Ranan Jumma'a su Ummi su ka zo daga Jos, murna wajen Farida ba'a magana. Ranan Asabat aka ɗaura auren *Hajara Musa Wase da Haladu Iliyasu* sai *Salima Musa Wase da Jabir Muhammad*
'Yan uwa daga Wase da Giyaɗe duk sun zo, da ke Baffa Musa da Baaba Sabuwa duka 'yan Wase ne. Ita Anty Hanne kuma 'yar Giyaɗe ce.
Haka aka sha hidima lafiya, duk da an ɗan samu rikici ranan yini saboda magulmata wanda su ka tisa Baaba Sabuwa a gaba kan rashin auren 'yarta Maijiddah. Maijiddah ta yi kuka har ta ƙoshi duk da ta san akwai alamun kukan na ta ya kusa ƙarewa amma kuma madamar ba auren ta yi ba, ita ko Baabarta ba wanda zai samu sukuni...
.......................
Shigar Abaya ta yi mai adon duwatsu kalar gold. Gyalensa ta yi rolling da shi sannan ta ɗau jakarta ta fito, gidan dai an watse sai 'yan tsiraru. Ummi ma ta tafi jiya saboda aiki da za ta koma.
"Allah dai ya sa Sir Najeeb ya haƙura idan ba haka ba kuma kin gama aiki kenan a Najeeb constructions"
"Ya ma isa ya koreni. Lallai! ai Yakubu ka zuba ido kawai ka sha kallo amma yau ko ana ha maza ana ha mata bazan ajiye aiki ba"
Yakubu girgiza kai kawai ya yi ya tada machine ɗinsa su ka tafi...
Sandy mai goge office ɗin Najeeb ne ta cewa Farida Najeeb ya zo lokacin da su ka haɗu, za ta shiga lifter ita kuma Faridan ta fito.
Ta na ajiye jaka ta wuce office ɗin sa. Yana duba wa su takardu ta shigo.
"Good morning Sir"
Ya ji shigowarta amma ya share ko ɗagowa bai yi ba.
"Sir akwai aikin da zan yi ne?"
Sai a lokacin ya ɗago ya kalleta.
"What part of my message did you not understand?"
"Sir na ga saƙo ta email ranan Laraba wai an koreni daga aiki"
Ya ɗaga ido ya ce "and?"
"Ban koru ba mana. Ba laifin da na yi sannan ko na yi laifi ma, tsarin da ka shirya min ya hana ka koreni"
"Listen Miss Salihu. Na san Saboda Anas ki ka dawo, but ki sani. This is my company, just like you Anas is my employee. So, na koreki ba abinda Anas zai iyayi akai. Now get out of this place bitch"
Fita ta yi daga office ɗin ba tareda ta ce ƙala ba. Minti biyu sai ga ta ta zo da takardu a hannunta
"Ga shi nan, wannan takardar shedar amincewarka ce da tafiyata. Wannan kuma kai ka amince zan yi aiki da kai na wata shida ba tareda ka koreni ba, idan har ka koreni to za ka dinga biyana salary har wata shida ta cika kuma......"
"Wait whats this? When did i sign this? I never signed this"
"Ka kalla dai da kyau Sir Najeeb Jibo. Ka san tabbas signature da ke jiki kai ka yi, you stamped and signed it"
"This is bullshit" ya faɗi tareda yaga takardun
Farida ta yi dariya ta ce " na nawa kuma wannan ma ba original ɗin bane. Original ɗin na nan, so ba inda zan je"
Ta fita daga office ɗin...
Anas ne ya shigo office ɗin ta da sauri "'yar uwa mi ya faru? Najeeb ya kira ni yanata kwarwa"
"Ce ma sa na yi bai isa ya koreni ba"
"Barin shiga na ji mi zai ce" ya shige office ɗin Najeeb da sauri...
Yadda Anas ya ɗau alamarin fa ba da sauƙi bane. Domin Najeeb faɗa ya ke ma sa kamar tsohon zaki, cewa yai ya kawo ma sa mahaukaciya, yarinyar ba ta ganin girma ko darajar sa.
"Amma Najeeb we've talked about this ai, na roƙeƙa ka bata wani chance ɗin"
"To hell with her. I dont want to work with her, can you imagine wannan yarinya ta creating documents ta sa na signing ba tareda na san miye a ciki ba. The girl is a crook, she's just...."
"Haba yallaɓai. Duk wannan tashin hankalin akan mace, ban sanka da haka ba"
Najeeb ya kalli Anas ido cikin ido ya ce " get her out of this office or i will use force, and you know i will do it"
Ganin yadda Najeeb ya bircike ya sa ya fita ya samu Farida ya ce dan Allah ta koma gida zuwa gobe idan Najeeb ya huce zai kirata sai ta dawo. Farida ta tafa hannu ta riƙe ƙugu ta ce "Ya Anas ba inda zan je. Ai yau idan bai haƙura ba zai ga haukata muraratan. Ba ri ma kaga"
Ta wuce office ɗin Najeeb.
"Ka ga Sir Najeeb kar ka bari na nuna ma ka haukata anan, kai shikenan ba dama mutum ya ɗan yi ƙaramin laifi sai ka ce kora, to yau ka gamu da gamonka. Ba inda zan je idan ka takura kuma na shigar da kai ƙara tunda da izininka na tafi hutu" ta san hakan zai iya faruwa shiyasa ranan laraba da ta zo ta typing documents ɗin ta haɗa cikin wasu da zai signing shi kuwa ko dubawa bai yi ba ya dinga signing ɗin su.
"Well lets see how tough you are" ya faɗi tareda ɗaukar waya ya kira security.
Anas da ya shigo office ɗin ya fara bashi haƙuri. "please dont do this. Ba girmanka bane wallahi. Za ta bar maka aiki amma banda koran walaƙanci dan Allah"
Farida ta ce " Ya Anas ka barshi, security ɗin su zo ina nan ba inda zan je"
"Farida ki yi shiru ki fita, i'll handle this"
"Yadda ya ke ji da taurinkai ni nawa ya ninka na shi. Mun fafata da arnan Jos ma balle shi"
Ana haka sai ga wasu murɗaɗɗun security sun shigo, dukkan su biyu da ka gansu ka san basu da mutunci da alama ma ba musulmai ba ne.
Najeeb ya tashi ya zo gaban Farida ya ce " for the last time, LEAVE"
"Allankatafir ba inda zan je"
Shi kam Anas baza ido kawai yai yana kallon wannan dramar.
Najeeb ya dubi securities ɗin ya ce " throw her out of my company, i dont want to see her here again"
Ɗaya daga cikin securities ɗin ya nufo ta yana ƙoƙarin riƙe ta, aikuwa ta yi tsalle ta faɗa jikin Najeeb ta cukwuikuyeshi tana ihu tana faɗin wallahi ba zan fita ba ko za a kashe ni.
Najeeb ya rintse ido lokaci guda kuma hankalinsa ya tashi. Cikin zuciyarsa ya ke mamakin abinda ya faru, ba wai rungumeshin da ta yi ba, sai dai effect ɗin da rungumar ya jawo ma sa. He cant believe he got erection because of this crazy girl.
Security ɗin ya kai hannu zai janyo Farida daga jikin Najeeb, Anas ya daka ma sa tsawa ya ce su fita daga office ɗin.
Najeeb har lokacin idonsa a rufe, ya rasa ya zai yi, he's afraid of pushing her away saboda Anas da securities za su ga yadda engine ɗinsa ta miƙe. He cant embarrass himself infront of this crazy girl dan haka cikin hikima ya sa hannu ya turata da ƙarfi before you knew it ya juya da sauri yai hanyar banɗaki.
Anas da ke recording abinda ke faruwa yai kan Farida da ta faɗi ƙasa warwas. " sorry 'yar uwa, tashi" da ƙyar ta miƙe da taimakon Anas saboda ƙugunta da ya bugu sosai...
Ya ƙara zuba ruwa a fiskarsa a karo na ba adadi. Ya kalli kan sa a madubi sai lokacin ya ga yadda jacket na shi ya ɓace da janbakinta.
"This girl is a witch. How could this possibly happen?"Rabon shi da shiga yanayi irin wannan ma ya manta....
"Oga ka fito ayi magana, ka haƙuran ne ko dai" muryan Anas ya katse shi.
Ajiyar zuciya yai sannan ya fito riƙe da jacket a hannunsa yadda ya riƙe ka ce kashi ne ajikin jacket ɗin. Yana fitowa Anas ya sa dariya.
"Get out Anas, i dont want to see anyone"
"Ka huta mutumina irin wannan al'amari sai da hutu ai"
Najeeb ya wurga ma sa jacket ɗin. Anas ya chafe ya ce " wannan jacket ɗin ta tarihi ce"
Sai da ya kai bakin ƙofa ya ce " kar ka manta za ka saurari presentation daga Team D ƙarfe goma. Zan sa sakatariyarka ta tuna ma ka idan lokaci ya yi"
Najeeb ya ce " Anas i'll kill you"....
Anas na fita ya samu Farida ya ce " gaskiyar Yaks da ya ce ke da Najeeb fire and fire ne sai dai gaskiya ta ki wutar ta fi tasa zafi. Kar ki bari kowa ya shiga office ɗin sa sai nan da 1hr kafin nan ya huce"
Farida ta amsa da " ok"
Ko ajikinta dan ta san haƙarta ya cimma ruwa...
Yana zaune ya sa hannu a ƙirjinsa yana shafawa ashe yarinyar nan har cizonsa ta yi, da ya duba wajen a madubi yai wani jaa abinka da farin mutum.
"She'll pay for this, i'm not sending her away. Not until she suffer, i'll make sure she cry and cry and cry"
Yana zaune ya kunna laptop ɗin sa " lets see what the witch is doing"
Tana zaune tana danna waya ga biscuit agefe tana ci. Har zai kashe sai ya tsaya saboda shigowar Khalidah da ya gani. " another bitch" ya faɗi a ran sa...
Kai tsaye hanyar office ɗin Najeeb ta yi Farida ta ce " Malama tsaya"
A gadarance Khalidah ta juyo "and who are you?"
"Idon ki dai bai makance ba ina?. Kin san dai aikin wanda ke zama a kujeran nan ko"
"Ya kamata ki sani, matsayin ki bai kai ya hanani shiga office ɗin Najeeb ba"
Farida ta taso " Sir Najeeb ya ce bai son ganin kowa sai nan da awa ɗaya dan haka. Ko ke wacece sai dai ki dawo anjima"
"Ki hanani shiga idan kin isa?" Khalidah ta faɗi tana ƙoƙarin shiga. Farida ta sa hannu ta jawota da ƙarfi.
"Ki riƙe matsayinki Malama, ko kuma wallahi ni da ke sai mun kwashi 'yan kallo"
"Ki matsa na shiga. Ke kin ma san ni wacece a kamfanin nan?"
"Najeeb constructions na gani ba Najeeba constructions ba dan haka duk matsayinki a ƙarƙashin mai kamfanin nan ki ke"
"Hmmm za ki sha mamaki yarinya, ko kwana ɗaya ba za ki ƙara anan ba Najeeb zai koreki, wanda su ka fi ki nitsuwa ma ba sa daɗewa balle ke shashasha"
"Eh na ji dai. A bi doka a zauna lafiya"
Khalidah ta yi tsaki ta fita. Sai da ta tafi Farida ta ja numfashi ta ce " wai! na sha da ƙyar. Wannan matar fa ta riƙe ni ba ƙaramin jin jiki zan yi ba. Allah ya yi halitta anan"
Najeeb da ke kallon komai ya ce "scary bitch"...
..............
Ƙarfe goma saura minti biyar ya fito daga office ɗin sa.
"Sir na biyo ka ne?"
Bai kulata ba ya fita bayan ya harareta.
Da ya tafi ta ce " ka ji dashi, ni kam kujeran nan tawa ce ina nan daram da kai"
Lokacin da zai dawo tare su ka dawo da Khalidah. Su na shiga office ta cigaba da bayanin abinda Farida ta ma ta sai dai hankalin sa ma baya gareta yanaga takardun da ya shigo da su.
"Najeeb ba ka ce komai ba"
"She's doing her job" ya faɗi ba tareda ya kalleta ba
"Najeeb yarinyar nan 'yar iska ce, ƙila ma 'yar ƙwaya ce kaga ɗazu wai za ta yi kokawa da ni idan na ce zan shiga office ɗinka"
"So?"
"Najeeb ka koreta, ina wancan Joseph ɗin nan da ya ke aiki da kai kafin na yi tafiya"
"Look Khalidah, i fire who i want to. For now that girl stays"
"Najeeb i demand you to sack that girl"
Da ƙarfi ya buga desk ɗin gaban shi.
"Look Khalidah, dan mahaifinki yanada 8% share a kamfanin nan doesnt mean you can make rules here. I owned 75%, i make the rules here. Understand that or ask your father, he'll explain to you. Now get the hell out of my office"
Khalidah ta fice fuuu cikin fishi.
.............
Cikin sati uku da Farida ta fara aiki a Najeeb constructions ba wanda bai santa ba. Wanda su ke tunanin ba za ta jima ba sai gashi har sati uku, shi kan sa Anas yai mamakin yadda Najeeb ya haƙura da Farida. A zuciyarsa kuma yana ganin kamar akwai lauje cikin naɗi.
Babban matsalar Farida a office ita ce Khalidah, a second floor ta ke amma kusan koyaushe tana third floor. Magulmatan kamfani su ka sanar da Farida cewa Khalidah son Najeeb ta ke, lokacin da ta zo ta yi service ɗin ta a Kamfanin ta haɗu da Najeeb tun daga lokacin kuma ta ƙi tafiya, da ke dama mahaifinta na da share a kamfanin sai ta samu ɗaurin gindi. Shekararta uku a Najeeb constructions amma ba alamar nasara sai dai ta ƙi haƙura...
Ta gaji da cin abincin canteen kullum sai kashe kuɗi ga abincin a zuba ma ka kamar kana roƙo duk da ma mafi yawancin lokuta Engr Mathew ko Arch Hamza wani cikin abokan Yakubu ke siya ma ta. Ba ma wannan ba abincin ma bai ma ta yadda ta ke so ba.
Ta zuba faten doya da ya ji ganyen alayyaho da kifi a plate. Gaba ɗaya ƙanshi ya baɗe office ɗin, ta na ci tana korawa da zoɓonta mai sanyi a haka Najeeb ya shigo. Bai ma ta magana ba ya shige office ɗin sa, yana shiga ta ji kira. Tsaki ta yi ta ce " yana gani fa abinci na ke ci" haka ta ajiye ta shiga office ɗin sa.
"Miss Salihu. The next time you eat in the office, 10% zan cire a albashin ki. Is that clear?"
"Ok Sir " ta faɗi ta fita tana ƙunƙuni...
.....................
Farida ta zaunar da Baaba Sabuwa ta yi ma ta bayanin abinda ke faruwa tsakanin AbdulWahab da Maijiddah. Da kuma ƙudurin AbdulWahab ɗin na son turo iyayen sa.
Baaba Sabuwa ta ce idan dai da gaske ne za ta sanar da Baffa Musa sai ya basu lokaci.
Farida ta ce " yanzu Baaba Sabuwa ba ki yarda ba kenan?"
"Farida na fi kowa damuwa da rashin auren Maijiddah, sai dai maganar AbdulWahab ɗin ne ta zo kamar almara"
"Addu'arta ne ya ƙarbu. Kin san tunda na zo gidan nan kullum dare Maijiddah sai ta fi awa ɗaya tana sallah tana roƙon Allah ya bata miji. Ko ba ta sallah sai ta tashi ta roƙeshi. To Ubangiji mai jin ƙan bayinsa sai ya kawo ma ta wanda ba ta taɓa tsammani ba. Baaba Sabuwa ki godewa Allah kawai ki cigaba da yi ma ta addu'a"
Cikin satin Alhaji Bello Hassan Kachako da wa su wakilan AbdulWahab su ka zo. Bakin Baffa Musa kasa rufuwa yai, shi ba dan ya gani zahiri ba ko lokacin da Baaba Sabuwa ta gaya ma sa bai gama yarda ba. Su zuwan da su ka yi idan an basu Maijiddah su na so bikin kar ya ɗau lokaci.
Baffa Musa kam zani ne ta tadda muje. Dan haka ya amince da sauri.
Sati na zagayowa aka kawo sadakin Maijiddah, dubu ɗari da hamsin. Wata uku aka sa biki su ka nemi a dawo da shi wata biyu Baffa Musa ya amince. Duk da kuwa bashida kuɗi a ƙasa dan ya gama kashe kuɗi wajen bikin su Salima. Sai dai ba zai bari damar da ya ke nema tun da jimawa ya kuɓuce ma sa ba. Allah na gani ya so a haɗa bikin Maijiddah da Farida sai dai hakan bai yiwu ba. 'Yan uwan Rayyan sun ce Rayyan yana so ya haɗa ginin sa kafin ayi biki...
Wannan babban al'amari ya sa kishiyoyin Baaba Sabuwa kowa yai tsit dan abin ya ba su mamaki, duk cikin yaran da aka aurar ba mai sa'an Maijiddah. A gaba ɗaya yaran ma Yayar Maijiddah wadda ita Maijiddan ta biyo wato Bilkisu ita kaɗai ta auri wanda yai boko sosai kuma ya ke da hali yana aiki a kamfanin insurance, sai gara-gara mijin Kulthum wanda shima ma'aikacin Kamfanin Airtel ne.
Abu kamar mafarki fa yadda su ke tsokanarta da Matar Custom sai ga shi har sadakinta an bayar saura a ɗaura aure kawai.
......................
Tana kwance wayarta ya fara ringing tana ɗagawa ta ga Sir Najeeb. Mi zai sa ya kira a wannan lokaci? Ta dai ɗauki kiran.
"Miss Salihu, i asked you to send me a copy of the proposal before you leave. What happen?"
"Ya Allah! Na manta zan turo ma ka yanzu"...
Yana zaune yana sipping tea ɗin sa ta turo ma sa saƙon. Sai da ya duba ya ga aikin bai yi kyau ba akwai gyararraki. Nan ya sake kiran ta.
Tana amsa waya ya fara faɗa "Miss Salihu what is this? Mi ki ka turomin? Haka na ce ki yi?" Jin ƙorafin yai yawa ya sa ta ce
"Domin kai ƙorafi danna ɗaya, domin neman ƙarin bayani gameda aikin da aka maka danna biyu, domin magana da Aisha Farida kai tsaye danna uku...."
Ba ta gama ba ya kashe wayar.
Farida ta yi tsaki, " shi agidan ma ba za ka huta ba aiki, ya san da ya na yi wannan ɗin. Wallahi ba za ka kasheni da aiki ba"
Najeeb ya cillar da wayar yana cize leɓen sa na ƙasa. He's waiting for the perfect time ya aiwatar da ƙudurinsa, just a perfect time. Yarinyar nan sai ta raina kanta...
*💮SAKATARIYA TA💮*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣0️⃣8️⃣
Washegari a office Najeeb bai ma ta maganar shaƙiyancin da ta ma sa ba, iya kaci tana nuna ma sa proposal ɗin ya ce ta je ta gyara.
Tana aiki sai ga Sister Munibat ta shigo.
"Sister Farida ya aiki"
"Alhamdulillah"
"Sir Najeeb yana ciki?"
"Eh ki shiga"
Minti biyar sai ga ta ta fito har za ta wuce ta ce " Sister Farida ɗan bani ruwa mai sanyi ma na, fridge ɗin office ɗina ya ɓaci"
Farida ta miƙa ma ta satchet water mai sanyi.
"Na gode sister" har za ta tafi Farida ta ce " yawwa idan kina son zoɓo ko kunun aya, gobe zan fara zuwa da shi"
Sister Munibat ta ɗan yi dariya ta ce " a cafeteria za ki dinga ajiyewa?"
"A'a anan office ɗina, mai so sai ya zo ya siya"
"Toooo, ke da Sir Najeeb kunfi kusa, amma bana tunanin zai amince da haka"
"Sister Munibat ke dai ki sanar da 'yan wajen kun nan kawai"
Sister Munibat tace "Allah ya kawo kasuwa" Farida ta amsa da Amin...
Washe gari Farida ta haɗa zoɓo gora shabiyar da kunun aya gora goma. Tun kan ta shigo ta ɗan bibbiya wajen mutanenta ta sanar da su, wasu a lokacin su ka ƙarɓa dan wa ya ke da garajen zuwa har Office ɗin Sir Najeeb siyan zoɓo...
Tana aiki a computer Najeeb da Anas su ka fito.
" 'yar uwa sannu da aiki ko"
"Na gode Yayana"
Har zai shige ta ce " Ya Anas ga zoɓo fa, harda kunun aya"
" ƙanwata kenan, kina sha'aninki"
"Yaya ai mai neman kuɗi kam kowani ƙofar samu ya gani shiga ya ke"
"Well Hakane, Allah ya kawo kasuwa"
"Na kawo ma ka zoɓo ko kunun?"
"Ki bari anjima yanzu zamu fita wani waje nida mutumunki ne"
Kafin ya gama surutun sa Najeeb kam ya yi gaba...
.....................
Tana tsugunne gaban fridge tana duba sauran zoɓonta wanda na Anas ne da na Sir Najeeb da ta ajiye mu su, yanzu Yakubu ya zo ya ƙarɓi na sa.
"Miss Salihu"
A firgice ta juyo dan ba ƙaramin tsorata ta yi ba.
"Ya Allahu! Sir Najeeb ai sai ka sa hawan jinin mutum ya tashi. You scared the hell out of me"
"To my office, Now"
Yana shigewa ta fara mimicking na sa " Miss Salihu, to my office now nnnnnnaa. Mtsww"
Ta ɗau zoɓo ɗaya wanda yai sanyi sosai ta shiga da shi.
Tana zuwa ta ajiye ma sa akan table ta ce "Sir na san kafi son shan tea ko coffee amma wannan zoɓon one in town ne. Albarkacin haƙƙin maƙotaka za ka dinga samun kyautar goran zoɓo ɗaya"
Tunda ta fara magana ya zuba ma ta ido har sai da ta kai aya. Duk yadda ya ke jin tsanar yarinyar nan wannan quality na ta na rashin tsoro yana impressing na shi. Idan ka cire Anas duk girman Kamfanin nan babu wanda ke iya tsayawa gaban sa ya faɗi magana son ransa sai ita. People fear him, but this skinny girl idonta ƙyam ya ke duk lokacin da ta ke gabansa babu tsoro ko fargaba a tattare da ita.
"Sir ka taɓa zoɓon ka ji, Allah sai ka yi santi"
"Miss Salihu, duk wani rules and regulations na wannan Kamfani yana da muhimmanci. But na ga alama ba ki ɗauke su da daraja ba. You dont wear cooperate clothes, you eat in the office you... you... you and only you Miss Salihu"
"Haba Sir, tun ranan da kace na dena cin abinci a Office fa na dena"
"Oh really, and that yellow thing you ate in the morning yersterday?"
"Kai Sir ya akayi ka gani? Ban karya ba na fito shine na karya a office"
"I see. And this" ya nuna goran zoɓo da ta ajiye"
"Alakoro na kawo ma ka fa. Tunda dai Allah ya haɗamu maƙotaka"
"Look Miss Salihu, get this in to your dumb skull. Office ba wajen ciye-ciye ko kasuwanci bane, you keep on doing it i keep on cutting your salary. Now out of my office"
Ji take kaman ta make shi amma ba hali. Ta juya a hankali tana tafiya.
"Miss Salihu" dama a kufule ta ke ta juyo da sauri ta ce " Sir yanzu kuma mi na yi"
"Take this stupid thing out of my sight"
Ta kalli zoɓon ta kalle shi tace "idan ka ga dama ka wanke bahayarka da shi"
"Wait what?" Ai da sauri ta fice daga office ɗin...
Sana'ar zoɓo da kunun aya kam Farida ba ta fasa ba sai dai ta chanja salo. Duk mai so zai yi booking ne tana zuwa tun kafin ta shiga office za ta bi ta rarraba ta ƙarɓi kuɗinta wani lokaci kuma sai an kusa tashi ta biya ta karɓi kuɗi. Anas na ɗaya daga cikin ma su son zoɓonta kullum sai ya sha gora biyu. Najeeb bai sake ma ta maganar sana'ar da ta ke ba duk da ya san bata dena ba.
Yau wani ƙaton kula ta fito da shi daga keke saboda sana'ar zoɓo da ya ƙarɓe ta. Dan ko gora hamsin ta yi sai ya ƙare.
Tana faman ɗauka sauke da kular Najeeb ya zo wucewa, a lokacin ta sauke ta na ƙoƙarin murza hannunta saboda zafi, ya tsaya yana kallonta. Haka kawai ya ji ta bashi tausayi. Yarinyar nan da garaje ta ke ina ita ina wannan ƙaton abu. Ya wuceta ba tareda ta ganshi ba, yana zuwa bakin ƙofa ya ce da security da ke wajen ya je ya ɗauka ma ta kayan...
Yau ɗan wake ta zo da shi dan haka da su ka je Cafeteria ita da Sister Munibat ta wuce wajen su Anas.
"Yayana ban san ko kanacin ɗanwake ba?"
Anas ya ce " ci kai. Ai duk lokacin da mu ka je gidan Hajiya Mama sai ta sa an yi min"
"To barin zubo ma ka"
Ta je ta zubo ma sa a plate harda dafaffiyar ƙwai akai da ɗan ganyen lettuce da albasa sai ƙamshi ya ke yi.
"Gaskiya na gode sweet sister. Allah ya miki albarka"
Ta yi murmushi ta tafi. Ko kallon inda Najeeb ya ke ba ta yi ba.
Anas ya fara haɗa ɗanwake da shinkafa yana ci yana santi.
"Are you flirting with her?"
Anas ya ɗago da mamaki ya kalli Najeeb.
"Wannan shine dalilin da ya sa yarinyar nan ta ke abinda ta ga dama a office. Because of you"
"Dude are you....are you jealous?"
" im serious Anas stop flirting with her"
Tashi yai ya bar wajen ya bar Anas da baki buɗe.
Idan dai idon sa ya ga dai-dai to tabbas kishi ya gani a idon Najeeb. But why?.... ko dai.....
Ya juya ya kalli Farida da ke ta zuba uwa surutu cikin zuciyar sa ya ce " indai abinda na ke tunani ne to, Farida kin ciri tuta. I wish ke za ki maye gurbin Sabreen a zuciyarsa"...
.....................
Tana ɗaki tana cin abinci taji alert na kuɗi ya shigo ma ta daga wajen aiki. Sai dai tashi ta yi cikin sauri saboda abinda ta gani. Ba abinda aka ce za'a biyata ba kenan, kusan kaso sittin kawai aka biyata cikin albashinta.
Cikin tashin hankali ta fara kiran numbar Najeeb sai dai bai ɗauka ba.
Ta kira numbar Anas shima bai ɗauka ba.
"Lallai ma! Kan Uba. Wallahi ba zai yiwuba na yi uwa ayyukan nan ba dare ba rana ace wannan kuɗin za'a turomin. Ta tashi ta fara shiryawa.
Maijiddah da ta shigo ɗaki ta ce " Anty ina zuwa haka"
"Wajen aiki zan je. Yau Sir Najeeb ya taɓo ni"
"Anty ba yanzu ki ka dawo ba"
"Ke dai bari zamu yi maganar idan na dawo"
A hanya Anas ya kirata akan ta yi haƙuri ɗazu suna meeting ne shiyasa bai ɗau kiran ba.
"Yayana kuna tareda Sir Najeeb ne?"
"Eh tare mu ka yi meeting ɗin amma ni na fito na barshi a office yana ƙarasa wasu ayyuka. Lafiya dai ko?"
"Ba lafiya ba Ya Anas 60% na albashina kawai na gani"
"60% kuma?"
"Eh. Na san Sir Najeeb ne yamin haka, dan haka yau ni da shi, sai ya bani cikaton kuɗina ko yaga bala'i" ta kashe wayar tana huci.
Kamfanin yai tsit saboda an riga an tashi. ID card ta nuna aka bari ta shiga duk da kuwa ma su gadin sun santa. Ba ta wuce ko'ina ba sai office ɗin Sir Najeeb. Ba ya main office ɗin sa dan haka ta je wani ɗaki da ya ke yin ayyukan sa na zane acikin office ɗin. Ta ƙwanƙwasa ƙofar.
Yana tsaka da zane ya ji ana ƙwanƙwasa ƙofa. Who could it be? Dan ya san Anas ya tafi tuntuni.
Na'urar computer da ke gabansa ya danna nan da nan Farida ta bayyana. Yadda ya ganta ya san maganar albashi ne ya kawota. Wajen da ya ke waje ne da bayan shi sai Anas babu wanda ya ke da access na shiga, work place na shi kenan. Anan ya ke duk wani zane-zanen sa. Wajen zagaye ya ke da glass. Glass ɗin daga ciki za ka ga mutum amma daga waje mutum ba zai ga na ciki ba. Kana shigowa ɗakin idan ba ka da katin buɗe ƙofar glass ɗin to ba tayadda zai buɗu...
Tana tsaye ya buɗe ƙofar ya fito.
"Sir Najeeb ban gane manufarka ba. Me na yi aka cire 40% na albashina?"
Yadda ta ke maganar kamar za ta doke shi.
Bai kulata ba ya je ya zauna a kujerar sa.
"Sir Najeeb i demand an explanation"
"Ofcourse Miss Salihu. Ni na cire 40% na albashinki as a compensation for all your irrational behaviours in this company"
"Sir Najeeb idan ma yaren China ka ke gara ka dena dan ni banjin wannan yare. Ka tura min cikaton kuɗina kawai, abinda na sani kenan"
Murmushin yaƙe yai sannan ya ce " next month ma ki dinga take dokokin kamfani and i'll keep on cutting your salary"
"Cabɗi! Wallahi ba ka isa ba"
Tasowa yai ya nufi kanta ta fara ja da baya.
"Mi za ki yi idan na cire? Yau ma hugging ɗina za ki yi? Go ahead and i'll make sure you get what you are looking for"
Ganin ta kai jikin bango ya sa ta haɗiyi miyau.
"Come on hug me. Na san abinda ki ke so kenan, well yau ba Anas ba yayanki, nobody is here just me and you"
"Idan ma giyan wake ka sha. Wallahi na fika hauka. Kkkka matsa min"
Kallonta ya ke yi yadda take fitar da numfashi da sauri-sauri har yanajin bugun kirjinta.
"Scary bitch..."
Buɗe ƙofar da akayi ya sa yai saurin juyawa to his dismay sai ga Joseph biye dashi kuma wasu zaratan maza guda uku.
"What the hell are you doing here Joseph?"
Bindiga su ka fito da shi Farida ta ƙwalla ƙara ta ɓoye a bayan Najeeb jikinta na rawa tana salati.
"If you comply, nobody gets hurt" a cewar Joseph
Najeeb ya ce "Let the girl go"
"Shut up" ɗaya daga cikin guys ɗin ya daka ma sa tsawa
"Tie them both"
Farida na jin haka ta ƙwalla ƙara ta ƙara ƙanƙame Najeeb....
..........................
A yadda ya tsara sai ƙarshen wata idan Aneesa ta zo Lagos zai ma ta bayanin komai sai dai ko a ina Aneesar ta ji labari?.
Yana zaune a office su na waya da gimbiyarsa, Aneesa ta shigo fuuuu.
"You liar, sai yaushe ka ke son sanar da ni? Bayan an ɗaura aure?. You evil son of a bitch"
"Anny minene haka kuma"
"Munafuki, asirinka ya tonu ai. Wato har sadaki ka kai. To barin gaya maka Abdul wannan auren ba zai taɓa yiwuwaba"
"Aneesa kenan. Dama abinda ya taso da ke daga Abujan kenan. To ki sani aure babu fasawa tunda dama na gaya miki ai"
"Abdul Wallahi ba zai yiwuba. Idan ma wasa ka ke gara ka janye, i will never share you with anyone"
"Ina son ki Aneesa amma duk abinda ya faru ke ki ka jawo. Ba ni da ra'ayin mata biyu sai da ki ka zaɓi aikin ki fiye da ni"
"Wallahi sai dai ka zaɓa ko ni ko ita dan ba zan zauna da kishiya ba"
"Its too late Aneesa. Wata biyar da su ka wuce da na gaya miki saƙon Hajiyata what did you say?"
"Haka za ka ce ko. To mu zuba mu gani and i'm taking my kids with me"
"Tunda daga gidan ku ki ka zo da su ba"
Ficewa ta yi daga office ɗin kamar wata zararriya...
............................
Har ƙarfe tara na dare ba Farida ba dalilinta ga numbarta ba ya shiga. Maijiddah ta je ɗakin su Yakubu lokacin shima ya dawo daga hira kenan zai ci abinci.
"Amarya Amarya, ya akayi?"
"Yaya Yakubu Anty Farida ta kira ka ne?"
" Farida kuma. Ai ni tun da mu ka dawo daga wajen aiki rabona da ita"
"Yaya numbarta ba ya shiga kuma ta ce za ta je Kamfani wajen Oganta"
"Sir Najeeb"
"Eh"
"To barin kira Anas na ji"
Sai da ya sake gwada numbar Farida still baya shiga kafin ya kira Anas.
Anas ya sanar ma sa yadda su ka yi da Farida sannan ya ƙara da cewa shima ya yi ta gwada numbar Najeeb amma ba ta shiga.
Yakubu ya ajiye waya ya kalli Maijiddah ya ce " barin je Kamfani in dubata. Ko tana chan dan numbar Sir Najeeb ma ba ta shiga"...
Anas ne ya riga shi isa Kamfanin, lokacin da Yakubu ya iso a wajen motar Najeeb ya tarar da Anas da wasu securities su na magana.
"An ganta kuwa?" Yakubu ya faɗa a kiɗime
Anas ya girgiza kai ya ce " Yaks i think they have been kidnapped"
"What!"....
*Free pages sun kusa zuwa ƙarshe*
*ga mai son cigaban labarin zai biya #200 kacal ta wannan account ɗin 3099546325 Azizat Hamza, firstbank. Idan kuma credit card ne to MTN card na 200 za a turo wa wannan numbar 08137311900. Sannan za a turo shaidar biya (screenshot) na kuɗin zuwa numbar nan still 08137311900. Ko kuma ka biya #300 ka samu labarai biyu sakatariya ta da kuma tsohuwar soyayya*
*💮SAKATARIYA TA💮*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣0️⃣9️⃣
"Wayyo Allah Ummi na. Wayyo Ummi naaaaa" abinda ta farka da shi kenan lokacin da ɗaya daga cikin mutanen da su ka sato su ya watsa musu ruwa.
"Shut up" ya daka ma ta tsawa. Nan kuma ta fashe da kuka tana cewa " dan Allah kar ku kashe ni, ni ɗaya ce a wajen Mahaifina kuma ko jika ban haifa ma sa ba"
Tare aka ɗauresu da Najeeb bayansu na gogan na juna sai dai tun da ya farfaɗo baice ƙala ba.
"Sir Najeeb ka ce su bar ni na tafi. Iyayena talakawa ne, ba su da kuɗin da za su basu, yanzu ma Baffa na cikin bashi yake saboda hidimar biki da yai..." saukar mari taji a fiskarta wanda ba shiri ta fashe da wani matsananci kuka.
"Chachachacha, you talk too much abeg"
Buɗe ƙofar ɗakin aka yi Joseph da sauran su ka shigo.
"Well well well. The Almighty Sir Najeeb, the perfect man. Mr get out of my office" ya sa hannu ya murɗe kunnen Najeeb da ƙarfi.
"I will make sure you suffer before this is over"
"Untie him" ya faɗi yana yiwa Najeeb kallon tsana.
Kunce shi su ka yi ya ce su ma sa tsirara ai Farida na jin haka ta fara bada haƙuri.
Ɗaya daga cikin su wanda ya ke kamar shine Oga ya zuƙa wiwi da ya ke sha ya ce ma sa ɗan uwa ba haka akeyi ba, idan kana so su biya kuɗi to dole 'yan uwan sa su tabbatar yana cikin ƙoshin lafiya.
"Emeka why now?" Joseph ya faɗi cike da takaici
"Bros let me handle it" wanda aka kira da Emeka ya faɗi. Zuwa yai ya cirewa Najeeb takalmansa da agogo yace " so na designer you wear" naushin cikin Najeeb yai wanda sai da Najeeb ya wantsila.
Shi kuwa Joseph zuwa yai ya taka kafar Najeeb. Ba ƙaramin zafi ya ji ba amma haka ya shanye bai nuna ba.
Lokacin da za su tafi Joseph ya tofa wa Najeeb miyau a fiska. Har su ka fita daga ɗakin bai buɗe ido ba saboda tsananin ƙyanƙyamin abinda Joseph ya ma sa.
Ɗankwalin atamfar ta ta ɗan yaga ta zo ta goge ma sa miyau ɗin.
"Wai mi ka yiwa wannan guntun ne? Joseph ko me su ke kiran sa"
Bai buɗe ido ba kuma bai yi magana ba.
"Dalla buɗe idon. Ba na riga na goge miyau ɗin ba"
A hankali ya buɗe rinannun idanunsa ya ɗaura akan na ta. Itama ɗin shi ta ke kallo for some weird reasons sai ta ji ya ba ta tausayi. Wannan fa ɗan gata ne gaba da baya, CEO na babban kamfani amma Joseph ya ma sa wannan walaƙanci.
"Wannan bayan kuɗi da su ke so akwai bita da ƙulli tsakanin ku. Allah ya sa dai kar su kashe mu"
Ta kalli ƙafar da Joseph ya taka yatsun wajen sun yi jaa sun kumbura. Ta kai hannu za ta taɓa ya janye ƙafarsa da sauri.
" kaa! Dan ma zan taimaka ɗin, to ka ci kan ka"
Ta koma chan gefe ta zauna. Yanzu da aka kuncesu ta ɗan ji saƙayau.
"Ni wallahi yunwa na ke ji, ba dan kai ba da yanzu ina gida ina cin abinci. Ni daga mun kai gida lafiya ma ajiye ma ka aiki zan yi. Irin wannan aiki da kasada ba dani ba"
Tana cikin surutu aka buɗe ƙofa, abinci aka kawo mu su, take away guda biyu na shinkafa da satchet water guda biyu. Ko kallon inda abincin ya ke Najeeb bai yi ba. Farida kam jawo abincin ta yi ta fara ci dan Allah na gani ba ta iya juran yunwa. Abincin ba wani yawane da shi ba hakanan nan taste ɗin dai ba laifi da alama daga restaurant su ka ƙarɓo.
"Sir Najeeb ka ci abinci fa, da zafin sa kar yai sanyi"
Tashi yai ya ɗau ruwa ya shiga wani ƙofa da ke cikin ɗakin wanda ya ke tunanin banɗaki ne. Banɗakin ne sai dai gaba ɗaya a ƙazance ya ke da ƙyar ya kama ruwa yai alwala ya fito dan ba ruwa a wajen, famfom baya aiki.
Sai da ta ga ya je gefe ya tada sallah itama ta ankara ba ta yi sallar maghrib da Isha ba, gashi ta shanye ruwanta.
Dole sai taimama ta yi bayan ta leƙa banɗakin ta ga ba ruwa.
Tana zaune ta jingina da bango ta fara gyangyaɗi ƙarshe baccin wahala ya saceta....
..........................
Kafin ƙarfe goma na dare iyalen Alhaji Adam Jibo sun samu mummunan labarin rashin Najeeb da Sakatariyar sa. Abinda ya ɗaure mu su kai har lokacin ba a kira su gameda ransom ba. Bacci kam ƙauracewa iyalen yai bama kamar baby da ta dinga kuka wiwi da ƙyar Mom ta shawo kan ta ta yi shiru.
Gidan Baffa Musa ma dai hankulansu a tashe ya ke. Ba ma kamar Baffa Musa wanda ya ke gani kamar sakacin sa ne ya sa Farida ta faɗa wannan hali. Yadda Baffa ya hana a sanar da Ummi amma hakan bai yiwuba dan kafin yai maganar ma tuni Anty Hanne ta kirata ta sanar ma ta an sace Farida. Hankalin mutanen Jos ya tashi a wannan dare, a daren Ummi ta so ta zo amma Baba da Nanna su ka hanata, su ka ce ba abinda za ta yiwa Farida sai addu'a ta bari idan gari ya washe sai ta je.
Haka aka wayi gari gidajen biyu ba kwanciyar hankali. Ƙarfe tara na safe aka kira Alhaji Adam Jibo bayan an tura ma sa hoton Najeeb da Farida ɗaure. Miliyan hamsin su ke buƙata cikin awa ashirin da huɗu ko kuma su rasa su gaba ɗaya.
Anas ya sanar da Yakubu cewa kidnappers ɗin sun nemi ransom na 50million. Ya kuma kwantar ma su da hankali akan za a kuɓutar da su.
Baffa Musa da Yakubu su ka nufi gidan su Najeeb. Sun samu su Alhaji Adam su na meeting da wasu special police kan al'amarin sai da su ka gama sannan Dad ya saurare su.
"Alhaji dama maganan kuɗin nan ne. Ni dai a wajena idan na shiga na fita za a samu miliyan uku sai dai kaga ko rabin abinda su ke buƙata ba a kai ba"
"Alhaji Musa ka kwantar da hankalinka Insha Allahu komai zai zo da sauƙi. Maganar kuɗi kuma Alhamdulillah an fara arranging na su. Kar ka damu"
.......................
Da safe Emeka ya shigo ɗakin ya fara faɗa harda marin Najeeb wai 'yan uwansa ba sa son shi suna buƙatar 48hrs su haɗa 50million.
"I thought your parents are super rich. They better not play games with me"...
Emeka cousin ɗin Joseph ne, ya jima yana fashi da makami kafin daga baya ya koma harkan kidnapping. A Kaduna ya ke operation ɗinsa sai dai wata ɗaya da ya wuce Joseph ya kira shi akan yanaso ya kidnapping Najeeb saboda ya ɗau fansar abinda ya ma sa. Wannan ya sa ya zo Kano su ka fara tsare-tsaren yadda komai zai tafi. Da ke Joseph yai aiki a Najeeb constructions hakan ya bashi daman sanin hanyoyin da za su aiwatar da ƙudirin su.
Da safe ba a basu abinci ba haka da rana, gaba ɗaya Farida ta galabaita. Tana chan ta cure gefe guda ta yi kukan ta yi surutun har ta gaji. Najeeb kam ko ehem bai ce ma ta ba.
Buɗe ƙofar ɗakin aka yi, ɗaya daga cikin ma su tsaresu ya shigo ɗauke da bindiga. Zuwa yai ya jawo Farida da ƙarfi, Najeeb ya tashi zai yi kan sa. Ya nuna ma sa bindiga tareda cewa "sit"
Farida ganin anyi hanyar waje da ita ta fara cewa Najeeb ya taimaketa.
"Dont hurt her" Najeeb ya faɗi da kakkausar murya
Wani ɗakin ya shiga da Farida bayan ya kulle Najeeb a ɗakin da su ke da farko.
Ganin ya yo kanta ya sa ta ƙwalla ƙara tana kiran Sir Najeeb da Umminta.
Guje-guje su ka fara yi a ɗakin wanda ya ke cike da tarkacen kayan maye. Cak ta tsaya lokacin da ƙafarta ya taka wata fashashshiyar kwalba. Hakan ya bawa mutumin damar kamata ya kwantar da ita da ƙarfi, sai ihu ta ke ta na ƙoƙarin tureshi amma ta kasa. Ya kama hannayenta da hannunsa ɗaya, ɗaya hannun kuma yana ƙoƙarin zuge zip ɗin wandonsa.
Wani razannannen ƙara ta ƙwala wanda gaba ɗaya gidan sai da ya ɗauka.
Emeka da wasu biyu su ka yo ɗakin da su ka ji ƙaran da gudu. Ganin Larry na shirin afkawa Farida ya sa Emeka ya ture Larry tareda kwaɗa ma sa mari.
"Are you crazy?"
Larry ya ce" the girl too hot Oga. I feel...."
"Will you shut up. You want to ruin my business abi"
Ce wa ɗayan yai ya maida Farida ɗakin da Najeeb ya ke.
Da ɗingishi ta shigo ɗakin saboda har lokacin kwalbar da ta caketa na ƙafar.
Tunda aka fita da Farida hankalinsa ya tashi yasan ba kasheta za'ayiba amma ba makawa sai sun yi raping ɗinta. Lokacin da ya ji ƙaran da ta yi sandarewa yai a wajen jikinsa ya fara ƙyarma yana ayyana abinda zai yiwa Joseph da crew ɗin sa idan sun fita anan. Ganin yadda aka shigo da ita ya sa yai kan ta da sauri. For the first time tun jiya da aka kawo su ya ma ta magana.
"Miss Salihu are you Ok. Mi su ka miki?"
Shiga jikinsa ta yi tana kuka jikinta na rawa. Ta gama tsorata dan ta sadakar Larry shigarta zai yi. Tausayinta ya mamayeshi dan ya san saboda shi ta shiga wannan haɗarin dan Joseph da shi yake gaba. Cuddling ɗin ta yai so tight yana ba ta haƙuri. " I'm sorry, i'm very sorry Miss Salihu"
Sun jima a haka shi kan sa ya rasa dalilin da ya sa ya ji wani nitsuwa ya shigeshi farat ɗaya, like kada ya saketa su cigaba da tsayuwa a haka.
Zafin da ta ji a ƙafarta ya sa ta tuno da kwalbar da ta taka. Cikin sheshsheƙar kuka ta ce "Sir Najeeb ƙafa na" sai alokacin ya saketa ya fara duba ƙafan wanda ke ta zubar da jini.
Zaunar da ita yai sannan ya ɗaura ƙafar a cinyarsa ya ce " zan cire mi ki kwalbar, sorry it will hurt"
Girgiza kai ta yi tareda rufe idonta, ta cize leɓe. A hankali ya cire kwalbar tareda ɗaure ƙafarta da farin hankerchief sannan ya sake jawo ɗankwalinta wanda ya faɗi lokacin da Larry ya fita da ita. Ya yaga ya sake ɗaure ƙafar sosai.
"Are you Ok?" Ya tambaya yana kallonta.
Girgiza kai ta yi ta ce nagode.
Bayan minti shabiyar aka kawo mu su abinci, ko kallon wajen Farida ba ta yi ba duk da kuwa yunwar na cinta.
"Ki tashi ki ci abinci" ya faɗi lokacin da ya ga ta share abincin.
"Ba zan ci ba. Wataƙila ma sun sa magani"
Zuwa yai ya ɗau take away ɗaya da ruwa ya kawo gabanta. " ba abinda za su sa aciki, because they need us alive. Besides na san yunwa ki ke ji"
Ta kalleshi ta kalli abincin ta ce " to kai ma ka ci, tunjiya ba abinda ka ci"
"Na saba da rashin cin abinci"
"Ana sabo da yunwa ne?" Bai amsa ma ta ba sai sokalin abinci da ya kawo dai-dai bakinta ya ɗaga ma ta kai alamar ta ci. Ba tai musu ba ta fara ci. Haka ya dinga bata abincin a baki har ta cinye.
"Kin ƙoshi?"
Ta gyaɗa ma sa kai...
Da dare zazzaɓi ya rufeta, tsoratar da tayi da kuma ciwon da taji su suka haɗu su ka sa mata ciwon kai da zazzaɓi. Tana kwance ta fara rawan sanyi harda kakkarwa. Daga inda ya jingina ya jiwo nishinta.
"Miss Salihu are you OK?"
Jin shiru ya sa ya taso ya je wajenta. Jikinta yai zafi sosai ga ba ruwa balle ya dinga shafa ma ta.
A hankali ya ɓalle buttons ɗin shirt ɗin sa ya mannata da ƙirjin sa. Thats the only option he can think of...
Ta jima a haka kafin zazzaɓin ya saketa amma bai janyeta daga jikinsa ba har bacci ya tafi da ita. Shi kam ya manta yaushe rabon da yai bacci without his pills.
Farkawan da za ta yi ta jita ajikinsa. For the first time tun haɗuwarsu sai ta ji kunyar sa. Da ƙyar ta iya tashi, nan ma sai da ya tallafa ma ta saboda ƙafarta da ya kumbura yana ma ta zogi.
Suna buƙatar ruwa dan haka ya je ya fara bubbuga ƙofa.
"What do you want?" Aka faɗa da kakkausar murya.
"Water"
"Una no go get any water for here ooo"
" please, give Us some water" Najeeb ya rintse ido saboda tuno matsayinsa ada da kuma matsayinsa a yanzu wai shi ke roƙon ruwa.
Da ƙyar wanda ke gadin ƙofar ya kawo mu su ruwa biyu, nan ma sai da ya cire belt ɗin Najeeb wai itama designer ce idan ya sayar zai samu kuɗi...
Ƙarfe shabiyu na rana Emeka da Joseph su ka zo mu su da albishirin yau za a sake su idan har an biya cikakken kuɗin da aka buƙata.
A fili Farida ta ce " miliyan hamsin ɗin. Kai amma karayar arziƙi ta sameka Sir Najeeb"
Dariya ta bashi saboda bata san networth na shi a shekara ba. Ko za a cire miliyan hamsin sau goma ba zai girgiza ba. Balle ya san idan har da gaske za a biya waɗannan kuɗaɗe to Dad ɗin sa ne zai biya, ba sai ya nemi taɓa masa kuɗi ba.
"Kenan za ka kori ma'aikata dayawa idan ka koma. Dan Allah kar ka kori ɗan uwana. Yakubu shi kaɗai yai degree a gidan Baffa Musa, kaga yayansa Faruƙu mai ƙaton hancin nan, ko sakandari bai gama ba, kasuwanci ya jona kaman na ubansa. Dan Allah ka min alƙawari ba za ka koreshi ba"
Murmushi kawai Najeeb ya yi.
"Sir Najeeb ka ga yadda ka yi kyau kuwa da ka yi murmushin nan. Dan Allah idan an koma office ka dena haɗa ran nan, ba ka kyau"
Juyar da kai yai yana kallon gefe duk da kuwa hankalinsa na ga surutun da Farida ke yi...
........................
Har za a tashi Dad ya ce ayi addu'a.
Aka ɗaga hannu aka yi addu'a sannan aka shafa.
Anas ya ce Dad " Insha Allah ko mi zai tafi according to plan"
"Allah ya sa Anas"
Anas ya kalli sauran officers ɗin ya ce "gentlemen, let's go"...
Emeka yana zaune da Joseph su na jiran Larry da ya tafi ɗauko kuɗi. Tun ɗazu aka ce an ajiye kuɗi a inda su ka buƙata.
Sun gargaɗi Larry akan ya tabbatar ba wanda ke binsa lokacin da ya ɗau kuɗin, shi ya sa ma su ka ce yana tabbatar da kuɗin na cikin jakar to ya sa jakar a ƙatuwar jakar Ghana-must-go da su ka bashi.
Minti biyu sai ga kiran Larry. Emeka ya sa ihu lokacin da Larry ya ce ya ɗauka kuɗin. Ya kalli Joseph ya ce "Bros we are rich"
Plan ɗin da su ka shirya shine, dama suna da mota, a daren za su bar Kano shi kuma Joseph saboda Najeeb ya ganeshi suna barin Kano daga Kaduna zai wuce ƙasar Ghana. Anan zai zauna har komai ya lafa kafin ya dawo.
Suna cikin tattauna plan ɗin su Larry ya shigo da jakar kuɗi.
Da sauri Emeka ya buɗe jakar ya ce su duba kuɗi sannan su duba ko akwai tracker aciki dan a matsayinsa na wanda ya kwana biyu yana aikin yasan ana iya samun wannan idan aka aiko da kuɗin ransom. Ganin babu tracker ya sa su ka fara jera kuɗin a wata jakar daban.
Abinda ba su sani ba shine sai da aka buɗe jakar aka sa ƙaramar tracker chip aciki sannan aka ɗinke kamar ba a sa komai ba.
Su Emeka na duba kuɗi sauran na shan giya suna ihu su ka ji kamar ana buɗe ɗaya daga cikin ƙofofin gidan.
Emeka ya ce su je su duba ko su Najeeb ne ke son guduwa.
"Larry, you sure say nobody follow you"
Larry ya gyaɗa ma sa kai.
Fitar sauran ke da wuya su ka ji ƙaran bindiga...
"Shi kenan, Sir Najeeb kashe mu za su yi. Ga shi sun fara harbin junan su" Farida ta faɗi kamar za ta yi kuka ta kuma matsowa kusa da Najeeb ɗin.
Shi Najeeb ya gane abinda ke faruwa dan ƙaran bindigan ba iri ɗaya bane.
Jin ana shirin buɗe ƙofa. Najeeb ya kalli Farida ya sa yatsunsa biyu a baki alaman ta yi shiru...
Joseph ne ya buɗe ƙofar ɗauke da bindiga,yana shigowa bai gansu ba zai juya kenan aka kwaɗe kan sa daga baya, sai bindigar ta faɗi, yai taga-taga zai faɗi shima Najeeb ya kuma jawoshi ya gwara shi da gini. Ƙiɓar Joseph ya ke kamar wanda aka aiko shi.
Wani police ne da Anas su ka shigo ɗakin lokacin da Farida ta ga Anas ta ce "Alhamdulillah ashe ku ne"
Najeeb kam yana kan Joseph yana ƙiɓar sa sai da Anas da police su ka zo su ka ɗaga shi, dan tuni Joseph ya suma jini na fita ta hanci da baki...
Da ɗingishi ta ke takawa lokacin da su ka fito, komai ya lafa, Anas ya ce mu su an kashe ɗaya daga ciki sauran kuma duk an kamasu. Emeka da yake ogansu ma an halbeshi a cinya.
"Miss Salihu" muryarsa ya doki kunnenta, ta tsaya da tafiya sannan ta juyo a hankali. Kafin ta yi magana ya sa hannu ya ɗauketa cak.
Mamaki ƙarara ya bayyana a fiskarta. Anas da ke gefe ma mamakin ne ya kamashi.
Kai tsaye motar Anas ya nufa da ita sai da ya kwantar da ita a backseat sannan ya dawo gaba ya shiga, Anas ya ja su su ka bar wajen.
Suna cikin tafiya Anas ya ce "asibiti za mu je ko gida"
"Asibiti" Najeeb ya faɗi a hankali....
Ƙarfe goma da rabi su ka baro asibitin bayan an duba ƙafar Farida. Ganin an yi wata hanya da ba ta gidan su ba ya sa ta ce " Ya Anas ka kaini gida ina so na ga Ummi na. Na san tana chan hankalinta ya tashi"
Anas ya ce " ai su Baffan na ki su na gidan su Najeeb"
Ba ta sake cewa komai ba har su ka isa gidan su Najeeb.
Ana jin tsayuwar mota gaba ɗaya aka fito dan dama duk iyalen gidan a matse su ke. Baffa Musa, Yakubu da Ya Faruƙ su ma suna nan suna jiran dawowarsu. Dama tunda abin ya faru su ke sintiri tsakanin gidan su Najeeb. Ummi ta so ta biyosu Baffa Musa ne ya hana...
Najeeb ne ya fara fitowa da sauri ya buɗewa Farida ƙofa ya taimaka ma ta ta fito duk da kuwa yanzu ƙafar ta rage zogi.
Baby ce ta fara zuwa da gudu ta rungume Najeeb kafin sauran su ka ƙaraso.
Baffa Musa abinda bai saba ba yau ya yi. Shima zuwa yai ya rungume Farida yana hamdala. Ita kaɗai ce ɗiyar ɗan uwansa, ita ya ke gani ya tuna da ɗan uwansa.
Daga compound ɗin gidan Baffa Musa ya ce za su wuce gida. Dad ya ce su bari sai da safe tunda dare ya yi. Baffa ya ce " Alhaji ai idan ban kai 'yar nan wa uwarta ba, uwarta za ta iya haɗiyar zuciya. Bari mu tafi kawai"
Musabaha su ka yi da Dad sannan su ka wuce wajen na su Motar. Yakubu ne ya tallafa ma ta har su ka isa wajen motar Baffan...
Idan ka cire yara ƙanana duk sauran kowa idon sa biyu saboda jiran dawowar Farida. Su Baffa ba su iso gida ba sai sha biyu saura na dare.
Su ma ɗin daga bakin gate aka taresu. Farida ta rungume Ummi tana kuka Ummin ma na yi. Da kyar aka raba su.
Wanka da ruwa mai zafi ta yi, ta gasa jikinta sosai, ta jima a banɗakin dan kwana biyu kenan ba wanka. Tana fitowa Ummi ta sa ta a gaba da abinci. Allah na gani bacci ne yanzu a idonta ba abinci ba amma da Ummi ta takura dole ta zauna za ta ci.
Ummi ta ƙarɓa cokali ta fara ba ta abincin a baki. Hakan ya sa Farida ta tuno lokacin da Sir Najeeb ke ba ta abinci, haka kawai sai ta tsinci kan ta da murmushi.
*💮SAKATARIYA TA💮*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣1️⃣0️⃣
Tana tsaye jikin balcony na gidan tana kallon mai yankan flower wanda ke faman gyara flowers ɗin gidan, ya saƙalo hannunsa ta ƙugunta sannan ya manna ma ta kiss a wuya ya ce "do you like it?"
"Gidan yai kyau sosai. Its perfect" ta amsa ma sa
Juyo da ita yai ya ce"This is our home Aysherh"
Murmushi ta yi ta manna ma sa light kiss sannan ta ce "our home is beautiful my love"....
A hankali ya buɗe idonsa wanda su ka ma sa nauyi saboda gajiya, ya rufesu saboda hasken da ya karaɗe ɗakin yaiwa idonsa ƙarfi. Ɗan wasu daƙiƙai ya ɗauka kafin ya sake buɗe idon a karo na biyu.
Lokaci guda kuma mafarkin da yai ya dawo ma sa. Da sauri ya tashi zaune saboda tunowa da yai da abinda ya gani a mafarkin. Agogo ya duba ya ga ƙarfe shaɗaya na safe, kenan ya jima yana barci. Idan ya tuna da kyau to ba maganin bacci ya sha ba jiya. Ya shigo ɗaki, ya taking hot shower ya sanya jallabiya ya gabatar da sallar maghrib da Isha, kaman yana azkar bacci ya tafi da shi. To wa ya maidashi kan gado? Ya janye tunanin ta hanyar tashi ya shiga banɗaki...
Fitowar da zai yi bayan ya shirya cikin ƙananun kaya baƙar shirt da guntun wando baƙi na jeans ya haɗu da Mom tana haurawa sama.
"Son ya jiki?" Ta faɗa a hankali
" lafiya Justice" ya faɗa ba tareda ya kalleta ba.
Mom ta bishi da ido tana haɗiye wani abu mai ɗaci da ya taso ma ta tun daga wuya.
Adama ya samu tana goge-goge a falo.
"Hey ina baby?"
"Sir ta tafi makaranta"
"Dad fa"
"Yana waje"
Fita yai daga falon dan ya san inda zai samu Dad ɗin.
A wajen gazebo da ke garden ya samu Dad, yana zaune yana karatun littafi.
"Come here son" Dad ya faɗi lokacin da Najeeb ke ƙoƙarin zama a ɗaya kujeran.
Zuwa yai ya tsugunna a gaban Dad, Dad ya manna ma sa peck a goshi ya ce "Allah ya ma ka albarka"
Najeeb ya amsa da Amin
"Ya jikin na ka?"
"I'm fine Dad"
"Allah ya ƙara sauƙi"
Dad ya ajiye littafin ya fara bayani
"Ka ga irin abinda na ke gaya ma ka ko. Joseph ya ce korarsa da ka yi shi ya sa shi ɗaukan wannan mummunan mataki a kan ka. Ɗa na, ka dinga danne zuciyarka kana haƙuri da mutane, Allah ya baka ɗaukaka da daraja ne domin ya jarrabaka. Su wanda su ke ƙasa da kai akwai haƙƙin su akan ka kuma Allah zai tambayeka ranar gobe"
Ƙaran wayan Dad ne ya katse hirar ta su. Yana ɗauka ya ce " to muna shigowa"
"Najeeb, Hajiya ce ta zo. Mu shiga ciki"
Ba mu su ya tashi su ka jera da Dad ɗin.
Hajiya Mama da kan ta ta yiwa Najeeb girki ta kawo, wai dole sai ya cinye dan ta san bai ci abinci ba a chan. Haka ta tisa shi a gaba yana cin abinci tana tambayarsa gameda kwana biyun da yai a hannun su Joseph. Mom na gefe tana kallon su, kwaɗayin wannan dama da ta rasa ta ke yi, hira tsakanin uwa da ɗa.
Ko sai yaushe Najeeb zai ba ta dama ta gyara kura-kurenta na baya?...
........................
Da yamma Yakubu ya kawowa Farida wayarta wanda aka samu a gidan da aka tsaresu duk da kuwa an yarda sim ɗin ciki.
"Anas ya ce zai zo ya gaishe ki bayan sallar isha"
"Allah ya kawoshi lafiya" ta faɗi tana cin farfesun kayan cikin da Ummi ta haɗa ma ta...
Tana sallar Isha aka kira wayar Maijiddah. Maijiddah ta duba numbar ta ja tsaki ta ajiye wayar gefe.
Kwana biyu kenan Aneesa matar AbdulWahab tana damunta da kira da texts, ranan da ta fara kira ba irin ɗibar albarkar da ba ta ma ta ba. Gashi ita ba mai iya maida magana bane, haka ta gama zagin ta kashe wayar. Lokacin jimamin rashin Farida ya sa ba ta wani damu da abinda Aneesar ke ma ta ba.
"Matar AbdulWahab ce ta kira ki ko?"
Maijiddah ta gyaɗa kai.
"Ban wayar na bata amsar maganganunta"
Maijiddah ta langwaɓe kai ta ce " Anty dan Allah ki barta. Idan ta gaji za ta bari"
"Hmmm a tarihin rayuwata ba na gani in ƙyale dan haka bani wayar kawai"
Maijiddah ta miƙo wayar dan ba yadda ta iya.
Bugun farko ba a ɗauka ba sai a na biyu.
"Assalamu Alaikum Uwargida ran gida, da fatan kina ta shirye-shiryen zuwan amarya?"
Daga ɓangaren Aneesa ta ce " who's this?" Dan muryan bai yi kama da na Maijiddah ba wacce ranan farko da ta kirata haƙuri ta dinga ba ta.
"Aisha Farida ce, yayar Amarya Hauwa Maijiddah. Na kira ne in gaya mi ki kar ki kuskura ki sake kiran ƙanwata saboda naga alama ƙwaƙwalwar kifi ce a kwanyar ki"
"Ke! ƙaramar karuwa ki kiyayi bakin ki. Ki kuma ja wa ƙanwar ki kunne karta yadda ta shigo gidana"
"Ashe ke Jaka ce, daƙiƙiya, Tinkiya mai kamar Aladu. Har kin isa ki hana Jidda zuwa gidan ki. Idan ba kwartonci ba, mijinki na Lagos kin maƙale a Abuja wai ke sarkin aiki. To tunda ke bakisan yadda ake riƙe miji a tarairayeshi ba, shi ya samu wacce za ta zauna kusa da shi ta kula da shi. Kuma wallahi wallahi ki ja girman ki ki dena kiran ƙanwata ko kuma mazaunanki su yi tsami"
Yadda Farida ke magana da faɗa-faɗa ya ƙara tunzura Aneesa.
"Ke matsa chan jahila mai kama da...."
Farida ba ta bari ta ƙarisa ba ta amsa da cewa " ke ce jahilar ai. Kwartuwa mai bin gindin maza, Allah ya wadai da halin ki. Tir da ke Aneesa mai ƙaton baki. Hooooo ashewo....Hoooo ashewo" (ashewo- karuwa)
Aneesa ta yi saurin kashe wayar saboda zuciyarta da ke bugawa da ƙarfi-ƙarfi.
Wannan wace irin yarinya ce haka, lallai kuwa Maijiddah za ta ci ubanta idan ta shigo ma ta gida. Sai da ta gama banbamin bala'i sannan ta dubi screen ɗin wayarta ta sa hannu ta shafa lips ɗin ta.
"Ko wa yace ma ta ina da babban baki? Ba dai AbdulWahab ba"...
Farida na jin an kashe wayar ta sa dariya ta ce " ƙaramar 'yar iska, da ki tsaya ma na"
Ta kalli Maijiddah da ta yi zuru-zuru da ido
"Ke kuma ki cigaba da yin shiru-shiru har wannan matar ta sa mi ki ciwon zuciya. Gara ki ɗaure ɗamara dan wannan matar da alama 'yar tasha ce"
"Sannu Malama Farida, expert a ɓangaren rashin mutunci"
"Kai Yakubu ba na son iskanci fa"
"Ki fito Anas na jiran ki a waje"
Gyale kawai ta yafa ta fita bayan ta gayawa Ummi. Gaishe shi ta yi lokacin da ta shiga motar na shi.
" 'yar uwa ya jiki"
"Da sauƙi yaya na"
" ashe ba ƙaramin jin jiki ku ka yi ba. 'Yar uwa ya abin ya faru ne? Najeeb ya ƙi ya bani labari"
Dama abinda ta ke jira kenan ta fara karanto ma sa yadda abin ya faru. Labarin da tun safe ta ke faɗawa 'yan gidan su da maƙota da ke zuwa gaisuwa.
Abu ɗaya ta ƙi faɗa wanda ita kanta duk yawar maganarta ta rasa dalilin ƙin faɗar da ta yi. Ta ƙi faɗin cewa Joseph ya tofa wa Najeeb miyau.
Sai da ta gama ba da labarin Anas ya ba ta wani envelope ya ce "wannan daga Najeeb constructions ne. Kuɗin magani"
ya miƙa ma ta wani envelop ɗin ya ce " wannan kuma Dad ne ya baki, kuma ya ce na gaishe ki da jiki"
"Kai na gode sosai, ka miƙa godiyata wajen Daddy dan Allah. Najeeb constructions kuma sai mun zo mu ku sallama"
"A'a, 'yar uwa sallama kuma. Ba dai aikin za ki bari ba"
"Eh yayana, zan ajiye aiki da ku"
"Gaskiya ban yarda ba. Ai hutu kawai za ki yi na sati zuwa kwana goma ki dawo bakin aikin ki"
"Ya Anas Ummi na ba ta so, ta ce na ajiye aikin"
"No Farida, Najeeb needs you. Ki ba wa Ummi haƙuri ta barki ki dawo dan Allah"
" to bari mu ga ni dai. Na gode Yaya"
Sai da za ta fita daga motar ta ce " Ya Anas ya jikin Sir Najeeb?"
" da sauƙi ƙanwata" ya faɗi yana murmushi...
Ita ɗin ma da ta shiga gida sai ta ji kamar ba za ta iya haƙura da aikin ba. Musamman idan ta tuna bikinta da Rayyan zai iya kaiwa wata shida ma su zuwa...
Washe gari su ka wuce Jos ita da Ummi bayan ta yi welcome back ɗin layinta.
.....................
Yana zaune a kujerar sa yana duba wasu files amma hankalin sa na kan wayar sa, jira ya ke ya ga ko an turo ma sa saƙo. Sai yanzu yai da na sanin ƙin bin Anas da yai ranan. Ko ba komai da ya ganta ya tabbatar lafiyar ta ƙalau.
Duk da ya san ba ta da numbar da ya tura saƙon. Ya ja dogon tsaki ganin har awa ɗaya kenan da tura saƙon na shi amma ba amsa, saboda ka da ta gano shi ma ya sa ya ke rubuta saƙonnin da Hausa. Da ya gama duba files da takardun da ke gaban sa ya tashi ya fita a office ɗin. Ganin kujerarta wayam ba kowa ya sa shi jin wani abu a zuciyar sa, ba dai da gaske barin aiki za ta yi ba. Kai tsaye office ɗin Anas ya wuce wanda ba nisa da na shi office ɗin.
Waya ya samu Anas na yi lokacin da ya shigo, ya samu waje ya zauna yana kallon sa.
"Miss Salihu ta bar aiki ne?" Ya faɗa da harshen ko in kula lokacin da Anas ya gama wayar.
"Ka fara kewar ta ne?" Anas ya amsa ma sa
"Oh please, ka amsa min tambayata ba na son shirme"
Dariya Anas yai sannan ya ce " well, ta ce za ta dawo amma sai Monday"
"Monday is too far"
"Mutumina da alama ka ƙagu ka ganta ko?"
Tashi Najeeb yai ya ce " idan ba ta dawo Monday ɗin ba, ka nemo min wata sakatariyar"
Anas ya ɗan yi dariya ya ce " kamar da gaske"......
...........
Ghana-must-go manya guda biyu ne a gabanta tana faman jera kayan gwanjo da ta saro da za ta kai Kano.
Adiyya wata jikar Nanna ta miƙo ma ta waya wai ana ta kiranta tun ɗazu.
Amsa wayar ta yi ta ranƙwashi kan yarinyar wadda ba za ta wuce shekara takwas zuwa tara ba. "Na hana ki ɗaukan wayata ba kya ji ko. Yanzu jiba yadda kuka cinye min chaji"
"Allah Anty ba ni kaɗai bane har da Mubashshir, shi ne ya ke game, ni kallon hotuna kawai na ke yi" yarinyar ta faɗa tana shafa wajen da Farida ta ranƙwasa.
Duba wayar ta yi ta ga missed call ɗin Maijiddah ne da na sister Munibat sai saƙo guda ɗaya wanda wani number ya turo. Numbar na yawan damunta da saƙo tun lokacin da ta yi welcome back ɗin layinta. Ta buɗe saƙon ta karanta kamar haka.
* Fatan ki na lafiya Aysherh? Ina so ki yadda da ƙaddarar da ta same ki, ki ɗauke shi a matsayin jarrabawar Ubangiji. Zai fi ki koma al'amuran rayuwar ki kamar da, ba tareda wani tsoro ba. N J*
Tsaki ta yi ta ce " shi wannan N J ɗin sai shegen naci, ka kira ba za ka kira ba, sai gatan tura saƙo kamar kamfanin Airtel."
Ta tura masa reply kamar haka *" Malam NJ ko Mr NJ, koma wa ka ke dai, ina ma ka gargaɗi da ka dena turomin saƙo, saboda ni matar aure ce. Idan ka cigaba kuwa duk inda ka ke, mijina zai nemoka kuma ba za ku wanye lafiya ba"*
Sai da ta tura saƙon ta ke ƙara alhinin wannan NJ ɗin wanda take tunanin ƙila cikin abokan Yakubu ne da su ke aiki tare a Najeeb constructions. Idan ba haka ba ta ya NJ zai san an kidnapping ɗin ta har ma ya san ta ji ciwo a ƙafa. Ƙafarta ya fara tambaya ranan da ya fara turo saƙonsa wanda kuma ta san idan ba Yakubu da Anas ba ba wanda ya san ta ji ciwo a wajen aikin su. Ta kawar da tunanin ta hanyar kiran Maijiddah dan ta ji mi ye labari...
Yana zaune ya ji ƙarar shigowar saƙo. Ya ɗauki waya ya duba, sai da ya karanta sannan yai murmushi dan ya san yanzu kam ta samu lafiya tunda har ta iya ma sa reply.
.........................
Yau sammako yai a office dan ko mai shara ba ta yi aikinta ba lokacin da ya shigo. Fakewa yai da cewa wasu ayyuka zai ƙarasa a office ɗin lokacin da Najdah ta tambayi dalilin fitarsa da wurwuri haka. Duk da kuwa dama shi ɗin mai fitar wuri ne amma na yau daban ne...
Har ƙarfe takwas da rabi ba ita ba alamarta. Haka dai ya ke aikin na shi ba tareda samun kwanciyar hankali ba...
Tun takwas saura ta zo, ta fara biyawa tana tallen gwanjon da ta saro a office-office da ke hawa na farko da na biyu. Sannan ga uwa uba labarin kidnapping ɗin su da ta ke bayarwa ga duk wanda ya ma ta jaje. Ba ta ankara ba tana office ɗin sister Munibat ta ga ƙarfe tara har da kwata.
"Kai ashe haka lokacin ya tafi barin je na kama aiki kafin Sir Najeeb yai ƙuli-ƙulin Kubra da ni"...
"Najeeb na samo ma ka wani secretary, he's a good guy idan ka amince zai fara aiki gobe"
Ya kalli Khalidah kallon ki na da hankali kuwa.
"Ban sa ki wannan aikin ba. Idan ina buƙatar secretary na san inda zan nema"
"Najeeb, sati ɗaya kenan wancar shashashar ba ta zuwa. Na san abinda ya faru ne ya sa ta ƙi dawowa, ni wallahi da da su...."
"Out"
"Najeeb.."
" i said get out"
Khalidah ta kai maƙura wajen ɓacin rai amma ba yadda ta iya dole ta kwantar da kai idan tana son samun Najeeb.
"Shi kenan zan fita amma ka yi tunani"
Tsaki ya ja sannan ya cigaba da aikin da ya ke akan system ɗin sa.
Shigowar Farida kenan Khalidah ta fito daga office ɗin Najeeb.
"Ina kwana Anty" Farida ta faɗa dan abinda ta ke kiran Khalidar da shi kenan idan tana son tunzurata. Khalidah irin matan nan ne da Allah yai wa baiwar jiki da tsayi.
" da kin rufawa kan ki asiri kin bar aikin nan da zai fi mi ki, dan ni Khalidah sai na sa Najeeb ya kore ki daga aiki"
"haba Anty! daga zuwa na. Ba ga ruwa balle ya hanya?" Farida ta faɗi tana farfari da ido.
Khalidah tai tsaki ta tafi...
"Sir Najeeb Ina kwana" ta faɗi lokacin da ta shigo office ɗin sa. Bai ce komai ba bai kuma ɗago ba.
"Miss Salihu you are late"
" na san ba ka son latti Sir, a min afuwa na yau ne kawai"
Sai a lokacin ya ɗago idon sa ya kalleta.
Shigar riga kalar maroon ta yi sai wando kalar ash da jacket shima kalar ash, ta yi ɗaurin turban da ɗankwali kalar maroon.
"Sir Najeeb ka gama kallon da kyau. Duk haɗuwar da na yin nan gwanjo ne ajikina, grade one ma kuwa. Kuma akwai irin su-irin su da na saro ko da za ka ɗaukawa ƙanwar ka ko..."
"Miss Salihu, go back to your office" ya faɗi yana sauke idon sa
"Haba Sir, ba sannu, ba ya jiki, ba..."
Wani file ya miƙa ma ta ya ce " ina son aikin nan cikin minti goma"
Ƙarɓan file ɗin ta yi a hannunsa tana kumbure-kumbure har ta fice daga office ɗin...
0 comments:
Post a Comment