Ina fita kofa yana tayar da mota, yaci taya ya bar gurin a guje ba tare da ko ya tsaya ya saurari ma'aikatan sa da suka biyo shi a baya ba. Nabi motar da kallo har ya fita daga gate, sai kuma na zame na durkusa a gaban wata flower bed na jingina kaina a jiki ba tare da ko damuwa da menene zai iya fitowa daga ciki ya cutar dani ba. I only wanted to wake up, wake up from this nightmare where Sadauki doesn't know me.
Ina jin su Saghir suka wuce suka koma ciki suna ta maganganu babu wanda ya lura dani, bayan mintina kadan kuma sai aka fara watsewa kowa yana fitowa yana neman shiga motarsa. A lokacin ne kuma naji muryar Saghir ya na nemana "Diyam! Diyam!" Amma na gaza bude baki ballantana in amsa masa har yazo inda nake sannan cikin whisper yace "what the hell are you doing here?" Maimakon in bashi amsa sai hawaye ya fara kwarara daga idona kamar an bude pampo, ya fincike ni ya tayar dani tsaye yana grinning at mutanen da suke wucewa sannan ya kaini mota ya cusa ni ya rufe kofar muma muka fita.
Ba wanda yayi magana har muka je gida, yana packing ya zagayo ya bude inda nake ya fige ni zuwa cikin gida ya jefa ni a kan kujera yace "me kike tunanin zakiyi archiving ne by embarrassing me a cikin mutane? By trying to destroy my carrier? Oga na yana miki magana ki wani tsaya kina kallonsa kamar statue? Sannan kuma ki fito ki zauna a cikin flowers are you nuts?" Na dafe kaina da hannuna, ni ihun da yake min ji nake kamar zai tsaga min kaina gida biyu. Har yanzu kaina yaki budewa balle in yi tunani. Farkon abinda nake so in fahimta shine me Sadauki yake yi a gurin aikin su Saghir? Kuma har nani suna addressing dinsa as if shine manager dinsu daya dawo daga karatu suka shirya masa party. Can it really be? In kuma har ya kasance haka ne to how comes? Ni dai Sadaukin dana sani sanda muka rabu seven years ago bashi da komai, kuma shekaru biyu bayan rabuwar mu Saghir ya samu wannan aikin then how comes Sadauki yayi kudin da har zai bude companyn motoci a cikin shekara biyu? Bayan wannan kuma shin sun gane juna ni suke playing ko kuma suma kansu basu gane ba? Anya kuwa Saghir zai karbi aiki a gurin Sadauki in har yasan shine? Sai wani tunani yazo min, as we were growing up ni da Sadauki, bazan iya tuna ranar da Saghir yaje gidan mu ba, lokacin ma shi kusan kullum baya kasar. And Sadauki was never allowed to enter gidan Alhaji Babba tun yana dan karamin sa har sai sanda naje nake shigo dashi a boye and even then basu taba haduwa ba. So what I was sure of shine basu san faces din juna ba.
But, me yasa Sadauki zai yi acting kamar bai sanni ba? He did looked surprised akan party din but he did not act surprised to see me there, meaning yasan dangantaka ta da Saghir. And then many things started to become clear to me, sunan subay'a, aikin Saghir. Tabbas Sadauki ya gane Saghir bayan yayi masa tambayoyi a gurin interview wannan shi yasa ya dauke shi aiki even with his pass certificate and lack of experience, kuma shi yasa har yanzu ba'a kori Saghir ba daga aiki duk da negligence dinsa. But why? Ina son insan me yasa Sadauki yayi haka? Is my Sadauki still behind the mask of Mr Abatcha?
Sai bayan na dawo daga tunani na nayi realizing har lokacin Saghir fada yake yi. Na tsaya ina kallon sa ina realizing cewa he had no idea mai ya faru a gurin nan. Shi kawai fada yake na wulakanta ogansa. Nayi gyaran murya nace "Allah ya baka hakuri. Ni ba'a saba cemin Madam bane ba shi yasa na kasa amsa masa. Amma kayi hakuri, nan gaba in ance min madam zan amsa" na mike zan hau sama yace "ina jakarki?" Sai lokacin na lura bata hannuna nace "ta fadi a gurin" nan kuma sai ya koma fadan yar da jaka "tunda bake kika siya da kudin ki ba ai dole ki yar" ni dai nayi wucewa ta sama na barshi a nan.
Ranar yadda naga rana haka naga dare. All I wanted to do is to see Sadauki again and ask him tons of questions da suke zuciyata.
Exactly a week after that. Muna palo ni da Subay'a ina kokawar yi mata kitso tana ta zillo tana kuka Saghir ya sauko daga sama. Ya saka hannu ya dauke ta daga cinyata ya suka hau kujera yana warware mata kitso dayan da da kyar na samu nayi mata shi. "Tunda bata so sai a rabu da ita, ke waye yake takura miki yanayi miki kitso in bakya so?" Ban ce komai ba danni yanzu bana cikin mood na musu da Saghir. Yace "wato idan Allah ya yi mutum shi mai sa'a ne a duniya to bashi da wani sauran stress kuma a duniya. Kinga a office dinmu tun daga dawowar oga yadda ake ta rububi ana shishshige masa kowa yana so ya kafa kansa, ni kuwa babu abinda ya dame ni dasu aikin gaba na kawai nake yi. Amma kinsan ina daki kawai yayi kirana a waya, wai dan Allah in an jima inje airport in dauko shi zai dawo daga Maiduguri, kinsan dan can ne ai, babarbare ne" na cigaba da harkokin gabana looking uninterested, Amma kirjina lugude kawai yake yi nace "hmmm, Allah ya taimaka" ya danyi shiru sai kuma yace "I have an idea, tunda kowa neman shiga yake a gurin oga why not me? Nima ai ina son promotion din. Idan na dauko shi daga airport nan gidan zan kawo shi, you prepare dinner for him tunda dama bashi da aure kuma bashi da gida a hotel yake zama, nasan zaiji dadi, in ya ci abinci anan sai in kaishi hotel din da take zama" na yi saurin juyo wa ina kallon sa, sai na samu kaina da girgiza kaina nace "no" no matter how much zuciyata take son ganin Sadauki nasan ba dai dai bane ba, shigowar sa cikin gidan aure na ba abu ne mai alfanu ba "Please ka zarce dashi inda zai sauka kar ka kawo shi nan" ya mike tsaye yana kwantar da Subay'a da tayi bacci a hannunsa yace "yes, nan zan kawo shi first. Zan fita in yo miki cefane and you cook something nice for him, abincin da kika san mutane irin sa zasu ci" kafin in sake retaliating ya fita. Na zauna a gurin na dafe kaina kirjina yana bugawa da karfi, wata zuciyar tana gaya min cewa in gaya wa Saghir waye ogan sa wata kuma tana hanani har sai na samu Sadauki munyi magana na fahimci inda yasa gaba tukunna. But yaushe zan same shi? Ni a matsayina na matar ma'aikacin sa? Ni a matsayina na wadda yayi addressing as Madam?
Ina nan zaune har Saghir ya dawo da ledoji niki niki ya shiga kitchen ya ajiye, ya fito yace "ga nama can da kayan miya da fruits, akwai wani abu da kike bukata kuma?" Na langwabar da kai "ni yanzu mai zan dafa masa?" Yace "think of something, nima ban sani ba". Daga haka ya fita ya barni.
Sai dana kai Subay'a islamiyya sannan na dawo na shiga kitchen, na saka ledojin a gaba ina kallo, me zan dafa? Kuma wai Sadauki zan dafa wa abinci a matsayin sa na ogan mijina. Lallai life is full of twists and turns.
Sai na tuno da tuwon Ummah da take yi mana muna yara ni da Sadauki. Tuwon laushi miyar yauki sai ta dagargaza kaza a ciki ta cire kashin gaba daya. Sadauki yana so sosai dan har cewa yake yi ayi dan haka na nutsu na fara shirya masa. Na gyara fruit din nayi smoothie na saka a fridge. Zuwa magrib na gama na shirya komai a dining table sannan na fita na dauko Subay'a sai kuma na sake gyara gidan na saka turaren wuta naja subay'a muka hau sama.
A sama nayi wanka nayi mata wanka itama muka yi sallah tare sannan ta kwanta ina yi mata kitson da taki tsayawa ayi dazu, a haka har tayi bacci sannan naji shigowar mota, gabana ya yanke ya fadi na kalli window amma wani barin na zuciyata yace "kul kika leka kallon haramun" sai na kwanta na dunkule a guri daya kamar mai zazza蓳i, naji an tsayar da motar an kuma bude an fito sai dai ba'a rufe ba, naji ina son in san me yasa ba'a rufe din ba. Na jawo pillow na dora a kaina na danne da hannayena amma the next second sai gani na nayi a bakin window a bayan labule ina leka waje.
Saghir na hango a tsaye a bakin mota yana magana dana cikin motar wanda shi bai fito ba, sun jima suna magana a haka, kamar na cikin baya son fito wa yayin da Saghir yake ta insisting akan sai ya fito. Sai kuma naga ya zuro kafafuwansa ya fito Saghir ya rufe masa kofar sai suka jero a tare suka doso cikin gida, yayinda fitilar gaban gidan ta haske min su.
Two men; one fair and the other one dark, fair one din shine mijina amma ni zuciyata dark one din take so; one taller than the other ni kuma tall one din nake so, one younger than the other ni kuma younger one din nake so, one frowning the other one smiling ni kuma me frowning din nake so, one employer the other one employee ni kuma employer din nake so. But the other one is my husband. That was how cruel my was.
For a split second, Sadauki smiled, a smile that went straight to my heart, nayi saurin sakin labulen naja da baya kamar wadda ta taba wuta. Ji nayi kamar an debo wani tarin sonsa cikin trailer an zuba min a zuciyata sai naji tayi min nauyi dan haka na ruke kirjina na zauna akan gado ina ambaton sunan Allah da niyyar ya kawo min dauki a cikin lamari na tun kafin inyi tabewar da zata kaini ga halaka.
Waya ta ta fara ringing, da kyar nayi karfin halin dauka na kara a kunnena Saghir yace ina whisper "mun shigo. Ki zo ki kawo masa abinci" nace "dan Allah Saghir ka bashi kawai, bana jin dadi wallahi" nasan banyi rantsuwa akan karya ba saboda yadda nake jin jikina tabbas nasan akwai zazza蓳i a tare dani, yayi tsaki ya katse wayar. Na koma na kwanta na jawo Subay'a jikina na lullube mu, amma muna fikin kunnena sai yake kokarin zuko min maganganun da ake a palo, wishing to hear muryar Sadauki.
Ina nan kwance kawai naji an hawo saman sai aka bude dakin, Saghir ya shigo fuskarsa kamar zaiyi kuka "Diyam? Me yasa ne wai ke kullum burinki kiga na tozarta a duniya, why?" Na tashi zaune ina girgiza kaina nace "me nayi kuma?" Yace "tuwo. For God's sake tuwo Diyam zaki yi wa wannan mutumin da bana jin ya taba cin sa? Ko ni ba cin tuwo nake yi ba kuma kin sani" nace "cewa yayi ba zai ci ba?" Yace "to ni ina zan iya bashi? Kin san da yadda nayi convincing dinsa ya shigo kuwa kuma kawai sai inkai masa tuwo?" Na tashi na zura jihab dina na fita ya biyo ni a baya.
Yana facing stairs, wannan yasa ina fara sauka na ganshi amma shi kansa yana kasa yana daddanna wayar hannunsa. Na dauke ido na daga fuskarta ina kallon gefe nace cikin wata muryar da naji kamar ba tawa ba "Barka da zuwa" ya dago kai, kallo daya sannan ya mayar da ganinsa kan wayarsa yace "Barka kadai Madam. Ya gida?" Still with the Madam, na fada a raina and my heart hurts. Ban amsa ba na mike naje dining na duba na tabbatar komai yana nan yadda ya kamata sannan na dawo na tsaya ina kallon Saghir da yake ta kokarin yi masa hira nace "ga abinci a table Ko nan za'a kawo muku?" Sadauki ya mike da sauri yace "thank you, zamu ci a can din. Ni am fine ma really, maigidan ki yace sai nazo naci, so I guess I will just have a taste and go" sai kuma ya tafi dining area da sauri Saghir ya bishi a baya, yana zuwa ya dauki plate zaiyi serving kansa sai plate din ya zame daga hannunsa ya fado ya tarwatse, and I noticed that his hand was shaking. Saghir ya kwalla min kira "zo da sauri ki gyara gurin nan" amma kafin in karasa Sadauki ya bar gurin da sauri yayi hanyar waje, Saghir ya kalleni da alamar tambaya na daga masa kafada, sai kuma ya bishi wajen.
Na tsaya da tarin abinci a gaba na ina kallon kofa, so the mask has fallen, my Sadauki is still in there kawai duk pretence ne.
Ina tsaye Saghir ya dawo yace "get a basket ki zuva warmers din a ciki, he is taking it away" naje na dauko na hada masa komai har drink din na rufe, Saghir ya karba yana cewa "Allah yasa ma yaci, wannan mutumi kamar aljanu ne dashi".
[2/12, 6:05 PM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty One: A Stranger in the Dark
Ina jinsu suka fita daga gidan, and some parts of me went with them.
A juya kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki na koma sama nayi alwala na gabatar da sallar isha sannan na kai kuka na gurin ubangiji na. Bayan na gama nayi shirin bacci na zauna akan gado ina jujjuya waya ta a hannuna, I wish zan iya sanin halin da Sadauki yake ciki, I can't even begin to imagine in dai har son da yake yi min ya kai wanda nake ji a raina a game dashi to kuma tabbas da nice zuciyata bugawa zata yi in fadi in mutu. It hurts so much to meet him bayan shekaru da yawa and not be able to talk to him, to ina ga shi kuma da yake kallona a matsayin matar wani?
Ina nan zaune naji shigowar Saghir, ya jima a kasa sannan ya hawo sama, nayi tsammanin dakinsa zai wuce kamar kullum amma sai naji ya turo kofar dakina ya shigo da tray a hannunsa ya ajiye akan side table ya zauna a kusa dani yana janyo table din gaban mu. "Sarkin yan tuwo gashi nan na debo miki, ko ba zaki ci ba?" Na zuba a plate ina cewa "Nagode" sai naga ya dauko chokali shima nace "au zakaci ne? Bayan baka cin tuwo?" Yace "albarka ta zan saka miki" murmushi kawai nayi zuciyata tana ayyana min abinda yake ransa. Sai da muka gama ci na kwashe kayan na mayar kasa na taho da ruwa da zuba masa a cup na mika masa ni kuma na zauna ina sha a robar ruwan. Sai dana gama na juya naga ya tsatstsare ni da ido kuma nasan irin wannan kallon but not today, I just can't.
Sai na mike zan bar gurin yasa hannu da yawo dani kan gadon, ya jawo ni jikinsa yana mammatsa min kafadu na amma sai nayi saurin ture hannunsa dan ji nake kamar wanda yake doramin garwashin wuta a jiki, kafin in matsa ya saka hannunsa biyu ya juyo dani ina facing dinsa ya jawo fuskata dai dai tasa yana kokarin hada bakin mu, nayi saurin juyar da kaina nace "Please stop, bana so" amma yaki hakura, na fara ture shi kuma yana jawo ni kamar dai yadda muka saba yi duk sanda yazo da bukatar sa, ganin yafi karfina yasa na fara kuka shabe shabe da hawaye ina rokonsa akan ya kyaleni amma yaki, can kuma sai ya sake ni da karfi ya hankada ni baya ya mike tsaye yana kallona da idonsa da fuskarsa da duk suka yi ja saboda bacin rai yace "nagaji, nagaji, nagaji Diyam nagaji. Yaushe ne wai zaki daina guduna? Yaushe ne zamu mori auren mu ni da ke? Tunda akayi auren nan shekara bakwai Diyam in na zauna zan iya lissafa miki adadin lokutan da kika bari na kusance ki suma kuma babu wanda kika kawo kanki kuma babu wanda kika karbe ni cikin son ranki. Ni fa mutum ne, inada jini da tsoka a jikina ina bukatar kulawar matata amma ke na fahimci da dutse akayi taki halittar. Kullum ina bawa kaina hakuri ina ganin kamar zaki dawo hayyacinki amma kin ki, ni Saghir ni da mata suke rubibi na a waje har kawo min kansu suke yi amma ni ne matata take guduna. Na gaji wallahi. Hakuri na ya kai bango" na sauko daga gadon ina goge hawaye na nace "then let me go, mu daina daukan alhakin juna haka nan, auren nan tun farko da aka yi shi ni da kai bama so, igiyar nan a hannunka take, ka saki igiyar ni da kai mu huta da kunan zuciya" sai ya tsaya yana kallo na yace "haka kika ce? To tsaya kiji, lokacin da akayi auren nan ni kaina banyi niyyar zama dake ba wallahi, after what happened on our first night I thought in na sake ki ban kyauta miki ba, nayi niyyar in rufa miki asiri in cigaba da zama dake a haka ina tunanin with time zaki soni. Amma har yanzu kinki sona, kina ganin kamar ban isa ba ko something like that, ni kuma nasan babu macen da ta isa tace bata sona, in na sake ki Diyam kamar kinyi winning a kaina kin nuna min ban isa ba, which is something I won't agree to. Kin san me? Nasan maganin ki. Aure zanyi. I will let you watch as a lady wadda bata kaiki komai ba take away your husband ta marar dani dan lelenta nima in mayar da ita yar lelena a gaban ki, maybe wannan shi zai nuna miki worth dina ki dawo cikin sense dinki" na mike na rike rigarsa cikin rarraunar murya nace "Saghir, ni ban hana ka aure ba, ni ba zan ma damu dan kayi aure ba ka auri duk matar da kake so Saghir but please ni ma ka barni in koma gurin wanda nake so" yace "ohh, wai dama har yanzu baki hakura da yaron nan ba, dama a saboda shi ne kike tayi min wannan wulakancin? Yaron da aka ce min babu wanda yasan inda yake watakila ma ya zama dan shaye shaye ko dan fashi amma ke shi kike so when you already have me?" Nace "so guda daya ne Saghir, kuma Sadauki naje yi wa shi" ya warce rigarsa daga hannuna yace "then you will rot here. Ke da Sadauki sai a mafarki" ya juya ya fita ya barni. Na jingina kaina da jikin bango ina jujjuya kan, sai kuma na zame na kwanta a gurin akan dandaryar tiles. Ina ji hadari ya hado aka fara ruwan sama mai karfi, tiles din dana ke kai ya dauki sanyi amma na kasa tashi ballantana in koma gado in lulluba, ji nake jikin nawa bashi da wani amfani dan haka lullube shima bashi da amfani. Anan assuba ta same ni, sai da akayi assalatu sannan na tashi da jan kafa na shiga toilet na dauro alwala na gabatar da sallah ina kara kai kuka na a gurin ubangiji na dan nasan shi kadai ne zai iya yi min magani, nasan yana gani na yana kuma jina kuma nasan bai manta dani ba dan yafi kowa sona.
A ranar na tashi da mummunar mura da tari, kuma nasan hakan yana da dangantaka da kwanan da nayi akan tiles. Na shirya Subay'a da kyar, na sha magani na kwanta daga nan kuma sai zazza蓳i ya rufe ni. Daga nan sai ciwo, zazza蓳i ciwon kai mura da tari amma Saghir ko leko inda nake baiyi ba ballantana yaga halin da nake ciki duk kuwa da cewa na tura subay'a ta gaya masa yafi a kirga. A haka nayi ta ciwo na, da kansa yake shirya subay'a ya kaita school kuma ya dauko ta yasiyo musu abinci suci kayansu. Ni kuwa sai naji yunwa tana neman illata ni zan tashi insha tea in koma. Har na kwana biyar a haka.
Ranar Thursday na kira Inna na roke ta ta turo min Asma'u tayi min weekend dan ta dan taya ni wasu abubuwan, na gaya mata bani da lafiya ne. Friday sai gasu sunzo har da Inna, wannan shine zuwan inna gidana na uku tunda nayi aure kuma duk duba ni take zuwa yi in bani da lafiya. A kasa muka zauna dan bata taba hawa sama in tazo, tana tayi min mitar yadda duk nabi na kara ramewa tana cewa me yasa banje asibiti ba? Ni kuma sai nayi shiru kawai dan ina ganin fada mata cewa Saghir ba zai kaini ba bashi da amfani tunda nasan ko tayi masa magana ba zai ji ba sai dai kawai ranta ya baci. Sai kuma nayi tunanin ko ingaya mata zancen Sadauki? Sai dai bani da tabbas din yanzu menene ra'ayinta akan Sadaukin bansan yadda zata dauki kasancewar sa a matsayin ogan Saghir ba. Na dai san tana nemansa akan gadon Ummah na gida dan haka dole zan gaya mata amma ba yanzu ba, sai na samu damar magana dashi tukunna first.
Asma'u ce ta tashi ta gyara min gidana tsaf, har dasu turaren wuta, sannan ta shiga kitchen tayi mana girki muka hadu muka ci tare harda Subay'a. Sai naji dadi sosai, maybe ciwon nawa harda rashin wanda zanyi wa magana da kuma yunwa. Ana yin la'asar Inna tayi sallah sai ta tashi ta fara shirin tafiya. Na fara mita "Inna daga yin la'asar? Ki bari mana sai kamar karfe biyar haka sai ki tafi" tace "uhm uhm, wannan gari na damina yanzu sai kiji ruwa ya sauko. Bana son mijinki yazo ya same ni a gidan nan" muka yi tayi mata dariya ni da Asma'u dan mu a gurin mu kamar babu komai dan sun hadu, ita kuma al kunya ce irin ta fulani.
Ai kuwa kamar ta fada da bakin mala'iku sai ga ruwan sama ya sauko, da yake muma daki babu wanda yasan ma da hadarin sai kawai zubar ruwa mukaji. Inna ta fara salati mu kuma muna dariya "yau kwana ya kama Inna a gidan Adda" inji Asma'u, Inna tace "kwana bai kama ni ba, ai komai dare ruwan nan in ya dauke sai na tafi gida, balle ma ba lallai ne ya kai daren ba". Wasa wasa ruwa har magrib, har isha yin sa ake kamar da bakin kwarya, Inna ta shiga dakin kasa inda Asma'u ta gyara dan anan take zama duk sanda tazo gidan saboda basu fiya shiri da Saghir ba, anan tayi sallolinta duk muka zauna muna hira ita dai tana ta bacin rai. Nace "Inna ki bari idan Saghir ya dawo sai ya kai ki a mota tunda ba kya son kwana" ta girgiza kai "ni da bana son ma yasan nazo? Bazan shiga motarsa ba. Allah ya tashe mu lafiya sai in tafi da safen".
Na dauki Subay'a muka tafi sama saboda naji dadin jikina sosai, na tafi da niyyar inyi mata wanka nima inyi, Asma'u kuma ta tafi kitchen tana gyara abinda muka bata. A lokacin Saghir ya dawo, yaga motsin Asma'u a kitchen sai ya leka, yana ganin ta yace "ke! Yaushe kika zo gidan nan?" Ta dan tsorata saboda bata san shigowar sa ba tunda shi dama ba sallama yake yi ba, ta gaishe shi sannan tace "dazu muka zo duba Adda, ni da Inna" yace "ita Addan taki ce tace muku bata da lafiya? ina gwoggon take?" Ta nuna masa daki a ranta tana tunanin yau Inna zata sha kunya in suka hadu da Saghir.
Ya tura kofar ya shiga, Inna tayi saurin tashi duk ta diririce saboda ganin sa haka a cikin dakin gashi tana kwance dan ma dai ba kaya ta cire ba, ya tsaya a tsaye yace "gwoggo Amina barka da zuwa, ashe waccan makaryaciyar cewa tayi bata da lafiya?" Inna tace "uhm uhm Saghir ba karya tayi ba, kowa yaga Diyam ai yasan bata da lafiya" ya daga kafada yace "to ai sai kuzo ku tafi tun kafin dare ya sake yin nisa kuma" Inna tace "mu tafi kuma?" Asma'u data shigo tace "dare ai ya riga yayi, ballantana daren damina? Anan zamu kwana da safe Inna zata tafi ni kuma zan zauna sai sunday" ya girgiza kansa "no, kuzo ku tafi yanzu. A Kano ai dare baya yi ko sha biyu kuka fita zaku samu abin hawa" ya ciri dari biyar ya ajiye a kusa da Inna "gashi ku hau adaidaita" ya juya ya fita.
Suka tsaya cirko cirko suna kallon juna, Asma'u tace "hamma Saghir bashi da mutunci Inna, bara inje in gayawa Adda tayi masa magana, yanzu ina zamu fita a wannan unguwa tasu duk kango? Ga shi har yanzu yayyafi ake yi" Inna ta girgiza kanta, "kar ki gaya mata. Dauko mayafin ki mu tafi. Allah yana nan ai shi zai kaimu gida lafiya" Asma'u bakin ciki ya ishe ta, Inna ma wani irin zafi zuciyarta take yi mata amma bata son gaya wa Diyam, shi da yayi din ai yasan ba dai dai bane kuma Diyam sai dai ta bata ranta kawai amma ba zata hana shi abinda yayi niyya ba, tasan ko bare Diyam ta aura ba zai musu wannan wulakancin ba ballantana 蓷an yayanta, 蓷an yayan mijinta. Ko Sadauki Diyam ta aura ba zai wulakanta Inna ba.
Mayafan su kawai suka dauka, lokacin karfe goma har ta gota Asma'u dan bakin ciki ko kayanta bata dauka ba suka fita ni ina can ban sani ba, ga duhu ga yayyafi anayi ga uban sanyin da yake kadawa. A bakin gate suka yiwa maigadi sallama, yace "Hajiya tafiya a cikin ruwan nan? Ku bari mana sai da safe ko kuma ayiwa mai gidan magana ya kaiku a mota" Asma'u tace "maigidan ai shi ya kore mu kuma yafi kowa sanin yana da mota".
Hanya duk ruwa ya kwanta haka suka ringa haskawa da wayoyinsu suna tafiya karnuka suna tayi musu haushi, babu alamar mutum ballantana abin hawa har suka fita bakin titi. Suka tsaya suna ta karkarwar sanyi amma babu abin hawa babu alamun sa. Asma'u ta fara kuka "Inna mu koma mu gaya masa bamu samu ba. In baya son mu kwana a gidan sa ba sai ya kaimu gida a mota ba? Ai muma muna da gidan ba'a titi muke ba" Inna dai bata ce mata komai ba. Can bayan sun gaji da tsaiwa sai suka fara tafiya a kafa suna saka ran maybe in sunzo round din yan kaba zasu samu adaidaita a can, ko babur ne ma in suka samu hawa zasuyi in dai zai kaisu gida. A lokacin sha daya na dare har ta wuce. Suna cikin tafiya ne wata mota ta tsaya a bayansu, suka juyo suna tunanin ko taimako ne tazo musu amma sai ji suka yi anyi musu fito, daganan suka gane yan iska ne dan haka suka kara sauri. Aka sake biyo su a baya aka ce "yan mata ji mana" Inna ta kankame hannun Asma'u suna sauri kamar zasu tashi sama amma sai motar ta sha gabansu, aka haske musu fuska da fitila sai wani yace "ashe ma tsohuwa ce da yarinya. Kyakykyawar yarinya" Inna ta tura Asma'u bayanta a lokacin da maza biyu suka fito daga motar. "Haba baba, Menene na boye ta? Rage mata hanya kawai zamuyi fa" dayan yace "kema in kina so sai mu rage miki hanyar amma a boot" suka kwashe da dariya sannan suka yo kan su Inna a tare. Da gudu su Inna suka diba, Asma'u tana gaba inna tana binta a baya mazan suna binsu a baya, daya yace "kunga tsohuwa ita ma ta iya gudu? Lallai itama da sauranta ashe". Basu yi wani nisa ba suka cimmasu suka kama su, Asma'u tana ta ihu, Inna tana ta rokon su su rabu dasu "me muka yi muku yaran nan? Ku sake ta dan Allah marainiya ce" daya yace "nima maraya ne, kinga mun dace kenan".
Sanda suke tisa keyar Asma'u cikin mota ne wata mota ta hawo ta bayan su a hankali, har ta gibta kuma sai tayi reverse da sauri ta tsaya. Asma'u ta fara kokawa dan ta samu karfin ganin taimako yazo mata wannan ya hana su tayar da motar har na cikin bakuwar motar ya fito da sauri ya taho gurinsu. Wanda yake rike da Asma'u ya fara zarowa daga motar yayi masa naushi biyu take sai ga jini a gaban rigarsa. Ba shiri ya sake ta ya shige motar, wanda yake seat din driver yayi saurin tayar da motar dan yana gudun karbar nasa rabon suka bar gurin a guje. Asma'u ta fadi a gurin tana mayar da numfashi cike da tsoro sannan ta juya tana kallon wanda ya taimaka mata, sai taga Inna ma shi take kallo amma maimakon tsoro mamaki ne kawai a rubuce a fuskarta. "Sadauki?" Ta fada da rawar murya "Sadauki!" Asma'u ma ta fada, tabbas, wannan fuskace da baza ta manta ba duk kuwa da cewa rabon data ganshi tun tana shekara tara a duniya yanzu kuwa shekarar ta goma sha shida. Sai ta mike da gudu ta tafi ta rungume shi. "Yar Asama" ya fada yana rabata da jikinsa, fuskarsa dauke da murmushi.
Ni ina can ina yiwa Subay'a wanka naji shigowar motar Saghir, har na gama yi mata wankan na shirya ta nima na shiga nayi na fito na tarar har ta yi bacci na shimfida sallaya na tayar da sallah, sai dana idar sannan na sauka dan in tabbatar su inna basa bukatar komai kafin in kwanta, amma sai naga dakin ba kowa, kitchen ma haka. Wasa wasa na chaje gidan amma babu su babu alamun su, hankalina ya fara tashi na koma sama na dauko waya da niyyar kiransu amma naji ance min "your account is not sufficient to make this call" bank da kudi, da zan kira Inna jiya ma ranta nayi a network dina. Hankalina in ya kai dubu duk ya tashi a lokacin dole na tafi dakin Saghir da sauri na fara buga masa kofa. Ya bude ya tsaya yana kallona nace "su Inna, ban gansu ba, ka bani aron wayarka dan Allah in kira su" yace "sun tafi gida. Ni nace su tafi. Da iznin waye kika gayyato min mutane zuwa gidana?" Na fara girgiza kai na saboda mamaki nace "mutane? Su Inna da Asma'u ne mutane?" Yace "ohh, aljanu ne ba mutane ba?" Ban jira sauran maganar saba na shiga dakina da sauri na dauko hijab dina, nayi hanyar stairs, nima gidan zan bari tunda har zai iya ya kori uwata daga gidan nan toni zaman me zanyi a cikin sa? Da sauri naga yazo ya wuce ni ya riga ni sauka, ban fahimci me yake yi ba sai dana ganshi a bakin kofar fita daga pallon, ya saka key ya rufe kofar sannan ya juyo ya wuce ni hau stairs yana kallona yace "nasan in na ce miki in kika fita a bakin auren ki da sauri zaki fita tunda abinda kike so kenan".
Na bishi a guje ina ihu "ka bude min kofa Saghir, ka bude min kofa nace" sai ma ya shiga dakinsa ya rufe kofa ya rabu dani. Na dawo kasa da sauri ina neman hanyar fita amma babu, duk windows din gidan akwai burglers a jiki, kofar kitchen ta baya kuwa dama tun ina amarya data lalace har yau ba'a gyara taba mun dai a amfani da ita. Sai na kama kuka ni kadai kamar mahaukaciya ina zagaye gidan. Ji nake a raina gwara in kwana a titi a ranar akan in sake kwana a gidan Saghir. A haka har karfina ya kare na zauna na jingina kaina da jikin kujera ina ajjiyar zuciya. A raina ina aiyana abinda zanyi wa Saghir in wani abin ya samu su Inna.
A lokacin ne waya ta tayi kara, nayi saurin dauka na duba naga sunan Inna da sauri na amsa nace "Inna me yasa zaku tafi a cikin daren nan? Kuna ina Inna?" A nutse naji muryar ta, hakan ya kwantar da hankali na sosai tace "ki daina kuka Diyam, muna gida mun iso lafiya" nayi ajjiyar zuciya nace "alhamdulillah. Inna hankali na ya tashi sosai" sayi shiru sai kuma tace "Diyam, Sadauki ne ya kawo mu gida. Ba dan Sadauki ba Diyam yau da bansan me zai same mu ba. Sadauki ne ya taimake ni Diyam a lokacin da Saghir ya wulakanta ni".[2/13, 10:26 PM] +234 818 247 0922: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Two: A backlash
"Sadauki?" Na maimaita cikin tsananin mamaki "a ina Sadaukin ya ganku?" Sai ta bani labarin abinda ya faru dasu bayan sun bar gidan. Wannan ya kara ruda tunani na, me Sadauki yake yi a wannan hanyar a wannan lokacin har ya gansu ya taimaka musu? Duk da bansan a wanne hotel yake zaune ba amma nasan babu hotel a kusa damu, sannan unguwar mu wajen gari ne ballantana inyi tunanin ko wani abu ya fito nema kuma ma ai mutane masu kudi irinsa ba zasu fito neman abu ba sai dai suyi order a kai musu har inda suke. Tabbas ina bukatar yin magana da Sadauki. Amma dai ko menene yake yi a gurin am greatful da taimaka musu da yayi saboda I can only imagine irin horror din abinda zai faru dasu da bai zo din ba, wannan kuma sai ya kara hura wutar kiyayya da nake yiwa Saghir saboda shine ya kusa jefa su cikin wannan halin. Naso in tambayi Inna a game da Sadauki amma sai tayi min sallama tace dare yayi sai gobe zamuyi magana. Anan palo na karasa kwana saboda saman gani nake kamar na kara kusa da Saghir.
Sa safe Subay'a ce ta tashe ni tana neman abinci, da yake ban samu nayi bacci sosai ba shi yasa na makara. Na jata muka shiga dakin kasa mukayi sallah tare sannan muka shiga kitchen na dora mata noodles na soya mata kwai, ina cikin aikin Saghir ya shigo Subay'a ta tafi gurinsa da gudu ya dauke ta suka tsaya a bakin kofa yana kallona yace "me ake dafa mana ne?" Ko kallo bai ishe ni ba, shi har yana da karfin halin pretending kamar babu abinda ya faru? Subay'a ce ta bashi amsa, sai yace "Subay'a mommy fushi take yi da Daddy saboda yace zaiyi aure" na juyo na watsa masa harara, ni har na manta ma da yace zaiyi aure. Ina jin Subay'a tana tambayarsa menene aure, na bar musu kitchen din sai ya biyo ni yana cewa "wai duk kishin ne haka? Ni na taba ganin anyi kishin wanda ba'a so?" Har zan wuce kuma sai na dawo na karbi Subay'a daga hannunsa nace taje kitchen ta dauki abincinta taci sannan nace masa "Saghir ko matan duniya zaka aura ko a tafin kafar Halima. Ni din ce dai ba zaka samu zuciya ta ba wallahi. Kuma su Inna sunje gida lafiya babu abinda ya same su, sun samu wani bawan Allah wanda yasan mutunci da darajar mutane ya taimaka musu kuma ya kaisu har gida a mota, bawan Allahn da basu hada dangantaka ta jini dashi ba" yace "ohh there is that, ashe fushin biyu ne" wato shi a nufinsa har ya manta da abinda yayi. Yace "to yanzu wanene bai san darajar mutane ba? Ni mutum ne mai ka'idoji kin sani kuma, ni bana son a shiga rayuwata sam bana son ake kawo min mutane cikin gidana" nace "gida? Amma dai kasan muma muna da gida ko? Kasan ba'a titi muke ba ko?" yace "sai su zauna a gidan naku kar su zo min nawa gidan, as simple as that" na girgiza kaina nace "ni Saghir bani da sauran karfi, na zuciya da na jiki da zanyi fada da kai, ka fadi duk abinda kake son fada ka kuma yi duk abinda kake son yi. Duniya ce, akwai ranar kin dillanci kuma ina sanar maka da cewa tana daf da zuwa" ban jira abinda zai ce ba na haye sama. Ina jinsa ya bude kofar palo ya fita, na leka naga shi da Subay'a ne suka fita a mota, na sauko kasa da sauri na tura kofa naji a rufe, wato rufe ni yayi daga waje ya tafi da key din.
Ina zama Inna tana kira na, dama tun dazu nake ta zuba idon ganin kiranta amma sai naji muryar Asma'u tace "Adda inna fa kuka take yi tun da muka dawo jiya da dare, tun da taga Sadauki take kuka na rasa dalili" na gyada kaina, ni nasan dalilin, nace "me Sadaukin yace sanda ya dauke ku?" Tace "baice komai ba fa, kawai tsokana ta yayi tayi har muka zo gida. Inna tace masa tana son ganin sa sai yace zai zo watarana" na tambayeta "ya tambaye ki ni?" Tace "a'a" na lumshe ido ina jin hawaye yana taho min. Idan ni ce na hadu da yaya ladi misali nasan abinda zan fara tambayarta shine Sadauki. Ko dai Sadauki ya daina so nane? Duk da dai Saghir yace min baiyi aure ba amma for all I know maybe yana da budurwa yanzu, maybe ma an kusa bikin. Maybe ma yaruwarsa zai aura a Maiduguri.
Nace da Asma'u ta kira Mama ta gaya mata abinda ya faru, ni ba zan iya zuwa in lallashi Inna ba saboda Saghir ya rufe ni a gida. Na san kuma yanzu inna tana bukatar wanda zasuyi magana dashi, musamman wanda yasan abinda tayi wa Sadauki da shi kuma sakayyar da yayi mata.
Ta barshi a titi a lokacin da yafi bukatar gida, shi kuma sai ya dauko ta daga titi ya kai ta gida a lokacin da tafi bukatar hakan.
Washegari Sunday, Saghir ya fita sai gashi ya dawo yana washe baki, ko kula shi banyi ba dan ban damu da insan me ya saka shi farin ciki ba amma sai ya zauna yana cewa "subay'a daddyn ki zai tafi kasar waje, me kike so in siyo miki?" Ta mike da murna tana tsalle tana yi masa list din kaya, shi kuma yana ta dariya, sai ya kalle ni yace "ki hada min kaya, gobe zan tafi oga ya tura ni zanyi signing contract da wani company a can" na dauke kai kamar ban ji shi ba sai yace "dama nan da two months ne tafiyar nan tazo, da da amarya ta zan tafi. Ohh ban fada miki ba ko? Nan da wata biyu ne aure na fa" nace "to ka daga tafiyar mana sai anyi bikin? Ohh na manta, ashe bada kudinka zaka yi tafiyar ba da kudin oga ne kuma dole sai abinda oga yace sannan zakayi tunda kudin sa ne. Mtsww i pity you" da naga dai neman magana yake yi sai na tashi na bashi guri saboda ni bana son rigima dashi a gaban Subay'a, amma kuma sai na samu zuciya ta da jin haushin Sadauki na budawa Saghir da yake yi.
Shi ya hada kayan tafiyar sa da kansa, da safe ya turo Subay'a ta kira ni naje na tsaya a bakin kofa yace "rashin kunyar ki, da rashin biyayyar ki shi yasa har yanzu auren mu yaki daidaita, da ace kin kwantar da kai, kin bini yadda nake so da ba karamin jin dadi zakiyi tare da ni ba. Kinga wannan tafiyar ma oga mu biyu ya biya wa, ni dake, yace in tafi da matata saboda wata daya zanyi kar in zauna gwauro a can, kinga da sai muyi tafiyar mu ni da ke da Subay'a but I guess I will have to go alone" ya ajiye kudi a kan mirror "ga kudin cefane nan, kinsan ni ina tsoron Allah dan haka ina kokarin sauke hakkin ki da yake kaina. Ban yafe ba, in kika fita ko da kofar gida ne indai ba abinda ya shafi makarantar Subay'a bane ba, sai kuma rashin lafiya, Allah yana kallonki in kika ci amana ta in bana nan" nayi murmushin takaici kawai, akwai amsoshi da yawa a raina wanda nake so in bashi amma ganin Subay'a yasa nayi shiru har ya dauki jakarsa ya fita yana cewa "gwara mutum ma ya dan bar kasar ya sarara na kwana biyu".
Tafiyar Saghir da kwana biyu Alhaji Babba ya kira ni a waya, I can't remember last sanda ya kira ni. Na dauka na gaishe shi sai naji muryarsa wani iri yace min "Diyam ki zo gida ina nemanki dan Allah" sai naji wani iri da yace min dan Allah, duk da dai Alhaji Babba yayi sanyi sosai tunda yanzu kusan hannu baka hannu kwarya suke zaune a gidan, bashi da komai sai yan abokai da suke taimaka masa da kuma kawu isa shima da yake dan bashi wani abu, duk sana'ar daya kama sai ta rushe, kullum muka je gidan yana ta cewa makiya ne suka sako shi a gaba ni kuwa deep down nasan inda matsalar dukiyar Alhaji Babba take, kudin mune da yaci, dukiyar marayu daya handame ya hada da tasa dukiyar da yasha wahala gurin nema dan haka sai yayi asarar har tasa dukiyar gabaki daya.
Na tambayeshi ko lafiya? Sai yace inzo dai kawai yana nema na. Na shirya ni da Subay'a muka tafi. Bayan mun gaisa da mutanen gida ne muka tafi palonsa na ganshi daga shi sai riga yar shara wadda duk tayi datti. Na durkusa na gaishe shi sai ya dauko wasu takardu ya miko min. Na bude a nutse ina dubawa a dan ilimi na sai na fahimci takarda ce daga kotu ta sammaci, mai kara shine 'Aliyu Usman Kollere" Wanda ake kara kuma "Alhaji Muhammadu Kollere" sai kuma sauran takardu da suka kunshi photocopy na takardar fili belonging to Aliyu Usman Kollere, da kuma takardar garage din Baffa, sannan anyi list na duk abinda yake ciki da kudinsa da kuma estimate na kudin business din gabaki daya, sai kuma akayi jimullar kudin wanda yawansu sai da yasa na kama baki na. Yanzu wannan ne dama kudin da Alhaji Babba yaci na mu? Wannan shine kudin da akace anyi min kayan daki dasu? Amma mai yasa alhajin yake nuna min a yanzu?
Kamar amsar tambaya ta sai naji yace "Diyam kinga abinda tsohon saurayin ki zaiyi min ko? Yaron da Usuman ya rike kamar shi ya haifeshi kinga sakayyar da zaiyi mana ko? Wai ya kaini kara wai naci dukiyar marayu to dukiyar ta ubansa ce? Ina ruwansa? Kudin nan ba aure nayi miki dasu ba? Ai na gaya wa Amina tun a lokacin kuma ra amince. Takamarsa shine da kason uwarsa a ciki shine yake so yayi min tonon silili" ni dai na ajiye takardun ina kallonsa har ya gama fadan sa sannan kuma sai yace "an ce min in na saka kika yi masa magana zai iya ya janye wannan maganar" na gyada kai, so that's it. Wannan shine dalilin da yasa aka shigar dani maganar. Nace "ni Alhaji bansan inda Sadauki yake ba ballantana inyi masa magana, kuma ma ba lallai ne ya saurare ni ba. Amma shi ne ya kawo takardun?" Yace "ina fa? Babu wanda yasan inda yake fa, lauyoyi ya dauka har guda uku, su suka shigar da karar alkali kuma ya aiko min da sammaci" ba gyada kaina, wato basu san waye Sadauki a yanzu ba. Nace "to ni Alhaji in zanyi masa ma maganar ai bansan inda zan same shi ba" yace "Amina ma tace bata san inda yake ba. Kuma ko number dinsa babu a jikin takardar sai ta lauyoyinsa" na dauki takardar ina kara dubawa sai naga numbobin, na dauki daya a waya ta nace "idan na same shi me zance masa?" Ya gyara zama yace "ki gaya masa ni ba matsiyaci bane ba, kaddara ce ta sauka a kaina da kuma makiya da suka sako ni a gaba wannan ne yasa a yanzu bani da kudin da zan bashi, amma kice masa yayi hakuri muyi aggrement zanke biyansa a hankali a tsakanin mu ba sai munje kotu ba" nace "shikenan Alhaji, zanyi kokarin ganin yadda za'ayi a fahimci juna" yayi ta saka min albarka sannan yace "ashe mijinki yayi tafiya? Sai da aka kawo takardar nan jiya na neme shi sannan naji ma wai baya kasar".
Na fito ina ta mamakin halin Saghir. Sai kuma na koma lissafin wannan lamari. Me Sadauki yake after? Na tabbatar ba kudin yake so ba dan yafi karfin wannan kudin a yanzu. Sai kuma na fahimci wannan shine dalilinsa na tura Saghir kasar waje saboda baya so yayi blowing cover dinsa ta matsayin ogan Saghir, duk da dai yadda ya shirya kai karar ba lallai ne ma a ganshi ba dan lauyoyinsa sun isa su wakilce shi amma me yake bukata?
Sai dana koma gida sannan na kira number din lawyer din. Ya dauka na gaishe shi ya amsa sama sama sai nace dan Allah ina son magana da client dinsa Aliyu Usman Kollere, yace "what for? Bana bada contact din client dina gaskiya" nace "na fahimta, but please ka gaya masa in ya tuna Halima Usman Kollere to tana son magana dashi" ya amsa zai fadi sakona sannan ya katse wayar. Jira jira har dare babu amsa, haka nayi ta duba waya ina karo volume wai dan kar a kira banji ba.
Sai safe around ten sannan kiran ya shigo, lawyer din ne dai yace "yace menene? Ki gaya min sakon sai in gaya masa" na runtse idona ina jin duniyar ma duk tayi min zafi nace "shikenan. Tell him nace dashi nake son magana ba da kai ba in bashi da guts din da zai saurare ni shi kenan na rike magana ta" na kashe watar ina jin zafin Sadauki a raina. Wato bama yason magana dani, baya son gani ba, ya manta dani yake nufi ko me? Ya manta alakar mu? Ya manta alkawarin mu? He said he will love me forever yanzu har forever din tayi? Amma sai wata zuciyar take tuna min da matsayi na na matar wani, wata zuciyar tana so in yi wa Sadauki uzuri na kin saurata ta da yayi, na gudu na da yake yi.
Around 12 wani kiran ya shigo wayata, saida zuciyata ta buga ganin sabuwar number, sai na samu kaina da rike wayar amma na kasa amsawa har ta kusa katsewa sannan na dauka a hankali na kai kunnena idona a rufe nayi sallama, shiru at first, sannan yace "kina son magana dani, ina jinki" muryar Sadauki, as clear as ever. Na hadiye abinda yaki tafiya a makogwaro na sannan nayi kokarin nima in yi irin nasa nace "maganar Alhaji Babba, yana son ayi negotiation. Can you do that?" Ya danyi shiru sannan yace "come to my office tomorrow morning, you know where it is" daga nan ya katse. Sai na zauna da waya a hannu ina mamakin wai da Sadauki nayi magana yanzu, but it sounded as if da wani stranger nayi maganar.
Ranar bana jin nayi baccin awa daya. Da assuba na tashi nayi wanka nayi sallah sai kuma na zauna ina kallon agogo yana ta lakaki yaki yin sauri balle gari ya gama wayewa. Na tashi Subay'a na shirya ta sannan nima na shirya tana ta tambayata inda zanje, na bata breakfast nima na hada tea na kurba amma sai ya tsaya a makogwarona yakasa wucewa. A haka har lokacin kaita school yayi, na kaita sai kuma nayi tunanin is too early inje office din Sadauki dan haka na dawo gida na cigaba da kallon agogo har saida ten tayi sannan na fita. Ina gayawa mai adaidaita Abatcha Motors sai yace "okay companyn motocin nan ko?" Sai da muka isa gurin sannan na kare wa building din kallo, so all of this is owned by Sadauki, how? Na shiga trying not to act like yar kauye, shi kansa building din anyi shine da shape din mota, haka round about din da yake tsakiyar gurin shima siffar mota ce dashi. Sadauki and cars bansan wacce irin soyayya ce a tsakanin su ba. Ina shiga reception din sai na tuno da ranar da akayi party, nayi tunanin ko wasu zasu gane ni? Amma kuma ranar babu haske sosai dan haka ba lallai bane su gane fuskata. Naje desk din receptionist, kafin inyi magana tace "Halima?" Na amsa mata sai ta dauki waya tayi magana a ciki sannan ta nuna min bene tace in hau, na hau na tarar da wata tana jira na sai ta bude min wata kofa tace in shiga, na shiga na tarar da wata mata da name tunanin secretary ce, kyakykyawar gaske gata ta sha make up sai kamshi take zubawa, ta yi min murmushi sai kawai naji ina jin haushinta ba tare da ta yi min laifin komai ba, ta wuce gaba sai naga kamar tana sane take murguda min bombom ta bude min wata kofa da card din hannunta na shiga sannan ta rufe.
Yana zaune a bayan katon table din gaban sa, as majestic as ever, bai ko dago kai ya kalle ni ba yaci gaba da rubutu a takardar gabansa ni kuma ina tsaye sai daya gama sannan ya dago fuskarsa blank yace "welcome Madam, have a seat please" naji kamar in juya in fita daga office din, nayi nadamar dana sani banzo ba amma ina bukatar amsa, ina bukatar ji daga bakinsa cewa ya manta da first twenty years of his life. Na zauna a kan cussion chairs din da suke jere a office din. Ya mike tsaye, sai naga ya kara cika min ido da kwarjini da girma baki daya ya zagayo ya zauna a kujerar gaban table dinsa sannan yace "kince Alhaji Muhammadu ya turo ki akan wani negotiation, ina jinki" naji wani sabon bacin rai, ni na ma manta abinda ya kawo ni kenan, sai kawai hawate ya fara bin fuskata. Nace "abinda zaka ce ma kenan? Irin karbar da zakayi min kenan? Sadauki nice fa Diyam, how can you even......call me Madam?" Sai ya mike tsaye ya juya bayansa ya saka hannu a aljihu yace "menene sakon da Alhaji yace ki fada min?" Sai na mike na nufi kofa da sauri ina goge hawayen fuskata, bai ce min komai ba har naje na kama kokawa da kofa amma taki budewa, na juyo ina kallonsa sannan yace "ba'a fita daga office dina sai nayi wa mutum izni" sai na dawo da baya da sauri na dauki wasu magazines na motoci na jefa masa, na debo tarkacen files din kan table dinsa suma na yi ta dukansa dasu har takardun suka tarwatse a gurin amma ko motsawa baiyi ba, na durkusa a tsakiyar gurin na kama kuka sai ya dawo ya zauna akan kujera yace "menene sakon da zaki gaya min?" Sai dana gama kukana sannan na tashi na zauna na goge fuskata nace "why? Sadauki why? Me yasa kame treating dina haka?" Yace "ya kike tsammanin zanyi treating mayar employee na?" Nace "shikenan? Matsayina kenan? Matar employee dinka? Me yasa ka dauke shi aiki ma? A ina ka sami wannan kudin kuma? I need answers Sadauki, I need to talk to Sadauki not this Mr Abatcha" yace "zaki samu answers dinki in due time. Now me Alhaji Babba yace?" Na goge hawayena nace "nasan kasan bashi da kudi yanzu, bashi da kudin biyanka ko da kuwa kotun koli zaka kaishi, dan haka I think you are just wasting your time" yace "really? To tunda bashi da kudin biya na fili na da gadona sai ya shirya zuwa prison for it. Kullum takamarsa kenan, kullum maganar sa itace zai saka a rufe ni, lokacin yana da kudi ni kuma bani dashi. Ki je kiyi masa albishir da cewa the table have turned, yanzu nine zan rufe shi" na bude ido ina kallonsa nace "you don't really mean that, me zakayi da kudin? Me zakayi da filin Sadauki look at this" na fada ina nuna office din nasa "zaka iya siyan hundreds of wannan filin, kafi karfinsa yanzu" yace "Baffa ne ya siya min remember? I was suppose to build us a house a kan filin nan, gidan mu ni da ke da yayan mu remember?" Sai kuma ya mike ta sake juya bayansa yana kallon window. Mun jima a gaka sannan nace "kayi tunanin abinda Baffa zai so, Alhaji Babba yayansa ne uwa daya uba daya ba zai so ya ganku a court dakai dashi ba, ba zai so yaga ka rufe masa dan uwansa akan kudi ba" ya juyo yana kallona yace "kamar yadda ba zai so a cire ki daga makaranta exactly 40 days bayan rasuwar sa ayi miki aure ba, kamar yadda ba zai zo a siyar da abinda ya kwashe rayuwarsa yana building abar iyalinsa da hamma ba" sai yakuma juya wa sannan yace "kamar yadda ba zai so a raba mu ba" na runtse idona ina jin wound fin zuciyata yana dawowa sabo, kewar Baffa na tana lullube ni, mun jima haka sannan yace "tell Alhaji Babba nace yana da options guda biyu, na daya shine ya bar mana gidansa da yake ciki tunda shi kadai ne yanzu abinda ya rage masa, na biyu kuma shine ya tafi prison for the rest of abinda ya rage na rayuwarsa"
Na mike tsaye, "Sadauki, ubangiji ma yana son rama sharri da alkhairi, kamar yadda kayi wa inna, dan Allah ka bar maganar nan, Allah ma daya halicce mu muna yi masa laifi kullum amma idan muka durkusa muka roke shi gafara sai ya yafe mana" ya juyo yana kallona, his eyes shining, yace "then tell him yana da third option, yazo ya durkusa ya roke ni gafara, ya saka gwuiyoyinsa a kasa ya roke ni in yafe masa kamar yadda na saka guiwowina a kasa na roke shi ya bani aurenki ya hana ni, ya durkusa kamar yadda na durkusa na roke shi kar ya aura miki that monster he calls a son amma duk da haka ya aura miki shi. Yes, I want him to cry and beg kamar yadda nayi in yaso in naki hakura duk da yayi haka sai yaji shima irin yadda naji".
Sadauki yayi tsauri da yawa ko? Lol
Not edited
[2/14, 10:05 PM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Three : Heartless
Raina ya kara baci, ina mamakin anya kuwa wannan Sadauki nane? Sadaukin da na sani will never do that amma kuma sai nayi wani tunani. Yes, Sadauki yana da kirki da kyawun hali sosai amma bashi da yafiya, musamman idan akan abinda ya shafe ni ne Sadauki bai taba daga kafa ba ko da kuwa waye ya taba nin indai ba Inna ko Baffa ba, na tuno ranar daya doka wa yaya Mukhtar ball aka a gaban Inna. Sadauki bashi da tsoro ko kadan tun a lokacin da bashi da komai ma, ballantana kuma yanzu da yake da masu garin.
Nace "abinda kake so kenan? Abinda kake after kenan? Revenge?" Ya girgiza kai "this is not revenge, this is justice" nace "wanne justice din ne kuma wanda yafi wanda Allah ya riga yayi? Shin in kayi haka Sadauki ka gode wa Allah kenan? Kaga kuwa halin da Alhaji Babba yake ciki a yanzu? Ka kuma duba kaga halin da kai kake ciki a yanzu, kai kanka ka fada, the table have turned, menene kuma saura? Shin in ka yafe wa Alhaji Babba mai zai ragu daga jikin ka? Sai ma daraja da hakan zai kara maka a gurin ubangiji. Yanzu in ya siyar da gidansa ina zai kai iyalinsa?" ya bar inda yake tsaye ya zagawa gurin kujerar sa ya zauna yace "sai su dawo gidan ku ku zauna tare, ai naga kuna da bene, sai su zauna a sama ku kuma a kasa" na saki baki ina kallonsa sai ya danna wani button a jikin table din sai naga kofar dana shigo ta bude, ya kalle ni yace "goodbye, Diyam" na tsaya kawai ina kallonsa ina girgiza kai, I can't believe Sadauki yayi tauri har haka, sai na je na tsaya a gaban table dinsa nace "I don't like this Mr Abatcha da nake gani a gabana, I want my Sadauki back, I want my brother back" sai na juya da sauri na bar office din.
Ina jin matar nan ta waje tana yi min magana amma ban ma fahimci abinda tace ba ni dai na gyada mata kai kawai na fita da sauri. Da saurin kuma na karasa wajen gate na tari abin hawa na shiga muka tafi. Sai da muka bar gurin sannan na saki kukan da nake rikewa, ma dauka hawaye ne kadai nake yi bansan ya fito fili ba sai da naji drivern yace "yammata kiyi hakuri, komai na duniya mai wucewa ne watarana sai kiga kamar ba'ayi ba" a goge hawaye na ina jinjina maganar sa, watarana zanga kamar ba'ayi ba? Yaushe?
Sai dana je gida sannan nayi realizing wani abu guda daya, ni da na tafi gurin Sadauki da niyyar samun answers amma ban samu ko daya ba sai karin tambayoyi da na debo wa kaina. Na sani Alhaji Babba ya zalunce ni kuma ya zalunci Sadauki kuma har cikin raina ban damu ba in wani abin ya same shi a saboda abinda yayi, abinda na damu dashi shine Sadauki, I don't like this person he as turned to bana son wannan hanyar da yake tafiya a kai. Ni da zai aje duk wannan kudin nasa ya koma former Sadaukin da na sani da sai nafi jin dadi.
Na biya na dauko Subay'a sannan muka karasa gida. Muna zuwa na shiga daki na hada mana kayan mu ni da ita a akwati na chanza mata kaya muka fito. Mai gadi yace tafiya zakuyi ne haka Hajiya?" Nace "cikin gari zamu shiga baba iliya, sai Sunday zamu dawo" ya taro mana abin hawa ya saka mana kayan mu muka tafi Subay'a tana ta murna.
Muna shiga gida naga Inna duk tayi wani jeme jeme da ita, bayan mun gaishe ta ta kalli akwatin kayan mu tace "da fatan ba yaji kika yo ba Diyam" na girgiza kaina nace "yayi tafiya ne Inna, shine muka zo gida muyi dan kwana biyu" ta gyada kai tace "duk da haka ina fatan da amincewarsa kika taho gidan. Nasan ba kya son Saghir, kin fada kin kara fada cewa ba kya son sa kuma har yau nasan ba kya son nasa din. Amma kuma rashin son nasa da ba kya yi ba zai cire shi daga matsayin mijinki ba. Ni nasan kiyayya Diyam nasan illolinta, tun zamanin yammatanci na na dora wa zuciyata kiyayyar Zainab kawai saboda baffanku yana sonta ni kuma ina sonsa. Kiyayyar ta karu lokacin da aka aura masa ni ina matsayin matarsa amma kullum sai ya tuna min cewa dole aka aura masa ni, sai ya gaya min cewa ga wadda zuciyarsa take so. Na kara kin ta kuma lokacin daya aure ta ya kawo ta gidan nan duk kuwa da cewa tayi aure ta fito amma bai rage soyayyar ta ba daga zuciyarsa. Sai ma ya dauki wani son daban ya dora akan agolan da tazo dashi har a gurina nake ganin kamar yafi sonsa akan ku yayan da na haifa masa. Sai ni kuma na tsani yaron ba tare daya yi min komai ba. Har yau ni bazan iya fadar wani abu na rashin kyautawa ko rashin kunya da Sadauki ya taba yi min ba. Na tsane shine kawai saboda na tsani uwarsa. A gaban Sadauki zan gaggayawa Zainab magana amma baya kulani saboda ta hana shi tace babu ruwansa da tsakanin mu. Amma haka na cigaba da rura wutan kiyayyar sa a zuciya ta yadda har mutuwar ita kanta wadda ta haife shi da wanda ya kawo su gidan bata wanke kinsa a raina ba a karshe ina ji ina gani na saka rayuwar yata ta cikina a wahala kawai saboda in bakanta masa" sai ta rufe fuskarta ta kama kuka "Diyam ki gafarta min abinda nayi miki,ni na haife ki amma na tauye miki hakkin ki na bawa azzalumai damar zaluntarki" sai na tashi daga gabanta na koma kusa da ita na dora kaina a kafadarta na fara kuka. Ta saka hannu tana shafa kaina tace "nayi nadama, nadama mai tsanani. Maganar baffanku ta tabbata, yan uwanmu sun watsar damu a titi Sadauki yazo ya dauke mu. Ohh duniya. Duk wanda bai godewa rahamar Allah ba to kuwa tabbas zai godewa azabtar sa. Diyam nayi nadama a lokacin da nadama bata da amfani. Wallahi da ace igiyar auren ki a hannuna take Diyam da tun haihuwar ki ta farko zan gutsire auren gwara ki dawo gida ki zauna a gaba na akan auren Saghir. Amma na kai ki na baro ki. Babu abinda zanyi sai dai in nemi gafarar ki" na rungume ta nace "Inna kinfi karfin haka ai, ni dama ban rike ki a zuciyata ba ballantana ki nemi gafara ta. Wanda zaki nemi gafara shine Sadauki. Shi kika fi zalunta ba ni ba" tace " to ni Diyam ina zanga Sadauki? Tunda ya kawo mu nan ya ajiye mu bai dawo ba. A lokacin na gaya masa ina son magana dashi sai yace min zai dawo amma tun lokacin nake zuba idon ganin sa sai dai shiru babu shi babu labarin sa".
Sai na bata labari. Na bata labarin asalin ko wanene Sadauki a yanzu sannan kuma na gaya mata yadda mukayi da Alhaji Babba da kuma irin amsar da Sadaukin ya bayar. Na karashe da "yanzu dai Sadauki yace Alhaji Babba yana da dama uku. Ko dai ya bamu gidan da yake ciki a maimakon kudin mu, ko yayi jail time, ko kuma yaje gaban Sadauki ya durkusa yana kuka ya roke shi gafara a bisa dukkan abinda yayi masa" Inna ta rike baki ta kasa magana. Nayi shiru ina kallon ta ina jiran ta inda zata fara jero tsinuwa ga Sadauki amma sai naji tace "to, kudin nan dai namu ne gabaki daya, ni dai abinda yake hakkina a cikin kudin nan na yafe wa Alhaji Babba tare da fatan Allah zai dubi niyya ta nima ya yafe min wasu daga cikin laifuffuka na. Amma a cikin ku ban tilastawa kowa ta yafe nata ba, duk wadda taga bata yafe ba sai ta bawa Sadauki goyon baya gurin karbo muku abin ku. Shima kuma Diyam kar ki kuma kokarin hanashi karbar hakkinsa, in ma zubarwa zaiyi ai nasa ne ko? Da basu san kina da amfani ba sai yanzu? Babu ruwan ki, ki fita daga harkar" na gyada kaina. Sai kuma ta tambaye mu in mun yafewa Alhaji Babba, nace "ni dama ai ni yace yayi wa kaya da kudin, to in ma ina da ciko na bar masa, wanda ya tara dukiyar ma ya tafi ya barta" Asma'u tace "ni kam in dai har hamma Sadauki zai iya karbar kudin nan to ina son kaso na. Shi da bai taimaka min da komai ba ni ba zan bar masa hakkina ba" na harare ta sai ta daga kafada tace "Inna tace kowa ya fadi ra'ayin sa".
Da daddare tare muka kwana gabaki daya a kan gado daya muna ta hira, Asma'u sai labarin motar Sadauki take yi min "wallahi ban taba ganin mota mai kyau da dadin wannan motar ba. Kai Adda ina ma dai shi kika aura da yanzu a wannan motar za'a ke kaiki unguwa kin huta da dan sahu. Nima in naje gidanki a irinta za'ake kawo ni gida" nayi juyi nace "Asma'u dan Allah ki rabu dani, bashi na aura ba chapter closed" sai kuma nace "motoci fa yake siyarwa. Dole ya hau mota me kyau".
Washegari na shirya, na bar Subay'a anan gidan na tafi gidan Alhaji Babba. Direct part dinsa na tafi tunda yanzu ba sai anyi wa mutum iso ba. Na same shi a zaune yana lazimi, sai da ya shafa sannan ya tambaye ni "Diyam kin same shi? Me yace? Jibi ne fa zamu fara zuwa court" nace "na same shi Alhaji" sai kuma na lissafa masa abinda yace. Ya kama salati, amma wannan yaro anyi asarar haihuwa, yanzu ni tsofai tsofai dani zaice in je in durkusa a gabansa? Sakayyar da zai yiwa rikon da Usman yayi masa kenan? Gwara da Allah yasa bamu bashi aurenki ba Diyam da yanzu da surikin mu zamu shiga Shari'a" ni dai nayi masa sallama na fita ina jinsa yana cigaba da maganganu shi kadai.
A cikin gidan ne zuciyata ta karye. Hajiya Babba ita kanta a jigace take dan yan uwanta sun gaji da taimaka mata. Muka gaisa tace "Diyam baku kyauta mana ba ke da Saghir, yanzu ace tafiya ta same shi amma sai bayan da yayi ta zamuji labari?" Nace "Hajiya ni wallahi bansan be fada muku ba, na dauka duk kun sani" ta girgiza kai tace "ina fa, mu Saghir sai yayi sati ban saka shi a ido na ba sai dai in na kira shi nace ina nemansa. Yanzu idan kunyi waya dan Allah kice masa ya kira ni" nace "to".
Dana shiga dakin Hajiya Yalwati ne na tarar dasu abin tausayi. Aunty amarya dama ta kara mai ta bar yaranta guda uku duk suna gurin Hajiya Yalwati ga sauran yayan da ake bari a gidan duk mata, ga kuma nata yaran dam haka wajan yara goma ne a part dinta, dan abinda manyan 拼a拼anta suke taimakawa dashi da kyar yake ciyar dasu. Ga yara uku sun isa aure sun kuma samu mazaje amma babu halin yi musu auren. Muka gaisa itama tayi min mita "yanzu Diyam shi mijinki ko shinkafa ba zai ke siyowa yana kawowa gidan nan ba?" Ni dai bance komai ba saboda bazanyi alkawarin da nasan ba zan cika ba.
Washegari Saghir ya kira wayata. Dama tunda ya tafi kullum sai ya kira sai in bawa Subay'a su gama maganganun su in kashe. Ranar sai yace ta bani zaiyi magana dani. Ina karba ya fara fada "da izinin waye kika fita kika je gidan Alhaji?" Nace "Alhajin ai shi yayi kirana ya hada ni da Allah da Annabi inje in taimaka masa" yace "ke kuma sai kika fita, saboda kina sauri za'a tura ki gurin saurayin ki ko? Ai Alhajin duk ya gaya min abinda yake faruwa, shegen yaro da bai san darajar manya ba wai har zaice zai kar Alhaji kara ya biya shi gadon uwarsa? Yanzu haka kudin wiwin da yake sha ne ya kare shi e yake neman refill" nace "amma Alhaji bai gaya maka lauyoyi ya dauka har guda uku ba? In kudin wiwi yake nema ya siya mana da kudin daya biya lawyers din dashi? In fitsari abinyi ne kaza tayi mana mu gani" yace "kar ki gaya min magana, kinsan dai dan bana gari ne da tuni zan biya shi kudin sa, ko Mr Abatcha na gayawa a take zai bani kudin in bashi" na girgiza kaina ina jinjinawa rashin sani da hausawa suka ce yafi dare duhu. Sai nace "to ko a daga shari'ar ne sai ka dawo sai ka karba a gurin Mr Abatcha ka bawa Sadauki?" Yace "to kudin ma ba Alhaji yace dasu akayi miki kayan daki ba? Ki gayawa Sadaukin haka in yaso in karar ce sai ya kai ki ke ki biya shi" sai na gaya nasa jimlar kudin, nace "ni nafi tunanin bayan kayan daki na har gidan da muke zaune a ciki da kudin aka siya, sannan aka kara jari da sauran. Dan haka dani da kai za'a gamai biyan kudi".
Da daddare lawyer din Sadauki ya kira ni, wai Sadauki yace kar muje court gobe. Inna tace ai dama babu inda zamuje. Washegari suka zauna a court. Sadauki ma baije ba kamar yadda nayi tsammani, lawyers dinsa ne kawai suka je a madadin sa. Suka gabatar da dukkan takardu da kuma dukkan shaidu da suka tabbatar da wanzuwar garejin da kuma filin, sannan suka kawo shaidun cewa an siyar, har wadanda aka siyarwa ne suka zo sukayi testifying da kansu suka kuma fadi kudin da suka siya. Alkali ya nemi Alhaji Babba daya fito da kudi shi kuma ya tabbatar cewa kudi dai babu su kuma bashi da hanyar samun su a yanzu, sai dai yana neman alfarmar a bashi lokaci yake biya a hankali har ya gama. A take lawyers din Sadauki suka gabatar wa court da shaidar cewa Alhaji Babba yana da gida mai number 43 a unguwar sharada, har da estimate na kudin gidan, dan haka suna so Alhaji Babba ya siyar da wannan gidan nasa ya biya wadannan kudade, a take alkali ya amince kuma ya bawa Alhaji Babba kayyadadden lokaci na siyar da gida shi kuma Alhaji Babba sai ya nuna cewa lokacin yayi kadan saboda sai ya samu mai siya, anyi ciniki anyi komai. A take lawyers suka ce Sadauki yace zai siya, ai kuwa alkali ya bada lokaci yace aje a daidaita a kan price.
Ana fitowa daga court kawu isa ya kira Inna ga Alhaji Babba nan hawan jini ya tashi an kaishi asibiti. Haka Inna ta saka mu a gaba muka tafi dubiya ni dai ba'a son raina ba amma dana ganshi sai naji zuciyata ta tsinke. Yana ta kuka shabe shabe da hawaye. "Yanzu ya zanyi in siyar masa da gidana? Gidan dana gina tun auren fari da gumina. In na siyar da gidana a ina zan saka iyalina kuma?" Sai naji tausayinsa,ko babu komai yayan Baffa ne shi uwa daya uba daya. Sannan ga tausayin iyalinsa ina zasu je? They are innocent. Su zan iya rantsewa basu mori ko kwandala a kudin ba.
Na fita na dauki waya ta nayi ta kiran number din Sadauki bata shiga. Ko kuma blocking dina yayi ne oho. Da daddare kawu Isa yazo gurin Inna, wannan shine zuwansa gidan mu na farko tun da su Inna suka dawo. Yace "kudi dai da za'a bawa yaron nan babu su. Dan ni kaina in nace zan fitar da kudin nan to kuwa tabbas zan kassara kasuwanci na. Gida kuma kamar yadda Alhaji ya fada in ya siyar ya kai iyalinsa ina? Dan haka third option shine a kira yaron nan a bashi hakuri, ku zakuyi mana jagora zuwa gurinsa a sasanta maganar nan as a family tunda shima ai kusan family din ne, shekarar sa ashirin a hannun dan uwan mu".
Ni aka saka in kira Sadauki. Na gaya musu ba dauka zaiyi ba amma suka ki dan haka a gabansu na kira kuma taki shiga din. Sai na tura masa text. "Third option. Kazo a baka hakurin da kake so" na tura masa. An jima kadan yayo reply "tomorrow evening. Gidan Baffa" na gayawa kawu Isa abinda yace sannan ya tafi da niyyar gobe zai zo tare da Alhaji Babba.
Washegari. Inna har dayiwa Sadauki girki tana ta gyaran gida ni dai ina kallonta kawai. Su Alhaji Babba ne suka fara zuwa, sai a lokacin ma yasan akwai yan haya a gidan mu. Suka zauna nan palo aka bawa Alhaji pillow ya dan kashingida saboda babu lfy. Sai after 5 Sadauki ya shigo gidan. Shi kadai, babu wani abu a jikinsa da zai nuna cewa shi mai kudi ne dan shirt da wando ne kawai a jikinsa ko agogo babu a hannunsa. Sai naga ya koma min wancan Sadaukin da na sani ba wai Mr Abatcha ba, kuma ganinsa a cikin gidan mu sai yayi adding to that feeling.
Yana shigowa palon muka hada ido sai ya dauke kai, fuskarsa babu walwala ko ta cikin cokali sai kawai naji gabana ya fadi. Ya gaishe da Inna ta amsa, the first time da naji Inna ta amsa gaisuwar Sadauki. Sai ya samu guri ya zauna yana kallon Alhaji Babba yace "ina jin ka," kawu Isa yace "dama cewa mukayi a kira ka muyi magana. Ayi hakuri a bar maganar nan ta wuce" sai yace "ba kai zaka bada hakurin ba ai" Alhaji Babba ya tashi daga kwanciyar da yayi ya matso gaban Sadauki yace "ka duba darajar rikon da Usman yayi maka, da kuma darajar yanuwantakar da take tsakanin mu ka bar maganar nan. In na baka gidana iyalina kuma ina zan kaisu? Ka duba halin da nake ciki na karayar arziki data same ni ka yafe min kudin nan. Banyi dai dai ba na sani, na aikata maka laifuffuka na sani, amma na hada ka da Allah kayi hakuri ka bar maganar nan" sai naji zuciyata ta karye, hawaye ya fara bin fuskata amma dana kalli Sadauki sai naga kamar da dutse ake magana. Sai ya mike tsaye yana kallon Alhaji Babba yace "na yafe maka kudin gadon Ummah. Amma kudin fili na ban yafe ba dan haka zan aiko a yankar min wani part na gidan ka a maimakon fili na, dama ina da sha'awar yin kiwon kaji sai inyi a gurin".
Na mike da sauri ina kallonsa cikin mamaki. Can his heart really be this dry? Bai jira sauran magana ba yayi hanyar waje na bishi da sauri ma sha gabansa nace "this is not you Sadauki. Ba kai bane wannan. Kai kace minzaka yafe masa in ya durkusa a gabanka ya roke ka and he did just that" ya harde hannayensa a kirjinsa yana kallona yace "ni ba haka na ce miki ba. Cewa nayi in ya durkusa ya roke ni gafara in naki yi masa a lokacin ne zai fahimci irin yadda naji. So, nayi kokari ma ai, na yafe masa rabi saura rabi".
Na dafe kirjina nace "are you this heartless Sadauki?" Yana kallona with straight face yace "do you blame me? Yes, I am heartless because they took away my heart. You are my heart remember?" Sai ya juya ya fice ya barni a tsaye.
[2/15, 10:48 PM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Four : Sweet Sixteen
Nabi bayansa da kallo ina jin kamar ya ciro tawa zuciyar ne ya tafi da ita. My chest felt empty kamar babu komai a cikinsa, ji nake kamar in bishi a baya da gudu in rungume shi kamar yadda naje yi sanda ina karama, ina son ya rungume ni nima kamar yadda ya taba yi min a gidan Alhaji Babba, but I couldn't saboda akwai wata igiya data ke rataye a wuya na, igiyar auren Saghir.
Bazan iya komawa palon ba saboda duk bana son kallon fuskokin su. Yes, Alhaji Babba ya cuce ni iyakacin karshen cuta amma kuma still yayan Baffa na ne, kuma va'a taba chanjawa tuwo suna, komai suka yi bazan taba cewa su ba iyayena bane ba. And there is wani satisfaction da ake samu a cikin forgiveness, wannan satisfaction din shi nake yi wa Sadauki kwadayin samu.
Sai na juya na tafi gurin Maman Iman duk da dai ita kuma surutu ne da ita ni kuma a lokacin bana son magana. So nake inyi shiru inyi jinyar zuciya ta. Dan haka ina zuwa sai nace mata bana jin dadi ne ina so zan kwanta, sai kuwa ta bude min dakin yaranta, dakin mu ni da Asma'u a da. Na shiga na kwanta, but sai dakin ya cigaba da dawo min da memories din da. Sadauki's memories, na sake gwada kiran wayarsa still bata shiga. Dai na kifa kaina a pillow na fara kuka. It really hurt to love someone so deep while you are married to another, another din kuma wanda ba ka so.
Sai da akayi magrib Maman Iman ta shigo ta tashe ni in yi sallah. Ayi alwala nayi sallah sannan na koma part din Inna, ina shiga na tarar sun tafi, Inna ta bini da kallo tace "kuka kikayi ko?" Na girgiza mata kai amma sai hawaye suka fito. Tace "me yasa kika masa magana dazu? Ba nace miki ki fita daga maganar ba? Tunda ke kince kin yafe shi ki barsa ya karbi abinsa. Na gaya musu nace Asma'u ma tace bata bari ba".
Ranar sunday, da safe muna shirye shiryen komawa gida ni da Subay'a kamar daga sama sai jin sallamar Sadauki nayi a tsakar gida. Na dakata da folding kayan da nake yi naji Inna tana amsa masa da yake tana tsakar gida ni ina palo, naji ya gaishe ta ta amsa tana tayi masa sannu da zuwa tace ya shigo palo, yana daga labule muka hada ido sai yayi sauri ya saki labulen ya koma yana cewa "basai na shiga ba Inna, dama zan dan shiga dakin Ummah ne" sai Inna ta kira saka mayafinta da kanta ta shiga gurin Maman iman ta gaya mata za'a wuce, saboda sai an bi ta nan za'a karasa dakin Ummah. Subay'a dake kusa dani ta tashi ta leka tsakar gida, sai naji yace mata "Subis, come here" sai ta makale a bayan kofa taki fita, yace "ba zaki zo ba? Dan kin ganni baki babanki kuma fari ko?" Sai inna ta dawo ta tarar dasu tayi dariya tace "Subay'a kizo ki gaishe da babanki mana?" Subay'a ta tura baki tace "ba baba na bane ba" inna tace "ji fitsararriya?" Yayi dariya yace "gado tayi ai" sai Asma'u ta shigo, tana ganinsa ta kama murna tana gaishe shi, yace "yar asama yammata" a raina nace "wato yana iya yiwa kowa magana faran faran, ni ce dai na koma aljana a gurin sa".
Asma'u ce ta raka shi ya bude dakin Ummah ya shiga, sannan ta dawo. Inna ta shigo tana kallona tace "kina jin Sadauki ba zaki fita ki gaishe shi ba?" Nace "baya son ganina inna. ganina a dakin ne fa yasa ya fasa shigowa". Inna tayi shiru kawai bata ce min komai ba ni kuwa zafin da nake ji a raina yasa na dauki kayan na koma cikin daki, amma sai na kasa cigaba da gyarawa na kwanta kawai. Ina kwancen ya dawo, ya leko yayi wa Inna sallama sai ta ce yazo tana son magana dashi. Ya shigo palon ya zauna tace "Sadauki. Ni dai kam bansan wanne kalamai wanda yayi laifi irin wanda nayi maka zai yi amfani dashi gurin rokon gafarar wanda yayi wa lafin ba. Na cutar da kai Sadauki iyakacin cutarwa kuma duk a bisa son zuciyata ba wai dan kayi min wani laifi ba. Amma a karshe sai ya kasance ni din dai nice a wahale. In kace ma ba zaka yafe min ba Sadauki bazan ji haushi ba saboda na cancanci koma menene zakayi min. Amma abinda na sani shine nayi nadama, Sadauki dan Allah...." Sai ya dakatar da ita yace "Inna na yafe miki ai, da ban yafe miki ba Inna ba zaki ganni a dakin nan ba. Maganar ta wuce tsakanin mu har abada" sai Inna ta kama yi masa godiya, har ya sake mikewa zai fita sai ta kira Asma'u, sai kawai zuciyata ta raya min in leka su, naje ta jikin labule ina lekawa sai naga ta kamo hannun Asma'u ta saka a cikin na Sadauki tace
"na hana ka auren Diyam a lokacin da kiyayyar ka ta rufe min ido, amma yanzu ga Asma'u na baka, duk abinda yayi Diyam shi yayi Asma'u har kamanninsu iri daya ne, ina fatan zaka karba kuma wannan zai wanke maka zuciyarka"
Na juya ina dafe kirjina kamar mai kokarin gana zuciyata fadowa kasa. Idanuwana kamar zasu baro mazauninsu ina girgiza kaina a hankali ina cewa "no, no, no" amma sai naga Sadauki yayi murmushi, sai ya cire hannun Asma'u daga nasa ya mayar wa da inna yace "Inna na gode da wannan babbar kyauta da kika yi min, kuma da gaske wannan kyautar ta wanke min zuciyata sosai amma kiyi hakuri bazan iya karba ba. Zuciyata Diyam take so ba kamannin Diyam ko asalinta ba, in na karbi Asma'u banyi mata adalci ba saboda zan tilasta mata zama dani alhalin zuciyata bata tare da ita. Kiyi hakuri idan ban kyauta miki ba amma hakan shine zaifi mana alkhairi a gani na".
Na saki labulen na zauna a gurin ina juya lamarin a kaina. He refused Asma'u, sweet teenage Asma'u, yana claiming that his heart belongs to me, how can that be? Bayan ni kuma I belong to someone else?
Sai yamma muka koma gida, daga nan kuma muka cigaba da lonely rayuwar mu nida Subay'a. Duk da ina kokarin ganin na rage tunanin Sadauki amma kullum tamkar kara min shi akeyi.
Two weeks after that akazo aka raba gidan Alhaji Babba. Aka ja katanga tun daga part dinsa har zuwa bakin gate, sai ya kasance part din nasa da filin compound din dayake gaban part din har zuwa dakin maigadi da gate din gidan duk na sadauki ne. Main house din kuma da sauran abinda ya rage na compound shi kuma na Alhaji Babba, amma ko gate basu dashi dan haka sai katanga suka fasa ake shiga gidan, ko kudin da za'a sayi kofa a saka babu.
Ba'ayi sati dayin haka ba dakunan Alhaji Babba suka zama dakunan kaji, Sadauki ya cika katon palon Alhaji da kuma two bedrooms dinsa da kajin gidan gona, broilers da layers. Compound din kuma akayi katuwar rumfa aka zuba raguna da tinkiyoyi, dakin maigadi kuma ya saka masu kular masa dasu.
Alhaji Babba kuma ya koma cikin gida, dakin da Inna ta zauna nan ya dawo da zama. Washegarin da aka zuba dabbobin da sassafe murja ta kira ni "Diyam wallahi yau bamuyi bacci ba a gidan nan. Yadda muka ga rana haka muka ga dare wallahi, ragunan nan tun magrib suka fara koke koke har garin Allah ya waye sannan kuma kaji suka dauki nasu suma. Ni dai gidan ki zan taho in taya ki zama kafin hamma ya dawo ya kore ni" nace ta taho babu komai. Sai kuma naji babu dadi a raina. Murya, Hajiya Yalwati da sauran yayan Alhaji Babba basuyi wa Sadauki komai ba amma har dasu ake paying. Isn't Sadauki taking this too far? Bayan gudun daukan alhakin wanda baiji ba bai kuma gani ba?
Da dare Sadauki yaje gidan mu. Ya gaishe da Inna sai yace da Asma'u. "Yar Asama kina son gidan gona?" Tace "gidan gona kuma hamma?" Sai ya ajiye mata takardu yace "gashi nan na baki kyauta. Duk karshen wata za'ake kayo miki kudin da aka samu a ciki" Asma'u sai murna da tsalle, yayinda Inna ta saki baki ta kasa magana.
Yana tafiya Asma'u ta kira ni tana son bani labari amma maganar ta kasa fitowa dan murna. Nace "kinga ki nutsu ki fada min, me ya faru?" Tace "hamma Sadauki ya bani kyautar gidan gonar sa da yayi a gidan Alhaji Babba" cikin mamaki nace "what?" Sai ta mikawa Inna tayi min confirming maganar. Har da sunan ta da komai a jikin takardun.
Na kira shi da niyyar yi masa godiya amma shiru wayar bata shiga kamar kullum. Nayi tsaki na yar da wayar feeling very frustrated sai kuma na dawo na sake dauka na tura masa message "ina yiwa Asma'u godiyar kyautar da aka yi mata. Allah ya kara arziki mai albarka" na tura sannan na zauna rike da wayar a hannu ina jiran reply. Can sai gashi ya shigo. Three words
"You are welcome".
Nayi tsaki ina jin haushin sa, amma bansan dalilin da yasa nake jin haushin nasa ba.
Bayawa ko? Sorry, busy weekend
[2/16, 9:32 PM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Five: Fauziyya
Murja tazo gidan muka zauna tare da ita, da yake ta gama makaranta kuma tun tuni ana ta zaune gida ba'a cigaba da karatu ba, ita tafi son tayi aure ma. Tace "wallahi Diyam na gaji, na gaji da zaman gidan nan wallahi. Gafa samarin nan ina dasu, kuma duk wanda nacewa ya turo a cikin su wallahi fitowa zaiyi amma Alhaji shiru har yanzu yaki yace wani abu, kuma maganar sa daya wai wasu kudi yake jira su zo kuma duk munsan babu wasu kudin da zasu zo fa. Ni so nake in bawa umman mu shawara duk ace da samarin mu su fito, in yaso kowa kudin auren ta da kuma kudin sadakin ta sai a hada ayi mata kayan daki yadda ya sawwaka kawai. Ai ba sai an kashe mana kudi ba mu auren mu ke so kawai" na jinjina maganar nace "amma biki fa? Gara fa?" Tace "wannan kuma mijin ki zaki yiwa magana dan Allah ya rage matsolancin sa yayi mana. Kudin yadin da yake sawa a jikin sa kadai ya isa ayi abincin biki da shi" nayi dariya nace "kai murja, hadda sharri kuma?" Tace "wallahi ba sharri bane ba kayan da yake sakawa ko sanda Alhaji yana da kudi baya saka irin su. Amma ya bar alhajin da yar shara".
Sanda Saghir yaji labarin abinda Sadauki yayi a gidan su ya kira ni ya zazzage min bala'i. Bance masa komai ba har ya gama sannan nace "ni dai bani na kar zomon ba, ni ratayar ma ba'a bani ba, ka bari in ka dawo sai kaje ka neme shi kayi masa masifar, but I doubt in zaka samu ganin sa dan kasan manyan mutane ba kowa suke bari ya gansu ba" ina fadar haka na kashe, yayi ta kira naki dauka dan nasan cigaba zamuyi daga inda muka tsaya.
Tun ana gobe zai dawo yakira yagaya min "ke yanzu ko dan I miss You din nan ma baki iya gayawa mijin ki ba. Kinga ni kuma har da tsaraba na siyo miki. Ina fatan dai kin tana de ni saboda da kishin ruwan ki zan dawo" sai naji ma abin ya bani dariya nace "duk wanda ka gama samu anan bai ishe ka ba? Mai zakayi da yar mitsitsiyar Diyam?" Bai musa ba yace "naki special ne. Da gaske nayi missing dinki fa" sai na kashe kawai. A raina ina jin inama yayi zamansa a can kar ya dawo?
Banyi niyyar yi masa komai na dawowa ba amma dai sai na daure nayi masa girki, wainar shinkafa na miyar taushe da taji tantakwashi. Na hada masa lemom kankana. Sanda zasu taso ya kira wai zai turo friend dinsa ya kaimu airport ni da Subay'a mu taro shi, nace ni aiki nake yi sai dai suje da Subay'a. Na shirya ta kuwa suka tafi, nima nayi wanka na shafa mai kamar kullum na saka normal kayana na gida nayi kwanciya ta a kan gado.
Ina jinsu suka zo, kawai naji wani bacin rai ya sauko min nayi tsaki na gyara kwanciya ta. An jima kadan Subay'a ta shigo tana ta tsalle. Mommy ki zo Daddy ya dawo, ya siyo min kaya da jirgi da mota" nace "kice kin gode, sannan kice masa ga abinci nan a dining" ta fita na koma nayi kwanciya ta. Sai gasu nan sun dawo tare, na tashi zaune ina kallonsa shima yana kallona, ya kara fari har da kumatu yayi alamar ya huta sosai, yace "shikenan? Babu oyoyo mijin ki yayi tafiya for two months amma ko dan welcome back hug ba zai samu ba?" Nace "na dafa maka abinci, nace maka sannu da zuwa sai menene kuma?" Ya saki hannun Subay'a ya hawo kan gadon sai nayi sauyi na sauka na fita na bar musu dakin.
Na tarar da lodin kayansa a palo, na dauka na kai masa dakinsa na tarar yana shirin wanka, na dauko abincin da nayi masa na kawo palon sama na ajiye sannan na koma kasa muka zuba ni da murja muna ci tace "ke ba zaki tafi gurin mijin ki ba ya dawo daga tafiya? Ke ana neman mijin ke kina wulakanta naki?" "Humm" kawai nace mata sai ga kira kuwa Subay'a tana yi min inzo inji Daddy. Yana zaune a kujera ya hade rai "ki zo ki zuba min abincin tunda ba zakiyi min wankan ba" bance komai ba na zuba masa na kawo table gabansa na ajiye masa. Yace "wai ke ciwon rashin magana ne ya same ki? Na fi so ina fada kina mayar min yafi dadi" nace "ba ciwon rashin magana bane ba, 拼ata ce ta girma shi yasa nake shiru a gaban ta" yayi dariya yana kallon Subay'a data zauna ta zuba mana ido. Na juya zan koma kasa sai ji nayi yace "kai! Matar nan wani duwawu naga kina yi fa" nayi saurin kallon Subay'a naga tana dariya sai kawai na girgiza kai na tafi.
Muna kasan Subay'a ta jawo wani karamin akwati da kyar, murja ta tashi ta taimaka mata suka sauko dashi tana cewa "Mommy kinga kayan da Daddy ya siyo min" tana ta bubbuda wa, kayan sawa ne masu kyau da takalma, sai toys, murja tana ta yabawa, sai kuma Subay'a ta koma sama da gudu sai gata da karamar travelling bag mai kyau ta kawo min. "Inji Daddy, wai irin kayan da turawa suke sakawa ne ya siyo miki kema kike sakawa. Ki koma irin su" na bata rai nace "to sarkin surutu" na karba na ajiye, murja ta dan dake ni tace "tashi zaki yi kije kiyi godiya sosai" na mike na tafi amma sai nayi kwana na shiga dakina nayi kwanciya ta.
Sai bayan magrib ya shigo dakin yana kallona ina ninke sallaya yace "zan fita, zan tafi zance" na dauke kaina nace "ba gidan Alhaji ya kamata kaje ba? Ka gaishe su kuma kaga abinda aka yiwa gidan?" Sai kawai naga yayi murmushi yace "au kishi kike dan zanje zance ko?" Na zauna a bakin gado nace "Saghir, na riga na gaya maka tun kafin kayi tafiyar nan ni ko mata goma zaka aura ba zanyi kishin ka ba. Ni da son samu nane ma hudu nake so kayi, yadda zaka bani takarda ta in kara gaba" ya karasa shigowa yana cewa "wato kin ganshi ko? Alhaji ya tura ki kin ganshi ko? To bara kiji, in shi yake zuga kima ki gaya masa, auren ki yanzu na fara. In kinga na rabu dake to mutuwa nayi" ya juya ya fita.
Ranar da wuri na yiwa murja sallama na hau sama tana tsokana ta "wato miji yazo shine zaki tafi turaka ko?" Nayi dariya kawai na tafi, na shirya Subay'a na kwantar da ita sannan nima na shirya na rufe kofa ta nasa key nayi kwanciya ta. Cikin bacci naji karar wayata, na dauka na ga Saghir ne sai na saka ta a silent na juya na cigaba da bacci na, sai kuma naji shi yazo yana knocking, ko kallon kofar banyi ba har ya gaji yayi tafiyar sa. Da sassafe ya bar gidan, a raina nace "Allah ya raka taki gona".
Da yamma sai ga Mama tazo, ni na dauka zuwa tayi gani na sai da naji ta kama yi min fada sannan na fahimci Saghir ne ya kai kara ta. "Diyam me kike nema wa kanki? Kin manta abinda annabi ya fada cewa mata sunfi yawa a wuta? Kuma mafi yawansu sun shige ta ne sakamakon rashin bin aure? Abinda kike so kenan? Wuta kike so ki kai kanki? To wallahi ki nutsu kiyi wa kanki fada. Ganin Sadauki ya dawo ne zaki kuma dorawa kanki kulafucinsa ko? So kike a lahira shi Sadaukin da kike yi saboda shi idan ya aikata aiyukan alkhairi ya kasance a aljanna ke kuma kina wuta saboda shi?" Nace "Mama ni ba dan Sadauki bane ba, Sadaukin da ko kula ni baya yi?" Tace "to ya zaiyi ya kula ki? Matar aure ce fa ke. Ke ai har yanzu ba hankali ne ya ishe ki ba shi kuwa da hankalinsa. Saghir yace shi yana sonki, yana son zama dake, me yasa ke ba zaki so shi ba? Shima Sadaukin nan fa dole watarana aure zaiyi, yadda yake da kudin nan ma sai ki ga ya auri hudu a rana daya. In haka ta faru kuma ya zakiyi?.
Sai dare Saghir ya dawo gida. Yana shigowa palo murja ta gaishe shi ya hade rai yace "ki shirya gobe ki koma gida" tace to sai ya wuce sama. Murja ta kalleni pleadingly, ni kuma na daga mata kafada. Kamar bazan tashi ba musamman ganin ko kallon inda nake baiyi ba kuma dai sai na tashi na bi bayansa. Ina shiga dakinsa naga yana kokarin cire kaya sai na kama masa ya cire nayi hanging rigar sai yace "Mama tazo gidan nan kenan" na rike kugu nace "tunda ka kai kara ta ba dole tazo ba?" Ya zagayo hannayensa a waist dina yace "naga kina neman ki kaini lahira ne shi yasa na nemo taimakon gaggawa" ya shafa fuskata yace "you really are beautiful" na ture hannunsa nace "bararojin kuma?" Sai yayi dariya yace "wai baki manta ba, ai bararoji suna da kyau so it was a compliment" ya saka fuskarsa a cikin gashina yana shakar kamshinsa yace "tell me duk abinda kike so inyi miki" nace "ka bar murja ta cigaba da zama a gidan nan" yace "done. Sai kuma me?" Nayi shiru, yace yana zuge zip din rigata "ba zaki ce in fasa aure ba? Say it and it will be done" na sake shiru na rufe idona ina jin daci a bakina yace "kice 'hamma Saghir Please kar kayi min kishiya" bance komai ba ya daga ni ya dora akan gado, hawaye ya fara bin fuskata yace "kice hamma Saghir ina sonka" nayi shiru sai yayi ajjiyar zuciya yana hawowa gadon yace "watarana zaki fada, ina nan ina jira".
Ina kallon sa yana ta shirye shiryen sa, ni ko su inna ban gayawa zancen auren sa ba sai da suka ji daga gidan Alhaji Babba, Hajiya ta kira ni a waya "yanzu Diyam da gaske Saghir auren nan zaiyi? Shi yanzu kudin da zai kashe gurin auren ya bawa Alhaji su mana ko shago ya bude ya fara dan kasuwanci. Yanzu kina ganin kofar gidan nan ma da kyar Saghir ya saka ta shi ko a jikinsa ma wannan cin mutuncin da akayi wa gidan nan" "sai hakuri Hajiya" shine kawai abinda nace mata.
Har dani akaje aka kai lefe, aka saka rana akayi komai aka fara hidimar biki. Kowa sai mamaki na yake yi wai ni ko a jikina mijina zaiyi aure. Shi kuma Saghir kullum sai ya ce ince masa ya fasa aure ni kuma naki fada. Sai yayi fushi ya daina yi min magana sai kuma dan kansa ya sauko. Sadauki kuma bai kuma bi ta kaina ba, sai dai yakanje ya gaida Inna, kudin gidan gona kuwa account ya bude wa Asma'u ake zuba mata a ciki sai dai kawai su dauko suyi amfani da abinsu".
Satin bikin Saghir yana kamawa Hajiya ta kirani tace ita fa babu wani taro da zata yi, ni kuma sai nace zanyi walima ranar kawo amarya anan gidan Saghir, yadda kowa yazo in an kawo amarya sai ya ganta. Saghir yana ji ya fara fadan wai za'a bata masa gida. Ranar kafi suka zo suna ta daddaga hanci, na saka murja ta nuna musu spare dakin da yake sama suka ce "dama yace ba sai anyi mata komai ba ya saka komai a gidan, gadon ma da cewa yayi kar ayi mune muka ce sai anyi saboda kar a mata gori". Ina jinsu suna gulmar "wannan yar karamar yarinyar ce uwargida?".
Aka daura aure Saturday, Sunday kuma aka kawo amarya. Duk yan uwa sunzo walimar dana shirya, anci ansha sai kuma aka karbi amarya. Ni dai ina dakina basu kawo ta ba nima banje ba har aka gama kowa ya watse. Na shirya Subay'a nima na shirya muka yi kwanciyar mu sai na jiyo hayaniyar maza a waje, ni na manta ma ashe ana siyan baki. Sukayi ta hayaniyar su suka gama suka tafi ninina ta karanta novel din da Rumaisa ta turo min kafin ta tafi, sai ga Saghir ya shigo dakin. Ya hawo kan gadon ya karbi wayar daga hannuna yace "uwargida ran gida" sai abin ya bani dariya ma, yace "ki fito kiga amaryar ki. In ba kyason ta kuma kinyi alkawarin kula dani yadda ya kamata a yau zata koma gidan su" na mike ina saka hijab nace "ta sha zamanta. Tunda ba'a kaina zata zauna ba ni kuwa ina ruwana da ita?" Sai na wuce na barshi a nan. Ina shiga palo na ganta a xaune tana kallon kofar dakina. But unlike abinda Saghir yace na cewa nafita komai ni sai naga kamar ta fini komai except kyawun fuska. Ta fini shekaru, daga gani ta fini ilimin boko, ta fini girman jiki dan duk abubuwan da Saghir yake yawan complain cewa bani dasu ita tana dasu sosai. Tasha heavy make up da wani uban attach har gadon baya. Rigarta kusan rabin kirjinta a waje, na tambayi kaina "a haka akayi siyan bakin?" Na zauna nace "sannu amarya" ta kalleni tana yamutsa fuska tace "yauwa, sannu" Saghir ya shigo ya zauna a kusa da ita, kamar jira take yi sai ta dora kanta a kafadarsa hannunta kuma a kirjinsa. Nayi murmushi ina kallonsu, yace "Halima ga Fauziyya, Fauziyya ga Halima" ya kama jawabin zaman lafiya, baya son hayaniya waye da waye ya gama sai yace "to yanzu amarya zata gama kwana bakwai dinta da musulunci ya bata a matsayin ta na budurwa, daga nan sai kuma ayi maganar rabon kwana. Sai dariya taso kubce min na rufe baki na juya fuska, yace "kina da magana ne, Diyam?" Na girgiza kai, yace "no ki fadi abinda yake ranki, naga kamar kina dariya" nace "kawai dai naji kace budurwa ne, ni kuma da na ganta na dauka bazawara ce" sai tayi sauri ta mike zaune sosai tace "excuse me? Shi da zai aure ni bai gaya miki budurwa zai aura ko bazawara ba?" Nace "ba muyi wannan maganar dashi ba kuma to be frank bani da problem da koma wacece, Allah ya bada zaman lafiya, aci sati daya lafiya, sannan akan sati dayan na kara muku shekara daya kyauta from me to you" sai na mike nace "Allah ya bamu alkhairi".
Ina shiga daki yana shigowa shima, ya jawo ni tace "what? What was that? Wacce maganar banza naji kinyi a gurin can?" Nace "kyauta nayi maka ko ba ka so? Ji nake mai kula da kai a gado kake nema kuma gashi ka samu, ko shekarar tayi kadan ne in kara muku wata?" Sai na kwace jikina nace "and don't touch me kasan ba kwana na bane yau" na haye gado naja bargo.
Ya tsaya yana kallona sai yace "yanzu har tsanar da kika yi min ta kai haka? To shikenan, saki kike nema na sani kuma ba zaki samu ba. Naji, Fauziyya zata kula da gado na amma duk abinda ya danganci aikin gida ke zaki ke yi, wanke wanke, shara, girki da komai" na gyara kwanciya nace "done. Shekara ta nawa ina wanke wanke da shara da girkin? Dan dai karin kwano daya ai ba zai gagare ni ba". Na rufe ido nace "in zaka fita dan kashe mana fitila Please".
[2/17, 8:57 PM] +234 818 247 0922: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Six: New Saghir
Jin yayi shiru kuma bai fita ba yasa na bude idona, na ganshi still a tsaye yana kallona, muna hada ido yace "me nayi miki me zafi haka Diyam? Still akan wannan dan iskan yaron ne ko? Saboda kina sonsa ne yasa kika tsane ni irin haka ko?" Na yaye abin rufar nace "don't bring Sadauki into this, babu ruwan Sadauki da tsakanin mu" yace "saboda an miki auren dole ne dani? It that it? Nima in kika tuna ba son auren nake yi ba lokacin da aka yishi" na girgiza kaina nace "ba dan an tilasta min aurenka bane ba Saghir. Su kansu wadanda suka tilasta min auren naka Inna da Alhaji ai ban rike su a zuciyata ba, babu komai a yanzu tsakanin mu sai kyautatawa da tausayi" yace "ni kuma fa Diyam? Menene nawa a ciki? Nasan ba kya sona but me yasa ba zaki bani dama ba?"
Na mike tsaye ina jin zuciyata tana karyewa nace "you......raped......me" sai jikinsa yayi sanyi, nace "in ka manta da dakin nan yana magana zai tuna maka, na nuna gado na nace "here, anan ka dasa irin kiyayyar ka a zuciyata. I was only 14 years then, ranar baffana kwanansa 47 a kasa and you raped me".
Hawayene kawai suke bin fuskata, ya diririce "Diyam na baki hakuri ai, I was drunk, I wasn't....." Nace "shine excuse dinka? Giya ce excuse dinka? Bayan kuma har yau shanta kake yi? How can you raped me and then expect me to enjoy sexual relationships da kai? Tun ranar gini ai tun ranar zane. Ka dasa tsiron 茩inka a raina sannan kazo ka zuba masa taki when you killed my babies" sai kuka ya kwace min "you killed my babies and you left me to die a asibiti".
Sai ya taho da sauri ya jawo ni ya rungume ni, na fara ture shi amma yaki sakina har na hakura nayi ta kuka na a jikinsa. Yayi kissing forehead dina yace "Diyam ba zan iya dawo da baya ba, amma nayi alkawarin gyara gaba. Kome kike so zan yi miki Diyam in dai zan goge baya, banda saki because I can't. I love you".
Knocking kofa akayi "Darling?" Fauziyya ta fada daga waje, na ture shi na hau kan gado na lulluba har kaina. Ina jinsa ya hawo yayi kissing Subay'a sannan ya fita gun darling din tasa.
Da safe tun dan tashi da assuba ban koma ba, fuskata duk ta kumbura tayi min nauyi saboda kukan da nasha jiya da dare na tausayin kaina da rayuwata. Yaushe zanji dadin aure ne ni? Na gabatar da adduoi na kamar kullum, ina rokon Allah ya bani ikon cin wannan jarabawar da nake ciki ta auren Saghir, idan har zama da Saghir shine mafi alkhairi abu a rayuwata Allah ya rage min kiyayyar sa daga zuciyata. Sannan kuma nayi addu'ar Allah ya bamu zaman lafiya da amarya. Dalilin da yasa na yarda da auren Saghir shine, ina ganin yin auren nasa wata hanya ce ta rage wa ksina tarin zunubin da nake dauka na gudunsa da nake yi, at least in da wata matar nasan wannan responsibility din ya ragu daga kaina.
Ina gamawa na sauka kitchen na fara fere dankali, sai ga murja nan ta shigo mu ka gaisa ta dauka ta fara tayani muna hirar mu, har muka gama na fara soyawa ita kuma tana soya kwai sai ga Saghir nan ya shigo, har yayi wanka yayi kwalliya, murja ta gaishe shi ta fita sai ya jawo stool ya zauna yana kallona "barka da assuba" nace ina kallon sa, yayi murmushi "good morning. Ina jin yunwa a bani abinci" nace "wai da so nake in hada muku kai da Fa'iza sai akai muku sama" yace "Fauziyya ba Fa'iza ba" na dafe kai "sorry. Fauziyya" ya girgiza kai "bacci take, ni kuma yinwa nake ji. Zubo min inci anan kawai" na zuba masa a plate na dora fork na mika masa, ya karba yace "naga Subay'a yau bacci take tayi" na hado masa tea na kawo masa na koma na cigaba da aikina shi kuma yana ci. Sai daya gama ya mike yazo bayana ya rungume ni yana shanshana gashina yace "am sorry Diyam kinji? I promise insha Allah zan saka ki murmushi more than yadda na saka ki kuka" ya juyo dani yace "da ace ina da dama da sai na bude nan" ya dora hannunsa a kirjina "na saka soyayya ta a ciki na rufe da kwado" na ture hannunsa ganin yana neman wuce gona da iri nace "stop it. Amarya tana sama tana jiranka" sai yayi murmushi kawai yace "zan fita. Sai na dawo".
Tare da murja muka gama aiyukan mu kamar kullum, sannan naje nayi wanka nayi wa Subay'a muka sauko muka fara cin abinci sai ga amarya ta sauko. Tana ta wani yayyatsina fuska, sai kawai na tsaya ina kallonta. Babu makeup din jiya, wannan ya sake fito da kamanninta sosai, sai nayi realizing ai na santa ma, tana daya daga cikin matan da suke zuwa har gida neman Saghir shi kuma yana ce min abokan aikin sa ne. Tazo ta zauna murja ta gaishe ta sai naga tana kallona irin kamar tana jira in gaisheta din nan tunda tana ganin ta girme ni. Nace "Subay'a ki gaishe da auntyn ki. Fa'iza ga Subay'a, koda yake nasan kin santa ma ai tun sanda kike zuwa" sai ta bini da kallo kawai. Na tashi na barta a dining nace "ga abinci nan Bismillah"
Na koma sama ina mamakin wannan rayuwar. Ni in nice Saghir ya zanyi in auri saura na, ai sabuwa zanso wadda ban taba testing ba, no wonder yazo yana shashshafa ni da sassafe.
Rayuwa ta cigaba da tafiya, har Fauziyya tayi sati a gidan. A ranar ne kuma Saghir ya tubure. "Babu wata shekara, ban yarda na. Eh an baku dama kuyi kyautar kwana amma sai da amincewar mijin ni kuma nace ban amince ba" na daga gira ina kallonsa a raina ina cewa 'zakayi saki reshe kama ganye kuwa' a dole na na hakura na karbi kwana na. Dokin da yake sai daya sa naji tausayin Fauziyya. Ni kuma kamar an saukar min da bacin rai haka naji nayi zamana a dakina amma sai gashi ya taho. Ina game a waya ya karba ya ajiye yace "me kike so inyi miki ne Diyam? Kuka zanyi ne ko tsallen kwado?" Na juya masa baya nace "duk wanda ranka yafi so" sai ya hawo gadon ya fara yi min tausa. Yace "da gaske fa nake. Say it, anything, yanzu zaki ga anyi miki" na tashi na zauna yace "kudi kike so?" Sai ya dauko bandir din 500 notes ya ajiye min akan cinyata yace "ki shirya gobe in kaiki shopping ki sayi kayayyakin ku na mata, kayan kwalliya, jaka, takalmi anything" na mayar masa da kudin sa nace "ka sayi kayan abinci ka kai gidan Alhaji" ya dawo min da kudin yace "angama. Can we please go to my room? Kinga Subay'a tana nan".
Washegari kuwa ya fita dani, yayi ta lodo min kaya komai ya gani na mata sai ya dauka, "wannan zaiyi miki kyau, wannan ma yana da kyau, wannan zai dace dake" haka dai yayi ta fama. Muna dawowa gida muka tarar babu abinci, bata yi ba tunda girkina ne dan haka na shiga kitchen na dora da yake weekend ne Subay'a tana sama tare da Saghir suna kallo. Riga da wando ne a jikina kaina babu dankwali na daga gashina sama ina ta aiki na ina jin kida a waya ta sai naji kawai wani strange kamshi da ban sani ba, ina juyo wa sai naga wani mutum a tsaye a palo yana kallona muna hada ido sai cewa yayi "Fauziyya tana nan?" Ni kuwa na zunduma ihu ina kiran Saghir, sai kuwa gashi nan a guje ya sauko kafin mutumin ya fita. Ya damko shi yana tambayarsa lfy sai cewa yayi wai shi gurin Fauziyya yazo shi dan uwanta ne kuma ita tace mishi ya shigo. Ranar naga bala'i a gurin Saghir, daga Fauziyyan har bakon nata ya ha蓷a ya balbale su da fada daga baya ma ya ha蓷a har da maigadi wanda yayi ta faman rantsuwa a kan cewa shi bai san mutumin ya shigo ba. Ni dai na dauki yata muka koma sama nace ku kare kalau.
Sai da daddare kuma Saghir yayi ta bani hakuri. Nace "duk wanda ya sayi rariya dama ai yasan zata zubar da ruwa. Tun da har ka auri yarinyar daka gama nema a waje ai kasan dole zata kawo maka maxa gida kaima. Duk abinda kayi ai kaima dole za'ayi maka. Haka rayuwa take" ya fahimci magana nake fada masa sai yace "kin san ai dalilin da yasa nayi auren nan ko? So nake kike kula dani yadda ya kamata sai nayi tunanin idan nayi aure kika ga wata tana kula dani kema zaki koya. Wannan shi yasa na auri Fauziyya saboda bana son in auri wata wadda itama bata iya din ba" a raina nace "oh, ita wannan ta iya din kenan"
Rayuwa ta cigaba da tafiya. Saghir har mamaki yake bani yadda yake yi min, gabadayansa ya chanja kuma duk abinda nace to kuwa zaiyi shi sai dai in bance din ba. Na saka shi ya ke kai kayan abinci gidan su, sannan kuma na daina jin warin giya a tare dashi duk da ban tabbatar ko ya daina sha ba. Fauziyya bata da problem, tana dai da daga kai da nuna irin ta fini dinnan amma tunda ta fahimci yadda Saghir yake ji dani sai ta ja baya. Bamu fiya zama muyi hira ba kowa harkar gabansa yake yi. In ranar girkin tane tayi ta iyayi da rawar kai ni kuma in ranar girkina ne Saghir yayi ta rawar kafa, duk da dai ba koda yaushe yake samun abinda yake so din ba dan wani lokacin rufe kofa ta nake in kashe waya, watarana kuma in naje in bata rai har sai ya hakura ya rabu dani. A lokacin ne kuma bikin Rumaisa ya tashi, za'a hada ayi tare dana yaya Mukhtar. Lokacin muna 22 years, tana kuma final year dinta a jami'a.
Bikin yana matsowa na tambayi Saghir sati biyu. Ya rike baki "sati biyu kuma Diyam? Kwana nawa za'ayi ana bikin da har zakiyi sati biyu?" Nace "nice fa babbar kawar amarya. In ina nan ta yaya zanyi shirye shirye?" Babu yadda zaiyi yace "shikenan" amma ina kira Mama na gaya mata zan taho tace "baki da hankali dama? Babu wani sati biyu da zaki zo kiyi, sati daya zakiyi shima kuma dan kina da abokiyar zama ne da ba zan barki ki taho ki barshi shi kadai ba" ranar har kuka nayi, I just needed a break from the house and from Saghir.
Sai satin bikin sannan Saghir ya kaini gidan Mama. Ya kuma buga min warning "saura kuma ki shiga cikin yammata kuyi ta shiririta. Kinsan dai ke mai aure ce ko?" Nace "uhm" a raina ina mamakin wai yau Saghir ne yake kishi na. Ko yaushe zan fara nasa ni?
Munsha bikin mu lafiya mun gama lafiya. Da muka je dinner naga yadda Rumaisa take nishadi da mijinta sai naji wani longing a zuciyata. I missed all this, ni banyi yammatanci ba kuma babu abinda zan adar na bikina. Ranar Lahadi muka kai amarya dakin ta. Litinin kuma na biyo su Inna muka dawo gida tunda satin da aka bani bai kare ba sai nan da kwana biyu. Muna zuwa naji Maman Iman tana soya wainar fulawa sai na aika Asma'u ta karbo min na zauna ina ci.
Ina tsaka da ci sai kawai jin sallamar Sadauki mukayi wai ashe duk mondays yake zuwa ya gaishe da Inna. Na sunkuyar da kaina ina jin wainar ta fita daga raina har ya shigo ya gaishe da Inna da Mama sannan na dago na gaishe shi. Ya amsa yace "ya family?" Sai na kasa reply. Ya mike zai tafi Mama tace "oh Sadauki kaki aure har yanzu? Ko so kake ayi maka kidan tuzuru ne?" Ta tsaya yana shafa kansa, muka hada ido yace "an kusa ai mama insha Allah" Inna tace "alhamdulillah, ai gwara ayi din, aure ai shine cikar kamala da kimar mutum. An sami matar kenan" yace "eh, a can gida ne. A Maiduguri ne" sai naji wainar dana ci duk ta tattaro ta dawo makogwaro na, da sauri na mike na shiga toilet sai da na amayo duk wainar da naci.
[2/19, 5:19 PM] +234 818 247 0922: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Seven : The Messages
Sai dana gama sannan na zauna akan toilet seat na dafe kaina, ina jin jiri yana juyani duk da cewa a zaune nake. Nayi iyakacin kokari na gurin ganin cewa ban yi tunanin maganar da Sadauki ya fada a palo ba sannan na mike na wanke bakina da fuskata na fita, ina tunanin ya riga ya tafi amma ina fita sai na ganshi a tsaye yana kallona yace "ba kya jin dadi ashe? Allah ya sawake" na sunkuyar da kaina ciki ciki nace "ameen" sannan na wuce shi zan shiga cikin daki Inna tace "ba kiji Sadauki yana miki sannu ba? Shine kika wuce ba zaki amsa shi ba?" Na juyo nace "Inna nace masa ameen, ameen, ameen summa ameen,me kuma yake so ince masa" sai kawai yayi murmushi ya juya ya fita, inna kuma ta rufe ni da fada Mama tana taya ta, na zauna kawai nayi tagumi da hannu bibbiyu ina jinsu har suka gama sannan na zame na kwanta a gurin ina jin jikina kamar mai zazza蓳i har Mama tayi mana sallama ta tafi.
Kwana biyun haka na kare su babu lafiya sosai, na so inki komawa saboda bana jin dadi amma Inna ta matsa Saghir ma kuma yace in ma zan zauna sai dai ya dauki Subay'a saboda makaranta ni kuma bana jin zan iya barin ta tare da Fauziyya dan nasan ba kunya ce ta ishe ta ba. Dan haka dole na shirya Saghir yazo muka tafi. A hanya ya kalleni yace "kin kara kiba, baki da lafiya amma kinyi kiba kin kara fari. What's the secret?" Na bata rai nace "what secret kuma?" Yayi murmushi "wai cewa nayi ko Subay'a ce zata yi kani? It is about time, tayi girma da yawa" na juya kai ina kallon titi" I missed my period wannan watan, a lokacin bikin nan ya kamata inyi kuma banyi ba but that doesn't mean anything tunda dama ina missing sometimes. Ina ganinsa yayi packing a bakery suka shiga shida Subay'a suka lodo kayan ciye ciye sannan muka tafi.
A toilet da zan shiga wanka na tsaya ina kallon kaina a mirror, da gaske nayi girma na ciko ta koina musamman hips, abinda da bani dasu sai yanzu suke zuwa kuma. A raina nace "sai yanzu makerin budurci ya tuna dani" after I lost mine long time ago.
Na fito daga wanka kenan ina shiryawa text ya shigo wayata. Na daga sai naga number din Sadauki, a raina nace "really? Ko dai batan kai yayi?" Sai kawai na ajiye wayar nayi shiryawa ta. Saghir ya shigo da magunguna a leda ya bani yana taba wuyana yace "gobe asibiti ya kamata muje in zazzabin nan bai tafi ba, test nake so ayi miki ma dan ni jikina yana bani ciki ne" nace "no fa ba wani ciki" amma a raina sai naji ina son ma ace cikin ne, I was really in need of love, kuma ina ganin haihuwa zata taimaka min sosai" na kwanta na dauki wayata yace "za'a fara karatun ko? Bana hana ba?" Nace "to me zanyi? Babu wani abin yi sai dai mutum yayi bacci ya tashi ya gyara gida yayi girki ya kuma komawa tayi bacci" ya danyi shiru yana kallona kamar mai tunani sai yace "kina son komawa school?" Nayi saurin kallonsa, ban taba tambaya ba saboda banyi tunanin zai bari ba amma raina yana so, ina son in zama abinda baffana ya ke kwadayi, nace "da gaske?" Ya daga kafada yace "why not? In dai zai faranta miki that's what I will do" sai na kama tsalle ina murna shi kuma yana dariya sannan ya jawo ni yace "so? Me zaki karanta?" Nayi shiru ina tunani. Na tuna wani visiting da Sadauk yaje min school shida wani abokinsa and we talked about carrier, a lokaci nace musu bani da choice sai Sadauki yace later in life zan fahimci role din daya kamata inyi playing a rayuwa, but yet still, bani da choice a raina.
Nace "me kake ganin ya kamata?" Yace "anything. Nasan ku mata da son harkar health, zaki iya yin nursing ko midwifery. In ma kuma medicine din kike so sai inyi wa Mr Abatcha magana ya hada ni da wani a samo miki admission" na ture shi ina jin raina ya baci nace "forget Mr Abatcha din nan" yace "why? Shi ya bani wannan shawarar ma fa, ya tambaye ni kina makaranta nace a'a sai yace ya kamata in saka ki. Kinga ai he will be willing to help" na girgiza kaina nace "na fasa karatun" sai kawai ya tsaya yana kallona da mamaki.
Sai da zan kwanta na bude message din Sadauki "ya jikin? Allah ya kara afuwa ameen" nayi tsaki na ajiye wayar na kwanta, sai kuma na tashi na sake karantawa sai kawai na kashe wayar na jawo drawer na saka ta nayi kwanciya ta.
Da safe muna breakfast gabaki dayan mu har Fauziyya, ya ajiye ledar drugs din daya siyo min jiya yace "kina gama cin abinci zaki sha magani, dan naga ashe jiya baki sha ba kwata kwata" nace " in tambaye ka mana Please" ya ajiye spoon din hannunsa yace "ina jin ki" nace "ya sunan ogan ku na office" ya bata rai yace "Mr Abatcha mana" na girgiza kai nace "sunan shi na gaskiya nake nufi. Like sunan da yake rubuta wa in an bukaci sunansa" ya danyi tunani yace "Engineer Aliyu Umar Abatcha" na gyada kai nace "ohh okay" yace "me yasa kika tambaya?" Nace "a bikin nan ne naji ana zancen wani, I tot shine ashe bashi bane ba" yayi murmushi ya fara praising Mr Abatcha "yana da kirki sosai, na girme shi amma mi gaskiya he is my role model. He is very smart and intelligent. Kuma yana sona. Kunga yadda yake korar mutane kuwa duk wanda yaga wasa yake yi ba aiki ba yanzu zai tura maka quiry amma ni ko sau daya bai taba bani ba. Diyam kin tuna sanda ya tura ni Germany? Sai da naje na fahimci ya tura ni ne kawai dan in huta ashe already ya riga yayi sighing contract din. Sai dan workshop dana ringa zuwa kawai" na girgiza kaina a raina nace 'ya tura ka ne dan ya samu damar zuba kaji a gidan ku'.
Munje asibiti anyi min pt and it came back positive. Sai naji dadi, maybe wannan haihuwar ta zamo min silar gyaruwar lamura na. Saghir kam doki har a gaban Fauziyya, ya bawa Subay'a labarin zata yi sister ko brother ita ma tayi ta murna. And yana fita sai gashi da sabuwar waya, yace "wannan tsohuwar wayar taki dai ya kamata ki ajiye ta haka" na karba nayi masa godiya sai kuma ya tambaye ni in akwai abinda nake so. Na zauna kusa dashi nace "so nake kayi wa su Murja aure" ya bata rai, nace "Please, auren suke so wallahi kuma Alhaji bashi da halin yi musu to waye zaiyi musu in ba kai ba? Su ba karatu ba, su ba aure ba me kake tunanin xasu yi?" Yana kallona yace "sai in kinyi min alkawarin kema zaki koma school" nace "sai in kayi min alkawarin zaka daina shan giya" ya daga kafada "na daina fa" na tsare shi da ido sai yace "na kusa dainawa. Seriously na kwana biyu rabo na da ita" nace "mata fa?" Yace "na daina wannan tunda na kara aure ai" sai kuma ya jawo ni yace "tell me, kishi kike yi?" Nace "Saghir ko bana sonka, kai mijina ne, kuma uban yayana, ba zan so kuma yayana su tashi suga babansu da wadannan halayyar ba". Yayi murmushi yace "am getting there".
And two days after that. Ina ta aiyukan gyaran gidana, da yake ni ban damu ba ko aikina ne ko na Fauziyya ni in dai na tashi zan gyara gida saboda bana son kazanta, it irritates me, ina mopping kasa Saghir ya leko ta stairs yace min "ina tsohuwar wayar kine? Naga har yau baki kunna sabuwar ba" nace "tana bedside drawer ta" na cigaba da aikina.
Na gama naje na wanke mop, na dawo ina saka turaren wuta Fauziyya ta sauko ta kunna tv ta kwanta tana kallo. Sai Saghir ya sauko da wayata a hannunsa, I looked at his face and I felt something knot in my stomach. Ya nuna min wayar "waye wannan?" Fauziyya ta mike zaune tana kallon mu. Message na gani a jikin wayar "ya jikin? Allah ya kara afuwa ameen" na girgiza kaina nace "duba ni ake yi, what's there?" Sai yayi scrolling sama, tun message din farko.
"Third option. Kazo a baka hakurin da kake so"
"tomorrow evening. Gidan Baffa"
"ina yiwa Asma'u godiyar kyautar da aka yi mata. Allah ya kara arziki mai albarka"
"You are welcome".
Na daga kafada, ni banga abin tayar da hankali a cikin maganganun mu ba. Ya sake cewa "waye wannan Diyam? Sadauki ne ko? Amana ta kike ci ko Diyam? Wato abinda yasa kike guduna saboda kina samu a wani wajen ko? I always tot, yarinyar nan sai kace dutse, ashe kina da tap din da kike karbar rabonki a gurinsa".
Na zaro ido "wanne irin magana kake yi? How can You even accuse me of that. Menene a cikin messages din nan da zasu saka har ka fadi haka? Yes, munyi magana sanda suke case da Alhaji Babba kuma yayi wa Asma'u kyauta na yi mata godiya. Menene a ciki?" Yace "to uban wanene ya gaya masa baki da lafiya har yake duba ki?" Nace "a gida ya same ni yaje gaida Inna yaga bani da lafiya. I don't even know me yasa nake defending kaina. Dan kana yin abu sai ka dauka kowa ma yi yake yi?".
A girgiza kai idonsa jawur yace "am going to trace him. Am going to enter his number into my phone and call him. In na gano inda yake kuma wallahi sai na daure shi. Sai yasan matata ya taba" ya juya da sauri zai koma sama sai nayi saurin rike rigarsa "Saghir ka tsaya ka saurare ni. Wallahi ba abinda kake tunani bane ba" ya juyo a fusace ya sauke min mari a fuskata, kafin inyi wani abu ya sake sauke min wani a same side. Na rine fuskata ina jin jini yana bin hancina, ganina yayi dusu dusu. Amma still na rike rigarsa i a girgiza masa kaina, ta gefen idona na hango Fauziyya tana dariya, sai ya warce rigarsa ya hankada ni da karfi na fadi, unluckily sai cikina ya bugu da kafar bene, na mirgina gefe ina rike marata da hannun bibbiyu shi kuma yayi sama da sauri ba tare daya kalli inda nake ba.
Na sake kokarin mikewa amma marata ta rike kam sai da kyar na daddafa stairs na mike, tunani na daya shine in Saghir yayi dialing number din Sadauki a wayarsa zaiga Mr Abatcha. And that can destroy Sadauki's reputation a gurin aikinsa. Na juya na kalli Fauziyya da take zaune tana kallo na da murmushi a fuskarta nace "get up from my chair. Munafuka"
Sai na kama bene ina tafiya a hankali nabi Saghir a baya. Ina hawa sama yana fitowa daga dakinsa hannayensa da waya ta da kuma tashi. Nace "ka saurare ni Saghir" bai ce komai ba ya fara daddanna wayar sa. A lokacin mara ta tayi wata irin murdawar da sai da na kai kan guiwowina na runtse idona, sai ji nayi yace
"Mr Abatcha? Menene hadin Sadauki da Mr Abatcha?"
[2/19, 8:38 PM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Eight: When The Going Gets Tough
Bature yace "when the going gets tough, only the tough gets going" hakane?
It is either you get tough ko kuma kana ji kana gani a tafi a barka.
"Mr Abatcha? Menene hadin Sadauki da Mr Abatcha?" Na dafa bango na mike ina kallonsa kawai. Babu abinda zance masa a yanzu, dama kokari na shine inyi preventing dinsa from finding out kuma ya riga yayi. So magana ta kare kuma.
Ya zuba min ido, "magana nake miki Diyam? Sadauki kike texting ko Mr Abatcha" kallon da nake masa yasa ya tsaya shima yana kallona and then the realization hits him. I saw lokacin da yanayin fuskarsa gaba-daya ya chanza, ya saki wayoyin duk guda biyun suka zube a kasa. His whole world came crashing down on him.
"Mr Abatcha? Mr Abatcha shine Sadauki? When? How?" Ya saka hannayensa duk biyun acikin kansa ya fara zagaya palon da sauri har wani gumi ne yake karyo masa. Idonsa ya ciko da kwalla. Ya taho da sauri ya tsaya a gaba na "you? You were playing me all these years? All these years kina tare dashi dama? My God!" Ya sake dora hannu aka jikinsa har rawa yake sai ya dafa kujera yana mayar da numfashi. Ya jima a haka sannan ya juyo yana kallona sannan yace "ke kika saka shi ya bani aiki ko? I remember ke kika ce inje in nemi aiki. Ke kika saka ya dauke ni without even looking at my credentials saboda ku kasance tare ko? Saboda kuyi controlling dina ko? Is that it?" Na girgiza kai kawai amma kafin inyi magana yace "kar kice min komai, ko inzo in babballaki anan. My God, wannan wanne irin cin amana ne, hatta sunan da zan sakawa yata shi ya zaba min" sai ya fara dukan kansa da hannunsa yana cewa "wawa, dolo, soko, dakiki".
Sai kuma ya zauna akan kujera ya dafe kansa da hannayensa yana girgiza kai. Yace "wato tare kukayi planning din abinda aka yiwa Alhaji ko? Shi yasa ya tura ni tafiya a lokacin. Da aka gayamin sharadan daya saka sai da nayi tunanin me yasa a ciki bai ce in sake ki ya aura ba, ashe baya bukatar wannan tunda already yana tare da ke".
Kamar wuka haka maganganun Saghir suke huda ni. Wannan accusations din yana daya daga cikin abinda na kasa mantawa har yau. Komai zan gaya masa ba zai fahimta ba, amma duk da haka zan gaya masa ruwansa ne kuma in ya dauka in kuma bai dauka ba matsalar sa. I was beyond caring a lokacin.
Nace "sanda Sadauki ya dauke ka aiki bansan shi bane ba, bai taba contacting dina ba, I had no idea yana ina ma har sai ranar da kuka shirya masa party, a ranar nasan shine oganka. Bansan dalilin sa na daukan ka aiki ba, zata iya yiwuwa ya dauke kane kamar kowa, wannan shi yasa ban gaya maka ba tunda ina ganin fadin bashi da amfani. Bamu taba magana ni da Sadauki ba in banda sanda Alhaji ya tura ni gurinsa, a lokacin ma yayi shutting dina out dan haka babu maganar da muka yi sai wadda takaini. Bamu taba waya da Sadauki ba. Texts din da ka gani sune a tsakanin mu. Wannan shine gaskiyar magana" na juya zan bar gurin naji kafafuwana sun rike tun daga cinyoyi na zuwa marata suna min wata irin suka. Nace "Saghir?" Bai amsa ba sai cewa yayi "karki gaya min karyar banza. Wallahi bai isa ba. Baku isa ba daga ke har shi kuyi min wannan cin mutuncin. Sai na nuna masa dukiyar sa ta banza ce wallahi sai ya raina kansa. I will destroy him ko zan rasa raina wallahi." Sai ya shiga daki ya dauko key din mota, zai wuce ni na rike rigarsa nace "Saghir bani da lafiya" ya kwace rigarsa yace "zaki warke ne ma, munafuka" ya fice ya barni without another look at my side.
Na daga rigata naga jini yana bin kafata a dai dai lokacin dana ji tashin motarsa. And I realized something, na rasa cikin jikina kamar yadda na rasa twins dina. And there and then na yanke shawara, na gama auren Saghir.
Nayi kokarin motsawa daga gurin na kasa. Ina so in taimaki kaina kuma ina son in warning Sadauki dan ban san me Saghir zaiyi ba daya fita amma na kasa zuwa ina waya ta take yashe a kofar dakin Saghir. Kafafuwana tamkar sun daina aiki haka nake jinsu sai jini ne yake biyo su zuwa kan tiles. Option dina daya, Fauziyya. Na fara kiranta da dan abinda ya sauwaka daga murya ta. "Fauziyya, Fauziyya" amma shiru, ban tabbatar ta jini ba ko a'a saboda nasan kallo takeyi. Na jima a haka sannan na jiyo hawowarta sama. Tana shigowa palon ta tsaya tana kallo na yadda na hada gumi ga busashshen jini a hancina ga kuma jinin da yake kwance a kasa na sai ta saki purse din hannunta ta taho da sauri "Halima? Me ya same ki haka?" Cikina kawai na iya na nuna mata, ta kama ni ta kwantar a gurin sannan ta koma ta dauko jakarta data yar ta dauko wayarta ta fara kira. Jikina ya bani Saghir take kira sai kuwa mukaji wayar tasa tana kara a kusa da tawa. Ta ajiye wayar tace min "ina ya tafi?" Kaina kawai na girgiza mata, sai tace "ko miscarriage kike yi ne? Ko asibiti zamu je?" Na gyada mata kai sai ta kama ni zuwa toilet dina, ta taimaka min na wanke jiki na amma fa jini zuba yake dan pad ma ba zata rike shiba sai face towel ta bani na saka muka tafi. She half carried my down the stairs sannan ta saka mai gadi ya samo mana abin hawa muka tafi asibiti. Wannan yasa ba zan taba mantawa da Fauziyya ba.
Bayan fitar Saghir daga gidansa ya shiga motarsa ransa a mugun bace, bai taba jin bacin rai irin na ranar ba danji yake kamar ya hada ni da Sadauki ya saka mana wuta mu kone. Sai kawai ya bude aljihun motarsa ya dauko wata tsohuwar ajjiyar sa da kullum in ya dauko zai sha sai ya tuna yayi wa Diyam alkawarin ya daina sha. But yau Diyam din ce da kanta ta bata masa dan haka with vengeance ya shanye kwalbar gabaki dayan ta sannan ya kunna motar ya fita daga gidan ya tunkari kamfanin Abatcha Motors.
Sadauki yana cikin meeting da ma'aikatan sa, meeting din da ba'a ko gayyaci Saghir ba sai assistant dinsa. Sadauki yana tsaka da yin bayanin sababbin dokokin da yake kafawa saboda ma'aikatan da suke incompetent da irin hukuncin da za'a ke dauka akan duk mai karya doka sai ga Saghir ya banko kofa ya shigo, duk suka juya suna kallonsa ya taho yana tangadi ya nuna Sadauki yace "munafiki. Allah ya tona asirin ka yau" gaba-daya gurin suka mike, wasu daga ciki suka mike suka yo kan Saghir amma sai Sadauki ya dakatar dasu da hannu yace "ku rabu dashi" ya gyara zama ya kalli Saghir yace "menene yake tafe da kai?" Saghir ya nuna Sadauki yana kallon mutanen gurin yace
"wannan da kuke gani is not who he is saying he is. Ba sunan shi Abatcha ba sunan shi Sadauki kuma Sadauki shine Mr Abatcha kuma shine saurayin Diyam kuma Diyam kullum sai ta fadi sunan Sadauki ashe shine Mr Abatcha. Shine kuma ya bani aiki sannan ya saka wa yata suna ya siya mata ragon suna. Yazo kuma ya kai Alhaji kara ya karbi rabin gidan sa yayi gidan gona. Sai yau na ga message din sa a wayarta sannan na gane ashe shine"
Wani a gurin yace "do you understand cewa baka making sense kwata kwata?" Sauran mutanen suka kwashe da dariya. Sadauki yayi ajjiyar zuciya ya nuna Saghir yace "Ladies and gentlemen, this is an example of one of the effects of shaye shaye" sai ya kalli security yace "get him out of my sight".
A asibiti akayi confirming fitar cikina. Amma suka ce bai gama fita ba. Sai suka bani wani tablet suka ce zai fitar da sauran. Muna can lokacin tashin su Subay'a daga school yayi, Fauziyya ta koma gida ta dauko ta ta kai makotan mu sannan ta dawo gurina.
Har muka koma gida gurin magrib Saghir bai dawo ba. Na sha tablet din sannan na kwanta, Subay'a tana ta jera min sannu. Na sake trying number din Sadauki bata shiga, duk da dai nasan koma menene zai faru ya riga ya faru. Na kwanta ina ta jiran shigowar Saghir amma shiru har bacci ya dauke ni banji ya shigo gidan ba. Cikin dare wani azababben ciwon mara ya tashe ni, ji nayi kamar raina zai fita gashi daga ni sai Subay'a a daki. Jini guda guda haka ya rinka fita daga jikina. Ban yi bacci ba sai da aka fara kiraye kirayen sallah.
Cikin bacci naji Fauziyya ta shigo dakin tana tashin Subay'a, sai kuma tace min "Daddy fa bai kwana gidan nan ba. Ga wayarsa kuma tana nan. Na kira Kabiru kuma yace basa tare. Ko zaki kira gidan Alhaji kiji ko yana can?" Nace mata to kawai, amma ba wanda na kira. Ita ta shirya Subay'a ta mika ta school sannan ta dawo ta kawo min tea.
Zuwa 12 na dan warware, sai dai weakness sannan kana kallona zaka ga nayi pale saboda ba karamin jini na zubar ba. Na tashi nayi wanka, na fito na shirya sai na tsaya ina kallon kaina a mirror. Na dora hannuna akan marata ina tabbatar wa kaina cewa it is gone. It is dead before it even begins living. It is going to be the last thing da zanyi loosing a sanadiyar auren Saghir. Ina saka kaya na sai na jawo akwati na fara zuba kayana dana Subay'a. Ina cikin zubawa Fauziyya ta shigo, yanayin ta kamar a rude tace "Halima, kizo inji Kabiru" ta fita na saka hijab dina na bita a baya. Yana tsaye a bakin kofa ya kalle mu yace "Saghir yana station tun jiya. Bansan me ya faru ba amma ance security din gurin aikinsa ne suka kama shi suka damka shi a hannun police. Ban san menene charges din ba. Nayi kokarin yin bail dinsa sun hana ni, sunce order ce direct from the commissioner of police cewa kar a bayar da bail dinsa".
Fauziyya ta zame ta zauna. Ni kuma sai na juya nayi hanyar sama. Kabir yace "Diyam ki kira gida ki fada. Maybe Alhaji yana da wani a sama wanda zai saka a fito dashi" na gyada masa kai kawai na wuce. Ina zuwa daki na karasa hada kayana na fito na wuce Fauziyya a palo ta zabga tagumi na je na dauko Subay'a na dawo na sake wuceta. Na shirya Subay'a sannan muka sauko tare da akwatin kayan mu. Fauziyya ta tashi tsaye tana kallon mu tace "ina zuwa haka?" Nace "gida" bata kuma cewa komai ba har muka fita. Mai gadi yayi min sannu da jiki sannan ya taya mu da kaya muka tari abin hawa muka tafi.
Inna tana ganina da akwati tace "lafiya" na ajiye kayan hannu na sannan na gaishe ta, bata amsa ba tace "lfy nace? Lafiya na ganki da tsakar ranar nan da akwati?" Na sunkuyar da kaina nace "Inna na gama auren Saghir" ta saka salati, "shi Saghir din ne ya turo ki gida ko kuma ke kika yi ra'ayin kin gama aurensa kika taho gida? Dama igiyar auren a hannun ki take?" Na girgiza kai nace "Inna Saghir fa...." Tace "Saghir me? Saghir din yanzu ai bana da bane ba. Kika zauna da wancan Saghir din ma ballantana wannan da kowa ya tabbatar ya chanja. Dama tun randa Sadauki yazo nan da maganar aurensa naga yadda kikayi nasan in ba sa'a akayi ba sai kin fito da wata maganar kuma" naji hawaye ya fara bin fuskata, nace "Inna ba a kan Sadauki na taho gida ba, tsakani na da Saghir ne, ni ba zan koma gidan sa ba Inna. Dan Allah karki mayar dani" tace "ina Saghir din?" Na share hawaye na nace "yana police station" ta sake wani salatin "me ya faru? Me yake yi a can?" Nace "Sadauki ne ya rufe shi." Ta mike tace "kuma kika ce ba'a kan Sadauki bane ba. kira min Sadauki yanzu yanzun nan" nace "na baro wayata a can gidan. Kuma ma ba daukan wayata yake yi ba" ta kwalla kiran Asma'u. Tana zuwa tace mata "kira min Sadauki da wayarki" Asma'u tana kallo na da alamar tambaya ta dauko wayarta ta danna kira ta saka a speaker. Har ta gama ringing bai dauka ba sannan ta sake kira shima shiru. Sai kuma gashi ya kira. Ta dauka tasa a speaker naji muryar sa yace "Yar Asama ya akayi?" Tace "Inna ce tace in kira ka. Gata" Inna tace "Sadauki me ya hada ka da mijin Diyam har ka rufe shi?" Yayi shiru, ni kaina sai da nayi mamakin karfin halin Inna. Sai ta ce "tazo gida yanzu tace wai ka kama Saghir ka rufe shi" ya sake yin shiru sannan yace "ita Diyam din ce ta kawo kara ta akan na rufe mata miji?" Nayi saurin girgiza kai zanyi magana Inna ta harare ni tace "eh fa, shine nayi mamaki nace me ya hada ku?" Yace "a ce wa Diyam tayi hakuri, za'a fito mata da mijinta gobe in Allah ya kai mu" sai ya katse wayar.
Na saka sabon kuka "Inna yanzu haushi na fa zaiji yace na kawo kararsa" Inna tace "na sani ai. Haka nake so saboda ki fita harkarsa ki barshi yayi aurensa kema ki zauna ki rike naki auren". [2/21, 12:53 PM] +234 818 247 0922: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Forty Nine : The Utterance
Inna taga ta kanta a gurin jama'a jiya. Duk inda na shiga kowa kokawa yake yi da abinda Inna tayi. But to me, laifin Inna a yanzu guda daya ne, rashin sauraron Diyam kafin ta yanke hukunci bawai hada Diyam da tayi da Sadauki ba. Wannan kuma shine halin kusan 70% na northern mothers. Kullum su dai burinsu shine yarsu ta zauna a gidan mijinta kar ta kashe auren ta dawo gida ta zauna a gabansu. But what if the marriage is not working? What if she is buying her ticket to hell fire instead of paradise a cikin auren?
And Saghir, Saghir yayi laifuffuka da dama a baya but a yanzu laifinsa shine dukan Diyam. Nothing, nothing gives a husband the right to hit his wife. Duk kuma namijin da yake dukan matarsa to ba mijin aure bane ba, ballantana mata mai ciki? Hmmm
Then Sadauki. Na lura Sadauki ya zama shafaffe da mai a gurin readers, sam basa ganin laifinsa komai yayi daidai ne dan ina jin few mutane ne naga sunyi comment akan laifin Sadauki. Sadauki is rather rude and very authoritative. Ba shi da right din da zai sa a rufe Saghir, yes Saghir yazo gurin aiki drunk kuma ya fadi maganganu wadanda babu wanda ya gane in banda shi Sadauki da ake magana a kansa. Abinda ya kamata Sadauki yayi shine yasa ka security su fitar dashi waje, in ya ga dama ya hada masa da takardar kora daga aiki. But bashi da right din kaishi station a rufe shi kuma wai without bail, saboda yana da kudi?
Let's continue
Na rufe fuskata ina girgiza kaina da sauri. "Inna kar kiyi min haka dan Allah. Inna ki tsaya ki saurare ni ki fahimce ni kar ki mayar dani gidan Saghir in na koma wallahi mutuwa zanyi" tace "da baki mutu ba shekara da shekaru sai yanzu da Sadauki zaiyi aure shine zaki mutu?" Sai ta mike zata shige daki nima na mike da sauri na rike hannunta da hannu na daya dayan kuma na daga mara ta da shi nace "Inna nayi bari jiya" sai ta juyo tana kallo na ido a bude, ta taba fuskata da hannunta tace "bari Diyam? Ya akayi kika san bari ne kinje asibiti?" Na gyada kaina nace "naje Inna, su suka tabbatar min da cikin jikina ya fita Inna. Saghir ya fitar min dashi" ta dan bata rai cikin rashin fahimta tace "Saghir? Ta yaya Saghir zai fitar miki da ciki?" Nace "dukana yayi Inna, dukana Saghir yayi ya buga ni da jikin bene ya kashe min baby na, kamar yadda shaye shayensa ya jawo mutuwar yan biyu".
Sai ta kama hannuna muka zauna tace "Diyam, kin tabbatar abinda kike gaya min gaskiya ne? Me ya hada ki da Saghir har ya dake ki haka?" Na shafa fuskata sai itama ta saka hannu ta taba fuskar tawa, side din da Saghir ya mare ni, na dan yamutsa fuska alamar zafi sai naga idonta ya kawo kwalla amma sai tayi sauri ta mayar da ita. Tace "me ya ha蓷a ku nace" sai na bata labarin messages din Sadauki. Tana girgiza kai tace "me yasa? Me yasa zaki ajiye sakon Sadauki a wayar ki har mijinki ya gani bayan kuma kinsan yasan tsakanin ki da Sadaukin" nace "inna na fada miki menene a cikin sakon nan, babu wata kalma ko daya data kauce hanya a ciki kuma in na goge su ai kamar bani da gaskiya kenan. Ina son Sadauki na sani, amma Allah ne shaidata cewa ko sau daya ban taba tunanin yin sabon Allah da Sadauki ba. Kuma ke kece shaida, Sadaukin nan tamkar dodanniya haka nake a gurinsa, ko kallon inda nake baya yi. Shi dai ya zarge ni ne saboda shi din yasan shi mai laifi ne, abinda yake cikin tasa wayar idanuwa ma ba zasu iya gani ballantana hankali ya dauka" Inna tace "akan wannan maganar ne Sadauki ya sa aka kama shi?" Nace "ni ban sani ba, amma ina jin akanta din ne. Ya dai fita a fusace yace sai ya wulakanta Sadauki, tun daga nan kuma bai dawo ba sai da safe Kabiru abokinsa yazo yace mana yana hannun yan sanda" Inna tayi shiru tana tunani sannan tace "yace za'a sake shi gobe, Allah ya kaimu goben, ya fito sai yazo yayi bayanin dalilin da yasa ya dake ki. Kar ki goge messages din ki barsu saboda shaida a gani cewa babu abin duka a cikin su".
Sai naji raina yayi min wani irin dadi, babu abinda yafi dadi irin a fahimce ka babu kuma abinda yafi ciwo irin ace kana da gaskiya amma a hana ka tsarawa ballantana a fahimce ka. Ina ma dai iyaye zasu ke bawa yayansu wannan damar? A fahimci kowa sai a hada both parties ayi wa kowa fada dai dai da laifinsa? Ba wai ace da mace ki komaki cigaba da hakuri ba tare da ko murya an daga wa shi namijin da yake maltreating dinta ba, wannan tamkar ana ce masa ka cigaba da maltreating dinta ne.
Amma dana fara tunanin abinda zai iya faruwa gobe sai naji duk hankali na ya kuma tashi. Nasan halin Saghir sosai nasan zai iya jujjuya maganar gabaki daya ta koma laifina kuma na tabbatar iyayen mu musamman mazan bayansa zasu bi, musamman in nayi la'akari da irin kiyayyar su ga Sadauki, da kuma soyayyar da suka san ina yiwa Sadauki, tabbas komai Saghir ya gaya musu yarda zasuyi. Ni kuma ba yardar su ko rashin yardar su ce problem dina ba a'a tirsasani in koma gidan Saghir shine problem dina. Na gama auren Saghir, ba zan koma gidan Saghir ba. Wannan is my decision. Ni a yanzu auren Sadauki ko rashin auren Sadauki ko shi kansa Sadaukin basa gabana. Abinda yake gabana shine rabuwa da Saghir.
Inna tace inje in kwanta in huta a daki. Na tashi na shiga ina jin Asma'u tane cewa "Inna amma ba za'a mayar da Adda gidan can ba ko?" Inna tayi shiru bata ce komai ba. Na kwanta kawai sai hawaye ya fara zubo min ina lissafin abin da zanyi in akace sai na koma. A ciki har da guduwa na lissafa amma inna gudu inje ina? Yan uwan uwata dai sune yan uwan ubana sune kuma yan uwan mijina. Sai kawai na yanke shawarar in aka matsa min akan in koma gidan Saghir to zan gudu gurin Sadauki, inje in tuna masa da amanar da Baffa ya bar masa ta kula damu, sannan in tuna masa cewa ni ma fa yar Baffa ce ba wai Asma'u ce kadai yarsa ba. In kuma roke shi daya shige min gaba in kai karar Saghir court alkali ya raba auren mu. Yes, wannan shine abinda zanyi.
Ina kwance Subay'a ta shigo ta kwanta a kusa dani. Sai naji tana sheshshekar kuka, na jiyo nace "Subay'a? Lafiya kike kuka? Wani gurin ne yake yi miki ciwo?" Sai tace "Mommy ki daina kuka kema" na jawo ta jikina nace "ba kuka nake ba Subay'a ido nane yake min ciwo" tace "kuka kike yi ai na sani, naji kuma aunty Fauziyya dazu da tana shirya ni zan tafi school tana waya tana cewa kunyi fa蓷a da Daddy shine ya dake ki kike kuka, kuma naji dazu kina fada wa Inna Daddy ya dake ki" sai na kasa ce mata komai, lallai yara duk abinda ake yi a gabansu suna sane. Ta goge min fuskata tace "kiyi hakuri Mommy, in Daddy ya dawo zance masa kar ya kara dukan ki".
Sai na dage da addu'a sosai ina rokon Allah ya shiga lamari na ya kawo min agaji. Dan nasan in na koma gidan Saghir to ba rayuwata ta duniya ba har ta lahirar ma tangadi take yi, two zero kenan. Saboda ni dai nasan a rayuwar auren da nayi da Saghir a baya ba karamin zunubi na lodar wa kaina ba ballantana in na koma nasan bazan iya yi masa koda rabin biyayyar da nayi masa ada ba. In kuma haka ta faru to nice a ruwa dan Ubangiji babu ruwansa, laifina daban a gurinsa laifin Saghir shima daban. Kowa littafin sa daban. Dan haka sai na kwana ina kaiwa Allah kuka na.
Washegari tun safe nake saka ran wani abu ya faru amma shiru, ko ya naji anyi motsi sai in tsorata in dauka Saghir ne zai shigo gidan. In naji wayar Inna tayi kara kuwa dai inji kamar zan saki fitsari a wando saboda tsoron ko kira ne a kaina amma shiru. Da safe Inna tayi min farfesun hanta mai romo tace in cinye, na cuccusa da kyar naci dan bani da appetite sam, sai kuma ta fita da kanta taje kasuwa sai naga tayo cefanen green vegetables kala-kala tazo ta hada min miyar ganye mai naman rago ta sani naci da tuwon shinkafa tace zai kara min jini. Daga ni har ita babu wanda yayi zancen Saghir amma dai nasan duk maganar tana ran mu.
Shiru shiru har dare. Har gayi ya waye wani daren ya sake yi. Har aka kwana biyu sannan aka kwana uku, hudu, biyar, sai akayi sati daya. A ranar ne Inna tace "to ni ko Alhaji Babba zan kira ne akan maganar Saghir din nan ne? Kar dai ba'a sake shi ba har yau. Ni kuma bana son in sake kiran Sadauki kar yaga kamar ina damunsa akan sirikina yaji babu dadi" Asma'u tace "dan Allah Inna ki rabu dasu, yayi ta zama mana a cell din wa ya damu ne wai? Itama yanzu ba gashi ta samu kina kulawa da ita ba da yana nan kuwa ba vari zaiyi kije gidan ki kula da ita ba kuma ba lallai bane ya barta tazo nan" Inna tace "Asma'u kenan, ke yarinya ce ba zaki gane ba. Maganar nan fa tana kara jimawa ne tana kara karfi. Dole ya kamata in bincika inji halin da ake ciki" sai ta dauko waya ta kira Hajiya Yalwati, suka gaisa sai take tamayarta ko taga Saghir kuwa? Nan take Hajiya Yalwati tace "dama yanzu nake niyyar in saka kati in kira ki. Me ya hada Saghir da Diyam da tsohon saurayin ta kuma? Tun jiya naji ana ta maganar a gidan nan ni dai ba'a yi min cikakken bayani ba amma na fahimci kamar ko sunyi rigima ne harda su yan sanda" inna tace "Saghir din yazo gidan kenan" Hajiya Yalwati tace "yazo gidan fa, jiya nan ya kusan wuni sai dare ya tafi".
Tunda suka gama wayar Inna ta zauna ta zabga tagumi, sai ajima tayi ajjiyar zuciya ta sake wani ragumin duk tabi ta damu kanta. Nima kuma na damu din amma ba kamar inna ba, ni damuwata shine bansan zurfin sharrin da Saghir yake shirya min ba. Muna zaune kuwa, Asma'u ta kawo mana lunch kenan sai gasu sunyi sallama. Na ajiye spoon din abincin kawai na fara ambaton Allah dan ji nayi zuciyata kamar ta dawo wuyana.
Daya bayan daya suka shigo palo, Alhaji Babba, Kawu Isa, sai kuma Saghir. Inna ta tashi tana musu sannu da zuwa babu wanda ya amsa ta suka zauna. Ta gaishe su babu wanda ya amsa mata, dan haka sai naja bakina naji shiru ban gaishe su ba kaina a kasa. Kawu Isa ne yayi magana "gamu munzo Amina, mun sauke girman mu mu da muke manya munzo mun same ki tunda haka kike so. Kin bamu kunya Amina, Allah yaji kan hardo da inno, Allah yaso ba zasu ga wannan rana ba ba zasu ga wannan bakin ciki ba na abinda suka raina suka rike kamar abinda suka haifa kuma yazo yana yi musu bita da kulli. Amina yanzu ke wato duniya ta bude miki ido ko? Yanzu wato kudi sunfi miki yan uwanki ko?" Nace "Kawu...." Inna ta daga min hannu tace "kar ki sake inji bakin ki" sai ta juya tace "hamma kudi ba komai bane ba akan zumunci da halacci. Amma yanzu ni me nayi da har kake cewa na zabi kudi?" Alhaji Babba yace "me kika yi?" Ya nuna ni yace "wannan bata gaya miki abinda ya faru ba?" Inna tace "ta gaya min, ta gaya min komai har dukan da Saghir yayi mata da barin da tayi ta gaya min" Kawu yace "kuma ta gaya miki labarin cin amanar Saghir din da take yi tare da wannan tsinannen yaron? Ko kuma dama kin riga kinsan wannan labarin?" Inna ta girgiza kai tace "shi Saghir din ne yace Diyam tana cin amanar sa da Sadauki? Zai iya rantsewa da Allah cewa ya gansu suna cin amanar sa? Ko kuma zai iya rantsewa cewa sakon daya gani a wayarta ya nuna wata alama na cewa suna cin amanar sa" Alhaji Babba ya dubi Kawu Isa yace "kaji ba? Na gaya maka dama ta sani sarai. Da hadin bakinta ne akeyi komai. Ba dai yaron yayi kudi ba? Ni kuma na talauce" Inna tace "in kuka ce haka baku kyauta min ba. Yaron nan, duk cikin ku babu wanda ya kuntata rayuwarsa kamar ni. Tun yana cikin zanin goyonsa bana binsa da komai sai harara da muguwar magana amma me? Shine ya dauke ni a lokacin da Saghir ya watsar dani. Ya baku labari? Naje gidansa duba Diyam ya kore mu ni da Asma'u cikin dare ana ruwan sama. Badan Allah ya bude mu ba badan Allah ya kawo mana Sadauki ya taimake mu ba da yanzu babu Asma'u a duniya. Sadauki ne ya taimaka mana. Tun daga ranar kuma nayi nadama mai tsanani na kuma yi alkawarin yin rikonsa tamkar yadda zanyi rikon dana. Wannan ne yasa tun ranar da Diyam tazo min da maganar na kira shi nace ya sa a saki Saghir, sannan kuma na zauna ina jiran shi Saghir din yazo yayi min nasa bayanin inji" Kawu Isa yace "to mu yaje yayi mana bayani, ya gaya mana komai har yadda shekara da shekaru Diyam take tare da tsohon saurayinta, ta saka ya bashi aiki dan suji dadin cin amanar sa, yanzu kuma mun kuma tabbatar cewa duk abinda ake yi da sanin ki Amina. Wato ke naki salon sakayyar kenan a bisa dukkan alkhairan mu a gareki ke da yayanki. To gasu nan mun bar miki su, gaki nan ga duniyar nan ga kuma Sadauki nan. Ba dai kudi ba? Kamar yadda nawa ya kare haka nasa shima zasu kare sai kuma muga wanne sarkin za'a bi. Saghir dai kam ya gama auren Diyam. Dama tursashi muka yi ya aure ta ba'ason ransa ba saboda muna son mu karfafa zumunci da iyalin dan uwanmu kuma muna so mu rufa muku asiri. Taje ta auri Sadaukin mu gani, ba dai mune masu daurin auren ba?"
Na dago kai na kalli Saghir wanda tunda suka shigo yake tsaye a bakin kofa ya rungume hannayensa ya zuba min ido, ina jin idonsa a kaina amma ban kalle shi ba har saida Alhaji ya gama maganar sa sannan na kalle shi.
Sai ya tako yazo gabana ya durkusa yana kallon cikin idona yace "tunda nake a rayuwa ta ba'a taba yi min wulakanci irin wanda akayi min akan ki ba Diyam. Zan rabu dake, amma ba wai dan na hakura na yafewa Sadauki abinda yayi min ba sai dan wadanda suka ce in aure ki sun ce in sake ki. Na sake ki saki daya."
Sai ya dauke idonsa daga cikin nawa ya mike da sauri. Har yakai bakin kofa kuma sai ya dawo yasa hannu ya dauke Subay'a da take kwance kan kujera tana bacci ya dora a kafadarsa ya yi waje. Na mike da sauri kamar wadda aka mintsina nace "Saghir ka bani yata" ya juyo yace "in da ita kika je gidan ba sai ki karbeta ba in gani?" Na bi bayansa da sauri. "Ka bani yata Saghir, Subay'a! Subay'a!" Sai ta farka firgigit a hannunsa ta sauke idonta a kaina. Ganin ina kuka yasa itama ta saka kuka tana miko min hannu "Mommy! Mommy" yana fita waje ya saka ta a mota ya rufe ya shiga da sauri yaja ya bar gidan tun kafin su Alhaji su karasa fitowa".
0 comments:
Post a Comment