"Miss Salihu...Miss Salihu" ta yi firgigit ta farka. Kallon sa ta farayi tana murza ido.
"Biyo ni"
Kafin ta wartsake ta tattara office ɗin tuni ya fita.
A hawa na farko ta sameshi yana yiwa wasu bayani. Anas ne ya ce ma ta yana ƙasa, dan da ba ta san inda yai ba.
Tana tsaye tana ƙoƙarin saita kan ta saboda har lokacin ba ta gama wartsakewa ba ta ga yai hanyar parking lot na kamfanin. Da sauri ta bi bayan shi tana jiran ƙarin bayani amma bai ce komai ba. Sai da su ka iso wajen motar sa ta ce "Sir fita za mu yi ne?"
"Shiga mota" abinda ya iya cewa kenan. Sai da ta zauna da kyau sannan ta kalleshi ta ce "Sir da ka gayamin fita za mu yi ai da na ɗan gyara fiskata ko. Yanzu ko ɗan hodan nan ban ƙara tisawa fiskata ba, fiskata ta yi wani bauu"
" Miss Salihu ina so ki sa a ran ki cewa wannan kamfani ba fashion industry ba ne inda ake gudanar da fashion shows. This is a constructions comp...."
"Daɗina da kai Sir Najeeb akwai wasge mutum. Kuma dan ina aiki a kamfani irin wannan sai ba zan yi ado ba. Yanzu idan a yamutse na ke fitowa kai kan ka ba za ka ji daɗin aiki da ni ba, balle ma su zuwa wajenka kullum"
"Miss Salihu..." ya faɗa da ɗan ƙarfi
"Sir Najeeb ina neman alfarma dan Allah"
Ɗan juyowa yai ya kalleta na ɗan daƙiƙai sannan ya maida hankalin sa ga tuƙin da ya ke yi.
"Sir dan Allah ka dena kirana da Miss Salihun nan. Shi fa Salihun nan yana chan kwance cikin kabari amma ka dinga kirana da sunan sa. Ga Aisha ga Farida duk bai maka ba, sai ka kirani da Salihu" ta ɗan yi ƙasa-ƙasa da murya ta ce "Salihun ma fa a hoto kawai na ganshi ban ganshi a zahiri ba, amma abi a dameni da Miss Salihu Miss Salihu"
Wannan karan muryarsa a kausashe ya ce " our relationship is strickly formal Miss Salihu. So ba abinda zai sa na kira ki da first name na ki"
"Abin ai son kai ne. Ita sister Munibat ai Miss Munibat ka ke kiranta ba Miss AbdulHamid ba. Ga wancan ƙatuwar nan Khalidah, itama sunan ta ka ke kira. Sai ni ne za a raina a dinga wani yaɓa mani Miss Salihu kamar wata marar suna. Gaskiya Sir ka dinga kirana da suna na nima"
"Or what?" Ya faɗi yana kallon ta
"Sir ni dai ka gyara dan Allah"
Bai sake cewa komai ba har sai da su ka iso inda za su je. Ya ce ta fito kuma ta kimtsa kan ta baya son yawan surutu. Wani ɗakin taro ya shiga ya barta a reception wai ta jira shi.
Kusan awa ɗaya yai a wajen sannan ya fito. Tunda su ka bar wajen su ke tafiya tun tana shiru-shiru har dai ta kasa jurewa ta ce "Sir Najeeb wai garin za mu bari ne kam?" Bai kulata ba sai ma ƙara volume ɗin kiɗan da ke tashi a motar da yai.
Haka ta haƙura ta yi shiru har su ka isa wajen. Tana fitowa a mota ta fara miƙa tana cewa " kai! yau na zaunu gaskiya. Irin wannan nisan waje haka"
Wani site ne da kamfanin su ke ginawa ya zo dubawa. Bayan zaunuwa to Farida ta taku domin kaf wajen sai da su ka zaga duk girman shi. Su kan tsaya da wasu ma'akata yai mu su tambayoyi da 'yan bayanai. Anan ta ke ɗan rubuta wa su abubuwa kamar yadda ya buƙata.
Ƙarfe uku sai ga kiran Anas ya shigo wayar sa. Lokacin su na hanyar dawowa. Yana ajiye wayar ya kalli Farida da ta yi lanƙwas a motar ya fara faɗa.
"Miss Salihu are you nuts?"
(Miss Salihu kin yi hauka ne?"
"Kin fixing meeting da Mr Abraham ƙarfe uku ba tareda kin gayamin ba a wani dalilin?"
"Sir, ba ka ce min za ka fita ba ai. Kuma mantawa na yi"
"To hell with mantuwar ki. Miss Salihu, akwai dubban mutane da su ke neman aikin nan, idan ba za ki yi aiki da kyau ba zan kore ki"
Shi kan sa sai abin ya zamo ma sa banbaraƙwai wai 'zan kore ki' ba ma 'na kore ki ba' kamar yadda ya saba faɗi.
"Sir Najeeb dan Allah ka dena ɗaga min hankali, dududu yaushe na dawo aiki bayan wannan iftila'in da ya sa me mu. Irin wannan rashin godiyar ne ya sa wallahi aikin nan ke fita min a ka. Ga shi mutum duk ya fiffige saboda aiki amma ba ka gani. Ni mutum ce kuma ba abun aibi ba ne ace na yi mantuwa tunda yana kan kowa"
Yana son maida ma ta martani amma ya rasa me zai ce. Yawan maganarta shi ne abu na farko da ya ja hankalinsa ranan da ya fara ganinta a restaurant, haka nan har yau bakin nan na nan. A kowani lokaci tana da abin faɗi choichoichoi. Tunowa da yai da kama su da aka yi da irin surutun da ya sha, ya sa ya san wannan Aisha Faridan a ko ina sai ta yi magana ba ta iya yin shiru......
............................
Tana zaune tana typing memo Anas ya shigo office ɗin ta.
Sir Najeeb ya jima da fita kuma a yadda ya ce ya tashi kenan saboda zai daɗe. So ta ke ta ƙarasa abinda ta ke yi ta tafi itama duk da kuwa ƙarfe biyu ne saura. Ciwon cikin period ke damunta tun safe shiyasa ta ke nan laƙwas ba kuzari sosai duk da kuwa ta sha magani ya lafa ma ta kaɗan.
" 'yar uwa yau ba zoɓo ne? Kin san i'm addicted to your zoɓo"
" Ya Anas ban yi ba yau. Ni zoɓon ma zan dena gaba ɗaya tunda Sir Najeeb ya nuna indai na cigaba da sana'a a office to cikin albashina"
"Ya Najeeb zai ma na haka kuma?"
"Hmm kaman ba ka san shi ba, watan da ya wuce da ya zare 40% ai har yau shiru ka ke ji. Wai jiya Halima tana duba gwanjo anan da ya shigo ya gani haka ya dinga faɗa har da cewa wai ya ƙara ganin na buɗe hajata a office zai cire 10% a cikin albashina. Kuma fa ya Anas lokacin break ne ba wai a lokacin aiki ba"
Anas yai murmushi ya ce " kin fara gajiya da shi ne Farida? Ko za ki bar aikin?"
"Yaya kenan. Ni fa idan ka ga na ajiye aikin nan to aure na yi, na gano take-takensa ai, dama so ya ke na yi wani abu ya koreni. Mutum sai shegen taurin rai"
"Well, ni na ga alamun tun fara aikin ki da shi ya chanja, he's becoming more tolerant now. Allah! Farida da Najeeb ɗin da ne da tuni kin bar aiki a nan"
"Hmm shi ya sani, wai ace mutum yai ta haɗe rai shi kaɗe ya ƙi shiga jama'a. Ai jama'a Rahama ne"
"Kowa da irin rayuwarsa 'yar uwa"
Har zai fita ya ce " ki ji har na manta. Akwai baƙin da za su zo gobe wajen Najeeb, ki scheduling lokacin meeting da su sannan ki sanarwa Najeeb on time kar ayi irin ta ranan"
"Ai ranan na sha kwarwa. Allah, Ya Anas na ɗauka mari na zai yi yadda ya dinga banbamin nan"
"Sai ki kiyaye"...
Yana fita ta cigaba da aiki, tana so ta ƙare ta tafi gida da wuri dan kar ta yi staining dan ba ta zo da pad ba, ta ajiye a bakin gado za ta sa a jaka ta manta shi a wajen.
Minti ishirin ta haɗa komai sannan ta turawa Najeeb lokacin meeting ɗin sa ta email. Tana kan tattare kayanta Halima ta shigo.
Halima Baballe tana aiki a hawa na ɗaya ne a HR department. Halima irin matan nan ne ma su gutsuri tsomi, 'yan haɗa waje. Bazawara ce aurenta biyu tana fitowa. Tun farkon zuwan Farida ta ke ƙoƙarin manne ma ta sai dai Faridan ba ta bata dama ba. Yawanci su ka haɗu a masallaci haka za ka ga tana liƙewa Farida tana kawo gulma da zunɗen mutane duk dan ta samu fada a wajen Farida tunda Farida sakatariyar Sir Najeeb ce, kuma kusan kowa a kamfanin yana son samun kusanci da Sir Najeeb.
"Anty nah Anty nah, ba dai kin tashi ba" ta faɗi tana washe baki
"Zan tafi gida, Sir Najeeb ba zai dawo ba kuma na gama aiki na"
"Sai na ga kin min wani lakwas, lafiya kuwa?"
"Halima yau ba na jin magana. Mi ya kawo ki?"
" Anty na kenan, baƙon wata ya zo kenan"
Farida ta yi tsaki ta saƙale jakarta a kafaɗa ta ce " mi ya kawo ki?"
"Anty na, za a yi bikin 'yar yata nan da sati biyu kuma wallahi adashen da na ke jefawa akwai mutum uku a gabana kafin na amsa shine na zo ko za ki ara min kuɗi?"
Kallon sama da ƙasa Farida ta ma ta sannan ta ce " kar ki kawo min rainin hankali nan wajen. Yaushe mu ka haɗa hanya da ke da har zan ba ki aron kuɗi na?"
Halima ta yi dariya tareda ɗan dafa kafaɗar Farida ta ce "ƙawata kenan..."
"Cire hannun ki a jikina tukunna" Farida ta katse ta
" duk yadda na ɗauke ki da zuciya ɗaya amma ke har yau ba ki ɗauke ni haka ba. Ita Sister Munibat ɗin da ki ke maƙalewa an gaya mi ki son ki ta ke? Kwanaki fa har cewa ta yi ke 'yar ƙwaya ce"
"Dalla gafara daga nan. Ba na son munafurci, halin ki na haɗa guri ya sa ba na son mu'amala da ke, idan da ba ki sani ba ki sani"
Halima ta ɗan haɗa rai ta ce " na rantse da Allah Munibat ta ce wai ke 'yar ƙwaya ce"
Farida ba ta ce komai ba ta ce biyo ni.
Tiryan-Tiryan su ka wuce office ɗin Sister Munibat inda ta ke ta faman aikin zane.
"A'a Sister Aisha ke ce tafe, ban ganki a masallaci ba ko lafiya?"
Farida ta kalli Sister Munibat sannan ta kalli Halima ta ce " maimaita abin da ki ka faɗa a office ɗina"
Halima ta ji ras dan ba ta ɗauka abinda Farida za ta ce ba kenan. Ta ɗauka su na zuwa za ta fara yiwa Sister Munibat masifa.
Sai dai kamar yadda ta ke pro a wannan ɓangare sai ta dake, ta kalli Sister Munibat ta ce " cewa na yi Sister Munibat ta ce ke 'yar ƙwaya ce"
"Astagfurullah" Sister Munibat ta faɗi da sauri tana yin wiki-wiki da ido tana ƙara cigaba da istigfari a zuciyarta.
Farida ta ce " to kin ji mi tace?"
Kafin sister Munibat ta yi wani magana Halima ta amsa da cewa " za ki ce ba ki faɗi haka ba, ranan a masallaci. Idan kin manta ni ban manta ba"
Ta ƙarasa maganar tana matsowa kusa da ita kamar za ta maketa.
Jikin sister Munibat ya fara ɓari musamman da ta tuno abinda ya faru.
"Kin gani ai ta ka sa magana saboda ta san gaskiya ne, munafuka, kina jikinta kina zaginta"
Farida ta kalli sister Munibat ta ce " ki faɗa min gaskiya. Kin faɗi haka ko baki faɗi haka ba?"
Sister Munibat ta buɗe baki za ta yi magana sai hawaye.
"Shikenan! Kukan munafurci. Dama yare, yare ai sai a hankali, dukkan su munafukai ne"
"Yi min shiru" Farida ta daka ma ta tsawa. Ta kalli sister Munibat ta ce " kin bani mamaki. Ina ɗaukan ki da daraja ina mugun mutuntaki. I consider you an older sister"
Ta juya ta fita saboda ba ta da ƙarfin yin masifa.
.......
Ƙarfe bakwai na yamma sai ga sister Munibat a gidan su Farida. Duk hayaniyar da ake na lissafe-lissafe a tsakar gidan, Farida ba ta ciki. Ƙarshen sati aka ce za a kawo lefen Maijiddah.
Tana chan kwance ta gama murƙususu akan gado saboda ciwon ciki. Maijiddah na gefe tana yiwa wata ƙaramar ƙanwarsu kitso.
"Anty Farida ga ƙawarki ta zo" Sadiq ya faɗa lokacin da ya faɗo ɗakin da gudu
Da ƙyar Farida ta ɗaga kai lokacin da sister Munibat ɗin ta shigo ɗakin su.
Sai da su ka gaisa da Maijiddah sannan ta zauna a gefen gado ta fiddo da ƙur'ani izub sittin ta ce " Sister Aisha na riga na yi alwala kafin na taho. Zan rantse mi ki akan abinda ya faru ranan da sister Halima ta ke faɗi"
Farida ta ɗan tashi jingine ta ce " bai kai har ga haka ba 'yar uwa. Ke dai ki gyara halin ki, zato zunubi ne ko da da gaskiya a cikinta. Sannan ki sani saka dogon hijabi ba shine ke nuna taƙawa ba"
"Na rantse da Allah sister Aisha ba abinda na faɗa ba kenan. Ranan da ba ki zo ba farko-farkon fara aikin ki, inaga lokacin bikin gidan kun nan ne. Ana taɗi shine aka kawo maganarki, cikin maida zance sai na ce *' sister Aisha kam wani lokaci idan ta yi wani abu kamar 'yar ƙwaya'*. Na rantse da Rabbil Arshi iya abin da na ce kenan"
Ta ja numfashi ta ce "dan Allah ki yafe ni sister Aisha"
"Ba komai, ya wuce. Sai ki kiyaye gaba, ki dinga taka tsantsan da mutane, dan abu ɗaya za ka ce ace ka faɗi goma. Ita kuma Halima Baballe gobe sai na ci ubanta tunda haɗi ta ke son yi tsakanin mu"
"Kin yafe min?" Ta tambaya kamar za ta yi kuka
"Wallahi na yafe mi ki, nima ki yafe ni" Farida ta faɗa tana ƙara kwanciya akan gado...
............................
Washe gari ko office ba ta shiga ba ta biya office ɗin su Halima ta je ta ma ta wankin babban bargo, a yadda ta tsara ma ko rabi ba ta ma ta ba saboda har lokacin ba ta warke be. Sai da ta gama silleta sannan ta wuce office ɗin ta. Tana zuwa ta samu Sir Najeeb ya zo sai dai ko da ta shiga bai ma ta magana ba kan latti da ta yi ba. Ta lura tun jiya da ya zo ya ke wani shiru-shiru kamar akwai abinda ke damun sa. Sai dai ta ja bakinta dan kar ya sauke matsalar sa akan ta.
Yau Jumu'ah kuma yau ne za a kawo lefen Maijiddah da yamma. Da ke ranan Jumu'ah ana tashi ƙarfe uku ne maimakon huɗu da aka saba shiyasa ta ke ganin za ayi komai da ita.
Da murnan ta ta shigo kamfanin, yanzu kam ba kasafai su ke zuwa tareda Yakubu ba.
Tun daga shigowarta ake ma ta wani kallo ana ƙus-ƙus sai dai ba abinda ya dameta tunda ba akan kowa ta ke ba. Lifter ta shiga ya kaita hawa na uku.
Abin mamaki sai ta ga Anas da Yakubu suna magana a office ɗin ta, ga Khalidah a gefe tana yamutse-yamutsen fiska.
"Sannun ku dai. Lafiya na ga wajen ya ɗau hayaƙi, Ya Anas me ke faruwa?"
Kallon tsana ya ma ta ya ce " na ɗauke ki a matsayin ƙanwata ashe kallon da ki ke min kenan?. Farida ashe za ki iya jefanmu da wannan mummunan ƙazafi. A dalilin me?
You know what? kafin ma Najeeb ya koreki ni na koreki, ba ma buƙatar mai hali irin na ki a wannan kamfani" ya shige office ɗin Sir Najeeb cikin fushi.
Mamaki, fargaba da tsoro ya cikata. Cikin rashin fahimtar kalaman Anas ta ce " Yakubu mi ya faru? Mi na yi?".....
*NB: free page zai ƙare @pg 15 Insha Allah, ga mai so zai iya biyan kuɗin karatu kafin lokacin.*
*ga mai son cigaban labarin zai biya #200 kacal ta wannan account ɗin 3099546325 Azizat Hamza, firstbank. Idan kuma credit card ne to MTN card na 200 za a turo wa wannan numbar 08137311900. Sannan za a turo shaidar biya (screenshot) na kuɗin zuwa numbar nan still 08137311900. Ko kuma ka biya #300 ka samu labarai biyu sakatariya ta da kuma tsohuwar soyayya*
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣1️⃣2️⃣
"Asirin ki ya tonu, Munafuka 'yar matsiyata. Yau dai dole ki bar aiki anan tunda an koreki" Khalidah ta faɗa tana murmushi.
"Yakubu mi ya ke faruwa ne, mi na yi da har Ya Anas ke faɗin maganganu marasa daɗin ji haka?"
Anas ya miƙa ma ta wayar sa ya ce "ki kunna ki saurara"
Ta amsa wayar ta kunna recording ɗin ta fara ji.
Muryar mace ce ke magana tana faɗin
*"kinga Oga Najeeb ɗin nan, babban ɗan luwaɗi ne. Kin san a ƙasar waje ya taso, so ya jima da zama gay, shi ya sa ma ya ƙi aure har yanzu. Ance fa ya kusa kaiwa 40yrs amma ba aure. Hmmm wani abin al'ajabi da na gano shi ne.... Amma kar ki faɗawa kowa fa, Halima. Oga Najeeb da Anas su na neman junan su, a yadda na jiyo ma, wai sun yi aure a sirrance. A office su ke haɗuwa su ci amarcin su. Ni Farida da ki ke ganin nan na taɓa kallon su sunayi da ido na. Bakiga yadda Anas ke zama boyi-boyi ba a gaban Najeeb , ai saboda shi ne matar Najeeb kuma mijin. Shi Anas fa ba wai son shi ya ke ba kawai kuɗinsa ya sa ya amince. Kin san Anas ɗan maigadin gidan su Najeeb ne"*
"Innalillahi. Yakubu ba muryata ba ne wannan. Wallahi ba murya ta ba ce"
Farida ta faɗa kaman za ta yi kuka.
"Ki ji ƙarya. Lokacin da ki ke hiran da Halima Baballe duk ta yi recording komai dan ma kar ace ƙarya ta mi ki. Kuma kin ji da kunnen ki"
Farida ba ta ce komai ba ta fita daga office ɗin da sauri.
.........
Lokacin da Anas ya shiga office ɗin Najeeb kuwa samun shi yai tsaye jikin window.
"Abokina ka yi haƙuri dan Allah, ban taɓa sanin Farida za ta iya faɗin maganganu haka ba. I'm so dissappointed in her. Kar ka damu, dana koma office ɗina zan typing takardar korarta"
"No need" Najeeb ya faɗi a hankali
"Ban gane ba? Kana nufin ba za a koreta ba kenan?"
Najeeb ya juyo ya kalleshi ya ce " ba muryarta ba ne. Its a trick"
"How?"
" ba muryarta ba ne, ba kuma yadda ta ke magana ba kenan."
Anas yai shiru saboda kansa ya ɗaure. Najeeb ya sake playing ma sa recording ɗin wanda Khalidah ta tura ma sa da sassafiyar yau tun ma kafin ya zo office.
Sai da ya gama ji Najeeb ya ce "barin ba ka satar amsa. Miss Salihu ba ta kirana da *Oga Najeeb*"
"Shit. Kuma fa haka ne" Anas ya faɗi ya na buga goshin sa da taffin hannun sa.
"Kafin Miss Salihu ta fara aiki anan, i know her voice"
"Wallahi na tafka shirme Najeeb. Barin je na bata haƙuri"
..............
Farida na isa office ɗin su Halima ta samu tana tsaye da wasu tana mu su bayani kan recording ɗin da su ka ji. Farida na zuwa ta yaficota ta wanke ta da mari, kafin ta ankara ta ƙara ma ta na biyu. Kafin ka ce me sun kaure da kokawa...
Ruwan cikin Halima Farida ta zauna tana kirɓanta. Halima na ihu. Da ƙyar mazan da ke wajen su ka janye Farida da ga kan Haliman.
"Ku sake ni na ci uban shegiya annamimiya. Ku sake ni na watsar ma ta da haƙora shegiya Munafuka"
Halima ta samu ta tashi tana rufe hancinta wanda ke fidda jini jikinta na rawa.
Kici-kici ta ke tana ƙoƙarin ƙwacewa. Ana ba ta haƙuri amma ina sai masifa ta ke.
"Ku bar ni na nuna ma ta banbancin da ke tsakanin mu"
Tana ƙwacewa ta yi kan Halima da gudu. Ta ɗaga hannu za ta kai ma ta duka aka riƙe hannun. Ta fara ƙoƙarin yakice hannunta amma ta kasa saboda riƙon da aka ma ta. Ta yi ta yi still ta ka sa dan haka ta juyo
"Ka sake ni na dak......" ta tsaya lokacin da ta ga Sir Najeeb ne riƙe da hannunta. Sake hannun yai ya ce " Miss Salihu to my office"
Ta juyo ta kalli Halima ta ce " wallahi ba ta tsaya anan ba. Sai na je har gida na ci ubanki, shegiya dama halin munafurcin da ya hanaki zaman gidan miji kenan"
Yakubu ya ɗauko ma ta gyelen ta da ke yashe a ƙasa ya miƙa ma ta. Wafcewa ta yi da ƙarfi tace " kai kuma zamu haɗu a gida"
Wucewa ta yi ta bar wajen tana cigaba da zage-zage....
Kai tsaye office ɗin Sir Najeeb ta wuce ranta cike da masifa. Ta san ba makawa takardar kora zai ba ta sai dai wannan karan za ta karɓa za ta bar Najeeb constructions amma sai ta wanke sunan ta.
Kaman ba abinda ya faru haka ta ganshi yana zaune yana duba wa su takardu.
"Sir Najeeb, na san ka ji abinda aka ce na faɗa amma ka sani ba muryata ba ce wallahi, ba ni ba ne"
Ɗagowa yai ya kalleta ya ce " Miss Salihu, let it be the last time da za ki maida Kamfanina wajen faɗa"
"Sir Najeeb, wallahi a liƙa min sharri kam ba zan zauna haka ba. Kowaye sai na ci kutumar uban sa, hakan ma sai hukuma ta shiga tsakani. Haka kawai dan an sanni da yawar surutu sai a kwaikwayi muryata a faɗi abin da ban faɗa ba"
Kafe ta da ido yai yana gani tana banbami kaman za ta ci babu.
Miƙa ma ta file yai ya ce " take this file to Anas, kuma ki sanar da Admin na HR inada zama da su anjima"
Mamaki ya kamata. Ta haɗiye miyau ta ce " ba korata za ka yi ba?"
"Ki na so na kore ki ne?"
Ta yi saurin girgiza kai ta ce " ba ka ji recording ɗin nan ba ne"
" muryan ki ne?"
" wallahi ba ni bane" ta faɗa da sauri
"Good. Then get back to work"
Ta ɗau file ɗin ta ce " wani lokaci idan ka yi abu kaman Salihin mutum, Sir Najeeb"
"Miss Salihu!"
Ai da sauri ta bar gaban shi tana dariya.
...........
Zuwa ta yi ta ajiye file ɗin a table ɗin Anas ta juya za ta tafi saboda ba ta son ko haɗa ido da shi.
"Aisha dan Allah ki tsaya"
Ai dama jira ta ke yai magana ta fara masifa " Ya Anas dama zumuncin kenan, idan na yi laifi a tureni gefe kamar wata kayan wanki balle ma banyi laifi ba. Iya zama na da ku yau wata ɗaya da sati uku amma har ka ji a zuciyarka zan iya maka ƙazafi, ai ba zama mai kyau ake ba kenan..."
"Dan Allah ƙanwata ki yi haƙuri. I was blind by anger, maganganun sun girgizani sosai to the extend na ka sa ma tsayawa na lura cewa ba muryan ki bane. Im really sorry ƙanwata"
"Ba wani, kai dai tabarmar kunya kawai ka ke son naɗewa da hauka. Ni ka ma barni na faɗi abinda ke raina dan abinda zai sa na huce kenan"
"To faɗa ina jin ki"
Yadda yai maganar sai ta ɗan ji kunyar sa.
"Shikenan Ya Anas na haƙura amma tsakani da Allah na ji haushin abinda ka yi min"
"Dan Allah ki yi haƙuri my ƙanwa"...
Farida na komawa office ɗin ta ta ji saƙo ya shigo wayarta tana buɗewa ta ga numbar NJ, ta yi tsaki sannan ta buɗe saƙon
*bai kamata ki watsar da kan ki ta hanyar yin dambe da wacce ba ta kai ki daraja ba Aysherh, kin fi ƙarfin haka. Ko kin manta ke matar aure ce ..... N J*
"Mtsww, wannan NJ ɗin ma wallahi sai na binciko shi a wannan kamfani, mutum sai shegen na ci, kai ba za ka kira ba idan kuma an kira ba zai shiga ba" ... ta ajiye wayar ta cigaba da aikin da ta ke.
..............
Turo ƙofar aka yi da ƙarfi. Najeeb ya ɗago ido da sauri don ganin wannan mai karambanin. Farida ma da ke jera wasu files a shelf ɗin Najeeb ta juyo da sauri.
"Najeeb wanni walaƙancin ne wannan? Ga wacce ta ma ka sharri amma ba ka ɗau mataki a kanta ba sai Halima. Ka manta Wannan Jakar har dukan Halima ta yi. You're supposed to sack her"
" ina ganin ba ki shiga office ɗin ki ba har yanzu. Go back to your office akwai saƙo da na sa aka ajiye mi ki"
"Najeeb i'm serious bai kamata ka kori Halima ba she didnt deserve it"
Ko kallonta bai yi ba ya ce " ki je office ɗin ki ki duba saƙona"
Ta juya a fusace ta bar office ɗin.
Farida ta fara dariya dan ta san saƙon, tunda ita ya ce ta typing suspension later ɗin Khalidan.
Ganin dariyan na ta ya ƙi ƙarewa ya sa ya daka ma ta tsawa.
"Miss Salihu!"
"Sorry Sir" ta faɗi tana ƙoƙarin gimtse dariyan...
Ta gama abinda ta ke amma ta fake dan tana son ganin reaction ɗin Khalidah idan ta dawo.
Ai kuwa sai ga Khalidan ta zo a rikice.
Ta cilla wa Najeeb takardar hannunta tana faɗin " Najeeb explain this"
" ba ki iya karatu ba ne ko me?"
"Najeeb one month suspension a kan me?"
Shiru yai bai kulata ba.
"Najeeb a wani dalilin za ka min haka"
Still Najeeb bai yi magana
"Najeeb magana fa na ke. I'm calling my Dad right now"
Tana ƙoƙarin kiran mahaifin na ta ta ji Najeeb yana magana.
"Alhaji Tukur na bawa 'yar ka Khalidah Siraj Tukur suspension na wata ɗaya, ko kana da ja akai?"
Saboda wayar a handsfree ta ke sai kawai Khalidah ta ji Babanta yana cewa "ba ni da ja My Engineer. Komai ka yi dai-dai ne"
Najeeb ya sa hannu ya katse kiran ko ɗagowa bai yi ba balle ya ga yadda Khalidah ta taƙune fiska.
"Shikechar inji wani almajirin mu. Asha hutun wata ɗaya lafiya ko, dama ance idan za ka gina ramin mugunta ka gina dai-dai kai" ta ƙarasa maganar tana dariya
Khalidah ta zo gaban Farida ta nunata da yatsa ta ce " sai na ga ƙarshen ki Farida, you'll see"
"Allah raka taki gona Anty Big"
Tsaki Khalidah ta ja sannan ta fice a office ɗin.
Tana cikin dariya Najeeb ya daka ma ta tsawa.
"Get out"
Simi-simi ta fita a office ɗin sa.
..............
An kawo lefen Maijiddah kuma ba ƙarya AbdulWahab ya kashe kuɗi wajen haɗa kayan nan. A wajen ƙarɓan kaya ma Farida ta ka sa ta tsare dan ganin komai ya tafi dai-dai.
Anty Hanne ƙiri-ƙiri ta nuna kishinta a fili saboda kayan da akaiwa Maijiddah ko rabinsa ba aiwa 'ya'yanta da aka aurar ba.
Baaba Sabuwa kam farin ciki fal ranta.
Ranan sunday da dare AbdulWahab ya zo yiwa Maijiddah sallama da ke ya zo weekend.
Farida ce ta tsarawa Maijiddan kwalliya ta kuma zaɓa ma ta kayan da za ta sa.
Falon Baffa Musa aka saukeshi. Wannan zuwan sa gidan kenan na biyu tun haɗuwar su.
Tareda Farida su ka zo bayan sun gaisa da shi sannan ta fita ta basu waje.
"Ina yini" ta faɗa a hankali dan ita har yanzu ta kasa sake jiki da shi.
"Lafiya gimbiya ta"...
Hiran na su yawanci shi ya ke maganar dan Maijiddah kam kunya ta hanata sakewa.
Ya ɗan taɓa abinda aka kawo ma sa sannan ya tashi akan zai tafi.
"Allah ya tsare hanya, ya kai ka gida lafiya. Ka gaida su Baby da Alizah"
"Amin tawan. Shikenan gimbiya ba wani ɗan abu da za ki bani"
"Abban Alizah mi ka ke so"
Ɗan matsowa yai kusa da ita ya riƙe hannunta ɗaya yana ɗan murzawa. Ya sa hannu ya saukar da gyalen da ta yane kan ta da shi sannan ya tufke ɗankwalin,
warware gashin da ta tufke yai sannan ya fara shafa gashin wanda ya zubo har tsakiyar bayanta ƙanshin man da ta shafa wanda ke fitar da ƙanshin mint leaf kaman kuma lemon grass. Ya kai hancinsa yana shaƙar ƙanshin.
Hannunta da ke trembling cikin na sa da kuma yadda bugun ƙirjinta ya ƙaro saboda closeness na su ya sa ya saita kan sa yai gyaran murya bayan ya miƙe tsaye sannan ya ce " Allah ya kaimu kwana ashirin da tara gimbiyata"....
....................
Yakubu ta sa ya ciro ma ta kuɗi bayan ta ga cikakken alert ɗin ta wannan karan Sir Najeeb bai cire komai ba.
Karfe goma saura kwata ta shiga falon Baffa dan bai jima da dawowa ba, sai da ta ba shi lokaci kafin nan ya ci abinci.
Ɗan gefe da shi ta zauna suna gaisawa.
"Baffana na kai na. Allah ya ja zamaninka ya ƙara ma ka lafiya amin"
"Amin 'yar Baffa"
Hannu biyu ta sa ta miƙa ma sa kuɗi. "Baffa a sa mana albarka"
" wannan bai yi yawa ba Farida"
"Baffa na so ya fi haka ma sai dai ka san mu mata sai a hankali, kuɗin na wa na sayo gwanjo da su kuma ban gama haɗa kan kuɗin ba"
"Allah ya miki albarka Farida" ta amsa da amin.
"Dubu hamsin yai yawa Farida, ba dai duka albashin na ki ki ka kawo ba?" Baffa ya faɗa lokacin da ya gama irga kuɗin.
"A'a Baffa"
Shiru ne ya biyo baya na minti biyu kafin ta ce " Baffa dama na ce tunda wannan shekaran ka yi bikin su Salima ga na Jiddah nan da wata ɗaya mi zai hana nawan a barshi wata shekaran kaga kafin nan ka tara wani abu"
" A'a Farida, idan na yi haka na ci amanar mahaifin ki. Duk cikin 'ya'ya na ba wadda ta wuce shekara ashirin na aurar da ita, Maijiddah ce ma har ta kai ishirin ɗin. Idan ba ƙaddara da ta faɗa miki ba ai da tun shekaru uku da su ka wuce anyi bikin ki"
"Baffa Allah ba matsala ka bari irin watan uku na wata shekara sai ayi kafin nan komai ya dawo normal"
"A'a Farida ko da duka gonakaina zan sayar dan na samu kuɗin yi miki aure zan sayar. Ai idan na bari wata shekara sai duniya ta zageni. Idan ba su iyayen yaron sun ce bai gama shiryawa ba ai da tareda Maijiddan zan haɗaki"
"Baffa dai" ta faɗa kaman za ta yi kuka.
"Tashi ki je ki kwanta. Allah ya kaimu watan December"
"Baffa nikam..."
"Tashi na ce" ya faɗa da ɗan ƙarfi.
Ta tashi tana guna-guni ta bar falon.
Sai da ta fita Baffa ya ƙara godewa Allah domin halin Salihu na kyauta kam Farida ta ɗauko, dan lokacin yana raye bashida rowa ko kaɗan, zai iya bayar da abu shi ya rasa kuma hakan bai dame shi ba...
................
Lagos
Ranan Monday da safe ya isa Lagos, kai tsaye office ya wuce kasancewa dama shi ɗaya ya je ya bar su Alizah a gidan maƙocin sa kuma abokin aikin sa Mr AbdulRazaƙ.
Bai ɗauka Aneesa za ta zo ba tunda ya gaya ma ta zai je Kano kuma zai bar yaran a wajen maƙota.
Ƙarfe takwas da rabi na dare ya isa gidan Mr AbdulRazaƙ dan ɗauko yaranshi. Sai dai da ya je ake ce ma sa Aneesa ta zo ta ɗauke su.
A take a wajen ya kira Aneesa amma ba ta ɗauka ba. Hankalinsa bai tashi ba sai da ya je gida mai' aikin su ta ce Aneesa ta wuce da yaran Abuja. Yai ta kiran numbar Aneesan amma ba a ɗauka. Ƙarshe dole ya kira numbar ƙaninta Nazir ya ce ya kaiwa Aneesa.
Minti biyar sai ga kiran Aneesa a wayarsa.
"Wannan wanni irin iskanci ne Aneesa za ki ɗauke min yara ba tareda kin sanar da ni ba"
"Iskanci kuma AbdulWahab, Ni da 'ya'ya na. For your information, kai da su Baby sai ka janye maganar auren ka. Ko kuma su zauna tare da ni anan amaryarka ta haifa ma ka wasu"
"Anny kin san yaran nan suna Makaranta fa"
"And so, zan sa su a wani anan"
"Look Aneesa, ki maido min da yarana gobe-goben nan ko kuma..."
Ƙiiit ta kashe kiran.
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣1️⃣3️⃣
Kwana biyu Aneesa ba ta turo ma sa yaran ba dan haka dole ya kira Alhaji, mijin Maman Aneesan kenan, ya ma sa bayanin komai shi baya ma gari dan haka bai san su Alizah na gidan sa ba. Ya jima yana yiwa Aneesa faɗa akan ta ajiye aiki ta je ta zauna da yaranta amma ta ƙi. Kasancewa Maman ta ba ta bashi goyon baya ba shi ya sa yai shiru ya zuba mu su ido. Ya auri Hajiya Salma ne lokacin Aneesa na da shekara goma shabiyu ƙaninta kuma na shekara tara. Bai taɓa banbanta su da 'ya'yan sa na cikin sa ba, makaranta mai tsada su ka yi da ta gama sakandare ya turata karatu ƙasar waje.
Aneesa ta haɗu da AbdulWahab ne a cikin jirgi, daga Lagos za ta wuce Abuja. Sun kusan shekara biyu su na soyayya kafin su ka yi aure saboda dagewa da Aneesan ta yi akan za ta yi masters kafin ta yi aure. Bayan sun yi aure ta fara aiki da wani Kamfani a Lagos. Shekaru biyu da su ka wuce Kamfanin su ka buɗe wani branch a Abuja kuma su ka nemi Aneesa ta koma wajen. Ƙarin matsayi da albashi su suka ruɗi Aneesa ta tsallake mijinta da 'ya'yanta ta wuce Abuja. Abdulwahab ya yi faɗan ya yi fishin amma duk a banza. Haka ya kira Maman Aneesan ya mata bayani akan ba da yawunsa Aneesa ta koma Abuja ba. Buɗan bakin Maman sai ta ce "AbdulWahab idan ta ajiye aikin za ka iya ba ta dubu ɗari shida da hamsin a wata ne (650,000)?" Wannan maganar shi ya sa AbdulWahab ya sauke makaman yaƙin sa ya haƙura ba dan ya so ba, sai dan inda ya ke ganin za a mata faɗan ma goyon bayanta ake. Bai faɗawa iyayen sa ba sai da ƙannensa su ka je ma sa hutu bagtatan su ka tarar Aneesa ba ta nan da farko ce mu su yai ta je gida ne kawai daga baya su ka gano komai, nan Hajiya Yelwa ta ce ba ta san zance ba ta ya za'ayi yana Lagos matar sa na Abuja wai sai ƙarshen wata za ta zo...
Alhaji yai waya ya ce maza Nazir ya maida yaran Lagos. Kasancewa Aneesa ta fita wajen aiki sannan Mama ma ta fita ya sa ya ɗau yaran ba tareda wanni cikin su ya hanashi ba. Ya na samun tiketin jirgi sai Lagos. Baby da Alizah sai murna dan dama sun ƙagu su koma school sannan su ka Dad ɗin su.
...................
Shirye-shiryen biki ake ba kama hannun yaro, duk da dai abubuwan sun zo a tsukekken lokaci amma hakan bai hana Baffa ko Baaba Sabuwa yin ƙoƙari wajen yiwa 'yar su gata ba. Da ke AbdulWahab na da gida a Kano anan za a ma ta jeren kayan ta.
Farida kam abun ya haɗu ya ma ta yawa kwana biyu su na aiki sosai a kamfani da ke akwai wani sabon contract da Kamfanin ya samu ga kuma shirye-shiryen biki. Har ɗan rama ta yi saboda zirga-zirga. A cewarta Maijiddah tana da gidadanci ba kaman ƙannen ta da idon su ya buɗe ba, dan haka ta ke sa'ido akan komai saboda ayi komai na zamani...
Gulma kam a Najeeb constructions sai ma abinda ya ƙaru musamman da aka kori Halima sannan aka ba wa Khalidah suspensio. Dayawa su na tafiya da cewa Najeeb da Farida su na soyayya ne musamman kasancewa har yanzu bai koreta ba duk da kuwa irin karya dokoki da ta ke. Sai dai duk gulman a bayan fage a keyi dan ba mai iya tunkaran Najeeb ko Farida. Irin dukan da Faridan ta yiwa Halima ma ya sa su ke tunanin ƙila Farida na da taɓin hankali...
Ɗan baccin da ba ta samu sosai cikin kwanakin nan saboda matsowar bikin Maijiddah shi ta ke yanzu a office. Sallaya ta shimfiɗa a ƙasa ta kwanta tana narkan bacci hankali kwance.
Ya kira telephone ba a ɗaga ba, ya kira wayarta still ba a ɗauka ba. Computer ɗin sa ya jawo ya duba ko ta fita ne sai ya hangota chan ƙasa tana bacci. Ya jima yana kallonta kafin ya tashi ya ɗau key da wayarsa ya fita.
"Miss Salihu" ya faɗa da ɗan karfi lokacin ya tsugunna kusa da ita. Sai da ya kirata a na uku sannan ta tashi a firgice. Ganin shi tsugunne ya zuba ma ta ido ya sa ta ɗan goge fiskarta ta ce " sannu Sir Najeeb"
"Bacci a bakin aiki Miss Salihu"
"Yanzu sai ka ce acikin albashina. To ka yi haƙuri gajiya na yi"
Yadda ta yi maganar ya bashi dariya sai dai haɗa rai yai ya miƙe ya ce ta tashi za su fita.
Bin sa ta yi zuwa office ya nuna ma ta takardun da za ta ɗauka. Bacci bai gama saketa ba amma haka ta tattaro takardun ta biyoshi. Tsabar mugunta sai ya ƙi ya bi lifter ya bi stairs.
Suna saukowa ta fito da biro ta ɗan ƙara sauri ta caka ma sa biro a bayan wuyan sa. Hannu ya sa ya shafa wajen ba tareda ya juyo ba. Ƙaramar tsaki ta ja ta sake kai hannu za ta sake caka ma sa sai kuwa ƙiris ya juyo.
"Wayyo Allah na!....Wayyo!" Ta faɗi cikin ihu, ta zubar da files ɗin hannunta ta koma baya da gudu.
Irin yadda ya ga ta tsorata ta fita da gudu sai abin ya sa shi dariya. Sometimes ya kan yi tunanin yarinyar nan na da taɓin hankali...
Kai tsaye office ɗin Anas ta je. Tana magana tana haki ta ce " Ya Anas.... ka taimakeni... yau na tsokano tsuliyar dodo"
"Mi ya faru? Mi ki ka yi?"
Ba ta bashi amsa ba sai ma ta cigaba " wallahi ba zan sake ba. Ni ban ma san ya akayi na ma sa haka ba, dan Allah ka je ka bashi haƙuri"
"Me ki ka yiwa Najeeb"
Ta ɗan yi ajiyar zuciya ta ce "biro na chaka ma sa a wuyan sa"
"Biro" Anas ya maimaita sannan ya kwashe da dariya.
"Ya Anas ba dariya za ka yi ba fa, haƙuri za ka je ka bashi"
"Yanzu ke Farida a wanni dalilin za ki ma sa haka?"
"Kawai haushi na ji ya tashe ni a bacci kuma ya ce wai mu sauko ta stairs"
Cikin zuciyarsa ya ce "lallai Farida na jinjina mi ki"
A fili kuwa cewa yai " yanzu dai kin amince kin yi laifi?"
"Na yi. Wallahi na yi"
"Shikenan, mu je na same shi"
"A'a kai ka fara zuwa tukunna, ni zan jira ka anan"
"Ki zo mu je ba abinda zai mi ki"
Jiki a sanyaye ta bi bayan Anas su ka wuce office ɗin Najeeb.
A zaune su ka sameshi yana waya. Daga bakin ƙofa Farida ta tsaya dan idan ma wani abin zai ma ta za ta samu ta gudu da wuri. Anas ya ƙarasa wajen sa ya zauna yana ɗan dariya ƙasa-ƙasa.
Yana ajiye wayan Anas ya ce "Yallaɓai mun zo biko, ƙanwar mu ta yi laifi kuma ta gane kuskurenta. Ayi haƙuri"
Shiru yai na ɗan daƙiƙai sannan ya ce " ta gaya ma abinda ta yi?"
"Ta gaya min, kuma na ma ta faɗa sosai"
"Good, akwai psychiatrist da na kira yanzu, zai zo ya gwada min ita dan ban yarda da lafiyar ƙwaƙwalwar ta ba"
Daga inda ta ke tsaye ta ce " haba Sir Najeeb, psychiatrist kuma. Sai kace mai taɓin hankali"
Kallon Anas yai ya ce " idan aka tabbatar min da lafiyarta ƙalau, then she can work with me. Idan tanada matsala kuma sai ta je ayi treating ɗin ta, dan ba zan iya aiki da mahaukaciya ba"
"Sir ka rama abin da na ma ka idan haka ne" ta faɗi da ɗan ƙarfi
Shiru yai yana kallonta sai chan kuma ya ɗau biro ya miƙe tsaye. Tana ganin ya nufota da biro a hannu ta tsume, wai a dole ba ta damuba irin ta surrender ɗin nan. Sai dai saura taku kaɗan ya isota ta buɗe ƙofa ta fita da sauri.
Najeeb ya ce " you see, she's crazy"
Anas yana dariya ya ce " she's just funny. Dan Allah kar ka ma ta komai"...
Fitan Aisha Farida kam ai sai gida, dan ba ta yadda ta tsaya ba. Sai da ta je ta tuna ai ko wayarta ba ta tsaya ɗauka ba jakarta kawai ta ɗauka. Ta yi tsaki sannan ta yi amfani da wayar Jiddah ta kira Yakubu ta ce ya je ya ɗauko ma ta wayarta a office.
"Yanzu ke tafiya gida ki ka yi ba tareda an tashi ba, Sir Najeeb ya sani?"
"Ya sani mana, kai dai je ka ɗauko min wayata kawai"...
Najeeb ya fito daga office ɗin sa zai fita ya ji wayar Farida na ringing, ganin bai ga jakarta ba yai tunanin ta tafi ne. Zuwa yai ya ɗau wayar amma kafin ya ɗauka kiran ya yanke, take kuma aka sake kira sai ya ga sunan mai kiran an saving da *My Ray*. Tsaki ya ja sannan ya saka wayar a Aljihu ya fita.
Yakubu da ya zo bai ga waya ba ya kira Farida ya gaya ma ta. Ita kuwa ta rantse indai aka sace ma ta waya a Najeeb constructions to za ayi ƙaramin yaƙi dan kuwa ba za ta yadda ba sai an fito ma ta da waya...
..................
"Yanzu kinga wannan jakar, duk kayan ciki na ki ne. Na fi awa ɗaya ina zaƙulo waɗannan kayan a wajen ma su gwanjo. Wallahi ko manya-manyan boutique ki ka je ba za ki samu kaya ma su kyaun wannan ba, ai gwanjo rufin asiri ne. Sai ki samu kayan da har ki gama yayinsa ba za ki taɓa ganin irin sa ajikin wani ba"
Maijiddah ta buɗe jakar ta fara fiddo kayan da ke ciki. Duk wanda ta ɗaga sai ta yi saurin ajiyewa saboda yanayin kayan sun bata kunya.
"Jiddah ya na ga kina wani yanƙwane fiska kaman kin ga kashi?"
"Anty Farida wannan kayan ai...."
"Ai me? Na ce ai me?. Dan Uban ki ina siya mi ki mutunci kina cewa ke tsiya ki ke so. Wannan kayan da ki ke gani da su ake cin gari. Balle ke da ki ke da kishiya, kishiyar ma wayayyiya 'yar boko"
"To Anty kuma sai insa wannan kayan in fito?"
Wani kallon banza Farida ta ma ta sannan ta ce " idan kin ga dama ki sa, idan kin ga dama kuma ki ƙona su idan kin je chan. Ni dai na san watarana sai kin kirani kince Anty Farida zan iya samun irin kayan nan wallahi ko nawa zan biya ki nemo min su. Lokacin ni kuma sai na karɓi kuɗi mai tsoka a wajen ki kafin na nemo mi ki"
"Ki yi haƙuri Anty"
"Ba batun haƙuri ba ne Jiddah, so na ke ki waye ki shigo gari kema. Idan kin je kin mallake zuciyan maigidan gaba ɗaya. And Wallahi zan faɗa mi ki gaskiya ba da hijabi ko manyan kaya ake sace zuciyan miji ba"
"Anty Farida wani mai ƙatuwar mota yana kiran ki a waje. Maijiddah ke kuma wai inji Rashidan Bala wai za ta samu kitso?"
"Zo nan Sadiƙ" Farida ta faɗa tana kallon molelen kan yaron da ya sha aski.
Yana zuwa ta kama shi ta ma sa dundu uku a baya.
"Ban hana ku kiran Maijiddah da sunan ta ba? Eh. Mi na ce ku dinga ce ma ta?"
Yaron cikin kuka ya ce "Anty Maijiddah"
"Good boy. Yanzu ka je ka cewa Rashida, Anty Maijiddah ta dena kitso"
Yaron ya fita yana kuka yana ƙoƙarin sosa bayan sa....
Ba ta gane motar wayeba amma ta san koma waye to babba ne. Ba ta tunanin kuma Alhaji Hussaini ne, wanda ta haɗu da shi a wajen aiki ya zo wajen Sir Najeeb ya nace ya nemi numbarta, sai da ta sissilleshi sannan ya haƙura ya dena kiran ta.
Tana ƙarasawa jikin motar ta zagaya wajen driver ta ƙwanƙwasa glass ɗin saboda tinted ce ba ta ga wanda ke ciki ba. Ɗan sauke glass ɗin aka yi sannan aka miƙo ma ta waya, tana ganin hannun ta ce "Sir Najeeb!" sai kuma ta yi saurin rufe baki tunowa da ta yi da abinda ta yi a office yau.
Ƙarasa sauke window ɗin yai sannan ya ce " Miss Salihu karɓi wayan ki"
Ta yi saurin karɓan wayan sannan ta ce "na gode Sir" bai ce komai ba ya ja motar sa ya tafi...
"Kaman motar Sir Najeeb na gani ɗazu a ƙofar gida"
"Shine. Waya ta ya kawomin"
Da mamaki Yakubu ya ce " Sir Najeeb ɗin?
"Iyi"
"Sir Najeeb ya kawo mi ki waya har gida"
"To miye aciki, ni ba sakatariyar sa ba ce"
Shiru Yakubu yai yana tunanin ko dai gulman da ake yi a office gaskiya ne. To idan ba haka ba Sir Najeeb ɗin da ya sani a da kam bai damu da damuwar kowa ba, kan sa kawai ya sani. To idan kuma akwai abu a tsakanin su fa? Baba ya ce a ƙarshen watan December za ayi bikin Farida.
Farida ce ta katse shi da cewa "yawwa Yakubu ka san numbar nan?" Ta nuna ma sa numbar NJ. Ɗaukan numbar yai ya sa a wayarsa sai dai bai da irin numbar ma a wayarsa...
...................
Fitowar sa kenan daga wanka ya ganta zaune abakin gadon sa.
"What are you doing here?"
"Son, Kakan ka ya rasu da safiyar yau" ta faɗi cikin muryan kuka
"Allah ya ma sa rahama"
"Zan wuce Bahrain gobe. Za ka je?"
"i'm busy" ya faɗa a taƙaice
"Saboda ni ko saboda Sabreen ne ba za ka je ba"
"Enough Justice Nabilah. Ki fita min a ɗaki"
"Najeeb please" Mom ta faɗa kamar za ta yi kuka.
"Ke ko Sabreen, ba ku da wani matsayi da zai sa na yi abu ko kar na yi abu"
Hawaye ne ya gangarowa Mom ta yi saurin sharewa ta ce " sai yaushe za ka yafe mi ni"
"When you are ready to tell the truth"
"Najeeb!" Ta faɗa da ƙarfi.
"Oh, Justice ki na tsoron gaskiyan ne?"
Shiru Mom ta yi tana ƙoƙarin maida hawaye.
Sai da ya ga ta fice ɗakin sannan ya sauke numfashi, zama yai a bakin gadon lokaci guda jikin sa ya fara maƙyarƙyata, abinda ya gani shekaru ashirin da ɗaya da su ka wuce ya fara dawo ma sa. Duk yadda yai ya manta da komai ya ka sa. He was only thirteen amma yana iya tuna komai harta fiskar wanɗanda su ka ɗau gawan a ranan...
...............
Washe gari da wuri Farida ta je office ta ajiyewa Najeeb takarda a table ɗin sa. Bai fi minti shabiyar da isowarta ba sai ga shi ya zo. Tana gaishe shi ma amma ko kallon ta bai yi ba. Sai da ta bashi minti biyar sannan ta bi bayan shi. Takardar ne a hannunsa lokacin da ta shigo.
"Sir na san na yi laifi amma ka yi haƙuri dan Allah"
Ya na so ya ma ta faɗa, ya na so ya nuna ma ta ko shi waye, amma ba zai iya ba saboda ransa da ke a ɓace saboda kuma...
Cillar da takardar ba da haƙurin da ta rubuto yai sannan ya ce " get back to work"
Ta yi mamaki da bai yi masifa ba ita kam hutarerenta ai. Har za ta fita sai kuma ta lura da yanayin sa kaman ba shi da lafiya ko kuma akwai abinda ke daminsa dan tsakanin jiya da yau ya chanja ma ta gaba ɗaya.
"Sir Najeeb ba ka da lafiya ne?"
"Get out Miss Salihu"
Simi-simi ta fita kar ma ta tunzura shi ya ce zai hukuntata.
Ya fara duba wasu takardu amma hankalinsa ya kau, tunanin kyakyawar fiskarta ya ke da murmushinta mai shiga zuciya. Ya missing ɗin ta sosai, *Aysherh* ya furta a hankali.
Ya na mamaki da Aysherh Farida ba ta da sanyi da haƙuri irin na Aysherh. Halin su ya sha banban duk da kuwa sunan su ɗaya....
***
Aisha Mustafah Jibo ta taso cikin soyayya da kulawar iyaye da 'yan uwanta. Kasancewarta kurmiya bai rage ma ta komai ba na jin daɗi a wajen iyayenta. Gata kam tana samu tun daga kan Alhaji da yayyanta ga uwa uba uwar da ta shayar da ita wato Hajiya Mama.
Karatu mai zurfi Alhaji Mustafah ke so Aisha ta samu saboda ya zamo ma ta gata ko ba sa raye, wannan ya sa ya turata ƙasar waje karatu wajen yayanta Adam. Komai cikin sauƙi Adam ya nema ma ta tundaga dreba zuwa ma su kula da ita a gida saboda shi da Nabilah ba zama su ke ba. Sabo mai ƙarfi ya shiga tsakanin Aisha da yaran Adam musamman Najeeb wanda ke da shekara tara a lokacin. Kamar wata babbar yayarsu su ka ɗauketa hakanan itama ta kan zama yarinya acikinsu duk da ita ɗin ma ba wai ta girme su da yawa bane dan shekararta goma shabakwai.
Yaran da sun dawo daga makaranta su na maƙale da ita, za ka gansu da biro da takarda suna hira da Aisha ko kuma suna wasa. A hankali har su ka iya maganan kurame ya zamo idan za su yi magana ba sa buƙatar su rubuta sai dai su yi yaren kurame.
Shekaru biyu kenan da komawar Aisha wajen Adam. Duk hutun ƙarshen shekara ta ke zuwa gida amma su Alhaji da Hajiya Mama su na kawo ma ta ziyara lokaci zuwa lokaci. A wannan ƙarshen shekaran da ta je ta tarar Alhaji ba lafiya. Nan ta tubure akan ba za ta koma America ba sai dai ta zauna kusa da Baban ta.
Adam daga Belgium ya taho dubiyan Alhaji saboda a lokacin an maida shi chan. Zuwan sa kuwa ya tarar jikin Alhaji yai tsanani. Shi da su Sulaiman su ka fara yunƙurin yadda za a yi su turashi ganin likita a ƙasar waje sai dai shi Alhajin ya ce ba inda zai je. Ana gobe Adam zai koma Alhaji ya nemi alfarma a wajen sa duk da alfarmar ta zo ma sa bazata amma Alhaji ya fi ƙarfin haka a wajensa dan haka ba tareda ya ja ba ya amince. A yammacin ranan aka ɗaura auren Adam Usman Jibo da 'yar uwar sa Aisha Mustafah Jibo. Washegari ya koma saboda jikin Alhajin ya fara sauƙi dan an sallamoshi daga asibiti.
Kwana uku da tafiyar Adam, Alhaji ya rasu mutuwar da ta girgiza 'ya'ya da 'yan uwansa musamman Aisha.
Sai da aka yi da gaske kafin Aisha ta yarda ta koma karatu duk da kuwa ta san da auren Adam a kanta dan Alhaji ya gaya ma ta kafin ya rasu.
Larabawa da shegen baƙin kishi, tunda Adam yai wa Nabilah bayanin aurensa da Aisha sai ta tuɓure ma sa ta ce ita ba ta san zan ce ba. Sosai abin ya jawo rikici tsakanin su.
A da ba ta shiga harkan Aishan dan ba ta da lokacin ta amma tunda ta zamo matar Adam sai abin ya chanja, kullum cikin tsangwamarta ta ke. Ta kori dreba da mai kula da ita da Adam ya ɗauka ma ta, ta hana yaranta kulata amma Najeeb bai daina ba sai ma ƙara jin son Aishar da ya yi.
Lokaci guda Aisha ta chanja kullum sai ta yi kuka a ɓoye saboda indai Najeeb ya ganta cikin ɓacin rai to sai ya yi ta tambayar ta dalili haka shima ranan ba za a gane ma sa ba.
Allah-Allah Aisha ta dinga yi ta gama makaranta ta bar mu su gidan ta koma Nigeria.
Shi Adam a nashi ɓangaren duk lokacin da ya zo yana ƙoƙarin ganin komai ya tafi dai-dai sai dai ita Aisha ba ta nuna ma sa tana cikin matsala haka nan Nabilah ma tana nuna komai na tafiya dai-dai.
Ganin ba abinda ya ke shiga tsakanin su ya sa Nabilah ta ɗan saki ranta kaɗan, sai dai shi a nashi ɓangaren ganin Aisha na karatu ya sa ya bari har sai ta gama tukunna ya tare da ita.
Wani hutu, Nabilah ta ɗau Najeeb da Najma ta wuce da su Bahrain wajen iyayen ta. Sai aka bar Aisha a gida.
Aisha tun tana tsoro har ta dena, kwana uku da tafiyar su Adam ya zo ya ɗauketa ya wuce da ita Belgium.
Ya kira Nabilah ne sai Najeeb ya ɗauka ya ke shaida ma sa ai sun bar Aisha ita kaɗai a gida kuma itama ta gama jarrabawarta.
A Brussels babban birnin ƙasar Belgium su ka sauka. Ba su tsaya ko'ina ba sai gidan shi. Haƙuri ya dinga ba ta na barinta da aka yi ita kaɗai.
Da dare ya zo dubata a ɗakin da ya sauketa sai ya samu tana kuka. Hankalinsa a tashe ya ce " Aisha mi ya same ki?"
Ya ɗauko biro da takarda ya ma ta rubutu. Ya miƙa ma ta biron akan ta rubuta ma sa amsa. Ta amshi biron ta rubuta " ina so na je wajen Mama"
" ba kya son zama da ni ne? Kin tsane ni ko? Saboda ba na zama ina kula da ke" ta yi saurin girgiza kai bayan ta karanta.
Jawota jikinsa yai ya rungumeta sosai ya na ɗan bubbuga bayan ta a hankali har bacci ya saceta...
Wannan sati ukun da ta yi a Belgium cikin gata da kulawa ta yi su. Adam yana tare da ita koyaushe, harta office mafiyawancin lokuta da ita ya ke zuwa. Har 'yar ƙiba ta yi saboda kwanciyar hankali.
Da hutun ta ya ƙare ya maida ita lokacin su Nabilah sun dawo. Ita da ta dawo ba ta ga Aisha ba, ta ɗauka Nigeria ta wuce sai da ta ga Adam ya dawo da ita hankalinta ya tashi. Ta san yadda ta gansu akwai abinda ya shiga tsakanin su nan da nan ta nuna sai dai Adam ya rabu da ita ba za ta iya zama da kishiya ba ko kuma ya rabu da Aisha.
Rikici sosai su ka yi har ya ma fi na farkon lokacin da ya ce ma ta ya auri Aisha.
Ƙarshe ta ce za ta shigar da shi ƙara a raba auren tunda ba zai saketa ba. Ta chanja gida ta ɗau yaranta amma Najeeb ya gudo ya koma wajen Aisha.
Abu sai ƙara rikicewa ya ke, wata rana da ta zo ɗaukan Najeeb sai ta lura da ciki ajikin Aisha, wannan ya sa hankalinta ya kuma tashi. Ƙarshe ta shigar da Adam ƙara, ganin ya ba da haƙurin ta ƙi haƙura ya sa ya ma ta saki ɗaya dan mutum mai matsayi irin na sa ace yana hayaniya da matarsa a kotu ba dacewa bane...
Ma su aiki biyu Adam ya ɗaukawa Aisha dan su dinga kula da ita lokacin cikinta ya girma.
Lokacin da cikin ta ya shiga wata na takwas Hajiya Mama ta ce za ta zo ta zauna da ita, ta shirya zuwa sai aka ma ta rasuwa Babban yayan su ya rasu sai ta ɗaga tafiyar zuwa wa ta sati....
***
"Sir Najeeb, Sir Najeeb"
Muryan Farida ya dawo da shi daga dogon tunanin da ya ke.
"Sir ka na da meeting ƙarfe tara"
"Ok" kawai ya faɗi ya miƙe tsaye.
Yanayinsa kaɗai ya nuna ma ta akwai abinda ke damun Najeeb, kuma koma minene to yana da girma.
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣1️⃣4️⃣
Tana zaune a office Faruƙ ya kirata wai gashi a kamfanin su. Kwatancen office ɗin ta ta ma sa sannan ta ajiye wayar tana cigaba da aiki. Minti biyar kacal sai ga Yakubu da Faruƙ sun shigo.
"Farida haka yaron nan ya zama luƙeƙe. Kin san da farko ban ganeshi ba"
"Kai ma ka faɗa ai, wannan sai ya goyeni yai yawo da ni duk faɗin garin nan bai gaji ba"
"Haba Anty, ɗan ni ɗin nan" Faruƙ ya faɗi yana dariya
Yakubu ya fita ya basu wuri, dama wajen Anas zai je ya haɗu da Faruƙ ɗin.
'Yan uwan biyu su ka zauna su na taɗi, su na yi su na dariya.
Wayar Farida ya ƙarɓa ya na duba hotuna. Ko ba a gaya ma sa ba ganin hotunan selfie da Farida ta yi da wani saurayi ya tabbatar ma sa shine Rayyan.
"Sis, wannan shi ne sirikin na mu ?"
"Kai ba na son gulma"
"Wallahi ba ku da ce ba, wannan ai kin fi ƙarfinsa. Hmm ina tausaya ma sa wallahi, aka yi auren nan mijin ta ce zai koma dan ba zai iya da masifar ki ba"
"Buuuuyagi" wafce wayan ta yi tana faɗin " ka ji min rainin hankali, wato dai ni ka ke zagi ko" ta maki kafaɗar sa ta ce " Faruƙ yaushe ka raina ni haka?"
Yarfe hannu ta farayi shi kuma ya fara dariya. " jikin ka kamar wani katako, wai yaushe ka girma ne haka? Faruƙ"
"Serious Anty Farida ba ki dace da shi ba, kin ga lokacin Lukman..."
"Faruƙ!" Ta faɗa da ƙarfi.
Ya haɗa hannu ya ce "afuwan Anty na ta kai na"
Haɗe fiska ta yi ta tsume.
Faruƙ ya sa hannu ya fara tattaɓa kumatun ta yana tsokanarta kaman yadda yake yi lokacin suna yara.
"Anty kumatu, Anty Kumatuttu"
Ba ta san lokacin da dariya ya kuɓuce ma ta ba.
"Yaron nan ka mugun raina ni wallahi"
Yai dariya ya ce " na tuna da, lokacin idan na ce mi ki Anty Kumatu har maƙota sai anji faɗar mu"
Ta fara dariya sosai harda kama ciki.
Faruƙ ya cigaba " lokacin tunda na gano bakya son sunan sai na samu abun tsokala. Kin tuna lokacin da ki ka kwaɗa min tukunya har goshi na ya fashe?"
"Ai ranan Ummi ta zane ni kamar ba gobe" ta faɗa cikin dariya. Suna cikin dariyan kakkausan muryan Najeeb ya doki kunnen ta.
"Miss Salihu"
"Sir" ta faɗi tana miƙewa tsaye.
"To my office"
Ya jima tsaye yana kallon su tun daga lokacin da Faruƙ ya ke shafa mata kumatu. Zuciyar sa ta yi baƙi haka nan idon sa ya kaɗa yai ja, a take ƙwaƙwalwarsa ta tariyo ma sa sunan da ya gani ranan *My Ray*
Ta ya za ta kawo saurayinta har office tana iskancin da ta ga dama. Enough is enough dole ya taka ma ta birki. Abinda zuciyarsa ta tsayar kenan dai-dai lokacin da Faridan ta shigo.
"Ga ni Sir" ta faɗi a hankali
Da ƙarfi ya fara masifa "Miss Salihu yaushe ki ka maida office wajen soyayya da iskanci?. Listen young Lady, idan ba ki san yadda za ki kama kan ki ba go and get married. Ki dena mayar min da office wajen karuwanci. And i..."
"Sir Najeeb ba fa ni na kar zomon ba balle a bani ratayar sa. Daga ƙani na ya kawo min ziyara sai ka maidashi wani zancen banza wai karuwanci. Ba Karuwanci ba a'a Kwartonci"
Kalmar *ƙani na* da ya ji shi ya sanya duk wani masifar da ke cinsa ta washe, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kamar kiftawar ido, muryar sa da yanayin sa su ka chanja. Cikin sanyin murya ya ce "Miss Salihu, da ƙanin ki da saurayin ki, nan ba wajen ziyara ba ne"
Haushin sa da ta ji kaman ta makeshi takeji sai dai yanzu ba ta son samun matsala da shi dan ankusa biyan albashi, ƙaramin aikinsa ne ya cire mata wani kaso a ciki.
"Zan iya tafiya?"
Yai ma ta nuni da hannu. Sai da ta fita ya sauke numfashi. Cikin zuciyarsa yana cewa to ma miye ruwansa idan ma saurayinta ne?.
Tana zama ta yi tsaki " shi komai masifa, yai wa mutum kyakykyawar fahimta ba zai yi ba"
"Sis Ogan kin nan ya burgeni fa. Saurayi da shi amma ya mallaki babban kamfani kamar wannan, gaskiya na jinjina mi shi"
"Ko za ka je ya baka aiki ne. Nan za ka san wannan saurayin zuciyar dutse gareshi"
"Oh really"
"Hmm ai ni ma ba dan bana barin hau ta hauni ba da tuni an jima da fatattaka ni"
"Kai Masha Allah, wa su kam Allah ya basu duniya, ga shi handsome, ga kuɗi, ga class..."
"Zan make bakin ka Faruƙu"
Dariya yai ya ce " Jiya na yi mafarkin kin auri wani millionaire. Wai gamu a wani haɗaɗɗen mansion, wai nan ne gidan ki"
"To Sayyadi Sheikh Umar Faruƙ, ma su mafarkin waliyyai"
"Da gaske fa Anty Kumatu"
Ta ɗau wani littafi za ta buga ma sa ya kauce yana dariya...
...................
Wannan karan ba ta yi garajen barin wajen aiki ba dan ta san yana ɗaya daga cikin babban dalilin da ya sa Najeeb ya rage albashinta a watan farko da ta fara aiki. Ranan Laraba ta tambayeshi leave ɗin kwana biyu ya ce ya bata kwana ɗaya. As usual sai da ta yi ƙorafi amma bai kulata ba.
Wannan karan bayan Walima ba abinda za'ayi. Baffa yai iya ƙoƙarinsa wajen yiwa Maijiddah kaya, duk da bikinta ya zo ma sa cikin matsi.
Ranan Alhamis aka je yi ma ta jere, su Farida ne 'yan gaba-gaba wajen ganin komai ya tafi dai-dai. Gidan yana da kyau sosai, tana da ɗakuna biyu na ta sannan an ware ma ta kitchen daban sai dai store ne za su haɗa da Aneesa...
Gidan ya cika saboda gobe ne walima jibi Asabat kuma a ɗaura aure. Farida tun da su ka dawo daga wajen jere ba ta samu zama ba, shiga ta yi cikin ma su haɗa kayan waliman gobe ana aiki da ita.
Cikin ma su aikin cupcake ta ke ana yi ana hira. Chan wata 'yar uwar su wanda ita kan ta Faridan ba ta san takamaimai ta ina su ka haɗu ba ta ce " Ikon Allah, kaman ba yau aka yi hidiman bikin Farida ba, na tuna cake ɗin da aka yi ranan mai daɗi, su Talatun Haruna ne su ka yi cake ɗin nan ko?"
Farida ta fusata da wannan zance. Ta miƙe tsaye " Inna Tabawa ki ke ko wane. Wallahi ki riƙe girman ki, na ga take-taken ki tun awajen jere. Ba zan miki da daɗi ba"
"Daga magana. Ni na ce kiyi sosayya da ɗan shege" Taas Farida ta wanke ta da mari ai kuwa matan kowa ya tashi wasu su ka ja Farida gefe wasu kuma su ka tsaya da Inna Tabawa da ta ke ta zage-zage...
Kai tsaye falon Baffa Ummi ta shige da ita bayan an kawota wajen Ummin.
"Mi ye haka Aishah?, zafin kan ki har ya kai ki mari mace kamar Tabawa"
"Ummi so ta ke ta ci mutuncina cikin jama'a. Tun a wajen jere ta ke ta min habaici ina shareta. So ta ke wanda ma ba su san abinda ya faru ba su sani"
" shikenan?" Ummi ta faɗi ranta a ɓace
Farida ta kalli mahaifiyarta da mamaki ta ce "Ummi maganan Lukman fa"
" da ta yi maganan akwai abinda ya ragu ko ya ƙaru a jikin ki ne?"
Farida ta girgiza kai.
"To ni banga abin ɗaga hankali ba anan. Ƙaddarar ki ce ta zo da haka. Kuma Alhamdulillah Allah ya chanja mi ki da mafi alkhairi sai ki yi ta gode ma sa, ki share 'yan gulma da gulmar su"
"Amma Ummi..."
"Kul. Ba na son jin wani magana, ki je ki nemi abinci ki ci ki samu ki huta"...
Ɗakin su Yakubu ta shiga ta ke cin abincin, ba wai daɗin abincin ta ke ji ba sai dai saboda Ummi ce ta takura sai ta ci. Gaba ɗaya zuciyarta na ma ta ɗaci. Duk yadda ta so ta basar da abin ta ka sa, kawai sai hawaye. Ta ya za ta manta da wannan rana a rayuwarta, ranan da ya kamata ace ya zamo ranan farin ciki amma kuma komai ya zo ya dagule, ya zamo ranan shine rana mafi baƙin ciki a tarihin rayuwarta. Sai da ta yi kuka mai isarta kafin ta share hawaye ta tattara kwanukan ta fita...
...................
Anyi Walima lafiya, sai dai duk yadda Farida ta ci burin ganin anyi komai da ita abinda ya faru daren jiya ya kashe ma ta jiki. Da farko ma shiri ta yi kawai za ta wuce office amma amarya Jiddah ta hanata.
"Dan Allah Anty Farida kar ki tafi, ki taimakeni ki tsaya ayi komai da ke. Ke ce support ɗina Anty"
"Na san kin ji abinda ya faru jiya, ba na son tsayawa anan wata ta gayamin maganan banza mu kwashi 'yan kallo. I dont want to ruin your day"
"Anty dan Allah ki mance da komai, Allah ina buƙatar ki kusa da ni fiye da kowane lokaci"
Da ƙyar Farida ta haƙura ta tsaya. An ci kuma an sha sannan an kira Malami ya yi wa'azi.
Washe gari Asabat ƙarfe shaɗaya aka ɗaura auren *Hauwa Maijiddah Musa Wase da AbdulWahab Bello Hassan Kachako*
Ɗaurin auren da ya samu halarcin manya-manya mutane, ta ɓangaren Alhaji Bello Kachako da shi kan sa AbdulWahab ɗin.
Da dare aka kai amarya gidan ta wanda kwana biyu kawai za ta yi su wuce Lagos...
Gidan Amarya Maijiddah kam bayan kowa ya tafi aka bar amarya da halayenta.
Tun safiyar yau ta ke gudawa saboda tsoro da fargaba.
Akwai mafiya yawancin mutane da idan su na cikin damuwa ko tashin hankali ko tsananin farin ciki ko baƙin ciki za ka ga yanzu-yanzu cikin su zai hautsine su fara ziryan banɗaki.
Maijiddah was nervous tun wayewar garin yau, abu ne da ta jima tana roƙo sai gashi ya tabbata, wai ga ta amarya. Ta sha Flagyl kam har ba adadi duk dan ta samu sauƙin wannan abun amma kaman tunda Maghriba ta do so abin ya fara ƙaruwa. Yanzu haka kafin Farida ta tafi sai da ta tabbatar ta sha magani amma yanzu da ta ke ita kaɗai sai ta ke jin cikin ta na ƙugi yana kuma murɗawa.
Tana cikin wannan yanayi wanda ta kira da ƙarshen kunya aka shigo ɗakin. Buɗe ƙofar ɗakin yai daidai da kukan da cikinta yai "ƙululululu"
A hankali ya tako wajen da ta ke ya ajiye ledar hannun sa akan drawer sannan ya tsugunna gaban ta ya sa hannu ya ɗaga gyalenta sama yana mai yin Bismillah.
Jikinta rawa ya ke, sai zufa ta ke haɗawa. Na farko saboda tsoro na biyu kuma saboda yanayin da ta ke ciki.
"Alhamdulillah, finally Gimbiya Allah ya nuna ma na wannan rana"
Duk maganan da ya ke yi sama-sama ta ke jin sa. Kamar ta saki ihu ta ke ji saboda kunya da haushin kan ta. Ta ya za ayi daren farkon su ace ta ɓarke da gudawa, wannan abin kunyan har ina.
Hannunta ya kamo yana wasa da yatsunta bayan ya zauna kusa da ita.
"Bari mu yi sallah sai mu ci abinci, na san baki ci wani abin kirki ba yau"
A karo na ba adadi cikinta ya sake yin ƙugi, wannan karan kam AbdulWahab ya ji.
"Sorry princess yunwa ko?"
Idan ta cigaba da shiru za ta cutu haka nan da kunya ace ta gaya ma sa matsalarta sai dai ya za ta yi.
"Ki shiga ki yi alwala ni inada alwalata" ya katse tunanin ta
Ai da sauri ta miƙe ta shige banɗakin. Duk yadda ta so ta daure ta yi alwala amma hakan bai yiwuba dole dai sai da ta je ta zauna a toilet. Ƙarshen kunya sai ga shi ƙaran gudawan na fitowa da ƙarfi wanda tabbas ta san AbdulWahab da ke ɗakin ya ji.
Ta gama amma kunya ya sa ta kasa tashi ta yi flushing, ta jima tana zaune daga baya ta yi ta maza ta tashi ta flushing na shi sannan ta yi alwala. Sai dai ka sa fitowa ta yi daga banɗakin dan ba ta san da wanni ido za ta kalli AbdulWahab ba.
Jin shiru kuma ta ƙi fitowa ya ce " gimbiya ko na zo na fitar da ke ne?"
Ta sauke ajiyar zuciya sannan ta fito. Daga bakin ƙofa ta tsaya kanta a ƙasa ta ce a hankali " I'm sorry, cikina ne ya ruɗe Yaya"
Tasowa yai har wajen da ta ke tsaye ya kamo hannunta ya ce " There's nothing to be sorry about my dear, mun riga mun zama ɗaya ai"
Sai da ya zaunar da ita sannan ya ce "kinsha magani?" Ta ɗaga ma sa kai.
"Barin haɗo mi ki tea sai ki fara sha"
Fita yai daga ɗakin wanda cikin minti shabiyar da ya ɗauka sai da Maijiddah ta sake zagayawa banɗaki.
Lokacin da ya dawo ya sameta a ɗan kwance gefen gado. He know she's nervous shiyasa ta ke experiencing wannan abun. Ya tuna akwai wani abokinsa mai irin wannan, ko exam za su yi sai ya ɓarke da gudawa, a ranan da za su fara exam na Waec shekaru da dama da su ka wuce sai da Hussaini ya makara saboda ruɗewa da cikinsa yai.
A yadda ya ganta she's already weak, idan yai yunƙurin yi ma ta wani abu that will label him a cruel man.
Taimaka ta yai ta tashi ta sha tea ya haɗa ma ta da kaza.
"Ki kwantar da hankalin ki ba abinda zan miki, ki ci ki samu ƙarfin jikin ki"
Shi da kan shi ya fara ba ta naman a baki har ta ƙoshi. Ya ce ta shiga ta yi wanka ta ce na yi.
"Kinga yanzu jikinki ya tsatstsafo da gumi saboda tea da ki ka sha. Ki je ki watsa ruwa"
Gaba ɗaya kunya sai ya sake rufeta. Ta tashi ta shiga ta sake wanka da ta fito ba ta same shi ba ya tattara wajen. Ta yi saurin buɗe closet ta nemo kayan bacci riga da wando ta sa, sannan ta ɗaura hijab akai.
Da ya dawo a zaune a bakin gado ya sameta.
"Hauwerh cire hijabin nan akwai zafi"
Ba mu su ta cire hijabin ta sunkuyar da kai tana wasa da bakin pyjamas ɗin ta.
"Ya cikin na ki?"
"Da sauƙi"
"Ki kwantar da hankalin ki ba abinda zai faru kin ji"
Ta gyaɗa kai.
"Now breath in and breath out"
Ba ta gane ba har sai da ya nuna ma ta yadda za ta yi da kan sa sannan ta yi yadda ya ce. Sai da ta yi kusan sau goma kafin ya ce ta kwanta.
Kafin ya shimfiɗa sallaya yai sallar nafila tuni bacci ya sace amaryar sa. Da ya idar sai ya gyara ma ta kwanciya sannan ya kwanta bayanta ya musu addu'a ya kashe wutan ɗakin...
Washe gari da kunyar sa ta tashi tunowa da tai da abinda ya faru jiya. Sai dai shi kam ko ajikinsa, nuna ma ta yai wannan shine amfanin auren domin sun riga sun zama ɗaya. Duk wani matsalarta na shi ne, haka nan duk matsalarsa na ta ne.
Da dare su ka je gidan su sallama, daga nan su ka wuce gidan su Maijiddan. A wannan lokacin Farida ta tambayeta ko gudawar ta tsaya kafin ango ya shigo. Maijiddah ta ce "inaa, Anty ni kam ai na sha kunya" a taƙaice ta gaya ma ta abinda ya faru Faridan ta yi ta ma ta dariya.
Ba su jima ba su ka wuce saboda da sassafe jirgin su zai tashi.
Daren ranan ya gaya ma ta basic abubuwan da ya kamata ta sani gameda airport da jirgi. Sannan ya jaddada ma ta ba abinda zai faru yana tareda ita.
Ko breakfast ba ta iya yi ba saboda kar ta ci wani abu ya dameta. Ƙarfe tara jirginsu ya wuce Lagos. Kuma Alhamdulillah Maijiddah ba ta yi gudawa ba, sai dai ta tsorata kam lokacin da jirgin zai tashi, ba dan AbdulWahab na riƙe da hannunta yana kwantar ma ta da hankali ba ƙila da ta yi kuka. Sai da jirgi ya lula sama sannan ta ɗan samu nitsuwa kaɗan...
Asha amarci lafiya Maijiddah (banda gudawa plz😁)
.........................
Safiyar Monday Farida ta fito aiki duk da kuwa gajiya bai saketa ba, sai dai kamar yadda ta yiwa Maijiddah dariya sai gashi itama tana tsaka da aiki cikinta ya hautsina. Da farko sharewa ta yi tana mita " mutum ya yi ta ciye-ciyen mai kwana biyu ba dole ciki yai ta kuka ba"
Sai dai fa lokaci guda ta kasa yin komai ta tashi ta nufi office ɗin Najeeb da gudu dan nan ne kusa da ita sannan ta ɗauka baya office ɗin dan ya fita ɗazu ya je meeting. Abinda Farida ta manta shine ya riga ya dawo tuntuni.
Da gudu ta zo ta wuceshi yana zaune yana aiki, kafin ta ƙarasa ma ta saki tusa a hanya.
Yana shirin buɗe baki yai magana kan shigo ma sa office da ta yi da gudu ya ji ƙaran tusan da ta yi...
Hankali kwance Farida ta zauna ta zazzage kayan cikinta, dama tun ran asabat rabon da ta yi, ga shi ba ƙaramin abinci ta ci ba a bikin nan. Ta jima a ciki kafin ta wanke ta yi flushing, kasancewa banɗakin yai gum sai ta ɗau air freshner ta feffesa ta ƙara buɗe windown banɗakin da kyau saboda iska ya ratsa.
Ta fito tana ɗan daddanna ciki tana faɗin "kai abubuwan da na ci a bikin nan ai sai barka. Kashi rahama ne Allah, ka ji yadda na ji wani saƙayau lokaci guda"
Cak ta tsaya da tafiya lokacin da muryan da ba ta taɓa tunanin ji ba a wannan lokacin ya doki kunnenta
"Miss Salihu"
Kaman ta nitse cikin office ɗin haka ta ji sai dai ita Aisha Farida ce dole ta nuna dakewarta. Tukunna ma dama yana office lokacin da ta shigo? ko dai bayan ta shiga banɗakin ne ya shigo office ɗin.
"Miss Salihu whats the meaning of this?"
Da ƙarfinta ta waiwayo bayan ta sauke ƙaramar ajiyar zuciya. Ita ɗin expert ce wajen waskewa, ta ce
"Daɗin abin ma kowa yana yi, abinda na yi ba farau ba ne akai na. Ni'ima ce da ubangiji ya baiwa bayinsa dan ya nuna ma na mu ɗin ba komai ba ne. Da Sarki da shugaban ƙasa da maikuɗi da talaka, malami da jahili, mai kyau da mummuna, mace ko namiji, fari ko baƙi. Dukkan mu muna da buƙatar wannan ni'ima. Abu ne ba babba ba yaro"
Ta ɗan haɗe rai ta ce " yanzu haka Sir Najeeb kai ma wannan ni'imar sai da ka yi ta kafin ka zo office yau, ko tun jiya rabon da ka yi?"
The girl is really crazy, taya za ta yi abin kunya and pretend kaman ba komai. Masifa ya ke so ya ma ta amma maganganunta sai su ka kusa sa shi dariya. Ya daure ya ce " Miss Salihu a wani dalilin ya sa ki ka yi min amfani da banɗaki?"
"Saboda ya fi kusa da ni mana"
"This should be the last time da za ki yi haka"
"Ok Sir"
Har za ta wuce sai ta juyo ta ɗan yi gyaran murya ta ce " Sir ina da magana"
Ido ya ɗaga ma ta alamar miye.
"Sir, tsakani da Allah tusar da na yi ɗazu ka ji ta?"
Kallon-kallo su ka tsaya yi. Har ga Allah tana son sani dan bayan ƙarar da tusar ta yi ba ƙaramin wari ne ya biyo bayan tusar ba.
"Get out of my offfice"...
*Tantaran taran taran...... kar ku manta free pages na Sakatariya ta zai ƙare @pg15 kuma yanzu ma aka fara labarin. Za ka biya 200 kacal domin cigaba da samun update na labarin ko kuma ka biya 300 ka samu harda labarin Tsohuwar soyayya. 'Yan Niger Insha Allah gobe zan sanar da ku yadda za ku biya na ku...#FARNAJ is waiting for you all*
Domin sanin yadda za ku biya ku min magana ta wannan numbar 08137311900
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Last Free page*
0️⃣1️⃣5️⃣
"Mama har yanzu bai kirani ba, ina ga bai san ma na yi yaji ba fa" Aneesa ta faɗa cike da damuwa a ran ta.
"Ya ki ke so na miki? Na kira AbdulWahab na ce ka zo ka bada haƙuri matar ka ta yi yaji ko ya?"
"Mama do something please, ba zan iya sharing mijina ba"
"An riga an ɗaura auren Aneesa live with it. Ke ne za ki san yadda za ki riƙe gidan ki ta yadda yarinyar ba za ta samu kan shi ba"
Aneesa ta ɗan ɓata fuska ta ce "Mama ta ya zan yi hakan bayan bana zama a Lagos"
"Za ki ajiye aikin ki kenan?"
"Hell no. Ta ya zan bar career ɗi na when i'm at its peak. Ko kaɗan"
Mama ba ta ce komai ba, to mi za ta ce. Itama mace ce da mijinta ba ya gabanta. Ta taso da aƙidar 'yan cin kai, yau tana Dubai gobe tana China wajen saro kaya, kasuwancin ta shine a gaban ta. Auren fari ta haifi Aneesa da Nazir, da ta auri Alhaji Abdullahi ma ɗa ɗaya ta haifa ta rufe haihuwa. Kuɗi kuɗi su kawai ta sa a gaba ba ta da lokacin kula da iyalin ta balle tarbiyyan yaran ta, shi ya sa ko kishiyoyin ta ba sa gaban ta, dama kuma kowa gidan ta daban...
.....................
Farida na zaune wani saurayi ya shigo neman Najeeb.
"Wa za a ce?" Ta tambaya lokacin da ta ɗau wayar.
"Ki ce ƙanin shi"
"Sir wai ƙanin ka na neman ka"
Ajiye wayar ta yi ta ce " ya ce ka shiga"
Ba a jima da shigar wannan baƙon ba Anas ya zo shima ya shiga.
Dukkan su uku zama su ka yi ana taɗin bayan rabuwa.
"Big B tunda ka ƙi auruwa mu zamu shige gaban ka fa, dan na gaji da zama tuzuru"
"Shege yaushe ka dawo da za ka fara maganar aure. Anas see this small boy fa"
Anas dai murmushin ya ƙe yai dan ya san inda maganar za ta tsaya ba za ta ma sa daɗi ba.
Farida ta shigo ta samesu a haka, bayan Anas ba ta taɓa ganin Najeeb ya sake yana taɗi da wani ba. Sai dai kamar yadda wannan saurayin ya ce shi ƙanin sa ne ƙila su na da alaƙa tunda dai a yadda Anas ya gaya ma ta ƙanwar Najeeb ɗaya ce wato Najdah. Wata 'yar girman kan kaman yayan na ta.
Kai tsaye wajen Najeeb ta nufa a wajen kujerun da su ke zaune wanda anan ya ke saukan baƙin sa.
"Sir ga wannan ana buƙatar signature ɗin ka anan" ta faɗi lokacin da ta miƙa ma sa wasu takardu.
Ya amshi takardun ya fara dubawa.
"Kai Big B wannan hottie as a secretary ai za ta ɗauke hankalin ma su zuwa wajen ka"
Najeeb ya ɗago ido ya ma sa wani kallo wanda ya sa yai saurin chanja magana fa cewa.
"Ba wanda ta kai sweety na kyau ai. Najdah is the epitome of beauty ba ƙarya"
Gyaran murya Anas yai sannan ya ce "Musty zan wuce office, sannu da zuwa"
Musty ya miƙa ma sa hannu su ka gaisa. Idon Farida na kan Anas wanda ta ga ya chanja lokacin da Musty yai maganar Najdah. Tun farko-farkon fara aikinta ta san Anas ya na son Najdah, duk da kuwa Anas ɗin bai iya buɗan baki ya faɗawa Najdan ba har yau.
"Ya Anas dan Allah ka ɗan jirani minti biyu" ta faɗa tana murmushi.
Sauke idon da za ta yi domin ƙarɓan takardun da Najeeb ya gama signing sai ta ga idon shi chul akan ta. Ba ta san ma'anan wannan kallon ba amma ta fassara shi da cewa kallo ne da ke nuni da zan gamu da ke.
Da ta amsa takardun ta ce "Allah na gani ni ban ci bashin kowa ba, kurwata kur"
Har ta fita daga office ɗin bai daina kallon ta ba.
Musty cikin fake American accent ɗin sa ya ce " Your secretary is funny and cute"
"Ba ka daina halin na ka ba ko?"
"Sorry Babban yaya"
Tana fita ta tadda Anas na tsaye yana jiran ta. Gaba ɗaya fiskar sa ta chanja bisa yadda ta san shi da, shi ba kaman Najeeb bane kullum fiskar sa a sake ta ke gashi da son barkwanci.
"Yaya na ban gane wannan ɗan adawar ba fa, shi waye?"
Murmushin ya ƙe yai ya ce "ɗan ma su gida ne. Mustafah Sulayman Jibo kenan"
Kalmar da ya faɗa ta 'ɗan ma su gida' ya sa ta tuna da audion da aka ce ta yi kwanakin baya inda ake cewa shi ɗin ɗan Maigadin gidan su Najeeb ne, kenan da gaske ne.
"Ya Anas kar ka damu mu akai za mu dangwalawa. Idan da so ai ya share komai"
"Ki na ga Najdah za ta tsallake ɗan uwanta ta zaɓe ni ko kuma Daddy ne zai watsar da zumunci ya zaɓe ni?"
"Ya Anas da wannan ma amma tun farko kai ka yi sake. Da ka gina soyayyar ka a zuciyar ta da tuni an wuce wajen"
Girgiza kai yai ya ce " Farida ba za ki gane ba"
Wucewa yai ya bar office ɗin ran sa ba daɗi...
Najeeb na zaune da Musty ne amma hankalin sa na kan tunanin mai Farida za ta faɗawa Anas. The girl is mischievous, yanzu haka wani gulma ta ke yi.
A wajen cin abinci Farida ta samu Anas shi kaɗai, bai ordering abinci ba, ruwa ne kawai a gaban sa, yana zauna amma hankalin sa yai nisa cikin tunani.
"Ya Anas yau da garau-garau na zo, za ka ci" Farida ta ajiye kular tana ƙoƙarin buɗewa.
" 'yar uwa yau ba na jin yunwa" ya faɗi ba tareda ya kalli abincin ba.
"Allah sai ka ci, nan nan na hana Yakubu abincin nan na ce a yaya na zan kaiwa amma ka gwaleni ba ka isa ba"
Ta fara zuba abincin a plate tana faɗin "Ya Anas yajin ya ji maggi fa, ga man ma sai ƙanshin albasa ya ke"
Sai da ta gama haɗawa ta tura gefen sa ta ce " dan Allah ka ci"
Ba yadda zai yi dole ya ɗau spoon ya fara ci. Ita ma ta haɗa na ta ta fara ci. So ta ke ta ma sa maganar Najdah shi ya sa ta zo.
"And what is the meaning of this?" Muryan Najeeb ya gauraye ilahirin wajen.
"Anas miye haka?, babu respect tsakanin Oga da mere secretary. Ta ya za ka bari ta zauna a inda na ke zama na ci abinci. Are you trying to disrespect me kamar yadda ta ke disrespecting ɗi na"
"Najeeb is not..."
"Shut up" Najeeb ya katse Anas da tsawa. Wannan ya ja hankalin kowa ya koma kan su.
Ta shi Anas yai zai bar wajen. Farida ta ce "Yaya dan Allah ka tsaya ka ci abincin ka, ni barin bar ma sa wajen"
"Bar shi na gode Farida" ya faɗi sannan ya bar wajen.
"Girma ya faɗi, kuma wallahi an ji kunya"
Hannu Najeeb ya kai zai ma ta mari sai kuma ya tsaya yana huci hannun na reto a sama " I'm warning you Miss Salihu, ki kama matsayin ki ko kuma na nuna mi ki"
Haɗiye miyaun da ya tokare ma ta maƙoshi ta yi lokacin da Najeeb shi ma ya juya ya bar wajen. Ta gama sadakarwa Najeeb marin ta zai yi. Har ta hango yadda fiskarta zai koma idan da marin ya sauka a fiskarta.
Ranan dai ita ɗin ma ka sa cin abincin ta yi. Mi ya ke damun Najeeb da har zai yiwa Anas haka, hakan ma agaban jama'a wanda duk a ƙasan Anas ɗin su ke...
Kai tsaye office ɗin Anas ta wuce da ga canteen. Yana zaune yana ta kan zane a takarda wanda da ka gani ka san yana zanen ne saboda huce haushi.
"Yaya na kar ka ce na cika gulma amma anya Sir Najeeb yana da lafiya kuwa. Gaskiya a binciki ƙwaƙwalwar sa"
"Lafiyar sa ƙalau Farida, kawai dai he has a rough life ne. Mahaifiyar sa then Sabreen, su suka maida shi haka"
"Sabreen?" Farida ta faɗa da alamar tambaya.
"Macen da Najeeb ya fara so ba"
"Dama duk girman kan Sir Najeeb ya taɓa soyayya? Abun mamaki"
"Kar ki damu da abinda ki ka ga ya yi ɗazu, anjima kaɗan za ki ga ya zo ba da haƙuri"
"Duk da haka Ya Anas, abinda yai bai ma ka adalci ba wallahi"
"Kar ki damu, abinda yai bai kai zuciyar sa ba"
"Wannan sirikin na ka Allah kaɗai ya san yanayin sa. Yau ka gan shi shiru anjima ya fara faɗa gobe idan ya fara banbamin bala'i har wani spark bakin sa ya ke yi"
Ai Anas bai san sanda ya fara dariya ba "kai Farida kinada abin dariya ba kaɗan ba"
"Allah Ya Anas wani lokacin kaman majnuni ya ke, ka san lokacin da aka kidnapping ɗin mu haka mu ka kwana mu ka wuni bai min magana ba daga baya kuma bini-bini sai ya ɗaukeni"
"To waya sani ko ke ce ke sa shi haukan"
"Ni Aisha Farida! Rufa min asiri kafin yanzu na ga query letter"
Ta ɗan gyara zama ta ce " yawwa, da ma maganar Najdah zan ma ka"
Ya ɗago ya kalleta
"Mi zai hana ka faɗa ma ta kana son ta, you never know, sai ka ga an dace. Balle ni ina ganin tana son ka ma"
"Baba na gadi yai a gidan su har ya rasu, karamci na Daddy ne ya sa ya sponsoring karatuna tun daga primary har masters da na yi shi ya sa na zama abinda na zama a yau. Daddy is like my father amma kuma na san indai akan maganar Mustafah ne to zai zaɓeshi ya bar ni, domin Mustafah jinin sa ne"
" tsoro shi zai sa ka rasa masoyiyar ka wallahi. Ba ka taɓa ce ma ta kana son ta ba, ba ka gayawa Najeeb ba balle kuma Daddy, to dan Allah ta ya za su san kana yi balle har a dubi wanne ya fi dacewa da ita tsakanin kai da Mustafah"
"Ki bari kawai Farida. Gara na zauna a matsayina"
"Dan Allah kar ka bani kunya ma na"...
...........
Lokacin da aka dawo daga break ta koma office ɗin ta. Ko da aka zo neman Najeeb ta kira office ɗin sa amma bai ansa ba, ta shiga office ɗin amma baya nan. Har banɗaki sai ta leƙa amma shiru. Numbar sa ta fara kira amma ba ta shiga.
Daga ƙarshe dai ranan har aka tashi ba ta ga Najeeb ba. Haka nan ba ta san inda ya je ba dan da ta fita ƙasa ta tambayi security aka ce ma ta Najeeb ya fita da mota tuntuni.
A zuciyarta ta ce "ai dole ka gudu tunda ka yi abin kunya"...
Tunda ya bar canteen kai tsaye motar sa ya je ya ɗauka ya bar kamfanin, ya na shiga gida ɗakin sa direct ya wuce ya samu gefen gado ya zauna tare da dafa goshin sa. He cant believe wai shi ne yai wa Anas tsawa. Anas fa, Anas da duk faɗin duniyan nan ba shi da aboki kamar sa. Saboda me?
Shi kan sa bai san dalili ba, ya san ba laifin Anas a zaman da Farida ta yi a wajensa. Sai dai ya rasa dalilin da ya sa maimakon ma ya ji haushin Farida sai ya kasance ya fi jin haushin Anas akan ta. Bai san ya za'a yi ya dena jin haushi ba duk lokacin da Farida ta ke tareda Anas.
Ya jima yana tunani a ran sa kafin ya tashi ya fara cire kaya dan ya watsa ruwa.
...............
Samun Anas ta yi akan dan Allah ya kaita gidan su Najeeb ta bashi wa su takardu sannan ta bashi saƙonnin wanda su ka zo ba su sameshi ba tunda wayar sa a kashe ya ke. Yana sauketa a compound ɗin su ya juya ya tafi dan shima bai shirya fuskantar Najeeb ɗin ba, ko da kaɗan ne to ya ji haushin abinda Najeeb yai.
Ranan da su ka zo gidan da dare ba ta lura da gidan ba, saboda dare da kuma hali na gajiya da rashin lafiya. Amma yanzu kam ta ga yadda gidan ya ke da girma da kyau, sai da ta gama yabon kyaun gidan a zuciyar ta kafin ta wuce ciki. Doorbell ta danna tana jira a buɗe.
Najdah da Afrah ke cin abinci a dining saboda har yanzu Mom ba ta dawo daga Bahrain ba.
"Adama.... Adama ki zo ki buɗe ƙofa"
Adama ta fito da sauri ta nufi ƙofan.
"Sannu, wa ki ke nema?" Adama ta tambayi Farida da ke tsaye a bakin ƙofa.
"Ni sakatariyar Najeeb ne, na kawo ma sa saƙo yana nan?"
" ki shigo"
Ta matsa ma ta ta shiga.
"Adama waye?"
Kafin ta bada amsa Farida ta ce "Aisha Farida ce"
Sunan ba baƙon suna ba ne a wajen su duka biyun, dan sun san labarinta a Najeeb constructions. Ranan da su ka fara zuwa wajen Najeeb farko-farkon fara aikin Farida. Hana su shiga office ɗin sa ta yi ta sa su ka jira shi a office ɗin ta har sai da ya dawo. Ranan cikin shagwaɓa Najdah ta dinga complain wa Najeeb har da cewa "Big B, your secretary was rude to us". Daga baya Najeeb ya ce wa Farida duk lokacin da ƙanwar sa ta zo yana nan ko baya nan ka da ta hana ta shiga office ɗin sa.
"Ehen, duk haɗuwar ku na office bai isa ba sai kin biyoshi gida" Afrah ta faɗa tana huhhura hanci.
"Idan aiki na ya tsone mi ki ido, kya iya zuwa ki ƙarɓa"
"Mtsww" Afrah ta ja tsaki
"Mi ki ka zo yi?" Najdah ta faɗa ita ɗin ma fiskan ba yabo ba fallasa.
"Na kawo wa Sir Najeeb wa su files ne, sannan na zo neman bayanai gameda masoyina Anas kasancewa kin fini sanin shi"
"Masoyin ki Anas?" Najdah ta maimaita
"Wanni Anas tukunna?" Afrah ta saka baki.
"Abokin yayanki ma na, ko kin san wani Anas ɗin bayan shi?"
Najdah ba ta ce komai ba sai haurawa da ta yi sama da gudu fuuuu itama Afran ta bi bayanta tana kiran ta.
Ganin su duka biyun sun bar wajen ya sa Adama ta je wajen SHS ɗin falon ta danna 6 muryarta na rawa ta ce "Ranka shi daɗe ga Sakatariyar ka ta zo neman ka"
Shiru kusan minti ɗaya ba a ce komai ba, har Adama ta fidda rai sai ga muryar sa ya na cewa " send her to my room"
"Ina ne ɗakin?" Farida ta tambaya
"Idan kin haura sama shine ɗaki na ƙarshe a ɓangaren hagu"
Ok kawai ta ce ta haura saman. Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin ta yi lokacin da ta iso. Ta tsaya na aƙalla minti biyu kafin aka buɗe ƙofar.
Sanye ya ke da jallabiya na 'yan Morocco kalar toka.
"What do you want?" Ya faɗi fiskar sa tamau.
"Ya Allah, wai haka gidan ma su kuɗi su ke ne, daga ka zo sai a fara tambayarka mi ka zo yi. To ni ba maula na zo yi ba ziyara na kawo"
Ƙofar ya jawo zai rufe ta yi saurin sa hannu ta ce " yi haƙuri Sir Najeeb saƙo na kawo"
Ya dakata da rufe ƙofar yana kallonta. Ta fito da wani file ta miƙa ma sa sannan ta ce " Sir MD na Hafzal suites ya zo neman ka ya ce da ka ji saƙon nan ka kira shi akwai magana mai muhimmanci da za ku yi sannan dan Allah ka bawa Ya Anas haƙuri abinda ka..." baam ya rufe ƙofar sa.
" Mr Egocentric" ta faɗa kafin ta juya ta fita.
A falo ta haɗu da Daddy shi ma ya shigo gidan kenan, har ƙasa ta rusunna ta gaida shi.
"Kaman na san fiskar nan"
"Yallaɓai ai ni ce sakatariyar Sir Najeeb wanda aka sace mu kwanaki"
"Oh Aisha ko?"
"E"
"Sannu ya Baban na ki"
"Ya na lafiya"
"Ki gaida min shi ko"
"Insha Allah zai ji"
"Gida za ki je ne?"
Ta amsa da E
"To to, Adama ki fita ki ce Iliya ya kaita gida ko"
"Na gode Daddy"
Ya fito da kuɗi a Aljihu ba tareda ya irga ba ya miƙa ma ta ya ce ta sha ruwa a hanya.
"Daddy ka barshi na gode"
"Idan ki ka yi haka ba ki ɗauke ni Daddy ba kenan"
Ai tuni Farida ta karɓa tana ƙara faɗaɗa murmushinta lokacin da ta ji kaurin kuɗin zai iya kaiwa dubu goma.
Ita kam bajau ɗin ta, ta tafi gida a mota mai kyau ga AC ga dubu takwas da Daddy ya bata...
Ai ba ta gama zama ba Anas ya kira ta.
" 'yar uwa mi ki ka faɗawa Najdah ne? Ta kira ni wai muna soyayya da ke kuma na ɓoye ma ta bla bla bla..."
Sai da Farida ta yi dariya mai isar ta sannan ta ce " Yaya na kenan, idan akwai kishi to akwai so. Najdah na son ka, ka saurari plan ɗina ka ji..."
............
Su na cin breakfast a dining Najdah ta ce " Big B wai ashe Ya Anas da sakatariyar ka soyayya su ke"
Tea ɗin da Najeeb ya kai baki ya furzar da sauri.
"Anas ya gaya mi ki?"
"Jiya da sakatariyar ka ta zo ta ke gaya min. Big B, Ya Anas ya rasa wanda zai nema sai masifaffiyar yarinyar nan, that girl fa ba za ta rasa mu'amala da ƙwaya ba"
Miƙewa Najeeb yai bai ce komai ba ya bar dining ɗin.
Ranan da Anas da Farida ban san wanda ya fi shan masifar Najeeb ba. Abu kaɗan masifa, lokaci guda Najeeb ya dawo wa Farida Najeeb ɗin da ta sani farkon zuwan ta. " get out, fuct you, stupid, nonsense" waɗannan kalmomi da su na tsiro da sun tsiro a jikin Farida saboda tsabar yadda ta ji su a wajen Najeeb. Idan ta kawo takarda ya signing kuwa yana gamawa zai wurgeta da shi ba zai miƙa ma ta da hannu kamar yadda ya saba ba.
Anas ma ya ɗauka da Najeeb ya zo zai ba shi haƙuri a wuce wajen sai ya ga saɓanin haka. Yana tambayar sa abu maimakon yai magana sai ya fara ma sa tsawa...
Farida na tattara wasu takardu da Najeeb ya watsar Anas ya shigo office ɗin.
"Najeeb ka dubi wannan presentation ɗin nan na gobe. Wannan shi ne final edit da na yi"
Ko kallon laptop ɗin da Anas ya ajiye a gaban sa bai yi ba ya ce " kar ka damu kan ka, ba za ka yi presenting gobe ba"
"What"
"Ka jini da kyau"
"Najeeb are you serious? I've been planning for this pitch for a week now"
Da ƙarfi Najeeb ya daki table ɗin sa ya ce " Ni Najeeb Adam Jibo, CEO of Najeeb constructions na ce Architect Anas Ali AlMustafah ba za ka yi presentation gobe ba, ka na da ja?"
Da Anas mai saurin kuka ne da ya yi a wajen nan saboda wannan cin fuska da Najeeb ya ma sa. Sai dai ya daure ya ce " ba ni da ja, Sir Najeeb"
Wannan karo na farko da ya referring Najeeb da 'Sir' kenan, a cikin shekaru bakwai da su ka fara aiki tare.
Gwiwar Farida yai sanyi. Tausayin Anas ya mamaye zuciyar ta. Da ta na da iko da ta je ta wankawa Najeeb mari.
Wai a wani dalilin zai yiwa Anas haka, a wani dalilin?
(Ni dai da 'yan group ɗi na ma su albarka mu ka haɗa baki mu ka ce *a dalilin ki*)
*plz numbar da za a nemi yadda za'a shiga paid group ɗin sakatariya ta ita ce 08137311900, duk wani number da ba wannan ba scam ne. Kar ku manta, #200 ne kacal ko kuma ka biya #300 ka samu sakatariya ta da tsohuwar soyayya. Za ka iya biya ta wannan account ɗin 3099546325, firstbank,Azizat Hamza. Ko kuma ka turo katin waya zuwa ga wannan layin 08137311900. (Plz duk wani means of payment da ba wannan ba, babu hannun marubuciyar a ciki. Mutanen Niger za ku iya biya ta link da zan turo da yamma Insha Allah a wattpad account ɗi na 000Azee)*
............
"Yakubu dan Allah ka nemo min super glue mai kamawa sosai wanda baya saurin bushewa"
"Yanzu dan Allah mi za ki yi da super glue? Ke ba mai gyaran takalmi ko radio ba"
"Ni bana son sa'ido, ka nemo min kawai. Harda gum na ruwa ɗin nan. Yau na ke so ba gobe ba"
"Ke wallahi case ce, na ji zan nemo"
Farida ta yi murmushi
Da wurwuri ta zo office yau. Tana daƙontar zuwan Najeeb dama ta gayawa security da zaran Najeeb ya ya shigo ya kirata.
Tana zaune kuwa security ya kira ya ce ga Najeeb ya shigo. Ta yi sauri ta shiga office ɗin sa ta samu kujeran sa ta fara matsa super glue ɗin da Yakubu ya kawo ma ta.
Za ta fito kenan ta yi kiciɓis da Najeeb zai shigo dama tuni ta sa tubes ɗin a jakarta.
"Good morning Sir"
Bai amsa ma ta ba ya wuce wajen zaman sa.
"Sir Ya Anas ya kawo flash ɗin da za ka yi amfani wajen presentation ɗin na ajiye a table ɗin ka" wannan magana shi ya ɗaukewa Najeeb hankali ya zauna ba tareda ya lura da kujerar sa ba.
Tana gani ya zauna ta yi murmushi.
"Ki tabbatar duk wanda ke cikin team ya isa conference room kafin ƙarfe tara"
"Ok Sir" ta fita tana murmushi.
Flash ɗin ya ɗauka ya sa a laptop na shi yana duba presentation ɗin da Anas ya sha wahala ya tsara.
Ƙarfe tara saura minti shabiyar ya gama bitar abin ya kira Farida. Ta san dole zai kirata domin ta ɗauka ma sa laptop da wasu files dama.
Ƙoƙarin tashi yai a kujeran ya ji ya ka sa tashi. Da ya tashi sai kujeran ta biyoshi.
"What's this" ya faɗi lokacin da ya ke ƙoƙarin raba takashinsa da kujeran amma hakan bai yiwu ba.
"Sir Najeeb ya dai?"
Farida ta faɗa kamar ba ta san mi ya ke faruwa ba.
Tsaki yai ya cigaba da ƙoƙarin raba jikinsa da kujeran.
"Sir idan ka ja da ƙarfi zai yaga ma ka wando ka ga anyi ba ayi ba kenan. Tsuliyar CEO Najeeb constructions a waje" ta sa hannu ta ɗau flash ɗin da ke kan table ta ce " tunda takashin Oga ya maƙale a kujera sai na kaiwa Ya Anas kawai yai presentation ɗin tunda dama shi ya kamata yai tun farko"
Sai da ta fara tafiya ya ƙwalla ihun sunan ta da ƙarfi "MISS SALIHUUU"
Ta waigo tana fari da ido ta ce " SIR NAJEEB YA DAI"
*difdifdifdif..... anan na kawo ƙarshen free pages. Na yi ƙoƙari ai har page 15. Well, za ka samu cigaban labarin idan ka biya 200 kacal. Stay safe and Allah ya mana albarka ya rufa mana asiri duniya da lahira ta ku AZIZAT*
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
0 comments:
Post a Comment