Ce ma sa su ka yi ya kai ta mota yayinda Iliya dreba yai sauri ya shiga gidan don ya faɗawa Daddy.
Daddy na falo har lokacin yana waya da Anas.
Ya na ma sa bayani Daddy ya ce muje-muje.
Daddy na gaba Yakubu na baya ɗauke da Farida wanda har lokacin ba ta farfaɗo ba duk da kuwa sun yayyafa ma ta ruwa. Kafin su isa asibitin ta farfaɗo amma ba ta san inda ta ke ba....
Chan gida kuma Baffa ne ya ke ta faɗa kan miyasa za'a bar Farida ta fita a wannan halin. Maijiddah ne ta ce tare su ka fita da Yakubu. Sai a sannan yai shiru ya zaro wayar sa a aljihu ya fara kiran numbar Yakubun amma bai ɗauka ba.
"Shima ɗan gatan'wa, ko ina ya shiga oho"...
Ruwa aka ɗaura ma ta aka ma ta alluran bacci dan sun ce jinin ta ne ya hau. Sai da ta fara bacci tukunna Yakubu ya samu damar kiran gida ya faɗa mu su.
Daddy ya dubi Yakubu ya ce " mi ya ke faruwa ne? mi Najeeb ya ma ta?"
Da kaman ba zai faɗa ma sa ba,sai dai girman Daddy da kwarjininsa ya fi gaban ya ƙi ma sa magana. Duk abinda ake ciki ya tsirge mi shi tundaga farko har ƙarshe.
Da ya gama bashi labarin Daddy ya ɗauko waya ya kira wata number.
"Anas ka na ina ne?"
Yakubu bai ji mi ake ciki ba ya dai ji ya ce "muna room 18 a sama"
Ba'a jima ba sai ga Anas ya shigo. Ganin Farida a kwance ya sa shi mamakin mi ya faru.
"Yakubu ya jikinta?, mi ya sameta?"
Da sauƙi kawai Yakubu ya iya ce masa.
"Ina ɗan banzan nan ya ke?"
Daddy ya tambayi Anas.
Ya gane Najeeb ya ke nema dan haka yai saurin cewa yana office nima daga office ɗin na ke.
"Har da kai ake rusa rayuwar mutane ko?"
Anas ya zaro ido ya ce "A'a Daddy"
Daddy ya miƙe ya ce "Yakubu Allah ya bata lafiya, ina nan dawowa anjima"
Yana Fita daga ɗakin Anas ga bi bayanshi da sauri.
A motan Anas ɗin su ka wuce Najeeb constructions.
Ya jima yana tunanin ko wani hali ta ke ciki. Wani ɓangare na zuciyar sa na faɗa ma sa bai kyauta ba wani ɓangaren na nuna ma sa ya yi dai-dai.
"She deserve it" ya furta a fili.
Yana ƙoƙarin duba wasu takardu da aka submitting ma sa tun da safe amma ya kasa fahimtar komai. Haka kawai zuciyar sa ke ma sa ƙunci....
A hanya Daddy ke sanar da Anas abinda Najeeb yai, Anas ya kaman salati yana salallami.
"Daddy ban san Najeeb zai iya yin haka ba especially saboda zargin da na ke masa akan yana son Faridan"
"Dan uban sa dan yana son ta sai ya mata sharri"
Anas dai shiru yai yayinda Daddy ke ta surfa ma sa masifa kaman wanda shi yai laifin.
Da ke an riga an tashi wajen shiru ka ke ji. Daddy da Anas su ka haura third floor.
Ya kifa kan sa akan kujera saboda wani zazzaɓi da ya rufeshi lokaci guda, ya rasa mi ya sa shi shiga wannan yanayi. He supposed to be happy ya rama kaɗan daga cikin asaran da Miss Salihu ta sa ya yi. But instead his sad.
Buɗe ƙofar office na shi da aka yi ya sa ya ɗago kan sa da sauri.
Ganin Daddy da Anas sai ya miƙe. "Dad " kaɗai ya iya faɗa kafin saukan mari ya sa ya haɗiye koma mi ya ke shirin faɗa.
A karo na biyu Daddy ya kuma marin sa, ji ka ke taas. Anas na gefe ya sha jinin jikin sa dan faɗan uba da ɗa sai Allah.
"I'm ashamed to call you my son"
"Dad" Najeeb ya faɗa a hankali
"Ashe tarin shekarun ne kawai akan ka ba hankali. Mahaukacin banza Mahaumacin wofi. Sai ka samu me idan ka hanata auren? Tukunna ma, miye dalilin yi ma ta sharri? Miye dalili? "
"she deserve it Dad, she wanted to ruin me. Na rasa big contract saboda ita saboda haka 2 project da mu ka fara su ka soke contract da mu. She tarnished my image and the repeatition of my company"
Wani marin Daddy ya kai ma sa. " i didnt know i have a monster son. Asaran kamfaninka yana dai-dai da ruguza mutuncin mutum kenan?. Shin ka yi tunanin halin da yarinyar nan za ta shiga? What if she died of shock, sai ka haɗa party kana murna ko"
Ya nuna shi da ɗan yatsa yace " Anas, kalli banzan yaron nan fa,8yrs ago da Sabreena ta gudu ta barshi kafin auren su he almost died, he was depressed for months. Ya je theraphy section na watanni huɗu kafin daga baya ya warke ya dawo Nigeria. Do you know that this fool here yana shan antidepressant drugs har yau saboda baƙin cikin yarinyar nan. Amma shi ne ya ke da guts da zai je ya hana auren 'yar mutane"
"Najeeb" ya ka sa magana ma saboda baƙinciki da ya tokare ma sa wuya.
Daddy juyawa yai ya fita, Anas ya kalli Najeeb, kallon ka bani mamaki sannan ya bi bayan Daddy da sauri.
Gidan su Rayyan Daddy ya ce Anas ya kai shi. Da su ka je su ka sa a yi sallama da Baban Rayyan ɗin, aka ce mu su yana kasuwa. Numbar sa su ka karɓa su ka kirashi jin sunan Alhaji Adam Jibo ne ya sa mahaifin Rayyan ya ce yana nan zuwa. Haka su ka zauna zaman jiran sa, kafin ya dawo ma an fara kiran sallan maghrib su ka yi sallah a masallacin anguwar.
A ƙofar gidan aka shimfiɗa mu su tabarma lokacin da Baban Rayyan ya zo.
Daddy bai ɓata lokaci ba ya ma sa bayanin ko shi waye da kuma abinda ya ke tafe da su.
"Malam Abdullahi, wannan hoto da aka kawo muku ba tare su ka ɗauka ba, editting na shi aka yi, kasan yanzu fasahar zamani ba abinda ba ayi. Wannan yarinya ta na da tarbiya kuma kowa ya shaideta da haka. Duk abinda Najeeb ya zo ya faɗa muku to wallahi ƙarya ne, ya yi hakan ne dan ya cimma wani banzan burinsa. Ku yi haƙuri a maida maganar auren yaron ku da Aisha"
Yadda Daddy ya ke magana cikin kwantar da murya ya sa Malam Abdullahi yarda da maganar sa domin Daddy babban mutum ne a gari kai a ma ƙasar gaba ɗaya ba zai yiwu ya zo wajen sa dan kawai ya ma sa ƙarya ba.
"Alhaji na fahimceka, sai dai gaskiya al'amarin nan ya riga ya ɓaci. Ni da Alhaji Musa mun samu saɓanin harshe a yau ɗin nan saboda wannan magana. Yanzu haka maganar da na ke maka an riga an dawo mana da sadaki da kuma kayan lefe da aka kai. Harta kayan yarinyar da aka kai gidan yarona sun je sun kwashe. Al'amarin ya ɓaci sosai gaskiya"
"Malam Abdullahi a duba dan Allah. Auren nan idan aka fasashi alhakin yarinyar nan zai bi Najeeb 'ya'ya da jikokin sa"
"Gaskiya zan faɗa ma ka Alhaji ko da za a dawo da bikin nan to ba gobe ba"
Shiru Daddy yai na tsawon lokaci kafin ya ce wa Anas su tafi.
...........................
Su Baffa da su Ummi sun zo asibitin da aka kwantar da Farida. Baffa kam a lokacin ma ya ƙara tabbatarwa kan sa ko mi zai faru to gobe sai ya aurar da Farida, domin idan gobe ta wuce bai san halin da Farida za ta shiga ba, balle ya san halinta yanzu sai ta ce ta haƙura da aure gaba ɗaya ta ce karatu za ta cigaba da yi.
Bayan ya tabbatar da ankawo duk abubuwan da za su buƙata sannan ya musu sai da safe saboda ance sai gobe za a sallameta. Ya zo zai fita daga asibitin da shi da Yakubu su kuma su Daddy su ka shigo.
"Alhaji Musa dan Allah ka tsaya" Anas ya faɗa lokacin da ya ga Baffa Musa ya gan su amma sai ya kau da kai yai kamar bai gan su ba.
Baffa Musa ya juyo ya kalli Daddy yana ƙarasowa wajen su, girman sa ya sa ya fasa masifar da ya ke shirin yiwa Anas.
"Alhaji Musa dan Allah ko za mu iya magana da kai"
"Ni yanzu gida zan wuce Alhaji, ina sauri"
"Ba komai Alhaji Musa za mu bika gidan"
Baffa Musa dai bai so ba amma ba yadda ya iya. Haka su ka wuce gaba, su ma su Daddyn su ka bi bayan su.
Daddy da Baffa Musa ne a falon. Yayinda Anas da Yakubu ke ƙofar gida suna tattauna wannan abin al'ajabi mai kama da almara.
Duk girman Daddy da matsayin sa haka ya fara yiwa Baffa Musa magana cikin sanyi da harshe mai taushi.
"Alhaji Musa dan Allah ka duba wannan al'amari. Na yiwa Malam Abdullahi magana kuma ya ce za su duba, kar a fasa auren nan gobe dan Allah"
"Aure ai ba za a fasa shi ba, kamar yadda na gayyace ka da farko ba chanji. Gobe ƙarfe shaɗaya na safe za a ɗaura auren Farida da ɗa na Yakubu. Tunda sun shaƙu da juna idan anyi auren za su fahimci junan su sosai"
"Alhaji idan ka yi haka ba ka yafe ba kenan"
"Alhaji ko ka san ni ɗin nan ni na shiga na fita har na ga na amso takardar Farida saboda ɗan shege mu ka aura ma ta ba mu sani ba. Yanzu kuma ace duk walaƙancin da iyayen Rayyan su ka mana sai na ba su auren Farida. Wallahi ba zai yiwu ba, gara ayi tuwona maina kawai "
Daddy yai shiru yana tunani chan ya ce " Alhaji Musa ina neman alfarma a wajen ka"
Zumɓur Baffa Musa ya tashi lokacin da ya ji buƙatar Daddy.
"Wannan zancen banza kenan, ba zan taɓa yiwa Farida auren cin fuska ba. Allah ya kiyaye"
"Alhaji Musa ka taimakeni dan Allah, yaron nan inaga son ta ya ke shiya sa yai haka"
"Alhaji ka tashi ka tafi dan Allah, abinda ka ke buƙata ba mai yiwuwa ba ne"
Maimakon Daddy ya tashi sai ya sa gwiwowinsa a ƙasa yana roƙon Baffa Musa. Tuni Baffa ya fara ƙoƙarin ɗaga Daddy yana faɗin "haba Alhaji ka fi ƙarfin haka, dan Allah ka tashi"
"Yaron nan yadda ka ke so ka ga ka aurar da Aisha haka nima na ke so yai aure. Nan da 'yan kwanaki zai cika shekaru talatin da biyar a duniya kuma har yanzu ba shi da niyyar aure. Shi kaɗai ne ɗa na namiji Ba na fata ya ƙarasa rayuwar sa a matsayin tuzuri"
Baffa dai rasa mi zai ce zai yi dan kan sa ya kulle. Alhaji Jibo ya girmeshi a shekaru nesa ba kusa ba ya girmeshi a matsayi da komai amma shine ya ke roƙon sa har kamar zai yi kuka. Farin cikin Farida ya ke so amma idan ya amsa buƙatar Alhaji Jibo anya ba baƙin ciki zai shuka a rayuwar Farida ba....
............................
Bayan fitan su Daddy ya shiga wani tashin hankali, bai taɓa ganin Daddy cikin ɓacin rai haka ba, he only mean to punish her. So ya ke idan an fasa auren ta yi kuka ta ji baƙin ciki sai ya koma ya nuna wa mahaifin Rayyan gaskiyar lamari cewa hotunan nan aikin photoshop ne. But is he stupid or what, idan ya je will that undo what has already been done.
Ya kira Anas sau ba adadi amma ya ƙi ɗauka. Ya fito da robar maganin sa ya ɗauko guda biyu sai kuma ya maida su. Ashe Daddy ya san halin da ya ke ciki all this while, shi bai san Daddy ya san da zuwan sa wajen theraphist ba, balle har ya san he has being on drugs all this while.
Duk da hasken da ke office ɗin na shi bai hana shi ganin duhu ba.
Mi ya sa koyaushe mace ce ke sa shi cikin ƙunci, first it was his Mom then Sabreen sannan wannan Miss Salihun.
Ya dafe goshin sa da ke sara ma sa kaman zai tsage...
..........
Bai san lokacin da ya isa gida ba balle ya san lokacin da bacci ya ɗaukeshi. Buga ƙofan sa da ake da ƙarfi ya sa ya farka. Tasowa yai da ƙyar ya je ya buɗe ƙofan.
Anas ya gani yana faɗaɗa murmushin sa.
"Maigida har yanzu ba ka tashi ba, yau fa ranan ka ce"
Najeeb ya juya ba tareda ya ce komai ba ya wuce banɗaki.
Anas ƙaramin walk in closet da ke ɗakin ya shiga yana duba kayan Najeeb ɗin.
Najeeb ya shimfiɗa sallaya ya gabatar da sallar asuba lokacin agogo ƙarfe bakwai saura kwata.
Anas ya fito da wasu kaya ya shimfiɗa akan gado barin ga wanne zai fi fito da kai. Blue ko fari ko ash.
"And what are you doing exactly?"
" ina nema ma ka kayan da zai dace da kai a rana irin ta yau"
Wayar Najeeb ɗin ce ta fara ringing ya ɗauka da sauri ganin Daddy ne.
"I'm coming Dad"
Anas dai dariya ya fara ƙasa-ƙasa lokacin da Najeeb ya fita.
A ƙaramin falon Daddy da ke sama ya sameshi yana zaune yana waya.
"E ƙarfe shaɗaya ne, e masallacin wajen ne. Abin ne ya zo bagtatan ayi haƙuri" ya na gama wayar ya kalli Najeeb da ke zaune opposite da shi ya yi zuru-zuru da ido.
"Muhammad Najeeb" ya faɗa da sigar jan hankali.
"Ka kunna wuta a rayuwarka kuma ni nan na nemi hanyar kashe wutan. Idan ka amince ni Adam ni na haifeka kuma ka yadda ina da hakkin na samu biyayya daga gareka to yau ina umurtar ka da ka je ka shirya, ƙarfe shaɗaya za'a ɗaura auren ka da Aisha"
"What!"
"Ka jini da kyau kuma ba na buƙatar wani dogon bayani e ne ko a'a, idan ka ce e to ka yiwa kan ka adalci, idan kuma ka ce a'a to ka zaɓi samun wani uban daban kenan ba ni ba"
"Dad i'll sort this out, zan je na gaya mu su gaskiya. You dont need to do this"
"NAJEEB!"
Shiru ya ratsa falon.
"Yes or no?"...
...............
Yana shiga ɗakin ya fara kaiwa Anas duka ta ko'ina.
"Dude ba fa ni na ma ta sharri ba fa da za ka sauke a kaina. Abinda ka shuka shi za ka girba"...
Duk da kasancewa abu ne da ya zo cikin ƙurarren lokaci hakan bai sa wannan aure ya tara jama'a ba. Daga ɓangaren Alhaji Jibo zuwa na Najeeb wanda Anas ne yai ta inviting mutane. Ma'aikatan Najeeb constructions da ma su son gulma da ma su zuwa dan Allah da ma su zuwa dan su yi tsegumi da zunɗen Ogan na su duk sun hallara.
Ranan ta asabat wanda ya kafa tarihi a ɓangaren gidajen biyu wato iyalen Alhaji Jibo da na Alhaji Musa Umar Wase.
Ƙarfe shaɗaya da 'yan mintoti aka ɗaura auren Engineer kuma Architect *Najeeb Adam Jibo, CEO Najeeb constructions* 😁 tareda amaryarsa *Aisha Farida Salihu* (ex- secretary @Najeeb constructions😂)
Mutane kowa mamakin auren babban Mutum kuma ɗan manya kamar Najeeb Jibo su ke. Aure ba IV ba sanarwa a kafafen yaɗa labarai ba komai.
Abunka da masu arziƙi a hakan sai da aka haɗa reception bayan an tashi a masallaci aka wuce venue wajen da aka ci aka sha.
Ƙarfe ɗaya saura motar da ta ɗauko su daga asibiti ta tsaya a ƙofar gidan. Ita da Ummi da Maijiddah ne a motan sai ƙanin AbdulWahab mijin Jiddah da ya ɗaukosu kasancewa motar Baffa Musa ta shiga garari.
A hankali su ka shigo gidan nan aka fara guɗa.
"Ayyiriri amarya a gidan manya, tsatson fulani tsatson larabawa. Kyakykyawa mai kyawun hali. Taka lafiya amarya agidan Alhaji Jibo."
Chak ta tsaya lokacin da ta ji kalmar ƙarshe " Alhaji Jibo"
"Mu shiga ciki Farida" Ummi ta faɗa tana hanata damar tambayar ma'anar abinda ta ji...
Zuwa bayan azahar Farida ta shiga ruɗani. Zancen da ake ma ta mai kama da shirin film ta ka sa processing na shi a ƙwaƙwalwarta.
Ba abinda Ummi da Nanna ke ce ma ta sai ta yi haƙuri haka ƙaddarar ta ya zo. Kodan ganin ba ta kuka ne ya sa su ke ma ta wannan zancen banzan wai ta karɓi auren Najeeb Jibo a matsayin ƙaddararta.
Ita da tun jiya da dare da ta fara jin sauƙi ta yankewa kan ta hukuncin komawa karatu ta yi pdg ta yi masters na ta. Sannan ace yanzu an aurar da ita wa Najeeb. Mutumin da ya rusa ma ta auren ta da Rayyan.
Zuwa yamma Baffa Musa ya sa aka kirata. Nasihar dai da su Ummin su ke ma ta shi ma ita ya maimaita. Wai ta yi haƙuri.
"Farida ke 'ya ta ce, kuma ba zan ga abinda zai cutar da ke na tura ki ciki ba. Wannan al'amari rubutacce ne daga Ubangiji. Ki yi haƙuri ki yiwa mijinki biyayya ki kuma zauna agidan ki lafiya. Ki rage yawar magana dan Allah"
Jin Baffa kawai ta ke yi amma aure da Najeeb kam ba ta ga ta zama ba.
Ummi ce ta sa dole ta yi wanka duk da ta ƙi kwalliya amma ta sa wani leshi mai kyau wanda Ummin ne ta siya ma ta saboda wannan rana duk da kuwa a maimakon gidan Rayyan da za a kaita yanzu gidan Najeeb Jibo ne...
Ummi hawaye ta ke tana roƙon Farida ta zauna lafiya da mijinta. " Aisha idan ba ki zauna ba haka za ayi ta irga mi ki aure. Kinga nima tawa ƙaddarar yadda ta kasance, aure na huɗu. Ba na fatan ki zama haka, idan ki ka bi a hankali da sannu za ki gano kan mijinki har ku daidaita kan ku" wannan nasiha na Ummi baƙaramin shigar Farida yai ba....
Ƙarfe takwas da rabi motocin ɗaukan amarya su ka zo. Ummi na kuka Farida na yi haka uwa da 'ya su ka rabu.
Kai tsaye gidan su Najeeb aka wuce da ita. Nanna da Baaba Sabuwa ne su ke tare da ita a mota ɗaya. Su suka ma ta jagora zuwa cikin gidan su mijinta. Su Mom da tawagarta sun ƙarɓi amarya lafiya kuma an karrama baƙin amarya daga ƙarshe aka kaita ɗakin Najeeb wanda anan za su zauna kafin Najeeb ya ƙarasa gyara gidan sa.
Anyi nasiha kuma anyi addu'a kafin wanda su ka kawo amarya su ka tafi.
Tun tana zaune tana jiran ko Najeeb zai zo har ta haƙura ta kwanta dan ba ƙaramin bacci ne a idon ta ba.
Washegari ba ta farka ba sai ƙarfe takwas na safe. Ta shiga banɗakin da ke ɗakin dan ta yi alwala nan ta ga ƙaton bathroom wanda sai ka kwanta ka yi minshari a ciki. Tsaf-tsaf ya ke sai ƙanshi, akwai bathtube na wanka sannan gefe akwai Inda aka kewaye da glass wajen shower kenan. Ta gama kallon banɗakin kafin ta yi alwala ta fito.
Karfe tara sai ga Adama tana ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin.
"Amarya wai ki fito ki karya in ji Hajia" ta ce da ita.
"To barin shirya"
Ta yi wanka ta nemi atampa ta sa cikin kayan da aka kawo ma ta daga gida.
Lokacin da ta sauko sun gama karyawa tana saukowa tanajin Najdah na yiwa Mom ƙorafi " Mom wallahi i cant believe wai Big B ya yi aure, wai hakan ma da lousy secretary ɗin sa"
"Be happy for your brother, finally ya yi aure @35yrs"
"Mom ba ta dace da gidan nan ba..."
"E'e'em" Farida ta yi gyaran murya
Najdah ta ɗago ido ta kalleta. Farida ta ɗan risina ta gaida Mom. Mom ta ma ta ya kwanan baƙunta.
"Najdah take her to the dining plz"
Maimakon Najdan ta yi abinda Mom ta ce sai ta fara kiran Adama.
Farida dai ta taune ta haɗiye duk wani maganan da ke bakin ta, kar ace amarya daga kwana ɗaya ta fara faɗa da ƙanwar miji.
Da Adama ta kaita dining ɗin ɗiban abinda za ta ci ta yi ta koma ɗakin Najeeb ko na ce ɗakin su.
Baƙi sun zo ganin amarya kuma ta fita an gaggaisa. Yawanci 'yan uwa ne da abokan arziƙi...
Tana sallar Isha ya shigo ɗakin zama yai a bakin gado yana kallon yadda ta ke sallah. He cant believe he got married to this girl, a mere secretary.
Lokacin da ta idar da sallan ya kalleta da kyau sannan ya ce " Daddy na son ganin mu ƙarfe tara"
Zuwa yai ya zauna kan kujeran da ya ke aiki idan yana ɗaki, ya kunna laptop na shi yana duba wa su saƙonni.
"Sir Najeeb dama ka min sharri ne dan ka aureni?"
Yi yai kamar bai ji ta ba sai da ta sake maimaita tambayar sannan ya juyo ya ce " i wanted to punish you, i wanted you to cry, but it backfires on me. Na aure ki ne saboda Dad, only because of him"
Shiru ta yi tana nazarin kalamanshi tareda tunanin mafita a rayuwar ta ko na ce a rayuwar auren ta.
"Dad ba ya zama a gida, Baby na zuwa makaranta, Justice Nabilah ma ba ta zama. You'll feel bored at home"
"Ina ruwanka" ta faɗa da ƙarfi.
Juyowa yai yana kallonta sosai, har lokacin tana zaune akan sallaya.
"I'm offering you a job. Har yanzu ban samu secretary da zai maye gurbin ki ba, so you can have your job back"
"Kan uba. Lallai ma Sir Najeeb ka raina ni"
"Well its just an offer, idan ki na so za ki iya fara aiki next week monday"
"Allah ya isa na Sir Najeeb, Allah ya isa bulluƙutu"......
(Mrs Najeeb Jibo, Najeeb constructions needs your service, Oya de go de go😁)
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi*
0️⃣2️⃣4️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
Tare su ka shigo falon Daddy, ya na zaune yana karatun littafi su ka same shi.
Farida ta zauna ƙasa tana gaida Daddyn.
" 'yata tashi ki zauna mana"
"Daddy na fi jin daɗin ƙasan"
Daddy ya ajiye littafin ya ce
"Aisha, ina so na baki haƙuri kan yadda al'amura su ka kasance. Kin ga wannan da ki ke gani" ya nuna Najeeb.
"Babban banza ne, ba abinda ya sani sai kan sa. Ina roƙon ki dan Allah, ki yafe ma sa duk abinda ya mi ki"
"Daddy komai ya wuce, na yafe ma sa"
"Allah ya mi ki albarka Aisha. Sai ki riƙa haƙuri da shi domin shi ɗin wani bahagon mutum ne"
"Dad" Najeeb ya faɗa yana tsume fiska
"Ai gaskiya na faɗa, ko ba haka ba 'yata?"
"Haka ne Daddy, wallahi wani lokacin kaman majnuni" sai da ta yi maganar kuma sai ta ji kunyar abin da ta faɗa, ta fara rufe baki da hijabinta.
"To kinga duk waɗannan halayen na sa marasa kyau, ke ce za ki shafe su, ke ce za ki inganta rayuwar sa. Ina muku fatan samun zuri'a ɗayyaba"
Farida ta ɗago ido ta kalli Najeeb wanda ya watsa ma ta harara.
"Za ki yi haƙuri ku managing wannan gida zuwa wani ɗan ƙanƙanin lokaci kafin ya ƙarasa gyara gidan shi sai ku koma chan. Ina so ki sake jiki damu domin nan gidan ki ne. Allah ya sa albarka a wannan aure na ku amin"
"Na gode Daddy, Allah ya ƙara ma ka lafiya ya ƙara arziƙi da buɗi amin"
"Duk abinda Najeeb ya mi ki ba dai-dai ba, kinga duk girman shin nan a gaban ki zan sa bulala na zane shi"
Farida ba ta san lokacin da ta kwashe da dariya ba ta ce " wayaga ana zane Sir Najeeb, har na hango shi yana tsala ihu"
Daddy ma ɗan darawa yai.
Najeeb kam haɗe rai yai yana yiwa Farida kallon za ki gamu da ni.
"Najeeb idan ba abinda za ka ce, za ku iya tafiya"
"Good night" ya faɗa ya tashi da sauri kaman wanda a ƙaya ya ke zaune da ɗin.
Farida ta bi bayan shi bayan ta yiwa Daddy sai da safe a nitse...
Tana shigowa ɗaki ta sameshi ya na kishingiɗe akan gado hannun sa ɗauke da waya ya na dannawa. Ƙarasawa ta yi ta cire dogon hijab da ta yi sallah da shi ta ninke ta kaishi saman bedside drawer.
"Ba a ajiye kaya anan"
"To hijabin sallah ne ai"
"Ba a ajiye kaya a nan Miss Salihu"
Dariya ta yi ta ce "yau na ji wani zance, Miss Salihu kuma? Jiya dai aka ce wai Najeeb Adam Jibo ya biya sadaki na naira dubu ɗari biyu, ko ba haka ba?. Gara ka san da me za ka kirani amma ba Miss Salihu ba"
Kallon ta ya ke yi itama ɗin ta zuba mi shi ido, doguwar rigan bacci ne a jikin ta wanda ya kai har ƙasa amma siririn hannu rigan ke da shi.
"Oh! so yanzu kin zama Mrs Jibo kenan? Congratulations"
"Ni kam Sir Najeeb mi ye acikin Aisha ko Farida da ba za ka iya kira na da shi ba?"
"Ki ɗauke kayan nan, ba a ajiye kaya a cikin ɗaki"
"To ka nuna min inda zan sa kaya na ne. Ina wancan wajen duk kayan ka ne a ciki, kaya sai ka ce wanda mutum ya buɗe boutique"
" This is my room Mrs Jibo, dole ki bi tsarin yadda ɗakin ya ke, ba na son datti, ba na son clumsiness. Kin ga yadda komai ya ke a tsare, haka na ke so komai ya kasance a inda ya ke. So ki ɗauke wancan tsummukoran a wajen nan"
"Hijabin nawa ne tsummokara, lallai"
Shiru ta yi tana kallon sa, ta ga ya maida hankalin sa kan waya.
Ƙaraman tsaki ta yi sannan ta ɗauki hijabin ta kai shi wajen closet ɗin.
Tana dawowa ta zauna bakin gado tana shirin kwanciya ya ce " and what are you trying to do?"
"Bacci ma na"
"A ina ɗin?"
" ni fa Sir Najeeb ka ƙyale ni tam. Idan ba haka ba na gayawa Daddy, ka san ya ce har zane ka zai iya yi a kaina"
" there's no way i'm sharing a bed with you ki na sakatariya ta. Ga chan sofa chan ki je ki kwanta akai"
"Da ka san ba za ka iya haɗa gado da ni ba miyasa ka aureni. Ni bance ka min komai ba dan na san abinda ka ke tsoro kenan" ta ƙarasa maganar tana kwanciya da kyau.
Ajiye wayar sa yai ya taso ya na ƙoƙarin ɗauketa daga kan gadon, ita kuma ta riƙe zanin gado tana " Allah ba inda zan je, ba zan kwana a kujera ba sai dai kai ka kwana"
Wuff yai sama da ita ya zo ya sauketa a kan sofar. Yana ajiyeta ta sake tasowa ta zo za ta kwanta, yasake ɗaukan ta ya maida ita kan sofa.
"Mrs Jibo, idan ba wani abin ki ke nema a wajena ba, sleep here"
"Tabɗijam, wallahi ko a makaranta ban kwana a kujera ba balle a nan. Wallahi ka barni na kwanta ko na gayawa Daddy"
"Go on, je ki gaya ma sa" har ta fara tafiya sai kuma ta juyo ta ce "ƙila ya yi barci yanzu"
Miƙa ma ta wata na'ura yai ya ce " za ki iya gaya ma sa ai ba sai kin fita ba, ga shi ki danna 2 ki yi ma sa magana zai ji ki a ɗakin sa"
Ita fa ta ɗauka wasa ya ke dan abin yai ma ta kama da wayar cellular ta ƙarɓa ta ce "ƙila ma ƙarya ne"
"Go on try it"
"Daddy ga Sir Najeeb ya hanani kwana a gado, ka zo ka ma sa magana" ta faɗa da ɗan ƙarfi.
Murmushi yai ya ce " stupid girl"
Minti biyu kacal sai ga shi ana ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin su.
"Najeeb be matured please, mi ye wannan shirmen"
Jin muryan Daddy ya sa Farida ta yi saurin kama baki tana dana sanin abinda ta ce.
"Sorry Dad, good night" Najeeb ya faɗa sannan ya kalli Farida da ke tsaye tana zare ido.
"On a second thought, za ki iya kwana akan gado but" ya nuna ta da yatsa "kar ki kuskura ki matso kusa da ni, i can bite"
"Ni ma kar ka kuskura ka matso kusa da ni, i can scratch"
Zuwa yai ya jera pillow biyu a tsakiyar gadon sannan ya kwanta.
"Wallahi wajen ka ya fi yawa, wannan ba tsakiya ba ne"
Sa hannu yai ya kashe wutan ɗakin. Dole ta laluba ta kwanta a haka.
Chan ƙasar ran ta tana tunanin anya akwai ranan da Najeeb zai iya jin son ta, ko da ɗan kaɗan ne? Anya za ta iya samun kan sa kamar yadda Ummi ta ce? Anya akwai ranan da za ta kwanta da shi ta yi rayuwar aure da shi?
Ta tuno abubuwan da ta yi ta sha da ci saboda samun amarci mai cike da tarihi tareda Rayyan, amma yanzu kam duk a banza. Tana cikin tunane-tunanen nan har bacci yai gaba da ita...
Ya na kwance ne amma ba wai ya yi baccin ba. He still wonders why everything turns out this way, jiya saboda bai san yadda zai haɗu da ita ba shiyasa ya kwana a office. Komai ya zamo ma sa wani iri, she's just his secretary and that's what she'll always be 🙄
Bai taɓa hango rayuwar aure da wata ba idan ba Sabreen ba. Sun planning komai tare, tun daga irin gidan da za su zauna har zuwa 'ya'yan da za su haifa. Yara biyu Sabreen ta ke so, kuma shi su ka tsara za su haifa ( ka ji fa😁). Ba su tsara zama a Nigeria ba saboda Sabreen ba ta so, a plan ɗin su Nigeria sai dai ziyara amma ba zama ba. But yanzu komai ya chanza and now auren Aysherh...
......................
Washe gari da asuba alarm ɗin Najeeb ya farkar da Farida, Ita kam ganin ƙarfe huɗu kuma akwai bacci a idon ta ya sa ta cigaba da bacci.
Ƙarfe biyar da rabi na ta alarm ɗin ya buga. Ta tashi ta hango Najeeb yana aiki a laptop ɗin sa. Cikin zuciyar ta ta ce "yanzu haka tun tashin sa bai yi sallah ba, shi komai aiki kaman machine"
Ta tashi ta shiga banɗaki fitsari ta yi sannan ta yi alwala ta fito.
Ta shimfiɗa sallaya ta tada sallah.
Da ta idar ta kalleshi har lokacin yana aiki.
"Sir Najeeb ina kwana"
"Morning" ya faɗa kaman ana roƙan sa amsan...
Tana azkar ɗin safiya ya tashi ya shiga banɗaki sai kuma ya fito ya ce "Mrs Jibo, next time ki ka yi amfani da toilet, you flush it immediately"
"Fitsari kawai fa na yi"
"Ba na son ƙazanta"
"Toh na ji, kuma ni ba ƙazama ba ce"
Ya jima a banɗakin har ta gama addu'o'inta ta koma gado ta kwanta bai fito.
Ya na fitowa ta bi shi da ido daga inda ta ke kwance, bathrobe ne ajinsa fari. Zuwa yai ya tsaya gaban mirror yana ƙoƙarin shafa mai. Duk abinda ya ke tana kallon sa har ya gama ya je ya shirya cikin wani grey suit na kamfanin Dolce and Gabbana. Dole ta rasa gane wani irin turare ya ke amfani da shi saboda turarukan da ya fesa sun fi biyar. Lokacin da ya gama ya taje gashin kan sa sannan ya matsa wanni mai a hannunsa ya shafa a gashin.
Ya sake shiga banɗakin kafin ya fito ya ce " i know you are staring Mrs Jibo, idan kin tashi ki kira Adama za ta gyara ɗakin"
"Ni mi zan gani, ni ba kai na ke kallo ba"
"Mrs Jibo think about my offer" yana faɗin haka ya ɗau brief case na shi ya fita.
Agogo ta duba ta ga ƙarfe bakwai saura minti ishirin. Kai dole Sir Najeeb ya dinga zuwa da wuri, duk da kamfanin sa ne amma ba ya wasa da zuwa da wuri.
Bayan fitan sa sai da ta mori bacci sosai kafin ta tashi wajen ƙarfe goma ta fara gyara ɗakin...
....................
"Dan Allah wa ya ke zuwa wajen aiki ranan ukun auren sa. Haba Najeeb ko a week break ba za ka ɗauka ba"
"A week break? Bayan asaran da Miss..." " i mean Mrs Jibo ta jawo min"
Anas ya kwashe da dariya " Mrs Jibo, haba nawan, ba wani sweet pet name da za ka sa ma ta sai Mrs Jibo"
"Mrs Jibo ma ai matsayi ta samu"
"Akwai lokacin da za ka kirata sweetheart, my love..."
"Oh please Anas"
"Allah Wallahi. Yanzu dai akwai wani Korede da zai fara aiki da kai yau, i hope you'll like him"
"No need, Mrs Jibo za ta resuming monday"
"Wait, Farida za ta dawo nan?"
"She has no choice"
"Ka san mi ka ke faɗa kuwa? Yanzu fa Farida matar ka ce"
"So what?"
"Wallahi ba ka ma ta adalci ba Najeeb. Ita da ya kamata ya zama tana zaune a gida, ana treating na ta kamar queen, sai ka kawota nan, nan ɗin ma a matsayin secretary"
"Ba na buƙatar shawaran ka, hold it to yourself"
"Amma Daddy ya sani?"
"Anas ba ruwan ka da al'amarin rayuwata. Dont meddle with my family affairs"
Anas ya sa dariya ya ce "sannu Mr Family man"
* ku yi haƙuri na yi update ɗaya yau, kuma ba shi da yawa. Bi izni kun fa ya kun, gobe Insha Allah 2 updates za ku samu. Thank you for your patience*
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣2️⃣5️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi*
Bayan fitan Anas da jimawa sai ga Khalidah fuuuu ta shigo office kamar wadda aka korota.
"Najeeb why?, why her?"
"Excuse me"
"Najeeb all this while da na ke zuwa wannan wajen ka ɗauka dan kuɗi na ke zuwa, ko an gaya ma ka ina son aikin wahala ne. Saboda kai na ke aiki a nan. Only for you"
"So?"
" Najeeb ka rasa wadda ta dace da kai sai Farida, miye ta ke da shi"
"Idan kin gaji da aiki za ki iya forwarding resignation letter ɗin ki, zan yi farin ciki da ƙarɓan sa"
"Najeeb dan Allah ka fahimce ni, Ina son ka, ina son ka fiye da yadda ka ke tsammani"
"Get out"
"Najeeb please"
"Out"
.......................
Bayan ta gama gyara ɗakin ta yi wanka ta shirya cikin atampa riga da skirt, ta sauko ƙasa dan yunwa ta ke ji. Gidan shiru sai ƙaran TV da aka bari a kunne. Zuwa ta yi wajen dining ɗin ta zauna ta zuba abinci ta fara ci.
Adama ta fito daga kitchen za ta haura sama Farida ta kira ta.
Sai da su ka gaisa sannan ta ce " mutanen gidan sun fita ne?"
"Eh"
"Ayya sannu da aiki"
"Na gode Anty"
"Anty kuma, ai sai ki sa na ji kunya. Ki kira ni Aisha ko Farida"
"Anty Farida dai"
Farida ta sa dariya.
"Dama na ce daga yanzu ba sai kina gyara ɗakin mu ba, zan dinga gyarawa"
"Na gode" Adama ta faɗa tana murmushi.
Da rana tareda Adaman su ka yi girkin rana, su na aikin tana ma ta tambayoyi gameda gidan. Su biyu ne ma su aikin ita da Tasallah. Tasallah kuma ta je gida an mu su rasuwa. Ita Adama matar Iliya dreba ne ita kuma Tasallah bazawara ce wanda aƙalla za ta kai shekaru arba'in zuwa arba'in da biyar.
Da su ka gama ta haura sama ta duba wayar ta ta ga miss call ɗin Maijiddah da text ɗin ta, inda ta ke sanar da ita ta isa gida lafiya. Kiran Maijiddan ta yi amma ba ta ɗauka ba sai ta kira Ummi. Sosai su ka yi hira da Ummin wanda ta ke ta ƙara ma ta nasiha akan haƙuri...
Ƙarfe uku saura Mom ta dawo, bayan ta kimtsa ta ci abinci ta sa Adama ta kira ma ta Farida.
Farida na bacci ta ji ana ƙwanƙwasa ƙofa kamar daga sama, ta tashi da ƙyar ta zo ta buɗe.
"Anty Farida Hajia na kiran ki"
"Ok tana ina? Tana falon sama"
"Ina zuwa"
Sai da ta wanke fiskarta sannan ta fito.
A ɗan kishingiɗe ta sameta kan kujera ta yi nisa cikin tunani.
Farida ta ɗan yi gyaran murya ta ce " Mom barka da yamma"
Mom ta ɗago kai ta kalleta tareda ƙaƙaro murmushi.
"Sannu da zuwa Aisha"
Sai da Farida ta gyara zama sosai sannan ta ce "you're lucky Aisha, Kin san, Najeeb yana son sunan Aisha sosai"
"Ayya! Amma bai taɓa kirana da shi ba kuwa"
"He likes you. Na san bai gane hakan ba amma nan gaba zai gane"
Farida dai shiru ta yi tana sauraron wannan mata wadda ta ke uwar miji gareta.
Mom ta ɗauki wanni takarda da ke gefen ta ta miƙawa Farida ta ce " na rubuta mi ki abubuwan da ya ke so da wanda ba ya so. Zai taimaka mi ki wajen ganin kun fahimci juna da wuri"
"Na gode Mom"
Ta miƙa ma ta wani ƙaramin jewelry box ta ce "wannan kyauta ne da na ke son bawa duk matar da Najeeb ya aura"
Farida ta ƙarɓi box ɗin tana godiya.
"Open it"
Tana buɗewa ta ga sarƙa ce ta dimond sai walwali ya ke.
"Its pure dimond" Mom ta faɗa tana kallon yadda Farida ke kallon sarƙan
"Mom na gode, Allah ya saka da alkhairi. Haƙiƙa banida ma bakin godiya, this is too much Mom"
"Ba komai, just make him happy"
"Insha Allah zan yi ƙoƙari Mom"...
Farida na shiga ɗaki ta ɗau sarƙan nan ta gwada sawa a wuyan ta, tana duba kan ta a madubi. Wannan duk taron da ta je ta sa ka shi sai ta zama topic of the day. Tana cikin dubawa sai kuma ta ji jikinta yai sanyi tunowa da ta yi wanda aka bata sarƙan domin sa ba wai ya damu da ita ba ne.
Ta maida sarƙan inda ya ke sannan ta ɗauko takardan da Mom ta ba ta, ta fara karantawa.
- ya fi son kala baƙi
- ya na son cin fruits (musamman apple, inabi da lemu)
- ya na son coffee
- ya na son ƙanshi
- ba ya son wari
- ba ya son ƙazanta
- ba ya son hayaniya
- ba ya cin doya
- ya fi son kifi akan nama
- ba ya son jan abu....
Wayar ta da ya fara ringing ne ya sa ta tsaya da karantawa. Ta ɗauko wayan sai ta ga Rayyan ke kiran ta. Har wayan ta katse ba ta ɗauka ba.
"Mi kuma zai ce min" ta faɗa a fili yayinda kiran sa ya sake shigowa. Sai a kira na uku ta ɗauka.
"Rayyan lafiya ka ke kirana?"
Daga ɓangaren Rayyan ya ce "My Farida ban san ya zan yi ba, yanzu na ke jin wai hotunan nan haɗa su aka yi, wai Alhaji Jibo ya zo ya samu Baba ya nemi a maida zancen auren mu. I'm sorry dear, ki bani lokaci mu zauna mu yi magana"
"A ina za mu zauna? A saman kwano ko a saman bishiyan mangoro. Look Rayyan, kar ka ƙara kira na, ni matar aure ce"
Ta na kashe wayar ta cillata kan gado ta cigaba da karanta takardar da Mom ta ba ta.
...........................
Kusan ƙarfe biyar wa su baƙi su ka zo Adama ta zo ta kirata ta sauko ƙasa. Su biyu ne, ɗaya ta ganeta domin jiya ta zo, ƙanwar Daddy ce da su ke kira Hajia Fatima. Ɗayar kuma ba ta san ta ba.
Sai da su ka gaisa Hajia Fatima ta gaya ma ta sun zo ƙarɓan sizes ɗin ta ne saboda lefe da za'a haɗa ma ta.
Hajia Salma da su ka zo tare wadda ta ke amaryar Uncle Sulaiman ne ta ɗauko Tab ɗin ta ta na rubuta sizes ɗin, tundaga na inner wears zuwa general measurement na ta.
Bayan sun gama aka buge da taɗi, su na haka sai ga Najeeb ya shigo.
"Yawwa ango dama kai mu ke jira"
"Ni kuma?"
"Yes, mun zo karɓan kuɗin haɗa lefe"
"What's that?"
"Ɗan iska, dan ka yi ƙwacen mata sai ba za ka ma ta kayan lefe ba. To ba zai yiwu ba"
Hajia Salma ta ce " Najeeb bar Hajia Faty da tsokala. Check za ka rubuta ma na za mu haɗawa Farida kayan lefe"
Sai da yai kamar ba zai yi magana ba sai kuma ya ce "how much?"
Hajia Fatima ta ma sa daƙuwa ta ce " ungo na ka da how much ɗin, blank check za ka bamu"
"Hell no, there's no way i'm giving you a blank check. Ki samu daman zuba jari a shagunan ki ko?
"Zan ci ƙaniyar ka Najeeb"
Najeeb ya zauna ya ciro check book na shi ya fara cikatawa Hajia Salma da Hajia Faty idon su ƙyam akan abinda ya ke rubutawa.
Hajia Fatima ta ce "Allah ya sawwaƙa Najeeb, mi wannan zai yi? Ka san ina da ina zamuje kuwa? Kai ka na sa kaya designer ba ka so matar ka ta sa designer ne?"
Farida kam dai kallon su ta ke yi dan ba ta ga nawa ya rubuta ba. Ƙarshe dai dole blank check ɗin ya ba su...
Yana shiga ɗaki ya ji wayar Farida da ke kan gado yana ringing haka kawai sai ya tsinci kan sa da ɗaukar wayan wanda kafin ta yanke ya ga sunan nan dai da ke tada ma sa hankali *My Ray* tsaki yai ya maida wayar ya ajiye.
Ya na cire kaya amma sai tsaki ya ke shi kaɗai.
Lokacin da ta shigo yana kan gado, ya kunna TV da ke ɗakin yana kallon tashar Aljazeera.
"Sannu da dawowa, ya aiki"
" your Ray ya kira ki"
Dam ta ji gaban ta ya buga. Ita wallahi ta manta ba ta goge numbar bane ɗazu.
"Sir Najeeb ba wai abinda ka ke tunani ba ne, Allah mantawa na yi ban goge numbar ba"
Bai ce komai ba sai ma remote da ya ɗauka ya fara chanja tasha.
Ganin yai shiru ta ce " Sir Najeeb ka yiwa Mom godiya ta min kyautar girma. She gave me a dimond necklace"
"Mrs Jibo" ya faɗa da sigar jan hankali.
"Kar ki ƙara yi min maganar matar nan"
Farida ta zaro ido "mahaifiyar ta kan"
"Idan ki na so mu zauna lafiya, to ki dena kawo min zancen ta"
" yau na shiga uku, Sir Najeeb...."
"Shhhhhhh"
Haɗiye maganar ta yi dan yadda ta ga ran sa ya ɓaci.
Zama ta yi a gefen gadon ta ce "Sir Najeeb zan yi aikin, amma sai ka amince za ka bani dama na wanke kai na daga zargin da ka ke min"
" good for you"
..........................
Zuwa yanzu ta gama gane yanayin gidan. Mom ba ta da matsala ko kaɗan hakan ya sa ta rasa gane dalilin da zai sa Najeeb ya dinga ma ta abinda ya ke yi. Najdah kam ƙiri da ƙiri ta ke nuna ba ta son ta. Ita kam ko ajikin ta, dan ba wannan ba ne a gaban ta.
Ranar asabat da ta cika sati ɗaya 'yan gidan su su ka zo ma ta gaisuwa. Ta ji daɗi sosai kuma ta karrama su, gayya guda su ka zo dan duka matan Baffa Musa ne su ka zo da yaran su kusan su goma. Da za su tafi ta haɗa mu su tsaraba...
Anas tun ranan da Najeeb ya ma sa zancen zai dawo da Farida aikin t, ya kira yana ma ta faɗa akan miya sa za ta amince da haka, ta nuna ma sa ba komai ita ke son komawa aikin...
"Sir Najeeb wai haihuwa ka ke a banɗakin ne? Tun ɗazu fa" ta cigaba da ƙwanƙwasa banɗakin.
Haƙura ta yi ta je ta zauna tana jiran sa, dama fitsari ne ya matseta.
Yana fitowa ta tashi da sauri ta shiga banɗakin.
Tunanin ko lafiyarta lau ya ke. If she's really pressed mi ya sa ba za ta je guest room ba.
Lokacin da ta fito ɗaure da towel ya riga ya shirya takalmi kawai ya ke sawa.
"Sir Najeeb ka jirani mu tafi tare dan Allah"
" i'm not your driver"
"Sir Najeeb ya ka ke so na yi, anguwar kun nan ba lallai mutum ya samu abin hawa da wuri ba"
"Akwai mota a gidan"
"Motan tuƙa kan ta za ta yi ne. Ni ban iya tuƙi ba"
Ya miƙe tsaye ya ce "good for you"
Har ya kai bakin ƙofa sai kuma ya juyo ya ce "idan kin je office ki yi aikin ki kamar yadda ki ka saba, cause our relationship is strictly professional"
"Na ji Mr professional"
...........
Ta ci sa'a da ta fito lokacin Mom za ta fita ta ce ta shiga ta kai ta. Da suna tafiya ta ce idan sun dawo ta zo ta karɓi key ɗin mota. Farida ta ce ba ta iya tuƙi ba, mom ta ce za ta sama ma ta dreba.
Lokacin da ta shigo kamfanin kowa kallon mamaki ya ke ma ta tunda dai kowa ya san ita Sir Najeeb ya aura. Kai tsaya office ɗin ta ta je, yana nan yadda ya ke ta ajiye jaka ta shiga office ɗin Sir Najeeb.
Yana waya lokacin da ta shigo dan haka ta samu waje ta zauna maimakon da da take tsayawa a gaban sa. Sai da ya gama wayar ya kalli agogon hannun sa ya ce "8:44am Mrs Jibo"
Ta langwaɓar da kai ta ce "na tsaya na karya ne kuma kai ma ka san..."
"Shhhhhh, kin san ba na son latti. Today should be the last time da za ki zo min office a makare. Sannan ba na son personal excuses na ki a nan. Here, our relationship is..."
"Strictly professional na sani" ta ƙarasa ma sa.
"Good, akwai wassu saƙo da zan tura mi ki ki printing na su ki distributing na su according to their respective specification"
"Ok" ta tashi za ta tafi sai ya ce "ɗauko min wancan green file ɗin" ya nuna ma ta shelf ɗin da ke office ɗin. Ta je wajen sai ta ga file ɗin yana ta ƙasa ne ta tsugunna za ta ɗauka dai-dai idon sa ya kai wajen dan ya tabbatar file ɗin za ta ɗauka. Wandon jeans ta saka baƙi sai shirt mai dogon hannu ash color, ta yi rolling da baƙin gyale. Ɗan tsugunnon da ta yi sai rigan ya ɗan ɗaga. Ya rintse idon sa saboda wani abu da ya ji ya tokare ma sa maƙoƙoro.
Farida ta ɗauko ta ajiye ma sa.
Gyaran murya yai ya ce "Mrs Jibo, akwai dokar da ta ba da dama wa duk wata matar aure da ke son saka hijabi a wannan kamfani da ta sa, ba matsala"
"So?" Ta faɗa tana harɗe hannayen ta a ƙirji.
"It means, za ki iya saka hijabi ko mayafi babba tunda ki na da aure"
"I see, amma ka sani ko nawa mijin bai damu da sa hijabina da rashin sawata ba"
"Still Mrs Jibo, ya kamata..."
"Shhhhhh, Sir Najeeb our relationship is strictly professional" ta kwaikwayi muryan sa.
Ya ɗan ji zafi a ran sa amma ya dake da ce wa "ok get back to work"
Har ta buɗe ƙofa idon sa na kan bayan ta. Irin kayan da ta ke sawa ne tun da, amma ya rasa dalilin da ya sa yanzu bai son ganin ta da wannan kayan...
Tana zaune tana typing Anas ya zo zai shiga office ɗin Najeeb sai kuma ya tsaya su na gaisawa. Labarin marukan da Najeeb ya sha a kan ta ya fara yi ma ta wanda ya sa ta fara dariya. Dai-dai lokacin kuma Najeeb ya fito, ba yau Anas da Farida su ka fara hira su na dariya ba amma yau gani yai dariyar ta yi yawa.
"Ango wajen ka na ke son zuwa amma tunda za ka fita barin jira ka a nan, idan ka dawo sai mu yi maganar"
Najeeb bai ce komai ba ya fita, bai yi nisa ba sai ya dawo, har lokacin magana su ke.
Yai gyaran murya ya ce "Mrs Jibo ki tuna min ina da meeting ƙarfe goma"
Ba tareda ta kalle shi ba ta ce to.
Ya sake fita amma ko taku biyar bai yi ba ya dawo.
"Mrs Jibo follow me"
"Ina zuwa"
"Follow me, now!" ya daka ma ta tsawa. Shi kam Anas ya gane kishi ke ran sa, tun ɗazu da ya fito ya ga irin kallon da ya ke ma sa kaman zai mangareshi.
Farida ta tashi da sauri ta ce " ina zuwa Yaya na"
Sai da su ka fita Anas yai dariya ya ce "muje zuwa Najeeb, da kan ka za ka hanata aikin nan"
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣2️⃣6️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi*
Har su ka isa second floor bai ce ma ta komai ba. Bin shi kawai ta ke yi amma har su ka dawo ba abinda ta ma sa. Su na dawo wa ta ce "Sir Najeeb dama ba abinda zan yi shi ne ka hana mazauna na su samu hutu"
"Dama hutu ki ka zo yi ne?"
"Sir Najeeb its not fair, ina zaman-zamana kawai ka zo ka tasheni ,na yi ta bin ka kaman wanda aikin bodyguard ka ɗauke ni"
Kafin ya ba ta amsa wayarta ya fara ringing.
"Your Ray?"
"To ba shi ba ne, Yakubu ne" ta faɗa tana picking call ɗin ta yi waje.
Shi ma ɗin ɗaukan waya yai ya kira Anas. Lokacin da Anas ya zo ya ce "ango-ango, ka gama yawo da amaryar ta kan. Can we discuss business"
Najeeb ya ɗan gyara zama ya ce "wannan Architect Yakubu ɗin whats his surname?"
"Yakubu Musa Wase"
"Ok"
Anas ya kalli reaction ɗin Najeeb ya kwashe da dariya yace " ba dan ka ma sa ƙwace ba da yanzu shi ne angon Farida"
"Kar ka ƙara cewa na yi ƙwace. You and Dad force me into this marriage"
"Ayya! Ashe abinda ya faru kenan ko. Sorry Najeeb angon Aisha"
"Cut this bullshit, ya ake ciki?"
"Dama maganar hutun ƙarshen shekara ne, ta ya za'ayi a gama duk wasu major project da mu ke da su a ƙasa kafin lokacin?"...
Tana duba wasu takardu sai ga mutum ya shigo ma ta office da sallama. Ɗagowar da za ta yi sai ga Rayyan.
Ta miƙe tsaye da sauri. "Rayyan lafiya?"
"Kin ƙi ɗaukan waya ta Farida kuma na ji labari kin fito aiki"
"Wato stalking ɗina ka ke yi?"
"Farida ki zauna ma na mu yi magana"
"Wanni maganan za mu yi?, ni fa matar aure ce Rayyan"
"Exactly, matar Rayyan ya kamata ki zama ba ta Najeeb ba. Duk abinda yai ya yi ne da sanin kan shi dan ya raba mu. Idan ba rashin sanin darajan mace ba, ta ya zai auri mace kamar ki just one week ya dawo da ke aiki, aikin secretary"
"Rayyan dan Allah ka tafi. Ka ga miji na na nan"
"Miji? My Farida miji fa ki ka ce. Ina ki ka saka alƙawurran da mu ka yiwa junan mu. Tun yanzu har kin fara cin amana ta kenan"
"Yau na ga ta kai na, Rayyan duk alƙawarin da na ma ka ba wanda na saɓa aciki, Na yi alƙawarin mallaka ma ka zuciya ta da duk soyayyata idan mu ka yi aure. Kuma ba mu yi aure ba mi ya kawo maganar cin amana a nan?"
"Saboda yana da kuɗi ko?"
" yes, saboda ina da kuɗi"
Su ka jiyo muryan Najeeb a bayan su.
"Daɗin abin ma sai dai mutum ya bi gefe yai zagon ƙasa amma bai isa ya tunkari mace ya nemi soyayyarta ba" Rayyan ya faɗa yana yiwa Najeeb kallon banza.
Najeeb ya ƙaraso kusa da shi ya ɗan buga kafaɗar sa ya ce " mutumina ka ɗan je ka ɗauki darasi a kan virtual reality ka ji"
Ya miƙawa Farida hannun sa guda ɗaya ya ce " Mrs Najeeb Jibo shall we"
Farida ta haɗiye miyau saboda kan ta ya ɗaure amma indai dan ta yi abinda zai sa Rayyan ya fita a rayuwar ta ne to za ta yi. Duk da ta so Rayyan a baya, amma yadda ya shure watannin da su ka yi tare ya fasa auren ta ana saura kwana biyu ɗaurin aure ya sa tana jin ko da akwai burbuɗin son shi a tareda ita to za ta kaɗe shi ta huta. Ko da ba ta auri Najeeb ba Rayyan ya dawo, to ba za ta iya auren sa ba bayan ya riga ya watsa ma ta ƙasa a ido.
Ta sa hannun ta cikin na Najeeb tareda matsowa ku sa da shi, maimakon ya tsaya a haka sai ya jawo ta jikin sa sosai. Ya kalli Rayyan da yai mutuwar tsaye a wajen saboda kishi ya ce " please feel free to visit Najeeb constructions some other time, yanzu Mr and Mrs Jibo za su huta. So get out"
Yadda ka san an sace balon-balon (balloon) haka gwiwar Rayyan ta yi sanyi. Yana son Farida sosai tun ranan da ya fara ganin ta a Keke kuma har yau yana son ta, hotunan da ya gani su suka birkita ma sa tunani ya rasa gane kan sa, musamman da ya kasance dama mahaifiyar sa ba son Faridan ta ke ba, ta dai haƙura ne a lokacin dan ba yadda za ta yi.
Juyawa yai zai fita dan bashida ta cewa a wajen. A yadda ya ke ganin su zai iya shaƙe Najeeb a wajen.
"One more thing, dont ever call Mrs Jibo again"
Rayyan ya ji wani abu ya suke shi a ƙirji. Ya haɗiye miyau da ƙyar sannan ya sa kai ya fita.
Rayyan na fita Najeeb ya ture Farida gefe.
Ta ɗan yi ƙara ouch.
"Sir Najeeb za ka karya min ƙafa"
Fiskar nan ba wasa ko kaɗan ya ce " kar ki sake kawomin tarkace office"
Ta gyaɗa kai saboda yadda ta ga ya ci serious.
Har aka tashi ranan Najeeb ba shi da walwala. Tana ganin ya fito zai wuce gida ta yi saurin bin bayan sa. Bai ma ta magana ba har su ka isa gida itama ba ta ce komai ba dan yunwa ta ke ji.
Shi ne ya fara shigewa ciki ita kan zuwa ta yi ta ɗebi abinci kafin ta haura sama da tray a hannunta.
Tana shiga ta gan shi tareda Najdah, Najdah na nuna ma sa hoton abu a wayarta wai ya zaɓa ma ta.
Sallama ta mu su amma ba ta ji an amsa ba, ko da kuwa an amsan to aciki su ka yi.
"Amsa sallama yana daga cikin haƙƙin musulmi akan ɗanuwansa musulmi"
Najdah ta ɗaga ido ta kalleta sai kuma ta sauke ido. Shi kam Najeeb bai ce komai ba ya san fitina ta ke nema and he's not ready for that.
Ta ajiye tray ta shiga banɗaki ta watsa ruwa, lokacin da ta fito Najdah ta fita. Ba ta san mi ya sameshi ba amma ta ga ko kayan jikin sa bai cire ba ya miƙe akan gado yana kallon sama.
"Sir Najeeb ba ka da lafiya ne?" Shiru
"Sir Najeeb ka tashi mu ci abinci"
Ta gama duk surutun da za ta yi amma bai ce komai ba sai daga baya ya tashi ya shige banɗaki...
.....................
Sati ɗaya kenan da fara zuwa aikin ta, ba za ta ce komai na tafiya dai-dai ba ba za kuma ta ce akwai matsala ba. Yawanci ma Najeeb ba ya zama a office ya kan fita supervising ayyukan da kamfanin sa ke yi kuma ya ke so a ƙarasa kafin hutun ƙarshen shekara.
Safiyar yau da ta shiga kitchen ta samu Mom na decorating wani chocolate cake, sai ƙanshi ya ke yi.
"Mom wa ke birthday?" Ta tambaya.
"Ya kamata a ci taran ki tunda ba ki san birthday ɗin waye gobe ba" Mom ta faɗa tana murmushi.
"Najdah?"
Mom ta girgiza kai, Farida ta leƙa cake ɗin ta ga shekarun da aka rubuta "wai-wai ashe na babban mutum ne"
Mom ta yi murmushi ta ce " he likes chocolate cake"
Farida ta ce "Ayya, cake ɗin ya yi kyau kuma"
"Akwai surprise family dinner da za ayi gobe da yamma. But dont tell him, idan ya sani ba zai zauna a gida ba"
"Allah ya kaimu gobe Mom"
....................
Safiyar asabat bayan ya iddar da sallah bacci ya koma. Haka kawai ta tsinci kan ta da kallon kyakykyawar fiskar sa, ta jima tana kallon sa, she cant believe he's 35yrs. Gaskiya jindaɗi da hutu na ɓoye shekarun mutum...
Da ta ɗan tattare ɗakin sai ta fita dan ta taimakawa su Adama da aiki.
Lokacin da ta dawo ɗakin kusan azahar ya riga ya fita. Ta buɗe akwatin kayan ta tana duba kayan da za ta sa. Mom ta ce iyalen gidan Uncle Sulaiman za su zo ga su Hajia Fatima, dole ta yi shigar da ba za a raina ta ba. Tana cikin duba wannan ta ajiye ta sake dubawa ta ajiye aka ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin,
Ta je ta buɗe ta ga Mom ne.
"Mom ki shigo"
Mom ta miƙa ma ta wani paper bag ta ce "ki sa wannan and please wear the dimond necklace"
Ta amshi bag ɗin tana ma ta godiya...
Ba ƙaramin kyau gown ɗin ciki ya ma ta ba tareda takalmi da purse wanda su ka shiga da kayan.
Ƙarfe huɗu ta fito bayan ta shirya cikin doguwar riga pink da Mom ta ba ta. Lokacin gidan an fara hayaniya, ta sauko ƙasa tana gaisawa da su Hajia Fatima...
Ya na gidan sa Dad ya kirashi akan maza-maza ya zo gida. Ya san ƙila surprise party su ka shirya ma sa. But he has no choice ba ya iya yiwa Dad mu su. Haka ya rufe gidan ya shiga mota ya dawo. Tundaga motoci da ya fara cin karo da su ya san hasashen sa ya tabbata.
Da sauri ya haura sama yana avoiding wata ƙaramar cousin ɗin sa 'yar shekara biyar da ke cewa ya ɗauketa.
Zuwa yai ya shirya a gurguje dan text ɗin Najdah da ya gani akan ya zo Garden su na jiran sa a wajen.
Komai sauri-sauri yai tun daga wanka zuwa sa kaya. Yana buɗe ƙofa ya gan ta a bakin ƙofa. Daga sama har ƙasa ya kalleta, she look beautiful, ga dimond necklace da ta sa da ya ƙara fito da ita.
"A ka ce na zo na kira ka"
*this page is total crap. Ba proofreading ba editting. Ga shi ɗan kucil, ga shi ya zo very late. Ku yi haƙuri i got a bit distracted saboda rasuwan Anty na kuma Oga na. Allah ya gafarta ma ta amin*
* a surprise page gobe for team Najeeb*
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣2️⃣7️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
*wannan labarin na kuɗi ne, dan Allah kar a fita da shi*
Da farko ya shagala da kallon ta amma tunda ya ƙyalla ido ya ga sarƙan da ke wuyan ta sai ya janye idon sa yana cewa "matsa na wuce"
"Sir Najeeb Happy birthday"
Bai amsa ba kawai wucewa ya yi. Ta bi bayansa tana cewa " Dan ma ka samu na wishing na ka Happy Birthday ɗin" yana takun sa na ƙasaita ta na bin sa a baya, da ke heel ta sa sai ya zama ba ta iya sauri ba sai ta ɗan sa gudu-gudu sauri.
Sai da su ka kusa isowa wajen sai ya tsaya, tana iso shi sai yafara tafiya a hankali ta yanda za su jera tare.
Su na shiga wajen aka sa tafi. Wani cikin cousins ɗin sa ya ce " ka ga salon soyayyar manya. Har ta tafiyar su iri ɗaya ce"
Najdah ta zo ta kama hannun Najeeb ta ma sa jagora zuwa inda zai zauna. Yana zama itama Farida ta zauna gefen sa.
"Happy Birthday babban yaya" Uncle Sulaiman ya faɗa yana kallon Najeeb da ke kujeran su na opposite.
Daddy ya ce " kar ka kumbura ma sa kai, wannan taron domin 'ya ta aka yi ba shi ba"
Najdah ta ɗauko cake ta kawo gaban sa. Ta kissing goshin sa ta ce " Happy birthday sweet Bro"
Murmushi yai sannan ya amshi wuƙar yanka cake ɗin ya sa zai yanka.
Aminu babban ɗan Uncle Sulaiman ya ce " ka yanka tareda amarya ma na mu san yanzu kam ka bar tuzuran ci"
Juyowa yai ya kalli Farida wanda itama shi ta ke kallo.
" he's right, 'yata help him cut the cake" Daddy ya faɗa yana kallon yadda Najeeb ya haɗa rai.
A hankali Farida ta ɗau hannun ta ta ɗaura akan na Najeeb. Ido ya ƙura ma ta ita ma cikin idon sa ta ke kallo. A. haka har wuƙar ya nitse cikin cake ɗin. Sai da aka fara tafi sannan su ka cire ido cikin na junan su.
Da ya yanka ma cewa aka yi Farida ta sa ma sa cake ɗin a baki bayan ta sa aka ce shima ya ba ta, relunctantly dai ya sa ma ta.
Ba a jima ba aka fara serving abinci ana yi ana taɗi ana dariya. Haɗa kujeru aka yi da table sai ya zama kaman a dogon table ake cin abinci. Sun jeru straight akan kujerun.
Anwar ɗan Hajia Fatima ya tashi ya ce " aga aga?"
Aka amsa ma sa da aga
"Aga waye yai aure @35yrs?"
Aka nuna Najeeb.
Aminu ya tashi "Aga Aga" aka amsa da aga
"Aga waye yai ƙwacen mata?"
Aka nuna Najeeb, wassu na dariya ƙasa-ƙasa.
Wani kallo ya watsawa Aminun dan ya girmeshi kusan shekara shida amma shi ya yi aure harda yarinyar su ɗaya.
Aminu ya zauna yana dariya.
Anas ya tashi ya ce "aga aga?"
Da aka amsa ma sa ya ce "aga waye yai auren soyayya da sakatariyar sa?"
Wassu su ka nuna Najeeb wassu kuma wanda ba son auren Najeeb da Farida su ke ba, su ka fara hararan Farida, irin su Najdah da Afrah wanda tunda ta dawo daga weekend ta tarar da auren Najeeb ta tattara ta koma gidan Uncle Sulaiman.
"Barin nuna wani short video clip na wannan masoya, there first fight and probably there first love"
Idan da yadda Najeeb zai yi ya je ya make Anas a inda ya ke tsaye da ya je. Dan wani mugun kallo ya ka aika ma sa daga inda ya ke zaune.
Anas ya ɗaga Tab ɗin sa sama ya playing video ɗin. Video compilation ne na wajen da Farida ta fara zuwa aiki har ta hana Najeeb shiga office, da wajen da ya koreta ta ƙi tafiya har ta rungumeshi lokacin da ya kira security. Sai wajen da Najeeb ya zo ya zauna akan superglue. Tun a clip na farko aka fara dariya, Daddy har da tari tsabar dariya. Wassu da ke gefe su ka dawo wajen da za su ga video ɗin da kyau.
Lokacin da video ɗin ya ƙare Anas ya ce " Thanks to CCTV footage na kamfani mun samu wannan video na masoya mai cike da tarihi"
Najeeb ya rintse ido ya cize leɓen sa na ƙasa. Wannan embarrassment ɗin da me yai kama. A gaban su Daddy da ƙannen sa, dan duk wajen idan ka cire iyayen to ya girme mu su.
A lokacin aka fara cewa ya tashi ya duba kujeran da ya zauna ko akwai superglue a kai. Wa su kuma su na kwaikwayon maganar Farida su na "Sir Najeeb ya dai?"
Farida kam idon ta na ƙasa saboda ta ji kunya. Duk uban mutanen da ke wajen nan sun ga asirin ta.
Uncle Sulaiman yana dariya ya ce " kai gaskiya Alhaji ka iya matchmaking. Ka haɗa Najeeb da dai-dai da shi"
Aminu ya ce " ai yanzu da take gidan sa idan yai mata laifi da ruwan borkono zai yi tsarki"
Anwar cikin dariya ya ce " sai ya zama tsuliyar Big B is on fire kenan"
Gaba ɗaya wajen kowa dariya idan ka cire Najeeb da ya cika yai fam.
Farida ma da ta sunkuyar da kai ɗan dariyan ta yi...
Ana cin abinci ana sake gulman abinda aka gani. " Hajia Fatima har da cewa immediately Anas ya tura ma ta video za ta forwarding wa Najma da su Uncle Abubakar da ba sa nan...
Daddy ya ce " kar ku sa 'ya ta a gaba. Idan ɓera na sata to daddawa ma na wari"
Yadda hannun Najeeb ke shaking, Farida da ke gefen sa sai da ta tsorata. Ta leƙa ta ga hannun sa ɗaya da ya sa akan cinyar sa ya tamke shi kamar mai shirin kai dundu amma still hannun na rawa, ɗaya hannun da ya riƙe tsokali da shi kuwa yai wa sokalin riƙon makami ne.
Ana cin abinci amma Najeeb ba ya ci. Farida ma tunda aka playing video ɗin nan ta ka sa cigaba da cin abincin.
Lokaci guda hayaniyar da ake ta tsaya chak. Wanda su ke opposite da su Najeeb su su ka ga matar da ta doso wajen da ake taron ita da Adama da ke riƙe da tray za ta kawo wani nau'in abincin.
Jin shirun yai yawa kuma su Daddy sun ƙurawa mai zuwan ido ya sa wassu daga cikin wanda ke zaune layi ɗaya da Najeeb su ka juya, cikin su har da Aminu.
Muryan Aminun ne ya fitar da sunan wacce ta doso wajen cikin takun ta na ainihin celebrity, yadda ta ke catwalking kamar a kan redcarpet ta ke za ta je karɓan Oscar award.
*"SABREEN"* ya faɗa da sigar mamaki
Jin sunan ya sa sauran su ka juya duk da ma ba kowane a wajen ya san Sabreen ba, balle labarinta. Idan ka cire Najeeb da Farida duk sauran sun juya.
Najeeb na zaune, takaicin abinda Anas yai ya cika shi, chan ƙasan ran sa yana tsara irin yadda zai ciwa Anas mutunci idan su ka haɗu, ya ji muryan Aminu ta fitar da sunan da ya tsana a rayuwar sa*"Sabreen)*
Yadda wajen yai shiru ya sa yai tunanin ko dai Sabreen ɗin ne su ka gani ko kuma su na so su sake playing prank a kan sa da sunan Sabreen.
Sanye ta ke da wani arnen baƙin kaya. Gown ce wanda ta kamata ƙyamƙyam, sannan ya fidda duk wani sura na jikin ta. Hannu ɗaya dogo ne har zuwa wuyan hannun ta(wrist) ɗaya kuma hannun vest gareshi. Jikin rigan yana da adon duwatsu wanda sai kyalli su ke, ta ɗan yafa wani ƙaramin gyale wanda gyalen yadda ka san abin tata haka ya ke, shara-shara da shi, gyalen ma an ɗan yane shi ne kaɗan amma duk rabin gashin na ta na waje. Tana ɗauke da wani designer purse wanda aƙalla kuɗin sa a ƙiyasin kuɗin Naira zai kai miliyan huɗu. Murmushi ta ke har ta ƙaraso wajen.
"Hi everyone" ta faɗi tana ƙarasawa wajen Mom da itama ke daskare akan kujera tana mamakin zuwan Sabreen, dan ba ta da masaniya akan zuwan na tan.
Ta kissing kumatun Mom kamar yadda Larabawa su ka fiyi idan za su gaisa da mutum.
"Masa'ul Khair Ammaty" ta faɗa tana ƙara faɗaɗa murmushin ta tareda sauke idon ta akan Najeeb wanda tun zuwan ta wajen Mom idon sa ke kan ta.
"Happy Birthday Noory" ta faɗa tana gyara gashin ta da ya zubo ya ɗan rufe ma ta rabin fiska.
Najeeb ya miƙe tsaye ba tare da ya ce komai ba ya bar wajen. Yadda ya ke tafiya kawai ka san yana cikin ɓacin rai.
Da ƙyar Mom ta iya haɗa kalmomin bakin ta tambayi dalilin zuwan Sabreen Nigeria. Maimakon ta amsa ma ta sai ta tambayi Mom ɗin da cewa ko ba ta son ganin ta ne. Mom ta girgiza kai.
Hajia Fatima ne kaɗai a wajen ta iya cewa " 'yar burauba, kin ji yai aure za ki zo ki ɗaga ma sa hankali ko"
Ba ta ji mai Hajia Fatima ta ce ba amma ta san zagi ta yi.
"Let me talk to Noory" ta faɗa sannan ta kama hanya ta bar wajen still cikin takun ta na ƙasaita.
"Tashin hankali kenan, ana wata ga wata. Ke Aisha ki je ki hanata magana da mijin ki dan wannan yarinyar sheɗaniya ce"
Daddy yai ajiyar zuciya ya ce " 'ya ta ci abincin ki, ba komai"
Ala dole Farida ta fara cusa abinci a baki. Lokacin da Sabreen ta zo wajen Mom Farida ta gan ta sosai, lallai dole wannan mata ta girgiza rayuwar Najeeb. Farida ta raina kan ta a gaban wannan mata da Allah yai wa baiwar kyau haka...
......................
Yana zuwa ɗaki ya fara safa da marwa a ɗakin, miyasa lokaci guda abubuwa guda biyu su ka zo su ka haɗu ma sa. Ga abinda Anas yai ma sa which ya san 'yan familyn su wannan abun har bayan shekaru sai sun yi ta tsokanar sa da shi. Ga uwa uba Sabreen.
What did hell is she doing here? Ya tambayi kan sa.
8yrs, 2months and 11days da tafiyar ta. May be da ba ta gudu ba da su na rayuwa cikin jin daɗi da 'ya'yan su biyu ɗan shekara shida da 'yar shekara biyu, dan shekara huɗu su ka tsara za su bawa yaran na su rata (o'o ni Azizat🙄 Najeeb da Sabreen sarakunan tsari)
Sai dai komai ga rushe lokacin da ta gudu ta barshi da takaici.
Cikin shekaru takwas ya gina kan sa a matsayin CEO kuma Founder na babban kamfani. Yayinda Sabreen ta samu fitowa a fima-fimai 11 a cikin 8yrs. Ta dating Tom cruise ta dating wani ɗan ƙwallo, ta dating wani hamshaƙin mai kuɗi ɗan ƙasar Italy. Shi gashi bai dating kowa ba amma an kakaɓa ma sa sakatariyar sa.
Cikin shi da Sabreen ba zai iya cewa waya fi wani samun cigaba da kwanciyar hankali ba a shekaru takwas.
Yana cikin wannan bulayin Sabreen ta buɗe ƙofa ta shigo. Ƙaran tafiyar ta ya ji ya gane ita ce.
"What do you want?"
"Noory i'm sorry"
Wani dariyan takaici yai ya ce ma ta " in 8yrs 2 months 11days ba abinda za ki ce sai I'm sorry? For kin maida ni mahaukaci ko"
"Noory" ta faɗa tana matsowa kusa da shi
"Go back to Hollywood" ya faɗa da ƙarfi
"I'm here to stay Noory, for you, for us"
"You're Crazy Sabreen"
Kuka ta fara mi shi tana faɗin cewa tana son shi har yanzu kuma ba ta taɓa dena son shi ba. Rasa ma mi zai ce ma ta yai ya fice daga ɗakin ya barta. Ba zai iya tsayawa a gidan ba, not after all that happened.
Ranan dai wannan dinner ta zama wani iri, an dai ƙarasa da ƙyar, wanda su ka kawo gifts wa amarya da ango sun miƙa. Daddy da su Uncle Sulaiman sun jima suna tattaunawa gameda zuwan Sabreen kafin daga baya kowa ya watse.
Da ƙyar Farida ta kai kan ta ɗaki dan gaba ɗaya ta shiga wani yanayi na ruɗu. Sabreen ta dawo, macen da Sir Najeeb yai dakon rashinta har shekara takwas, macen da Anas ya ce ma ta ita Najeeb ya fara so kuma ya so ta so mai tsanani. Idan Sabreen ta dawo miye amfanin zamanta tareda Najeeb tabbas nan ba da jimawa ba zai sallameta ya auri Sabreen. Ta jima tana zaune akan gado tana tufka da warwara kafin daga baya ta tashi ta shiga banɗaki dan ta watsa ruwa...
Daddy yai ta kiran Najeeb amma ba ya shiga. Ya na son ma sa magana akan zuwan Sabreen dan ya san halin ɗan na sa. Daddy ba zai iya ƙin karɓan baƙuncin Sabreen ba saboda kamar 'ya ta ke a wajen matar sa.
Najeeb gidan sa ya je ya kashe wayoyin sa ya kwanta, ba wai bacci ya ke ba, ya kwanta ne yana tuno abubuwa dayawa da su ka faru musamman soyayyar sa da Sabreen. He gave her all his heart, he loved her with every beat of his heart. Ya ma ta alƙawarin samun rayuwa mai kama da aljannar duniya idan u ka yi aure amma...
Ranan bai koma gida ba dan ba ya son sake ganin Sabreen saboda yadda ya ke ji a zuciyar sa. Farida kam bacci ƙaurace ma ta yai. Makomarta ta ke nema a wannan lamari, idan tana ganin za ta iya samun soyayyar Najeeb to yanzu kam chances ɗin ta ya bouncing back to zero.
*Sabreen* ta maimaita sunan a karo na ba adadi...
.................
Washegari Lahdi Farida ba ta tako ko ƙofar ɗaki ba, a ɗaki ta wuni Adama ce ta ke kawo ma ta abinci har ɗaki, wanda abincin ɗan tsakura kawai ta ke iya yi. Rashin kwanan Najeeb a gida ya tabbatar ma ta nata zancen ya kaɗe domin ta san yana chan yana kitsa yadda zai yi aure na gani na faɗa shi da Sabreen.
Ga mamakin ta ƙarfe tara na dare sai ga shi ya shigo ɗakin, bai ce ma ta komai ba ya je yai wanka ya shirya cikin ɓakin pyjamas na shi ya kwanta.
Daga inda ta ke zaune ta ce "Sir Najeeb miye matsayi na yanzu?"
Bai kulata ba, shi idan ba dan Daddy ya ce lallai ya dawo gida ba da bai san ranan da zai dawo nan ba. He feels empty.
"Sir Najeeb magana na ke"
"Oh please Aysherh" ya faɗa ba tareda ya realising da sunan ta ya kira ta ba
Jin sunan ta for the first time a bakin sa sai ta tsaya ta na jin yadda sunan ke ringing a ƙwaƙwalwarta *Aysherh Aysherh Aysherh*
Ringing ɗin wayar ta ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, ta yi saurin zuwa ta ɗauki wayan sai ta ga Sister Munibat. Ta ɗauki wayan su ka gaisa, jin muryan ta kaman tana kuka ya sa ta tambaya ko lafiya. Sister Munibat ta sanar da ita mahaifinta ne ya rasu ta gayawa Sir Najeeb ba za ta zo aiki ba ta ɗau hutun sati ɗaya.
"Allah ya jiƙan sa, kar ki damu Sister zan faɗa ma sa. Daga satin nan ma za a shiga hutun ƙarshen shekara so kar ki damu. Allah ya ma sa rahama"
Da ta gama wayar ta fara gayawa Najeeb ko ya ji ta ko bai jita ba oho, dan bai amsa ba.
....................
Yau ma Mom ce ta kaita wajen aiki dan Najeeb tun ƙarfe shida ya fita. Su na tafiya tana ba ta haƙurin zuwan Sabreen tareda ma ta alkawarin duk yadda za ayi sai ta sa Sabreen ta koma inda ta fito.
Farida ta tambayeta ko miya sa ta ke supporting ɗin ta ba Sabreen ba. Mom ta ce "saboda Sabreen is his past, ke ce present and future ɗin sa" da wannan ya sa Farida ta ɗan ji sanyi a ranta...
Tana aiki a laptop Sabreen ta shigo office ɗin ta still cikin shiga mai ɗaukan hankali.
Cewa ta yi za ta ga Noory. Farida ta haɗe fuska tana jin haushin sunan da Sabreen ke kiran Najeeb da shi.
"Sabreen ki ke ko Siren ne?Najeeb zaujy, Ana Zaujy Najeeb" ta faɗa tana nuna kan ta.
Sabreen ta kwashe da dariya saboda shirmen larabcin da Farida ta yi. Ta san da zancen auren Najeeb kuma ta san wanda ya aura, but seeing Farida ya sa ta ƙara yarda Najeeb ba auren son ran sa yai ba, saboda Farida ba ta dace da irin matan da Najeeb zai so ba balle har yai tunanin yin rayuwa da su.
"Fuck off girl, i have his heart"
Tana faɗin haka ta shige office ɗin Najeeb.
"Shegiya karuwa" Farida ta faɗa tana tsaki...
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
0 comments:
Post a Comment