NI DA ABOKIN BABA NA....!!*
©JeedderhLawals
01
A nutse nayi sallama dakin Daddy na, dakin a shimfide yake da tattausan carpet sakar hannu kirar kasar India, ruwan hanta ne kamar yadda jeren kayan dakin suke. A hankali na zauna a kusa dashi ina kallon yadda yake sarrafa laptop dake hannunshi cikin kwarewa, ganin bashi da niyar dawo da hankalinshi gare ni, dama dai nasan halin baba in dai yana aiki baya maida hankalinshi ga kowa har ni er gaban goshin shi kuwa har sai ya gama. Remote na dauka na canza channel daga sports zuwa Zee World. Na ma manta ranar suna shirin da nake nacin kallo, Love Look Like What You Made Me Do. Dan Murmushi nayi nace woah, ni na ma manta da shirin nan. Daddy ya dan yi glancing din wajen da nake zaune ya kafin ya maida hankalinshi ga laptop dinshi. A takaice har aka gama shirin suka fara tallace-tallace Daddy bai gama abinda yake yi ba. Ba a jima ba naji na fara hamma, remote na dauka na mayar mishi da tashar da yake kallo na mike, daidai lokacin daya rufe laptop din nashi ya kalle ni cike da kulawa. "Uwata, ya aka yi ne?" sunan mahaifiyar shi gare ni shi yasa yake kirana da Uwata, su Mommy kam Ummi suke ce min. Baki na turo cikin dan jin haushi nace "ni barci nake ji..... Sai da safe!" er dariya yayi ya kamo hannuna ya rike ya janyo ni na koma kusa dashi na zauna ina kara tura baki na. Kumatu na ya dan ja, "ohhh m soooo sorry princess, na tsaida ki koh? Akwai muhimman bayanai dana tura ne yanzun shi yasa, ayi hakuri. Gobe zamu je mu sha ice cream ni da princess dina, are we good now?" kaina na kawar daga kallonshi, yasa hannu ya juyo da fuskata zuwa gare shi, "hey, m trying to pay for what I did, aren't we good yet?" bansan lokacin dana yi er dariya ba ganin yadda yayi da fuskarshi, Ina son babana fiye da tunaninku saboda yana sona sosai, kaunar da yake min ko mahaifiyar data haife ni bata nuna min kwatankwacinta. Ban sani ba ko don hakan yana da nasaba da cewa ni Kadai ce diyar su??. Kai na girgiza ina dan murmushi, "naji na hakura, but we will also go for shopping, agree??" ya gyada kai, yes. Tashi tsaye nayi nace to sai da safe Daddy. Murmushi yayi, ki tashi lafiya Uwata.
A main parlour naci karo da Mummy, da alamun turaka zata tafi ganin yadda taci kwalliya, ba wai ta fuska ba, ta jiki sai tashin kamshi take. Murmushi nayi naje na rungumeta, "Mommy sai da safe!" bayana ta dan shafa, "OK, sweet dreams baby" ta sake ni ni na wuce dakina ita kuma ta tsaya tana kashe wutar falon.
Ina shiga dakina wuta na kunna na shiga zare kayan jikina daya bayan daya, towel na zara na daura a jikina na fada toilet din dake manne a dakina. Cikin bathtub na shiga na zauna bayan na tara ruwa mai dumi, ban jima a ciki ba na fito. A cikin toilet nayi shafe shafen da zanyi, na fito. Kayan barci na saka marasa nauyi, kayan dana bari a tsakar daki na tsince na watsa cikin kwandon da nake tara kayan datti don nasan idan na bari Mommy ta gani gobe sai raina ya baci. Mommy mace ce mai tsabta da bata jurar kazanta ko ta anini. Kan katoton gadona nayi tsalle na haye kamar wata karamar yarinya, wayana na cire daga jikin socket na kunna data, social media na shiga na fara chat da friends dina. Ban samu barci ya dauke ni ba sai wajen karfe goma sha biyu na dare. Ban jima da fara barci ba naji numfashi ya fara min wahalar shaka, rigar jikina na fara adjusting daga jikina, ji nake kamar ita ta shake min wuya na kasa numfashi. Daga karshe tashi nayi gabadaya na cire rigar na jefar kasan gado na koma na kwanta. Dama don dole nake saka riga idan zan kwanta saboda fadan Mommy, ban cika kwanciya da riga a jikina ba saboda a yawancin lokuta na kan ji kamar rigar na shake ni ne, ban sani ba hakan sabo ne ko kuwa hali ne ko cuta? Ban sani ba, n I don't give a damn akan lallai sai na sani.
*☆☆☆☆☆*
Kiran sallar asubahi a cikin kunnena da yake masallacin unguwar mu a jikin gidanmu yake. Na saki gurnani a hankali saboda barcin daya cika min ido, da kyar na samu na iya bude idanuna suna komawa suna rufewa, na dauki kusan mintuna biyar kafin na iya tashi zaune, gashin kaina daya tattare ya barbaje min a fuska na tattara na maida shi baya, a hankali iska ya shiga kada sassan jikina hakan ya ankarar dani yanayin da nake ciki na babu riga, da sauri na dira daga kan gadon na dauki rigata na saka. Daidai lokacin Mommy ta leko, ganina a tsaye yasa ta maida kofar ta rufe ba tare da ta min magana ba. Sighing na danyi softly cike da jindadin bata kama ni ba. Bandaki na fada direct na dauro alwala, nazo nayi sallah na zauna Ina lazumi har sai da gari ya danyi haske, tashi nayi na fita daga dakina. Sai dana je na gaida Daddy sannan na shiga kicin inda na samu Mommy da Mama Sauda wadda take taya ta en aikace-aikace suna ta kokarin hada break fast, a nutse na gaida su sannan nima naje na kama musu.
Muna gamawa na koma daki nayi wanka na fito, na bata lokacina sosai wajen fente fuskata da nau'in kayan kwalliya Kala-kala kamar wadda zata je biki. Sai dana gamsu da kwalliyar fuskata sannan na tashi na bude wardrobe dina wadda take shake da kaya kamar na mutane biyar ko fi. A hankali nake kare musu kallo har idanuna ya sauka akan wata atamfa cote d'voire ruwan coffee wadda aka mata zane da peach da yellow a jiki, dinkin riga da siket ne. Siket din pencil ne sai rigar doguwa don ta kusa kai kin gwiwa, ita kuma dinkin ya kama ni cif daga kirjina, daga uku ne ya saki sosai yayi baza. Ina gama saka kayan nayi simple daurin dan kwali, na dauko gyale mai dan fadi peach color da er karamar jakar vincci na rataya na fita bayan na dauki wayar hannuna da takalmi coffee color mai dan tudu. Akan dinning na samu Mommy da daddy har sun fara karyawa, duka kallona suka yi ganin yadda naci kwalliya cike da alamun tambaya. Kujera naja na zauna a kusa da daddy ina kallonsu, "School zan shiga in amso IT letter na daddy" daddy ya gyada kai yaci gaba da cin kosan shi yana korawa da kunun gyada mai gardi, nima kunun gyadar na tsiyaya a cup na bude nadarar peak na kara a ciki na fara sha. A nutse muka gama cin abincin, na tashi na dauki jakata tare da yafa gyalena Ina kallonsu, "Mom, Dad, zan wuce sai na dawo" mom tace Allah ya kiyaye, daddy yace "ko dai in sa driver ya kaiki tunda ba jimawa zaki yi ba?" kai na girgiza, noo daddy, zan bi bus kawai. Ya gyada kai, "kudi pa?" nan ma kai na girgiza, "I've enough money wit me daddy" nan ma kai ya gyada, "OK, take care baby" Murmushi nayi na juya na fita cike da jindadin yadda iyayena suke kulawa dani, ta kowane fanni ni kam sai dai in godewa Allah daya bani iyaye kamar su.
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!!*
©JeedderhLawalS
*02*
Bus na hau directly har kofar gate din KadPoly inda anan nake karatun Diploma na akan Science Lab Tech. Kasancewar an tafi hutu makarantar babu mutane sai tsilli-tsillin wadanda basu tafi hutu ba kawai, a hankali nake takawa har cikin ofishin IT coordinator namu na karbi IT letter na na fita. Hostel din mata na wuce daga can dakin kawata Ramla don nasan bata tafi hutu ba, ila kuwa, Ina sallama cikin dakinsu muka ci karo da juna. Cike da doki muka rungumi juna muna juyi a tsakar dakin kafin daga karshe muka dire a Kan gadonta muna dariya. Kallona tayi tun daga sama har kasa har sama, ta gyada kai tana er dariya, "inye diyar daddynta! Wannan fresh haka kamar wadda aka wanke da inji?" duka na kai mata a cinya Ina dariya, "ke ba baki da mutunci Ramla, duk uban kashin wannan dana tara a wuya zaki ce wai nayi fresh?" sai da muka gama shakiyancinmu na abokai sannan na kalleta, "ke ni ba wannan ba, ya zancen inda zamu je muyi IT ne don ban karbi letter na da wuri ba ban sani ba cikin wajajen da suka bamu ko zan samu?" Ta girgiza kai, "duk an cika a wajen pa gaskiya babu, nima tun last week na kai nawa suka ce wae an cika" fuskata ta dan yamutse, "lallai! Ya zanyi kenan?" kafada ta daga, "oho! Bake wae dadi gida ba kinje kin zauna kina hutu ba? Gashi next week zamu fara. Ni a Kano zanyi nawa" na kalleta "Kano? A Ina??" "cikin BUK, kin san Aunty Habi tana aiki da Lab dinsu, shine tace in je can inyi kawai. Har an kai letter sunyi accepting. Abinda ya shigo dani makarantar kenan na kawo accepting letter din" shiru nayi ina jijjiga kai, "Ramla ko dai nima can zanje inyi nawa IT din kawai? Nasan mawuyaci ne in samu waje anan" ta kalleni, "wa kike dashi a Kano?" nace oho! Daddy yana da mutane da dama acan, nasan ba za a rasa ba. Idan can dinne sai in dinga zuwa weekend gida..... Zan tambayi daddy inji dai tukun. Yaushe zaki tafi Kanon?" "ranar assabar kila" ta bani amsa. Na gyada kai kawai. Kayanta na tayata hadawa, tare muka fito da ita na janyo mata trolley ita kuma tana jan karamar jaka. Muna tafe muna hira da ita har bakin gate, anan muka ci karo dashi, My Crush!. Wata irin farinciki da murna suka rufe ni, Ya Allah ji nayi kamar in daka tsalle. Ta gaban mu ya wuce without glancing at us, duk yadda naso in daure kasawa nayi, ban san lokacin dana kira shi ba. "Muneer!!" cikin wata iriyar murya mai kama da whisper, duk da haka sai daya dakata da tafiyar da yake yi ya juyo ya kalleni, Kai na sadda kasa ina jin wasu irin abubuwa na min yawo a jiki. Cikin siririyar muryar shi da zan iya cewa ita tafi daukar hankalina game dashi yace, "ohh Ummie, ya kike?" Murmushi na saki a hankali kaina a kasa, nace "lafiya qalau, ya karatu?" "Lau..." ya amsa, "....bari in wuce sai anjima..... By the way, I like ur dressing" bin shi nayi da kallo yana tafiya a nutse ina wani irin murmushi kamar kumatuna zasu hade da kunnuwana. Sai dana daina ganin kurar shi sannan na maida Kallona ga Ramlah wadda ta coge a gefe tana jifana da harara, murmushi kawai nayi tare da daga mata kafada naja trolley din nayi gaba. Tsaki taja ta biyo bayana, "wallah Tallahi Babe kina bashi haushi a rayuwa akan Muneer dinnan, kin rabe wa namiji yana yazga ki. Yanzu kaf fadin KadPoly waye bai san cewa kina crushing din wannan player din ba, abun haushi ma da alamun baya yi dake!" fuska na hade sosai. Abinda ke hada ni da ita kenan, kushe Muneer. Bata damu da yadda na hade fuska ba taci gaba, "haba babe, ki daina bayar damu mana. There r so many guys out there ciki da wajen makarantar nan dake karakaina akan ki, don Allah ki kyale wancan yaron. Ba son ki yake yi ba!" a fusace na kalleta, "yeah right! Ai dama ban ce miki yana so na ba koh? Hakan bai dame ni ba, inda rai da rabo, zan ci gaba da bibiyarshi kuma har sai ya so ni Ramlah! Idan hakan yana bata miki rai ki kauda idanun ki daga gare mu, dats all" Kallona ta tsaya tana yi kawai, ba wai yau muka saba irin wannan musun ba in dai akan Muneer ne, Kai ta girgiza a hankali tare da furta Allah ya ganar dake! Cikin gatse na amsa da Ameeen. Muka ci gaba da tafiya har bakin gate ba tare da kowa ya sake cewa komi ba, dama zuciya ce ta kowa a wuya, magana kadan sai ta tunzura mu. Muna fita bakin gate kowa yayi nashi bangaren, ita ta hau motar Abuja ni kuma na dau drop din tricycle har Unguwar Rimi.
Lokacin dana isa gida karfe sha biyu na rana bata karasa ba, kayan jikina na cire na saka na shan iska marasa nauyi na tafi kicin. Tare da Mommy muka hada abincin rana, ta shiryawa daddy nashi a cikin wani katon Basket mai kyau har da wani kayata shi da roses. Wannan Al'adar tunda na tashi naga Mommy tana yin ta, Indai daddy yana gari to abincin shi daga gida ake kai mishi, ba zan boye ba, abin yana burge ni, ina da niyar yin wannan Al'adar idan nayi aure. Direba ta ba ya kai mishi ofishin kula da harkar shigi da ficin jirage ta jahar Kaduna inda anan ne yake aiki a matsayin President na wajen. Ni kam sallah nayi sannan na fito dinning din, tuwon semovita ne muka yi da miyar danyen kubewa wadda ta sha busasshen kifi da tantakwashi da man shanu sai tashin kamshi take yi, sai zobo mai sanyi Shina anyi decorating dinshi da fruits. Muna hira da Mommy jefi jefi muna cin abincin na gaya mata yadda muka yi da Ramlah game da IT dina, shiru tayi tana Kallona kafin tace "zaki iya kuwa Ummi?" er dariya nayi, "haba Mom! It's not like ban taba zaman Kanon nan bane. I will b fine, after all anan zan dinga yin weekend dina ai" kai ta gyada, "sai ki jira daddyn ki ya dawo".
Koda na fadawa daddy abinda ake ciki ya dan nuna damuwarshi akan gida da zan bari, yace "Uwata tafiya zaki yi ki barmu mu biyu ne a cikin gidan nan kamar mayu?" ni kaina kuma sai a lokacin naji jikina ya fara sanyi, a sanyaye nace to daddy ko dai zan bari ne sai shekara mai zuwa sai inje? dariya suka saki shi da Mommy, daddy yace "oh ma silly princess! M not that wicked da zan hana ki karatun ki, bari in kira Dr. Ibrahim abokina ne, lecturing yake yi a BUK sai muji yadda za ayi" muna zaune ya kira shi suka gama magana suka yi sallama, "wai yace zaki samu sai dai a microbiology lab din su" Murmushi nayi, "daddy kasan fa dama nace maka idan na gama wannan program din zan nemi microbiology a ABU" yace faduwa tazo daidai da zama kenan? Na gyada kaina Ina Murmushi. Yace gobe zan tura mishi letter din sai a kai, Allah sarki princess dina zan yi kewar ki!.
Da dare kuwa kamar yadda daddy ya min alkawari muka fita, chicken republic muka je ya sai min gashin kaji muka tsaya a freeze center ya sai mana ice cream da tarkacen snacks muka koma gida. Tare muka zauna muka ci komi, sauran kayan mommy ta je ta adana su. Mun danyi hira dasu kadan har zuwa karfe tara da rabi, kafin na musu sallama na wuce dakina. Kayan barci nasa na kwanta a rub da ciki idanuna a rufe, daddy gaskiya ya fada. Tun yanzu nake ji kewar su tana dabaibaye ni, anya zan iya kuwa???!
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!!*
©JeedderhLawalS
*03*
Tun da muka gama hada breakfast na koma na kwanta barci, ban tashi ba sai wajen karfe goma na safe. Brush nayi na fita falo na karya, daddy ya fita wajen aiki. Dama dai Mommy full house wife ce, babu aikin da take yi. Shi yasa nace muku rayuwar auren iyayena tana matukar burge ni, Mommy tayi karatu har matakin masters akan Pharmacy amma daddy ya hanata aiki, duk wasu bukatu nata kuma ya dauke su ba kamar sauran mazajen yanzu ba da idan matarsu tayi karatu taki yin aiki sai labari yazo ya sha banban saboda ba zasu raba hidimomin gida tare ba. Wanka na shiga nayi, na fito na shirya cikin doguwar riga ta wani material grey mai dan nauyi, dinkin ya kamani tsam ya bi jikina, sai daga kasa ne ya baje sosai. Saboda yanayin kirar jikina dama ba wai kiba gare ni ba, er siririya ce ni amma fa Akwai kira, daga sama har kasa kam sai dai in gode Allah. Kalar fatar jikina baki ne, duk da ba wai can ba, zaku iya cewa chocolate color dai. Gyale na dauka na dora shi akan kafada ta na fita. Dakin mommy nayi knocking na shiga, tana zaune a gefen gado da dan littafin hisnul Muslim a hannunta. Kallona tayi na zauna a gefenta, a dan shagwabe nace "mommy dan Allah inje gidan Anty Uwani?" anty Uwani kanwar mommy ce, yaranta hudu duka maza, mun saba dasu sosai saboda zumuncin iyayenmu. Lokaci zuwa Lokaci na kan je can har in musu weekend. Mommy tace "kinga baki tambayi daddy dinki ba Ummie, babu ruwana pa!" kara shagwabe fuska nayi nayi nace "mommy da wuri pa zan dawo Allah" Kallona tayi na lokaci kafin ta gyada kai, "shikenan, but kar ki kai yamma fa!" cikin murna na gyada mata kai. Cike da doki na tashi, har na fita na sake komawa, purse dinta na bude na zari dubu biyar na fita da sauri ina dariya, kallo kawai ta bini dashi. A Unguwar Rimi suke zaune, sai dana tsaya na sai dangin fruits a bakin hanya sannan na karasa gidan. A can na wuni sur, sai gab da magrib sannan ta sa direba da danta na biyu AbdulJalal wanda yake kusan sa'ana ne suka rako ni gida. Daddy har ya dawo, Allah ya taimake ni ban sha fada ba saboda Daddy baya son yawo ko kadan. Bayan sallar isha'i ina zaune ina kallon film din Kaabil daga cikin laptop dina Ramla ta kira ni, murmushi nayi da naga sunanta a jikin wayata, wato har ta gama fushin kenan?? Da er dariya ta na daga kiran, "Lauratu ya ne?" haka nake kiranta idan naso tsokana. Ina jin dan siririn tsakin data saki, "ke pa u r a prof a ruining mood din mutum wallahi, meye wani Laure kamar wata Goggo a kauyen kayau?" dariya na sheke da ita cikin tura haushi, hakan ya kara tunzura ta kuwa. Sai da na gama tsokanarta sannan na tsaya ina sauraronta, hakuri ta bani game da abinda ya faru ranar, nima hakurin na bata tunda dukanmu we are at fault. Daga nan hira muka hau yi da ita, mun share fiye da awa daya muna hira har sai dana gaji don ni dama can ba gwanar hira bace musamman ma hirar waya, sallama muka yi kowa ya ajiye wayarsa.
Da dare muna falon daddy mu duka muna en hirarraki, aka kira daddy a waya. En maganganu suka yi kafin ya ajiye wayar yana kallona, "Uwata kinji an karbi letter dinki pa!" ban san dalili ba, gabana ya fadi ras! Rasa abin cewa nayi kawai na tsaya ina kallonshi, yaci gaba, "ranar Sunday zaki tafi mun gama magana da Ibrahim din. Sai ki fara shiri koh?" jikina naji yayi sanyi sosai, kafin kace me! Hawaye sun fara min yawo a kumatuna, cike da damuwa daddy yake kallona, "Uwata lafiya?" kai na gyada mishi a hankali, "I just started missing u ne daddy!" Dariya ya saki yayin da mommy tayi murmushi, hannu na ya rike a tausashe, "ohh my loving princess.... We gonna miss u!" group hug muka hada kamar zamu yi kuka.
Shirye-shiryen zuwa Kano na fara yi, hada tarkace, sallama da dangi da en abubuwa. Komi cikin sanyin jiki nake yin sa, wannan shine karo na farko da zanyi tafiya ta fiye da watanni uku. Daddy dinmu dan asalin garin Malumfashi ne ta Katsina, danginshi duk a Katsina suke zaune don haka mu kan je can idan mun samu hutu in musu kwanaki zuwa sati. Amma Ina jin wannan tafiyar ta banbanta, zuwa zanyi fa in zauna da mutanen da ban sani ba na tsayin watanni hudu zuwa biyar, a garin da ban sani ba duk da cewa mun yi zaman Kano na shekaru biyu, amma that was then, I think tun ina primary 5 ne??? Haka dai naci gaba da Shirye-shiryena har zuwa ranar Sunday. Sai wajen karfe biyar na yamma muka bar Kaduna, daddy ne ke jan motar, mommy na gefen shi ni kuma ina gidan baya. Tafiyar tayi min wani irin sauri, sai naga kamar muna tafiya ne akan iska ba kan kwalta ba. Cikin dan lokaci kankani mun isa Kano, unguwar Tal'udu muka wuce tunda anan gidan yake. Naji daddy yana ba Mommy labari game da abokin nashi, yace lecturing yake yi amma ba a staff quarters yake zaune ba, yace dan asalin garin Kano ne kuma yanzu haka yana neman kujerar dan Majalisa ne. Yaran shi uku da matar shi daya..., ni dai tunda naji yace yana harkokin siyasa na maida hankalina kan wayata, dan siyasa? Allah ya gani basu cika burge ni ba, ban son siyasa.
Kugi na karshe da motar tayi a cikin garejin gidan ne, tun daga cikin mota nake karewa gidan kallo. Ba wai yanke hukunci kai tsaye ba, yanayin gidan tafiy kafin ace mallakin just a lecturer (sorry lecturers, m not underestimating ur payment or something). Gida ne hawa daya, parking lots din gidan cike yake da manyan motoci ba na wasa ba, ga bikes da kekuna ina ji na yaran shine. Daga nan kana iya hango wani dan karamin garden a can gefen gidan, har wani dan karamin wajen wasanni na gani.
A hankali muka fito daga cikin motar, already wani da nafi kyautata zaton mai gadi ne ya fara kwasar kayana yana shiga cikin gidan dasu. Shi yayi mana jagora zuwa wani babban falo daya min kama da fadar uwargidan sarkin Kano, ya sha jere na wasu narka narkan leather seats kala biyu, farare da browns, ko wane jeren kaya yana da nashi dinning table, Plasma TV wadda zaka yi zaton zata cinye bangon falon saboda girmanta. Kafafunmu suka nutse cikin wani tattausan rug carpet kamar auduga, nayi iya bakin kokari na wajen ganin cewa ban hangame baki nayi kauyanci ba, maganar gaskiya ban taba shiga tsarraren falo irin wannan ba duk da cewa ba laifi nayi shige-shige a parlours da gidaje na manyan mutane, wannan kam looks extraordinary sosai. Kujera muka samu muka zaun 3 seats, ina tsakiyar su daddy, er aikin gidan ta fito daga kitchen ta gaida su daddy kafin ta shige wata kofa a cewarta zata kira madam. Ina jin lokacin da daddy yake gayawa Mommy ai Ibrahim din baya nan, yaje wani seminar. Ni dai ba baki, I was very nervous a lokacin. Mintuna kamar goma sai gata ta fito, Ya Allahu!! Meye wannan a gabana? Naji zuciyata tana tambaya lokacin da nayi tozali da matar. Don fari fa Akwai fari kamar Baturiya, kyawu ma Akwai shi Masha Allah, wata irin kiba marar fasali ne da ita. Lokacin data zauna akan kujera suna gaisawa dasu daddy sai naga ta shirge a waje guda kamar kayan wanki. Da kyar na iya saisaita kaina na dan zame daga kan kujerar na gaisheta, da er fara'ar ta ta amsa har da ambatar sunana, "Safeenah ko?" na gyada mata kai a hankali. Ta maida kanta gasu daddy suna er hira, idanuna suka ci gaba da wandering a cikin falon bana ma jin me suke fada. Aka kira magrib daddy ya fita sallah, ni da Mommy kuma muka yi a cikin falo don bamu samu albarkacin samun gayyata zuwa dakin matar gidan ba, kuma ba a nuna min inda zan zauna ba, karewa kayana ma suna nan baje a tsakiyar falon. 'yar aikin gidan muka tambaya ta nuna mana bayi dake nan cikin falon muka shiga muka dauro alwala, motar daddy naje na dauko prayer mat muka shimfida anan muka yi sallah abinmu.
Daddy yana dawowa daga sallah yace mommy ta tashi su tafi, nan fa idanuna ya raina fata da naga Mommy ta yiwa er aikin gidan magana akan taje ta gayawa matar gidan zasu tafi, idanuna suka yi raurau kafin kace me na fara hawaye shabe-shabe. Ba a dauki mintuna biyar ba sai gata ta fito tana taku da kyar, ban sani ba na takama ne ko kuwa dalilin kibar ta ne? Sallama suka yi dasu ta koma daki abunta. Hannuna mommy ta kama na musu rakiya har bakin motar su, zuwa lokacin kam kuka nake har da shessheka, suka saka ni a tsakiya suna lallashina har na samu kukan ya lafa. Ina nan tsaye suka shige mota suka ja suka tafi bayan na sha nasihohi daga gare su. Na bi bayan motar nasu da kallo har suka bar gidan aka maida gate aka rufe, na maida kallona ga dankareren gidan da zan rayu a ciki zuciyata cike da tarin damuwa iri-iri, daga can kasan zuciyata ina jin wata irin nadama na dabaibaye ni, Me ya kaini???? A hankali wasu siraran hawaye suka biyo kan Kumatu na.....!
Just want to say thank u for those following me, commenting and voting on this story. Please keep it up, keep voting, comment, and share it with your friends......
T
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!!*
©JeedderhLawalS
*04*
Sai dana kwashe lokaci mai tsawo a cikin farfajiyar gidan a tsaye kafin na samu kwarin gwiwar jan kafafuna da kyar na koma falon. Ina shiga na ci karo da er aikin gidan wadda saboda tsabar wata irin shiga mara fasali da tayi yasa na kasa gane ko wace irin yare ce, cewa tayi in zo muje ta nuna min dakin da zan kwanta inji madam dinta, babu musu na dauki jakar hannuna na janyo daya daga cikin jakunkunan dana taho dasu nabi bayanta bayan itama ta dauko wasu. Abinda na kula duka dakunan gidan a falon kasa suke, ni tunda nazo ban ga kowa ya hau saman ba. Wani dan madaidaicin daki cikin jerin dakunan dake cikin falon ta bude muka shiga ciki. Dakin yana da fadi ba laifi, Akwai toilet a ciki ga wani medium size gado ruwan golden, mirror da closet sai er karamar sofa da study table. A tsakiyar dakin an malala wani tattausan circle carpet baki, sauran dakin kuwa malale yake da wasu en ubansun marbles fari da gold, well, ba laifi ya burge ni sai dai yadda aka tsara dakin ne sam bai min ba. A raina nace sai na canza shi. Ina ta karewa dakin kallo har ta gama shigo min da kaya na duka, ta tambayeni idan Akwai abinda nake bukata? Kai kawai na girgiza mata tare da mata godiya, ta min sai da safe ta wuce abinta. Jakar hannuna na jefa akan gado na samu gefen gadon na zauna Ina kara karewa dakin kallo, tashi nayi na leka toilet, Shima babu laifi ya hadu, na dawo na bude closet din babu komi a ciki sai er guntuwar kura data yi, tsumma na lalubo na goge ta tas na lalubo turaren kaya a cikin kayana na watsa a gefen closet din kafin na fara shirya kayana a ciki, sai dana cika ta tsil da kaya wasu ma da kyar suka shiga, na makare kan mirror na da tarkacen kayan shafa dana kwalliya da nau'in perfumes kamar a wani dan karamin super store. Sallar isha'i nayi na hada da shafa'i da wutiri, ina gamawa naji wayana tana kara, ringing din dana sakawa daddy ne. Da sauri na tashi na daga kiran, gaisawa muka yi ya fada mun sun isa gida lafiya, mun danyi hira kadan yaba mommy wayar itama muka dan yi hira, sai data kara min da en nasihu akan wadanda ta min sannan muka yi sallama na ajiye wayar. Ruwa na watsa a jikina na nemi kayan barci marasa nauyi na saka na kwanta, amma kwata-kwata barci yace bai san idanuna ba, tunanika iri-iri suka dinga min yawo a kwakwalwa, daga karshe waya ta na dauko na fada duniyar gizo.
Washegari kamar yadda na saba da asubahi na tashi nayi sallah, shiru Ina kan abin sallah a zaune ina debating akan in fita in taya matar gidan aiki ko kuwa in zauna a daki? Daga karshe dai kawai na tashi na fada wanka, usual ways din harkokin rayuwata na bi, kwalliya data kwashe ni kyawawan mintuna talatin, minti ashirin na fiddo kayan sawa da shiryawa, zuwa lokacin dana tsaya a gaban dogon yaro ina sake duba kaina, karfe bakwai da mintuna ashirin. Cike da tunanin yadda zan karasa cikin makarantar BUK na fito falo, babu kowa a cikin falon amma na jiyo motsi a can wata kofa dake gefen dakin matar gidan. A hankali na karasa tare da lekawa, hangame baki nayi kamar zai rabe biyu. Wani dankareren kicin dana gani wanda zan iya cewa ya lunka dakina sau biyu, kayan electronics na kicin babu kalan wanda babu. A gaban gas cooker na hangi er aikin gidan tana soya plaintain, karasawa wajenta nayi muka gaisa cikin girmamawa, na tambayeta matar gidan tace min wai bata tashi daga barci ba, Kai na gyada cike da mamaki. Wace matar aure ce ke kai karfe takwas na safe saura tana barci?? Tambayarta nayi yadda zan isa wajen IT dina, tace ai Direban da zai kaini yana waje yana jirana, tun dazu yayi magana. Juyawa nayi na fita, daga kicin din tace min breakfast fa? Nace mata zanyi acan. A farfajiyar gidan na hangi direban, a mutunce na gaida shi ya bude min gidan baya na shiga yaja motar muka wuce. Mintuna talatin mun shiga cikin BUK, har gaban microbiology lab muka je yayi parking, tare dashi muka shiga lab din ya samu lab attendants suka yi maganganun da zasu yi, ya tafi ya barni bayan ya fada mun lokacin da zai dawo ya dauke ni. Ina zama sai ga Ramla sun shigo ita da Antin ta, nan muka rungume juna cike da murna, itama Anty Halima tafiya tayi ta barmu anan. Da yake ranar farkonmu ce a wurin babu wasu ayyuka da muka yi, wajen karfe goma sha daya muka fito ni da ita zuwa Cafeteria din dake cikin department din. Tafiya muke yi a hankali, tsarin makarantar ya burgeni kwarai, er hira muke yi da ita game da wajen har muka shiga cikin cafeteria din, babu students sosai zama kawai muka yi muka yi order din abinda zamu ci.
Muna gama cin abincin lab muka koma, lab attendants din were very friendly don haka cikin dan kankanin lokaci muka saba dasu. Wadanda suke yin aikin project dinsu sun kawo ayyuka, nan ne fa muka tashi muka fara aiki. Sai wajen karfe biyu muka tashi, wani dan karamin garden muka zauna muna ta hirarmu ni da ita ina jiran Direba yazo tunda ita sai ta jira Anti Halima ta gama ayyukanta, sai wajen karfe biyu da rabi sannan Bala Direba ya iso. Ina hango motar na gane ta saboda a cikinta muka zo. Da sauri nawa Ramla sallama na tashi nayi wajen da yayi parking, a mutunce na gaida shi na bude bayan motar na shiga.
*♡Jeedderh♡*
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!!*
©JeedderhLawalS
*05*
Wata kyakkyawar yarinya cikin kayan makaranta dogon wando navy blue da shirt fara ta dago kyawawan idanunta tana kallona, ban san lokacin dana sakar mata murmushi ba saboda tsananin burge ni din da tayi, a gaban motar kuma maza biyu ne suma cikin shigar kayan makaranta irin na yarinyar, duk suka juyo suna kallona. Zama nayi sosai a gefenta ina ta watsa musu Murmushi yayin da direba yaja motar, yarinyar da nake tunanin shekarunta zasu kai bakwai zuwa takwas tace min ke ce bakuwar da daddy yace zata zo mana gida? Na gyada kai ina kallonta, nice beauty, ya sunanki? Murmushi tayi, sunana Hafsah amma daddy yana ce min pretty Hafsey, su yaya Abdallah kuma suna ce min Hafsatu... Ta karasa tana pouting cike da shagwaba. Er dariya nayi tare da jan kumatunta, "kai amma Yaya Abdallah bai kyauta ba! Hafsatu ai sunan tsofi ne" ta gyada kai tana turo baki tare da kallon wanda yake kama da shine babban yayansu, "ai kullum sai na gaya mishi amma sai yace wae ai nima tsohuwar ce" na kalli yaron Ina Murmushi, "Yaya Abdallah baka kyauta ba gaskiya, tana yarinyarta ka dinga ce mata tsohuwa?" yaron yayi dariya, "sunan maman Daddy gareta pa, don Allah ba tsohuwar kenan ba?" daya yaron na gefenta ya kwashe da dariya, "tsohuwa ce mana, baka ga har ta fara furfura Akanta ba?" Hafsat ta kai mishi duka a kafadar shi, ya kauce yana mata dariya. Tsokanarta suka ci gaba dayi suna dariya har sai data fara kwalla sannan na tsaida su, "here, enough with the teasing, a kyale pretty haka nan ko?" ta gyada kai tana min murmushi, kanta na shafa ina jinta har cikin raina. Yarinyar tana da wani irin kyau duk da suma sauran yaran suna dashi amma ai kun san kyan mace ya banbanta dana namiji, ina mamakin inda ta gado shi a raina nace kila sai dai wajen mahaifinsu don babu mai kama da mahaifiyar su, dama dama dai Qaseem mai bin Abdallah, naga suna dan yanayi da Anti Mubeenah. Kafin kace me mun saba da yaran, dama ni bani da wahalan sabo suma naga hakan a tattare dasu. Muna isowa gida na dauki school bag din Hafsat ita kuma ta rike lunch box dinta, hannunta cikin nawa muka shiga falo ina taya ta miming din wakar twinkle little star. A daya daga cikin kujerun falon, Anti Mubeenah ce zaune ya harde tana duba jarida, yaran suka zube a gabanta suna bata labarin makaranta, sai dana bari suka gama hayaniyar su sannan na duka na gaida ta. Fuskarta dauke da dan murmushi ta amsa tare da ce min Akwai abinci a kicin, godiya na mata tare da cewa sai nayi sallah, dakina na wuce nayi sallah, na janyo wayata na kira mom don nasan daddy yana office ni kuma ban cika son kiranshi a wajen aiki ba, mun jima muna hira da ita kafin muka yi sallama, ana kiran sallar asr nayi na janyo system dina na kunna kallo tunda babu abinda zanyi, da a gida ne kila na shiga kicin ina taya mommy na girkin dare.
Ina zaune anan ina kallo Hafsat ta shigo cikin kayan makarantar islamiya, na daga Kaina na kalleta ina dan murmushi, "pretty Hafsat an dawo ne?" ta zauna a gefena tana turo baki, "malam ya bamu aiki a makaranta kuma ban iya ba, gashi Abbu da yake koya min karatun baya nan" zama nayi sosai akan gadona nace bani littafin in gani, ta bude jakar ta ta miko min na duba, Tawheed ne, tambayoyi akan imani. Murmushi nayi na kalleta nace "yanzu dai je ki kiyi sallahr magriba tunda an kira, bayan isha'i sai ki dawo mu yi" da murnarta ta tashi ta tafi, har ta kai bakin kofa ta dawo da gudu ta rungume ni, "Aunty thank u" dariya nayi na bita da kallo har ta bar dakin, kai na girgiza na tashi na fada bandaki.
Bayan sallar isha'i ina kan sallaya a zaune Qaseem yayi sallama ya shigo dakin, yace Aunty Nafeesah wae Mami tace kizo mu ci abinci, ba musu na tashi nabi bayanshi don dama yunwa nake ji. A kan dinning na samesu su duka suna cin abinci, gefen Hafsat naja kujera na zauna. Ganin kowa serving din kanshi yake yi yasa na dauki plate na bude flask din abincin, tuwo ne kaman na semovita miyar danyen kubewa, tunda naga miyar tsululu kamar ba danyen kubewa ba nasan cewa tuwon sai a hankali, Illa kuwa ina kai loma daya bakina da kyar na hadiye, tuwon gashi nan latab kamar danyen gari alamun bai gama dahuwa ba, miyar sai dan banzan yaji kamar da taruhu kadai aka yi ta, babu taste ko na anini sai shegen karnin kifi. Da kyar na iya hadiye lomar farko, ban yi kuskuren kai wata bakina ba don na tabbata idan na kuskure ta sake shiga bakina sai na amayar da dan guntun abincin daya rage a cikina. Su kansu na ga tsakura kawai suke yi, kallonsu kawai nake yi cike da mamaki. Ta ya za ayi mutane su rayu da irin wannan abincin a duniya? Koda yake yau ne karo na farko dana ci abincin gidan, ban sani ba kila rana ce ta bacewa mai girkin kawai, da wannan tunanin na gyada kaina na tashi daga kan table din bayan na wa Anty Mubeenah sai da safe. Dakina na koma naje nayi brush na wanke bakin da mouth wash, cikina wani irin hautsinawa yake yi saboda yunwa, jikar dana fita da ita dazu na bude, wata irin ajiyar zuciya na sake ganin Pack din cookies din New Yorkers, na manta dashi ma ni shaf dazu muka saye shi a cikin makaranta. Zama nayi akan gado na bude shi na fara ci, wayata na hannuna ina chatting, Hafsat ta shigo dakin. Tare da ita muka cinye cookies din, daga nan na koya mata aikin da aka basu, kallon film dina da nake kallo muka ci gaba dayi sai wajen karfe goma da rabi ta min sai da safe, na shafa kanta nace ki tashi lafiya pretty., kar ki manta pa kiyi addu'ar kwanciya barci kinji? Ta gyada kai, "thank u Aunty, sai da safe" na dan hade fuskata, "ohh pretty, sau nawa zan gaya miki bana son Aunty dinnan? Call me Yaya Nafee, bai fi dadi ba?" ta girgiza kai cikin tsokana, "babu dadi gaskiya" kofar dakin na nuna mata "oya, bi can sai da safe" ba musu ta tashi ta fita tana er dariya kasa-kasa. Tana fita na janyo wayata ina kallon screen din, a cikin messages nake ina shawara da zuciya ta akan abinda nake shirin aikatawa, daga karshe dai nayi typing, *"you sleep?"* na turawa Muneer, tsawon mintuna sha biyar babu amsa, na sake tura *"seems like you are, good night!"* na kashe wayar na dorata akan bedside table na kashe wuta tare da yin addu'ar kwanciya barci na kwanta.
*♡Jeedderh♡*
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!!*
©JeedderhLawalS
*06*
Nayi tunanin idan na tashi zan ga reply daga Muneer ko kuma missed call dinshi, sai dai har na gama shirina tsab babu shi babu alamun shi. Sai zuwa lokacin ne na fahimci imma dai yana sane yaki min reply jiya ko kuma yayi barci wulakanci ne ya hana ya biyo sahuna da safe, kwafa nayi ina jijjiga kai.
Ranar ma dai abincin safen sai godiyar Allah, plaintain ne aka soya da shayi da soyayyen kwai, tsakani na da Allah nasan ba zan iya cin abincin nan ba, haka nan dai na dan tsakura har zuwa lokacin da Bala yazo muka dunguma gaba daya har su Hafsat muka fita. A mota daya muka tafi dasu, sai da muka biya ta makarantar su muka ajiye su sannan muka wuce. Da rana koda muka dawo bamu samu Anti Mubeenah a gidan ba, har dare bata dawo ba sai bayan isha'i likis sannan. A zaman sati dayan da nayi a gidan zan iya cewa zama ne na takura, if not for Hafsat dasu Abdul I didn't think I would've survived. ita dai matar gidan yadda na kula da ita, bata cika jan mutane a jikinta ba, ni dai tunda nazo gidan ban ga bare ya leko ba, makota ne, abokai ko dangi. Tsakanina da ita gaisawa ne kawai, idan mun hadu a dinning mu danyi hira sama-sama, ga yawo, idan ta saka Kafa ta fita daga gidan tun safe sai dare take dawowa duk da Hindatu mai aikinsu naji tace tana da saloon da take kula dashi. GA er aikinsu kuwa ban ma san me zan ce ba, ni ban ga dalilin da zai sa in dauko er aiki ba kuma ba zata min gamsasshen aiki ba in kyaleta duk da cewa ni har ga Allah I dont have any plan na daukar er aiki Ina nayi aure, ga Hindatu dai kam abin babu bayani, ita ba ga girki ba, ita ba ga gyare-gyare ba. Aikin data iya daya; ta sha kona sanwa idan ta dora ta fara kallo.
A takaice dai kafin zagayowar ranar juma'a sai da naji Kano ta fita daga raina, ni ban saba irin rayuwar kadaici dinnan ba. Ranar juma'ar kuwa Ina dawowa daga wajen IT dama dan karamin kit dina a Shirye yake tsab, Anty ta fita yawon data saba sai sako na bari a wajen Hindatu nace tace mata na tafi weekend gida, dama Daddy ya turo wanda zai dauke ni, a farfajiyar gidan ma na dawo na tarar dashi yana jirana don haka babu bata lokaci muka wuce Kaduna. Sai wajen karfe biyar da rabi muka isa gida saboda yanayin go slow da muka samu a hanya kafin mu fita daga cikin Kano, da ihu na da komi na shiga gidan, kit dinma sai driver ne ya shigo min dashi. Mommy tana kicin tana girki ita kadai, na rungumota ta baya ina tsallen murna, juyowa tayi tana kallona cikin murmushi, "oh ni wannan yarinya tawa ban san yaushe zata girma ba" na buga kafa cike da shagwaba nace "mommy!!" dariya tayi ta rungumo ni jikinta cikin nuna kewa. Dakina na shiga an share min shi tass sai tashin kamshi yake yi, na cire kayan jikina na fita zuwa kicin na kamawa Mommy girkin, muna yi muna hira, yawancinta tambaya ce akan wajen da nake zaune, babu matsala dai ko? Kina cin abinci? Tambayoyi dai iri-iri. Muna nan Daddy ya dawo, har cikin kicin din ya shigo ya daga ni sama Cak yana juyi dani, dariya na saki na rirrike shi har ya dire ni kasa. Sannu da zuwa na mishi ya amsa yana shafa kaina, na amsa brief case din hannunshi na raka shi har dakin shi kafin na fito na barshi ya shirya.
Bayan isha'i muna falo zaune akan babbar tabarmar cin abinci, hira nake musu, duk abinda nake yi a Kano babu wanda ban tsallake ba, su kuma suna sauraro cikin nuna rashin gajiyawa na dariya su yi, na mamaki kuma su jinjina kai. Ranar kam sai wajen karfe sha daya muka yi barci muna ta hirar yaushe gamo. Kwana na biyu a gida na koma Kano cike da kewar iyayena, ji nake kamar inyi zama na acan.
Hindatu kadai na samu a gidan, tace yaran dama a gidan kakannin su suke yin weekend, ita kuma Anty Mubeenah tace wajen bikin kanwarta mawuyaci ne ma idan ba kwana zata yi a can ba, na jinjina kai tare da kwaso tsarabar fruits dana musu a hanya na shirya su a cikin fridge. Wajen karfe takwas na dare ina zaune gidan shiru babu motsin kowa, nasan da su Hafsat suna nan da yanzu suna dakin ko dai muna hira ko kallo ko kuma ina koya musu assignment. Horn din mota naji a bakin gate kafin naji karar bude gate, a raina nace Anty Mubeenah ta dawo kenan. Hasken motar ya ratso ta cikin windown dakina zuwa cikin labulaye na da yake window din dakin a kusa da garejin gidan take. Minti kamar biyar na bata na tashi na fita da niyar inje in mata sannu da zuwa. Tsaye a jikin fridge hannunshi dauke da gorar ruwan Sanah yana sha directly daga cikin gorar, hannunshi daya rataye da suit dinshi yana kuma rike da brief case. Dogo ne ba can ba, idan da ba don na sanshi a hoto ba to da zan iya rantsewa da Allah ince bashi bane, saboda ko a cikin hoton ban hangi yarintar dana gani a tattare dashi ba a lokacin, da nace yarinta ba wai ina nufin yaro bane, aah Ina nufin wanda bai kai girman daddy na ba; Abban su Hafsat ne. Wata irin gigicewa naji nayi, haka kawai naji kafafuna sun yi wani irin sanyi wanda ban iya daurewa ba sai dana dangana gwiwoyina da marble din dake malale a tsakiyar falon, ban sani ba tsabar kwarjinin da yayi min ne yasa gabana ya tsananta faduwa ko kuwa wani abu daban?? Cikin rawar murya nace "sannnnnu da..... Zuwa...... Abbbbuh!!".........
*♡Jeedderh♡*
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*07*
_*"There are no rules when it comes to love. I just let love surprise me because you never know who you're going to fall in love with. You never know who's going to come into your life.....*_ ___Taylor Swift.
Wasu kyawawan idanu farare tas suka dago suka kalleni, ban sani ba ko tsananin hasken da falon yayi ne ta dalilin hasken chandeliers din falon ko kuwa idanunshi ne a haka? Brown eyelids suna ta wani sparkling da sheki, haka kawai na tsinci kaina da faduwar gaba. Ya sauke robar ruwan daga bakinshi ya jefa ta cikin waste bin tare da cewa, "lafiya qalau Nafeesah! Kin zo bana gari koh? Hope komi lafiya?" na gyada kaina da kyar, wani irin nauyin mutumin naji ya dabaibaye ni. Ya gyada kai, "OK!" ya wuce dakin Anty Mubeenah abin shi. Kafa na na masifar rawa na tashi na fada daki, hannuna dafe da kirjina kamar wadda take kokarin tsayar da racing din da zuciya na take yi wanda ya wuce misali. Idanu na zare sosai ina kallon reflection dina a jikin mirror, I couldn't believe wai a haka na fita gaban Abbu. Kafar wando na daya a gwiwa, gashin kaina wani yayi baya, wani ya zubo a kafaduna, wani kuma ya tattare a gaban goshina saboda hular dana saka., idan ka ganni dai a lokacin babu bata lokaci zaka danganta ni da psychiatric patient dinnan irin stage one ma, kunya ta rufe ni sosai kamar in nutse a kasa haka naji. Tsalle nayi na dira akan gado na fara birgima, sai da nayi kaca-kaca da gadon sannan na saurara ina maida numfashi...
Karfe bakwai da mintuna biyar na safe na fito daga dakina a shirye na tsab, babu kowa a cikin falon. Kan dinning an shirya kuloli manya masu kyau, kila saboda dawowar maigidan ne aka fiddo sabbin kuloli don ban taba ganin irin su a gidan ba. Na bude kulolin, farfesun kan sa ne sai kamshin er daddawa da tafarnuwa yake yi, sai masa fara tas itama tana ta tururi a cikin wata kula, kunun gyada har da kosai. Kujera naja na zauna na zuba farfesun na fara ci kunnena har motsi yake yi, duk yadda aka yi abincin ba daga cikin gidan yake ba, idan ma daga gidan yake to ba Harira er aikin su bace ta dafa. A raina nace kila Anty Mubeenah ce ta dafa, Amma koda wasa ban ji kamshi yana tashi ba jiya ai. Na dai ture tunanin komi na ci gaba da dura abinci abu na, ina nan zaune na kusa gamawa Anti Mubeenah ta fito daga dakinta sanye da wando da riga na barci, ni kaina ina mace sai da shigar ta bani haushi. Gabadaya kirar ta marar fasali ta fita, tumbinta da zai sa kayi tunanin cikin en biyu ne ya fito yayi nashe-nashe a gaban ta, gashin kanta yayi buzu-buzu dan ma wai tana da yalwar gashi babu laifi, fuskarta sai naso take yi bana tunanin tunda ta tashi da safe ta wanke ta. Nayi kokarin kauda takaicin ta daya taso min na gaishe ta, ta amsa a kaikaice tana wani basarwa irin yadda take amsa min ta bude kofar dake fuskantar dakinta ta shiga, ina tunanin nan ne dakin maigidan don ban taba ganin ta shiga ciki ba tunda nazo gidan. Ni dai na gama cin abinci na na wuce abina. A farfajiyar gidan Malam Bala yana jira na, cike da girmamawa na gaida shi na bude bayan motar da kaina na shiga saboda na hana shi ya dinga bude min. Y'all ja motar muka tafi har cikin makaranta, ranar an kai wasu sabbin en IT lab din daga Leather Research Zaria don haka bamu samu cunkushewar ayyuka ba. Cikin dan lokaci muka saba dasu. Ranar tun karfe daya da rabi muka tashi, bayan mun fito daga lab din Zainab da Ikram suka mana sallama suka wuce gida, ni da Ramlah muka zauna a dan karamin garden din da muke zama muna tattaunawa akan saurayinta da yake so ya tura gidansu ita kuma tana ki wai bata so tayi aure yanzu ni kuma ina nuna mata rashin dacewar hakan, muna nan na hangi motar gida tana tunkaro mu duk da ba wadda aka saba kawo ni bace amma nasan duk motocin dake gidan, wannan shine karo na farko ma da aka zo daukar mu da motar, Anty Mubeenah naga tana jan motar. Na tashi muka yi sallama da Ramlah na tunkari motar, sai da nace tazo mu sauke ta tunda gidan su a hanyar mu yake amma tace zata jira Anti Haleemah don haka na kyaleta. Tun daga nesa Hafsatu ta fito daga cikin mota a guje tana min oyoyo, na tare ta da dan guduna muka fara juyi a wajen kamar wata yarinya, sai da muka gaji sannan na ja hannunta muka tunkari motar. Sai dana jira ta shiga sannan nima na shiga, na daga baki da niyar gaida Malam Bala kamar yadda na saba, "Malam Bala barka da war hak.....!" naji maganar ta kakare min sakamakon wanda na gani a gaban motar yana kokarin tada ta, da saurin na sadda kaina kasa tare da cewa "Abbu ina yini?" ya amsa idanunshi na kan titi. Ji nayi kamar wadda aka jefa ni cikin kankara, na kasa maida hirar dasu Qaseem suke min kamar yadda muka saba idan muka taho sai dai in gyada kai ko in bisu da uhm da ehh har muka isa gida. Cikin sauri na bude murfin motar na fita har ina hadawa da tuntube, ban tsaya a ko ina ba sai cikin dakina. Na zauna a gefen gado ina ajiye numfashi da kyar da kyar, ni kam me ke damuna ne haka? Ni dai nasan bani da wahalar sabo da mutane, amma me yasa a gaban mutumin nan nake ji na kamar wata haliita daban? Me yasa na kasa sakewa dashi? Me yasa nake jin kwarjinin mutumin har cikin tsakiyar kaina? Wata zuciyar tace min saboda ban jima da sanin shi bane, after all babban mutum ne kuma idan zan iya tunawa tun daga kan abokan daddy na har zuwa en uwanshi ni dai bude ido nayi na gansu tare, wannan kuwa daga sama kawai na san dashi, hakan da nake ji rashin sanayya ne kawai, idan na saba dashi komi zai daidaita. Da wannan tunanin naji na samu hope, na maida bayana na kwantar akan gadon tare da lumshe idanuna, a hankali barci ya sure ni, nasan biyan bashi ne tunda jiya ban samu nayi barcin kirki ba.
*♡Jeedderh♡*
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*08*
*...Then I cross a bridge for over million reasons to hold on.., hide away with me, walk away with me......*
*.....Then I cross a bridge for over million troubles to meet....., nothing is easy, nothing is easy......!* -Savina Drones_Glass Bridge.
Sai wajen karfe biyar da rabi na yamma na tashi daga barcin, toilet na shiga nayi wanka na fito na kimtsa jikina cikin wasu simple Pakistan riga da wando marasa nauyi, turare kadai na fesa a jikina da yake bana yin Sallah sai na koma kan gado na fara sana'ar chatting da kallace-kallacen film. Babu wanda ya leko dakina sai bayan isha'i Hafsat ta leko wai inje mu yi dinner, ina jin yunwa amma jin muryar Abbu a falon yasa nace mata a koshe nake, tayi tayi dani naki fita dole ta juya ta tafi tana gunaguni. Can kuma sai gata ta dawo dakin, "wai Abbu yace mai kika ci?" nace ban ci komi ba, Tun lunch ne amma ciki na a cike yake. Ta juya ta tafi, mintuna biyu ta sake dawowa, "Abbu yace ki fito ki ci abinci ko ran ki ya baci!" nayi shagaraaaa da baki ina kallonta cikin rashin abin cewa, ganin bani da niyar tashi yasa ta juya tana fadin "bari inje in gaya mishi kin ce ba zaki zo ba" da sauri na tsayar da ita tare da tashi tsaye na lalubi hijabi dogo har kasa na saka, Hafsatu ta saka ni a gaba kamar wadda zata gudu har gaban dinning table din Inda suke zazzaune bayan ta gama mitar wai gidan wa zan je dana saka hijabi, ban tanka mata ba, fargabar yadda zan zauna a teburi daya da Abbu ta cika min ciki, tsakani na da Allah ina jin kunyar shi. Naja kujera daya na zauna a hankali kamar wadda tayi laifi, daga Qaseem sai Abdul a wajen sai shi Abbu din Anty Mubeenah bata nan ban sani ba ko bata gidan ne? Tun kafin in gaida Abba ya tare ni, "wasa da cin abinci ko Nafeesah??" na sadda kaina a kunyace nace "Abbu na koshi ne" ya girgiza kai, "that's not an excuse, dokar nan gidan ba a skipping meals uku ko da wasa, idan ma mutum bai jin yunwa sai ya tsakura, idan kuma ya ki dura muke mishi koh?" ya kalli su Qaseem kamar yana tambayar su, yaron ya gyada kai yana er dariya wadda ta fito mishi da goyen hakoran shi, ni kaina I couldn't help it sai da nayi er dariya jin abinda yace, yace oya ci abinci. Babu musu na dauki spoon na jefa cikin jollop shinkafa da aka yi an kawata ta da nama, kifi, coleslaw da wainar kwai. Kamar dazu da safe abincin yayi dadi sosai kamar kunnen mutum zai tsinke, ga zobo mai sanyi a gefe ya sha kayan kamshi an yanka kankara, apple, cucumber da wasu nau'i'kan fruits dana kasa tantance ko menene. A nutse muke cin abincin, su Hafsat suna hirarsu da Abbu jefi-jefi su kan Sako ni a ciki ina amsawa da uhm ko a'ah, tun dai ina nodding har na dan sake na fara maida musu amsa sosai, Abbu yake tambayana game da karatu na ina bashi amsa a nutse. Muka gama cin abincin na kwashe kayan duka na kai kicin, sauran abincin da drink din na saka su a freezer su kuma kayan na wanke su tass. Falon na koma na zauna don Hafsat tayi kini-kini ta hana ni tafiya dakina dole na zauna a cikin su, su Abdullahi game suke yi a laptop din Abbu ita kuma Hafsatu na canza channels, bayan dogon lalube muka tsaya a mbc 3 suna hasko Despicable Me part 1. Muna cikin kallon muna kwasar dariya ni da Hafsat, gabadaya mun hade falon da hayaniya. Abbu ya fito daga dakin da yake fuskantar dakin Anti Mubeenah sanye da bakar jallabiya a jikinshi, take nayi tsit kamar bani ce nake ihun dariya ba. Ya zauna a kujera tare da daukar Hafsat ya dora ta akan cinyar shi tare da kallona, "are u a kindergarten kike kallon cartoon da girman ki??" kafin inyi magana Hafsat tayi caraf tace "Abbu tana dasu da yawa a cikin system dinta, har dasu na Disney princesses da fairy tales da......." ta fara jero mishi sunayen films kala kala ni wasu ma ban rike su ba, Abbu sauraren ta kawai yake yi yana gyada kai amma fa idanunshi suna kaina, hakan yasa naji gabadaya kamar wadda aka zare mata duk wani kuzarinta. Sai data gama lissafin sannan ya magantu, "wato dama saboda fina-finai kika sa aka sai miki laptop ba don karatu ba koh?" nayi saurin girgiza kaina, "a'ah Abbu! Ina yin karatu fa. Akwai text books a ciki da yawa da videos dinsu kuma Akwai docs da dama duk a ciki, da gaske ina yin karatu" ya kalli Hafsat, wai?? Ta gyada kai da sauri ehh Abbu, watarana ma tana koya min, kuma har Assignment take koya mana ni dasu Yaya Abdullahi. Ya daga gira daya, "Ohh really? A wani mataki kike a Islamiya?" kaina a kasa nace "nayi saukar Al-Qur'ani mai girma, na gama harda watanni biyar da suka wuce, na sauke littafin Umdatul-Ahkam, Riyadussaaliheen, Tafseerul-Jalalaini da Tafseerul-Ibn-Khatheer, da littafai da dama. Na fara Annissa'u war-rijaalu fil jannah amma ban gama ba har yanzu" yace "Mashaa Allah! I am impressed gaskiya" na sadda kaina kasa ina murmushi zuciyata cike da kaunar iyaye na da suka tsaye min na samu karatu mai inganci, tun ina primary six na sauke Al'Qur'ani mai girma, ban fara harda ba sai dana sake yin wata saukar sannan na fara tare da wasu manyan littafai na addini nasan ko a haka na tsaya Alhamdulillahi bani da matsala amma ban tsaya din ba, har yanzu ina cigaba da karatu na duk da cewa har gida Malamin yake zuwa yana koya min. Ganin ban yi magana ba yasa ya cigaba, "da alamu nima zan kawo nawa littafan ki dinga koya min don cikin wadanda kika ambata Akwai wadanda har yau ban gama su ba, zaki koya min?" mamaki ya matukar Kama ni, duk cikin saukin kan mutumin ne haka ko kuwa wani abu daban? Dana rasa abin cewa sai kawai nayi murmushi na maida kallona ga TV ba wai don ina fahimtar abinda ake yi ba anymore, sai don in janye yawan tambayoyin Abbu wanda nasan da kyar ne in samu amsoshin su. Ina ji yana tambayar Hafsat karatun ta tana gaya mishi abinda suka yi a Islamiya ranar, ta karanto mishi Hadisi da Qur'an ya saurara tare da gyara mata Inda ta kuskure.
Karfe tara da rabi suka gama film din da muke kallo, Abbu ya umarce mu da muje mu kwanta saboda makaranta. Sai da safe muka mishi kowa ya wuce dakin shi, anan muka bar shi yana danne-dannen laptop. Ina shiga daki su Mommy na kira don gabadaya ranar bamu yi waya dasu ba, muka gaisa dasu mun jima muna hirarraki kafin na musu sai da safe muka kashe wayar. Bayi na shiga na kimtsa jikina nazo na kwanta.
Washegari abincin mu marar taste da armashi ya dawo, Ashe wanda muka dinga ci daga gidan su Abbu aka kawo shi. Ni dai na tsakuri iya wanda zan iya ci na tashi, suma yaran haka nan dai suka tsattsakura muka tashi muka tafi makaranta. Ranar juma'a kamar satin daya wuce, ina dawowa naci karo da direba yana jira na, sallama nawa Anty da Hareera na tafi Kaduna wajen Mommy da Daddy na.
●●●●●●●●●●
Kimanin wata na daya da zuwa Kano, na riga nayi adopting da garin da yanayin gidan da nake zaune. Abbu bai cika zama a gida ba, it's hardly yayi sati daya cur a gida, yawanci zuwa seminar ko kuma harkokin shi na kasashen turawa, na Ji Malam Bala ne ranar nan yace wai suna shirye-shiryen bude wani kamfanin kirar kayan sawa ne a China shi da abokan shi. Anti Mubeenah ma dai bata cika zama a gidan ba, yawanci ko tana gidan ma bata cika zama a falo ba shi yasa har zuwa lokacin bamu wani shaku da ita ba, tsakani na da ita gaisuwa ne kawai. Abin yana matukar daure min kai, ban taba ganin wani daga cikin dangin Abbu ba a gidan, amma nata da abokanta suna yawan zuwa har yini suna yi, daya daga cikin nasihun da Mommy ta min lokacin da zamu taho Kano shine kada in kuskura in shiga harkar da babu ruwa na, banda shisshigi da sa ido a rayuwar mutane, don haka na kauda kaina daga rayuwar su, koma meye ke faruwa dai rayuwar su ce ba tawa ba.
Wannan satin ina gida ban je Kaduna ba saboda su Daddy sun tafi Malumfashi wajen bikin dan gidan Yayan Daddy din, ina zaune a daki ranar assabar da safe Hafsat ta shigo dakin, a shirye take tsaf cikin riga da siket na atamfa da dankwalin atamfar a saman kanta bata daura ba. Na kalleta da mamaki nace Hafsy ina makaranta ne yau baki je ba? Tace "hutu muke yi ai" na kalli kwalliyar da tayi nace "ina zaki je?" ta langwabar da kai, "Yaya Nafee ke da na gaya miki yau sunan Anti Raliya kanwar Daddy?" na dan dafa kaina, "na manta ne wallahi, har zaku wuce kenan?" ta gyada kai, "mu duka fa zamu tafi, idan kina so ki zo muje" cike da jin dadi na kalleta don dama gabadaya na takura da zaman hakanan da nake yi tun safe, nace "really? Can I??" tace why not? Bari in jira ki shirya. Dama ban dade da fitowa daga wanka ba, a gaggauce na shirya, na saka wata doguwar rigar material sky blue dinkin buba ne ta min tsaf a jikina, ban yi wata kwalliya ta azo a gani ba na shafa turare kawai na dauki gyale na yafa. Na kalli Hafsy nace "mu je?" dankwalin hannunta ta miko min tana turo baki yadda ta saba idan tana jin rigima, "dan Allah ki daura min irin yadda kika yi dinnan ranar nan?" ba musu na amsa na nada mata shi kamar gwaggwaro, ta kuwa yi kyau sosai wayata na dauka muka fara hotuna har sai da muka Ji karan horn sannan muka fita da sauri. Su duka suna cikin motar Abbu picnic yana zaune a seat din direba Anti Mubeenah a gefenshi su Abdullahi kuma a baya, ban san ko yaushe Abbu ya dawo daga tafiyar da yayi ba don tun ranar Laraba baya nan babu mamaki jiya da dare zai dawo. Gabadayan su suka bimu da kallo ni da Hafsy har muka shiga motar, a nutse na gaida Abbu. Thank goodness na daina jin wannan faduwar gaba da rikicewar idan ina kusa dashi, yaja motar a hankali muka bar farfajiyar gidan muka cilla kan titi. Muna baya ina nunawa su Abdullahi hotunan da muka yi ni dai Hafsy su Abbu kuma suna hirarsu shi da Anti Mubeenah kadan kadan Abbu ya kan juyo ya kallemu ko yaja Hafsy da hira har muka isa Gwamna Road inda anan ne ake sunan, ko shiga gidan Abbu bai yi ba yana ajiye mu ya juya tare da cewa bayan Magriba zai zo ya dauke mu.
*♡Jeedderh♡*
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*09*
Muna shiga gidan sunan su Hafsat suka yi nasu wurin ko dakin mai jego basu karasa ba. Ni da Anty Mubeenah muka karasa har uwar dakan mai jegon lokacin babu mutane ma sosai, aka dan yi en gaishe-gaishe Anty ta hakimce a gefen gadon ta janyo wayar hannunta ta fara danne-danne da kiraye-kirayen waya. Gabadaya naji na takura don bansan kowa a wajen ba gashi su Hafsat sun bace a cikin gidan kwata-kwata, wata farar mata ta shigo itama kana ganinta Kasan er uwarsu Abbu ce don ga kama nan kamar an tsaga kara, da dan saurinta ta shigo tana mitar ina su Ni'ima suka shiga ne sun barta da aiki ita kadai? Ta kalli sauran matan dake dakin tace ku taso muje mu gama aikin samosa din can don Allah kafin rana tayi mana, duk suka mimmike yayin da Anty Mubeenah ta kara hakimcewa akan gado, ni kam ganin zan takura na tashi na bi bayan wadanda suka tashi. A can BQ suke yin aikin, na shiga na kama musu muka fara aikin suyar Samosa, Anti Amina kamar yadda naji ana kiranta ta Kalle ni tana murmushi tace "kece wadda take IT a gidan Ibrahim ko?" na gyada kaina, tace ai last week na sha labarin ki wajen Hafsat har sai da kunnuwana suka gaji. Nayi er dariya nace Ai Hafsat Akwai surutu, ta gyada kai. Kafin mu gama aikin mun saba da Anti Amina sosai, su Ni'ima suka dawo dauke da plastic robobi wadanda za a zuba soye-soyen da za ayi a ciki, kusan dukan su sa'annina ne Sa'adiya ce ta girme mu sosai don ta bamu kusan shekara uku zuwa hudu, dukansu suna jami'ar Bayero ita Ni'ima a level two tana mass comm yayin da Sa'adiya take shekararta ta biyan karshe a BS. Kafin kace me mun saba dasu kamar wanda muka yi watanni da sanin juna, muna gama suyar samosa din muka fara shirya abubuwan a cikin robobi muna sawa a cikin Leda, abinci dama odar shi aka yo. Sai gab da la'asar muka koma cikin gidan, Anti Mubeenah bata nan wai ta tafi gidan wata er uwar su dake aure anan cikin unguwar, ina jin kananun maganganu na tashi game da halayen Anti Mubeenah din kun san taron mata ba a raba shi da kananun maganganu balle harka ta hado ku da dangin miji dama sai a hankali, ni dai nayi kunnen uwar shege dasu naki maida hankalina kansu don ba harkar shiga ta bace. Wanka muka sake yi Ni'ima ta bani wasu riga da siket na Swiss lace na saka saboda nawa na lalata su da abun fulawa sun yi fari tas. Bikin suna yaci gaba da gudana lafiya qalau, ina daga cikin masu kai da kawo na entertaining din baki, kawo abinci, dauke kaya, daukar gifts din maijego da wasu abubuwan. Duk Inda na motsa da sannun Anti Ameenah nake motsawa, naga alamu na shiga ran matar sosai. Anti Ameenah itace babbar Yayar su Abbu kuma babbar diya a wajen Alhaji Mad'udu Galadanchi, su shida ne wajen iyayensu kamar yadda Sa'adiya take bani labari, Anti Ameenah ce babba sai Abbu, sai Anti Rahina, Aminu Yayan Sa'adiya yana Bangladesh yana karatu sai Sa'adiya da Ni'ima auta. Family din sun burge ni sosai a gaskiya, na kula da hadin kansu kwarai da gaske abin ya burge ni ba kadan ba, ina son ganin yan uwa wadanda suke kula da zumuncin su sosai.
Bamu muka samu kanmu ba sai bayan isha'i, mutane duk an tattafi sai baki na nesa da dangin maijegon na kusa, muna wani daki dake kusa dana maijegon inda anan muke bidirin mu, hira muke dasu Ni'ima lokacin da Hafsat ta leko dakin tace in fito Abbu yazo zamu tafi, na dan hade fuska jin an katse min hira mai dadi da muke yi amma haka nan na tashi saboda bani da yadda zanyi na fito su Ni'ima suka biyo bayana, dakin Anti Rahina na shiga da niyar mata sallama. Abbu na zaune a cikin falonta kusa da Anti Ameenah yayinda maijegon take zaune a kujera daya rungume da babynta da alamun hirar en u want aka ce ake yi na durkusa na gaida Abbu tare da yiwa su Anti Ameenah sallama, Abbu ya mike nabi bayanshi. Su duka har maijegon suka fito mana rakiya, su Qaseem na jikin motar Abbu din suna jiran mu, duka muka shiga cikin motar. Su Ni'ima suka leko suna kara min sallama dama mun yi exchange din number waya dasu, Anti Ameenah ta miko min wata Leda mai dan girma tana kara min godiya tare da jaddada min in fa nemi maganin ciwon jiki in sha ina amsa mata da toh, Mai jegon MA ta leko tana min Allah huta gajiya da godiya sosai. Abbu kam baki a sake yake kallon en uwan nashi cike da mamaki, wannan shine karo na farko da suka fito wai da sunan mishi rakiya, sai daga baya ya kula ashe ma ba shi aka yiwa rakiyar ba, kulawar daya kamata ace matar shi ce suke wa sun kare da ba wata can, abinda yakamata ace matar shi ce tayi suke mata wannan yabawar wata can ce ta samu romon. Koda yake bai ga laifin su ba, Mubeenah ita tayi wasa da garinta har yayi ruwa, shi kanshi yaji haushin abinda tayi yau a wajen sunan nan, ance tunda taje ta gaida mai jegon bata kara yiwa kowa magana ba ko Anti Ameenah bata gaida ba, daga baya ma suka ce wai ta ajiye musu dubu goma ta tafi tun kafin ayi Azuhur abinda ya bata ran Anti Ameenah kenan, ya girgiza kai cike da takaicinta, duk iya kokarin shi na ganin Mubeenah ta ra6u da dangin shi don su saba abin yaci tura. Shi har bai san me zai mata ba kuma.
Sai da muka gama sallamar mu sannan suka koma gefe suka tsaya suna kallonmu tare da daga mana hannu har Abbu yaja mota muka tafi. Tunda muka fara tafiya babu wanda yayi magana, su Hafsy tuni tayi barci akan cinya ta. Muna isa gida na ciccibe ta muka wuce Abdullahi ya dauko min ledar da Anti Ameenah ta bani, dakin Hafsy na fara wucewa na kwantar da ita. Closet dinta na bude na ciro mata kayan barci na dawo na cire mata na jikinta na saka mata wadannan, addu'ar kwanciya barci na tofa mata tare da sauka daga kan gadon a hankali gudun kar in tashe ta daga barci, ina juyawa naci karo da Abbu a bakin kofa a jingine yana kallon mu. Na sadda kaina kasa na je zan wuce ta gefenshi, packet din magani ya miko min, nasa hannu na amsa ina kallon shi cikin alamun tambaya, yace maganin ciwon jiki ne Anti Ameenah tace in baki, ki sha kafin ki kwanta. Na gyada mishi kaina, "sai da safe koh?" ya fada yana kaucewa daga bakin kofar dakin, na bi ta gefenshi na wuce ya bini da kallo. Ina shiga dakina kayan barci kawai na saka na afa maganin a baki, sai dana bata mintuna kusan goma yadda maganin zai yi settling a jikina sannan na kwanta, babu dadewa barci ya kwashe ni, ni kaina nasan cewa a matukar gajiye nake saboda ba karamin aiki muka sha a gidan sunan nan ba.
Sai karfe goma na safe na tashi, nayi mika mai tsawo ina jin ga6o6ina kamar an bubbuge min su, kai tsaye toilet na fada nayi wanka da ruwa mai dumi, nayi brush kafin na fito. Wandon jeans na saka wanda bai kama jikina ba da shirt, na daure kitson kaina a cikin tafkeken hair band na dora hula a kaina. Falo na fito saboda wata mahaukaciyar yunwa da take nanikata, babu kowa a cikin falon haka babu hayaniyar yara nasan suna makaranta. Anti Mubeenah na hakimce a kan kujera a falon da takardu a gabanta tana buga lissafi, na durkusa a gefenta ina gaidata. Hankalinta yana kan takardun ta amsa min, baki na dan tabe na mike, har ga Allah halayen matar basa burge ni, wata na daya a cikin gidanta amma wani idan ya ga yadda take yazga ni sai yayi zaton bakuwar jiya ce a wajenta. Kan dinning table na wuce kaina tsaye sai dai kwalam! Babu komi, cike da mamaki na tsaya ina kallon wajen a raina ina tambayar ko lafiya? A iya sani na ni dai a gidan nan ko an gama cin abinci ba a dauke kayan sai idan za a sake shirya wani meal din. Daga bayana naji Antin tana cewa "Yau bamu yi girki ba, Harira bata nan taje garinsu wajen biki. Yara ma sai oats na dama musu, kije kicin kema ki dama anjima kadan zan bada a yo take away" na jinjina kaina cike da mamaki, oats? Yaushe rabona da in sha Abinnan? Kicin din na wuce, kulolin da aka yi amfani dasu ba a wanke ba suna cikin sink har sun fara wari, nayi iya dube dube na a kicin din ban samu abu mai sauki da zan saka a bakina ba don bazan iya dama oats Inci ba, kawai ledar da Anti Ameenah ta bani jiya ta fado min a rai da sauri na koma daki na janyo ledar na bude, tarkacen su doughnuts, cake, cincin dasu biscuits ne a ciki har da naman suna, falo na koma na bude fridge na dauko lemun exotic na dawo nayi daidai a tsakiyar daki na fara ci, sai da naji nayi nak sannan na tattare sauran na ajiye a gefen gado. Waya na dauko na bude, missed calls na gani bila adadin nasu Ni'ima dana Daddy sai wata bakuwar number da ban sani ba, su Ni'ima na fara kira suka min ban gajiya sannan na kira bakuwar number nan ashe Anti Ameenah ce, itama dai ban gajiyar ta min har sai data saka ni jin kunya yadda take ta yaba min tana sa min albarka, muna yin sallama da ita na kira Daddy, nan muka kwashe lokaci mai tsaye ina bashi labarin abubuwan da suka faru cikin week din, bayan mun yi sallama kan gado na koma na kwanta ina sake-sake, ban san iya lokacin dana dauka ina tunanika ba sai dai na bude ido naga karfe sha biyu tayi, a raina nace su Hafsat karfe biyu suke dawowa daga makaranta, and I can't stop imagining ya suke manejin oats a cikinsu fiye da awowi biyar. Cimak na tashi na fita falo, Anti ta gama lissafin nata tana zaune ne kawai tana kallon tashar CBN, na zauna a gefenta nace "Anti me za a girka ne na rana naga su Hafsat sun kusa dawowa?" dagowa tayi tana kallona cikin wani kallo dana kasa gane ma'anar shi, ta yamutse baki kafin tace "ke har kin iya girki ne dama?" nace sosai ma, ina taya mommy idan tana yi. A raina kuwa cewa nake "a yadda nake jina akan girki Allah na tuba ai gani nake zan iya karawa ko da wani irin chef ne!" saboda ba yabon kai ba, dishes dai tun daga kan na hausa, na Yoruba da abinda ya danganci na mai jajayen kunne na kware a yin su don mommy na gwana ce in dai akan girki ne. Sai daga kare min kallo kafin tace ki dafa shinkafa da miya to, zaki iya kuwa? Na danyi murmushi kawai, da alamu gani take girki wani katoton aiki ne bata san a wajena kamar shakar ruwa ne, nace "zan iya Anti" tace to shikenan, je ki fara" babu musu na tashi na fada kicin din ina tattare hannun riga ta.
*♡Jeedderh♡*
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*10*
*You're the right time at the right moment...., You're the sunlight, keeps my heart going.... Know when I'm with you, can't keep my self from falling...... Right time at the right moment It's You...., You....., It's You....!*
A song by; Henry, It's_You dedicated to My Fans.
Tsaye nayi a tsakiyar kitchen din ina tunanin ta Inda zan fara, sai dana danyi sighing kafin na tunkari freezer na bude, kayan vegetables da nama ne da dangin kifi a shirye kala-kala a ciki saboda tsabar ajiya duk da cewa a cikin freezer suke amma sun fara sauya kama musamman vegetables din. Kashe freezer din nayi yadda zan samu in ciro kaya ta sauqi, na shiga store nan ma kayan abinci ne dankare kamar a super market babu nau'in da babu daga na gida har na waje. Maimakon shinkafa da miya sai nayi fried rice wadda na wadata ta da dangin veggies, na yanka hanta kanana a ciki. Na dauko fresh sardines na wanke na yanyanka shi na soya wanda zan yi decorating din shinkafar dashi. Ina tsaye ina slicing din albasa wadda zanyi onion sauce da ita, ban ji shigowar mutum kicin din ba sai magana naji a baya na, "what are you doing here?" na juya a firgice na kalli wajen da sautin maganar ya fito. Abbu ne tsaye a kofar kicin din ya rungume hannuwa a kirjin shi yana kallona, naji na diririce da kyar na iya cewa "ammmm.... Girki?!" na fada kamar ina tambayar shi, ya shaki numfashi yana lumshe idanu, yace "woah! What a delicious smell!! meye kike dafawa haka ya cika mana hanci da kamshi?" dan murmushi na saki kadan, "fried rice ne" yace I hope kin kusa saukewa? I can't wait to taste it. Na gyada kai nan ma, nan da en mintuna zan sauke. Ya juya zai bar kicin din, "OK! I'll go and take a shower then sai in dawo" ya karasa fita daga kicin din yana uttering "thank Goodness!" a kasan zuciyar shi, dama dawowa yayi yayi wanka ya fita ya samo musu abincin da zasu ci sai kuma yana shigowa yaji wani mahaukaciyar kamshin abinci yana fitowa daga kicin wanda ya taso mishi da yunwar shi ta kwana da kwanaki da yake dannewa da lemuka, yana shiga kicin din yaci karo da "beautiful sight' a cewar shi, tana yanka albasa a cutting board cikin kwarewa kamar irin chief cook dinnan a 5 stars hotel, da kyar ya iya suppressing din urge din daya taso mishi na aikata wani abu da yasan will never ever be appropriate, wanda yasan mawuyaci ne idan bai zubar mishi da kimar shi ba a idon yarinyar na har Abadan. Sai kawai ya buge da jingina da bango.
Ina gama yin sauce din na juye shi cikin wani kwanon tangaran, itama fried rice din sauke ta nayi don ta gama, ta min yadda nake so kuwa, wara-wara, yellow shar sai tashin kamshi take yi, na fito da babban food flask na zuba ta a ciki. Oranges na dauko manya da apple da water melon, na bare lemun na saka a juicer ta markada min shi na tace ruwan, na yanka kankanar itama na cire yayan tas, na yanka ta kanana a cikin lemun tare da tuffa, na kawo syrup sugar na zuba a ciki na watsa kankara na fara ciccibar kayan zuwa dinning table. Ina gama shiryawa su Hafsy suka fado falon a guje da alamun gajiya a tare dasu, lokacin dana tare su sai na dinga jina kamar wata Mummy dinnan mai jiran 'ya'yanta su dawo daga makaranta, nayi kokari na kauda weird tunanin daya lullube min zuciya na karbi jakar hannun Hafsy na kai mata daki, ai ko kayan makaranta basu cire ba kowa yayi settling akan kujera na fara serving dinsu kafin na zauna a gefen Hafsy nima na fara ci. Zo kaji santi kuwa, Qaseem har da cewa wai shekarata nawa a makarantar koyon girki? Dariya kawai nake musu acan kasan zuciyana kuwa jin kaina nake a sama, me yafi yabo dadi a duniya?? Abbu ya fito daga dakinshi sanye da wandon jeans da shirt na shan iska, Shima kan dinning din yazo ya zauna. Na mike na fara serving din shi abincin yayin da yake gaisawa da iyalan shi, na zuba mishi komi na ajiye a gaban shi na koma mazaunina na zauna muka ci gaba da cin abincin mu. Wajen cin abincin ya koma shiru, Abbu bai yi magana ba sai kai kawai da yake girgizawa, rashin magana ma yabawa ce. Sai da kowa ya cinye abincin plate din shi duka, suna gamawa kowa ya wuce dakinshi saboda ranar ba zasu koma makaranta ba. Na fara tattare plates din da muka yi amfani dasu na kai kicin, Abbu yana zaune a har a lokacin yana cin dura abinci a cikinshi cikin alamun rashin saurarawa, na fahimci matsananciyar yunwa a tattare dashi. Na kai hannu da niyar dauke jug din juice din da nayi, cikin rashin sa'a shima ya kai nashi hannun don haka nayi saurin janye nawa hannun amma duk da haka sai da hannunshi ya dan gogi hannuna, Ya Allah!! Wani irin current naji ya taba ni kamar na taba budaddiyar wayar wuta. Naja baya da sauri ina shivering, shi kam hannunshi ya kurawa idanu yana kallo kamar wani bakon abu kafin ya dago idanunshi yana kallona mai cike da ma'anoni wadanda na kasa pathorming abinda suke nufi. A hankali ya maida kanshi ga plate dinshi ya cigaba da cin abincin amma fa cikin rashin kuzari, ganin haka yasa sumi-sumi na wuce dakina kafafuna na shaking. Ina bada baya ya maida kanshi ya jinginar da kujera yana ajiyar numfashi da sauri-sauri, what the hell did he just felt??! Yake tambayar kanshi embarrassingly.
Ina shiga dakina na zube a bakin kofa rawar da jikina yake yi ta karu, Innalillahi!! Kadai naji bakina yana furtawa da karfi, da kyar na iya daidaita natsuwa ta. Wannan wani irin abu ne haka? It's not as if ban taba gogar hannun namiji bane, God Forgive me amma ni har hugging dinsu nayi amma ban taba jin rabi rabin abinda naji ba yau da Abbu ya taba ni, ban taba jin hakan a tattare da ko wane namiji ba sai shi, ko me yasa hakan?? Ban zurfafa tunani na ba na mike na fara gyara daki na ba wai don yayi wani abu ba sai don bani da aikin yi kawai. Har bayan la'asar ina gyara, dana gama wayata na dauka na shiga dakin Hafsy, tana zaune a kasan carpet tana kokarin warware kitson kanta, na zauna a gefen gado ina kallonta, "ya ne pretty?" as usual sai data yi pouting kafin ta kalleni da dara-daran idanunta, "na manta ban fadawa daddy a kaini saloon ba har ya fita, kuma idan Anty Kate taga kaina a haka gobe sai ta dake ni!" na shafo kitson kaina nima ina kallonta, yakamata ma in tsefe shi don ya fara tsufa. Nace "to taho in taya ki" ta waro hakora, "yauwa, kin iya kitso ai koh?" na girgiza mata kai, ta 6ata fuska, nace "noo, kar ki damu, zamu san dabarar da zaa yiwa kan yadda Anti Kate ba zata taba min ke ba koh?" ta gyada kai tare da zuwa ta zauna a kusa dani. Haka kuwa aka yi, muna gama tsifar ta dauko kayan kitso dasu ribbons na fara gyara mata kai, kalba na mata manya wadanda na kayata da ribbons din da dutsunan kitso kuma ga mamaki na yayi kyau sosai, ita kanta data kalli kanta a madubi tsalle-tsalle ta hau yi. Ni kam dariya na mata na tashi na fada kicin don yamma tayi sosai, sakwara nayi da miyar ganye, na wadata miyar da nama da busasshen kifi, na hada fruit salad na kai komi kan dinning na ajiye. Da wuri na tattaro kan yaran muka ci abincin mu kowa ya koma daki ya kwanta duk a dabara ta na kaucewa haduwa da Abbu, sai Allah ya taimake ni har na koma daki bai dawo gidan ba. Sai da na gama shirin kwanciya barci sannan na jiyo tashin muryar su shi da Anti a falo da alamun tare suka dawo gidan.
Washegari tun da safe na fada kicin, potato chips nayi da egg sauce sai ruwan shayi wanda yasha kayan kamshi, na soyawa su Qaseem doya da kwai wanda zasu tafi makaranta dashi na zuba musu a lunch boxes dinsu, yin komi nake yi cike da kuzari da walwalata. Aikin daya jima yana burge ni kenan, kullum naje gidan Aunty Uwani ina ganin tana hadawa yaranta abincin tafiya makaranta irin haka, abin yana burge ni ba kadan ba, at last yau gashi dai nima na hadawa nawa. A gurguje na shirya na fito saboda lokaci daya fara wucewa, yanzu ma mu hudu kadai muka karya don daga Abbu din har ita Aunty din babu wanda ya fito, muka gama karin mu muka wuce makaranta.
Gabadaya kwanakin girkin gida da kula da gidan ya koma hannuna yayin da ita uwar gida mai gayya mai aiki kullum sai dai tayi rashe-rashe sai dai a dafa ta zauna taci ta tashi ta kara gaba abun ta babu godi bare na gode, dama dama ma Abbu. Yana nuna jin dadin shi kwarai game da hakan, ina kuma shan godiya a wajen shi sosai wanda ina ga hakan ne yasa nake dagewa tun karfi na ina musu dadadan girki wadanda zasu sa zuciyar shi a farin ciki yayi ta mun addu'ar daya saba, halin Aunty kam tun ina damuwa dashi har na daina. Matar is really complicated, gane halinta da Inda ta saka gaba abu ne mai wahala kam, to mai wahala mana. Ban ka kula da cin abincin miji, baka san shan miji ba, Baka san gyara muhallin mijinka ba, ba ido na saka musu ba, amma nasan bata kwanan dakin miji, ko ina suke ko a gaban wa suke she is always making it obvious that bata damu da mijinta, rayuwar Aunty Mubeenah fa tana bukatar gyara sosai da sosai. Allah Allah nake juma'a tazo in wuce Kaduna, va wai don na gaji da hidimar da nake yi dasu ba in fact, kwanaki biyar zuwa shidan da nayi ina yiwa Abbu da iyalan shi girki has been the best and happiest moment na rayuwata, sun kara min kusanci da iyalan, sun kara min so da qaunar su kamar yadda suka kara musu sona da qaunata. Kawai dai nayi kewan su Mommy da Daddy ne don haka ranar juma'a da wuri na dawo na hada kayan da nasan zan bukata, Abbu baya gari yayi tafiya ranar Thursday. Direba yana zuwa na fito tare da kulle gidan don babu kowa, Hajiya Aunty Mubeenah an tafi neman kudi bayan babu abinda ta nema ta rasa a gidan auren ta.
*♡Jeedderh♡*
[01:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*11*
*"Paradise is a home of Honor, Dignity, Rest, Satisfaction, Beauty, Joy and Peace., May Allah make it to be your permanent Home Ameeeen, Jumma'at Kareem!!"*
Abinda na karanta kenan daga wayana bayan na shiga dakina, Kimanin awowi biyu da dawowa na kenan. Na duba kasan message din inda nake zaton zan ga sunan wanda ya turo text din saboda babu suna a jiki sai number kawai. *'_Galadanchi!'* shine sunan dana gani. Crap! Abbu ne!! Zuciyata ta hau fadi ina jin tana wani tsalle-tsalle, wayar na zurawa idanu ina lalubo abinda zan tunana amma komi ya tafi blank, na lalubo su da kyar na shiga jefawa kaina su kamar ni ce Abbu din, "Friday message kuma? Why would he?" zuciya ta tace stupid! Kuma ba zai miki message ba kike nufi ko me? You know this is a normal thing tsakanin mutane yanzu, ke da Daddy da sauran uncles dinki ba kuna exchanging irin wannan messages din a tsakanin ku ba?? Na gyada kai a hankali kamar wawiya, sai a lokacin kuma na gano shirmen da nayi, God! I can be silly sometimes, saboda Allah addu'a ya min mai dadi amma ban amsa mishi ba na hau tuhumar dalilin da yasa ya turo min sakon. Da kwarin gwiwa ta na tura mishi amsa, *'Ameen Abbu, and same to you. How's your presentation? Allah ya dawo daku lafiya Ameen!'*. Shiru har aka dauki lokaci babu reply, na daga kafada ta, watakila I've gone too far ne, meye nawa na wani tambayar yadda harkokin shi suke tafiya kamar wata shakikiyar shi? Na tabe baki na tashi daga kan kujerar dana zauna don wai da zama nayi ina jiran amsar shi kamar wata sakara. Kayan jikina na shiga cirewa ina jifa dasu cikin laundry bin, na daura towel a jikina nazo fada bathroom.
☆☆☆☆☆☆☆☆
Idanunshi kur akan wayar yana kallo cikin wani irin yanayi, kalmomi ne da rabon daya jisu daga bakin matar auren shi har ya manta su, anya ma ya taba jin su kuwa? Ta yaya ma aka yi tasan cewa presentation yaje? He can't recall telling her, wani sashe na zuciyar shi yace ba mamaki wajen su Pretty taji don ya kula tana son yarinyar sosai, yana mamakin yadda idan suna hira da Hafsy take maida kanta kamar yarinyar har ka kasa tantance yaro da babba a cikinsu. Ya lumshe idanu a hankali...... Bai san cewa ya zurfafa a tunani ba sai daya ji muryar Chairman dinsu ta microphone, "Dr. Galadanchi?? Anything from you??" yayi firgigit ya dawo daga duniyar imagination daya tafi, "yeah of course Mr. Collins..." ya jefa wayar shi a aljihu ya dauki wasu takardu ya tafi kan step fara bayani a nutse....
●●●●●●●●●●
Wannan weekend din ziyara nayi, naje gidan Anti Uwani na musu yini a can, daga nan ni da AbdulJalal muka shiga gari sai bayan isha'i ya sauke ni a gida bayan mun tsaya a Mcbae mun sayi tarkacen chocolates da ice cream. Washegari lahdi sai wajen karfe biyar na bar gida cike da kewar Mom da Dad, amma fa can kasan zuciyana wani farin ciki da doki ne dankare a cikinta, dokin in koma inci gaba da yiwa Abbu dadadan girki na yana ci yana yaba min har da santi. Sai dai koda na isa sai na tarar Hareera ta dawo daga biki, Abbu kuma baya gari, gwiwa na yayi sanyi sosai, jiki a sanyaye na shige daki na.
Washegari a tsaitsaye muka ci abinci muka wuce makaranta, ranar mun sha ayyuka a lab kamar me! A matukar gajiye muka zauna akan dakalin da muka saba zama ni da Ramlah cikin dan garden din da muke hutawa, na kalle ta ina dan murmushi, "ke jiya fa muka hadu da Muneer" bata nuna alamun abun ya dadata da kasa ba kamar yadda nayi zato, tayi fuskar shanu tace a ina? Nace "McBae, mun shiga siyayya ni da AbdulJalal. God! Baki ga yanda gayen nan ya kara kyau ba, yayi fari yayi kiba sosai, I think he misses me so much, kin kuwa ga irin fara'ar daya dinga min? Rabona da in....." tayi saurin katse ni, "ai fa kin kika fara bada labarin Muneer kamar wata radio mai jini ba kya ko son kiyi shiru, to sai ki tashi an zo daukar ki" na kalli inda suka saba tsayawa idan suka zo, gabana ya fadi sosai, Abbu ne yazo daukar mu! Ganin Qaseem ya fito yana tunkarar wajen da nake yasa na mike ina lalubar jakata nawa Ramlah sallama. A hankali kuma a sanyaye na bude bayan motar na shiga, "Abbu ina yini?" na furta cikin siririyar murya ta, ya amsa "lafiya qalau Nafeesah, ya kika baro Kaduna?" na amsa da lafiya lau. Yaja motar muka tafi babu mai furta uffan. Hafsat ce ta ciro drawing book dinta daga cikin school bag dinta tana nuna min Assignment din dana taya ta jiya akan zanen gidaje da motoci, tace "Kuma Uncle Jamilu yace ni na cinye 20 over 20 duk cikin class din" na shafa kanta ina murmushi, "Ohh that's very good princess, am proud of you" tayi dariya tana kwantowa a jikina na rungume ta. Muna isa gida sallah muka yi, na bude fridge na ciro fura da nono dana kawo daga gida, musamman Mommy ta bada aka yi, na zauna na dama ta da dan kaurinta na saka kankara da dan sugar, cups na dauko na zuzzubawa su Abdullahi. Muna zaune a falo muna sha kafin lokacin zuwa Islamiyar su yayi. Abbu ya fito daga daki hannunshi dauke da jakar laptop dinshi, dan karamin coffee table din dake gefen mu ya janyo ya dora laptop din nashi akai, kasa kasa yake kallon mu har ya zauna. Ya kalli kofin dake hannuna yace meye wannan kuke sha haka babu tayi? A kunyace nace fura ce! Idanunshi suka dan ware cikin mamaki, "wow, daga ina muka samu fura?" Hafsat tayi caraf tace "daga gidansu tazo da ita jiya!" ya jima sosai idanunshi suna kaina ban san ko tunanin me yake yi ba, ya kauda kanshi ya maida shi ga laptop dinshi, "tunda ba a mana tayi ba ni zan yiwa kaina, a bani idan da akwai" da sauri na tashi naje na dama mishi na kawo na ajiye mai a gefenshi. Su Hafsy suna wucewa makaranta na koma dakina na zauna ina kallo.
Tara da rabi ta nuna lokacin dana kalli agogo, nayi mika ina hamma ina jin kasusuwan jikina na amsawa saboda gajiya, ban kai ga kwanciyar da nayi niyar yi ba na jiyo kamar muryar Abbu a falo yana kwala min kira. Na saurara sosai har zuwa lokacin dana sake jin wani kiran kafin na warci hijabi na zura na fita, yana kan dinning a zaune yana kokarin rufe daya daga cikin food flasks din da aka ajiye akai, ya kalleni fuskar shi dauke da wani irin expression dana rasa ko wani iri ne; na jin haushi ne, embarrassment ne ko fusata? Shi dai ya bar wa kanshi sani. Na dan duka a gefenshi nace Abbu gani a sanyaye. Sai da yayi gyaran murya sannan yace "Please samo min noodles ko simple abu da zan ci, am quite hungry" na danyi jim kamar ba zan tashi ba suna da er aiki, yana da matar shi, ba za a ga laifi na ba idan na tashi na fada kicin na dafa mishi abinci? Koda yake ban ga laifin shi ba, abincin da Hareera tayi yau yadda kasan faten shinkafa saboda yadda shinkafar ta cafke, ita kanta Anty Mubeenah sai data mata fada yau dai har da ce mata idan ba zata gyara ba to lallai tana gab da barin gidan don ita ta gaji haka nan.... Abbu ya dan sake gyara murya ya kalle ni, "well??" nayi saurin dawowa cikin hankali na, "umh.... Dama zan ce ne noodles din kadai ta isa?" ya gyada kai, da sauri na tashi na wuce kicin cikin hardewar kafafu, zuciyana na gaya min cewa idanunshi shi a kaina suke. Tukunya na dora akan gas na hada duk abubuwan da nake bukata, ruwan yana tafasa na zuba indomie a ciki na kara da sardines, na dora ruwa a cikin kettle na zuba danyar citta da kanumfari er garlic don naga alamun kamar mura tana dan damun shi. Ina sauke indomie din na soya kwai na dora a sama, na juye shayin a cikin flask na dora duka kayan akan tray mai fadi na fita. Yanzu ya dawo tsakiyar falon ya zauna hannunshi rike da waya yana karatun labarai, na ajiye su a gefenshi na tura indomie din gaban shi da fork a ciki, na dauki kofi na tsiyaya shayin na mika mishi, shayin ya fara kaiwa bakin shi, ya dan yamutse fuska yana kallon shayin jin kamshin tafarnuwa na tashi, da sauri nace "umh... Naga kamar kana mura ne shine....." na kasa karasawa saboda kalmomin sun kare min kuma sai ya girgiza kai kawai ya fara kurbar shayin a hankali. Naje na dauko mishi ruwa da lemu irin wanda naga yana sha masu rangwamen sanyi a cikin fridge na kai na ajiye a gefenshi, "Abbu kana bukatar wani abu kuma?" ya girgiza kanshi, "babu Nafeesah, nagode. Sai da safe koh?" na tashi da sauri na bace a wajen. Duk zaman da nayi jina na dinga yi kamar akan kaya, zuciyana wani irin duka take kamar zata tsaga kirjina ta fito, ban san me yasa Abbu yake da wani irin effect a kaina na saka ni cikin rashin natsuwa ba.
Washegari ba laifi anyi abinci mai sense don mun zauna mun ci sosai, Abbu ya kalle ni yana ajiye spoon din hannunshi, "Nafeesah ko zaki iya dora min shayi irin na jiya?" a hankali na saci kallon Inda Anty take zaune, abincin ta take ci Hankalinta kwance kamar bata san Allah yayi ruwan tsirar mu a wajen ba. Na dan jijjiga kai na tashi, cikin mintunan da basu gaza bakwai ba na gama na juye a cikin flask, na hada da cup na fito falon. A gaban shi na ajiye su, ya kalle ni yana furta thanks! Kafin ya kalli su Hafsy, "oya a tashi a tafi koh? Malam Bala yazo" duk suka mike kowa yana daukar school bag din shi, muka musu sallama muka tafi.
Muna zaune da Ramlah a lab muna hira na kalleta, "babe ya za ayi ne? Ina bukatar wankin kai da kitso fa kaina yayi datti wallahi" tace ba damuwa, idan mun tashi sai mu biya ta saloon din Anty Haleemah, nima ranar Saturday naje aka wanke min" nace "to shikenan". Muna tashi kuwa Allah yasa su Malam Bala sun zo kenan, nace su wuce gida kawai ni Akwai inda zani. Muka je saloon aka wanke min kaina aka min kitso, da yake ba laifi Masha Allah ina da gashi sosai, Mommy irin bakaken fulanin nan ne, na gado zubi da kira irin tasu da kuma yalwar gashi, kalar fatar jikina kuma ta daddy ce, haka dangin shi suke wankan tarwada duk da cewa Akwai farare, kyawawan dara-daran idanu farare tas da bakaken eyelids, dogon dan siririn hanci kamar an zana da biro, dan karamin zagayayyen baki da jerarrun hakora kanana kuma farare tas da er siririyar wushirya a tsakiyar su. Muna gamawa da saloon gidan Anty Haleemah muka wuce, gidan flat ne dan madaidaici mai kyau dakalin ganshi kaga gidan mutum daya. Mijinta navy ne don haka bai cika zama a gidan ba, tare suke zaune da kanwar mijinta Khaleesat, mun dan saba da ita saboda a cikin BUK take karatu, tana yawan zuwa wajen Anti Haleemah din. Danta daya Mahmoud, nan muka wuni a gidan sai bayan Magriba ta hada ni da direba ya maida ni gida, kafin mu isa tuni an kira sallar isha'i. A bakin gate ya ajiye ni, na gaida maigadin gidan na wuce ciki. A hankali na tura kofar falon na shiga baki na dauke sallama, babu kowa a cikin falon. Na maida kofar na rufe na fara tafiya zuwa dakina, kamar daga sama naji maganar, "Where the heck have you been???". A gigice na juya, Abbu ne zaune akan kujera yana kallona kamar a fusace? Cikina ya bada sautin kululu.... It seems like m in trouble.
*♡Jeedderh♡*
[09:11, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*12*
Ya Allah! Cheerful Abbu din dana sani ya tafi, wannan Abbu din ban taba ganin shi ba, a fusace yake sosai kamar wanda zai tashi daga zaunen da yake ya hau ni da bugu, gabadaya jikina ya dauki rawa hawaye suka ciko idanuna, bana son fada ko kadan a rayuwata. Cikin rawar murya irin ta wanda yake so ya fashe da kuka nace, "Naje saloon ne shine na biya gidan su kawata Ramlah" ya galla min harara, "da ixinin wa??" nace "umh, ai na fadawa su Malam Bala da suka zo dauka na dazu", yayi shiru kawai yana kallona. Malam Bala ya fada mishi tun dazun, that means he have no right to be angry at her, but still, he's just pissed up. Dan siririn tsaki yaja ganin har na fara shesshekar kuka, ya shafa tattausar sumar kanshi da a koda yaushe a gyare take tana sheki, "it's okay.... Bani ruwa a fridge" da sauri naje na dauko na kawo mishi, yasa hannu ya amsa fuskar shi har lokacin a murtuke, ganin nayi tsaye naki in tafi yasa ya juyo yana kallona, "what?" he sounds so pissed up at me, da sauri na hau share kwallar data fara xubo min again nace "Abbu don Allah kayi hakuri, wallahi ba zan kara ba don Allah" ya lumshe idanunshi a hankali, "it's okay Nafeesah, banji dadin abinda kika yi ba, a gidanku kina kai har Magriba a waje?" nayi saurin girgiza kai, "to me yasa a gida na? Saboda kin raina ni ne ko kuma don kin baro gidanku kina tunanin zaki yi duk abinda kike so anan ba tare da an miki fada ba?" nan ma kai na girgiza a hankali nace "tun dazu muka taho, gidan Akwai dan nisa ne daga yau" yace "bana tolerating abubuwan nan Nafeesah kin gane? Daga yau kada ki sake wuce bayan Magriba a waje...... No! Duk inda zaki fita you must tell me first indai kina cikin garin Kano, understand?" nayi saurin jijjiga kaina, yace "you can go now!" kamar wadda take akan kaya, da sauri na wuce dakina. Sallah na fara yi kafin na kira mommy muka gaisa, labarin abinda ya faru na shiga bata, budar bakinta cewa tayi "ai yayi min daidai wallahi, wato har kin fara yawo barkatai ko?" sai lokacin naga wautata dana fada mata, na batan fuska kamar ina gabanta tare da turo baki, "mommy! Saloon fa naje saboda Allah daga can na wuce gidan su Ramlah, Ramlah ce fa kawata ke kanki kin shaida sau nawa take zuwa gidan mu ta kwana?" tace "but still baby, bai kamata ki tafi ba tare da kin fada mishi ba, kin san dole ranshi ya baci dama" na shiga diddira kafata a kasa ina gunaguni, "ni dana sani dama ban fada miki ba tunda ba zaki goyi bayana ba" ta sassauta muryar ta, "Ohh Nafeesah baki fahimta koh? Ba goyon bayan shi nayi ba, it's just the fact. Ke yanzu amanar muce a hannunsu, kina ganin ya dace ya barki ki dinga fita kina dawowa duk lokacin da kika ga dama a garin da yake bakon ki iye? Ko kina ganin girmamawa ce ki kama hanya ki fita ba tare da kin sanar dashi ba? Wani Malam Bala is not an excuse tunda ba a karkashin kulawar shi kike ba kin gane?" na gyada kaina a hankali she's right. Muryar daddy na jiyo ta cikin wayar, "Habibty ke da waye kuke waya kika kyale ni ni kadai a falo?" da sauri na shiga mata magiya akan Kar ta fada mishi hirar da muke don nasan kadan daga cikin aikin Mommy ne, ta ba daddy din muka gaisa. Hira muka shiga yi yawanci ta wajen aikin shi ce, mun jima sosai kafin muka yi sallama dasu. Kayan barci na na zura na bi lafiyar gado ko abinci ban nema ba.
Ina kan sallaya ina lazumi bayan nayi sallar asubahi, ban cika komawa barci ba a irin wadannan lokutan, kofar dakin naji ana kwankwasawa, na tashi naje na bude, Harira ce. Muka gaisa da ita a mutunce tace "dan Allah Nafeesah ko zaki taimake ni da girkin yau? Bana jin dadi ne" nayi fuskar tausayi nace "Eyyah sorry pa! Meye za a dafa?" tace "ki dafa duk abinda kika ga ya dace nace "to shikenan" tace nagode ta wuce dakinta. Daki na koma na dauko karamar hijabi data tsaya a kuguna na saka na fita zuwa kicin, yam delight nayi, kafin dahu sai na dauko fresh kifi a cikin fridge na fara shirin yin farfesun kifi.
(Kuyi hakuri da wannan zuwa gobe please, da kyar ma na samu na warci lokaci nayi typing dinshi wollah)
*♡Jeedderh♡*
[09:11, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*14*
Da gudu na karasa wajen shi na riko hannunshi dake rike da brief case, tambayoyi nake watsa mishi ba kakkautawa, "Abbu lafiya? Abbu mai ya samu kafar ka? Abbu accident kayi a kan hanya?!....." ya zauna akan kujera yana maida numfashi, "it's just a minor targade, an gyara min. Kar ki damu" jin hanyaniya su Hafsy duk suka fito daga dakunan su, ganin halin da yake ciki tuni Hafsy ta fara kuka, sai da Abbu ya jata jikinshi ya rarrashe ta sannan tayi shiru. Ya kallemu duk munyi carko-carko a gabanshi muna muzurai, bai san sanda ya saki dan murmushi ba. "nace muku lafiya ta lau guys, oya Nafeesah dauko min abinci anan zan ci" jiki ba kuzari na koma na zubo mishi iya wanda zai iya ci na dora akan karamin coffee table na kai mishi, na koma kicin na dauko ruwa shima na ajiye mishi. Mu kuma muka koma kan dinning table muna cin abincin amma fa hankulan mu suna kanshi, muna cikin ci Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, hankalina yana kanta har ta tsaya kusa da Abbu kamar suna yin magana ne, ta kalli kafar shi da yake nuna mata ta yi magana kafin ta nufo kan dinning din. Duk muka gaishe ta kafin muka koma wa cin abincin mu. Muna gamawa na tattara komi na kai kicin na wanke kayan tas na dawo falo, Abbu baya falon, na zauna ni dasu Abdullahi muka danyi kallo kafin na musu sallama na tafi dakina. Shirin kwanciya barci nayi na janyo wayana na shiga chats da friends dina ta whatsapp, dp din Muneer naga ya dora hoton wata kyakkyawar yarinya matashiya da alamun ta dan girme ni, naji wani abu ya soke ni a makogaro, kasa daurewa nayi na tura mishi tambayar "who is she?" mintuna biyu kyawawa kafin reply ya shigo, "a sister" nayi ajiyar numfashi lokacin dana ji wani sukuni yana ratsa ni, "Ohh! Ashe sistern ka ce.... Ya kake?" muka danyi chatting sama sama kafin ya min sai da safe wai barci yake ji, ni kuwa har da tura mishi hearts da clouds. Yana sauka nima na kashe wayana don dama saboda shi na tsaya.
Washegari ta kama daya ga watan mayu, public holiday ne don haka muna gida. Sai wajen karfe goma na fito daga dakina, nayi break fast na koma daki nayi wanka na sake fitowa falon. Su Qaseem suna zaune yanzu suna game, na zauna a tsakiyar su muka fara bugawa. Muna nan zaune muka ci karan intercom, Abdullahi yaje ya bude, sai gasu sun shigo shi da Aunty Ameenah. Da sauri na mike tsaye ina mata sannu da zuwa har ta zauna akan kujera, na shiga kicin na dauko mata lemu da ruwa na kawo mata, gaishe ta nayi ta amsa da fara'ar ta na koma gefe ina kallonta, wannan shine karo na farko da naga wani dan uwan Abbu a gidan tunda nazo. Qaseem ta tura yaje ya gayawa Abbu tazo, tare suke fito dashi, har yanzu yana dingisa kafar shi. Na bishi da kallo cike da tausayi har ya zauna, na gaida shi tare da mishi ya jiki ya amsa. Aunty Ameenah tace "tare muka zo da Abban Ikhlas, zai shigo ya duba maka kafar" na kai dubana ga kafar tashi, sai da cikina ya kada ganin yadda kafar ta kumbura suntum! Ya yamutsa fuska "kema na fada miki ba wani abu bane ba, targade ne an gyara min shi kuma, kumburin saboda targaden ya dade a jikina ne shi yasa" ta Harare shi, "ai ba cewa nayi kayi lecturing dina ba koh?" ta daga wayarta ta kira wata lamba, ba a jima ba wani kamilallen mutum da zai yi sa'an daddy na ya shigo falon, ya ba Abbu hannu suka gaisa. Kafar tashi ya kalla yana girgiza kai, "Anya haka zamu yi da kai kuwa Farfesa?" Abbu ya rausayar da kai kamar wani karamin yaro, "Abban Ikhlas kawai neman rigima ne irin na matar nan taka, sai dana fada mata targade ne amma taki yarda" ya kara kallon wajen, "anya targade anan wajen kuwa? Bari dai mu duba mu gani" ya fiddo kayan aiki, wata er karamar naura ya fiddo ya jona da wani abu, ya kara abun a kafar Abbu sai ga komi na kafar dake kasan fatar shi ya fito a jikin na'urar, amma babu abinda muka fahimta tunda ba profession dinmu bane, ya gama dube-dubenshi ya daga ido ya kalli matar shi, "tsagewar kashi ce!!" ta zaro idanu yayin dana dafe kirji, yace yanzu bari in kira mai gyara yazo tukun. Muna nan zaune jugum-jugum har mai gyaran yazo, har kuma zuwa lokacin bamu ga ko giccin Anty Mubeenah a cikin falon ba. Wani dan tsamurmurin farin dattijo ya shigo falon, maigadi wanda ya rako shi ya duba jikin uban gidan shi kafin ya juya ya fita. Mai gyaran ya fiddo kayan aiki ya fara, yana taba kafar Abbu na saki kara saidsai da duk suka juyo suka kalleni, jikina rawa yake, tsigar jikina tana tashi, Ji nake kamar nice naji ciwon. Abbu yace mu tashi mu koma daki amma fir naki, ganin mun ki tashi yasa ya kyale mu. Tunda aka fara gyaran kuka nake har da jan shessheka, ganin ina kuka sai Hafsy itama ta fara, nan da nan falon ya karade da kukan mu ni da ita, Anty Ameenah dariya ma ta hana ta lallashe mu. Mai gyaran ya gama gyaran da zai yi yawanci fara maida tarkacen kayan gyaran cikin jaka yana dan murmushi, "da alamun amaryar ce koh?" ya tambaya yana kallon Abbu, kusan a lokaci guda shi da Aunty Ameenah suka ce "ehhh?? Aah!!" ya bisu da kallon mamaki kafin ya murmusa yace to Allah ya kara sauki. Ya dauki jakarshi ya saba a kafada ya mike, mijin Anty Ameenah ta rufa mishi baya. Abbu ya kalleni a sanyaye, "bani ruwa Nafeesah!" da sauri na mike har ina hardewa, na dauko ruwan na kawo mishi na koma kusa da Hafsy na zauna.
Mijin Anty Ameenah yana dawowa falon ya mana sallama ya tafi, Anty Ameenah ta dan taka mishi kafin ta dawo suka hau hira da Abbu. Mu kam muna zaune muna kallon news don in Abbu yana falo bamu cika kallon tashoshi barkatai ba, motsi kadai zai yi in Allah ya yarda da sannu na yake motsawa, bana ji a rayuwata na taba jin irin wannan feeling na 'protecting' da 'caring' ga kowane Bil'adama irin Abbu ba. Aka kira sallar Azuhur, Anty Ameenah ta umarce mu da mu tashi muje mu yi sallah, duk muka mike, mazan har Abbu suka fita zuwa masallaci ni kuma na tashi zan wuce dakina, Hafsy tana kan kujera tana barci, har na kai tsakiyar falon sai na juya na kalleta, "Anty ko zaki shigo kiyi sallah a daki na?" ta kalleni tana dan murmushi, "Eyyah, hutu nake yi Nafeesah, je ki abinki" a dan kunyace da jin kalamanta na juya. Ina gama sallah na koma falon, ina zama suma su Abbu suka shigo, muka bi Abbu da sannu ni da Anty Ameenah har ya zauna akan kujerar daya tashi. 'yar aikin gidan ta fito da niyar dora abincin rana, bata san abinda yake faruwa a gidan ba, ita dai taga bakuwa ta gaishe ta sannan ta wuce kicin abinta. Muna nan zaune sai ga Anty Rahina ta shigo goye da danta a baya, na tashi da sauri ina mata sannu da zuwa, hannu na mika a bayanta ta sauko min da babyn, na rungume shi tsam a jikina, Ya Allahu!! Ina son yara kamar me!
Anty Rahina ta zauna a gefen Abbu, sannu take jera mishi kamar bakinta zai tsinke na kula suna matukar ji da kanin nan nasu, fuska cike da damuwa take kallonshi, "me ya faru Ibrahim? Garin Yaya??" yayi shiru kawai yana kallonta, to me zai ce??
*_Flashback_*
Yana tsaye a bakin titi a kokarinshi nason yayi crossing ya shiga wani babban shopping mall a garin Lagos kafin su taho ya tuno da ita, haka kawai ya tsinci kanshi da son yi mata tsaraba ko don shima ya faranta ranta yadda itama take faranta mishi ta hanyar yi mishi dadadan girke-girke masu kara lafiya. Don haka ne ya ciro wayar shi ya tura mata da text.
"......yes, In shaa Allah. A dawo lafiya Allah ya kiyaye hanya....". Reply din data dawo mishi dashi kenan, yayi murmushi sosai, har kullum kulawar yarinyar zuwa gare shi tana matukar burge shi ba kadan, tunanin amsar da zai tura mata yake yi lokacin da aka ba wadanda suke kasa hannu su wuce, taku daya biyu yayi, bai tantance mai ke faruwa ba sai jin shi yayi kwance a kasa rike da kafar shi ta dama, ashe yabi ta wrong way ne, daidai lokacin an ba ababen hawa dake wajen hannu, ba tare da su duka sun kula ba wani mai mashin yabi ta kan kafar shi ya wuce.....!
*********
Yaja numfashi a hankali bayan ya gama tunano abinda ya faru, kallonta yayi yana dan murmushi, "kawai ikon Allah da tsautsayi" ta girgiza kai, "to Allah ya kara kiyayewa" duk muka amsa da Ameeeen. Maigadi yayi sallama ya shigo dauke da manyan kuloli, Malam Bala ya biyo bayan shi rike da wasu, Anty Rahina ta umarce su dasu kai kan dinning su ajiye, suka ajiye suka juya. Ta kalli Abbu, "na dafo maka abinci daga gida, kana jin yunwa ne?" ya gyada kai, ta mike "bari in zubo maka toh" da sauri na mike ina kara rungume Baby Jameel a hannuna, "Anty bari in zubo mishi" tayi murmushi tace to shikenan. Ta koma ta zauna ni kuma na wuce kicin. Harira nata kokarin hada miya, nace "kiyi abincin kadan fa, Anty Rahina ta kawo abinci" tace to shikenan. Na kwashe plates da spoon da zasu isa na koma falo, na zubawa Abbu abincin na kai mishi kafin na koma na zubowa su Anty Ameenah, ni da yara kuma muka hau dinning. Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, na kalli agogo. No wonder! Lokacin cin abinci yayi ai! Ganin su Anty Ameenah a falon sai data danyi turus! Kafin ta karasa, ta zauna akan kujerar dake kusa data Anty Ameenah tana dan murmushin yake, wai "su Yaya Ameenah ne? Ai ban san kuna gidan ba, ina daki ina ta barci" Anty Ameenah ta danyi murmushi, "Allah sarki! Muma mun zo duba mai jiki ne ai" tayi shiru kanta a kasa, Anty Rahina kam bata tanka ba Hankalinta na ga shayar da dan jariri. Ta gama kame-kame dai ta tashi tazo ta zuba abinci ta fara ci, Kai kawai nake girgizawa, rayuwar Auren bayin Allahn nan tana da matukar daure kai. Ita ta fara tashi daga kan dinning din, sai dai wannan karon maimakon ta koma dakinta, kan daya daga cikin kujerun falon ta koma ta zauna. Muma muna gama cin abincin na kwashi kayan da muka bata na kai kicin na sake dawowa falon, Baby Jameel kamar yadda nake kiranshi tunda suka shigo na amsa daga hannun maman shi, yaron ya bude idanunshi farare tas Mashaa Allah dasu yana ta walainiya dasu a tsakiyar falon, Ji nake kamar in lashe shi saboda yadda yake burge ni. Na fara jujjuya shi ina jan kumatun shi ina mishi en wasanni kafin na fara manna mishi kisses a kumatu, Abbu ya maida kanshi jikin kujera ya kwantar idanunshi a lumshe; "What he'll pay to become that baby!!".
*♡Jeedderh♡*
[09:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*14*
Da gudu na karasa wajen shi na riko hannunshi dake rike da brief case, tambayoyi nake watsa mishi ba kakkautawa, "Abbu lafiya? Abbu mai ya samu kafar ka? Abbu accident kayi a kan hanya?!....." ya zauna akan kujera yana maida numfashi, "it's just a minor targade, an gyara min. Kar ki damu" jin hanyaniya su Hafsy duk suka fito daga dakunan su, ganin halin da yake ciki tuni Hafsy ta fara kuka, sai da Abbu ya jata jikinshi ya rarrashe ta sannan tayi shiru. Ya kallemu duk munyi carko-carko a gabanshi muna muzurai, bai san sanda ya saki dan murmushi ba. "nace muku lafiya ta lau guys, oya Nafeesah dauko min abinci anan zan ci" jiki ba kuzari na koma na zubo mishi iya wanda zai iya ci na dora akan karamin coffee table na kai mishi, na koma kicin na dauko ruwa shima na ajiye mishi. Mu kuma muka koma kan dinning table muna cin abincin amma fa hankulan mu suna kanshi, muna cikin ci Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, hankalina yana kanta har ta tsaya kusa da Abbu kamar suna yin magana ne, ta kalli kafar shi da yake nuna mata ta yi magana kafin ta nufo kan dinning din. Duk muka gaishe ta kafin muka koma wa cin abincin mu. Muna gamawa na tattara komi na kai kicin na wanke kayan tas na dawo falo, Abbu baya falon, na zauna ni dasu Abdullahi muka danyi kallo kafin na musu sallama na tafi dakina. Shirin kwanciya barci nayi na janyo wayana na shiga chats da friends dina ta whatsapp, dp din Muneer naga ya dora hoton wata kyakkyawar yarinya matashiya da alamun ta dan girme ni, naji wani abu ya soke ni a makogaro, kasa daurewa nayi na tura mishi tambayar "who is she?" mintuna biyu kyawawa kafin reply ya shigo, "a sister" nayi ajiyar numfashi lokacin dana ji wani sukuni yana ratsa ni, "Ohh! Ashe sistern ka ce.... Ya kake?" muka danyi chatting sama sama kafin ya min sai da safe wai barci yake ji, ni kuwa har da tura mishi hearts da clouds. Yana sauka nima na kashe wayana don dama saboda shi na tsaya.
Washegari ta kama daya ga watan mayu, public holiday ne don haka muna gida. Sai wajen karfe goma na fito daga dakina, nayi break fast na koma daki nayi wanka na sake fitowa falon. Su Qaseem suna zaune yanzu suna game, na zauna a tsakiyar su muka fara bugawa. Muna nan zaune muka ci karan intercom, Abdullahi yaje ya bude, sai gasu sun shigo shi da Aunty Ameenah. Da sauri na mike tsaye ina mata sannu da zuwa har ta zauna akan kujera, na shiga kicin na dauko mata lemu da ruwa na kawo mata, gaishe ta nayi ta amsa da fara'ar ta na koma gefe ina kallonta, wannan shine karo na farko da naga wani dan uwan Abbu a gidan tunda nazo. Qaseem ta tura yaje ya gayawa Abbu tazo, tare suke fito dashi, har yanzu yana dingisa kafar shi. Na bishi da kallo cike da tausayi har ya zauna, na gaida shi tare da mishi ya jiki ya amsa. Aunty Ameenah tace "tare muka zo da Abban Ikhlas, zai shigo ya duba maka kafar" na kai dubana ga kafar tashi, sai da cikina ya kada ganin yadda kafar ta kumbura suntum! Ya yamutsa fuska "kema na fada miki ba wani abu bane ba, targade ne an gyara min shi kuma, kumburin saboda targaden ya dade a jikina ne shi yasa" ta Harare shi, "ai ba cewa nayi kayi lecturing dina ba koh?" ta daga wayarta ta kira wata lamba, ba a jima ba wani kamilallen mutum da zai yi sa'an daddy na ya shigo falon, ya ba Abbu hannu suka gaisa. Kafar tashi ya kalla yana girgiza kai, "Anya haka zamu yi da kai kuwa Farfesa?" Abbu ya rausayar da kai kamar wani karamin yaro, "Abban Ikhlas kawai neman rigima ne irin na matar nan taka, sai dana fada mata targade ne amma taki yarda" ya kara kallon wajen, "anya targade anan wajen kuwa? Bari dai mu duba mu gani" ya fiddo kayan aiki, wata er karamar naura ya fiddo ya jona da wani abu, ya kara abun a kafar Abbu sai ga komi na kafar dake kasan fatar shi ya fito a jikin na'urar, amma babu abinda muka fahimta tunda ba profession dinmu bane, ya gama dube-dubenshi ya daga ido ya kalli matar shi, "tsagewar kashi ce!!" ta zaro idanu yayin dana dafe kirji, yace yanzu bari in kira mai gyara yazo tukun. Muna nan zaune jugum-jugum har mai gyaran yazo, har kuma zuwa lokacin bamu ga ko giccin Anty Mubeenah a cikin falon ba. Wani dan tsamurmurin farin dattijo ya shigo falon, maigadi wanda ya rako shi ya duba jikin uban gidan shi kafin ya juya ya fita. Mai gyaran ya fiddo kayan aiki ya fara, yana taba kafar Abbu na saki kara saidsai da duk suka juyo suka kalleni, jikina rawa yake, tsigar jikina tana tashi, Ji nake kamar nice naji ciwon. Abbu yace mu tashi mu koma daki amma fir naki, ganin mun ki tashi yasa ya kyale mu. Tunda aka fara gyaran kuka nake har da jan shessheka, ganin ina kuka sai Hafsy itama ta fara, nan da nan falon ya karade da kukan mu ni da ita, Anty Ameenah dariya ma ta hana ta lallashe mu. Mai gyaran ya gama gyaran da zai yi yawanci fara maida tarkacen kayan gyaran cikin jaka yana dan murmushi, "da alamun amaryar ce koh?" ya tambaya yana kallon Abbu, kusan a lokaci guda shi da Aunty Ameenah suka ce "ehhh?? Aah!!" ya bisu da kallon mamaki kafin ya murmusa yace to Allah ya kara sauki. Ya dauki jakarshi ya saba a kafada ya mike, mijin Anty Ameenah ta rufa mishi baya. Abbu ya kalleni a sanyaye, "bani ruwa Nafeesah!" da sauri na mike har ina hardewa, na dauko ruwan na kawo mishi na koma kusa da Hafsy na zauna.
Mijin Anty Ameenah yana dawowa falon ya mana sallama ya tafi, Anty Ameenah ta dan taka mishi kafin ta dawo suka hau hira da Abbu. Mu kam muna zaune muna kallon news don in Abbu yana falo bamu cika kallon tashoshi barkatai ba, motsi kadai zai yi in Allah ya yarda da sannu na yake motsawa, bana ji a rayuwata na taba jin irin wannan feeling na 'protecting' da 'caring' ga kowane Bil'adama irin Abbu ba. Aka kira sallar Azuhur, Anty Ameenah ta umarce mu da mu tashi muje mu yi sallah, duk muka mike, mazan har Abbu suka fita zuwa masallaci ni kuma na tashi zan wuce dakina, Hafsy tana kan kujera tana barci, har na kai tsakiyar falon sai na juya na kalleta, "Anty ko zaki shigo kiyi sallah a daki na?" ta kalleni tana dan murmushi, "Eyyah, hutu nake yi Nafeesah, je ki abinki" a dan kunyace da jin kalamanta na juya. Ina gama sallah na koma falon, ina zama suma su Abbu suka shigo, muka bi Abbu da sannu ni da Anty Ameenah har ya zauna akan kujerar daya tashi. 'yar aikin gidan ta fito da niyar dora abincin rana, bata san abinda yake faruwa a gidan ba, ita dai taga bakuwa ta gaishe ta sannan ta wuce kicin abinta. Muna nan zaune sai ga Anty Rahina ta shigo goye da danta a baya, na tashi da sauri ina mata sannu da zuwa, hannu na mika a bayanta ta sauko min da babyn, na rungume shi tsam a jikina, Ya Allahu!! Ina son yara kamar me!
Anty Rahina ta zauna a gefen Abbu, sannu take jera mishi kamar bakinta zai tsinke na kula suna matukar ji da kanin nan nasu, fuska cike da damuwa take kallonshi, "me ya faru Ibrahim? Garin Yaya??" yayi shiru kawai yana kallonta, to me zai ce??
*_Flashback_*
Yana tsaye a bakin titi a kokarinshi nason yayi crossing ya shiga wani babban shopping mall a garin Lagos kafin su taho ya tuno da ita, haka kawai ya tsinci kanshi da son yi mata tsaraba ko don shima ya faranta ranta yadda itama take faranta mishi ta hanyar yi mishi dadadan girke-girke masu kara lafiya. Don haka ne ya ciro wayar shi ya tura mata da text.
"......yes, In shaa Allah. A dawo lafiya Allah ya kiyaye hanya....". Reply din data dawo mishi dashi kenan, yayi murmushi sosai, har kullum kulawar yarinyar zuwa gare shi tana matukar burge shi ba kadan, tunanin amsar da zai tura mata yake yi lokacin da aka ba wadanda suke kasa hannu su wuce, taku daya biyu yayi, bai tantance mai ke faruwa ba sai jin shi yayi kwance a kasa rike da kafar shi ta dama, ashe yabi ta wrong way ne, daidai lokacin an ba ababen hawa dake wajen hannu, ba tare da su duka sun kula ba wani mai mashin yabi ta kan kafar shi ya wuce.....!
*********
Yaja numfashi a hankali bayan ya gama tunano abinda ya faru, kallonta yayi yana dan murmushi, "kawai ikon Allah da tsautsayi" ta girgiza kai, "to Allah ya kara kiyayewa" duk muka amsa da Ameeeen. Maigadi yayi sallama ya shigo dauke da manyan kuloli, Malam Bala ya biyo bayan shi rike da wasu, Anty Rahina ta umarce su dasu kai kan dinning su ajiye, suka ajiye suka juya. Ta kalli Abbu, "na dafo maka abinci daga gida, kana jin yunwa ne?" ya gyada kai, ta mike "bari in zubo maka toh" da sauri na mike ina kara rungume Baby Jameel a hannuna, "Anty bari in zubo mishi" tayi murmushi tace to shikenan. Ta koma ta zauna ni kuma na wuce kicin. Harira nata kokarin hada miya, nace "kiyi abincin kadan fa, Anty Rahina ta kawo abinci" tace to shikenan. Na kwashe plates da spoon da zasu isa na koma falo, na zubawa Abbu abincin na kai mishi kafin na koma na zubowa su Anty Ameenah, ni da yara kuma muka hau dinning. Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, na kalli agogo. No wonder! Lokacin cin abinci yayi ai! Ganin su Anty Ameenah a falon sai data danyi turus! Kafin ta karasa, ta zauna akan kujerar dake kusa data Anty Ameenah tana dan murmushin yake, wai "su Yaya Ameenah ne? Ai ban san kuna gidan ba, ina daki ina ta barci" Anty Ameenah ta danyi murmushi, "Allah sarki! Muma mun zo duba mai jiki ne ai" tayi shiru kanta a kasa, Anty Rahina kam bata tanka ba Hankalinta na ga shayar da dan jariri. Ta gama kame-kame dai ta tashi tazo ta zuba abinci ta fara ci, Kai kawai nake girgizawa, rayuwar Auren bayin Allahn nan tana da matukar daure kai. Ita ta fara tashi daga kan dinning din, sai dai wannan karon maimakon ta koma dakinta, kan daya daga cikin kujerun falon ta koma ta zauna. Muma muna gama cin abincin na kwashi kayan da muka bata na kai kicin na sake dawowa falon, Baby Jameel kamar yadda nake kiranshi tunda suka shigo na amsa daga hannun maman shi, yaron ya bude idanunshi farare tas Mashaa Allah dasu yana ta walainiya dasu a tsakiyar falon, Ji nake kamar in lashe shi saboda yadda yake burge ni. Na fara jujjuya shi ina jan kumatun shi ina mishi en wasanni kafin na fara manna mishi kisses a kumatu, Abbu ya maida kanshi jikin kujera ya kwantar idanunshi a lumshe; "What he'll pay to become that baby!!".
*♡Jeedderh♡*
[09:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*15*
*'In a nation where the Poor face hardships, suffering and fears, only the riches and the one's that has power lives in peace, thrives and prospers....... Assalamu Alaikum Wa Rahmatullah Ya Ibaadullaheessaaliheen!!!......'*
Sai gab da Magriba su Anty Ameenah suka mana sallama zasu tafi, na leka dakin Anty Mubeenah wadda tunda aka kira sallar la'asar ta tashi da niyar zuwa tayi sallah bata dawo ba, na gaya mata zasu tafi ta leko suka yi sallama ta koma dakinta. Ni dasu Hafsy har Abbu mai kafa sai da muka taka musu har gaban motar da Anty Rahina tazo da ita. Anty Ameenah ta kalleni na goya baby Jameel a bayana yana ta shakar barci abin shi, tayi murmushi cike da tsokana tace "to Hajiya Nafee a bamu baby din koh?" na fara kokarin sauke yaron daga bayana, "Allah Anty ji nake kamar ku bar min shi!" su duka suka kwashe da dariya, Anty Raliya tace "kina son yara ne har haka?" nayi dan murmushi, "sosai ma! Amma mommy taki ta haifo mana wasu" na karasa ina pouting kamar inyi kuka dana tuno diramar da muke sha da ita idan ina mata maganar me yasa bata kara haihuwa daga kaina ba? Sai tace ai Allah ne bai kawo ba, ranar nan ma dana takura mata da tambaya zagi ta dankara min tace in cewa daddy na ya karo aure mana sai a Haifa min yaran, na tuna lokacin kuka na fashe dashi saboda zagin data min, shi kuwa daddy dariya ya dinga mana. Daga ranar ban kara mata korafi ba, sai dai in yiwa daddy. Su Anty Ameenah kam dariya suke min, sun fahimci tsantsan yarinta da sokancin da aka san Yaya irinmu nayi a tare dani. Anty Ameenah tace "Kar ki damu, in shaa Allah kema zaki haifi naki, kinga kin huta kenan koh?" na gyada kaina ina murmushi, "daddy ma haka yace ranar nan!" suka kara sakin dariya kafin suka shiga motar, na mikawa Anty Ameenah babyn tare da maida murfin motar na rufe mata tare da daga musu hannu, suka ja motar suka tafi. Na dan saci kallon Abbu kallona yake sosai with astonishment in his eyes, murmushi yake yi kamar kunnen shi zai zage, na samu kaina da tambayar dalilin sudden change dinshi curiously. Na kama hannun Hafsy muka koma cikin gida ya biyomu a baya. Muna gama dinner na musu sai da safe na koma dakina, sosai nake jina a gajiye ga wani barci daya rufe min idanu.
Kwana uku muna jinyar Abbu ni da yaran shi, ba laifi ya warke duk da cewa bai fara fita ba, kuma har zuwa lokacin Tafiyar shi bata koma irin ta normal people ba. Cikin wannan lokacin mun ga jama'ah ba kadan ba, ko wace rana sai mun ga bakin fuska cikin masu zuwa duba shi gaskiya Abbu yana da jama'ah sosai. Saurayin Ni'ima zai kawo mata ziyara ranar alhamis, ranar a lab muka wuni tare dasu suna jira mu tashi su wuce gidan su dani, na gaya musu Abbu ya hana ni yawo amma ina! Suka ce they wouldn't take no for an answer, dole suka saka ni kiran shi. Na fita daga cikin lab din bayan na danna mishi kira, bugawa daya biyu ya dauka ana uku, a sanyaye na gaida shi tare da tambayar jikinshi ya amsa da lafiya, nayi shiru ina kamo bakin zaren daga inda zan mishi maganar har sai daya tambaye ni ya? Sannan na gaya mishi kamar wadda take tsoron tayi maganar, shiru ya biyo baya kafin ajiyar numfashi mai nauyi, "amma kada ki wuce karfe bakwai baki dawo ba" da sauri nace "in shaa Allahu Abbu" daga nan muka yi sallama. Ranar tun kafin lokacin tashin mu yayi muka tafi. Unguwar Galadanchi muka nufa, ashe mahaifin su shi yake rike da sarautar Galadanchi ta garin Kano, babban gida ne wanda ginin shi na asalin gidajen sarauta ne, sashen Hajiya Fati muka fara shiga ita ce mace ta biyu a gidan, mace mai karimci ta tarbe mu da faraarta, na kula su Ni'ima kamar babbar Yaya suka dauketa don a sashenta ma suka ce zasu saukar da Bashir din. Cike da girmamawa na gaidata ta amsa da fara'ar ta tare da sawa aka kawo mana ruwa, mun dan jima a sashen nata kafin muka mata sallama muka wuce sashen Hajiya Siyama mahaifiyar su Abbu. Sashen nata in ka shiga baka taba cewa dakin er dattijuwa ka shiga duk da cewa shima sashen Hajiya Fati babu laifi. Babban falo ne wanda yasha saitin royal kujeru ruwan zuma, muka zube a kan wani tattausan carpet muna gaishe ta tana zaune akan sallaya tana lazumi, kana ganin kamilalliyar fuskarta zaka san cewa ka kalli fuskar ma'abociyar addini, babu abinda Abbu ya baro nata sai dogon siririn hancinshi, ita nata yana da dan fadi, sai data gama lazuminta kafin ta amsa mana cike da kulawa. Daga nan su Ni'ima suka jani muka je dakin su muka yi sallah, kayan jikina na canza muka shiga kicin muka fara shirya kayan abinci kala kala. Na bata shawarar mu yi snacks wanda zamu basu a matsayin tsaraba idan zasu tafi gobe, don haka muka yi doughnuts wanda muka yi icing dinshi muka watsa shredded cheese da chocolate akai. Karfe biyar suka karaso shi da abokin shi, mun riga mun kai komi sashen Hajiya Fati, mun shirya koina sai kamshi kawai dake tashi a wajen. Ita uwar gida ta musu rakiya zuwa inda aka tanadar musu mu kuma muka tsaya karasa gyara kicin din, sai da muka gama gyaran jikinmu sannan muka je muka gaisa dasu. Bashir din nata kamar yanda take fada dan kyakkyawa dashi ga barkwanci, abokin nashi ne ma bai mun ba ko kadan, sai wani shisshige min yake yi yana jana da hira duk ya takura min don haka na mike nace musu zan wuce gida, duk suka kalleni da mamaki ni kuwa Na Kauda kaina gefe don ma kar suga fuskar hana ni tafiya. Sa'adiya ta taso ta kama hannuna muka fita, abokin Bashir da naji yana kira da Fahad ya taso ya biyo mu, ganin babu fuska yasa ya juya. Na saki tsaki kasa kasa, Sa'adiya tayi dariya tace da alamun gayen bai miki ba, kai kawai na girgiza mata muka wuce sashen Hajiya Siyama. Tana kan daya daga cikin kujerun falon tana kallon tashar Saudi, ta kalle mu cike da mamaki, "lafiya dai ko?" Sa'adiya tace "wai gida tace zata wuce!" tace Haba ai kin tsaya kici abinci koh?" nace "Hajiya Abbu...." tayi saurin katse ni, "kyale shi kawai, ba zaki tafi ba sai kinci abinci fa" bani da zabi dole na wuce dakin su Ni'ima don bazan iya komawa wajen su nataccen abokin Bashir ba kuma bazan iya zama kusa da Hajiyar ba.
Sai wajen karfe bakwai da rabi sannan muka fito ni da direban da xai maida ni gida, bayan naci tuwon tsakin masara da miyar kalkashi wadda taji yajin daddawa, tantakwashi da man shanu ga kunun aya mai sanyi da Gardi a gefe. Tare dasu Ni'ima muka ci abincin bayan Tafiyar su Bashir, ta bude tarkacen kayan tsarabar daya kawo mata ta ciro min kayan shafa, turare ne da kayan makulashe naki amsa, sai da suka yi kamar zasu yi fushi sannan na saka hannu na dauko turaren 'splendid' tsohon turarena ne tun a secondary school, daga baya ya bata na gaji da nema na komawa kamfanin lily cool, Sa'adiya ta kara min da tarkacen sweets muka fita falo. Kicin na shiga na dauko doughnuts din dana debar wa su Hafsy, Hajiya na falon a zaune na durkusa a kusa da ita na mata sallama, ta min godiya sosai har sai dana ji kamar in nutse a kasa. Ta mikawa Ni'ima wata karamar silver grey din jaka tace ta bani, na mata godiya sosai kafin muka tashi, sai da muka je ta sashen Hajiya Fati na mata sallama kafin muka fita waje inda direba yake jira na, na shiga motar muka kara yin sallama dasu kafin muka tafi. Nayi shiru a bayan mota ina tunanin abinda zan fadawa Abbu, a raina addua nake ina karawa akan kada Allah yasa yayi fushi dani, naki jinin fushin Abbu kamar yadda na tsani bacin ranshi. Har cikin gida direba ya shiga dani, na fito daga motar ina mishi godiya tare da sai da safe, iska ake yi sosai kamar ta dauki mutum tayi yawo dashi, idanuna a rufe saboda kasar da iskar guguwa ta watsa min na shiga falon bakina dauke da addu'ar da ake yi idan guguwa ta tashi, kamar hadin baki ina shiga aka dauke wuta. Na bude idanuna da kyar ina murza su, kafin inyi adjusting da dan guntun hasken falon wanda ya ratso ta cikin shara-sharan labulayen dakin daga farfajiyar gidan wanda lantarkin solar ta samo dashi, naji kafana tayi stepping akan wani abu mai tsananin sul6i, kafin in tantance meye naji ni na fara tafiya sululuuuu.....!! A tsakiyar dakin, na kwala ihu sosai ina salati tare da laluben abinda zan kama in rike tunanin farko daya fado min a cikin raina shine hango ni da nayi na kai da bakina, kyawawan kananun hakora na guda biyu na gaba malale a cikin jinin dake fita daga bakina....... Karo na kaiwa wasu hard muscled chest wadanda ko a cikin duniyar mafarkina ban taba hangoni a kansu ba, sai ga gangar jikina a jikinsu yau kamar a mafarki, dogayen tausasan hannuwa suka zagaye bayana, daya a kuguna daya a gadon bayana, jikina yake dauki rawa kamar wadda ta rungumi kankara cikin hunturun sanyi yayin da naji wasu dogayen zara-zaran yatsu suna suna tapping din gadon bayana a hankali., ban san lokacin dana saki ledojin hannuna, purse dina da wayata akan tiles din dake cikin falon ba.....!!.
*♡Jeedderh♡*
[09:15, 12/4/2017] +233 50 348 1936: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*16*
*-Search across the Oceans for who are been lost for two long......*
*'Searching for a secret in coming home we find we have what we need.....!'*
*-New Empire-* _Across the Ocean_
Hankalina gabadaya ya dauke daga jikina, babu abinda nake fahimta sai tattausan kamshin dake fita daga jikin Abbu, bugawar da zuciyar shi take yi da dan sauri-sauri, dumin dake fita daga jikinshi....... Ya dago fuskata daga jikinshi yana kallona kamar hadin baki, aka dawo da wuta lokacin. Na samu kaina starring at his brown oily eyes da suke wani irin sheki kamar zaiba, "Nafee, are you ok??" cikin daukewar tunani na daga baki nace "umh???" ba tare dana yi kokarin dauke idanuna daga kanshi ba, ya dan jijjiga kafadata, "hey!" kamar wadda aka daddaba daga barci, nayi firgigit ina kallon cikin falon, Ya Allahu! What the heck just happened?? Da sauri na durkusa na tattara kayana da suka zube nayi hanyar dakina a sukwane, da sauri ya riko tsintsiyar hannuna, nayi cik ina sauraren abinda zai ce ba tare dana juya na kalleshi ba, "lafiyar ki kuwa Nafeesah?" da sauri na gyada kaina, "lafiya lau, kayi hakuri dan Allah" ina jin sautin murmushin daya saki, ya sakar min hannu dama abinda nake jira kenan don haka na bazama dakina a sukwane. Kofar dakin na maida na rufe tare da murza key, nayi wuri-wuri a tsakiyar dakin kamar wadda take neman wajen buya kafin na zube a kasan dakin akan gwiwa na, zuciyana wani irin gudu take yi, na rasa abinda yake min dadi a lokacin. Ban san iya lokacin dana dauka a wajen ina zaune ba, tare da taimakon Innalillahi.... Dana dinga ja na dan samu sukuni a cikin raina, tashi nayi na fara bandaki na watsa ruwa mai sanyi a jikina duk da sanyin da ake yi sakamakon iskan da aka gama yi. Na fito daure da tawul a jikina na tsaya a gaban mirror, lotion na shafa na saka rigar barci wadda ta tsaya min a gwiwa, duk abinnan da nake yi idanun Abbu suna cikin memory na, na rasa abinda zan yi da zai dauke min tunaninshi daga cikin raina, chatting! Zuciyata ta tuna min, da sauri na tafi inda nayi jifa da kayan hannuna tare da wayar na dauko ta, ina daga ta na dan saki kara ganin yadda screen dinta ya tsattsage, na ciza tattausan lebena na kasa ina ji kamar in dora hannu aka in saki ihu saboda yadda nake son wayata dinnan, bana so ko datti ya hau kanta. Ganin chatting din ma bai mun abinda nake so ba yasa na janyo system dina na kunna na fara kallon Baywatch, ajiyar zuciya na dan saki ganin hankalina ya dauke zuwa ga film din.
Sai Washegari na ba su Hafsy doughnut din dana kawo musu, tare dasu ma muka cinye shi a cikin mota. Yau Daddy da kanshi yazo daukata, yazo duba jikin Abbu ne. Sai da aka yi sallar la'asar muka wuce Kaduna, bakin daddy bai yi shiru ba a hanya yana ta bani labarin kirki da mutunci irin na Abbu, bai san cewa yanzu bana cikin mood din sauraren labarin Abbu bane, ko sunan Abbu aka ambata sai naji faduwar gaba, shi yasa yau nayi duk kokarin da zanyi wajen ganin na kaucewa haduwa dashi, nayi, sai dai dole sai da na ganshi lokacin da muke mishi sallama ni da daddy. Kaina na jinginar da jikin seats din da nake kai na lumshe idanuna kamar mai barci, hakan yasa daddy ya kama bakinshi ya bame har muka isa Kaduna.
Da dare Ni'ima ta kira ni, bayan mun gaisa take fada min wai Fahad dinnan ne abokin Bashir ya dame ta akan ta bashi number na, na tabe baki nace "kada kiyi kuskure bashi Ni'ima" tace me yasa? Nace ban gane ba? Waye a cikin ku bai san cewa Akwai wanda nake dating ba? Taja tsaki, dallah dating ko crushing?? Waye bai san cewa crushing din Muneer kike yi shi baya son ki ba?? Na dan dakata kadan kafin inyi magana, "Ramlah mai bakin Aku!! Ita ta fada muku koh?" daga can tace that doesn't matter ko kadan ai, ni ai zan bashi number! Nace cikin gatse, "ki bashi din toh, zaki gani ne" na katse wayar tare da jifa da ita akan gado. Muneer!! Na maimaita sunan, it's kinda strange. Rana bata taba fita ta koma ga ubangijinta ba ba tare dana tunana bawan Allahn nan a cikin raina ba, amma har ga Allah yau dai, yau gabadaya na manta da existing dinshi a duniya, Anya lafiya ta lau kuwa??! Tashi nayi na koma falo wajen su daddy muka sha hirar mu, sai dana fara hamma sannan na musu sallama na wuce dakina.
Da safe na ba daddy waya na nace a canza min screen din, Koda ya tambaye ni dalilin tsagewar ta cewa nayi faduwa tayi, to me zan ce mishi? Kafin azuhur sai gashi da sabuwar Samsung edge plus, nayi tsalle, nayi ihu na rungume shi, wayar da nake masifar so kenan sai dai bana so in takurawa iyayena da zancen wayar da nasan kudin abincin wani na shekara daya ne, shi yasa nayi shiru, sai gashi yau Allah ya bani ba tare dana roka ba. Daddy kam yasha addu'a ranar kamar bakina zai tsinke, haka nake ni kam, idan aka min kyauta sai in wuni ina wa mutum godiya. Mommy na cewa ta bada ayi fura don na kula Abbu yana so sosai, duk ranar dana kai fura ranar ita ce abincin shi har ta kare. Washegari na doshi hanyar Kano cike da tsaraba don sai da muka shiga shago na saiwa Hafsy dasu Qaseem sannan muka wuce, cike kuma da wani longing, longing to see someone wanda na ma rasa a wane matsayi zan ajiye shi cikin raina., abokin Babana ko kuwa Abokin Rayuwata??!
Aunty Mubeenah da wata kanwarta Shakirah kadai na taras a gidan, ina ga Abbu ya fita zagaya unguwa kamar yadda yake yi lokaci zuwa lokaci da er sandar taimaka tafiya, na durkusa na gaida su, Anty Shakirah ta mun sannu da zuwa har tana tsokanata da ina tsarabar ta tunda Allah yasa tana nan nazo. Matar tana da kirki, duk tafi sauran en uwan Anty Mubeenah da suke zuwa gidan, wasu idan suka zo ko kallon mutane basa yi balle su amsa gaisuwar su, wasu kuwa kallon mutane suke yi kamar kiyashi shi yasa nima bana kula da kurar data debe su. Dariya na dinga yi tana tsokanata, na ciro chocolate din kit-kat babba na bata nace ta kaiwa yara, na ciro wani hadadden turaren wuta na asalin en maiduguri na ba Anty Mubeenah inji Mommy na, ta amsa babu yabo babu fallasa, babu godiya ba komi kamar wadda ta bani ajiya, naji haushin abun ba kadan ba, na mike daga zaunen da nake na dauki jakar hannuna na wuce dakina. Kayayyakina na ciro na shirya komi a inda ya dace, na ciro fura da nonon da aka wa Abbu na Kai fridge na ajiye, daga kicin ina jiyo hirar dasu Anty Shakirah suke yi saboda a falo na biyu suke wanda yafi kusa da kicin din, Anty Shakirah ce take tambayar Anty Mubeenah mai yasa bata son turaren? Tace to mai zanyi dashi? Idan baki so ki bani ai ban rasa wanda zan ba bane, da sauri naji tace ina so wallahi, turaren ne yana da tsada naga gashi yana da wahalar samu shi yasa! Nayi kwafa ina girgiza kaina, wato kyauta ma tayi da turaren wutar da babu yadda ban yi da mommy akan ta bani in kaiwa Anty Haleemah ba mommyn taki ita ala dole sai ita, to ga abinda ya faru nan ai!. Dakina na koma cike da takaici ban jima da shiga ba naji hayaniyar su Hafsy a falo, da sauri na fita. Suna gani na suka kwashi ihun murna duk suka rugo, kowannen su so yake ya rungume ni, ni kam dariya kawai nake ina ihun su sake ni daga cakumar da suka kin kar su kayar dani amma ina! Sai da suka gaji dan kansu sannan suka sake ni, Abbu yana bayansu ya jingina bayan shi da kujera yana kallonmu cikin murmushi, da sauri na zube a kasa ina gaida shi, can kasan zuciya ta wani irin farin ciki yake mintsini na. Yaran naja muka tafi dakina tun kafin inyi abinda zan zo ina dana sani don wani sashen na zuciyata wai rada min inje in rungume shi yake yi. A daki na baza musu tsarabar dana kai musu, nan muka baje muka ci wasu a gun wasu kuma suka diba suka tafi daki lokacin da aka kira Magriba, ni da Hafsy kuma muka yi tamu a daki.
Muna gama dinner na mike da niyar inje in kwanta, Abbu ya kalleni yace "Nafeesah Akwai fura ne?" na gyada kaina a hankali, wata irin kasala ta rufar min saboda yadda ya kira sunana, yace dama min pls. Na wuce kicin na dama mishi furar, nasa ayaba lokacin da nake damawa dana gama kuma na watsa kankara a ciki na dauki bowl din dana juye furar a cikin na koma falo, yana sec parlour a kishingide akan kujera da alamu waya yake amsawa, cikin harshen turanci yake wayar. Na ajiye a gabanshi na fara kokarin zubawa a cikin cup ina satar kallonshi, wayar yake amsawa cike da wata irin yanga yana yi yana wani lumshe ido, accent din turancin shi ko kadan bai yi kama dana bahaushe ba, idan kana ji sai kayi zaton ko rainon kasar Ingila ne, to waya sani? Naji ance a LA ya kammala digiri dinshi na farko. Na danyi murmushi ina girgiza kai, sau tari ina mamakin yadda Abbu yake da yanga kamar wata mace, zaka iya mistaking kace yanga ce kam idan baka zauna dashi ba don a zahirin gaskiya haka yake naturally. Ya ajiye wayar hannunshi akan kujerar yana zama sosai, "what's funny?" da sauri na girgiza kaina "ba komi?" na mika mishi cup din, ya kura min idanu kamar yana so ya karanci abinda ya saka ni murmushin da kanshi, nayi kasa da kaina, ina jin sighing din daya saki kafin ya amshi cup din, da sauri nayi niyar tashi ya tsayar dani ta hanyar tambayana ya Daddy na? Nan fa na zauna na fara zuba mishi labari har na wayar da daddy na ya canza min, ya daga girarshi yana dan murmushi, "inye! Her daddy's girl!!" na sadda kaina kasa ina murmushi in ma zan iya cewa kila har da blushing, ya jefo min tambayar data kada min ciki, "garin yaya har screen din wayarki ya fashe?" na yi wuki-wuki da idanu kamar wadda aka kama tayi karya, ya sake tambayana, kafin in lalubo abinda zan ce wayar shi tayi kara, yana dauka na lallaba na mike da sauri sai dakina. Ina shiga na ajiye numfashi da karfi, Allah ya cece ni yau. Kayan barci na saka, na dauko log book dina na bude na dan dudduba kafin na janyo system dina na cigaba da kallon Pinocchio dana fara yi. Wajen karfe tara da rabi naji wayana tayi kara, na daga ganin bakuwar number yasa na daga da sallamata, daga can wata familiar murya ta amsa sallamar tare da karawa da "gorgeous!" cike da mamaki nace "waye?" sai dana kusa dakin zagi lokacin da naji yace "Fahad ne, abokin Bashir Saurayin Ni'ima" na hade fuska kamar yana gani na, jin nayi shiru yasa yace "gorgeous, baki gane ni bane?" a raina nayi exclamin kalmar 'wai gorgeous!' cike da jin haushi nace na gane ka mana, and please suna na Nafeesah ne ba wani abu wai gorgeous ba ka gane!" ya saki wata dariya data kara kular dani, "Haba gorgeous! To me kin cancanci abinda yafi wannan sunan ma. Kawai ki bani dama in nuna miki how precious you are to me, wallahi tun ranar dana saka ki a idanuna naji cewa na samu macen dana dade ina nema a rayuwata, tun daga ranar na baki wani matsayi mai girma a cikin raina, Gorgeous, wallahi u've become a very special part of my being, you are my happiness, you've got everything I need from my wife you are classy, beautiful, hafiza.....!!" blah-blah-blah ya shiga jero labarai har na gaji da saurare, ganin yaki dasa aya yasa na tsaida shi, "please Malam! Ita wadda ta baka number dina bata yi maka bayanin ina da Mijin aure bane?" ya kara sakin dariya, "ta dai fada min cewa kina da wanda kike so and unfortunately though to my relief baya sonki in return, baby just leave him, bai san ciwonki ba. I promise you zan so ki fiye da yadda yake sonki, na miki alkawarin mantar dake cewa kin so gayen can baby, just give me a chance kinji?" ni kam ina baki? Zuciyata cike da takaicin tonon sililin da Ni'ima ta min. Da kyar na saisaita kaina daga ihun da nake ji a cikin kaina na son in sossoka mishi zagi na dai yi kokari nayi calming din kaina, after all ai ba laifin shi bane, zamu gauraya da mai laifin. Duk da haka ban iya tsaida tsakin daya fito min ba, nace "Malam I don't need your love or whatever trash you are talking about ka gane? Don Allah Kar ka sake kira na!" na kashe wayar da sauri. Ni'ima na kira, cikin sa'a ta dauka a ringing din farko, ko sallama ban bari tayi ba na fara zazzaga mata ruwan masifa, daga farko hakuri ta fara bani, daga kuma sai ta fara tsokanata wai akan ta ma taimake ni? Nace taimakon ki din banza? Nace miki ina so ne? Tace baki fada ba, zuciyar ki ta fada min. Ganin ta maida abun wasa na kashe wayar ina kara maimaita mata ta kira Fahad ne koma uban waye sunan shi ta gaya mishi kada ya sake kiran wayata don duk ranar daya kuma sai naci Mutuncin shi, ita kuma ta jirayi haduwar mu gobe!! Tace "Allah ya kaimu" cike da izgilanci, na kashe wayar ina kwafa. Ajiyar zuciya nake saukewa cike da takaici kamar zan hadiyi zuciyata in mutu. Karan wayata naji, da sauri na wawuri wayar ina tunanin kalar zagin da zan narka, ganin sunan Mommy ne yasa na dan saki fuskata kafin na dauka, gaisawa muka yi ta tambaye ni na sauka lafiya? Na amsa mata da lafiya lau. Mun danyi hira da ita kafin muka yi sallama, na dora wayar akan bedside drawer ni kuma na kwanta bayan nayi dimming din wutar dakin.
0 comments:
Post a Comment