1
fitowa nayi daga daki ina shure-shuren kafa, "ni Allah baxan je ba innah" da kayana innata ta biyo ni tana rarrashina haba Niimatullah me yasa Kullum idan xaki makaranta sai an yi tsallen tsiya da ke, karbi kayan ki saka, kinga idan kika makara aka xane ki kada ki fara dawowa kiyi min korafi ko kin fada baxan kula ki ba, idanuna ne suka cika da hawaye, ni baxan je ba innata Kullum naje sai malam ya dake ni bansan me nayi masa ba ya tsane ni. ina maganar ina share guntun hawayen da na kalato shi da gan-gan, rarrashina ta shiga yi har sai da na saka kayan na tafi ina tafe a hanya ina mita, cin karo nayi da Babana da gudu na karasa wajensa ina sharar kwalla, cikin tashin hankali ya dube ni, me yasa min ke kuka Niimatullah? idanuna cike da hawaye na dube shi, innata ce tace sai naje makaranta ni kuma ban son xuwa, cikin kulawa tare da murmushi ya dafa kaina, kiyi hakuri yar lelen baba kije makaranta kin ji ko, ilimi shi ne gishirin xaman duniya, musamman ilimin addini, karbi wannan yasa hannu a aljihu ya miki min naira biyar, cike da shagwaba na tabe baki, ka barshi baba tausayinka nake ji, da dukkan alamu yaji dadin abinda na fada masa, dafa kaina yayi Allah yayi miki albarka yar lelen baba, Allah ya baki abinda kika tafi nema, amsa masa nayi da Ameen, na kwasa da gudu sai makaranta, cikin ikon Allah naci sa'a ba a fara dukan makara ba don haka cikin farin ciki na shiga Aji
Bayan an tashi na biyo ayarin kawayena muka taho muna tafe muna sha'anin mu irin na kuruciya, muna gab da shigowa ciki unguwa wata mota tayi parking a gaban mu, gaba daya muka ja da baya, saboda innata ta dade tana min gargadin idan naga mota na rika matsawa saboda masu satar yara, xuge glass din motar aka yi wani kyakkyawan dattijo ne ya leko da kansa, kallo daya xaka yi masa ka tabbatar da cewa kyakkyawa ne na ajin farko duk da ya fara manyanta hakan baxai hana ka fahimtar kyakkyawa bane, farin glass din da ke sanye a fuskarsa ne ya kara xayyana masa kyansa, sanye yake da farin voil wanda aka yi wa aiki da farin zare, kansa sanye yake da hula fara, babban mutum ne mai kamala duk inda ka kalle shi sau daya sai kayi marmarin sake kallonsa, saboda yadda Allah ya tsara masa halittar sa, cikin tattausar muryar sa ya kira mu, ku yaran nan ku xo, gaba daya muka fara ja da baya saboda mun tuna gargadin da iyayen mu suke mana, kwarjinin da yayi mana ne yasa muka kasa tafiya mu kyale shi, sake maimaita maganar da yayi a baya yayi, ku xo yara tambayar ku xan yi, daya daga cikin mu ce tayi karfin hali ta karasa inda yake cikin ladabi ta gaida shi, dagowa yayi tare da shafa kwantaccen farin gashin da ke kewaye a fuskarsa, kira min ragowar yan uwan naki xan tambaye ku gaba daya, da gudu ta karaso wajen mu, yace kuxo xai bamu sako ne, ba mu yi mata musu ba muka bita har wajen wannan mutum, murmushi yayi sannan ya fara yi mana magana, tsoro ku ke kada na gudu da ku ko, abinka da yara muka yi saurin amsa masa da eh. girgixa kai yayi to ku kwantar da hankalin ku ni ba irin wadanda ku ke zato bane, ke yarinya ya nuna ni da hannunsa ke nake son tambaya, hannu yasa ya dakko biron dake soke a jikin aljihun rigar sa sannan ya dakko takarda, tambayata ya fara yi ya sunanki gabana na dukan uku-uku na amsa masa da sunana Niimatullah, a wane unguwa kike, a nan bayan layi gidan mu yaje ba nisa daga nan, kafin na gama bashu amsa har hawaye ya cika idanuna, cikin damuwa ya dube ni, me yasa xa kiyi kuka Niimatullah, cikin kukan na bashi amsa, tsoro nake ji kada kaxo ka gudu da ni tsakar dare ni da innata, dariya na bashi sosai ki kwantar da hankalin ki ni ba haka nake ba, ku shige ku tafi gida kada a ga kun dade, wucewa muka yi kirjina na dukan uku-uku, ina shiga gida na fada jikin innata ina kuka, tambayata ta shiga yi me ya faru da ke yar lelen baba, cikin kuka nke bata labarin yadda muka yi da mutumin da muka hadu da shi, shiru innah tayi tana naxarin maganata, ki kwantar da hankalin ki Insha Allah alheri ne, tashu ki dauro alwalar magariba kinga lokacin sakkah ya gabato, tashi nayi na dauro alwala na dawo jikin innah na kwanta saboda fargaba ce fal a cikina.
*Jeeddahtulkhair😘*
[9/26, 6:08 PM] Itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*dedicated to Fatima sammani Alatu*
2
Sunana Ni'imatullah muhammad, iyayena yan asalin garin kano ne muna xaune ne a unguwar tarauni, ni kadai iyayena suka haifa, wannan dalilin yasa suke kaunata duk abinda nake so shi suke min matukar bai saba ka'idar shari'a ba, sai dai tafiya bata yi tsawo ba Allah yayi musu rasuwa sakamakon hadarin mota da ya ritsa da su,wannan dalilin yasa kulawata ta dawo hannun kakannina na wajen uba, suna ji da ni sosai saboda ni kadai ce jikar da suka mallaka kuma ni suke kallo a matsayin mahaifina, kasancewar babana shi kadai dan su a duniya. dangin mahaifiyata duk suna kauyen bichi idan an yi hutu nakan je musu xiyara.
ni yarinya ce kyakkyawa son kowa kin wanda ya rasa, Allah ya tsara min halitta ta dai-dai gwargwado idan ka ganni xaka iya cewa na fito ne daga salsalar buzaye ko larabawa. ni ba fara bace haka xalika baxa a saka ni a layin bakake ba, amma xa a iya kirana da (chocolate colour)idanuna manya ne kuma farare tas, hancina dogo ne wanda shi ne yake kara fito min da ainhin kyawuna, bakina kuwa dan karami ne, ga kuma dimple wanda yake kara bayyanar da asirtaccen kyauna, ni ba doguwa bace amma kuma baxa a saka ni a layin gajeru ba, xan iya kiran kaina da matsakaiciya, gashin kaina kamar auduga yake saboda santsi da laushi da ake da shi yasa bana yin kitso saboda ina yi yake warware wa, mutane da dama suna kirana da mai kyau, rayuwa mai dadi nake yi tare da kakannina sun hana ni kukan maraici babu abinda na nema na rasa a rayuwata.
Da gudu na fito daga bandaki ina kiran innah, a firgice ta fito daga dakinta tambayata ta shiga yi me ya same ki Niimatullah kuka nake ina nuna mata bandaki, kije ki gani innah na shiga uku, a raxane ta shiga bandakin ta fara lalube, ni ban ga komai ba Niimatullah, sake rushewa nayi da kuka ki duba pant dina ki gani innah, tana budewa taga ashe na fara jinin Al'ada ne, damuwa ce ta bayyana a fuskarta, bata so na fara da wuri ba saboda har yanzu ban gama mallakar hankalina ba, kwata-kwata shekaruna sha uku a duniya, gyara kayana ta shiga yi sannan ta jawo ni jikinta ta rungume ni, ni kuwa sai faman rusa ihu nake yi, lallabani ta shiga yi kiyi hakuri yar lelen baba haka Allah ya tsarawa kowace ya mace a rayuwarta, wannan ba wani abin damuwa bane ki kwantar da hankalin ki kin ji jikanyata, idona cike da hawaye na dubeta to yanxu yaushe xai tafi? shafa kaina tayi nan da sati daya ko kwana uku wata ma sai tayi kwana sha biyar bai tafi ba, xaro idona nayi kwana sha biyar fa kika ce innah, eh mana amma ya danganta da yanayin yadda Allah ya tsara miki, xai iya tafiya yau ma. bayan ta gama koya min yadda xan kula da kaina da jikina sannan ta yi min nasiha mai ratsa jiki, kinga yanxu kin xama cikakkiyar mace duk abinda yake kan tsohuwa yar shekara dari ya hau kanki don haka ki kula da ibada sannan ki daina guje-gujen da kike yi, kuma kada ki bar wani da namiji ya taba miki jiki ko da kuwa hannunki ne domin yana taba ki ciki xai iya shigar ki, saurin dagowa nayi na dubeta ciki fa kika ce innah, dama idan aka aurar da mace ba a ruwan randar gidan da aka kaita take sha ba? gyada kai innah tayi idan namiji ya taba hannunki ne kike daukan ciki don haka sai ki kula ki kiyaye. narai-narai nayi da ido xan yi kuka, ni dai ki bani magani nasha na daina yi innata, na karasa maganar tare da kwantar da kainaa jikinta, shafa bayana tayi kiyi hakuri Niimatullah xan yi miki addua xuwa gobe xai tafi, da murnata na dago na dubeta, da gaske xai tafi innah? xai tafi ke dai ki kwantar da hankalinki, da farin ciki na kwana a raina tun daga ranar kuma na kulke a rajna duk namijin da yayi min magana baxan sake kula shi ba.
*Jeeddahtulkhair😘*
[9/27, 3:04 PM] Itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*Jeeddahtulkhair)*
*dedicated to Niimatullah muhammad rafin dadi (miss rafin dadi)*
3
washe gari kuwa ko makaranta ban je ba, ina gida kan cinyar innah tana jinyata,da sallama Baba ya shigo dakin da muke hannun shi rike da ledar kayan miya mikawa innah yayi sannan ya samu guri ya xauna, sannu da xuwa inna tayi masa, har naxo yi masa magana na tuna da hudubar da innah tayi min a kan daina kula maza, juyo da kallonsa yayi gare ni, yar lelen baba ya na ganki kwance ko jikin ne ba dadi? shiru nayi masa sai da ya maimaita maganar kusan sau uku har sai da innah tayi min magana, baki ji abinda ake ce miki bane Niimatullah?.
turo baki nayi ina shusshura kafa, ba kince kada na kara yiwa namiji magana ba. kama baki innah tayi tana salati, to ai wannan kakanki ne baya cikin wadanda xaki 'ki yiwa magana kin ji ko? gyada kai nayi tare da gyara kwanciyata.
cike da mamaki baba ya dubeta, me ke faruwa ne naji kina mata wannan dogon bayanin? fuskar innah cike da damuwa ta bashi amsa, malam Niimatullahi ta fad'i, a raxane ya kalleta ta fad'i fa kika ce yaushe abin yaxo? jiya yaxo malam,ba karamar damuwa baba ya shiga ba da yaji abinda ya same ni, cikin damuwa yake magana, tunda ta fadi da wuri haka mu ma da wuri xamu aurar da ita tunda tana da saurin girma, ina ganin hankalin mu xai fi kwanciya.
tashi nayi daga kwanciyar da nake, aure fa kace baba tabdi ni dai wlh ba yanxu ba, kallona baba yayi yana min magana, to sannu babarmu tsayawa xa mu yi muna kallon ki ba aure, tunda kin girma me muke jira da ke? mikewa nayi ina duba kaina, ka ganni fa yar karama baba, Allah ban isa aure ba, haka muka rika muhawara da baba yana cewa na girma ni kuwa nace sam ba haka bane, tun daga lokacin nake ta tunanin ya xan yi idan aka aurar da ni yanxu ni da ko sanwa ban iya dorawa ba.
wata rana innah bata nan bayan na fito daga wanka na shiga dakinta, sanye nake da xani wanda nayi daurin kirji da shi, duba kaina na fara yi a mudubi naga yadda na fara xama cikakkiyar mace, kirjina har ya fara cika da dukiyar fulani, shape din jikina ma haka, komai yaji masha Allah ga kyawuna ya kara fita da yake makerin budurci ya fara tsara ni, murmushi nayi ina godewa Allah da kyawun surar da yayi min, lallai ban ga laifin su baba ba da suka ce xasu aurar da ni.
Bayan innah ta dawo daga unguwa na kwanta kan cinyarta ina mata shagwaba, nace a lallai sai tayi min tatsuniya ko ta bani labari mai dadi, ture ni nayi tana min fada, na gaji da wannan sa aikin naki Niimatullah ke kenan Kullum a cikin danne min tsohuwar cinyata, kallonta nayi ina murmushi yanxu idan ban danne ki ba wa xan danne innata? ke kadai fa kika rage min a rayuwata, tausayi na bata ta jawo ni ta kwantar da ni bisa cinyarta, haka ne Niimatullah kin fadi gaskiya.
Hirar mu muka cigaba da yi cikin nishadi, baba ne ya shigo hannunsa rike da carbi da butar alwala, kiran sunana yayi, Niimatullah tashi ki sanyo hijabin ki kin yi bako yana nan a soro yana jiran ki, da sauri na tashi xaune ina xare idanu, wane bako nayi baba, daure fuska yayi babu alamar wasa a tare da shi tashi ki kintsa idan kin je kya ga ko wane ne, jikina a salube na mike na shiga daki hijabi na sako sannan na sharbana silifas din innah xuciyata na tafasa na karasa soron.
dattijon da muka hadu jiya na gani, jingine yake da 'kyauran soron mu, yau ma sanye yake da fararen kaya wannan ya nuna min cewa shi ma'abocin son fararen kaya ne, saurin ja da baya nayi saboda ban taba xaton xai biyo ni gida ba, tambayarsa nayi, dama kaine bakon nawa me ka biyo ni gida kayi min? ina cikin maganar na tuna da alkawarin da na daukarwa kaina na daina yiwa maxa magana, a cikin xuciyata nace Allah na gode maka da ka tunasar da ni, ashe ban sani ba har maganar ta fito sarari.
tsare ni yayi da ido yana tambayata, me Allah ya tunasar da ke Niimatullah? sunkuyar da kaina nayi gaba daya na kasa dagowa saboda kwarjinin da yayi min, magana yake ta yi na kasa bashi amsa, har sai da ya gaji ya tambaye ni dalilin 'kin maganar da nake yi, idanuna a kasa na bashi amsa da innata ce ta hana ni magana da maxa, murmushi yayi tare da kad'a mukullin da ke hannunsa, lallai innar ki ta cika mai hikima, amma idan ta hana ki magana da maxa ai baxa ta hana ki magana da mijinki ba, a fusace na juyo na kalle shi mijina fa kace? Allah ya sauwake na aureka, dariya na bashi sosai. menene don kin aure ni Niimatullah shikenan kinga sai a rika kiran ki da *MATAR DATTIJO* tabe baki nayi ni ai matar yaro ce, kuma yaron ma sabon jini xan aura, shafa fuskar shi yayi tare da kallona.
A fuska nake dattijo amma a jiki nafi yaro kuruciya, baxa ki gane hakan ba har sai kin aure ni mun hadu a sunnah na fara baki soyayyar da baxa ki sameta a wajen yaro ba. shiru nayi na rabu da shi saboda bana son na rika yin doguwar magana da shi, naga alamar abinda yake so kenan, haka ya yi ta surutansa ya gama ba amsa, da ya tashi tafiya ya miko min ledar da yayi min shopping, da sauri na wuce gida na kyale shi da kayansa, sai yaro ya bawa ya shigo da shi gida, ina shiga na fada cinyar innah ina hawaye, tallafo fuskata tayi.
wa ya taba min ke niimatullah, share hawaye na shiga yi, innata wai wannan bakon da nayi sona yake yi ni gaskiya ya min tsufa Allah, rarrashina ta shiga yi, kada ki tada hankalin ki Niimatullah baxa mu aurar da ke ga wanda bakya so ba, sai kin xaba kin darje yar lelen mu.
kalaman innah su suka kwantar min da hankali nayi bacci mai dadi.
Alhaji Sadeeq Yusuf shahararren dan boko ne kuma tsohon minster na man fetur, ya rike mukamai da yawa wannan dalilin yasa ya tara dukiya mai yawa, gidansa a unguwar bompai yake titin durbin katsina, yayansa biyu ne duk maxa munir sai Hanif munir na da shekara talatin da biyar shi kuma Hanif na da shekara ashirin da biyar, tun daga kansu bai sake haihuwa ba, yana matukar son ganin kananan yara a gidan sa amma matarsa hajiya maryam ta dakatar da haihuwa kasancewar yar boko duk nacin da yayai akan kada ta dakatar da haihuwa taje tayi gaban kanta.
A hanyar xuwa islamiyya yaga Niimatullah, tunda ya ganta yaji ta kwanta masa a ransa kuma yayi niyyar mallakarta ko don ya gyara mata rayuwa.
*Jeeddahtulkhair😘*
[9/27, 3:04 PM] Itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
4
Ina cikin bacci naji wayar innata tayi ringing, a cikin baccin na rarrafa na dauka, bakuwar number na gani, da farko har naki dauka sai aka dame ni da kira na saka wayar a kunnena, sallama nayi cikin dasasshiyar murya, wata iska naji an hura min cikin kunnena wanda har sai da sautin ya tsirga min cikin jikina, cikin sassanyar murya aka amsa min sallamata tare da cewa na tashe ki kina baccin ki ko??
shiru nayi ba tare da na bada amsa ba, cikin raina nace lallai dattijon nan ya fiye nacin tsiya.
shirun da yaji nayi ne yasa ya cigaba da magana.
kiyi hakuri gimbiyar mata, nasan dama dole xan dame ki saboda tunda na ganki kika kwance min tunanina, yanxu haka na kasa bacci saboda tunanin ki, nasan baxan iya lafiyayyen bacci ba idan ban ji muryar ki ba.
cikin tsiwa nake masa magana, to kaji muryar tawa sai me? murmushi yayi wanda har sai da naji sautinsa a kunne na, Niimatullah sarkin tsiwa, kiyi hakuri ki rage wannan tsiwar taki, idan ba haka ba kuma na kamaki a dakin mu xa kiyi bayani ne. hararsa na rika yi kamar yana kallona Allah ya sauwake naje dakin dattijo, na fada maka ni matar yaro ce ehe.
dariya yayi wannan tsiwar taki ba karamin burge ni take yi ba Niimatullah, haushi ya bani na kashe wayar, shi kuwa sai juyi yake bisa gado duk ta tayar masa da wani sabon kwadayi, shaawarta da shaukinta sun mamaye shi a ranar da kyar ya iya bacci saboda tunanin Niimatullah har sai da yayi ciwon mara, kasancewar matarsa bata damu da kulawa da hakkinsa ba, burinta a Kullum bai wuce ta karbi kudi a hannunsa ba, wannan ne kawai amfaninsa a wajenta amma duk wani hakki nasa tasa kafa ta shure.
washe gari da safe nake fadawa innata yadda muka yi da shi, murmushi tayi tare da ce min ke yanxu wane hukunci kika yanke a kan son shi, bata fuska nayi ni Allah bana son shi innah, baki ga gemunsa ba duk furfura, dariya na bata har sai da ta kusa tuntsirewa, menene da farin gemun nasa Niimatullah, indai xa a samu xaman lafiya ai babu wani abu, ke dai kiyi addu'a Allah ya zaba abinda ya fi Alkhairi.
tashi nayi na fara shirin tafiya makaranta, naxo daukan jakata kenan wayar innah tayi ringing a hankali na mika hannu na dauka, number da ta kira ni jiya na gani, wurgi nayi da ita gefe guda, innata ce ta lura da abinda nayi cikin tausasa lafazi take min magana.
ya kika jefar min da waya Niimatullah? turo baki nayi wannan mayen ne ya kira ni, ni dai tun wuri kiyi masa magana ya daina kula ni, ba aure xan yi yanxu ba sai na kara girma. kallona innah tayi banda wannan girman da kika yi wane girma kuma xaki kara yi Niimatullah? tabe baki nayi ni dai ban girma ba innata abinda ko girki ban iya ba, ajiyar xuciya innah tayi, har yanxu yarinta na damun ki ni'ima Allah ya kara miki nutsuwa.
ba Ameen ba innah indai don a aura min wannan dattijon ne baxan taba hankali ba, naira goma ta bani sannan na dauki flask din abincina, a damuwa na kasance a makaranta domin kwakwalwata ta daina karbar komai saboda maganganun da aka bijiro min da su.
yau ma da yamma yaxo gidan mu har tsakar gida ya shigo don gaisawa da innah, tarar da ni yayi ina ta sharawa jikina ruwa duk na jika kayana, kallona ya shiga yi ya kasa dauke idonsa daga kaina, da dukkan alamu ina burge shi, magana innah tayi min Niimatullah baki ga bakonki ba, shiru nayi mata na cigaba da abinda nake yi. A soro tayi masa shimfida komawa yayi ya xauna yana jiran fitowa ta, wajena innah ta dawo tayi min magana, ban saurareta ba na cigaba da tsallena ina shara ruwa a kaina, duka ta kai min Allah yasa na kauce bata same ni ba, fada ta shiga yi min
wuce daki ki kintsa kin bar bawan Allah a tsaye, dukan kasa na rika yi da kafafuna, ni Allah ki kyale ni innata. lallaba ni ta rika yi har sai da na cire jikakkun kayan da ke jikina na sanya wasu na tafi wajen shi.
xaune na tarar da shi ya hada kai da gwiwa, yana dago manyan idanunsa ya kalle ni naga ya tafi wani xuxxurfan tunani, shauki da begen Niimatullah ya cika masa xuciyarsa a duk lokacin da yaga yarinyar wata jaraba ce ta musamman ke kama shi ya rasa dalilin da yasa yake shaawarta haka, tsayawa nayi a kansa tare da cewa gani, wani tattausan murmushi ya sakar min gami da kashe min manyan idanunsa, Niimatullah!! ya kira sunana da tattausar muryar sa, guri na samu na xauna raina a bace yake saboda irin kallon da yake min, tsare ni yayi da ido har sai da na tsargu na rasa me yake kallo a tare da ni, gyara xama nayi na sunkuyar da kaina kasa.
Yar amaryata naji ya kira ni, cikin tsiwa nake masa magana, kada ka sake ce min amaryarka ni ta mai rabo ce, murmushi yayi ai nine mai rabon, jira kawai nake baba ya dawo nan da sati daya nake son a yi mana aure, saboda hakurina ya fara karewa na kosa naji matata a kusa da ni, saurin xare ido nayi, a kusa da wa xaka xauna tabdi? murmushi yayi tare da bani amsa a kusa da ke mana, tsaki naji Allah ya kare ni daga auren *Dattijo* ragowar wata, ni sai yaro danye sharaf kamar ni, murmushi yayi xaki gane amfanin dattijo da dadinsa wajen ibadar aure ke dai kiyi fatan xuwan ranar da xan kasance da ke.
mikewa nayi na tafi gida saboda kaina baxai iya daukan maganganunsa ba, kirana ya shiga yi nayi banxa da shi na wuce gida, haka ya hakura ya kyale ni.
*Jeeddahtulkhair😘*[9/28, 8:53 AM] itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO* 💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam* *(Jeeddahtulkhair)*
*dedicated to maimuna Aminu othman (Ommy)*
5
A ranar duk kiran da yayi min ban dauka ba yayi min missed calls ya kai talatin, haka ya hakura ya har ya daina kiran. gari na wayewa naji tsayuwar motarsa a kofar gidan mu, tsaki naja wannan tsohon nacin sa yayi yawa kamar tsohon maye, me kuma yaxo yayi min da sassafe haka, sallama yayi da baba ya fita xuwa gare shi.
A dakin soro aka sauke shi magana naji suna yi kasa-kasa don bana fahimtar abinda suke tattaunawa, bayan sun kammala ya fito ya ja motarsa ya tafi.
cikin gida baba ya shigo tarar da ni yayi ina wanke-wanke, kirana yayi da sauri na tsame hannuna daga ruwan wanke-wanken, tsugunnawa nayi cikin ladabi, magana ya fara yi min.
Niimatullah ya kira sunana, cikin sassanyar murya na amsa masa da na'am baba, gyaran murya yayi sannan ya cigaba da magana, kinga yanxu kin fara girma ko yar lelen baba? daga kai nayi alamar eh, to ina so naga na aurar da ke saboda sauke nauyin amanar da na dauka a wajen iyayenki da kuma cika hakkin da musulunci ya dorawa kowane uba a kan dansa.
a xabure na dube shi, aurar dani fa kace baba ka ganni fa yar mitsitsiya har yanxu ban girma ba, ni dai ba yanxu ba Allah. nasan har yanxu ke karama ce yar lele amma ai girma ya fara kama ki, don haka xan aurar da ke yanxu, amma baxa ki tare a dakin mijinki ba sai kin kara hankali da wayo, ina so na baki kariya ne daga fitintunun xamani da matasa ke afkawa sanadiyyar rashin samun abokin rayuwa, don haka xan aurar da ke ga Alhaji Sadeeq fatana dai ki xama mai biyayya a gare ni.
kuka ne yaxo min, hawaye duk ya cika idanuna baxan iya ketare umarnin baba ba saboda kulawar da ya bani a rayuwata ban san kowa ba sai shi da innah, cikin kuka na amsa masa da xan yi biyayya a gare ka baba.
cikin kulawa yace min,na gode Niimatullah Allah yayi miki albarka, amma idan bakya son wannan mutumin kiyi min magana saboda na yi wa kaina alkawarin baxan taba yi miki auren dole ba, girgixa kaina nayi bana 'kinsa baba ina son shi, kawai auren ne bana so gaba daya. murmushi baba yayi
ki daina cewa bakya son aure Niimatullah aure sunnar Annabi ne don haka daga yau kisa a ranki ke matar aure ce, mikewa nayi na shiga daki wayar innah na dauka na kira Dattijon da ke sona cikin kuka nake masa magana.
me yasa kake son raba ni da gidan da tunda na taso nake a cikin sa, na saba da baba da innata baxan iya tafiya na bar su ba, rarrashina ya rika yi.
duk mace matar wani gidan ce Niimatullah ki kwantar da hankalin ki ko da an daura mana aure baxan tafi dake gidana ba, xan barki a wajen su innah har sai kin kara wayo kin bukaci mijinki da kanki, wani dadi ne ya mamaye min xuciyata, ban san lokacin da nayi wani ihu ba nace yauwa naji dadi, kasan wani abu kuwa??
da sauri ya amsa min da a'a, ko girki fa ban iya ba, innata bata bari nayi girki saboda bata so na kone, kuma kaga ai ba a aure sai an iya girki ko? amma dai na iya shara da wanke-wanke.
shirmen da Niimatullah ke yi ba karamin faranta masa rai yake ba, ko yana cikin damuwa idan ya saurari muryarta sai yaji dadi ya kama shi, murmushi yayi tare da cewa.
kada ki damu sai kin iya komai xan kawo ki gidana kin ji ko yar yarinyata?
murna na rika yi xa a koya min komai, ranar cikin farin ciki muka rika waya ya tsokane ni na tsokane shi, Kullum yaxo hira sai ya taho min da kayan kwalliya da na gyaran jiki.
da kwalayen biscuit da goro naga ana ta shigo da shi cikin gidan mu, tambayar innata nayi ko na menene, cikin kulawa ta bani amsa.
na daurin auren ki ne Niimatullah, murna na shiga yi har da danne innah ina mata tsalle a ka. Alhamdulillah na kusa xama matar aure nima na fara samun lada, naji ance komai na matar aure ya fi na mara aure lada wai haka ne innata?. murmushi innah tayi kwarai kuwa, ke dai kin yi sa'a tun kina yar karama xaki fara samun ladan aure, murna muka rika yi ni da innah.
da misalin karfe biyu na rana aka daura min aure da Dattijo, ko a ranar ma sai da naje islamiyya, yan ajin mu sai mamaki suke yi wai ina da aure naje makaranta, ni kuwa ko a jikina don ban gama sanin ciwon kaina ba, yan manyan aji sai xuwa suke suna kallona, wasu su ce nayi kankanta da aure wasu su ce iyayena sun yi dai-dai, kowa dai da irin abinda yake fada.
ina komawa gida na tarar da shi har yaxo, tsintar kaina nayi ina jin kunyar sa, yau a dakin innata aka sauke shi ita kuma innar tamu ta koma tsakar gida ta xauna.
09077389712 yawan comments yawan typing
*Jeeddahtulkhair😘*
[9/28, 10:12 AM] Writer: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO* 💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam* *(Jeeddahtulkhair)*
*dedicated to Aysha sabo Abdullahi*
6
Da sallama na shiga dakin tarar da shi nayi xaune ya tsurawa kofar da nake shigowa ido, ina tafe ina tuntube saboda jarababben kallon da ya takura min da shi.
har kasa na tsugunnah na gaida shi, cikin sakin fuska ya amsa min, gefe na samu na xauna, matsowa yayi daf da ni, ya dan riko hannuna saurin janye hannun nayi tare da matsawa gefe, cikin rashin kunya nake masa magana.
"me yasa xaka taba ni sai ka janyo min nayi cikin shege" saurin toshe min baki yayi, ni mijinki ne idan na taba ki ba komai, kuma wai wa ma ya gaya miki idan na taba miki hannu xaki samu ciki? turo baki nayi, innata ce tace kada na bari wani namiji ya taba min hannuna ana yin ciki.
murmushi yayi tare da cewa wannan shirmen naki yana burge ni Niimatullah, harararshi nayi nice ma nake yin shirmen ko? tashi nayi xan bar dakin kamo ni yayi ya xaunar da ni yana sumbatata.
kwala ihu nayi ka sake ni sai ka janyo nayi cikin shege ko? kafe ni yayi da manyan idanunsa, kada na sake jin kalmar nan a bakin ki indai ni ne xan miki ciki, to ba shege bane da uban sa kuma nine uban nasa, don haka kada na sake jin kin ambaci shege a nan.
gyada kaina nayi alamar eh, sake matsawa nayi daga gare shi, cikin shagwaba da narkar da murya yake magana.
me yasa kike guduna *MATAR DATTIJO* ko har yanxu babu soyayyata a ranki, a'a nace masa a takaice.
Bayan mun gama gaisawa ya miko min wrippers na dari biyu, karbi wannan ki siya duk abinda kike bukata, makale kafada nayi cikin shagwaba nace ka barshi ba abinda nake bukata komai innah da baba suna yi min, ajiye min yayi tare da cewa yanxu nauyin ki ya bar kan baba ya koma kaina don haka ya xama wajibi a gareki ki karba.
fita yayi ya bar dakin ni kuma na bishi a baya, har kasa ya tsugunna ya yiwa innah sallama sannan ya tafi.
jingina kaina nayi kan gwiwar innah ina mata magana
innata haka kawai sai wannan Dattijo ya rike min hannu, Allah yasa dai ba nida ciki, bina tayi da kallo ta rasa bakin magana, mikewa nayi ina duba cikina duba min innah ko na samu ciki har sai da guntun hawaye ya fito min.
ganin na tayar da hankalina ne yasa ta bani amsa wannan mijinki ne ko ya taba ki ba komai, wani namijin ne daban aka hana ya taba ki kin ji ko?
to nace amma xuciyata bata gama amincewa da amsar da ta bani ba, ko da naje islamiyya sai da na tambayi kawata ita ma irin amsar innah ta bani, kasancewar ta fini wayo da shekaru.
A kan hanya wata mota ta Parker a gaban mu wasu fararen mata ne guda biyu suka fito daga cikin motar, shan gaban mu suka yi tare da cewa wacece Niimatullah??
jikina na 6ari na amsa da gani nan, jawo ni daya daga cikin matan tayi ta shiga duba ni sama da kasa, daga karshe ta bushe da wata dariya, dayar ce tayi magana.
Tabdi Gaskiya dadyn munir ya raina miki hankali, ya rasa wacce xai auro miki a matsayin kishiya sai wannan kwailar kaxama da ita, dubeta fa ko nonon arxiki ba tada shi, sake bushewa da dariya suka yi suka tafa, dayar ce ta tabe baki tace.
nima dai haka na gani me xai yi da wannan yar tayin yarinyar, ga ta da gani ko tsaftar arxiki bata isheta ba, amma dai tana da kyau ba laifi.
Haka suka gama ci min fuska tsaf sannan suka sake ni suka shige mota suka tafi, kuka na fara yi abokan tafiyata sai tambayata suke a ina na samo wadannan marasa mutuncin matan, kasa basu amsa nayi saboda nima ban san su ba ban taba ganin kalar su ba.
ina xuwa gida na fadawa innata abinda matan suka yi min, fargaba ce ta kama innah saboda tasan babu mai yin wannan aikin idan ba matar Alhaji sadeeq ba, rarrashina ta shiga yi.
kiyi hakuri Niimatullah kada kisa damuwa a ranki, Insha Allah sai kin xamewa matar nan dan hakin da ka raina.
*Jeeddahtulkhair😘*
[9/30, 4:44 PM] itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Hafxiyya Nasidi*
*ina godiya masoya littafin Matar dattijo, tun daga kan masu kirana a waya da masu biyo ni private ina matukar godiya ALLAH ya bar xumunci*
7
Gaba daya naji auren ya bar kaina saboda cin mutuncin da matar nan tayi min, sai na gwammace xamana ba auren na hakura da samun ladan da ake samu kukana nake tayi inna na rarrashina.
yana kirana a waya na fara yi masa kuka, rarrashin duniya yayi min amma naki yin shiru, cikin kulawa yake min magana, fada min damuwar ki Niimatullah, cikin shashshekar kuka nace ni dai na fasa auren nan ka sake ni na huta.
A firgice yace min me kika ce Niimatullah lafiyar ki kalau kuwa, kike wannan maganar? ta cikin wayar naji an daka masa tsawa, kayi asara tsohon banxa ka rasa wacce xaka auro sai kaxamar yarinya yar cikinka.
muryarsa na karkarwa naji ya ajiye wayar, daga lokacin bai sake kirana ba har sai da muka yi kwana daya a haka, sabo turken wawa kwana biyun nan da ban ji muryarsa ba har na shiga damuwa, ko makaranta na kasa xuwa ban tabbatar da irin kaunar da nake masa sai a yanxu da yayi nisa da ni.
A ranar da xamu cika kwana biyu yaxo gidan mu, kansa na gani daure da bandage, a hankali yake takawa da dukkan alamu yaji jiki, tausayinsa ne ya kama ni, da sauri na karasa wajensa ina tambayarsa dattijona, a hankali ya dago ido ya kalle ni, sake tambayarsa nayi me ya taba min lafiyarka haka? dago ido yayi tare da yi min murmushi, accident nayi jiya, sannu muka rika yi masa ni da innah, sannan na shimfida masa tabarma a daki.
shagwaba na fara yi masa ina kuka, shi ne ka tafi ka manta da ni ko, ka kashe wayarka baka neme ni ba.
Hakuri ya fara bani, ki saki ranki nayi miki bayani sannan ki daina wannan kukan kada ya taba min lafiyar ki, jiya mai mota ya ture ni ya take wayar da ke hannuna shi yasa ban kira ki ba. ban gamsu da kalamansa ba don haka na sake jefa masa wata tambayar da ta firgita shi.
to naji Allah ya kiyaye gaba, amma wacece wacce naji tana xagina tana xaginka? dabarbarcewa yayi anya kuwa, ni babu wanda ya xage ni ko ya xage ki, ina ganin matsalar network ne kin san wani lokacin yana hadewa.
girgixa kaina nayi sam ban yarda ba, gashi nan naji tana ce min kaxama, ni Allah na fasa auren baxan je a rika xagina ba, duk wankan nan da nake yi sau biyu a rana wata ta rika kirana da kaxama, rausayar da kansa yayi gefe yana ta kallona ina fada har da shure-shuren kafa, kiran sunana yayi cikin sassanyar murya da alama yana cikin damuwa
ki kwantar da hankalin ki Niimatullah idan kin tashi tarewa gidan ki daban xan miki, gyara xama nayi ina kallonsa.
gidana daban fa kace ni dai Gaskiya ban yarda ba, gara ka saka ni a gidan da mutane suke, kasan ni akwai tsoro, murmushi yayi tare da cewa, Allah sarki wato shi yaro ala kulli halin yaro ne.
jawo ni jikinsa yayi na rika kokarin sai na kwace na matsa gefe amma na kasa, rada ya shiga yi min a kunne na, Niimatullah!!cikin sauri na amsa masa saboda na kosa ya sake ni, cikin raunananniyar murya yake min magana.
xaki taimaki mijinki?? da sauri na dago ina ware idanu, wane irin taimako kuma, dama ana taimakon dattijo kamarka? saurin rufe bakina yayi, daga yau na hana ki fadar dattijon nan, ki rika kirana da babynki. xaro idanu nayi kaine babyn nawa?? kafe ni yayi da ido eh mana wata rana har wanka da tsarki sai kin yi min, xa kiga rigima kala-kala a dakin mu.
tabe baki nayi Allah ya sauwake nayi maka wanka tabdi, cigaba da kokarin guduwa nayi shi kuwa ya rike ni gam, yaki sakina kuka na fara yi masa ka sake ni ko nayi maka ihu na kira innata.
tsare ni yayi da kallo kira innar mana ai kowa ya shaida ke matata ce, ko ta ganni babu abinda xata ce.
bata fuska nayi xan yi kuka ni fa Allah ka sake ni, sake riko ni yayi tare da kallon fuskata.
ina jin wani abu a raina idan naga kin turo min wannan kyakkyawan bakin naki, sai naji kamar na shanye su, xaro idanu nayi ka shanye fa kace Allah ya sauwake maka, ka cika ni na tafi fitsari nake ji, ki tsaya mana na fada miki irin taimakon da xaki yi min.
sunkuyar da kaina nayi kasa, ina jinka fada min dan Allah na gaji.
yan uwa a yi hakuri da typing kadan matsalar ba daga ni take ba, wayaa ce mai matsala idan nayi da yawa sai tayi deleting typing din gaba daya
*Jeeddahtulkhair😘*
[9/30, 4:45 PM] itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Aysha sani sagir*
8
kashe min idanu yayi tare da cewa, tausa nake so ki yi min yar amaryata, to cika ni xan yi maka, mike kafafun shi yayi yana cika ni na fita da gudu sai wajen innah a soro na sameta tana kadin lagwani, yadda ta ganni a guje yasa ta tsayar da abinda take yi, tambayata ta fara yi.
lafiya na ganki haka Niimatullah? kuka na fara yi mata, wallahi innah baxan sake xuwa wajen wannan mutumin ba Kullum naje sai..........kafin na karasa innah ta toshe bakina
kul na sake jin kin fadi sirrin mijinki, dukan kasa na rika yi da kafata ki daina cewa mijina, ni wallahi na fasa tunda abinda xai rika min kenan. A dai-dai lokacin da nake fada mata ya fito daga dakin ya same ni a soro, duk kunya ta kama shi, kansa a sunkuye ya yiwa innah sallama.
Har ya kai bakin kofa na sake cewa innah kiyi masa fada ya daina yi min........ xan karasa kenan ta daki bakina me yasa bakya jin magana ne Niimatullah, ba nace miki ki daina fada min ba,shi kuwa gogan naku don kunya kamar ya nutse a kasa, magana innah ta fara yi masa.
kayi hakuri Alhaji har yanxu Niimatullah yarinya ce sai a hankali xata saba, kansa a kasa ya amsa mata da ba komai innah, shi yasa dama na dakatar da tarewar sai ta dada wayo. sallama yayi mata ya tafi.
yana tafiya na dubi innah, innata wai dame xan saba, naji kin fada masa kin ce ban saba ba? murmushi tayi da cin shinkafa mana, da ba likita yace ki rage cinta ba saboda basir? gyada kai nayi alamar eh, bayani ta cigaba da yi min
to shi kuma mijinki yana so ki rika ci shi yasa nace a hankali xaki saba, girgixa kaina nayi, au na gane innata.
karbar lagwanin nayi na fara tayata kadawa muna yi ina mata mitar dokar min bakin da tayi, hakuri ta rika bani saboda tasan rigimata xan iya kwana ina mata kuka.
shi kuwa Alhaji Sadeeq na komawa gida matarsa ta saka masa bala'i, kadan ka gani daga irin abinda nayi maka, saura ita kucakar yarinyar da ka auro, muddin ta shigo gidan nan xaman lafiyarka ya kare, daka mata tsawa yayi.
ki saurara na gaji da cin kashin da kike min, kin hanani hakkina kuma kin hana ni aure,so kike yi na lalace, na fara bin matan banxa? ki sani aure an riga da an daura shi sai dai ki rungumi kaddara.
bushewa tayi dariya, wannan kwailar da ka dakko yar cikinka, ni baxa ta daga min hankali ba, yar shara da wanke-wankena xan mayar da ita sai me? kallon raini yake mata wannan yarinyar da kike gani ta fiki komai da komai, duk da cewa kin fita ilimi kin fita shekaru da wayewar rayuwa, amma kuma ta miki wayo domin ta fiki iya tarairayar miji, don haka kin ga nan gaba xata xame miki kadangaren bakin tulu.
shigewa daki yayi ya barta tana balbala masifa, yana shiga ya dauki waya ya dannawa Niimatullah kira.
sai da wayar ta dade tana ringing ina kallonta ban dauka ba, ya kira wajen sau uku innah ce ta dauki wayar da kanta ta manna min ita a kunnena.
Hello nace sannan ya fara magana, yau kin kunyata ni a gaban innah, Niimatullah ni fa mijinki ne duk abinda nayi miki babu haramci, turo baki nayi.
ni ina ruwana ko yanxu ka kara yi min abinda bana so sai na fadawa innata, haka kawai ina xaune lafiya xaka jawo min abin kunya nayi ciki.
murmushi yayi, har yanxu dai baxa ki daina wannan maganar ba ko Niimatullah, babu wani abin kunya da xa kiyi duk abinda ya faru tsakanin mu halal ne a musulunci.
sauke ajiyar xuciya nayi to ni na haramta ehe, dariya yayi xaki ga kin haramta idan kika shigo hannuna, baxan ma shigo ba gara ma ka sani.
kukan shagwaba ya shiga yi min a wayar wai naxo na taimaka masa, na kasa bawa kaina amsar irin taimakon da yake nufin nayi masa, don haka na kashe wayar gaba daya na kyale shi.
*Jeeddahtulkhair😘*
[9/30, 4:46 PM] itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Zahra musa*
9
kwanan shi biyu bai xo gidan mu ba saboda kunya sai dai mu yi magana da shi ta waya, amma duk abubuwan da nake bukata yana aiko yaron shi ya kawo min, a wasu lokutan ma innah ke dakatar da shi saboda hidimar tayi yawa.
A lokacin da aka yi mana hutun makaranta yaxo gidan mu, a soro ya tsaya ya aiko yaro ya kira ni, saboda har yanxu yana jin nauyin hada ido da innah saboda tonon asirin da nayi masa.
cikin nutsuwa yaron ya shigo tare da sallama, gaba daya muka amsa masa mayar da hankalin mu muka yi gare shi, muna sauraron abinda xai fada mana, a ladabce yake mana magana.
wani dattijo ne yace yana sallama da Niimatullah, inna ce ta dauki mayafi ta fita, yana ganinta ya xube a kasa yana gaidata, cikin sakin fuska take masa magana. me yasa ka tsaya a nan Alhaji? ka shigo ciki Niimatullah din tana nan. sunkuyar da kansa yayi, nan ma ya isa innah ai ba dadewa xan yi ba, takura masa ta shiga yi, a'a Alhaji baxa a yi haka ba, kwala min kira tayi da sauri naxo wajen, kallon shi nayi ba tare da na gaida shi ba, innah ce ta dube ni karbi kayan da ke hannunsa mana, cikin ladabi na karbi kayan.
biyo ni yayi a baya har muka shiga daki, ajiye kayan nayi a gabansa xan fita, cikin marairacewa ya kira sunana, Niimatullah ina xuwa? a hankali na juyo na bashi amsa wajen innata xan koma, cikin rarrashi yake min magana haba babyna ina xaki tafi ki bar marayanki wanda bai san komai ba sai soyayyar ki domin na ganki fa naxo gidan nan.
turo baki nayi ni baxan dawo ba, salon naxo ka rika dankoni kamar wata yar tsana, cikin sigar tsokana ya bani amsa ai yar tsanar ce, mikewa yayi yana shirin kamo ni da gudu na fita wajen innah ina haki, ina xuwa na xube a kasa ina kuka, ni Allah innah na gaji da halin mutumin nan Kullum ba shi da aiki sai son ya kamoni, ni wlh na gaji innah.
shiru tayi tana kallona ta kasa bani amsa sai jinjina kai kawai take yi, da yaji shiru ba nida niyyar dawowa ne yasa ya fito yaxo wajen mu, ajiye ledar kayan yayi a gaban innah godiya ta shiga yi masa bisa ga dawainiyar da yake yi mana, cike da girmamawa yake wa innah magana ai wajibina ne na kula da ku.
ni kuwa sai hararasa nake yi a raina ina cewa dube shi sai kace mutumin arxiki, kansa a sunkuye yake wa innah magana.
innata dan Allah idan babu damuwa ina neman wata alfarma a wajen ku, hankalinta ta bashi sannan tace, ina saurarenka Alhaji ai babu abinda xaka nema bamu yi maka ba indai muna da hali, yaji dadin abinda innah ta fada masa don haka ya saki ransa ya fara yi mata bayani.
dama so nake ku bani aron Niimatullah xa tayi min rakiya Abuja, na nemi matata ta raka ni to abubuwa sun mata yawa, ni kuma bana so nayi tafiya ni kadai, gabana ne ya fadi nan da nan na fara kuka.
ni wlh baxan bishi ba innah tabdi, duka ta kai min, me yasa kike haka ne Niimatullah ansa da ke ne da xaki sa mana baki, Alhaji dai mijinki ne tunda ya bukaci ya tafi da ke ba mu da ikon hana shi, ke ma kuma dole kiyi biyayya ga mijinki. kallon shi rayi, bari na yiwa malam magana nasan shi ma baxai hana ba.
tashi tayi ta shiga dakin baba ta sanar da shi yadda suka yi da mijina, gaba daya suka taho inda muke, fada suka rika yi min sosai, dukan su bada damar na bi shi, ina kuka suka dakko kayana kala uku suka xuba min a leda, cikin kulawa yake wa su innah magana a mayar da kayan nata xan siya mata wasu a hanya.
kuka nake kamar raina xai fiti ta bakina, har bakin mota su innah suka rako ni ina ta xabga ihu. bayan mun tafi suka koma cikin gida innah ce ta dubi baba.
malam ni fa ina fargabar tafiyar yarinyar nan kada taje ta samu rabo saboda alamu sun nuna wannan mutumin yana da bukata da yawa, kada ciki ya fito kafin aje ko'ina, ajiyar xuciya baba yayi nima dai haka nake tunani hankalina xai fi kwanciya idan aka yi bikin nan ko menene ma yayi a dakin matarsa, amma ni baxan ji dadi ya rika xuwa yana daukar mana yarinya ba yana yawo da ita a gari kawai don an daura musu aure.
Har muka kusa xuwa inda xamu je na kasa yin shiru ashe ba wani Abuja da xan raka shi karya ya shararawa su innah.
A yi hakuri da wannan wlh ba nida lafiya yanxu ma karfin hali nayi na baku wannnan don kada ku ji shiru
*Jeeddahtulkhair😘*
[10/1, 12:42 PM] Itz B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*معذرة🤦🏼♀*
*masu yi min magana ta private su ga kamar wulakanci ne yasa bana son amsawa wlh matsalar network ne maganarku na shigowa amma tawa bata tafiya dan Allah a yi min afuwa ina kaunar ku kamar yadda kuke kaunata*
10
Bakin wani hotel muka Parker leko da kanshi yayi inda na sunkuyar da kaina, to mun xo amaryata sai ki tashi mu shiga, cikin tsiwa nace wlh ba inda xan je har sai ka mayar da ni inda ka dakko ni idan ba haka ba kuma sai dai mu kwana a nan, murmushi yayi tare da kanne ido daya, menene idan mun kwana a nan ni tayi min dai-dai kinga sai nayi abinda naga dama da matata babu mai sa min ido.
Hararar shi na shiga yi, to yi din wallahi xaka janyo a fasa auren nan kowa ya huta, murmushi yayi min auren nan fa a hannuna yake amma kullum sai ki rika cewa a fasa, to ni baxan taba sakin ki ba mutuwa ce xata raba mu, yana gama fada min ya bude motar ya fito, leko da kan shi yayi ta window ki fito idan ba haka ba kuma na dauke ki cak na kai ki inda xamu je.
Harararshi na tsaya yi gami da jujjuya idanuna, bismillah dauke ni din idan tsayawa xan yi ina kallonka, dariya yayi min wai me yasa bakinki baya mutuwa ne Niimatullah gaki yar mitsitsiya sai tsiwar tsiya da rashin ta ido, tunda kika ce min bismillah xaki ga aikin bismillah, bude murfin motar yayi daukana yayi can cak,da kafarsa ya mayar da murfin motar ya rufe, kokawar kwatar kaina na fara yi, amma na kasa, sai da ya kaini har cikin dakin da xamu sauka, sannan ya ajiye ni kuka na rika yi masa ina magiyar ya mayar da ni gida.
kumatuna ya rike yana min murmushi yau ina tsiwar taki Niimatullah? cikin kuka nace masa na daina baxan kara yi maka ba kayi hakuri, rungumo ni yayi ya hada ni da kirjinsa kin tabbatar da cewa baxa ki sake yi min rashin kunya ba kuma baxa ki sake yi min tonon asiri ba? da sauri na daga kai nace masa eh, murmushi yayi tare da cewa yau ba a turo min da dan bakin nan ba ko don ba a gidan innah ake ba? shiru nayi masa cikin shagwaba nace masa ina jin kishiruwa.
kallona yayi ya tsare ni da ido ba daxu na baki ruwa kika sha ba, wannan ba na bayarwa bane idan kuma kika sha min sai kin biya ni, da sauri nace eh bani na sha idan naje gida xan debo maka wani a randar innah.
dariya yayi min wa ya gaya miki irin wannan biyan xaki min da jikinki xaki biya ni saurin dafe kirjina nayi, dama ana iya biyan ruwa da jiki? murmushi yayi tare da cewa kwarai kuwa idan kuma baki yarda ba gashi kisha.
girgixa kaina nayi ka barshi ni bana so Allah, shafa fuskata yayi, yi hakuri babyna ai baxan iya hana ki kisha ruwana ba, ko don alfarmar yayana da ke jikinki, saurin xare idanu nayi wane yayan naka kuma? nan da nan na mike tsaye ina duba kaina, wayyo na shiga uku me xan je gida na fadawa innata, dama ta dade da fada min indai na bari aka taba ni xan iya samun ciki, watakila ma cikin yan biyar ne dani tunda kusan sau biyar kana taba ni.
Hankalina ya tashi sosai sai ihu nake shi kuwa yana gefe yana tuntsura min dariya, sai da nayi kukana na koshi sannan ya kira sunana cikin salon soyayya, Niimatullah a hankali na dago jajayen idanuna da suka sha kuka na dube shi, ki daina damuwa yanxu ba ki da komai a cikin ki sai nan gaba xaki samu ciki ki haifo min yaya kyawawa kamar ki, kin ji ko yar yarinya ta. cikin kuka nace masa to naji tashi mu tafi gida kada innata taga na dade, dagowa yayi daga kwanciyar da yayi, mu tashi mu tafi fa kika ce? baki ga har kwanciya nayi ba to ina nufin tafiya ba yanxu ba har sai na koya miki hankali kin daina wannan surutun da kike yi, sai mun kwana daya a nan, da sauri na dago na kalle shi kayi hajuri nayi hankali wlh baxan sake gayawa inna ba, murmushi yayi naji kin yi hankali amma ni kudin kwana daya na biya mana baxan tafi ba sai na ci kudina don baxan yi asara ba, yana gama fada ya mayar da kansa gefe
kuka na fara yi Allah baxan kwana a wajen nan ba sai na tafi gida, bakin kofa na nufa na fara jijjiga kofar ina kokarin budewa amma na kasa saboda key din na aljihunsa, dawowa nayi na fara yi masa magiya, dan Allah kaxo ka bude min kaga magariba ta kusa.
lumshe idanunsa yayi ya dube ni, idan kina so na mayar da ke gida sai kin taimaka min, da sauri na karasa wajensa fada min taimakon da kake so nayi maka, xaune ya tashi ya dube ni, xo na fada miki a kunnenki, makale kafada nayi Allah a'a sai dai ka fada min a nan ina jin ka, murmushi yayi, me yasa kike jin tsorona haka Niimatullah alhalin ni ba dodo bane, bata fuska nayi to ai har gara dodon dama nasan dodo ne amma kai ka rika kama ni kuma bayan kasan haramun ne, murmushi yayi wato bakin ki baxai yi laushi ba ko, to sai gobe xaki tafi gida, kuka na fara yi har sai da nayi ya ishe ni sannan ya fada min irin taimakon da xan masa, tausa xaki yi min, amma da sharadi baxa ki ce min kin gaji ba, idan kika ce kin gaji sai kin kwana kina yi, da kyar naja kafa naxo kusa da shi na fara yi masa tausar, xuciyata cike da tsoron kada ya kamo ni, bayan na gama masa ya tashi ya shiga wanka yana fitowa muka hau mota ga mayar da ni gida.
09077389712
*jeeddahtulkhair?*??????????
*MATAR DATTIJO*
??????????
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*Don Allah don Annabi masu hade min pages 2 ya xama daya dan Allah ku daina bana so, gaskiya idan na kara cin karo da irin wannan xan dakata da typing*
11
Ina shiga gida naji wani bakin ciki ya tokare ni a makogoro, tambayar kaina na shiga yi me yasa har na amince da auren wannan dattijon gashi nan yana kokarin shigar min rayuwa, muna daf da shiga cikin gidan ya kira sunana.
Niimatullah!!! a sanyaye na waiga na dube shi, matsowa yayi daf da ni har ina jin kamshin turarensa, dafa kaina yayi tare da dago fuskata saura kuma mu shiga cikin gida kiyi min tonon asiri don nasan ki akwai surutu a wasu lokutan, kina yi xan dawo gobe na tafi da ke kin san dai innah da baba baxa su hana ki bini ba, shiru nayi masa saboda haushi yake bani yanxu.
muna shiga innah ta tarbe mu da murnarta,ya naga har kun dawo da wuri haka Alhaji, sunkuyar da kansa yayi tare da shafa fuskarsa, tafiyar tamu ce bata samu ba innah, cikin jimami innah ta bashi amsa, ayyah ai dama komai sai Allah ya nufa, hira suka fara yi ni kuwa sai kallon fuskarsa nake yi muna hada ido da shi sai nace na fada??
yana ji na fadi haka sai ya sunkuyar da ido kasa saboda kunya, sake maimaita masa maganar na rika yi, na fadawa innata inda muka je da abinda nayi maka? da hanxari innah ta dube ni, wai ke wace irin yarinya ce Niimatullah idan kika sake magana sai na hada miki kayan ki kin bishi, kuka na fara yi haba innata gidan wannan mutumin xaki kaini Kullum fa sai ya matse ni kamar wata yar tsana, duka ta kai min ke dai baxa ki daina halin ki ba ko, dole ma a tattara ki a kai ki gidan miji ko kya yi hankali a can bari malam yaxo na fada masa tunda abinda kike yi kenan, idan kika koma can kika tare sai ki bada labarin gidan mijin da hujja, kuka na fara yi ina mata magiya tayi hakuri, shi kuwa dattijo kamar ya nutse saboda kunya ya rasa bakin magana, basu gama hirar ba ya tattara kayansa ya tafi, inna ce ta dube ni baxa ki tashi kiyi masa rakiya ba ko, cikin shagwaba nace yasan hanya fa innah, maficin da ke hannunta ta kwado min, idan ina magana kina min musu sai mun fara fada da ke a gidan nan, ina tafe ina turo baki na bishi soro, tsayawa yayi yana kallona domin ya rasa bakin yi min magana.
gajiya nayi da tsayuwa na dube shi, ni xan tafi gida don na gaji da wannan tsayuwar da nake yi, lumshe idanunsa yayi tare da cewa lallai ina da aiki har yanxu akwai haukan kuruciya a kan matata, tsugunnawa yayi har kasa yana rokona, dan Allah ki daina yi min irin wannan abubuwan da kike fada a gaban innah ina jin kunya na rasa ina xan sa kaina, me yasa kike haka Niimatullah ba fa a kanki aka fara aure da wuri ba, iyayenmu da kakannin mu duk kusan irin wannan auren aka yi musu, kuma akwai yara kanana da ake aurarwa a kai su gidan maxajensu kuma su basu hakkkinsu babu mai ji, amma ke daga na taba hannun ki sai ki rika yawo da ni kina kunyata ni.
Hararar shi nayi ni ba ruwana da su kaina na sani tunda innata tayi min karatun kada na bari wani ya taba ni baxan xubar da wannan karatun ba, kuma ko yau ka kuma yi min, sai na fada a gida idan baka gaji da taba ni ba nima baxan gaji da baka kunya ba.
Haushi na bashi don haka ya fara magana, tunda abin naki haka ne baxa ki daina ba ko, to nan da sati xaki tare a gidana ki fara taka irin rawar da sauran matan aure ke takawa a gidan maxajen su, sunkuyar da kaina nayi ina sauraren sa, kafin na ankare ya rungumo ni ya hada fuskata da tasa idanunsa naga ya canja ya rika aika min da sakonnin soyayya kala-kala, sai da ya dawo cikin nutsuwarsa ya dube ni
tonon sililin da kike min ne yasa nayi miki haka yanxu ma idan kin koma gida ki sake fadawa inna xaki ga yadda xamu kwashe ni da ke, yana gama fada min ya wuce ya tafi, jikina a sanyaye na shiga gida, duk maganar da nayi wa inna bata amsa min ba, jikina ba karfi na karasa wajenta, kawar da kanta gefe guda tayi tare da juya min baya, cikin sassanyar murya na dora hannuna a kan cinyarta ina mata magana, me yasa xaki juya min baya innata ki daina kulani ni fa ba wani laifi nayi masa ba ko da muka je can din tausa yace nayi masa kuma nayi.
A hankali ta dube ni wannan rashin sirrin naki shi yake hada ni da ke, a ce baxa ki rika rike sirrrin mijinki ba kullum ina nuna miki illar hakan kin kasa ganewa, kuka na fara yi to ni innah me yasa yake min haka, dama haka aka ce ya rika yi min,shi yasa fa nake xuwa na fada miki don ki rika yi masa magana, ni bana son abinda yake min,hawaye na rika sharewa ita kuwa innah saboda takaici ma ta kasa cewa komai sai da nayi kukana na koshi sannan ta rarrashe ni tace xata yi masa magana.
Baba na shigowa take fada masa yadda ta kaya tsakanina da dattijo, kama baki yayi lallai Niimatullah ba hankali, yanxu da hankali xa a rika wannan xancen, amma dai xan nemi mijin nata nayi masa magana ya dan saurara har xuwa tayi wayo tunda bata san ciwon kanta ba xata iya xuwa wani wajen ta fadi abinda ke faruwa tsakaninsu.
ba karamain dadi naji ba da baba yace xai neme shi yayi masa magana.
*Jeeddahtulkhair??*
😘*💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
12
Baba ne da kanshi ya kira shi a waya yace yana son ganin shi, ba a fi minti biyar da fada masa ba yaxo, da sallama ya shiga dakin baba sun fi kusan minti goma suna tattaunawa babu abinda nake jin dattijona na fada banda wallahi baxan iya jurewa ba baba xan iya shiga wani hali a hakan ma hakuri nake yi, shi kuwa baba sai hakuri yake bashi, gabana ne ya rika faduwa ina tunanin menene baxai iya jurewa ba, bayan sun gama tattaunawa ya fito ya tafi gida.
washe gari bayan mun yi sallar magriba yaxo, cikin nutsuwa ya tako ya shigo har tsakar gidan mu tare da yin sallama, idanun shi a kaina ya kasa daukewa sai wani asirtaccen murmushi mai kunshe da abubuwa da yawa yake sakar min, gefe na koma na buya a bayan innata, bayan sun gama gaisawa nima na gaishe shi daga haka babu maganar da ta sake hada ni da shi, sai da suka gama magana tsaf da innah ya juyo ya kalle ni.
cikin sassanyar muryarsa ya kira sunana Niimatullah!! idanuna a kasa na amsa masa, dama form na koyon girki da gyaran jiki na kawo miki, ina so ki fara xuwa nan bada dadewa ba, yanxu xan cike miki duk ranar alhamis da juma'a xaki rika xuwa, na xabi wadannan ranakun ne saboda kina xuwa islamiyya, ina so ki tsayar da hankalinki ki yi abinda ya kamata har kula da miji duk xa a koya miki a can, shiru nayi ina saurarensa har ya gama bayaninsa.
innah sai murna take xan koyi abubuwan rayuwa, cike da xaulaya ya tambaye ni, sunana xan saka miki ko na Baba naga kowace mace a wajen da sunan mijinta take amfani? Turo dan tsukekken bakina nayi, sunan babana xaka saka min, murmushi yayi niima kenan har yanxu baxa ki daina rigima ba ko, cike min form din ya shiga yi bayan ya kammala yake fada min cewa Kullum shi xai rika xuwa ya kaini, shagwaba na shiga yi masa ni Allah baxan bika ba da kaina xan rika tafiya, lallaba ni ya shiga yi kiyi hakuri na rika kai ki wajen da nisa shi yasa bana so kije ke kadai ko so kike wasu su dauke min ke su gudu da ke? da sauri na girgixa kai alamar a'a, sallama ya yi da innah sannan ya rika kifta min ido alamar na biyo shi nayi masa rakiya, makale kafada nayi ni baxan bika ba, sai da yaga ba nida niyyar bin shi ya tafi ya kyale ni.
tafiya yake a mota amma gaba daya tunanina yake yi, kafin ya isa gida ya kira ni a waya, dauka nayi na kara wayar a kunnena cikin shagwaba ya fara yi min magana my Niimatullah, idan kina kusa da innah ki matsa xan yi magana mai muhimmanci da ke, ban yi masa musu ba na shiga daki, gaishe shi nayi tare da yi masa ya yaje gida, cikin shagwaba ya amsa min ba lafiya matata, cikin kulawa nace me ya same ka dattijona?muryarsa a marairace ya amsa min da kece, da sauri na sake tambayarsa me nayi maka dan Allah?har ka tayar min da hankali kasan bana so na cutar da kai innata ta fada min kai ne Aljannata wai haka ne? murmushi yayi har ga Allah yana jin dadin maganganun Niimatullah da sauri yace haka ne mana, da baki sani ba? eh nace masa.
kukan shagwaba ya hau yi min, kin shiga cikin rayuwata kin yi kane-kanen da baxa ki iya fita ba Niimatullah, nayi nisa a cikin kaunar ki ina jin rayuwata baxa ta tafi dai-dai ba idan babu ke,na kosa na fara rayuwa bisa kulawarki, ganinki da nayi yanxu ba karamin tayar min da wani miki kika yi ba a xuciyata, ki taimaka kixo inda nake ko driving na kasa yi saboda shaukinki, na tabbatar da cewa yau baxan yi bacci mai dadi ba musamman a lokacin da dare ya tsala na duba gefena ban ganki a kusa da ni ba, ki taimaki dattijonki ki fadawa su innah su bani ke kada sonki ya halakar da ni. kuka naji yana yi sosai.
A hankali na sauke ajiyar xuciya to kayi hakuri na gama xuwa makarantar girkin idan na iya komai ba sai na tare ba, katse min maganata yayi ni duk wannan bai dame ni ba babyna, indai girki ne da kaina xan rika yi mana,wata rana kuma mu je restaurant mu ci, ni burina kawai naga na fara rayuwa da ke, xaki amince a kawo ki gidana yanxu? da sauri na dakatar da shi.
ni dai wallahi a'a ba yanxu ba kuma idan ma xan tare da innata xan tafi na rika ganinta ina jin dadi, murmushi yayi ita ma innah ai da dan mijinta baxai bari ta tafi ta bar shi ba, don haka kema sai ki taho ki tarairayi naki mijin ki samu lada, makale kafada nayi kamar yana kallona, ni fa baxan taho yanxu ba har sai na iya girki da komai so kake yi matarka ta rika yi min gori ban iya girki ba kamar yadda tayi min na tsafta.
dariya ya rika yi lallai niimatullah bakya mantuwa yanxu har kin haddace wannan abin a kanki? ki kwantar da hankalinki baxa ta yi miki glri ba ai tasan amaryar tawa ta musamman ce ta hadu ta kowane bangare, kin san me nake tunawa a tare da ke kuwa??
cikin sassanyar murya nace masa a'a, lokacin da na dauke ki dama haka kike ba ki da nauyi kamar yar tsana, Gaskiya xan fadawa innah ta daina baki abincinta tunda kin ki yin nauyi, turo baki nayi kamar yana ganina ni din ce ba nida nauyi lallai ma ka raina ni da yawa.
murmushi yayi ni ban rainaki ba amma gaskiya na fada tunda duk nauyin kii ai baki kaini ba ko? shiru nayi masa sai can nace ai dan kai dattijo ne shi yasa ka fini nauyi.
murmushi yayi da ina kusa da ke sai na murde wannan bakin da har yanxu bai daina kirana da dattijo ba na fada miki ni babynki ne, kada ki sake cewa dattijo.
ni fa ina wani tunani Niimatullah, da sauri nace masa tunanin me kake yi?
Anya xaki iya daukan nauyina kuwa? au na manta fa na yiwa baba alkawarin mun daina wannan maganar da ke, takura masa nayi sai ya fada min amma yaki fada haka muka gama magana ya kashe wayar.
*Jeeddahtulkhair😘*💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Amina Bashir (maman siyama)*
13
Suna kammala wayar ya ja motar shi ya wuce gida, yana driving yana tuna irin hirar da suka yi da Niimatullah, ba karamin shiga ransa tayi ba, ji yake kamar ya jawo lokacin da xata tare a gidan sa.
A bakin kofar parlour ya ci karo da matarsa xaune a kan kujera ta dora kafa daya kan daya, tana harare-harare tare da turo dan kwalinta gaban goshi, da sallama ya karaso wajenta wani mummunan kallo tayi masa tare da kawar da kanta gefe guda, cikin tausasa murya yake mata magana, sannu da gida maman munir a fusace ta amsa masa, kaine da sannu tunda kai ka dawo daga wajen kaxamar matarka wacce ilimin addini da na boko bai wadaceta ba, wallahi ina ganin kokarin ka da har kake iya kula wannan jakar da bata san kanta ba, ka xubar da ajinka da nawa, ka rasa wadda xaka hada ni kishi da ita sai yar matsiyata, wadda iyayenta ke rayuwar wahala, tunda aka haifi yarinyar nan nasan bata san menene dadin duniya ba saboda talauci, amma don ka raina min hankali xaka hada ni da ita salon ta shafa min kwarkwata da kudin cizo. tana gama magana ta cigaba da girgixa kafarta.
ji yayi xuciyarsa na tafasa kamar xata tsaga kirjinsa ta fito saboda irin maganganun da take fadawa wacce ba shi da tamkarta a rayuwarsa, cikin fushi ya mayar mata da martani.
kucaka, kuma kaxamar da kika raina kike ganinta a banxa ta fi min ke a yanxu domin a inuwarta nake samun nishadi da jin dadin rayuwa, dadin da ban ji shi sama da shekaru talatin ba yanxu na same shi a wajen jaririyar yar da kika haifa, kin yi sake yar cikin ki ta kwace miki miji, domin da ke da babu duk daya na dauke ku a cikin gidan nan.
Baki ajiye komai ba sai girman kai da raina miji, da kwalliyar banxa amma ta bangaren ibada salam ba dadi, yana gama fada ya saki wani shu'umin murmushi.
zan baki shawara daya kije wajen Niimatullah ta koya miki iya xama da miji da tarairayarsa, kuma ki lallabata tayi miki addu'a Allah ya axurta ki da irin ni'imomi da baiwar da Allah yayi mata, domin bakin Niimatullah mai kyau ne ina da yaqinin addu'arta xata karbu saboda farantawa mijinta da take yi.
sake juyawa yayi ya kalleta, hannunta dafe da kirjinta ta rasa bakin magana, tunda na samu Niimatullah nasan menene dadin aure, ashe da duk hakuri nake ina rayuwa da dusar mace ban sani ba.
Hannu ta dora a ka ta fara rusa ihu tana ci masa mutunci tunda suke da shi bai taba tsayawa ya fada mata magana irin na yau ba, shi kuwa shigewa daki yayi saboda yasan ya gama munana mata, a falo ta kwana tana masifa ko bacci bata iya yi ba. kalmar da ya fada mata ita tafi tsaya mata a rai domin ta maimaita kalmar wajen sau goma, yanxu saboda wannan yar iskar yarinyar xaka rika kirana da dusa, Allah ya isa tsakanina da kai, kuka ta rika yi shi kuwa yayi kwanciyarsa bisa gado yasan baxa ta kara marmarin xagin Niimatullah a gabansa ba tunda ya yiwa tufkar hanci, ajiyar xuciya ya sauke sannan ya juya yayi kwanciyarsa.
washe gari da wuri na kammala shiryawa na gyarawa innah dakinta, saboda nasan dattijona yana kan hanyar xuwa ya tafi da ni wajen koyon gyaran jiki, kusa da innata na xauna ina jiran karasowar sa, horn din mota naji don haka na saka takalmana, sallama na yiwa innah sannan na fita.
tarar da shi nayi jingine da motarsa ya harde hannayens a kirjinsa, tunda na taho daga nesa yake sakar min wani kallo tare da yi min kyakkyawan murmushi, daga nesan na tsugunnah na gaida shi, cike da kulawa ya amsa min ,bude murfin motar yayi na shiga, sannan shi ma ya shigo, kafin ya ja motar mu tafi sai da ya kare min kallo yana min magana kasa-kasa wacce bana fahimtar abinda yake cewa, dago fuskata yayi yana min wani kallon da ke sanyaya min jikina, cike da kulawa yake min magana.
ki tsayar da hankali ki koyi yadda xaki tarairayi marainiyar xuciyar mijinki kin ji my Niima, gyada kai nayi kawai ba tare da nayi magana ba, sai da ya gama yi min nasiha sannan muka dau hanya.
muna isa ya juyo ya dube ni har mun xo babyna, sannu da driving nayi masa sannan ya xagayo ya bude min kofa, hannuna ya rike muka shiga har Office din matar da xata koyar da ni, a xaune muka sameta tana cike wasu forms, cikin girmamawa ta gaida dattijona, hannu biyu ta karbe mu, cike da kulawa ya nuna ni,wannan sabuwar amaryata ce, an daura min aure da ita amma bata tare ba, don haka ina so a koya mata komai kafin lokacin da xata je gidana, a koya mata da kyau yadda xata kware a komai fiye da macen da ta dade a gidan miji, kuma special class nake so a sakata, ina ganin xata fi sakewa idan bata ganin idon jama'a.
cikin sakin fuska ta bashi amsa, lallai Alhaji kana so amaryar nan taka ta kwace gida tunda ka kawo ta nan, murmushi yayi ba tare da yace komai ba.
kada ka damu Alhaji xaka ga yadda xata dawo wallahi komai nata sai ya canja, har sai ka dawo kayi min kyauta ta musamman saboda yadda xan kula maka da amaryarka, dan wasa da dariya suka yi ni kuwa ina gefe ina sake-sake a xuciyata, ita kuwa wannan matar me xata koya min haka da har xata canja ni??
kudi mai yawa ya xaro ya bata sannan ya mika mata form din don yin submiting, tashi yayi xai tafi karasowa yayi wajena ya rike hannuna ya kai ni kusa da ita.
ga amanata nan a kula min da ita, sumbatar goshina yayi sannan ya tafi da niyyar idan an tashi xai dawo ya dauke ni.
*Jeeddahtulkhair?💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(Jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
14
Tsayawa tayi ta kare min kallo sannan ta kira sunana cikin nutsuwa, Niimatullah!! A hankali na dubeta, sunanki mai dadi da kuma kyau, kamar yadda wannan sunan naki yake haka nake son mayar da ke, amma sai kin bani hadin kai,kuma sai kin saki ranki sannan xaki iya koyar komai don farantawa mijinki, duk abinda baki sani ba kada ki ji tsoron tambayata ki dauke ni a matsayin kawarki. kece mace ta nawa a wajen mijinki?? kaina a sunkuye na amsa mata da nice ta biyu, girgixa kai tayi, yayi kyau tunda kuwa haka ne dole ki lura ki xage damtse ki iya komai idan ba haka ba xaki xama yar kallo a gidan miji maybe akwai abubuwan da matarsa ta saba masa da shi matukar kika xama banxa bakya yi masa sama da abinda take yi xata kwace miki miji, kiyi amfani da kuruciyarki ki mallake mijinki.
Ajiyar xuciya tayi sannan ta sake jefo min wata tambayar kin tare a gidan mijinki? daga mata kai nayi tare da cewa a'a sai na kara wayo, murmushi tayi ai kuwa mijinki yayi dabara da ya kawo ki nan don xaki koyi wayon da ko a gidan mata dari xaki xauna kiyi xaman aure, amma fa darasin mu yana bukatar a cire kunya, kuma yana bukatar a rika gwadawa, dubanta nayi tare da tambayarta.
malama ya xa a yi na cire kunya innata ta fada min kunya adon mace ce, murmushi tayi tare da dafa kaina, a wajen mijinki kunya haram ce amma a wani wajen kunya aba ce mai kyau abinda hausawa suke nufi kenan.
wani abu ta dakko a kwalba ta tsiyaya min a cup, karbi wannan kisha tun Yanxu nake son na fara hada ki ta yadda xaki rikita tsohon nan, karba nayi na fara sha, ina kurba daya na fitar da shi, Allah baxan iya sha ba Aunty karbi kayan ki, bata fuska tayi haka xaki daure kisha dama ba dan kiji dadi xaki sha ba, sai dan farantawa mijinki, takura min tayi har sai da na shanye gaba daya.
bayan na gama sha ta mika min wani abu a roba karbi wannan turaren da xaki rika tsarki da shi ne, ina so ki rika kamshi ko ta ina, sannan ki nisanci tsarki da ruwan sanyi, da shan ruwan sanyi domin wadannan abubuwan suna taka muhimmiyar rawa wajen mayar da mace salam, sannan ki daina xama a kasa ba tare da shimfida ba ki daina yawo ba takalmi a tsakar gida hakan yana ragewa mace ni'imarta, ki daina wanka da ruwan sanyi, sannan ina so a Kullum ki dafa lalle ki rika wanka da shi hakan yana karawa mace dumin jiki, kuma kin san mace mai dumi darajarta daban take a wajen miji, yau nake so ki fara duk wadannan abubuwan da na xayyana miki bana son wasa, idan kika karya dokata guda daya xaki ga bacin raina, cike da ladabi na amsa mata baxan karya miki doka ba insha Allah.
Tafiya ta shiga koya min salo daban-daban, idan tayi wani abin har kunyar kaina nake ji, haka ta rika koya min kala-kala duk wacce aka koya min sai na gwada idan nayi dai-dai ta gode min idan nayi kuskure ta gyara min ta sake koya min, bayan mun gama ta kira dattijo yaxo don ya tafi da ni, bata dade da kiran shi ba ya iso.
Har bakin kofa ta rako ni, umartata tayi da na fara gwada abinda ta koya min tunda dai mallakina ne, dubanta nayi kamar xan yi kuka. Allah baxan iya ba Aunty kunya nake ji kiyi hakuri na fara gwadawa gobe.
hararata tayi, haka muka yi da ke Niimatullah, bana son taurin kai kiyi abinda nace kafin ranki ya baci, a hankali na fara wani irin taku mai cike da burgewa da kayatarwa, a hankali na bude hannayena na fada kirjinsa, shafa gashina kaina yayi tare da dago fuskata yana min wani kallo saurin kawar da kaina nayi saboda duk kunyarsa ta kamani, tafa min naji suna yi tare da cewa kin yi kokari Niimatullah, shi kuwa kin sakina yayi sai da muka fi kusan minti biyar a haka sannan muka hau mota muka tafi.
kallona yayi yana murmushi, lallai idan kika dade a makarantar nan abinda xa a min sai ya fi haka, gashi yau daga xuwa har na fara ganin canji,Gaskiya dole na karawa malama kudi don kwalliya ta fara biyan kudin sabulu, ina turo baki na dube shi.
nifa na fara gajiya da makarantar nan naga akwai takura komai aka koya wai sai an gwada ni Gaskiya baxan iya ba, gashi har wani abu mai daci ta bani da nace baxan sha ba ta takura min wai na faranta maka ne, ni wlh na gaji, shafa fuskata yayi to ai ta haka ne xaki kware Niimatullah idan bakya gwadawa ai sai ki manta, kuma menene don kin sha abinda xaki faranta min ki tuna ni fa aljannarki ne.
kuka na fara yi masa ni baxan koma ba Allah tunda haka ne, lallaba ni ya shiga yi har sai da na yarda xan koma, yau har cikin gida ya kaini sannan ya tafi nasa gidan.
0 comments:
Post a Comment