anda dama basu san kome ba sai duniyar, wallahi idan lokacin sallah yayi banga mutum a masallaci ba gobe...yayi kwafa, Nasmat tace"shi fa wannan Game Master muguntar shi har tafi ta Discipline Master.Ke tafi can shi ai ba makaho bane yana ganin k'atan masallaci ai a makarantar,na kuma tabbata da kun fad'a mishi sallah za kuyi bazai hana kuba,ai kowa ya san duk inda musulmi yake ba a rabashi da sallah,sai dai in sallarce bata dame shiba...Yaya D'ansarai... yatari numfashin ta"ke ba nace kar inji bakin kiba?Tasunkwui da kai"wannan mutumin wallahi yanada matsala,tafad'a a zuci,tad'anja tsaki. Nasmat takalleta"ke Sudaida tun d'azu kiketa k'unk'uni abin harda jan tsaki ke da wa? Shiru ma amsace.
A k'ofar gidansu yatsaida motar bai k'arasa dasu gidansu kamar yadda yasaba ba,yakashe motar yafito yashige gida.Sudaida itama tabud'e bangarenta tafito tana masifa"aikin banza sammakon gaida makiyi,aiko ba a motarka zamu dawo gida.
Aminu yana hangota yafara dariya"ke fa Sudaida naga alama raguwa za a yi.Ta turo baki gaba "Yaya Aminu me nayi to? Kinga fuskarki kuwa?Gaskiya yunwar makaranta ba ta dad'i har na tuna lokacin da mukayi makaranta a Bauchi.Yad'an kalleta kinsan yau me su Mama sukayi a gidan? Tagirgiza kai "Tuwon shinkafa miyar shuwaka"Sai kawai tad'ora hannayenta aka"Wayyo ALLAH! ni gaskiya yau ana ta 6ata min rai.Suwaye suketa 6ata miki rai?Takaryar da kai gefen dama ta marairaice "Yaya D'ansarai da su Mama,wallahi gidan Hajiya zan tafi ina canja kaya,dan bazan mutu da yunwaba.Yamik'a mata wasu nannad'ad'd'un carbon paper,Top-bond,babban pensir HB dawasu k'ananan tarkacen zane-zanenshi(Artistry Euipment) to tafi min dasu gida,yanzu haka Bakin Gogi zan tafi wani aikin signboard zanyi.Tasa hannu biyu takar6a "Yaya Aminu ALLAH yatsare.Amin Sudaida suka daga hannayensu suna ma juna adabo,sukayi murmushi sannan kowa yajuya yacigaba da tafiyarshi.
...Dare da rana suna aiki tuk'uru a kanmu,to muma kamata yayi mu zage dantse muyi aiki tuk'uru a cikinsu.Ubangijinmu kabamu rabo me amfani fid-dunya wal aakhirah.
21 Rabi'a Thani 1441
18 December 2019
We Ibrahim' Daughters 👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
DANGIN NONO WRITERS ASSOCIATION
{Da Inganci Mukayi Fintinkau}
Bismillahi wabihi nasta'in
...GWAJIN DAFI💔
Almost true story
Daga alk'alamin🖊
Ya'yan Ibrahim
Saudat A.Baba (Asdilat KD)
Da
Bara'atu Ibrahim (Ra'ibs)
Shafi na shida.
Da yammacin juma'a jikokin Hajiya sun cika gidan,tun daga zaure za ka fara jiyo hayaniyarsu sun tasata a gaba da shak'iyanci. Sudaida da Nasmat suma suka shigo,suna k'are mata kallo tasha had'ad'd'an leshin auduga ja da k'ananan fararan duwatsu,wuya,hannayenta, da d'an kunnanta na zinare sai d'aukar idanu sukeyi. Suka kalli juna suka k'yalk'yale da dariya"Hajiya manya wannan irin cakarewar k'uda a gefen gyambo?inji Nasmat. Sudaida tagyad'a kai "Gaskiya kin had'u saura had'uwarki da ALLAH, wannnan k'ure adaka haka?To dawalakin goro a miya,bazawarin tane zai iso da yammacin nan. Gaba d'ayansu suka kuma k'yalk'yalewa da dariya, abinda yahanasu jin abinda Hajiyar take fad'a.
Aminu yashigo sai suka sa ihu da tafi "Yehhh... gashinan, gashinan shine bazawarin data k'urema adaka.Yakama ha6a🤔 wai wai wai, ai kowa ya san Hajiya ba dani take yiba,dan ta san ni bazan juri al'alarta na bani bani kamar mak'ogwaro kullum a bashi ba,bani da wannan hak'urin,kusa idanu anjima kad'an za ku ganshi. Khausar tace Alkasim ne.Aminu yace gajan hak'urine dake koma wanene za ku ganshi. Yamatsa wajan Hajiyar suna maganarsu.
Sudaida tafara shak'o k'amshin turarenshi da iska takad'o mata kafin tayi magana yashigo yana musu wannnan rikitaccen kallan na shi"ku wallahi kun cika hayagaga bud'ar kan karya,sai kusama mutum ciwon kai.Sudaida da dama takejin haushinshi tace"sai dai dama can mutum da ciwon kanshi yashigo,kace kawai a baka magani za kasha. Suka k'yalk'yale da dariya.
Nasmat tace"su autan Inna manya, kace kawai kazo tad'i wajan Hajiya kuma katarar mun tare inda za ka zauna.Sudaida tad'anja tsaki tana mishi kallan sama da k'asa yana cikin fararan kaya yayi shar dashi"Kuma wai haka zai zo hannu rabbana"Yatsareta da idanun shi"ke yarinyar nan wai meye damuwarki da ni ne? Yanunata da yatsa"za fa kisha na jaki,idan baki daina shiga harka ta ba.Ta turo baki gaba"Indai aka k'i jininka ko ruwa kafad'a sai a ce ka tada k'ura,ni kad'ai nayi magana?Ni kamayar marainiyar wayon ka ko?Tahaye gadan Hajiya tana k'unk'uni. Hajiya tace"kai Julaibib yi tafiyar ka anjima sai kadawo muyi hirar mu cikin dad'in rai,lokacin duk sun kama gabansu.Yayi murmushi yana kallan Sudaida data juya musu baya.
Sudaida...
yakirata.Sai tamishi kunnan uwar shegu.Ke Sudaida ba kiranki nake yiba? Hajiya tasa baki"yau na ji yarinya ba dake yake yiba?Shiruma amsace. Hajiya tashiga tafa hannaye da sallallami.Yad'aga mata hannu"kyaleta Hajiya na jaki kawai zata sha.Eh gwamma haka tunda abin nata tsiyane d'inkin ludayi.Yace"ke Asma'u d'auko min bulalan can.Tana jin haka tafara"Ihu sai tajawo k'atan bargon Hajiya ta duk'unk'une aciki.Yayi murmushi "k'aramar mara kunya kawai,fito a cikin bargon kika yadda zan miki walmukalifatu "wallahi bazan fito ba.Yama Hajiya sallama sai bayan sallar Isha'i zai dawo.
Suna hirarsu da Inna tasako mishi maganar A'isha.Yasunkwui da kai tad'anyi murmushi dan ta san halinshi indai yayi haka to zaiyi wuya yayi magana.Kaga kwantar da hankalin ka niba dole zan maka ba,munyi magana ta fahimta da Musaddiq nima banga aibun taba shawara kawai nake ba ka, kanemi auran ta Insha-ALLAH ba kome sai alheri amma fa karka takura kanka idan ba ka so,dan aure ba abin wasa bane zamane da ake fatar yinshi har k'arshen numfashi.Yad'an shafa kwantaccen bak'in gashin kanshi sannan yad'ago cikin natsuwa ya kalleta "nagode Inna ALLAH yak'ara girma na kar6i shawararki da hannu biyu.Tayi murmushin jin dad'i "Ubangiji yamaka albarka ya taimaki rayuwarka. Amin Innarmu.
Wannan makon ya so zuwa wajan A'isha to amma bai samu sarari ba saboda sun gama TP(Teaching Practice)sun koma makaranta. Sai bayan makonni biyu sannan yasamu yashirya ranar juma'a cikin shigarshi ta fararan kaya kanshi da farar hula zita.Yana shiga lungun gidan yahango ya'yan gidan maza suna wasan Hockey.
Nasir abokin Abdul yana hangoshi yak'arasa wajanshi yana dariya yace "Kawu" kamar yadda yaji Abdul yana fad'a "yau kaine a k'ofar gidanmu? Ko kazo gaishe da Mamanmu ne?Yagyad'a kai"eh nazo gaisheta ne amma ba shiga zanyi ba ka gaisheta zamuzo da Musaddiq na musamman mu gaisheta.Yayi tsallan murna"to zan fad'a mata.Aisha tana ciki? Julaibib ya tambayeshi.Eh tana ciki inkira maka itane?yagyad'a kai. Nasir yashige gida da gudunshi yana k'wala kiran sunanta.
Tayi mamaki tare da k'aryata Nasir.Nasir yafara rantse-rantse da gaske ne yana k'ofar gida.Tarik'o hannunshi "To muje ai ba a k'arya kusa da gida,amma na rantse da ALLAH idan ba shi bane?tayi kwafa wallahi ka san sauran"Eh na yadda.Kanshi a k'asa kamar yana k'irga tsakuwan da suke yashe a wajan.Sai tasaki hannun Nasir da yake mata dariya ai dama na fad'a miki,yajuya wajan wasansu.
Yaya Julaibib...
Tafurta sunan kamar tana cikin shakkar shi d'inne ko wani me kama dashine?Yad'ago yad'an kalleta"na'am A'isha... Wani murmushi ya su6uce mata "ALLAH da gaske kaine a k'ofar gidanmu? Lallai yau farar rana ce me kyakkyawar suna "Juma'a.A mutunce ta gaishe shi,sai tayi shiru dan bata san abinda yakawo shiba.Shima shirun yayi na wucewar wasu dak'ik'u.Yad'an sake kallanta "na zo gaishe kine,inafatar banyi laifi ba?Tagirgiza kai"wani irin laifi? Gaskiya nagode da wannan ziyara ALLAH yabar zumunci. Ina Yaya Musaddiq? Ya tafi Kaduna.Hirar tasu jefi-jefi,bai wani dad'e ba yamata sallama yatafi.
Tabi bayanshi da kallo har yasha kwanar lungunsu ya bace ma ganinta tana tsaye a wajan cikin mamakin ganinshi a k'ofar gidan su,kuma wai wajen ta yazo dan sada zumunci, tasake juya kwalban turaren arabian perfume d'in daya bata,tabud'e tashaki k'amshin me wani irin dad'i,bata zata za suyi magana irin na yau ba,dan sunsha had'uwa ta gaisheshi amma sama-sama yake amsawa.Ashe dai Sudaida gaskiya take fad'a mata,Yaya Julaibib fa yana da matuk'ar kirki,shi kawai baya san a dameshine,kuma baya san magana da yawa. Tajuya zuwa cikin gida ba tare data kawo kome a zuciyarta game da zuwan shiba.
Bayan Musaddiq yadawo suka tattauna. Musaddiq yakad'a kai"gaskiya da ka sani kafad'a mata dalilin zuwanka"ai da zafi-zafi a kan daki k'arfe.Yagyad'a kai na fahimceka nagode yamik'a mishi hannu sukayi musafaha.
Ranar juma'a data zagayo yaso kwarai yaje wajan A'isha d'an yafad'a mata kome,to amma hakan shi bai tadda ruwa ba" dan sun fara jarabawa me zafin gaske,ba wanda yakoma gida dan itace jarabawarsu tak'arshe a College Of Education Gidan-Waya,sai kuma a zauna zaman girbe abinda aka shuka.ALLAH yaba me rabo sa a.
Lidiya tabita da kallo ita da d'akin, dan ta had'a k'aramin hazo ne da hayak'in taban da take ta zuk'a, takalli Ash-tray d'in da take karkad'e tokar guntayen taban data zuk'e,sai tazaro idanu da mad'aukakin mamaki,"Eh ta san Kasham tana shan taba amma sai ran ta yayi mugun 6aci,kuma bai wuce tasha kara uku ba,amma yau bata san ko kara nawa bane,tamatsa jikin taga tad'aga labulan tare da bud'e gilasan,hayak'in da gauraye d'akin yafara raguwa.
Kasham...
Lidiya takirata,tad'ago tana kallan ta manyan idanunta masu maik'o sun kad'a jawaur fuskarta har ta kumbura saboda kukan data sha bana wasa bane.
"Inzayadami Kasham?(Kaham me yafaru)
Shar...shar...wasu hawaye masu d'umi suka fara sintiri a kyakkyawar fuskarta"Kasham...dasauri ta d'aga ma Lidiya hannu "Don't dusturb me!
Lidiya tagyad'a kai,tarungume hannayenta a k'irji tana kallanta,Tabud'e dirowa tana dube-dubenta "oh no dammed it"ta dunk'ule hannu ta naushi iska,da alama bata ga abinda take nema ba,takoma ta zauna tasake kunna taba, tabi taban da kallo da tunanin yadda karan zai kare a zuk'a d'aya,takai baki tamata wata irin zuk'a data kusa tafiya da numfashin ta,nan take kuma tari ya sark'afeta.
Tari tadinga yi kamar na shika, abin har yaba Lidiya tsoro ta kamo ta suka fito waje dan tasha iska. K'irjinta yana mata wani irin suya,mak'ogwaranta ya bushe k'amas kamar miyau bai ta6a bi ta wajan ba. Tad'ago a galabaice takalli Lidiya" ruuwa.Lidiya tagyad'a kai"o barin siyo miki,tana k'ok'arin jinginar da ita ajikin bango dan ta fara wata irin shakuwa abinda yadad'a rikitar da Lidiya kenan.
Hey...please come and help meee...!!!
Yadda akayi furucin cikin yanayin tashin hankali da tsoro yasashi waiwayawa inda yajiyo sautin. Tasake yafito shi da hannu... Tabbasss ko su wanene wad'ancan taimako suke nema sai yatafi wajen.Bai gane Kasham da Lidiya bane sai da yakusa k'arasawa inda suke yaji Lidiya nafad'in ban san me yashiga kwakwalwarki da zaki karar da karan taba a zuk'a d"aya ba, gashi nan za kije ki kashe kanki abanza...wani irin abu yaji da yabi ilahirin jiki da zuciyarshi"Kasham kwance wanwar a k'asa,farin wandan legging d'inta yayi dabbare-dabbare da k'asa...
Dan ALLAH ka taimake mu karta mutu,har lokacin tana dafe da k'irji tana wani irin numfashi,gefe da gefen fuskarta busassun hawayen wahala ne,idanunta suna rufewa da bud'ewa bak'i ciki yana 6acewa.
K'amshin arabian perfume d'in data shak'a yasa tad'ago dak'yar takalleshi...sai tamik'a mishi hannunta na dama.Tausayinta yakamashi dan tana cikin wani irin mawuyacin hali,wallahi mutum ba a bakin kome yake ba"Ubangiji👏kamana kyakkyawan k'arshe.D'azu- d'azun nan yahango su,da yan course d'insu sunci kwalliya mazansu da matansu suna ta hotuna suna hayaniyarsu ta dandazon d'alibai.
Sai da ya durk'usa sannan ya tabbatar lallai tabar tasha dan gaba d'aya warin ta takeyi"me zan baki ne?Dak'yar tayi furucin"ru.rr... ruwa...yabud'e ragowan ruwan swan d'in daya ke hannunshi.Ya waiwaya inda Lidiya take durk'ushe dan ta taimaka mata ta tashi, amma bai ganta ba.Sai kawai yad'agata ta jingina da bango, yamik'a mata ruwan.Saida tashanye shi duka sannan ta sauke gwauran numfash."Sannu...Yace mata da yana yinshi na natsuwa"Kwallah suka cika idanunta,inama inama ace sunyi aure ne yake bata wannan kulawar?Bata ta6a zatan D'ansarai zai taimaketa idan ya ganta a mawuyacin yanayi ba,saboda halin-ko-inkulan da yake nuna mata.
"Kasham...yakira sunan ta.Tad'ago tana mishi kallan k'auna me cike da shauk'i,wallahi kasancewar su a tare,sai ta jita garas...kamar ba ita bace a mawuyacin hali d'azu ba.
Haba Kasham kina mace me kima, amma ace kema kina k'arama sama hazo?(shan taba) abin nan ya bani mamaki fa,ga ki da ilmi kina kuma ganin abinda su masu yin tabar suke rubutawa ajikin kwalin"Mashaya taba suna iya mutuwa da k'uruciyarsu"haba Kasham meye amfanin shan taba sigari ne?Kina sane da "nicotine"gubar dake cikin taba ba karamin jazama hunhu matsala yakeyi ba.Dan ALLAH... yahad'a tafukan hannayen shi 🙏alamar magiya kamar yadda take mishi "Ki daina shan taba sigari dan babu kome a cikinshi sai illah.
Wata irin k'auna da soyayyarshi ta dad'a mamaye zuciyarta"Oh God...ALLAH kamallaka min wannan bawa na ka.Tajijjiga kai "shikenan D'an Sarai nagode,na kuma maka alkawari ko muna tare ko bama tare, na sha taba na k'arshe a rayuwata,daga yau d'in nan na barta har abadan duniya.Yad'an saki fuska"yauwa Kasham.Ungwai bu gangan(Kasham nagode sosai) dakika kar6i nasiha ta.Tad'an zaro idanun ta"kaii dama kana jin yarenmu?Saita kyalkyale da dariya dai dai da dawowar Lidiya da roban ruwa swan.Sai kuma tayi saroro cikin mad'aukakin mamaki "wannan me shegen girman kan dama d'azu takira?Lallai hankali ke gani ba idanu gululuba.Shima mik'ewa yayi bai sake magana ba yajuya yayi tafiyarshi.
Tadinga binshi da idanunta har sai da yayi nisa ya6ace ma ganinta sannan tamik'e tsaye itama tana yar dariya,wallahi wani irin nishadi ta tsinci kanta a ciki, takad'a kai" ALLAH dai yakai damo ga harawa ko bai ciba yayi burgima.Dama duk tunanin rabuwa dashi ne yajaza mata 6acin ran daya sa ta dinga k'arama sama hazo na rashin hayyaci.
Lidiya taja dogon tsaki "mahaukaciya kawai, ya gama zaginki ke kuma kamar wata wawuya kina jin dad'i.Wani murmushin yasake su6uce mata"karki d'auki alhaki dan D'ansarai bai ta6a zagina ba,bare kuma yau da yamin nasiha,na kuma kar6eta da hannu biyu. Lidiya ta jefeta da ruwan swan d'in rubbish girl.Dasauri tacafe ruwan tana dariya"kanki akeji Lidiya...
Haka nafi so an cema makaho je ka ka gani.
23 Rabi'a Thani 1441
20 December 2019
We Ibrahim's Daughters👇
Asdilat KD...2geda with Ra'ibs.
0 comments:
Post a Comment