Tana fita daga office ɗin Sir Najeeb office ɗin Anas ta wuce. Ta sameshi ya yi wani jugum da shi. Tabbas abinda Najeeb ya ma sa ya mugun kashe ma sa jiki.
Ajiye flash ɗin ta yi a gaban sa ta ce "Yaya na ga shi ka je ka yi presentation ɗin"
"Roƙonsa ki ka yi? Ko kawai ɗaukowa ki ka yi?"
"Ko ɗaya, Yaya na shi da kan sa ya bani ya ce na kawo ma"
"Ban yarda ba, Najeeb ba ya chanja magana da wuri. Kar ki damu ƙanwata, Najeeb shi ke da kamfani yana da ikon hana ni ko ya sa na yi abu"
"Ya Anas da gaske na ke fa, idan ba ka yarda ba ka zo muje ka tambayeshi"
Da farko dai Anas bai amince ba daga baya da ta takura sai ya tashi su ka fita, har lokacin dariyan Najeeb na cinta.
A ɓangaren Najeeb kuwa yayi nasarar raba jikin sa da kujeran amma kamar yadda Farida ta faɗi sai da wandon shi ta farke, wasu daga cikin pattern na wandon suna manne da gum ɗin a jikin kujera, wandon ya koma har ana ɗan ganin boxers na shi.
Najdah ya kira akan ta kawo ma sa kaya daga gida, ta ce ma sa tana school ai kuwa ya fara babbaleta da masifa abinda bai saba yi ma ta ba, idan ba masifa akan Mom ba, normally ba ya taɓa ɗaga ma ta muryarsa. Ganin yadda ya ke faɗa ya sa ta san lallai akwai matsala, dole haka ta bar class ta wuce gida.
Yana ajiye wayar sai ga Anas da Farida sun shigo, yai saurin komawa ya zauna akan kujeran dan kar Farida ko Anas ɗin su ga yadda bayan wandon sa ya koma a rarike.
"Sir Najeeb ina kai ka ce Ya Anas ya je yai presentation ko?"
Sai da ya ma ta kallon banza sannan ya kalli Anas ya ce " ka je ka yi pitch ɗin nan, its already time"
Anas da mamaki ya ce " miyasa ka chanja ra'ayin ka?"
"Oh please, just go"
"Ya Anas, Sir Najeeb ba shi da ja fa, kai ɗin ne dai za ka yi presentation ɗin"
Anas yai shiru yana nazarin Najeeb, akwai ɓacin rai mai tsanani a tattare da shi amma yanzu bai da halin tambaya saboda chanjawar da abokin sa yai. Ya karɓi flash ɗin daga hannun Farida ya juya. Farida ta bi bayan sa tana gwada irin tafiyar Najeeb. Sai da su ka kai bakin ƙofa ta juyo ta ce " Sir Najeeb asha zaman kujera lafiya" sannan ta sa dariya.
Bayan fitan su da kusan minti arba'in Najdah ta zo mi shi da wasu kaya daga gida.
" Big B mi ya faru ka ke ta min tsawa ɗazu?"
"I'm sorry baby, i was just pissed off ne"
"Barin koma school muna da class"
Ok kawai ya ce ya jira sai da ta fita daga office ɗin sannan ya wuce banɗaki ya chanja kaya.
Lokacin da ya ga wandon wani haushin Farida ne ya zo ma sa har wuya. He's 100% sure ita ta sa wannan abun a wajen, kuma ta yi ne domin ta hanashi presentation ɗin nan.
"All because of Anas" ya furta a fili.
Ya kalli kan sa a madubin banɗakin ya ce " Did she really love him?"
Wanni ɓangare na zuciyar sa yana cewa miya shafeka idan tana son Anas, wani ɓangare kuma na cewa bai dace su yi soyayya ba, Anas is a good person amma wannan Ayshern, bai san ma ya zai kwatantata ba.
Shi dai abinda ya barwa ran sa shine dole ne ya hukuntata. Ya rasa miyasa ya ke kasa aiwatar da komai a kanta despite the fact cewa ta raina shi kuma tana karya dokokin sa son ran ta....
Najdah daga office ɗin Najeeb sai ta wuce office ɗin Anas. So ta ke ta sake tambayarsa ko da gaske ne yana son Farida, domin ranan ba ta barshi yai magana ba ta kashe wayar.
Ganin baya office ya sa ta yi yunƙurin tafiya idan ya so sa haɗu daga baya, sai hankalinta ya je kan wani hoton sa da ke kan table. Ta ɗauka hoton ta ƙura ma sa ido. A cikin tarihin rayuwarta tana son baƙin namiji, ita baƙin mutum na burgeta. Farar fata gareta amma many a times tana envying skin ɗin baƙaƙen mutane. Tun tana ƙarama ta san Anas, lokacin idan sun zo hutu Nigeria, su na tare koyaushe saboda tafi kowa kusa da Najeeb shi kuma shine kaɗai abokin Najeeb. Wani lokacin ko da Najeeb bai zo hutu ba to kullum tana tareda Anas, wannan ya sa ta shaƙu da shi tun a yarintar ta, shekaru uku da su ka wuce kuma ta fara jin wasu baƙin lamura game da shi wanda ita kan ta ba za ta iya fassara su ba. Ta ɗan shafa hoton sannan ta ajiyeshi.
Tana fitowa ta yi kiciɓus da Anas da Farida, da alama office ɗin na sa za su shiga amma maganar da su ke yi ya sa su ka tsaya a wajen. Dariya Anas ke yi sosai harda riƙe ciki. "Farida you are too much wallahi, abinda ki ka yiwa Najeeb kenan"
Doguwar tsaki Najdah ta ja wanda ya ja hankalin su.
"Najdah" Anas ya faɗa lokacin da ya juyo ya kalleta.
"An dai ji kunya" ta faɗa sannan ta bar wajen. Da sauri Anas ya bi bayanta yana kiran sunan ta.
Ta shiga lifter amma kafin ƙofar ta rufe Anas yai saurin sa hannu ya tare sannan ya shiga lifter ɗin shi ma.
"Najdah wai miya faru ne?"
"Dont pretend kamar ba ka san abinda ya faru ba. Sakatariyar Big B fa ka ke so. Sakatariyar sa"
A wannan dama da Allah ya bashi yau, dole ya cire tsoro kamar yadda Farida ta ce.
A hankali ya furta " to miye a ciki? Ita sakatariyar Najeeb ba mutum ba ce?"
Wannan karan kaman za ta yi kuka ta ce "Yaya yanzu duk faɗin garin nan ka rasa wanda za ka so sai ita, that cheap girl"
Ƙwarai ya gane kishi ta ke amma bashida 100% assurance cewa kishin sa ta ke, sai dai dole ne ya tabbatar wa kan sa domin shi ta ke kishin.
"Najdah wa ki ke so na so? Wa ki ke ga zai so ɗan Maigadi"
"Yaya you know we love you, ka riga ka zama ɗan uwan mu yanzu"
Matsowa yai kusa da ita ya riƙe hannunta ɗaya ya ce "so idan ɗan Maigadi ya nemi 'yar masu gida za ta amince?"
Jikinta yai sanyi haka nan kuma kusancin su da hannunta da ya riƙe ya sa ta fara jin wani baƙon yanayi ajikinta, zuciyarta na bugawa da sauri-sauri.
Zuciyar sa ce ta ce 'Anas is now or never'
A hankali ya kai bakin sa dai-dai kunnenta ya ce "i love you Najdah, only you"
Maganar yai dai-dai da tsayuwar lifter dan haka ta wafce hannunta ta fita da gudu. Bai bita ba, sai ma murmushi da ya fara yi saboda jarumta da yai yau, finally he said it...
Farida na zuwa office ɗin Najeeb ta tadda ya chanja kaya.
"Manyan mutane kenan, Allah ya ja zamanin ka CEO"
Fiskar nan ba fara'a ko kaɗan ya ɗago ya kalleta ya ce "your two weeks suspension starts now, Miss Salihu"
"Suspension"
Sai kuma ta yi shiru.
"Two weeks suspension is not all, bayan kin dawo za ki serving punishment na ki"
"Hutarere wallahi. Hutun sati biyu ai gaba ta kaini, ka ga zan fara azumi a gida kenan dan Jos zan wuce. Na gode Sir Najeeb Allah ya ƙara daraja"
"Leave" ya faɗi da ƙarfi
"Sir Najeeb ina da magana" ba ta jira ya ce komai ba ta ce "tsakani da Allah abinda ka yiwa Ya Anas bai dace ba, ka san yadda mutumin nan ke ganin girma da darajarka amma ka walaƙantashi. Irin walaƙancin kun nan na ma su kuɗi ya sa ya kasa furtawa ƙanwar ka kalmar so, kaima kuma da ke ba ka damu da shi ba, sai ba ka gano son da ya ke yiwa ƙanwar ka ba"
Ɗago ido yai yana mamakin maganganun ta.
"A rage girman kai Sir Najeeb. Shi girman kai rawanin tsiya ne"...
Bai san lokacin da ta fita daga office ɗin ba saboda ƙwaƙwalwarsa da ta tafi duniyar tunani.
Anas na son Najdah, how when,why?. Kenan ba Aysherh ya ke so ba?
Da sauri ya miƙe ya bar office ɗin...
Wasu takardu Anas ke dubawa lokacin da Najeeb ya shigo, da ka gan shi ka san yana cikin farin ciki.
"You love my sister?" Ya tambayeshi lokacin da ya shigo.
"Najeeb..."
"Idan har kana son Najdah, why Miss Salihu again"
Dariya yai ya ce "tsaya Najeeb, waya gaya ma ka akwai abu tsakanina da Farida? I love your sister, ita kaɗai na ke so"
Ɗan ƙaramin tsaki ya ja sannan ya bar office ɗin.
Nan zuciyar Anas ta ɗauko kan zan cen.
"Najeeb kishi ya ke da ni. Haba, dole biri yai kama da mutum ai. I suspected this tuntuni, Najeeb is inlove"
Murmushi ya biyo bayan maganar da yai wa kan sa, duk wani abinda Najeeb ɗin ya ma sa sai ya ga ya washe ko kaɗan baya jin haushin sa. The fact that Najeeb has feelings for someone else bayan Sabreen ai abun farin ciki ne. After 8yrs of loneliness.
Cikin kwana biyun nan abubuwa sun chanja. Najeeb ya koma yana jin kunyar Anas saboda abinda ya ma sa duk da kuwa Anas ɗin ya nuna komai ya wuce. Shi kan sa Najeeb ba zai iya faɗan dalili ɗaya da ya sa yai ma sa haka ba domin haushinsa ya ke for no reason amma kuma yanzu ya washe.
"Yau zan fara zuwa hira officially, sirikina ka gaya min tips wanni irin kaya Najdah ta fiso namiji ya sa"
Najeeb ya dundeshi ya ce "ɗan iska, ta fi son gwanjo"
Kalmar gwanjo da ya faɗi ya sa sunan Aysherh ya zo ma sa, kwana uku kenan da ba ta nan.
" abokina dan Allah kar ka manta a shigemin gaba wajen Daddy"
"Fuck you, Daddyn ne sai ni ne zan ma sa magana, kai ma ai ɗan sa ne you can talk to him about it"
"Ni ba marar kunya bane irinka ai"...
Anas na fita daga office ɗin sa ya tura wa Farida text akan an janye suspension ɗin ta resuming aiki gobe. Lokacin da text ɗin ya shigo Farida na bacci so ba ta gani ba.
Shigowar Khalidah office ɗin ne ya sa shi deleting ɗin text ɗin da ya ke shirin tura wa Farida ta ɗaya layinsa.
"Kwana na biyu da dawowa banga sakatariyar ka 'yar gold ba. Ko ka koreta ne?"
" get out"
"Maida wuƙar Najeeb. Na zo maganar project da ake yi a Kaduna ne"
Ya nuna ma ta kujera akan ta zauna...
Farida na ganin text ɗin Najeeb ta yi tsaki ta tura ma sa reply kamar haka
*Sir Najeeb ni ba zan dawo ba sai sati biyu sun cika, kana gani za a fara azumi nanda kwana biyu ka ce na dawo, gaskiya sorry*
Lokacin da ya gama karanta text ɗin yai ƙaramar tsaki.
...................
Sati biyun dai ba ta yi shi ba, sati ɗaya ta yi ta dawo saboda yadda Anas da Yakubu su ka takura akan ta dawo.
Duk da an rage awa ɗaya cikin lokacin aiki, hakan bai sa ta jin haushin aikin ba yanzu saboda watan azumi da aka shiga.
8-3pm ba wasa ba ne a wajen Farida ga ɗan karen zafi da ake yi a garin na Kano, ga ruwan sama ma dai har lokacin da azumi ya kai goma ba wani alamunsa sosai dan sau ɗaya aka yi ruwa. Daga ƙarfe shabiyu za ka ga Farida ta yi laushi. Da ƙyar ta ke kaiwa lokacin tashi.
Yau ma wani aikin da za ta yi Najeeb ke ma ta bayani.
Burping ta fara yi akai akai har sai da Najeeb ya fusata ya ce " Miss Salihu will stop sounding like a frog"
(Burping kaman ƙwanafi kenan, ban san Hausa word na shi ba. Irin dai abinda ma su ulcer su ke yi ɗin nan ko kuma idan mutum ya cika cikinsa da abinci dayawa za ka ga daga maƙoƙoron ka kana fitar da sautin irgh irgh irgh )
"Sir Najeeb ba fa da gangan na ke ba, ulcer na ne ya tashi..." ba ta ƙare maganan ba ta kuma yi ya ce "Gosh! Miss Salihu get out"
Ba ta musa ba ta fita dan dama a gajiye ta ke...
Ya dawo daga sallar Azahar ya shiga office ɗin sa sai ya ji ƙanshin abinci. Abinci in his office a watan Ramadan? Ya juya inda ya ke jin ƙaran sokali and there he sees her. Ta barraje a ƙasa tana cin jollof ɗin taliya da macaroni.
"Since when did my office become your dining room?"
Ɗago ido ta yi ta kalleshi hannunta ɗauke da sokali totse da abinci.
"Ni ban ɗauka za ka dawo yanzu ba"
"Miss Salihu"
"Dan Allah Sir Najeeb ka barni, ka ga office ɗina kowa na shigowa ƙarangatsau, na ka office ɗin akwai privacy"
Zuwa yai ya zauna bai ƙara cewa komai ba. Lokaci zuwa lokaci yana ɗaga ido ya kalleta. Shi mamakin yadda ta ke cin uban abincin nan ya ke. Ko za a matse shi ba zai iya cinye abincin nan ba amma ita ya san zuwa anjima kaɗan za ta take shi.
Wata rana ana azumi goman ƙarshe, ranan anyi tsananin rana. Ƙarfe biyun rana sun je wani site Farida tana tsaye tana jin maganganun su har ta koma ba ta jin komai sai yijib ta faɗi ta suma. Najeeb da mutanen da ke wajen su ka yi kan ta.
Wanni Emmanuel na shirin kai hannu zai taɓa ta Najeeb ya daka mi shi tsawa "dont touch her"....
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣1️⃣7️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
Bayan ta farfaɗo ya sa aka kawo ma ta ruwa, maltina da madara akan ta karya azumi.
"Kai za ka biyamin ai idan na karya" abinda ta faɗa kenan lokacin da ya miƙa ma ta maltinan.
Ranan daga wajen ma ya maida ita gida ba tareda sun koma kamfani ba.
Haka dai a dararance ta cigaba da azumi har aka ƙare. Ana gobe Sallah aka ba su hutun kwana uku akan rana ta ukun sallah za a dawo. Farida kam cewa ta yi ba ta san zance ba sati ɗaya za ta yi. Ta wuce Jos ta yi sallan ta achan, duk da Kano za ta ga hawan sallah amma wannan baya gaban ta ta fiso ta ji ta jikin Umminta. Ƙila ma daga wannan sallah ita da sallah a Jos sai ta Allah.
.................
Lagos
Sati uku Maijiddah da angonta su na kwasan amarci, ba ta da matsala dan yaransa ba ma su hayaniya sosai bane.
Iya Bose ke mu su girki, amma tana kwana uku da zuwa ta fara shiga kitchen tana taya Iya Bose sarrafa abinci duk da kuwa Iya Bosen ba ƙarya ta iya girki sosai. A wajen ta ta san favourite na mijinta ta kuma koyi yadda ake sarrafa su. Shi ba bayarabe ba amma yana son cin amala da sakwara, dan haka ta dage tana koyon su a wajen Iya Bose. Miya kam ta ga ikon Allah, domin ita dai a gidan su idan ba kuka, kuɓewa, ko alayyaho ba to ba wani special miya da ake yi. Akan yi miyar egusi wani lokacin saboda Baffa na so amma a wajen Iya Bose sai ta ga miyar egusin ma ba kala ɗaya ba ce. Haka ta dinga ɗaukan darasin girki a wajen 'yar tsohuwar matar nan.
Daren Jumma'a da ya cika sati uku da auren su sai ga Aneesa ta zo.
Suna zaune su na kallo da yara a falo ta shigo, yaran suna ganinta su ka fara ihun mommy mommy.
A hankali Maijiddah ta fara satan kallon Aneesan duk da kuwa ta taɓa ganin hoton ta, amma ganinta a fili sai ta ga ta ƙara zama ma ta wata Madam. A ƙalla Aneesa za ta kai 36yrs ko 37yrs, amma jin daɗi da kuma samun mayuka ma su tsada sai ya ɓoye shekarun ta.
Sai da ta raba su Baby da Alizah a jikinta sannan ta kalli inda Maijiddah ke zaune sanye da doguwar riga ta atampa ɗinkin ya amshi ɗan jikinta ɗas-ɗas da ita.
Sai da Aneesa ta ƙare ma ta kallo sannan ta ja tsaki ta ce "ashe househelp Sweetheart ya kawo min"
"Sannu da zuwa" Maijiddah ta ce da ita.
"Nonye, Nonye" Aneesa ta fara ƙwalla sunan nannyn su Alizah.
Matar ta fito da sauri.
"Welcome ma"
"Je ki gyara min ɗakin Seeetheart, na san by now it most be stinking of filth"
Nonye ta haura sama ɗakin AbdulWahab. Dama ita ke gyarawa sai dai zuwan Maijiddan ne ta hanata ta ce ta dinga gyara ɗakin yaran kawai da sauran wajen.
Kallon kirki Maijiddah ba ta samu daga wajen Aneesa ba. Aneesa ta haura sama don ta je ta shirya kafin AbdulWahab ya dawo.
Maijiddah kam sai duk jikinta yai sanyi. Tsoron Aneesan ne ya kamata ganin wannan kallo da ta ke ma ta. Ta na da ƙuruciya amma Aneesa ta fita wayewa da komai. Ba za ta iya haɗa kan ta da ita ba.
Ƙarfe tara saura sai ga AbdulWahab ya dawo daga office. Yaran su ka fara sanar da shi gameda zuwan Aneesa. Bai yi mamaki ba dan rabon sa da magana da ita tun ranan da aka ɗaura aurensa da Maijiddah.
Maijiddah ba ta yi yunkurin raka shi ɗaki ba kamar yadda ta saba tunda Aneesa ta dawo.
Ɗakin sa ya je ya cire kaya ya watsa ruwa sannan ya fito bayan ya sa kayan gida.
"Hauwerh yau na yi laifi ne ko ya hanya ba a min ba?"
Rasa mi za ta ce ma sa ta yi dan gaba ɗaya zuwan Aneesa ya birkita ma ta lissafi.
Sai da ya zauna sannan ta fara serving na shi dama yara sun riga sun ci abinci, ita ɗin ma saboda zuwan Aneesa ta ci abincin tareda yaran dan ba ta son hayaniya.
Da ta gama ta juya za ta tafi ya riƙe hannunta " gimbiya ta zauna"
Ba ta musa ba ta zauna amma hankalinta ba a kwance ya ke ba. Ƙanshin turarukan Aneesa shi ya sanar da su isowanta falon. Irin kayayyakin da Farida ta bata a matsayin gudunmawa, irin sa ke jikin Aneesa yanzu. Wata arniyan riga ce ta saka wanda ya tsaya ma ta iya rabin cinyar ta, rigan ba ta da hannu, rabin nonuwan ta a waje. Tana catwalking har ta iso wajen su.
Kai tsaye ta mannawa AbdulWahab kiss a kumatu tana faɗin " Sweetheart sannu da zuwa. Shine har ka fara cin abincin ban da ni"
Da ƙyar Maijiddah ta sauke wani wahallen numfashi sannan ta tashi ta bar wajen. Ashe rashin ganin Aneesa a kusa ne ya sa take ganin kaman ita ba ta da kishi.
Kai tsaye ɗakin ta ta wuce ta ja ƙofa ta sa key. Maimakon bacci ya ɗauketa kamar yadda ta so sai bacci ya ma ta ƙaura. Ta ga yadda idon AbdulWahab ya chanja lokacin da ya ga Aneesa, to irin wannan shiga ai ko ita da ta ke mace ma ta yaba. Sai dai anya ita Maijiddah za ta iya saka irin waɗannan kaya kamar yadda Farida ta yi ta ja ma ta kunne?...
...............
Satin da Farida ta ce za ta yi shi ta yi duk da kuwa Yakubu ya kira ya ce Sir Najeeb ya yi faɗa akan wanda su ka ƙara hutu. Ita kam ba damuwarta ba ne.
Ranan da ta resuming aiki Najeeb bai yi faɗa ba, kodan ta ga kamar hankalinsa na kan wani aiki da aka damƙawa kamfanin na su satin da ba ta nan. Sati biyu bayan sallah aka kawo sadakin Farida sannan aka sa rana uku ga watan december wanda yai dai-dai da wata uku ma su zuwa.
Farida ta so Baffa ya sa bikin irin wata biyar ɗin nan, dan ta samu ta haɗa wasu kuɗaɗe wanda za ta yi hidiman biki da su.
Sai da aka tashi daga aiki ta shigo office ɗin sa, lokacin ma shi duba wasu zane da aka submitting ma sa ya ke.
"Sir ga goron sa ranan aurena da akayi, na kawo ma"
Ɗago ido yai ya ga baƙar ledar da ta ajiye akan table.
Ƙura ma ta ido yai yana son gano wani abu a tattare da ita. She was excited as she talked to him.
"Sir idan ka ɗan ƙara haƙuri da ni, nan da wata uku zan bar aiki da kai"
Still bai ce komai ba
"Ka san anguwan da zan zauna ɗan karan nisa ne da kamfanin nan, ga kuma aikin ku 8am-4pm. Ina matan aure kam ba zan iya ba"
Duk maganganunta ba wanda ya tanka a ciki a dole da ta ga ba shi da niyyan yin magana ta haƙura ta ce "Sir Najeeb tunda ko fatan alkhairi ba za ka min ba. Sai da safe" ta gyara zaman jakarta ta fita daga office ɗin.
Certainly Anas ya ce ma sa Farida is engaged tuntuni, amma shi bai ɗauki abin serious ba. Tukunna ma wani mahaukacin za ta aura da zai iya zama da ita. Ya kalli ledar da ta ajiye ya ji wani takaici ya shigeshi. Haka kawai ya tashi ya ɗau ledar ya je ya jefa a dustbin da ya gama ya shiga banɗaki ya wanke hannun sa. Da ya dawo ya zauna, ran sa ya riga ya dagule, aikin da ya ke son yi ma kasa yi yai dole sai tattarawa yai ya bar office ɗin shima.
.........
Its like tunda Farida ta yi maganan sa ranan ta sai Najeeb ya rasa kan sa. Mafiya lokuta idan Farida ta zo sai ya ji wanni haushin ta fiye da da, haka nan kuma ba shi da abinda zai ma ta. A da tana ɗan tsoron masifar sa amma yanzu kam kamar ma ta maida shi kakanta ne.
Yau ya dawo a gajiye ya tarar da Mom ta dawo. Kamar ko yaushe bai kulata ba, ita ne ta ma sa sannu da zuwa amma bai kula ta ba.
"Sabreen asked about you"
Tsayawa yai da tafiya ya juyo ya kalli mahaifiyar ta sa.
"Dont you dare, kar ki ƙara min maganar ta"
Juyawa yai ya wuce ɗakin sa. Yana cikin banɗaki ya kunna shower ruwa na zubo ma sa ya fara tuno rayuwar sa da Sabreen.
Sabreen ta kasance 'yar uwar sa ce, Mahaifinta da Mahaifiyar sa cousins ne. Ita ɗaya ce a wajen iyayen ta kuma mahaifinta yana da mahaukacin kuɗi. Shekara uku ya bata amma tun suna raya su ka shaƙu, duk lokacin da su ka je hutu ƙasar Bahrain to su na tare. Ko lokacin da ya ke fama da matsalar rasuwan Aisha, Sabreen ta kasance macen da ya ke son kasancewa da ita a wannan lokacin. Duk da alaƙarsa da Mom ya ruguje hakan bai hana shaƙuwar sa da Sabreen ya lalace ba. Shaƙuwa ce tun da ga yarinta ta girma ta zama soyayya. Saboda Najeeb Sabreen ta dawo America da zama wanda ya zamo musabbabin komai.
Sabreen tana da kyau kuma tana ji da kan ta. Bayan ta yi karatu a Newyork Film Academy ta nuna sha'awarta na acting film maimakon directing da ta ce za ta yi da farko. Sun riga sun tsara yadda rayuwar su za ta kasance idan sun yi aure. Matsayin mai bada umurni da ta ce za ta zama, Najeeb bai da ja akan haka, kuma tun kafin a sa ranan auren su ta riga ta fara aiki da Hollywood inda ta zama assistant director a wani romantic film da yai tashe a lokacin.
Shirye-shiryen biki ake yi wanda iyayen biyu ke ta sake kuɗi kamar ba su san wahalan neman sa ba. Mom a wannan lokaci tana so ta yi abin gwaninta ko Najeeb zai yafe ma ta amma kash abu bai yiwu ba.
Saura sati biyu a ɗaura aure Najeeb ya koma Bahrain saboda anan za a fara hidima kafin daga baya a wuce Dubai daga Dubai kuma a wuce Italy sannan a ƙare hidiman a Singapore.
Lokacin Najeeb yana ji da kan sa matashi ɗan shekara ashirin da bakwai. Sai dai kash! Saura kwana biyar a ɗaura aure Sabreen ta gudu bayan ta ajiye wasiƙa akan Najeeb yai haƙuri tana son sa amma ba ta shirya aure yanzu ba. Wannan shi ya ƙara birkitar da al'amarin Najeeb. Cikin ƙanƙanin lokaci ya lalace ya koma mara haƙuri mara fara'a kwata- kwata.
Wannan dalilin ne ya sa ya dawo Nigeria ya buɗe kamfanin sa, kuɗin da ya ke da shi da kuma aron kuɗi da ya ƙarɓa a wajen Daddy da su ya haɗa ya tada Najeeb constructions har ta zama abun da ta zama a yanzu. Shekaru bakwai kenan da su ka wuce ana cikin na takwas. Ba abin da ya ƙara ɗasawa Najeeb tsanar Sabreen irin bayan wata takwas da guduwa da ta yi sai ga shi an saki film ɗin da ta yi cikin turawa har tana kissing ɗin wani ƙaton kafiri a cikin film ɗin....
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣1️⃣8️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
Farida na zaune a office wani babban mutum ya shigo office ɗin. Cikin fara'a ta gaida shi saboda irin su ne idan sun zo wajen Najeeb su ke ba ta alkhairi idan za su tafi.
"Barka da zuwa ranka shi daɗe"
"Yawwa beauty, sannu da aiki"
"Wa za ace ya zo?"
"Alhaji Matawalle"
Ta ɗau phone ta kira Najeeb. Yana ɗauka ta gaya ma sa ga Alhaji Matawalle ya zo.
Tana ajiye wayar ta ce " ka shiga"
Sun ɗan gaisa kafin su ka fara tattaunawa kan abinda ya haɗa su. Kusan 30mins suna magana kafin su ka cimma matsaya ɗaya. Najeeb ya ƙarɓi takardun hannun Alhaji Matawalle yana dubawa kafin yai signing.
"Na ce ba, wannan sakatariyar kan nan..." bai ida maganar ba Najeeb ya ɗago ido ya ma sa wani kallo.
Maganar da Alhaji Matawalle ke son faɗa daban amma dole ya haɗiyeta ya buge da cewa
"matar aure ce?"
"Alhaji Matawalle ka zo waje na ne ko wajen sakatariya ta ka zo?"
"Kai Allah yarinyar nan tana da kyau ga fara'a ga...."
Najeeb ya ture takardun hannunsa gefe ya ce " idan ka shirya aiki da ni sai ka dawo"
"Haba Najeeb, wanni irin magana ne wannan?"
"Ka jini da kyau Alhaji Matawalle, now leave"
"Shashashan banza shashashan wofi. Har ni za ka kora a office ɗin ka. Za ka gani"
Alhaji Matawalle ya ɗau takardun ya fita fuuuu...
............
Ranan Jumma'a bayan an dawo daga sallar jumu'ah Najeeb ya kira ta.
"Ki shirya, za mu je Lagos ranan monday"
"Haba yallaɓai ai ko ni buhun gawayi ce iya ka ci. Haka kawai ka ce in shirya mu je Lagos ba tareda na san abinda za muyi ba"
Ya ɗan yi shiru na wasu daƙiƙai kafin ya ce " akwai 2days bid da za'ayi a Lagos and its important for this company"
"Zan tambayi Baffa, idan ya barni to idan bai barni ba shike nan sai ka je kai kaɗai ko ka ɗau wani ku je tare" daga haka ta fita daga office ɗin.
Da dare ta samu Baffa Musa da maganar amma ya ce ba za ta je ba.
"Baffa ni da Oga na ne fa"
"Ogan na ki mijin ki ne da za ki bi shi har Lagos da sunan aiki, ku je kuna kwanan hotel"
"Baffa daɗina da kai gidadanci"
Daƙuwa ya ma ta ya ce "zan ci uban ki Farida"
"Yo Baffa ai kai ne Uban nawa, sai ka ci kan ka, kawai"
Baffa ya taso zai mangareta ta fita daga falon da gudu tana dariya.
"Wannan yarinya wannan yarinya, Allah dai ya shirya min ke"
Baffa bai amince da tafiyar ba sai ranan Lahdi bayan ta ma sa alkawarin a gidan Maijiddah za ta kwana ba a hotel ba.
Ranan monday Najeeb da Farida su ka wuce airport da sassafe, wanda dreban Daddy ne ya kai su, ba su jima ba jirgin su ya lula sama.
Wannan karan ne farkon hawa jirgin Farida, ta dinga surutu tana cewa " dama ance albarkacin Kaza ƙadangare kan sha ruwan kasko, Sir Najeeb na gode Allah ya samu a damshin ku, irin wannan matsayi haka. Wa ya ga Aisha Farida ta shiga jirgi"
As usual bai tanka ma ta ba dan ba ya da abinda zai ce. The girl talks too much...
Kamar yadda aka tsara ɗin su na gama taron na ranan dreban gidan AbdulWahab ya zo ɗaukan ta.
Da za ta tafi ta ce "Sir Najeeb ka zo mu je a rage ma hanya"
Idon sa ne ya ba ta amsa ba baki ba. Ta san ma'anar Kallon na sa dan haka ta ce "Allah ya ba ka haƙuri, sai gobe"...
Gidan Maijiddah ya ma ta kyau ɗakuna shida ne a gidan. Uku a sama uku a ƙasa, ɗakin AbdulWahab Aneesa da kuma yara su ne a sama ita Maijiddah kuma na ta na ƙasa.
Saboda traffic ba su isa da wuri ba duk sai da ta gama gajiya kafin su ka iso.
Maijiddah a ɗakin ta ta sauketa, tana tsananin farin cikin ganin ta.
"Barin kawo miki abinci Anty Farida, kafin nan ki ɗan watsa ruwa, ga banɗakin" ta nuna ma ta ƙofar banɗakin da ke cikin ɗakin.
"O'o su Jiddah Amarya, muma dai za mu zo wajen"
Har Maijiddah ta kai bakin ƙofa ta ji Farida na salati. Ta juyo da sauri "Anty miya faru?"
"Jiddah ashe duk jan kunnen da na miki duk a banza. Dan Allah a ina kika samo wannan bujen kayan"
Maijiddah ta kalli kan ta, pakistan ta saka riga da wando amma wandon irin mai buje ɗin nan ne.
"Anty a cikin kayan lefe na ne"
"Ki na amarya auren wata biyu da 'yan kai, ki ɗauko wannan bujen wandon ki saka, dan Allah dan Annabi. Wallahi ko ni budurwa ba zan sa bujen wando haka ba balle ke matan aure, ga pakistan ma su pencil wanduna ba ki sa ba sai ki sa mai bujen wando. To maza ki cire kuma idan ba wai kin kai an shaping wandon ba kar ki ƙara saka kayan nan"
"Anty na ji, ki shiga ki yi wanka ina zuwa"...
'Yan kwana biyu da Farida ta yi a gidan Maijiddah ta sha faɗa kaman ba gobe, musamman da Jiddan ta ba ta labarin irin kayan da Aneesa ke sawa idan ta zo.
"Ke me ya hanaki sa irin kayan?"
"Anty Farida, a gaban yaran sa sai insa ƙananan kaya 'yan ficil-ficil ɗin nan. Idan uwar su ba ta da kunya ni inada shi"
"Lallai ke jaka ce Jiddah, dama ustazan nan yawancin ku sai a hankali. Wacce ayar ce ta hana ayiwa miji shiga ta ado da jan hankali"
"Anty Farida ba fa mukaɗai ba ne a gidan"
"Maza na shigowa ne?"
"A'a"
"To wallahi ki shirya zama boyi-boyi a gidan nan, very soon idan kin gama amarcin nan za a ajiye ki gefe saboda ƙauyanci da gidadanci da ya mi ki yawa"
Maganganun Farida shi ya ke ta yawo a ƙwaƙwalwarta lokacin da ta ke dudduba ƙananun kayan da Faridan ta ba ta lokacin auren ta.
Ranan laraba su Farida su ka tafi ita kuma Aneesa ta zo ranan Alhamis da dare. Duk cikin weekend ɗin nan a takure ta yi shi. Dama tsarin AbdulWahab ɗin ko na Aneesan ne ma oho, duk lokacin da Aneesa ta zo to yana ɗakinta har sai ta tafi, ita kuma sauran ranakun na ta ne.
Yau da safe Aneesa za ta koma Abuja. For once a rayuwarta tana so ta cire kunya da tsoro.
Ta tuno faɗan Farida lokacin da ta ce kunyan saka kayan ta ke ji.
"Shegiya kunya ya ƙare a abinda kukeyi da dare. Miye bai ganiba ajikin na ki da za ki dinga ɓoye ma sa"
Ta ɗauko micro mini skirt na blue denim jeans ta saka, cikin tops ɗin da Faridan ta haɗo da shi ta ɗauki wata fara wanda ta fi kama da vest amma V-neck gareta. Ta tsaya jikin madubi tana kallon kan ta, da ke guntuwa ce sai ƙananun kayan su ka amsheta sosai. Ta tufke gashinta da ta sawa ribbon ta nannaɗe shi kamar doughnut. Idan akwai abu ɗaya da ta san mijinta na so kuma ya ke ja ma sa hankali bai fi gashin ta ba. Dama Farida ta gaya ma ta kowanni namiji akwai abinda ya fi attracting na shi a jikin mace. Wa su ƙirji, wa su hips, wa su ƙafa wa su gashi da sauran su. To itakan ta san dogon gashin ta ne, AbdulWahab ba ya gajiya da shafa gashinta yana sa fiskarsa ciki yana shaƙar ƙanshin sa.
Takalmi mai ƙasan wedges ta saka dan ba ta iya tafiya da heel ba...
Su na cin breakfast a dining ta fito. Alizah ce ta fara hangota ta ce " Wow! Anty you look beautiful"
Ta ɗan yi murmushi ta ce "Thank you dear"
Sai da ta zauna Baby ta ce " i love your hair Anty"
Maijiddah ta yi murmushi, ta sa hannu tana wasa da gashin na ta ba tareda ta yi yunƙurin ɗiban abinci ba.
Normally idan Aneesa na nan ba ta zama ta ci abinci da su amma yau tana so ta rama abinda Aneesan ke ma ta ne.
Shi kam AbdulWahab tunda ya ɗaga ido ya kalleta bai iya saukewa ba. Sandwich da ya riƙe tuntuni shine bai sauke ba kuma bai ci ba. Sai da Aneesa ta yi magana sannan hankalin sa ya dawo jikin sa.
"Sweetheart za ka dropping ɗina a Airport ko?"
" No Anny, zan makara idan na kai ki"
Ta gama gane mijin na tan ya ɗan bircike akan Maijiddan. Ta san mijinta na son ya ga mace ta sa sexy ƙananan kaya, shi ya sa duk lokacin da ta zo ta ke sawa dan hankalin mijinta ya tsaya a kanta, sannan a tunanin ta Maijiddah ba za ta iya saka irin waɗannan kayan ba dan tun day one da ta ganta ta ke ma ta kallon local girl. Sai ga shi kuma yau ta proving na ta wrong.
Nonye ta zo ta tafi da yaran bayan sun karya saboda makaranta da za su je. Su ma su Aneesan sun gama karyawan amma ta ƙi tashi saboda AbdulWahab ya ƙi ya ƙare cin abincin.
"Sweetheart time fa ya tafi"
Ya ɗan yi gyaran murya ya ce "yanzu zan gama. Yau na tashi da muguwar yunwa ne"
"Namiji munafiki" Aneesa ta faɗi a zuciyarta. Ta san dalilin Maijiddah ya sa shi ka sa ƙarasa abincin akan lokaci.
Ala dole ya tashi saboda Aneesa da ta tsaya a kan sa. Tare su ka fita daga gidan amma minti shabiyar kacal sai ga AbdulWahab ya dawo. Maijiddah na kan tattare dining ɗin ta ji an rungumeta ta baya. "Princess yau ba kya so na je office ko?"
" Yaya ni a su wa, ka je Allah ya kiyaye hanya"
"Wasa ki ke yarinya, wani office kuma bayan ban gaisa da gimbiya ta ba" ya ɗauko wayansa ya ma ta hoto kafin nan ya ɗauketa cak su ka shige ɗakin ta wanda shine mafi kusa.
............
Wannan weekend ɗin ta je Jos kuma ba ƙaramin jin daɗi ta yi ba domin weekend ɗin ƙarshen wata ne, kaso mai tsoka ta ware cikin kuɗin ta ta tafi nemo sexy gwanjuna a kasuwa, tanaɗin biki takeyi tun kafin abin ya matso daf ta rasa lokacin zuwa Jos.
"Kin gaya ma sa kin taɓa aure?" Maganar da ta sa Farida ta ka sa kai lomar tuwon da ta yanko kenan.
"Ba na so a samu matsala kin san 'yan gulma, gara ki gaya ma sa tun kafin ya ji a waje"
"Ummi na ga ban tareba ai"
"Duk da haka, Farida ba na son a samu matsala a bikin ki irin na wancan karan. Gara duk wa ta ƙofa da zai kawo fitina a toshe ta tun kafin lokacin.
Da wannan zance ta koma Kano, zuciyar ta na tsoron abinda Rayyan zai ce idan ya ji wannan ba tu.
Sai da ta kwana biyu tana tunanin yadda za ta faɗa ma sa kafin daga baya ta yanke shawaran komai ta fanjama fanjam.
Tun kafin ya zo dama ta gaya ma sa tana da magana da shi. Dan haka da ya zo hira yau sama-sama su ka gaisa ya ce yana sauraron maganar ta.
"My Ray akwai abinda ya kamata ka sani gameda ni. It will come to you as a shock amma ka yi haƙuri"
"Ina jin ki"
"Na taɓa aure"
Ya zaro ido yana jiran ƙarin bayani.
"Yes, shekaru uku da su ka wuce an ɗaura aurena da Lukman, sai dai ko tarewa ban yi ba aka raba auren saboda matsalar da ta taso"...
Lokacin da ta gama bashi labarin Lukman yai shiru yana nazari daga ba ya ya ce " kin ga ke rabona ne, shi ya sa komai ya wargaje a lokacin"
Ta yi mamakin maganar sa dan ta ɗauka zai yi fushi saboda rashin gaya ma sa da ba ta yi ba da wuri.
*waye Lukman?*....
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣1️⃣9️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
Khairat Ilyas Magaji ta taso cikin gata da jin daɗi a gaban iyayen ta. Iyayen ta ita kaɗai su ka haifa wannan ya sa su ka ɗaura dukkan ƙaunan su a kan ta. Mahaifinta da Mahaifiyar ta dukkan su mutanen Kebbi state ne.
Tana ƙare secondary school mahaifinta ya turata karatu ƙasar South Africa inda anan ta haɗu da Lawrence su ka fara soyayya.
Lawrence Schneider asalinsa Bayahuden ƙasar Germany ne amma a South Africa aka haifeshi.
Rashin isashshiyar ilimi na addini,rashin tarbiya mai kyau da kuma son zuciya su suka sa Khairat ta sakamar Lawrence ragamar rayuwarta har ta koma ko Sallah ba ta yi saboda idan Lawrence ya ganta tanayi yana fushi da ita.
Gidan da iyayen ta su ka kama ma ta, ya koma tamkar gidan ta da na Lawrence, domin kusan koyaushe anan ya ke kwana. A wani hutun dogon zango da ta zo Nigeria, lokacin shekararta na uku kenan a makarantar ta fara rashin lafiya. Aka ma ta treating ɗin shi sai kwana biyu kuma zazzaɓin ya sake dawowa. Wannan karan da su ka je asibiti aka ma ta gwajin ciki, sai ga shi result ya fito tana ɗauke da cikin wata uku.
Alhaji Magaji da matar sa ba su shiga tashin hankali ba sai da Khairat ta ce ai cikin na Lawrence ne.
"A Jew! Khairat ba ma Christian ba Jew. Wanda sun fi kowa tsanar musulmai" Alhaji Magaji ya faɗa cikin masifa.
Sun yi ƙoƙarin zubar da cikin aka ce mu su akwai haɗari saboda Khairat ta jima tana shan maganin hana ɗaukan ciki kuma ya sa mahaifarta yai rauni.
Lokacin komawa makaranta yai Alhaji ya hana Khairat komawa. Shi da kan sa ya je har South Africa neman Lawrence. Abin takaici a gidan da ya kamawa Khairat anan ya samu Lawrence yana hutawa da wata baturiyar karuwar sa.
Ko da ya shaidawa Lawrence Khairat na ɗauke da cikin sa dariya yai ya ce "who wants to have a baby with a moslem whore"
Alhaji dan takaici bai san lokacin da ya mari Lawrence ba. Abu kamar wa sa sai ga shi an kama Alhaji Magaji saboda ya mari Lawrence. Kasancewar sa baƙar fata ya sa abun ya kuma sawa kotu ta ɗau tsauri akan al'amarin. A ƙalla Alhaji Magaji sai da yai wata kusan uku a ɗaure kafin aka fitar da shi nan ma bayan ya biya tara wa Lawrence.
Wannan ya ƙunsawa Alhaji da matarsa baƙin ciki. Itama Khairat ɗin tunda ta ji abinda Lawrence yai sai jikin ta yai sanyi.
Duk min lalacewar ɗa dai na ka ne. Haka Khairat ta raini cikin shegen ta a gidan su har lokacin da ta cika watannin haihuwa. Wata rana da tsakar dare ta tashi da naƙuda iyayen ta su ka kaita asibiti. Ta jima tana labour kafin ta haifi ɗa namiji.
Nurse ɗin da ta sanar da su haihuwar Khairat ita ta cikata maganar da cewa Allah ya yiwa Khairat rasuwa.
Bayan an yi bakwai ɗin Khairat Alhaji ya fara shirye-shiryen barin Kebbi saboda gulmace-gulmace da ake yi akan mutuwar Khairat.
Garin Jos Alhaji ya dawo da iyalin sa, inda su ka cigaba da rainon Lukman tamkar ɗan cikin su. Tarbiyan da ba su bawa Khairat ba, shi su ka duƙufa su na ba wa Lukman.
Lukman Ilyas Magaji ya taso cikin tarbiyya mai kyau, ga shi dama yaron mai biyayya ne. Tun yana shekara shahuɗu yai haddar ƙur'ani, yana da ilimi na boko da addini. Alhaji Magaji da Hajia Zainab su ya sani a matsayin iyayen sa har ya girma ya zama ƙwararren Likita.
Wata rana a asibitin Juth inda ya ke aiki aka kawo wata yarinyar cikin uniform mota ya bigeta. Wasu couples ne Mr and Mrs Owulum su ka kawota saboda su ne su ka bigeta da mota.
Yarinyar tun kan a fara duba ƙafarta ta fara ihu tana kuka tana faɗin Allah ya isa.
Lokacin da aka fara stitching kuwa tana kuka tana lissafta abinda Mr Owulum za su kawo.
"Wallahi Kaji goma za ku kawo, na gida biyar na Agric biyar. Kuma wallahi luƙa-luƙa dan ba na son ramammu"
Dr Lukman bai san lokacin da ya fara dariya ba. Ƙarin dariyan ma, Mr Owulum da matar sa ba sa jin Hausa. Ita kuma ta dage sai lissafo abubuwan da za a kawo ta ke yi.
Sai da a ka gama ya kalleta ya ce " Aisha duk lissafin nan fa ba su gane ko ɗaya ba, ba sa jin Hausa."
"Kan Uban chan! To wallahi chicken, 10 big chicken Mr Igbo man"
Lukman mi zai yi ban da dariya. Kafin su tafi da ita sai da Lukman ya kusa fitsari a jiki saboda dariya. Ko da ya je gida sai da ya bawa Mom da Dad labarin Aisha mai Kaji goma.
Washegari ma Mr Owulum ne ya kawota amma wannan karan har da Ummi da Nanna. Anan ya ke tambayar ta ko an kawo ma ta Kajin.
Ummi ta ce "ashe a gaban ka aka yi ko?"
Dr Lukman ya ce "na ga alama Aisha na son kaza"
Da za su tafi ya ce "Aisha Kaji nawa su ka kawo"
"Dan uban su shabiyu, shabiyu su ka kawo"
Dr Lukman yai murmushi.
Duk zuwan da za su yi sai Dr Lukman ya tabbatar shi ya duba ciwon Aisha. Bayan sati biyu da haɗuwar su wata ranan Jummu'a sai ga Dr Lukman a gidan su ya zo gaisheta. A wajen Mr Owulum ya samu
address ɗin ta.
Har cikin gida ya shigo ya gaida Baba da su Nanna da zai tafi Farida ta rakashi har wajen motar sa.
Ya shiga mota ya miƙo ma ta ledoji guda biyu.
"Dr green eyes har da wahala haka to an gode"
Dr green eyes ta ke ce mishi tun ranan da ta fara ganin shi, kasancewa ƙwayar idon sa green ne, wanda ya samo asali daga mahaifinsa Lawrenc.
A hankali Farida da Dr Lukman su ka shaƙu har soyayya ta shiga tsakani. Ko da ta zana WAEC da NECO Lukman ne ya ƙara ma ta ƙarfin gwiwa akan ta ci gaba da karatu. Da ba ta samu university ba ya ƙarfafa ma ta gwiwa akan kar ta zauna haka.
Lokacin da Farida ta ke aji biyu na diploma aka bayar da ita wa Lukman da zimmar tana ƙarewa za su yi aure.
Kowa ya san Alhaji Ilyas Magaji dattijon arziƙi ne, haka nan ɗan sa Lukman shima saurayi ne da aka ma sa shaida mai kyau a ko ina.
Rana ba ta ƙarya Farida ta gama diploma, aka fara shirye-shiryen bikin ta da Lukman.
A Wase za'ayi auren dan haka sati ɗaya kafin ɗaurin aure Farida ta koma chan. Mutanen Kano da Dukku duk sun hallara a wannan biki. Ba wanda ya fi jin daɗi ma kamar Baffa Musa saboda shi bai so har ta kai harka ba tareda an aurar da ita ba. Shi Mutum ne da bai yarda da karatun mace a gidan su ba.
Anyi kamu, anyi walima komai ya tafi lafiya. Ranan Asabat aka ɗaura auren Lukman Ilyas Magaji da Aisha Farida Salihu. Bayan an ɗaura aure ana ɗan gaggaisawa cikin 'yan uwan Alhaji Magaji da su ka zo daga Kebbi, wani ya fara magana da Alhaji Magaji bayan ya tabbatar a kusa da Baffa Musa su ke kuma maganar ta su ba a hankali su ke ba.
"Allah ya jiƙan Khairat, yau da kun ma ta tarbiya kaman yadda ku ka yiwa Lukman da Lukman bai zama ɗan shege ba"
Alhaji Magaji ya haɗe rai yana hararan ɗan uwan na sa wanda su ke 'yan uba.
Cikin rashin fahimta Baffa Musa ya ce " ban gane ba Alhaji Magaji. Wani irin ɗan shege?"
"au ba ku san Lukman ɗan shege ba ne? Lallai! Ai Lukman jikan Alhaji Ilyas ne, wadda 'yar sa ta haifa ma sa shi shege. Ance ma saurayin na ta ma wani bayahuden bature ne" Alhaji Kamalu yai wa Baffa Musa bayani.
Lokaci guda Baffa Musa ya hau faɗa yana masifa, kafin ka ce me wajen ɗaurin aure ya hautsine. Alhaji Magaji ba abin da ya ke sai hawaye.
Lukman na wajen masallaci su na hotuna da abokan sa aka zo ma sa da wannan mummunan labarin. Da farko bai yarda ba sai da ya shiga masallacin ya ga Alhaji Magaji yana hawaye. Shi kuma Alhaji Kamalu yana ƙara zuba bayani kan yadda Alhaji Magaji ya sakalta 'yar sa Khairat har ya kaita ga karuwanci a ƙasar waje.
Lukman dai a take a wajen ya suma.
Amarya Farida tana cikin ƙawayen ta ana hira ana ma ta kwalliya. Sai tsokanarta su ke wai yanzu kam an ɗaura aure ta zama Mrs Lukman Ilyas Magaji.
Wajen ƙarfe sha biyu ta gota kaɗan labarin abinda ke faruwa ya iso mu su gida.
Wassu cikin 'yan uwan su mata su ka fashe da kuka ana ta kururuwa ciki har da Inna Tabawa.
Wannan hayaniya ya sa Farida da ƙawayen ta su ka fito daga ɗaki su na tambayar abin da ke faruwa.
"Wai ashe Lukman ɗan shege ne" wata ta faɗa da ƙarfi.
"Ɗan shege kuma?" Farida ta faɗa cikin rashin fahimta.
"Wallahi, ance uban sa ma kafiri ne. Yanzu haka su Baffa Musa sun ce sai ya sake ki dan ba za ki auri ɗan sheg..." ta tsaya da maganan lokacin da Farida ta yafuto ta tana dukan ta ta ko'ina.
Da ƙyar aka raba Farida da matar nan. Farida sai zage-zage ta ke tana faɗin ita ko Lukman ɗan Alade ne za ta aure shi.
Gidan biki fa sai ya zama tamkar gidan makoki. Zuwa ƙarfe tara na dare kafin su Baffa Musa su ka dawo kowa so ya ke ya ji mi ake ciki amma Bai yi magana ba cewa yai kawai a fara haɗa kayan lefen da aka kawo da duk wani abu da aka san daga gidan su Lukman aka kawo.
Farida ta yi kuka kamar idon ta zai zazzago. Zuwa tsakar dare zazzaɓi ya rufeta a inda ta ke zaune ta fara kakkarwa, ƙarshe ta faɗi ta suma...
A ɓangaren Lukman ma ko da ya farfaɗo sai da ya sake suma sau uku. Zuwa yamma da jikin sa ya ɗan warware su Baffa Musa su ka zo gadon sa da buƙatar ya rubutawa Farida takardar saki, tareda cewa sun mayar ma sa da sadakin sa yana wajen Alhaji Kamalu tunda Alhaji Magaji ya ƙi ƙarɓa.
Lukman bai ce mu su ƙala ba sai hawaye kawai da ya ke ta yi.
Washe garin da wannan al'amari ya faru Baffa ya karɓo takardar sakin Farida wanda har lokacin tana kwance a asibiti.
Duk da 'yan uwan Lukman ba su buƙaci kayan da aka kaiwa Farida ba amma Baffa Musa sai da ya sa aka mayar mu su.
Wasa-wasa sai da Farida ta yi sati biyu a kwance a asibiti kafin aka sallamota. Tun daga nan ta koma kamar ba ita ba, ba ta surutu balle hayaniya. Kano Baffa Musa ya so ta bishi a lokacin amma ta ƙi, ta koma wajen Ummin ta a Jos.
Bayan wata ɗaya da dawowanta Jos, Lukman ya zo ya ma ta sallama akan zai tafi Egypt ƙaro karatu. Ya ma ta fatan alkhairi tareda cewa har abada ba zai dena son ta ba. Duk yawan surutun Farida ranan ka sa cewa komai ta yi sai kuka.
"Aisha ina miki fatan alkhairi, ina kuma mi ki kwaɗayin ki cigaba da karatu, and above all" ya goge hawayen da ke shirin zubo ma sa.
"I want you to open your heart for someone else. I want you to always be happy no matter what"
Ta fi jin tausayin shi fiye da kan ta. Shekaru talatin da ɗaya ace rana tsaka kawai a sanar da kai kai ɗin ba ka da asali, kai ɗin ɗan shege ne.
"Greeneyes, yanzu duk alƙawurran mu, duk burikan mu sun tafi a banza kenan?. Yanzu duk yadda mu ke son junan mu ba za mu kasance tare ba?"
Ajiyar zuciya yai ya ce " za ki samu wanda ya fini Aisha. Kyau, ilimi, dukiya da wayewa za ki samu wanda ya fini su. Za ki samu wanda zai so ki fiye da yadda na ke son ki Aisha. You never know, sai ki ga idon sa ma yafi nawa kyau"
Farida ta ɗan yi dariya ta ce " green eyes babu mai irin wannan siffan fa"
(Ni kam na ce ba ki je Kano ba ne😁)
Wannan ne ƙarshen Farida da Lukman. Tun daga ranan ba ta sake ganin sa ba har yau.
(Amma ta ga mai siffofin da Lukman ya bayyana😁)
Lokacin da aka fara saida form ɗin HND ta siya ta koma makaranta.
Wannan kenan.
........................
Satin su ɗaya da dawowa daga Lagos aka aiko cewa sun winning bidding ɗin da su ka je, kuma an ba su dama su yi samfurin (modelling) wannan gine-gine da za a yi.
Wannan karon kam ta ga seriousness sosai a kamfanin, domin ko yaushe ana kan meeting yadda komai zai tafi dai-dai domin aiki ne da za su yi wa federal government kuma ba ƙaramin miliyoyi za su samu ba idan su ka yi aikin.
Wani lokacin Sir Najeeb a office ya ke kwana. Cikin kwana biyar har ramewa Farida ta ga Sir Najeeb ya yi. Yadda ta ga kowa na kaffa-kaffa da shi haka ya sa itama ta ke taka tsan-tsan da shi.
Yau monday aka shirya meeting a conference room na su, duk wani babban Engineer ko Architect da ke aiki a Najeeb constructions sai da ya hallara.
Bayan an playing mu su power point da ke ƙunshe da zannen da aka yi. Sannan Najeeb ya zo gaban wani table mai faɗi ya ce "Ladies and Gentlemen. Ga biggest project na mu na wannan shekara, project Alpha"
Lokacin da ya buɗe mayafin da aka rufe teburin da shi sai ga modelling ɗin ginin da za su yi. Har ta Farida da ba ta san komai akan aikin zane-zane da ƙere-ƙere ba sai da wannan modelling ya matuƙar burgeta.
Maganar Farida ta ranan ya tuno lokacin da ya ga Farida ta buɗe ido da baki tana ganin model ɗin.
Jawabin godiya ya fara bayan an gama kallo.
"Ina godiya wa team Alpha da su ka taimaka da bani ideas, wanda da su na yi amfani na fito da wannan zanen. Special thanks to Architect Anas, Architect Ifeanyi, Engineer Ɗayyabu, Engineer Mathew..." haka ya kira mutane goma da su ka yi aiki tare ya mu su godiya.
"Sir Najeeb ni ma a gode min, na yi ta aikin zirga-zirgan kai saƙo da ƙarɓo saƙo ai" muryan Farida ya ƙaraɗe hall ɗin. Nan aka fara dariya. Najeeb kam kallon " are you for real" yai wa Farida...
........
Tana shirin fita daga gida ta ji shigowar alert a wayan ta. Ta ɗauko wayan ta duba dan ta san ba ƙarshen wata ba ne. Dubawan da za ta yi sai ga alert ɗin miliyan biyu da ga VESTAC.Inc......
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣2️⃣0️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
Tana zuwa office ta samu ana ta shirye-shiryen baƙin da za su zo. Ba ta yi maganar kuɗi da kowa ba dan dama Yakubu ta ke son tambaya ko ya san kamfanin VESTAC. Kafin ta tafi Bank ta bi bahasin wannan uban kuɗi da ba ta san ko ɓatan kai yai ya shigo account ɗin ta ba.
Ba ta ga Sir Najeeb ba, ta san shima yana chan yana ta shirye-shirye.
Sai ƙarfe tara da rabi Najeeb ya zo office. Wankan yau ma daban ta ke, ta san yana da kyau kuma ya iya wanka ba ƙarya sai dai yau wani extraordinary kyau ya ma ta na daban.
Minti goma da shigan sa office Anas ya zo ya wuce a bircike, ko amsa gaisuwan Farida bai yi ba.
Maganar da yaiwa Najeeb ne ya sa Najeeb ya tashi a hargitse yana faɗin What!
"Najeeb takardun zanen ba sa nan and the model is..."
Najeeb bai saurari ƙarshen ba ya fita da gudu.
Farida na zaune tana cin aya ɗanya da ta siya jiya ta ga Najeeb ya fito da gudu. Kasancewar ance Aya na sa ƙarin ni'ima ya sa ta lazimci cinsa ko kuma ta yi kunun aya ta sha tunda ta kusa shiga daga ciki.
Shima Anas bin bayan sa yai da gudun.
Yana tsaye gaban table ɗin yana kallon yadda aka faffasa model ɗin da ya sha wahala wajen haɗawa, and box ɗin da aka ajiye takardun zanen, shi ma empty ba komai a ciki.
Yana tsaye yana huci idon sa ya kaɗa yai ja hannun sa ya fara kakkarwa. Leɓensa na ƙasa ya ciza da ƙarfi amma still bakinsa bai bar rawa ba.
"Na sa an duba camera footage ɗin amma kuma tun jiya da rana baya aiki. It seems kamar an tampering na shi ne"
"Who is the last person to enter this place?" Ya faɗa cikin muryarsa mai fidda amo.
Anas yai shiru dan bai san ta yadda zai fara ma sa bayani ba.
"Who?" Ya sake faɗa da ƙarfi.
"Ba na tunanin za ta yi haka, CCTV footage ya nuna ta shiga ta duba model ɗin har ta ɗau hoton su sai ta fita daga nan kuma bai sake aiki ba"
"Who?" Ya faɗa wannan karan a hankali.
"Farida, your secretary"
Juyowa yai a hankali yana huci, yadda Anas ya ganshi sai da ya tsorata.
"Najeeb i'm sure ba ita ta faffasa abun nan ba, there's explanation to this"
"Sir Najeeb baƙin sun iso" wani staff ya shigo ya faɗa.
Kawai sai Najeeb ya fashe da dariya, dariya sosai har da ƙyaƙyatawa.
"Najeeb fa za mu yi?"
Cikin dariya ya ce " ya za mu yi? Hhhhhhhh. Dude she won, she succeeded. Abinda ta ke so kenan dama, to make me look stupid. Ka san mi ta yi ranan? Na san ta gaya ma ka ma, but let me tell you again. This crazy bitch puts superglue on my seat, and ...and do you know what she said?"
Ya sake fashewa da dariya " she said *Tsuliyar CEO Najeeb Constructions a waje* the bitch dare say that to my face. Yanzu na san mi ta ke nufi, she wants me to be humiliated, to look stupid"
"Najeeb plz calm down" Anas ya faɗa yana ƙoƙarin dafa abokin na sa.
"Calm down?"
"Za mu nuna mu su 3-D powerpoint ɗin sannan mu ba su haƙuri akan modelling ɗin sai gobe, then kafin goben...."
"If you are stupid i'm not Anas, we've lost this contract"
Ya mangaje Anas ya fita a wajen. Wajen baƙin ya je aka gaggaisa sama-sama. Anas na wajen yana tunanin mi Najeeb zai yi.
Kawai sai ya ce baƙin su biyoshi. Su na zuwa ya nuna mu su modelling ɗin da aka ɓata.
"I'm sorry but a bitch secretary i hired did this"
Nan su ka fara masifa " this is unprofessional, Mr Jibo taya za ka bari mu zo tundaga Abuja only to see a destroyed work"
Anas ya shiga ba su haƙuri yana ƙoƙarin nuna mu su hoton zanen a Tab ɗin sa amma ba su saurare shi ba. "We are highly dissappointed in you Mr Jibo" babban cikin su ya faɗa sannan ya juya su ka tafi. Najeeb bai ce komai ba shi kuwa Anas bin bayan su yai yana ƙara ba su haƙuri amma ba su saurare shi ba...
Najeeb ya jima a ɗakin kafin ya fito, yadda ya ke tafiya kaɗai ka san yana cikin tsananin ɓacin rai.
Yana shiga office ɗin ta ya tadda Farida tana waya sai dariya ta ke.
Kallon tsana ya fara ma ta kafin daga baya ya nuna ta da ɗan yatsa " i will revenge Miss Salihu, bit by bit"
Tunda ta ga yadda ya shigo fiskarsa ba alamun wasa ko kaɗan ta yi saurin kashe waya tana sauraron mi zai ce dan ta ɗan tsorata da yanayin sa.
"Ni kuma mi na yi" ta faɗa lokacin da faɗi kalmar ɗaukan fan sa.
Ba a jima ba Anas ya shigo.
"Najeeb mutanen nan sun tafi, we lost the project"
Najeeb bai kulashi ba ya ma rigingina kansa jikin kujera yana kallon sama ya ɗan juyawa a jikin kujera a hankali.
"Najeeb lets investigate this issue. Ina da yaƙiƙin ba Farida ba ne ta yi wannan aiki"
"She did it" Najeeb ya faɗa a hankali.
Kafin Anas ya fito Yakubu ya zo office ɗin Farida yana ba ta labarin abinda ya faru. Farida ta dafe ƙirji tana faɗin " wayyo Allah, yanzu wahalan Sir Najeeb duk a banza"
"Farida mi ya sa ki ka shiga wajen nan?"
Ta ɗan rage murya ta ce " ba dai kana tunanin ni na yi wannan aika-aikan ba"
"Farida camera ya nuna ke ce ki ka shiga wajen nan na ƙarshe and ke yanzu ake zargi"
"Na shiga uku wata sabuwar sharrin da za a min kenan. Ni fa abin ne ya min kyaun na je na ɗau hoton sa. Ga ma hotunan a wayana" ta ƙarisa maganar tana ƙoƙarin buɗo hotunan a wayarta.
Anas ya fito ya same su, the same tambaya ya ma ta akan miya sa za ta shiga ɗakin nan, amsar da ta bawa Yakubu shi ta bawa Anas.
Anas ya girgiza kai ya ce " Farida akwai matsala fa, Najeeb yana zargin ki, kuma idan ba'a gano wanda yai wannan abin ba i'm sorry but abinda Najeeb zai iya mi ki ba zai tsaya a kora kaɗai ba"
"Wayyo ni Aisha, yanzu ba za a barni na rabu da Sir Najeeb lafiya ba"
Bayan sun bar office ɗin ta ta shiga office ɗin Najeeb, har lokacin yana zaune yana kallon sama.
"Sir Najeeb wallahi wallahi ban ruguza ma ka aikin ka ba, hoton abin kawai na ɗauka saboda ya birgeni" haka ta dinga zancen ta ita ɗaya ba tareda ya tanka ma ta ba, da ta gaji da kan ta ta fita daga office ɗin.
Wannan abu ya sa ta manta da batun miliyan biyu da ta gani a account ɗin ta da safe.
Zuwa rana duk Farida ta shiga damuwa, wannan ya shigo ya ma ta Allah wadai da halin ta wannan ya shigo yana son yi tsaigumi da gulma. Tun tana mu su masifa har ta gaji ta haƙura, idan mutum ya zo har ya tafi ba ta tanka ma sa. Ranan fa gaba ɗaya kamfanin ya rikice. Rashin samun wannan contract zai jawo mu su asara sannan sunan Kamfanin su zai samu mummunan shaida a gari da ƙasar ma gaba ɗaya.
Lokacin da aka tashi Farida da ƙyar ta tashi ta tafi bayan ta leƙa Sir Najeeb wanda har lokacin ke zaune a kujera.
"Sir na san inada rigima amma wallahi ba zan yi abinda na san zai janyo wa kamfanin ka asara ba, tunda na san dukkan mu nan muna ci a ƙarƙashin ka" abin da ta faɗa kenan lokacin da za ta fita.
Ko da ta je gida ka sa taɓuka abin kirki ta yi. Jira kawai ta ke Yakubu ya dawo ta ji mi ke faruwa. Sai dai Yakubu bai dawo ba har chan dare lokacin ita kuma ta yi bacci.
Washe gari da sanyin jiki ta shirya ta tafi wajen aiki.
Ta fara zuwa office ɗin Yakubu amma ba ya nan. Haka ta wuce office ɗin ta tana fargaban mi za ta tarar.
Tana zuwa ta leƙa office ɗin Sir Najeeb amma ba ya ciki. Ta koma na ta office ɗin ta yi jugum. Ƙarfe tara saura Anas ya shigo, fiskar sa ba yabo ba fallasa.
"Yaya na ya aka yi?"
"Akwai babban matsala Farida. Kina cikin matsala, za'ayi board meeting a kan ki anjima. A ina ki ka san kamfanin VESTAC Farida?"
"VESTAC kuma?"
"Account details ɗin ki ya nuna kamfanin sun turo mi ki kuɗi miliyan biyu jiya"
Sai lokacin ta tuno da maganar kuɗi.
"Yaya ni ban san su ba, jiya nima na ga alert, abinda ya faru jiya ne ma ya sa ban yi maganar ba"
"Farida.." shigowar Najeeb ya sa ya katse maganar ya tashi ya bi bayan Najeeb ɗin.
"Allah ga ni gareka ni 'yar marainiyar nan. Wanda ya nufeni da sharri ka mayar ma sa ya Allah. Ya Rabbil Alaamin ka ceceni" ta faɗa a fili
Ba a jima ba Najeeb da Anas su ka fito, daga baya kuma Yakubu ya zo ya kirata.
"Farida ki yi ta addu'a kawai" abinda ya iya faɗa ma ta kenan lokacin da su ka baro office ɗin na ta.
Da Bismillah ta shiga hall ɗin.
Su kusan tara ne ko goma a wajen kowa yana zaune Najeeb na tsakiyar su.
Nu na ma ta kujeran da ke tsakiyar wajen aka yi ta je ta zauna. Kowa ya zuba ma ta ido. Ba ma kaman Najeeb da ke ma ta kallon tsana.
"Miss Aisha Farida Salihu, bincike ya nuna ma na ke ki ka lalata modelling da aka yi, ki ka sa aka sace takardun zanen. Mi za ki ce gameda wannan?"
"Ni ba abinda na yi, kawai dan na shiga na ɗau hoto. Ni ba abin da na yi"
Wani a gefe ya ce " Miss Salihu binciken mu ya nuna kin haɗa hannu da Kamfanin VESTAC domin ki lalata sunan kamfanin nan ta hanyar sace takardun zane da kuma faffasa modelling ɗin da aka haɗa"
"Ni ban san su waye VESTAC ba, jiya su ka turomin kuɗi batareda na taɓa sanin su ba"
"Ƙarya ki ke Miss Salihu, kin je bid ɗin da aka yi a Lagos tareda Mr Najeeb kuma kamfani VESTAC na ɗaya daga cikin wanda su ka je wannan bid ɗin, su na neman a basu wannan project"
" Allah ya isa na"
"Miss Salihu ga details na account ɗin ki, miliyan biyu sun shigo mi ki jiya daga Kamfanin VESTAC, mi za ki ce gameda haka? " wani acikin su ya kuma faɗi.
"Ni kam kun sani a gaba da tambaya kamar wanda na kai ziyara ƙabari. Ni ban san VESTAC ba balle na san dalilin da za su turomin kuɗi"
Wani daga cikin su ya ɗau waya yai kira ya ce " ku ce ya shigo"
Wani tsoho ne ya shigo, masinja ne a kamfanin tun farko-farkon buɗeshi, da ke a first floor ya ke aiki Farida ba za ta ce ta san shi ba sai dai kaman ta taɓa ganin sa.
Ce wa aka yi ya shigo yai bayani.
Ya zo ya tsaya gefen Farida saboda kujera ɗaya ne a wajen ya ce " Ranka shi daɗe. Sakatariyar Oga Najeeb ta zo ta sameni akan an ba ta aiki amma ba ta san ya za ta aiwatar ba dan za a iya ganeta. Ta sanar da ni kamfanin Vekta"
"VESTAC" wani aciki ya gyara ma sa.
"Yawwa kamfani VESTAC sun ce ta lalata aikin da aka yi ta kuma sace takardun zane saboda ba sa so kamfanin nan ta samu wannan aiki. Sun ce za su ba ta miliyan biyu. Ni kuma ta min alkawarin za ta bani dubu ɗari biyar aciki idan na yi wannan aiki"
"Innalillahi wa Inna Ilaihi Raji'oun. Tsohon banza ka ji tsoron Allah. Ni yaushe ma na taɓa magana da kai"
"Na rantse da Allah, kai na rantse da mutuwata ita ta sani na je na ɓata abun nan na kuma sace takardun zanen, ba na baku takardun ba ɗazu"
Malam Muntari irin tsofin Najadun nan ne, wanda sun yi ƙuruciyar bariki tsufan su kuma ya zo ya zama a lalace.
"Malam Muntari munji bayanin ka za ka iya tafiya"
Sai da ya fita wani da ke gafen Najeeb ya ce " Miss Salihu kin dai ji abinda ya ce, mi za ki ce gameda abinda ya faɗa domin ki kare kan ki"
Ajiyar zuciya Farida ta yi sannan ta ce " ni ba abinda zan ce, tunda tsoho kamar wannan bai ji tsoron Allah ya faɗi gaskiya ba ai ba abinda zan ce. Allah ne shaida ta, ni ban san VESTAC ba, wannan tsohon kuma ban taɓa magana da shi ba"
"To Miss Salihu ki ɗan bamu Minti biyar"
Har ta zauna a lobby ɗin wajen ba ta daina maimaita kalmar Hasbunallahu wa ni'imal wakil ba.
Minti shabiyu ta yi a wajen sannan a ka kirata.
Tana zama wanda ke gafen Najeeb ya ce " Miss Salihu mun sameki da laifin ɓata sunan kamfani. Daga yau kin bar aiki a Najeeb Constructions sannan kamfanin nan tana bin ki taran miliyan biyu da rabi za ki biya cikin kwana talatin, idan ba ki amince da wannan hukunci ba ko kuma ki ka ƙi biyan wannan kuɗi to za mu shigar da ke ƙara kotu"
Kallon Sir Najeeb ta ke idon ta ya ciko da hawaye. Shima ɗin kallon ta ya ke amma wannan karan ita kan ta ba ta san kallon tausayi ya ke ma ta ba ko kallon madallah.
"Sir ka na da abin cewa?" Wanda yai maganar ɗa zu ya tambayi Najeeb...
*Allah ya kaimu daren yau da rai da lafiya sai ku ji mi Sir Najeeb zai ce*
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣2️⃣1️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
"She stays" abinda ya faɗa kenan.
"Sir amma..."
"Za ta biya taran kamfani but she stays"
Daga haka ya tashi ya fita. Tana zaune a wajen ta kasa tashi, ji ta ke kamar an kafe ƙafafuwan ta a wajen. Tana ji su na wasu maganganu a kanta da Sir Najeeb amma kuma ba wannan ne damuwar ta ba. Ita da ta ke shirin aure ina za ta samu 2.5M, 'yan kuɗaɗen ta duk ta yi amfani da su wajen siye-siyen abubuwan biki. Ummi da Baffa Musa da wanne za su ji, da siya ma ta kayan ɗaki ko da biyan miliyan biyu da rabi.
Har su ka gama fita ba ta tashi a wajen ba sai da Yakubu ya zo.
"Farida wani hukunci su ka yanke?"
Maimakon ta bashi amsa sai ta ce "Yakubu kai ma ka yadda ni na yi abun nan?"
"Na san duk tsiyar ki iya maganar baki ta tsaya, wannan ba halin ki bane"
"Yakubu 2.5M ina zan samu?"
"Malam Muntari ɗan giya ne, zai yiwu an biyashi dan yai miki wannan sharrin ne, amma Allah ya fisu koma waye ne"
"Ni kam aikin nan nawa ake bani da mutane su ka sa mun ido a kanshi haka?"
"Akwai Allah Farida, tashi mu tafi"
Office ɗin sa ya kaita ta zauna yana daɗa ba ta baki, sai da ya ga ta samu nitsuwa kafin ya rakata zuwa office ɗin ta.
Ta zauna ne amma kaman a ƙaya ta ke, ko da ta cigaba da aiki anan, hankalinta ba zai kwanta ba domin kowa da wannan abun za a dinga ganin ta.
Tana cikin wannan tunanin Anas ya shigo.
" 'yar uwa dan Allah ki yi haƙuri, wallahi ban yadda ke ki ka yi abin nan ba. Zan cigaba da bincike har sai na gano gaskiya"
"Ba komai Yaya na. Allah shi ne shaidata"
"Kin yi magana da Najeeb ne?"
"A'a"
"Barin sameshi"
Anas na shiga office ɗin ta yi ajiyar zuciya sannan ta jawo wayan ta ta fara dube-duben hotuna. Sai da ta kai kan hotunan modelling ɗin nan sannan ta tsaya. Hoto kawai ta je ɗauka ga shi ya zame ma ta jaraba. Tana kallon hoton ba ta san lokacin da hawaye ya fara zubo ma ta ba, hawayen da ba ta yi ɗazu ba shi ta ke yi yanzu...
"Na ji hukunci da aka yanke, amma Najeeb kai ka san Farida ba za ta iya samun 2.5M cikin 30 days ba"
Yai ajiyar zuciya ya ce "zan biya ma ta"
"No need"
"Ban gane ba?"
Najeeb yai dariya wanda ya fi kama da dariyar yaƙe.
"Ni ta yiwa laifi, so only i gets to punish her. Wannan duk formalities ne na Kamfani and i've cleared it up"
"Wait, ka biya ma ta 2.5M ɗin?"
"Ina da abinyi Anas, so get out"
"Najeeb are you inlove with her?" Tambayar da ta sa Najeeb ya tashi tsaye lokaci guda, cikin fushi ya ce "how dare you say that to me"
"Dude, abin ne da mamaki. Tunda Farida ta zo kamfanin nan ka chanja, when it comes to her ba ka iya taɓuka komai. What could that be if not love"
"Get out, get the hell out of here"
Anas dai ya fita ne amma zuciyar sa ta gama amincewa da Najeeb na son Farida. Its so obvious all this while bai gane ba...
"Wai wani irin magani ki ka yiwa Najeeb ne? Duk abinda ki ka yi sai ya shanye. Gaya min wani malamin ki ka riƙe?"
Takaici ma ya sa Farida ba ta tanka ma ta ba.
"Farida da ke na ke magana"
Wannan karan ba za ta ɗauki cin fuska daga wajen Khalidah ba.
"A wajen uwar ki na ke karɓan magani. Ki fita min a office kafin ki ga rashin mutunci"
"Its not over yet Farida" ta snapping a dai dai fiskarta sannan ta fita.
"Kai ya Allah daga wannan sai wannan. Ni da na san wannan cin fuskan zan fiskan ta a wannan kamfani da tun farko da Sir Najeeb ya koreni na tattara koli na na tafi"
Ba ta idda zancen zuci ba wayar ta ta fara ƙara.
Tana ɗauka ya ce " to my office"
Saɓanin ɗazu da ta ganshi a wancan hall ɗin yanzu fiskar sa ta sauya akwai ɗan fara'a a tattare da shi.
"Ki fixing meeting da team Alpha anjima"
"Sir Najeeb ba abinda za ka gayamin, ba za ka tambayeni gameda gaskiyar lamari ba"
"Miss Salihu, ba yau na fara gaya mi ki ba. Our relationship is strictly professional, anyi investigation kuma an sameki da laifi, kuma an hukunta ki. What else do you want me to say?"
"Sir Najeeb ko da na cigaba da aiki anan, daraja na ta zube, mutunci na ya zube"
"Wanni daraja ki ke da shi dama? You are just a secretary, my secretary"
"Shikenan tunda abinda ka ce kenan. Amma duk min daren daɗewa gaskiya za ta fito kuma da kai da sauran ma'aikatan na ka duk sai kun ji kunya"
................
Wata ɗaya kenan da ya wuce. Aiki a Najeeb constructions ya zamewa Farida sabuwa, zuwa kawai ta ke amma ba ta jin aikin a ranta. Ko da Anas ya ce ma ta Sir Najeeb ya biya ma ta kuɗin ba ta ma sa godiya ba. Ta so ajiye aikin amma sai ta yi tunanin idan ta bari to wanda basu yarda akwai hannunta a abinda ya faru ba ma za su yarda, shiyasa ta cigaba da zuwa. Dama niyyarta da zaran saura wata ɗaya auren ta za ta je ta rubuta takardar barin aiki.
Sir Najeeb bai chanja ma ta ba, yadda ya ke da ɗin haka ya ke, wani lokaci yai ihu yai faɗa wani lokaci kuma yai magana a hankali. Saɓanin da da ta ke maida ma sa magana yanzu kam ko mi zai ce ba ta kulashi.
Ta koma ba ruwan ta da kowa aikinta kawai. Ko sallah a office ɗin ta ta ke, balle wajen cin abinci kam ta dena zuwa...
"Sir ga resignation letter ɗi na" ta faɗi lokacin da ta ajiye ma sa takardar a gaban sa.
"Ok" iya abinda ya faɗa kenan ko ɗagowa bai yi ba balle ya kalli idon ta.
Ta yi mamaki dan Najeeb ɗin da ta sani da ba zai yi shiru ba.
"Allah ya sada mu da alkhairi Sir Najeeb. Na gode da taimako da kulawar ka"
Cikin zuciyar sa ya amsa da amin.
*na riga na yi alkawari shiyasa na yi page ɗin nan. And na san ku na jira. Its very short so plz manage gobe da safe idan Allah ya kaimu sai mu cigaba*
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
0️⃣2️⃣2️⃣
https://m.facebook.com/Inside-Arewa-Writers-107691760958755/?ref
𝕀ℕ𝕊𝕀𝔻𝔼 𝔸ℝ𝔼𝕎𝔸 𝕎ℝ𝕀𝕋𝔼ℝ𝕊©
*(Ƙungiyar Nazarin Harshen Hausa)*
Waɗanda ta ke mutunci da su kawai ta je ta yiwa sallama. Lokacin tashi yai ta haɗa yanata-yanata ta tattara office ɗin,ta ɗauko office laptop da Najeeb ya ba ta dawo ma sa da shi.
"Sir Najeeb zan tafi, ka yafeni dan Allah, na san a zaman da mu ka yi na yi laifuffuka dayawa amma ka yi haƙuri. Allah ya yafemu gaba ɗaya"
Shiru ne ya ratsa office ɗin na lokaci mai tsawo. Tun tana ganin Sir Najeeb zai buɗe baki yai magana har ta cire rai ta fita daga office ɗin.
Sai da ta fita daga office ɗin sannan ya ɗago idon sa ya ce " i'm not done with you yet Miss Salihu"....
Office ɗin Anas ta je dan ta ma sa sallamar ƙarshe.
"Yanzu ƙanwata shikenan kin bar aiki da mu?"
"Yaya na ai ana tare ko da bana aiki anan"
"Gaskiya ban ji daɗi ba, yanzu idan ki ka tafi wa za mu samo ya replacing ɗin ki. Ke ce the second longest surviving secretary a wajen Najeeb"
"Ya Anas kenan, ai da ƙyar mu ka sha mu ɗin ma"
" ba wani, da ƙyar dai Najeeb ya sha a wajen ki"
Dariya ta yi sannan ta ce " ya Amaryar ta mu?"
"Tana nan sai rigima"
"Ta kaini rigima"
Anas ya zaro ido yana dariya "ai Farida idan ta kai ki rigima bulaguro zan yi a garin. Irin ki ai sai su Najeeb"
"Hmm Ya Anas kenan. Nikam ina abokin adawar ka? Ko ya janye ne?"
"Ai tunda Daddy ya sa min stamp na yaƙice shi. Ga shi dama gimbiyar wannan ɗan baƙin kaɗai ta ke gani"
"Allah ya kaimu lokacin biki Yaya na"
"Amin ƙanwata, kar a manta da IV ɗin mu fa"
"Ai kune ƙarɓan fari".....
...................
Shirye-shiryen biki ake ba kama hannun yaro saura sati uku aure aka kawo lefen Farida kuma gaskiya Rayyan ya yi ƙoƙari sosai.
Farida ta duƙufa da gyaran jiki da shirye-shiryen yadda biki zai kasance.
Yau ana saura kwana goma sha takwas aure, Baffa Musa ya kirata.
"Wani shirme na ke ji za ki yi ranan Alhamis?"
"Baffa friends day za ayi ranan Alhamis tunda ka hana ayi kamu"
"Enemies day za ki yi ba friends day ba. Yanzu ke Farida ba za ki yiwa kan ki faɗa ba. Ayi miki walima salamun alaikum a kaiki ɗakin ki hankali kwance, sai kin bijiro da wani shirme"
"Baffa a cikin gidan nan fa za'ayi kuma iya mata ne ka san inada jama'a"
"Ungo na ki ke da jama'an na ki"
"Mun gode Baffa"
Taɓe baki yai kawai yana bin ta da kallo. Bakin tan nan yana fata ya zaunar da ita lafiya a gidan ta, ba ya kawo fitina ba.
"Baffa ina ka amince?"
"Ya na iya uwata. Allah ya kaimu lokacin ya kuma kaɗe fitina"
"Baffa thank you" ta faɗa tana tashi da sauri...
................
Duk yadda ta ke ji gameda auren sai da auren ya zama saura sati ɗaya sai jikinta yai sanyi. Haka kawai sai tsoro ya shigeta gani ta ke kamar za a kuma wani chakwakiyar kamar yadda aka yi lokacin Lukman. Ummi ta zo amma su Nanna sai Alhamis za su shigo. Ranan talata da safe ta wuce Najeeb constructions. Ta fara biya wa office ɗin Sister Munibat ta ba ta katin gayyata tareda cewa idan ba ta zo ba to sun ɓata.
"Sister Aisha kenan, ai indai ina da rai da lafiya to bikin ki da mu za ayi"
Farida ta ɗan harareta " kaman da gaske, kin sayi ashobe na kuwa?"
Sister Munibat ta fara sosa kai.
" hmmm ai dama na sani, Dan Allah ki daure ki zo"
"Insha Allah sister Aisha zan zo"
Daga wajen Sister Munibat ta wuce wajen Anas. Ta jima a wajen sa, inda ya ke ba ta labarin sakataren da aka ɗauka bayan ta tafi.
"Farida kwanan sa huɗu ya ajiye aiki, wai ba zai iya ba"
"Ai Sir Najeeb idan ba jan wuya ba ba mai iyawa da shi"
"Jan wuya kamar ki ba"
"I'in ai mun sha fama da shi"......
Lokacin da ta shiga office ɗin sa yana jikin shelf ya na neman wasu files. Ta tsaya tana kallon yadda ya ke ta dibi-dibi a wajen. Da ta na nan yanzu da ita ke wannan aiki.
"Sir Najeeb mai ka ke nema?" Muryan da bai yi zatan jin sa ba ya ji a ta bayan sa. Bai san lokacin da ya sake file ɗin ya faɗo ba. Tsayawa yai yana kallonta, ta wani yi haske tana sheƙi, ga wani ƙanshi mai daɗi da jikinta ke fitarwa.
Tsugunnawa ta yi ta ɗauka file ɗin sannan ta miƙa ma sa. "Ga shi na ma ka aikin ƙarshe"
Bai amsa file ɗin ba sai ma juyawa da yai ya je ya zauna a kujerar sa.
"Iko sai Lillahi, daga ganin Sarkin Fawa sai miya ta yi zaƙi. Sir Najeeb ba fa aiki na zo ba da za ka min jan ajin da ka saba"
"Oh really"
"Gashi, dama IV na kawo ma ka" ta yi saurin ajiye file ɗin tareda ciro IV ta ajiye ma sa.
"Dan Allah a daure a zo. Duk da ma dai i'm just a secretary"
Ta ɗan yi dariya ta ce " was just a secretary"
"Congratulations Miss Salihu"
"Thank you Sir Najeeb"
Ya ɗan kurɓi coffee da ke gaban sa sannan ya ci gaba da latsa laptop.
"Sir Najeeb ina da magana. Dan Allah ka ɗan rage halin kan nan. Ka ga ba kowa bane zai iya jurewa. Ni ma da ƙyar na sha a wajen ka. Allah, watarana idan na koma gida daga office har ƙaramin zazzaɓi na ke saboda stress da zafin kai. Kai ba a maka gwanin ta sannan..."
"Out"
"Ka ga irin halin na ka ko"
"Miss Salihu get out"
Ta yi shiru tana kallon sa sai da ta ga zai sake ɗaukan mug ɗin coffee ɗin sannan ta yi wuff ta ɗauke.
Ta kai baki da nufin ta kurɓe duka lokaci guda sai ta ji shi da zafi sosai. Ta ɗan kurɓi kaɗan ta sake kurɓa sannan ta ajiye ma sa.
Dariya ta yi saboda yadda ta ga ya zaro ido.
"Sir Najeeb tsokalar ƙarshe ne fa. Na tafi"
Harta juya sai kuma ta juyo ta ce "Sir Najeeb a yafe mu"...
Sai da ta rufe ƙofa ya ce "devil in a dress" ya jawo wani dogon envelop ya buɗe, hotuna ne guda uku a ciki " happy never marriage Miss Salihu" ya faɗa a fili.
(🙄Sir Najeeb ya dai?)
.......................
Farida na komawa gida ta tarar da Maijiddah ta zo.
"Kai-kai Jiddah mi ki ke ci haka? Kin ganki kuwa"
"Kai Anty Farida"
"Zo zo mu shiga ɗaki ki gaya min sirrin"
Sai da su ka zauna ta ce " Jidddah ciki gareki, wannan ƙiban da walakin"
Maijiddah ta rufe ido tana murmushi.
"Masha Allah, Allah ya raba lafiya. Ina kishiyar ki? Har yanzu tana Abuja?"
"E, amma yanzu sau biyu ta ke zuwa a wata"
" 'yar kusun'wa, za ta ma ajiye aikin ta dawo gidan ta, ko kuma ta ji ta a silencer dan mune ma su gidan yanzu"
"Na gode Anty. Kayan da ki ka bani sun min rana"
"Zauna a wajen, ai mazan yanzu sai da shigar bariki. Nima na je Jos na kwaso nawa suna nan jingim"....
Biki na matsowa jikin Farida na ƙara sanyi kullun ta yi bacci sai ta yi mafarkin an fasa aurenta. Abin ya dameta ta gayawa Ummi, Ummi ta ce ta dinga addu'a. Itama ɗin Ummin Allah-Allah ta ke ayi bikin lafiya ba tareda wata matsala ba.
Ranan Alhamis aka je aka yiwa Farida jere a gidan Rayyan. Rayyan ya gina 3-bedroom flat mai kyau. Baffa yai ƙoƙari dan ya kashe kuɗi sosai wajen sayen ma ta kaya, 'yan uwan Ummi ma sun yi ƙoƙari gaskiya...
........... ..........
Ya na zuwa ƙofar gidan ya sa yaro ya kira ma sa maigidan. Da yaron ya fito ya ce yana zuwa...
Musabaha su ka yi da dattijon sannan su ka gaisa.
"Yi haƙuri ban ganeka ba"
Ya miƙa masa envelop sannan ya ce " ɗan ka zai yi aure ranan Asabat ɗin nan ko?"
"Insha Allahu"
"Matar da zai aura ba matar aure ba ce"
"Ban gane ba"
"Ka dubi cikin envelop ɗin nan za ka ga zahiri" daga haka ya juya ya tafi.
.....................
Anyi friends day lafiya kuma ba laifi ƙawayen ta na Jos sun zozzo, anci an sha kuma an girgije.
Ƙarfe goma sha ɗaya na dare lokacin ba ta fi 'yan mituna kaɗan da kwantawa ba kiran Rayyan ya tashe ta. Tana ɗauka ya ce ta fito waje yana ƙofan gidan su.
"My Ray lafiya ka zo da daddaren nan?"
"Ki fito Farida akwai saƙon da zan ba ki ne"
Maganar saƙo da ya ce sai ta ji zuciyar ta ya buga. Ta tashi ta sa hijabi ta fito.
Akwai wa su baƙi da ke kwance a barandar tsakar gidan su na hira, da ke ba su jima da tattara tsakar gidan ba.
"Amarya ina zuwa haka?"
"Ƙofar gida zan je an kawo min saƙo"
"Samarin zamani dai, angon ne ya ka sa hakuri haka"
Ita dai ba ta sauraresu ba ta fita.
Wajen motar sa ta je ya buɗe ta shiga.
"My Ray minene, hankalina ya mugun tashi fa"
Da ke dare ne ba iya kallon fiskarsa ta yi sosai ba balle ta ga yanayin sa.
"Farida ashe za ki iya cin amana ta"
Dum ta ji ƙirjin ta ya yi.
"Wallahi ban ɗauka za ki min haka ba"
"Na shiga uku ni Farida ba dai za a kuma ba. Rayyan mi na yi?"
"Ashe soyayya ku ke da Ogan ki. Ashe duk yadda ki ke zagin sa a gabana iya fatar baki ta tsaya"
"Rayyan dan Allah kar ka sa zuciyata ta buga yanzu. Idan ma wasa ka ke ka dena please "
"Da kan sa ya je gida ya ce wa Baba ke karuwarsa ce"
"Innalillahi wa Inna Ilaihi Raji'oun, Lahaula wala ƙuwwata illa billah. Sir Najeeb ne ya faɗi hakan?"
Miƙa ma ta wayarsa yai ya ce ga hotunan da ya kawo. Ina tunanin ma waɗannan lokacin da ku ka je Lagos tarene ku ka yi holewarku achan.
Ta amshi wayar ta fara kallon hotunan. Hoton farko tana zaune kan cinyar Najeeb ta sa hannayen ta a kafaɗun sa tana murmushi, ɗaya kuma suna tsaye ya rungumeta ta baya, lips ɗin sa a daidai wuyan ta. Ta swipping na gaba wanda tana kallo hawaye na ɗiga a jikin wayar. Suna rungume da juna bakinsu a haɗe kamar suna kissing.
"Ba ni bane, wallahi ba ni bane. Wannan sharri ne. Rayyan ka yarda da ni"
"Dama na zo na faɗa miki ne da kaina kafin gobe a zo gida a faɗa. Na fasa auren ki Farida, ina son ki amma ba zan iya auren ki ba. Najeeb yana da kyau yana da kuɗi, ko bayan mun yi aure idan ya neme ki za ki amince da shi. Ba zan iya aure da zargi a ciki ba"
Bakin ta ne ya fara rawa, tana so ta yi magana amma ko me ya taho zai fito sai ya maƙale a wuyan ta. *"Na fasa auren ki Farida"* shine maganar da ke ta maimaituwa a ƙwaƙwalwarta.
"Gobe za su zo su karɓi sadaki da lefe, sauran abubuwan na yafe. Na gode da Allah ya tona asirin ki kafin ma ayi auren, dama Umma ta sha faɗamin ba ta yarda da ke ba dan 'yan Jos ɗin nan yawancin ku 'yan iska ne"...
Ba ta san ya akayi ta buɗe ƙofa ba, ba ta san kuma ya akayi ta shiga gida ba. Zuwa ta yi ta zauna a bakin gado hawayen da ta ke yi ma ya tsaya. So take ta gane mafarki ta ke yi ko gaske ne. Bacci kam ranan ba bu shi a idon Farida.
Washe gari da safe aka tashi da shirye-shiryen walima. Farida ta kasa magana ta kasa faɗan abinda ya faru jiya, ita har lokacin gani ta ke mummunan mafarki ta yi jiya da dare.
Zuwa ƙarfe goma sai ga Baffa ya shigo yana faɗace-faɗace. Kiran Ummi da Nanna da Baaba Sabuwa yai zuwa falon sa. The next thing da akaji sai kukan Ummi. 'Yan gulma su ka yi falon da sauri Baffa musa ya fatattake su.
"Amina ki dena kuka, ni ban yarda da abin da su ka ce ba, kuma koma hakanne dole sai na aurar da 'ya ta gobe. Ba zai yiwu a fasa aurenta har sau biyu ba, sai duniya ta zageni. Ni nawa 'ya'yan ina aurar da su lafiya ita kuma da ta ke amana gareni ake samun matsala duk lokacin bikin ta"
Nanna da ita kaɗai ce ba ta fara kuka ba ta ce "yanzu wa za ta aura?"
"Yakubu, Yakubu zai aureta, ku cigaba da shirye-shirye Allah ya kaimu goben"...
Farida na ɗaki har lokacin tana zaune jugum, Maijiddah ta yi tambayar duniyar nan amma ba ta kulata ba.
Ummi ta shigo ɗakin tana hawaye. Zuwa ta yi ta tsugunna gaban Farida ta ce "faɗa min gaskiya Farida, akwai abinda ke tsakanin ki da Ogan ki?"
Farida ta kalli Ummi da rinannun idanuwan ta ta ce "da gaske ne ko? Da gaske Rayyan ya fasa aurena?. Ummi banida sa'a a rayuwa kenan? Ummi ina son na yi aure, ina son na samu gidan kai na, ina so na haihu na tara 'ya'ya, ina so na samu ladan biyayyar aure, ina so na cika miki burin ki Ummi. Ummi ko dai aure ba ya cikin ƙaddara ta ne?"
Ummi ka sa magana ta yi sai kuka.....
Zuwa ƙarfe shabiyu 'yan gidan su Rayyan su ka zo karɓan kaya. Daga wajen ma su ke cewa aje a kwashe tarkacen da aka jera a gidan ɗan su. Abubuwa dai su ka rinchaɓe a wajen.
Kowa a gidan da abinda ke ran sa, wassu baƙin na shirin komawa amma da su ka ji Baaba Sabuwa ta ce aure ba fashi za ayi, sai su ka tsaya dan su ga ƙarshen Farida.
Farida tun safe ko sau ɗaya ba ta fito a ɗaki ba, ko wanka ba ta iya yi ba balle abinci kam ba a zancen sa.
Da yamma Yakubu ya dawo daga wajen aiki sai a lokacin ya ke jin labarin abinda ke faruwa. Baaba Sabuwa ce ta ma sa maganar auren Farida da ya koma kan sa. Duk da bai shirya aure yanzu ba sannan bai taɓa kawo auren Farida a ransa ba amma indai dan ya cececi mutuncin 'yar uwar sa ne to zai aureta da gudu ma. Abinda ya ƙara ɗaure ma sa kai baifi yadda aka ce wai 'yan gidan su Rayyan sun ce wai FARIDA karuwar Ogan ta ba ne. Ya san Farida kuma ya san Sir Najeeb, ko da dai chan ƙasar zuciyar sa yana zargin Sir Najeeb na son Farida amma bai kai har ace wai suna neman junan su ba.
Yana cikin wannan tunanin ya ji wayar sa na ringing. Yana dubawa ya ga Farida ai da sauri ga ɗauki kiran.
"Dan Allah Yakubu ka sameni a ƙofar gida"
Da sauri ya tashi ya fita.
Lokacin da ya ganta wani tausayinta ne ya kuma shigan sa. Lokaci guda Farida ta chanja ta zama wata iri, fiskanta ya kumbura ga idon ta da su ka ƙanƙance saboda kuka. Tunowa yai da shekara uku da su ka wuce exactly haka ta lalace lokacin da aka raba aurenta da Lukman. Gara lokacin da sauƙi tunda matsalar daga Lukman ne to yanzu fa.
Ya ƙarasa wajenta yana faɗin "Farida dan Allah ki yi haƙuri, ki kwantar da hankalin ki komai zai wuce"
"Ka kaini gidan su Sir Najeeb" abinda ta faɗa kenan cikin muryarta da baya fitowa sosai saboda dashewa da yai...
Adama ce ta buɗe ƙofa lokacin da ta danna doorbell ɗin.
"Daddy na nan?"
"Eh ki shigo"
A tsaye ƙiƙam ta tsaya idon ta na kallon ƙasa, kan ta ke sarawa, duk yadda ta ɗaga kan sai ta ji wani raɗaɗi.
Mom ce ta fara saukowa ganin yadda Farida ta ke ya sa tasan yarinyar na cikin damuwa.
" 'yan mata ki zauna mana" ta faɗa da Hausanta da bai gama nuna ba.
Farida ba ta ce komai ba sannan ba ta zauna ɗin ba. Kitchen Mom ta wuce ganin Farida ba ta cikin hayyacinta.
Minti huɗu sai ga Daddy ya sauko.
"Ina wuni Daddy" ta faɗa da disashshiyar muryarta.
"A'a Aisha Amarya?"
"Na'am Daddy"
"Lafiya dai ko?, shekaranjiya Baban ki ya kawo min katin biki, ina ce ba wata matsala ba ne ta taso ?"
"Daddy kai uba ne na gari amma ɗan ka bai ɗauko hali na gari ba. Najeeb ya min sharri, ya raba ni da farin ciki na. Ya sa min tabo a rayuwata wanda ban san ranan da wannan tabo zai gogu ba. Ni marainiya ce, ba ni da gatan da ya wuce Allah, kuma na haɗa Najeeb da Allah. A kamfanin sa ban tsira ba, na bar aiki da shi ma ban tsira ba. Allah zai saka min" ta fashe da kuka ta fice daga gidan da gudu. Daddy yana kiran ta amma ba ta tsaya ba. Daddy kan shi ya ɗaure dan bai gane ina maganganun Farida su ka dosa ba.
Tana fitowa ta tsaya ta goge hawaye sannan ta fara tafiya duk da kuwa ba ta da ƙwari a jikinta. Ta kusa isowa wajen Yakubu da ke jiran ta jiri ya ɗebeta ta faɗi ta suma. Yakubu ya yiwo kan ta da gudu...
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
0 comments:
Post a Comment