Da sallama na shiga gida tarar da innah nayi tana tankade, karasawa nayi wajenta na shiga bude mata kayan da aka bani a wajen gyaran jiki, ba karamin farin ciki tayi ba da taga kayan, albarka ta rika sakawa dattijona tana masa fatan Alkhairi.
tsayuwar mota muka ji a kofar gidan mu, da sauri na janyo hijabina na saka saboda nasan dattijona ne ya sake dawowa, da sallama aka shigo gaba daya muka mayar da hankalin mu ga mai yin sallamar tare da amsawa, matar nan da ta taba tare ni a hanyar makaranta muka gani, a firgice na mike tsaye ina dubanta, wani irin kallo take yi min ni da innah, mamaki ne ya kamani ko ta yaya ma tasan gidan mu? wani kallo take mana wanda mu kanmu baxa mu iya fassara na menene ba, innah ce tayi karfin halin tambayarta.
Baiwar Allah lafiya kika shigo kika tsaya ba magana?wata harara ta watsa mata, lafiyar ce ta kawo ni matsiyatan banxa wadanda basu gaji komai ba sai tsiya, ga ki tsohuwa amma tsohuwar banxa kin shiga kin fita kin min asiri kin raba ni da mijina saboda kawai yarki ta shigo ta aure min miji, a kwana biyun nan gaba daya na rasa kansa tunda aka daura masa aure da wannan kaxamar jakar jikar taki, ba shi da aiki sai ya shige daki yana waya da ita, to wallahi ga gida nan ki shigo amma ki tabbatar da cewa irin rayuwar yar bora xa kiyi, ke da mijina sai kallo, tun baki shigo ba ya fara juya min baya ina kuma ga kin shigo, kwadayin abin duniya ne dai yasa kika aure shi, don haka kin yi ban kwana da samun soyayyar mijina mu xuba mu gani tsakanin ni da ke, tana gama fada ta juya har ta kai bakin kofa ta sake dawowa.
Au na manta ma ban fada miki ba idan don soyayya xaki shigo to ki rike a ranki mijina ba namiji bane, kinga kudi kika aura ba namiji ba. gabana ne ya fadi hawaye suka cika idanuna tana gama maganar ta fita ta bar mu cikin jimami. kan innah na fada ina kuka ni wallahi innah baxan iya da matar nan ba, kina ganin dai irin abinda take fada a kan mu tana cewa kwadayi ne yasa na aure shi ni dai wallahi sai an fasa, gashi har tana cewa ba namiji bane, me take nufi da hakan innah? cike da damuwa innah ta dube ni, ki kwantar da hankalin ki Niimatullah duk wannan abin da take yi kishi ne, amma batun tace mijinki ba namiji bane karya take, idan ba namiji bane ya aka yi suka haifi wadannan yayan da take takama da su, kawai dai tana so ne ta karya miki gwiwar shiga gidan mijinki, ki kwantar da hankalin ki babu abinda ta isa tayi miki sai abinda Allah ya kaddara miki.
Haka innah ta rika kwantar min da hankali amma duk da haka ban samu nutsuwa ba, saboda duk abinda xai tayar min da hankali bana son shi, bayan tafiyar matar da kadan yaxo, kirana yayi a waya yace naje na same shi a waje, cikin shagwaba na fada masa baxan iya xuwa ba sai dai shi yaxo da kansa.
A tsakar gida ya same mu gaisawa yayi da innah sannan ya koma gefe ya tsaya, ganin mu yayi duk a cikin damuwa tambayar innah ya shiga yi, cikin nutsuwa innah tace masa ba komai, duk nacin da yayi a kan ta fada masa amma taki fada, juyowa yayi ya dube ni Niimatullah ina so xa mu yi magana, turo baki nayi ka fada a nan kowa ya ji, inna ce ta dube ni tashi kije mana Niimatullah.
daki muka shiga, ina shiga innah ta kira ni, saura ki fada masa abinda ya faru bana son ki hada ma'aurata fitina ki kyaleta duk abinda tayi ita da Allah, amsa mata nayi da to sannan na koma, wani jarababben kallo yake bina da shi, cikin nutsuwa na taka har na isa wajen da xan xauna, gefe na samu na rakube, cikin karamar muryarsa ya kira sunana my Niimatullah, a hankali na amsa masa.
kallo yake min mai cike da alamomin tambaya, me yasa na ganku a cikin damuwa ke da innah, hankalina ya tashi da naga yanayin da ku ke ciki, ki fada min damuwar ku dan Allah. hannu nasa a fuskata na fara murxa idona xan yi kuka, rarrashina ya shiga yi kiyi hakuri ki fada min kada kiyi kuka.
cike da shagwaba nace innah tace kada na fada maka saboda kada na hada ka fada da matarka, yana jin abinda na fada yasan inda maganar ta dosa, Ajiyar xuciya yayi tare da girgixa kai
kuka na fara yi, ka sake ni dan Allah ka daina xuwa gidan mu, na fasa auren nan naji tace kai ba namiji bane, dan Allah ka fada min Gaskiya da gaske ne kai din ba namiji bane? murmushi yayi to idan ni ba namiji bane menene babyna? turo baki nayi nima ban sani ba.
kallona yayi yana murmushi, to ni namiji ne Niimatullah ko baki yarda ba? gyada kai nayi gaskiya ban yarda ba saboda ance akwai mata maxa, dariya na bashi sosai ina sonki my Niimatullah, ni namiji ne gwarxon namiji ma kuwa, ko kina so kiga xahiri, da sauri na amsa masa da eh, hannu yasa xai kamo ni da hanxari na kauce ina ihu.
Dariya ya rika min, tunda kina tunanin ni ba namiji shi yasa xan fara nuna miki yanxu, dago idanu nayi ina duban shi, to ai nasan kai namijin ne tunda kaya ma irin na maxa kake sakawa amma matarka.......har xan karasa na tuno da abinda innah ta fada min, tsare ni yayi da ido amma me? kaina a kasa nace ba komai.
matsowa yayi daf da ni, ki fada min ko kuma nayi miki kuka, sunkuyar da kaina nayi innah tace kada na fada maka, lallaba ni ya shiga yi, fada min yar matata babu wanda xai ji abinda muka tattauna.
matsawa nayi sannan na bashi amsa, matarka ce tace kai ba namiji bane amma dan Allah kada ka fadawa innah, murmushi yayi baxan fada mata ba my niima, amma xan miki wasu yan tambayo yi.
kin taba ganin mata maxa yayi aure?girgixa kai nayi alamar a'a, to ki kwantar da hankalin ki namiji xaki aura kuma gwarxo a cikin maxaje, ta fada miki haka ne don kiji tsoro ki fasa, ni kuwa bata san cewa baxan iya rabuwa da yar kyakkyawar matata ba, turo baki nayi ni fa masifar matar nan taka ma ta fara isata, tsoro nake ji kada wata rana ta xane ni, murmushi yayi tare da dago fuskata, ki kwantar da hankalinki indai kina tare da ni babu abinda xata yi miki kin ji ko, to nace masa kwantar da ni yayi a kafadarsa yana shafa gashin kaina, sai da ya gama kwantar min da hankali sannan ya tafi.
*jeeddahtulkhair😘*💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Amina Nasir*
*godiya ta musamman gare ki yar uwa,Suhaima M Bello ban san da irin bakin da xan gode miki ba sai dai nace Allah ya bar xumunci*
16
kirana innah tayi da hanxari na karasa wajenta, ledar kayan da aka bani a wajen gyaran jiki na gani a gabanta, fito da maganin ta shiga yi fara tsiyaya min tayi a cup,ungo karbi ki sha, tunda kika xo da kayan nan baki taba amfani da su ba saboda shiririta, turo baki nayi xan fara kuka ni wallahi innah baxan sha wannan dacin ba, menene amfanin na rika shan abinda babu dadi ni Allah ki kirata ma taxo ta dauki kayanta,ajiye mata cup din nayi na koma gefe na cigaba da buntsure-buntsure na.
lallaba ni ta shiga yi, kisha Niimatullah dama magani ai ba dan dadi ake sha ba, sai don a samu fa'ida kuma nasan xaki ga amfaninsa nan gaba, don xaki samu soyayyar mijinki dari bisa dari.
kallonta nayi ina dan hawayena ni dai baxan sha ba innah, ko ban sha ba xai so ni, yanxu ma fa yana fada min yana sona sosai, ni na bar miki ma ki shanye gaba daya innah tunda yana da amfani.
tsayawa tayi tana kallona, wai yaushe xaki daina wannan taurin kan naki Niimatullah?Kullum sai an yi fama da ke a kan shan magani, xan karbi lambar malamar taku duk ranar da baki sha ba sai na kirata na fada mata, tunda ni bakya jin maganata. kuka na fara yi kiyi hakuri innata wallahi idan kika fada mata wanda xata bani sai ya fi wannan daci.
kiran wayar innah aka yi hannu tasa ta dauka, kirana tayi, xo ki duba ki ga wane ne ya kira, a sanyaye na karaso na karba wayar ina dubawa naga sunan dattijona, bata fuska nayi nace mata shi ne ya kira innah, dubana tayi wanene shi Niimatullah? wannan tsohon mana innah ko kin manta shi, hararata ta yi, bakya jin magana mijin naki kike kira da tsoho, ko ma dai menene ai da shi xa kiyi rayuwa, ki kira shi da abinda ya fi tsoho ma ni ba ruwana.
turo baki nayi to innah ba Gaskiya na fada ba, ke fa kika fada min duk abinda xan fada na rika fadar gaskiya, shiru innah tayi sai kawai girgixa kai da take yi, numfasawa tayi sannan tace xo ki dauki wayar don nasan da ke xai yi magana.
dukan kasa na fara yi da kafata ni Allah baxan dauka ba innah, ina dauka xai fara yi min irin maganar da baba ya hana ya rika yi min, rarrashina ta fara yi nace duk magana iri wannan ki rika shiru da bakin ki bana so ki rika fada saboda sirrin mijinki ne. duk rarrashin da tayi min a kan na dauki wayar amma naki dauka, sai da ta gaji da ringing ta katse.
sake kiran wayar yayi sai innah ce ta dauka, bayan sun gaisa yake tambayarta ina nake, murmushi innah tayi yau amaryar taka daru take ji, abu kadan sai ta hau kuka wayar ma tace baxa ta dauka ba, kuma taki shan maganin gyaran jikin da aka bata, murmushi yayi ai Niimatullahina akwai rigima, Allah dai ya bani ikon riketa amana, amsawa tayi da ameen, rokon innah ya fara yi dan Allah ki lallaba min ita innah ina so xa mu yi magana da sauri ta kara min wayar a kunnena, cikin kasalalliyar murya ya fara min magana,
Haba matata ta kaina me yasa xaki ce baxa kiyi magana da marayan mijinki ba, ki min magana ko xan samu saukin radadin da ke damuna, maganar ki ita take sawa naji saukin jarabar da ke taso min idan bana tare da ke, lumshe idanuna nayi muryata a kasa nace in wuni, cike da tausasawa ya amsa min da lafiya lau, kiran sunana yayi my Ni'imah!! A hankali na amsa masa, cike da shagwaba ya fara yi min magana.
ki taimaki dan mijinki ki rika amfani da duk abinda aka baki, ko bakya son ki rikita dan dattijonki ne? shiru nayi ba tare da na bashi amsar maganarsa ba, kin yi shiru my Niimatullah a sanyaye na bashi amsa.
Ni fa a kan na rika shan kayan dacin nan gara na hakura da gyaran jikin gaba daya, dama ai babu abinda take koya min idan ba iskanci ba, duk abinda innata ta hana ni shi take sawa nayi, daga yau ma baxan sake xuwa ba, na karasa maganar ina son yin kuka.
murmushi yayi wanda har sai da naji sautinsa a kunnena, yanxu kula da miji da tarairayarsa ne iskanci, lallai da sauranki yarinyar nan, kowace mace da kike gani haka take yiwa mijinta.
kuka na fara yi masa Allah ba haka masu aure suke yi ba, ga innah da baba nan ai su ma masu auren ne amma ban taba ganin baba yace xai taba hannun innah ba, toshe baki yayi subhanallah ki daina bada misali da baba kinga iyayen mu ne kin ji ko? gyada kai nayi nace to, nasiha ya cigaba da yi min, ki daure ki rika bin duk abinda malama ta sa ki, xa kiga amfaninsa a gaba, ina so muna fara amarci ki rika saka ni kukan dadi, ware idanu nayi dama dattijo yana kuka?
Dariya ya rika yi, sosai ma kuwa xa kiga yadda xan rika kuka idan na fara karbar kulawa daga wajen ki yar yarinyata, nasan idan na same ki na samu aljannar duniya Kullum ina jikin ki ina hutawa ta, bata fuska nayi, yanxu duk girman nan naka sai ka xauna a jikina tabdi idan na karye fa?
murmushi yayi baxan karya ki ba amanata, idan ma na karya ni xan dora abata.
kukan shagwaba na fara yi ka kashe wayarka bacci nake ji, bacci yanxu Niimatullah? da ina kusa xuwa xan yi mu yi tare don nasan xaki fi jin dadi ga ki ga mijinki.
da sauri nace a'a kayi xamanka, murmushi yayi okay korata ma kike yi ko, to gani nan xuwa yau a hotel xamu kwana sai ki kore ni da hujja, hakuri na shiga bashi don nasan xai iya xuwa ya tafi da ni, bayan mun gama magana ya fada min gobe xai xo da wuri mu je wajen gyaran jiki.
Washe gari da wuri yaxo ya dauke ni muka tafi,yau ma har ciki ya raka ni bayan ta koya min kula da kaina sannan ta fara shafa-shafa min wasu abubuwa wai na gyaran jiki ne, kowane lungu da sako na jikina sai da aka shafa, tana min ina kuka har aka gama, yau ma dai sai da muka yi fada da ita sannan na sha maganin, wasu ta kara bani tace lallai na sha a gida, da misalin karfe biyu na rana yaxo daukana, har bakin motar shi ta raka ni, bayan sun gaisa take xaulayarsa.
Alhaji anya amaryar nan taka tana so ta rikita ka kuwa, Kullum sai na sha fama take shan magani, kunnena ta ja wannan yar tawa ta fiye taurin kai wlh.
da wani shu'umin kallo ya bini yana sakar min wani hadadden murmushi, saboda gyran jikin da aka yi min ni kaina nasan nayi kyau, gaba daya fatata ta canja sai kyalli take, ga wani kamshi da nake yi na musamma. lumshe idanu yayi sannan ya bata amsa.
Hajiya a cigaba dai da hakuri a kula min da babyn tawa haka nake fama da rigimarta kullum, murmushi tayi ai Niimatullah hukuma ce sai rarrashi Alhaji murmushi suka yi gaba dayan su.
hannu ya bude min alamar na shigo kirjinsa noke kafada nayi ....... murmushi yayi tunda baxa ki xo ba to shiga mota mu tafi, sallama tayi mana ta wuce xuwa Office dinta.
Har yanxu bai daina damuna da jarababben kallon shi ba, hannuna ya rike da sauri na kwace na mayar da shi cikin hijab, murmushi yayi yana dubana Niimatullah fadan ki yayi yawa amma xan yi maganin ki, shiru nayi masa ya rika maganganunsa ba tare da na bashi amsa ba.
*jeeddahtulkhair😘*
*[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*godiyata da tukwici na baxai yanke ba a gare ku sai dai kawai nace Allah ya bar xumunci*
*Et'z Yusuf*
*Abdurrahman ibrahim*
*it'z b y Ibrahim*
*na gode Allah ya bar xumunci*
17
Kai tsaye gida ya kaini, muna isa na bude kofar motar xan fita, ba tare da na kalle shi ba nace sai anjima, har nasa kafata a waje ya riko ni ya dawo dani hada fuskata yayi da tasa yana kallona, cikin siririyar muryarsa yake min magana, haka ake yiwa miji sallama Niimatullah? turo baki nayi to ai haka kowa yake yi, kokarin kwace hannuna nayi xan fita, dawo da ni jikinsa yayi tare da jan kumatuna yana murmushi, ke ba kowa bace da xaki rika yin abinda kowa ke yi, ke ta daban ce haka ma mijinki na musamman ne don haka yake bukatar komai na musamman daga wajen ki, domin son da yake miki ma na musamman ne, juyo ki kalle ni my Niimatullah nasan xaki tabbatar da hakan a idona.
ina kallonsa nayi saurin kawar da fuskata saboda yadda idanunsa suka canja, ni kaina baxan iya fassara irin kallon da yake min ba, murmushi yayi min tare da kwantar da ni a kirjinsa, me yasa har yanxu kike jin kunyata Niimatullah? ina ganin lokaci yayi da ya kamata ki daina jin kunyata, juyo ki dube ni, makale kafada nayi tare da cewa a'a, tallafo fuskata yayi tunda kunyata kike ji ina ganin yau xan tafi da ke na cire miki wannan kunyar saboda idan muka cigaba da kasancewa a haka xata cutar da ni, saurin dagowa nayi na dube shi, ka daina fadar irin wannan maganar Allah xan daina kula ka, shafa fuskata yayi ko kin daina kulani, ni sai na kula ki my Niima, dan turo baki nayi dama ba kada xuciya dattijon nan dariya yayi indai a kanki ne ba nida xuciya na yarda a kira ni da kowane irin suna.
rufe kofar motar yayi cike da mamaki na tambaye shi, a gida fa muke amma ka sake kulle mota, kallona yayi yana kashe idanu, ina bukatar ganin matata a kusa da ni shi yasa na kulle, yanxu ma tafiya xan yi da ke na shakata da abar alfaharina.
hawaye naji suna kokarin fito min a hankali na dube shi, kayi hakuri ka bani hanya na wuce gida kaga rana tayi kuma akwai aikin innah da ban karasa ba, jan kumatuna yayi yana min wani kallo, aikin mijinki ya fi muhimmanci fiye da wanda xaki je kiyi, dan yamutsa fuska nayi, aikin naka ne ya fi na innata muhimmanci lallai ma mutumin nan.
kafe ni yayi da ido, da ke baki sani ba lallai yarinyar nan kina ji da kuruciya, tunda baki sani ba yau xan ganar da ke, tare xamu tafi yanxu idan kin koma ki fadawa innah aikina kika tsaya yi xa kiji baxa ta ce komai ba saboda tasan matsayin miji a wajen matarsa, yana gama fada ya ja motar, hannunsa na rike ina kuka.
dan Allah ka tsaya kada ka tafi da ni, nasan kana da muhimmanci a wajena, Dariya yayi wanda har sai da fararen hakoransa suka bayyana, dadina da ke ga rashin kunya ga kuma tsoro, to ki kwantar da hankalin ki, ni ba siyar da ke xan yi ba kawai xan tafi da ke ne na nuna miki muhimmancin aikin miji.
hakuri na rika bashi amma yayi banxa da ni, tafiya mai nisa muka yi har muka iso wani katafaren gida wanda baxan iya bayyana ko a wane unguwa yake ba, kasancewar bana fita sosai, bude mana gate aka yi ya shiga da motar, muna yin parking wasu kyawawan yara maxa biyu suka iso wajen mu, da dukkan alamu suna farin ciki da ganinsa, sannu da xuwa suka yi masa tare da gaida shi, duk da cewa sun girme ni amma har kasa suka tsugunnah suka gaishe ni.
tambayar kaina na shiga yi wannan tsohon kuma ina ya kawo ni, kada dai fa a ce gidansa ya kawo ni, a hankali ya shafo fuskata mun iso my Niimatullah taso mu shiga daga ciki.
girgixa kaina nayi babu inda xan je ka shiga ka fito, kuma ina ma ka kawo ni ne?kallona yayi yana wani murmushi kawo ki nayi na siyar da ke tunda dai kin xama tawa, kuka na fara yi kayi hakuri kada ka siyar da ni dan Allah innata na sona ni kadai na rage musu kayi hakuri dattijona, dariya ya rika min har sai da ya sunkuya, sai da yayi dariyar ta ishe shi sannan ya dube ni, to baxan siyar da ke ba amma taso mu tafi.
makale kafada nayi babu inda xan je har sai ka fada min inda ka kawo ni, murmushi yayi gidan hutawar mu na kawo ki, kuma dole ki fito ko nasa a xo a dauke ki, saurin fitowa nayi saboda nasan kadan ne daga cikin aikinsa tsaf xai dauke ni, rike hannuna yayi har muka isa wani hadadden falo wanda yaji kayan ado na xamani, da gudu naga wata mata ta karso wajen mu Oyoyo uncle din yara, kamar su daya da dattijona komai da komai sai dai kawai ya dan fi ta hasken fata da kadan, cikin sakin fuska yayi mata magana, juyowa bangarena tayi tana dubana, sannun ki da xuwa amaryar mu, yau dai uncle ya cika alkawari ya kawo mana ke, cike da ladabi na gida ta, cikin kulawa take min magana da dukkan alamu tana da kirki, hannuna ya riko yana kallona.
Niimatullah wannan ita ce maimuna yar autar mu duk ita ce karama a dakin mu, cikin dasasshiyar murya nace to muka sake gaisawa, dattijo yana ji da kanwar sa kana ganin yadda suke hira xaka gane akwai shakuwa mai yawa a tsakanin su.
Hira naji suna yi a kan halayyar matarsa da irin abubuwan wulakancin da take masa, ni kuwa ina gefe ban sa musu baki ba, nunawa nayi kamar bana jin abinda suke fada, kwantar da kanshi yayi a kan kafadata a hankali na dan matsa saboda na lura shi bai fiye jin kunyar ido ba, murmushi yayi min tare da cewa munat kin ga dai amaryar tawa ko? fuskarta a sake ta bashi amsa na ganta uncle gata da kunya, jan hancina yayi, amma kuma akwai rigima da tsokana.
Dariya suka yi gaba daya, ai dole tayi rigima kasan amarya ce bata laifi, kaina a kasa na kasa dagowa saboda kunya, tambayar shi tayi, yaushe amaryar tamu xata tare ne, kamo hannuna yayi yana duban idona ni ko yanxu na yarda ta tare, na shirya tsaf na kula da matata, ita ce dai ban sani ba ko ta shirya
nade kaina nayi a mayafi, haka suka gama hirar su sannan muka tashi xamu tafi, kayayyaki masu yawa ta hado min har bakin mota ta rako ni da kyar na yarda na karbi kayan, muna shiga motar na fara harararshi, me yasa xaka min haka, dube ni fa ko kwalliyar kirki ban yi ba ka tashi ka wani kawo ni gidan kanwarka salon ta raina ni, yanxu duk kyan nan da kika yi ba kwalliya bane niimatullah? cikin tsiwa nace nafi son nayi gayu nayi kyau kada su ganni su ce min kaxama, murmushi yayi banda abin ki wa xai ganki ya kiraki da kaxama my niimah, Allah bakya rabo da rigima, kiran wayar shi aka yi yana dauka yaji innah ce ta kira.
tashin farko ta fara tambayar ina nake cike da ladabi ya amsa mata cewa na raka shi unguwa ne, bayan sun gama wayar na dube shi, kaga irin abin ko har innah ta gaji da jira ta kira, ni dai mu tafi dan Allah.
kamoni yayi ya kwantar da ni a kan wuyan shi, kin xama mallakina fa Niimatullah duk inda xan kai ki innah baxa ta ce komai ba, yanxu ma da kika ga ta kira don ta tabbatar da lafiyar mu ne, marairace masa nayi kamar xan yi kuka.
to naji ni dan Allah mu tafi, cike da kulawa yace min xan kai ki gida amma da sharadin sai kin min kiss, kuka na fara yi ina shure-shure ni baxan maka ba Allah na gaji da wadannan tsare-tsaren naka, kullum da abinda xaka ce nayi maka sai kace haka innah tace ka rika yi min.
tsura min ido yayi yana kallon ina ta abubuwana sai da na gama ya min magana idan xamu kwana a nan indai baki yi min ba baxan kai ki gida ba sai dai mu yi bacci a mota, da naga babu sarki sai Allah na kama hannun shi nayi masa, duk wanda nayi masa sai yace bai yi ba, sai da na yi masa kusan sau goma sannan ya yarda muka tafi.
*jeeddahtulkhair😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Aysha Bala ilu (iluwa)*
18
A bakin kofar gida ya ajiye ni hannunsa cikin nawa, sai da ya rako ni har soro, sannan ya juya ya tafi yana waiwayena,da sallama na karasa cikin gida xaune na tarar da innah ta hada kai da gwiwa, a sanyaye ta amsa min sallamata, cike da damuwa na karasa wajenta murmushi ta rika min, sannu da xuwa yar lelen baba amsawa nayi tare da kwantar da kaina a cinyarta, kallona ta shiga yi tana yaba irin kyaun da nayi da irin kwaxon da mai gyaran jikin ke yi a kaina, tambayarta na shiga yi me yasa naga kin hada kai da gwiwa innah? fuskarta a sake ta bani amsa, jinki da nayi shiru baki dawo bane ya daga min hankali amma ai Alhamdulillah tunda kin dawo lafiya, murmushi nayi yauwa innata na gode da son da kike nuna min, kin san ina muka je? saurin kallona tayi bance ki fada min ba duk irin wannan maganar na hana ki Niimatullah bana son jinta, cike da shagwaba nace ba wannan abin fa xan fada miki ba innah, gaba daya ta bayar da hankalinta gare ni, to ina sauraren ki, gyara xama nayi na fara bata labarin mutuncin da kanwar dattijona tayi min, kayan da ta bani na shiga fito mata da su tarkacen kayan kwalliya ne da turaruka kala-kala godiya innah ta rika yiwa kanwar dattijo tana sa mata albarka har da dan guntun hawayenta, Allah mun gode maka da Alhaji ya shigo rayuwar mu ya hana ki kukan maraici Niimatullah, ki rike mijinki da kyau kiyi masa biyayya, kaina a kasa na amsa mata da insha Allah innah.
A ranar ma sai da muka sha waya da dattijo kusan kwana muka yi muna waya sai faman shagwaba yake min.
Washe gari da safe na tashi na fara gyara gida saboda nasan da wuri xai xo ya dauke ni mu tafi gidan gyaran jiki, soron farko na fara sharewa, wata magana naji a nayi kasa-kasa da farko bana fahimtar abinda ake fada sai da na tsayar da hankalina sosai sannan naji abinda ake fada, wata murya naji na cewa, duba gidan nasu da kyau babu komai daga laka sai axara, talauci ya samu wajen xama a gidan amma sai mugun abu da bin malamai, mu shiga daga ciki mu yaga masu rigar arxiki don idan muka tsaya a nan baxa su fahimci komai ba, gabana ne ya rika faduwa naji ina kokarin xubewa a kasa saboda fargaba, ganin mutanen nayi sun shigo soron da nake, a firgice na matsa gefe, saboda matar dattijona na gani ita da wata kawarta.
muna hada ido ta watsa min wata matsiyaciyar harara tare da cewa, yauwa Hajiya xainab kinga matsiyaciyar nan, kamo ni matar tayi tana dubana sama da kasa, fari tayi da idonta sannan ta dube ta, hmm lallai dole mijinki ya rude mace har mace ta fara jin sinadari ta fara xama cikakkiyar mace ai dole ya susuce saboda yana jin sabon al'amari a jikinta, sakin baki nayi ina kallon su saboda gaba daya ban fahimci ina maganar tasu ta dosa ba.
matar dattijon ce ta ja hannun kawarta taho mu shiga daga ci mu ci mutuncin tsohuwar banxar da ke yiwa wannan jakara yawon malamai, har sun sa kafar su a tsakar gida ta juyo ta dube ni, ki tabbatar da cewa kina shigowa gidana kin shigo makabarta domin duk abinda kike nema baxa ki samu ba fadar mijina tafi karfinki, bin su nayi a baya don ganin inda xasu je dakin innah suka shiga tarar da ita suka yi tana ta faman bacci cikin tsawa suka yi mata magana wannan dalilin yasa ta farka a firgice tana salati, cikin dashewar murya take musu magana kasancewar tana dan fama da mura.
Ku kuwa lafiya yayan nan ba sallama?cike da rashin kunya suka fara yiwa innah magana, wajen ki muka xo ki fara warware sharrin da kike kullawa na sai kin fitar da ni daga gidan mijina idan ba haka ba kuma yau a yita ta kare don baxan fita daga gidan nan ba har sai an warware auren banxar jikar ki da mijina, girgixa kai innah tayi
kayya! me yasa xaku haramta abinda Allah ya haramta, Allah ne ya bawa mijinki dama ya auri mace sama da daya, me yasa xaki rika jayayya da hukuncin Allah? hannu tasa ta dakatar da innah, dakata min tsohuwar tsiya ke mijinki mata biyu ya aura ba ke kadai kike rayuwar ki ba gashi nan har kun tsufa a haka, ke da kike gidan talauci ma kika guji kishiya ballantana ni da nake a gidan wadata
ina jin abinda take fadawa innah nayi wani tsalle na dawo gabanta ina huci, cikin tsawa nima na mayar mata da martani
Ba innata ce tsohuwar banxa ba
kece babbar banxa wawiya da kika kasa kula da mijinki har sai da yaxo ya like min ya nace na aure shi, ki dube ni da kyau ni ba mummuna bace ballantana kice lika masa ni aka yi,shi ya ganni ya nace don haka ba mu xaki yiwa hauka ba mijinki xaki je ki yiwa, da yaxo nace
idan har kin cika mace mai ji da kanta mai xai sa mijinki ya gano mitsitsiyar yarinya kamata ya nace mata har ya rika kuka a kan na so shi
mun gaji da cin fuskar da kike mana, an gaya miki talauci hauka ne,wlh baxan juri wannan jahilcin da xaki rika yi mana ba, kuma miji sai an aure shi don ba ni nace kiyi sake har ya rika kallon mata ba.
sakar baki suka yi suna kallona, saboda basu taba xaton xan musu haka ba,ni kaina nayi mamakin maganganun da na rika fada mata, ji nayi na fita daga hankalina duk abinda xai faru sai dai ya faru indai a kan a taba innata ne, kamo ni innah tayi ta xaunar da ni tana min nashiha, ki daina rama abinda aka yi miki na rashin kyautawa saboda bai kamata kare yayi maka haushi ba kaima ka bishi ka rama, a fusace matar ta kamo ni ta shake min wuya wanda sai da na kusan suma saboda shakar da tayi min cikin xafin rai take min magana.
dan ubanki har kin yi girman da xaki fada min magana yaushe aka haife ki, shegiya kaxama kucakar banxa, nasan ba haka kika bar min miji ba shi yasa amma da me xai yi da ke shashasha, kuma wlh daga yau idan baki fita a harkarsa ba xaki ga abinda xai faru da ke sakina tayi na ja da baya kamar xan fadi, wani kallon raini na shiga yi mata.
cike da rashin kunya nake mata magana gara ni kucaka ce amma ke kin fi kuca kucakanci kina cewa kina da ilimi amma bakya aiki da shi banda tsabar jahilci da rashin sanin ya kamata kixo kice xa kiyi fada da ni a matsayina na yar cikin ki dube ki fa duk tsufa yaxo miki ko ta ina, amma baki san Annabi ya faku ba,kuma aure da mijinki yau aka fara baxan rabu da shi ba ko dafa ni xa kiyi ki cinye ni sai na shigo gidan ki, xagin mu ta rika yi tana aibata mu innah ce ta dakatar da ni amma ban yi niyyar kyaleta ba saboda a duniya na tsani abinda xai taba min xuciyar innah haka suka gama xagin mu suka tafi.
gaba daya muka fashe da kuka saboda masifar matar tasha kan mu bata gajiya da bala'i abinda ya fi daga min hankali yadda tace xata yi da ni idan na shigo gidanta kuka sosai muka rika yi, a dai dai lokacin baba ya dawo ya tarar da mu a wannan halin cike da damuwa ya dube mu.
meke faruwa na gan ku haka? inna ce ta fara yi masa bayanin komai ba karamin baci ransa yayi ba, cikin damuwa yake magana ina ganin lokaci yayi da mutumin nan xai sauwakewa Niimatullah cin
kashin da matar nan take mana yayi yawa kada yarinyar nan ta tare ta samu damar cutar da ita,tunda tana ganin ba tada wani gata mu kuma Kullum karfin mu karewa yake baxa mu iya biyewa wannan tashin hankalin ba don haka ko yana so ko baya so sai ya sauwake mata baxa mu iya masifa ba, fita baba yayi, ni kaina yanxu nafi son ya sake ni saboda ina jin baxan iya xama da ita ba.
su Hajiya na fita suka bushe da dariya, ina ganin wannan itace hanya mafi sauki da xa mu yi maganin auren nan saboda wlh idan muka bar yarinyar nan ta shigo xaki xama yar kallo dubeta fa tubarkalla komai ya ji ba tada wata makusa, kuma yadda suka ga xata shiga gidan hutun nan dole su rika karfafa mata gwiwa mu kuma ta hanyar yi musu tijara xamu samu mu karya auren kowa ya huta hirar da suka rika yi kenan har suka isa gida.
*jeeddahtulkhair😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©Jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Dr fatee sabitu*
*ya Allah ka bawa daughter Aysha yar london lafiya*
19
A ranar baba ya tura aka aka kira masa dattijona, a soro nayi musu shimfida cike da ladabi ya samu guri ya xauna, kallona ya rika yi yana min murmushi tare da kashe min ido da alama dai so yake nayi masa magana, banxa nayi da shi na wuce gida saboda ji nake gaba daya na tsane shi, tsakar gida na koma na barsu su yi magana da baba.
Bayan sun gaisa baba ya fara yi masa bayanin makasudin haduwar su, gyara xama baba yayi sannan ya fara yi masa magana, nasan xa kayi mamakin kiran da nayi maka Alhaji, kansa a sunkuye ya amsa kwarai kuwa baba, Allah yasa dai lafiya gyaran murya yayi sannan ya cigaba da cewa, xamu iya cewa lafiya amma ba lau ba.
cike da mamaki ya dago yana tambayar sa me kuma ya faru baba?damuwa ce ta bayyana a fuskar baba, Alhaji ina ganin ya kamata kayi hakuri mu ma mu yi hakuri ka sauwakewa Niimatullah aurenka, a firgice ya dago me kuma ya kawo wannan maganar baba? girgixa kai yayi ba komai Alhaji kayi hakuri mu ma dole ce tasa xamu fasa amma mun san kana son yarinyar nan ita ma tana sonka, amma Niimatullah bata dace da kai ba, saboda kai mai kudi ne kuma mai ilimi kuma ka fito daga babban gida, ita kuwa yar talakawa ce kuma marainiya mara gata, ina jin tsoron barin Niimatullah ta aureka saboda furucin matarka a kanta kada ta hallaka mana ita wata rana saboda na fuskanci tana da kishi da yawa shi yasa na duba naga abinda ya fi alkhairi shi ne ta bar mata mijinta, kaga a kullum karfin mu karewa yake kada a yi auren nan wani abu ya biyo baya, tunda Niimatullah yarinya ce karama har yanxu bata gama mallakar hankalin kanta ba gashi ba tada wayo ga rashin gata ko cutarta tayi ba mu da halin karbar mata hakkinta,dan haka nake rokonka dan girman Allah ka sauwake mata, saboda maganin a yi shi ne a bari, kusan xuwanta biyu gidan nan tana ci mana xarafi, har shake Niimatullah tayi har sai da ta kusa suma yanxu haka wuyanta ciwo yake, don haka mu baxa mu iya fada da abinda ya fi karfin mu ba don Allah ka saketa.
Tunda dattijo ya sunkuya bai dago ba wani gumi ne ya rika yanko masa ta ko'ina,nan da nan idanunsa suka yi jawur saboda takaici, bai san ya xai yi ba idan aka ce ya rabu da Niimatullah ba, cikin rawar murya yake wa baba magana, kayi min arxiki baba wlh baxan iya sakin Niimatullah ba, dan Allah a yi hakuri xan tsawatar mata wallahi ban san tana xuwa tayi muku haka ba, dafa kafadar shi baba yayi ka kwantar da hankalinka Alhaji wannan duk ba wani abin tayar da hankali bane, abu ne da muke so a yi maslaha saboda Allah ya sani amanar Niimatullah a hannuna take, duk wani abu da ya sameta muna da alhaki a kai kuma sai Allah ya tambaye mu wannan dalilin yasa dole a warware auren nan saboda gudun bacin rai.
Hawaye ne ya cika idon dattijo rokon baba ya fara yi a kan yayi masa alfarma ya janye maganar, duk nacin da yayi hakarsa bata cimma ruwa ba, jikinsa a sanyaye ya dubi baba.
dan Allah ina so xan yi magana da Niimatullah, cikin sakin fuska baba ya bashi amsa ba komai Alhaji ai baxan hanaka magana da iyalinka ba tunda har yanxu a karkashin ikonka take.
kirana baba yayi cike da ladabi na tsugunnah tare da cewa gani baba, cikin kulawa yace mijinki ne yake son magana da ke yana gama fada ya bamu guri, kan shimfidar da aka yi masa na xauna, sunkuyar da kaina nayi saboda yadda na ganshi yana cikin tashin hankali da damuwa karasowa yayi ya xauna kusa da ni, fadawa jikina yayi yana Hawaye tare da tallafo fuskata Niimatullah me nayi miki kike neman yanke alaka da ni? me yasa kike son na sake ki alhalin kinsan xuciyata baxa ta iya jure hakan ba, ke kika fadawa baba kina son na sake ki? sunkuyar da kaina nayi tare da cewa.
Eh na xabi hakan ne saboda hankalina xai fi kwanciya dama na dade ina tunanin hakan saboda cin kashin da matarka take mana ya fara yawa, na yanke shawarar hakura da kai indai hakan xai yi sanadiyyar farin cikina dan Allah ka sake ni ko xan huta da wulakancin da matarka take mana.
kallona yayi da jajayen idanunsa lallai baki san adadin yadda nake sonki ba Niimatullah, ke yanxu a tunaninki xan iya rabuwa da ke wallahi son rayuwata nake miki baxan iya hakura da ke ba saboda ina matukar sonki, a halin yanzu kawai kina ganin kaso ne mafi kankanta daga cikin irin son da nake maki, amma lokaci na nan zuwa da zan nuna miki tsantsar soyayya mara misaltuwa, bayan mun yi aure. ba zan ta6a mantawa da sadaukarwar da kika min ba, kina yarinya kika aure ni a matsayina na dattijo, kina tunanin xan manta da wannan sadaukarwar? don haka babu macen da xata samu gurbin soyayyar da kika samu a xuciyata, kisa a ranki baxan iya rabuwa da ke ba,ya xan yi da rayuwata idan na wayi gari bakya tare da ni, ki tuna a wajenki kawai nake samun farin ciki, yana karasa maganar ya fashe da kuka.
nima kukan na rika ni kaina nasan ina son dattijona amma hangen abinda xai je ya dawo nake yi, cikin kukan nake masa magana nasan kana sona amma dan Allah ka duba halin da xan fada ka sake ni, matarka bata kaunata tana xagina ta xagi innata me xan je gidanka nayi, ni tuni na bawa xuciyata hakuri a kan rabuwa da kai kuma ta hakura da kai.
kamo ni yayi hada da kirjinsa yana rarrashina, me yasa xaki min haka Niimatullah, kin san irin kaunar da nake miki da xaki ce sai na sake ki, indai aka takura na sake ki wlh nasan sai na rasa raina, saboda soyayyar ki ta gama yi min illah.
xame jikina nayi na nufi bakin kofar shiga gida ina share Hawaye, hada kansa yayi da bango yana ta kuka kamar karamin yaro, baxan iya jure ganin shi yana kuka ba wannan dalilin yasa na shige gida gudun kada xuciyata ta buga saboda bacin rai.
*jeeddahtulkhair😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*ina gaida ku yan group din matar DATTIJO 1,2,3 ina tare da ku kuma ina jin dadin comments dinku ana mugun tare, masoya DATTIJO kwalelanku😜*
20
A soron na barshi
ya fi kusan minti talatin yana kuka cikin kukan yake kiran sunana, Niimatullah ki tausayawa rayuwata ki aure ni, ki tuna irin yadda nake sonki da kaunar Ki,tun lokacin da na fara ganinki, kika shiga raina kin samu gurin da baxa ki taba fita ba har abada. ke ta daban ce Niimatullah, kina da wata baiwa wadda ba kowace mace Allah ya bawa ba, ina samun nutsuwa idan ina tare da ke,kada ki guje ni Niimatullah ki kusanta da ni, zan wadatar da murmushi a saman fuskar ki,zan yi kokarin wadata ki da jin dadi daga cikin nau’ikan ababen jin dadin rayuwar duniya. Ina tsanin sonki babyna baxan iya barin ki ba ya karasa maganar tare da fashewa da kuka mai tsanani.
cikin gida na shiga ina xuwa na fada gado ina kuka, ban san halin da xan tsinci kaina ba idan aka raba ni da shi, shi ne mutum na farko da ya fara koyar da ni soyayya, a Kullum burinsa ya tarairayi jaririyar xuciyata wacce bata san komai ba sai soyayyarsa da karfi na rika fadar hakan ina cigaba da kukana, innata ce ta shigo inda nake saboda taji sambatun da nake yi dafa kafadata tayi tana rarrashina, kiyi hakuri Niimatullah indai Alhaji rabonki ne xaki aure shi,mu dai fatan mu ya yiwa tufka hanci wannan matar tasa ta daina xuwa tana ci mana mutunci, nasan Malam xai sakko saboda yana son abinda kike so, a ranar cikin damuwa na wuni.
A bangaren dattijo kuwa yana komawa ya tarar da gidansa ba kowa, kwafa yayi ya samu kujera ya xauna a falo yana jiran dawowar matarsa, tunanin Niimatullah ya shiga yi da yadda xai shawo kan baba ya kyale shi ya tare da matarsa, baya jin xai iya rabuwa da ita saboda duk wani farin cikinsa ya hango shi a tare da ita, yana cikin tunanin yaji wasu xafafan hawaye sun xubo masa, hannu yasa ya share gani yayi an tsaya a kansa, a hankali ya dago ,matarsa ya gani tsaye tana yi masa wani kallo a fusace ya mike yana nuna ta da hannu, ji yayi bakinsa na rawa saboda takaicin da ya cika xuciyarsa kasa ce mata komai yayi.
cike da gadara take masa magana, naje na lalata auren yar iskar yarinyar da kake so, saboda baxan taba iya sharing dinka da wannan kaxamar yarinyar ba, kuma wlh ka sani na rika yi maka haka kenan Har abada ba kai ba kara aure, duk inda kaje neman aure sai na rika xuwa ina ci musu nutunci a haka har su yi xuciya a fasa auren, mutumin banxa Kawai mara alkawari, a fusace ya dubeta.
ni kike kira da mutumin banxa Hajiya Maryam? tsare shi tayi da ido tana harararsa na fada duk abinda xa kayi sai dai kayi, karya nayi maka ba mutumin banxan bane kana tsoho ka auro yar cikinka saboda son xuciya da kwadayi an girma ba a san an girma ba, lalata aure yanxu na fara idan xaka nemi yan mata dari ni kuma sai na lalata auren har sai ka hakura ka daina.
komawa yayi ya xauna saboda idan ya cigaba da tsayawa tsaf xai fadi wani bakin ciki ne ya cika xuciyarsa cike da fushi ya mayar mata da amsa wlh ba dan arxikin yayan da kika haifa ba da xamana ya kare da ke yau,a matsayina na uban yayanki kike kirana da mutumin banxa saboda ba ki da hankali, auren Niimatullah ne bakya so kuma kisa a ranki kamar amarya ta tare a dakinta ne, kuma ki shirya ganin wulakanci kala-kala Allah dai ya kawota da alkhairi, da sannu sai na ganar da ke kuskurenki sai kin yi nadamar kirana da mutumin banxa shashasha mara amfani, sai kin xama tamkar shara a gidan nan dama ba ki da wani amfani a wajena banda bata min rai babu abinda kike yi mahaukaciya kawai, yana gama fada mata ya wuce dakinsa.
Yana shiga daki ya jawo waya ya kira Niimatullah, ina kallon wayar na ringing na kyaleta, sai da ya kira ni wajen sau biyar sannan na dauka, ina jin yanayin yadda yake magana nasan yana cikin matsananciyar damuwa, mun kai kusan minti daya ba tare da mun cewa juna komai ba, nice nayi karfin halin kiran sunan shi.
Dattijona!! cike da damuwa ya amsa min da na'am my Niimatullah, cike da damuwa nake masa magana, idan har akwai wani abu da xan roka a wajenka bai wuce na rokeka a kan, ka amince mu kasance tare ba har abada, domin tabbatuwar mafarkin da ya jima yana bayyana a cikin baccina, ina sonka amma dole na barka tunda iyayena sun hango min matsala a tare da Kai.
Cikin sanyin murya yake min magana yanxu baxa ki tausayawa mijinki ba niima, ina cikin damuwa ko abinci na kasa ci, yanxu babu taimakon da xaki neman mana a wajen baba ya taimaka ya kyale mu muyi rayuwar farin ciki da juna,shikenan duk ginin da muka yi a baya ya rushe my Niimatullah, ki duba halin da xan shiga ki tallafi rayuwata, ji nayi hawaye sun fara xubo min hannu nasa na goge.
ina sonka dattijona amma baxan iya aurenka ba saboda mugun halin matarka saurin dakatar da ni yayi, tsaya Niimatullah bana son kina kawo tunanin wannan matar a ranki, babu abinda ta isa ta hana game da auren mu rayuwa mai dadi xa kiyi da mijinki, ki tallafi rayuwata ki shawo min kan innah da baba su yarda da ni, a sanyaye na amsa da to xan yi insha Allah sallama muka yi da shi ya kashe wayar.
ina ajiye wayar bai fi da minti biyu ba naji shigowar message din shi, a hankali nasa hannu na bude.
*Ina fatan xuwan ranar da xan kasance shinfide a saman kafadun ki na kwana a cikin dakin Ki, na kasance a tallafe bisa hannuwan ki,wato ranar da xa a kirani da angon ki. Ki duba kaunar da nake miki ki shawo min kan baba, ina sonki ki huta abar alfaharina*
Ina gama karantawa naji wani hawaye ya xubo min na tabbatar da cewa mijina yana sona idan na bar shi ban yi masa adalci ba.
Wajen innata na koma fadawa nayi jikinta ina kuka, cike da tausayawa ta dube ni, me ke faruwa da ke Niimatullah? cikin kuka na amsa mata da dattijona innah kada ya mutu ta sanadina na samu alhaki, yana cikin damuwa yace na roke ku, ku janye maganar nan dan Allah.
cikin kulawa inna ta dube ni tare da girgixa kanta, kiyi hakuri Niimatullah xan samu malam nayi masa magana nasan xai janye idan yaga halin da kuke ciki,ni kaina bana son auren nan ya tarwatse saboda Alhaji mutumin kirki ne Kuma tsakani da Allah yake sonki kiyi hakuri Insha Allah xai sakko, rarrashina ta rika yi har sai da hankalina ya kwanta.
wayar da ke gefen mu ce tayi ringing, hannu innah tasa ta dauka,sallama tayi cikin kulawa aka amsa mata tare da cewa dan Allah ina neman Niimatullah ne, da sauri innah ta miko min wayar na kara a kunnena tare da yin sallama
muryar matar da take min gyaran jiki naji cikin ladabi na gaida ta, tambayata dalilin da yasa kwana biyu banxo makaranta ba ta fara yi, muryata na hardewa na bata amsa saboda bakin cikin da ke cike a raina, an fasa auren shi yasa na daina xuwa.
A raxane ta tambaye ni me kike fada min haka Niimatullah bana son shirme fa, ina innar ki?cikin kuka nace gata nan kusa da ni, da sauri tace min mika mata wayar xa mu yi magana.
cikin girmamawa take wa innah magana, sannu baba ya gida ya yara, nice matar da nake gyarawa Niimatullah jiki naga kwana biyu bata xo ba shi yasa na kira nasan jiki da jini, sai kuma yanxu da na tambayeta dalilin rashin xuwanta naji tana min wata magana wai an fasa auren nata menene gaskiyar abinda take fada min baba? kana ganin Innata xaka gane tana cikin damuwa don damuwar har a maganarta ta bayyana, bayani ta fara yi mata ba karya Niimatullah ta fada miki ba gaskiya ne abinda ta fada, cike da mamaki take tambayar innata, to menene dalilin hakan baba?
sauke numfashi Innah tayi mun fasa ne saboda muna ganin hakan shi ne abinda xai fi xama Alkhairi a gare mu da kuma ita, mijin Niimatullah yana sonta nasan kema kin san haka, amma kishiyarta ce ba tada kirki xuwanta biyu gidan nan tana ci mana mutunci har tana ikirarin xata hallaka Niimatullah wannan dalilin yasa muka fasa.
cikin nutsuwa malama ta fara yiwa Innah bayani, ina ganin ba haka ya kamata a yi ba baba, tufkar kawai xa a yi hanci, amma batun a fasa ma bai taso ba, saboda xa a cutar da xuciyoyi biyu da suka dade suna son juna, tunda matsalar nan ba daga wajen bawan Allahn take ba bai kamata a fasa ba, saboda idan aka fasa an ji tsoro kuma an bata damar ta cigaba da yin haka nan gaba, ita wacece da xata ce ita kadai xata rayu da mijinta,tunda Allah ya bashi dama kuma yana da ra'ayin kara aure dole yayi, baxai yiwu a ce duk gyaran da muka yi ya tashi a banxa ba baba, gobe insha Allah xan xo tare da Alhajin duk inda matsalar nan take sai an warwareta, godiya Innah tayi mata sannan suka yi sallama.
ba karamin dadi naji ba da jin kalaman malama nasan tana xuwa komai ya xo karshe insha Allah.
*jeeddahtulkhair😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Asma'u sharif Gambo yako (maman Sharifa)*
*Ya Allah ga yar uwata abar alfaharina sister Suhaima M Bello ba tada lafiya, ya Allah ka bata lafiya kasa ya xama kaffara a gareta👏🏼*
21
Baba na dawowa innata ta sanar da shi yadda suka yi da malama, shiru yayi na wani dan lokaci yana naxarin maganarta a hankali ya dago da kansa yana duban mu ni da innah, ni kuwa gabana sai faduwa yake saboda ban san irin amsar da xata fito daga bakin sa ba, cikin nutsuwa ya fara yi mana magana.
ina so ku fahimci wani abu ko kadan ban taba jin na tsani auren Niimatullah da Alhaji ba, hasali ma xan fi kowa farin ciki idan aka ce sun yi aure saboda nasan kyakkyawan hannu na kai ta, baxa mu taba yin da na sani ba, amma abinda xa a duba matsalar matar nan da irin furucin da take yi a kanta, nasan irin wadannan matan ba tun yanxu ba idan suka yi yaki da baki suka ga bai ci ba komawa suke su bi mutum ta kasa, shi yasa bana son abinda xai xo ya tayar mana da hankali muna cikin xaman mu lafiya.
ji nayi kamar nayi kuka wata sabuwar soyayyar Dattijona ce take dada bijiro min ban ki a ce na tashi na koma gidansa da rayuwa ba, duk wata matsala da baba yake hango min ni a yanxu bana ganinta,saboda ko kadan Allah ya cire min tsoron matarsa kuma ina jin xan iya yin fito na fito da ita ba tare da wata fargaba ba, nasan nayi nisa a xuciyar mijina wanda bata isa ta kamo ko rabin son da yake min ba, kaina a kasa na fara yiwa baba magana.
ni dai baba idan da yadda xa a yi dan Allah ka bari na aure shi wallahi ina son mijina, cike da mamaki innah ta dube ni, inye Niimatullahi har kin san dadin mijinki, lallai yaran xamani sai dai a barku kawai, shi kuwa baba kallona kawai yake y rike baki Innah ce take ta bayani.
malam tunda har Niimatullah ta furta mana tana son mijinta ina ganin ba mu da wani xabi wanda ya wuce mu tattara ta mu kai ta dakinsa, girgixa kai baba yayi, nima tunanin da nake yi kenan shi yasa kika ga na kasa magana, amma xan nemi Alhaji yaxo ya tattara ta su tafi
kuka na fara yi cike da shagwaba nake magana a tattara ni fa kace baba sai kace wata kayan wanki ni Allah sai ma na fasa auren, murmushi baba yayi ko kin fasa sai an kai ki tunda ina yi miki gata har kina cewa kina son mijinki ni ba ruwana dole sai kin tare, kuka na fara yi a kan ni baxan tare ba na fasa tashi baba yayi ya bar mana wajen, kan cinyar innah na fada ina cigaba da kukana.
Washe gari Dattijo da malamar mu suka iso gidan mu a tsakar gida suka same ni ina hada kwanuka, sauri nayi na sanya hijabina saboda baxan iya jure kallon da yake bina da shi ba, a dakin innah nayi musu shimfida, shiga malama tayi ta xauna shi kuwa dattijona a tsakar gida ya tsaya yana cigaba da kare min kallo, cike da tsiwa nake masa magana.
menene ka tsura min ido kamar baka saba ganina ba, murmushi yayi tare da matsowa daf da ni riko hannuna yayi cikin sigar shagwaba yake min magana shi ne don kin ganni kike wani saka hijabi ko,naga dai komai na jikin ki mallakina ne to me xaki boye min?
Harar shi nayi tabdi wallahi ba mallakinka bane nawa ne ko innah xa a tambaya tasan da haka, murmushi yayi gami da jan kumatuna kina da dabaru na sanya ni murmushi my Niimatullah ko da a ce ina cikin fushi idan kika yi magana sai naji wni snyi a raina,kin zamo wata ta daban a gare ni, shi yasa ina ganin ki dukkan shaukina yake tashi,bana gane cewa ni namiji ne sai ina tare da ke, don haka ki daina tuhumata idan ina kallon ki, tunda kina sona ko matar dattijo?a hankali na gyada kaina alamar eh, murmushi yayi sannan ya cigaba da magana nasan da cewa tunanin ki a kullum bai wuce neman hanyar da xaki inganta rayuwata ba ki bani farin ciki mara misaltuwa,wannan dalilin yasa na sadaukar miki da soyayyata kuma nake fatan kasancewa da ke har abada my Ni'ima, baxan iya daina kallonki da begenki ba har sai ranar da numfashina ya kare
duk maganganun nan da yake yi kaina na kasa saboda kunyarsa gaba daya ta kama ni,maganar da innah tayi masa ne yasa ya dawo hankalinsa, a sanyaye ya cika ni tare da sumbatar hannuna, sai na fito my Niimatullah
na sake ki ne ba dan na koshi da ke ba,sai dan xuwa na samo mana mafitar yadda xamu rayu da juna har abada, sakina yayi na koma gefe na xauna.
Tattaunawa suka fara yi a kan maganar tarewa ta a gidan dattijo, kwala min kira innah tayi da hanxari na karasa dakin cikin ladabi na tsugunna tare da cewa gani innah, cike da kulawa ta dube ni kira mana malam a waje, takalmana na saka ina fita naci sa'a na same shi, yana shigowa malama ta fara magana.
mun xo ne baba a kan maganar tarewar yarinyar nan, naji ana cewa kun fasa shi ne naxo na baku hakuri a kan bai dace a yi saurin yanke hukunci haka ba,tunda dai suna son junansu, kuma maganar kishiya baxa ta tsoratar da mu ba tunda yarinyar nan mijinta na sonta duk wani abu da xai cutar da ita xai yi kokarin kawar mata da shi.
gyara xama baba yayi, ni dama ban xafafa ba Hajiya fatana dama yaxo ya fada mana irin matakin da xai dauka a gidan sa saboda ina jin tsoran abinda xai je ya dawo ko ba haka ba.
cike da xumudi dattijo ya fara magana, wallahi baba babu wata matsala da xa a samu duk wani matakin da ya kamata na dauka naje na dauka, na yi mata magana a kan ba ita ba Niimatullah idan kuma ta cigaba xa tayi a bakin aurenta.
saurin dakatar da shi baba yayi, a'a ba a haka Alhaji kada auren nan yayi sanadin rabuwar ka da uwar yayanka idan kayi haka baka yi adalci ba sannan duniya xata xage ka mu ma xata xage ma, a xaci don ka auri jikar mu ne kayi mata wannan wulakancin, baxa a duba girman laifin da tayi ba namu xa a gani, don haka kada ka fara aikata haka, kawai kai dai kayi niyyar tsayar da adalci a gidanka sai kaga Allah ya taimake ka amma batun kace xaka saketa ma bai taso ba.
cike da ladabi dattijo ya amsa da insha Allah xan kokarta baba, na gode da wannan shawarar da ka bani, haka suka cigaba da tattaunawa daga karshe aka tsayar da lokacin tarewar mu nan da sati biyu masu xuwa, ba karamin dadi dattijo yaji ba, nima farin cikin ne ya kama ni saboda duk kusan hirar da suke yi a kunnena ake yinta.
tashi suka yi xasu tafi, a tsakar gida dai suka kara tarar da ni, kirana malama tayi ta fara yi min nasiha.
kinga yanxu tarewar ki ta matso don haka gyaran jiki xamu rika yinsa ba dare ba rana idan kuma baki tsaya an gyara ki ba kin xauna kina gaddama kishiya ta raina ki,ni ba ruwana don haka yanxu duk abubuwan da na baki ki mayar da hankali ki shanye, idan kin xo gobe xan baki wasu ki kara sha,so nake ki rikita mijin nan naki ya kasa gane hanyar garin su, dariya muka yi gaba daya har mun yi sallama ta tafi ta dawo ta kira ni, kije mijinki na son magana da ke, makale kafada nayi ni Allah bana son xuwa, hararata tayi kinga irin abinda yake hada ni da ke ko wuce mu je nace miki.
wucewa nayi na tafi a cikin mota na same shi don haka ya bude min motar na shiga tare da rufo murfun motar.
*masu karatu ku nemi littafin kalubale na juwaira domin fadakarwa nishadantarwa da kuma wa'axantarwa kada ku bari a baku labari*
*jeeddahtulkhair😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Salma Nura*
24
Washe gari ma sai da aka sake gyara ni sosai kyawuna ya kara fita duk inda ka kalle ni sau daya sai kso ka kara kallona, shi kuwa dattijona kullum yana kan hanyar xuwa ganina, a lokuta da dama idan yaxo da kyar yake tafiya, saboda yadda yake yaba kyauna kullum da rigima muke rabuwa.
yau da sanyin safiya na shirya don xuwan wajen kunshi, soro na fita na xauna na hada kaina da gwiwa saboda kaina yau ya dau caji, ina jin ciwo sosai a raina idan na tuna gobe xan bar gida, wasu xafafan hawaye ne suka rika kwarara a fuskata tambayar kaina na shiga me yasa har na amince da auren dattijo gashi nan yana son raba ni da rayuwar gidan innata, ji nayi an kira sunana a hankali na dago kaina, dattijona na gani tsaye yana min murmushi fuskar sa cike da damuwa yake tambayata lafiya kike kuka my Niimatullah?lumshe idanuna nayi cikin kuka na bashi amsa, ina ji a raina kawai xan fasa auren nan bana son rabuwa da innata, rarrashina ya shiga yi gami da kawo min hadisan da suke magana a kan muhimmancin aure a haka har hankalina ya kwanta xuciyata tayi sanyi.
Hannu yasa ya tayar da ni tsaye, ina rungume a jikinsa har muka isa bakin mota, bude min murfin motar yayi na fara shiga sannan ya shigo, kallona ya rika yi a xahiri naji yana godiya ga Allah,Allah na gode maka da wannan babbar kyautar da ka bani Allah ka bani ikon riketa amana, shafawa yayi sannan ya dube ni yana min murmushi
Kece kaddarar da na jima ina tsimayin tarar da ita a rayuwata, zan kasance a duk inda kike Niimatullah,zan tsaya a duk inda kika tsayar da ni. Ina sonki, adadin son da kalmomi ba zasu iya siffantawa ba,
xan kasance mai
baki kulawa da kuma kaucewa dukkan abinda zai sanya ki a damuwa fatana ki tabbata a cikin farin ciki,ban son irin dadin da xan ji ba idan na ganki gobe a dakina, fatana dai Allah ya bamu xaman lafiya.
amsa masa nayi da ameen muna xuwa ya sauke ni a kofar gidan,kudi ya dakko ya bani, cike da shagwaba nace masa baxan karba ba, dago fuskata yayi yana min murmushi ki karba my Niimatullah kinga ba a yin kunshi kyauta, langwabar da kaina nayi to ka rage kudaden sun yi yawa, murmushi yayi tare da cewa ban san me yasa kike tausayina ba Niimatullah, kaina a kasa na amsa masa saboda ka xama mijina kuma innah ta fada min tausayin miji abu ne mai kyau, girgixa kai yayi yana murmushi gaskiya innah ta iya tarbiyya Allah ya saka mata da aljannah da take kokarin saita min uwar yayana. fitowa nayi na shiga gidan kunshin.
ba tare da bata lokaci ba aka fara yi min, gaskiya kunshin yayi kyau domin ya dace da kafata sosai, da misalin karfe hudu ya iso daukana, tun daga nesa yake min murmushi jikina a sanyaye na karaso wajen sa tare da cewa an gama, shafa fuskarsa yayi tare da cewa miko min hannun na gani, makale kafadata nayi a'a baxan bayar ba, jan hancina yayi me yasa kike min rowar jikinki kin xama tawa fa Niimatullah babu abinda yayi saura. cike da tsiwa nace Allah da akwai abinda yayi saura tunda saura kwana daya naje gidan ka, murmushi yayi tare da jan hannuna to naji taho mu tafi bana son wannan rigimar taki.
A kofar gida ya ajiye ni ya wuce gidansa, ina shiga gida nayi sallah na fada bandaki nayi wanka sannan na koma dakin innah na kwanta kasancewar yanxu bana son hayaniya nafi son na kebe ni kaina na rika tunanina, yau ko baccin kirki ban samu nayi ba saboda bakin cikin xan bar gidan innah cikin dare na tashi ina kuka ina bankwana da gadon da nake kwana.
rana bata karya sai dai uwar diya taji kunya, A yau lahadi 14-10-2018 ta kama ita ce ranar da xa a kaini dakina, da kyar aka yago ni nayi wanka saboda duk wata gwiwa ta jikina tayi sanyi, yan uwa da abokan arxiki daga gurare daba-daban sun halarci bikina, duk wanda yaji labarin irin son da dattijo ke min sai yayi mana fatan alkhairi da samun xuri'a ta gari, anci an sha duk abincin da aka ci a wajen dattijo ne yasa aka kawo mana daga 10 to 10 restaurant, an yi komai cikin rufin asiri.
xaune nake a daki na xuba uban tagumi ina tunani, cikin nutsuwa aka yi sallama a hankali na dago don ganin mai sallamar daya daga cikin kannen mahaifiyata ne, gefena ta samu ta xauna, tashi ki kintsa Niimatullah an kawo motocin tafiya gidan ki, a xabure na dago na kalleta, tun yanxu xa a tafi ni gaskiya yayi wuri a bari sai an yi sallar magariba, cikin kulawa take min magana ki tashi mu je ga ruwa can an kai miki bandaki gara ki shirya da wuri yanxu xaki ga magaribar tayi, hawaye ne suka cika idona cikin kuka nake mata magana, wai dama da gaske ne sai an kai ni gidan mutumin nan Aunty, ni wlh ba inda xan je. lallaba ni ta shiga yi har sai da na tashi na tafi ina wankan ina kuka.
Bayan na kammala na fito na sanya kayana, wajen baba aka kaini inda ya fara yi min nasihohi masu ratsa jiki a kan biyayyar aure da kuma kyautatawa miji bayan ya gama aka kaini wajen innah don sallama da ita da kuma yi min nasiha.
muna hada ido da ita ta fara kuka da sauri na fada jikinta muka rungume juna, cikin kukan take min nasiha ki bi mijinki sau da kafa Niimatullah, duk abinda yace kiyi masa kiyi banda gaddama, sannan kuma ki xama mai hakuri da kau da kai, kada kice duk abinda kika gani sakin yi magana, kiji ki qi ji, ki gani ki qi gani, ki xama mace mai kawaici da hakuri, kada ki bari mijinki yaji wani abu mara dadi daga gare ki, ki kiyaye masa ganinsa da jinsa da hancinsa, abinda nake nufi da ki kiyaye masa ganinsa shi ne kada ki bari yaga wani abu na aibu a gare ki, abinda nake nufi da ki kula masa da jinsa,kada ki bari ki fada masa wata magana mara dadi da har xata bata masa ransa, duk abinda xai ji daga gare ki ya xama mai dadi ne, abinda nake nufi da ki kiyaye masa hancinsa kada ki bari yaji wani wri daga gare ki kullum ki kasance cikin tsafta da kamshi ki kula da tsaftar hakoran ki, Allah ya baki sa'a yasa kin shiga a sa'a Allah ya kare ki daga dukkan sharri yasa ki xama tsohuwar gidansa.
kuka sosai muka rika yi ni da innah da kyar aka raba ni da ita aka saka ni a mota, gidansa da ke unguwar bompai aka kaini bangare biyu ne a gidan, don haka bangaren kishiyata aka fara kaini inda aka damka mata amanata, a wulakance ta karbe mu amma duk da haka ba wanda ya kula da abinda tayi mana.
kai tsaye bangare na aka wuce da ni, ina shiga na godewa Allah da irin namijin kokarin da dattijona yayi min,ko iyayena masu hali ne iya abinda xa a saka min kenan a dakina komai yaji, daya daga cikin dakunana aka shigar da ni inda aka xaunar da ni bisa gado, bayan an yi addu'a an shafa kowa ya watse ya bar ni ni kadai, kuka na ne ya tsananta na rika kiran innata, tashi nayi na fara kewaye gidan dakuna ne guda uku gaba duyan su an saka masu kayan gado na alfarma, kujeru na ma duk masu kyau ne wadanda aka yi musu ado da yadi launin orange sai kuma pillow din su da suka kasance launin baki, kitchen dina ma cike yake da kaya gwanin sha'awa, taku naji alamar xa a shigo wajena da sauri na koma gado na nade kaina a mayafi.
*jeeddahtulkhairi😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Ummy xie ina godiya da abin arzikin da kika yi min*
23
kwanci tashi asarar rai, komai aka sawa rana wata rana sai yace, yau ya rage saura kwana uku na tare a gidan dattijona, tun safe na tashi ina kukan rabuwa da innata nice har da su birgima, wani irin kaunar gida ne naji ya kamani sai na tsinci kaina cikin rashin son nisa da innah da baba.
innah ce ta shigo dakin da nake rarrashina ta fara yi gami da kwantar min da hankali, kiyi hakuri niimatullah duk ya mace yar gidan wani ce, mu ma duk haka aka rabo mu da gidajen iyayen mu tun ban kai kamarki ba gashi nan yanxu har abin ya xame mana jiki, kiyi hakuri ibada xaki tafi Allah xai baki kada, cikin kuka nake magana ni na fasa samun ladan innah a barni a wajen Ki na cigaba da xaman, ko kuma ki biyo ni gidan da xan xauna.
Cike da kulawa ta dube ni,imar ai ba a haka Niimatullah yadda na Saba kema haka zaki saba a hankali, kukana na rika yi har da majina.
A dai-dai lokacin ne malamar da ke min gyaran jiki ta iso, gaisawa suka yi da innah cike da kulawa take min magana.
"niimatullah me ya same ki kike kuka haka har da su majina" idanuna cike da hawaye na dubeta, malama dama idan xa a yiwa mutum aure dole ne sai ya bar gida? Dan Allah ki roki dattijo ya kyale ni a wajen innata.
Dariya ta rika yi sosai lallai niimallah da sauran ki, a ina kika taba ganin an yiwa mace aure ta xauna a gidan su, ko a garin gaba-gaba ba a taba yi ba ballanta a wajen masu hankali, dole sai kin bar gidan innah ta haka ne xaki fi samun ladan da kowace matar aure take samua gidan mijinta, idan aka barki a nan me aka yi kenan ai anyi ba ai ba.
Kuka na cigaba da yi ina shura kafata ni a lallai baxan tare a gidan dattijo ba,kiran wayar innah aka yi da sauri ta mika hannu ta dauka, dattijona ne ya kirata yake fada mata cewa ya iso tare da wadanda zasu jera min kayan dakina baya so ya ka isu gidan kai tsaye ba tare da an samu wani wakili daga bangarena ba, saboda gudun gorin matarsa, godiya innah ta rika yi masa har da dan kukanta tana sa masa albarka.
Yan uwan mamana daga bichi duk sun iso don haka aka samu wasu suka tafi jera min dakina
dakin innah muka shiga inda aka fara gyara ni, bayan ta gama shafa min wasu abubuwa ne ta bani wani abu a kwalba wanda take fada min cewa tsumi ne da ke karawa mace ni'imar jiki, har sai da ta koya min hadinsa, inda ta fada min cewa xan samu sassaken baure da kanumfari da citta kadan da mazarkwaila da minannas da kuma, xan fara dafa sassaken bauren ne idan ya dahu na tsame shi na xuba kayan hadin da ta lissafa min a baya, idan ya dahu na sauke ta koya min ne kasancewar tana so na dauwama ina yin shi. godiya nayi mata duk da cewa ban gane abinda take nufi ba game da amfanin abinda ta fada min.
Bayan na kammala shan wannan tsumin da ta bani lalle ta dakko ta matsa lemon tsami ta xuba gishiri da kuma man zaitun kadan murje min jiki ta shiga yi sannan ta fada min amfaninsa don gyaran jiki ne, kuma ta fada min larabawa da mutanen sudan sukan yi amfani da wannan hadin don gyaran jikin su. tayi min amfani da turaruka masu kyau da kamshi duk wata gaba ta jikina sai da aka shafa mata turare.
Daga karshe ta dakko min wani hadi na musamman wanda ta fada min cewa na gyaran breast ne kuma muddin mace ta juri amfani dashi breasts dinta baxa su taba faduwa ba, shi ma ta fada min cewa larabawa ke amfani da shi, amma bata koya min hadin ba saboda tace sirrin sana'arta ne.
bata kammala gyara ni ba sai wajen sallar Magariba nayi kyau na fita, kana matsowa wajena xaka ji ina tashin kamshi na musamman, daga karshe taja kunnena a kan daina amfani da ruwan sanyi wajen tsarki ta koyar da ni dafa ganyen magarya da lalle, tace na rika amfani da su a lokuta da dama saboda rigakafi ne na kamuwa daga cutar infection.
Ba karamar godiya nayi mata ba, innah kuwa sai sa mata albarka take yi saboda malama tana iyakar kokarinta wajen ganin na xama sarauniya a wajen dattijona.
bayan nayi sallar isha'i na koma daki na kwanta saboda ba karamar gajiya nayi ba, ga tunanin barin gida da ya sanya jikina yin sanyi, ji nayi kamar xaxxabi ke shirin kama ni, innah na gani ta shigo kiran sunana tayi niimatullah tashi kije soro mijinki yazo yana son magana da ke.
Bata fuska nayi haba innah bacci fa nake yi kice masa kawai bana nan, kallona innah tayi tare da hararata bana son gaddamar nan fa niimatullah tashi kije kika sani ko abu mai muhimmanci xai fada miki, raina a bace na tashi na nufi soron, a tsugunne na same shi da alama ya gaji da tsayuwa ne shi yasa ya xauna.
karasawa wajen shi nayi tare da dan taba kansa a hankali ya dago ya dube ni yana murmushi sai an ja min aji xa a xo ko niimatullah?
Cike da shagwaba nake masa magana, ba kai bane ka tashe ni ina baccina mai dadi, tashi tsaye yayi yana dubana tare da yin murmushi
ke da kin kusa xama tawa wata rana ma baccin xan hana ki yi gaba daya, cike da mamaki nake kallonsa Allah baka isa ka hanani baccina ba tabdi jam kayi kadan yaro.
Murmushi yayi tare da lakace min hancina, xaki ga nayi kadan yarinya saura dai kwana uku Ki shigo hannuna don haka ki daina tsiwa da cika baki, kallon shi nayi kamar xan kuka, Allah tunda haka kace sai na fasa auren tunda xaluntata xaka rika yi.
Hannuna ya riko yana min murmushi ina matukar sonki baxan iya xaluntarki ba babyna, kuma da nace zan hana ki bacci ai ba wani abu bane duk soyayya ce xata sa hakan, amma fa kema a lokuta da dama kina hana ni bacci, da sauri na dube shi yaushe na hana ka bacci banda sharri fa.
dariya ya rika yi min wallahi kina hana ni niimatullah ko baki sani ba? da sauri na amsa masa da eh fada min lokaci da ranar da na hana ka.
cikin salon soyayya yake min magana, idan dare ya tsala na juya ban ganki a gefena ba sai tunanin ki da shaukin ki su hana ni runtsawa, ko yau din nan ban yi bacci ba saboda begen ki.
Turo baki nayi Allah ba kada kunya dattijon nan, murmushi yayi tare da kai hannu xai kamo ni, da sauri na kauce, zaki ga ba nida kunya yanxu baki fara ganin komai ba my ni,ima sai kin shigo fadata.
hakuri na shiga bashi, kayi hakuri to kana da kunya mantawa nayi na fada, murmushi yayi tare da riko hannuna ina sonki niimatullah ga tsiwa ga tsoro.
cike da shagwaba na fara yi masa magana ka fada min abinda ya kawo ka kaga sauro har ya fara cizona, dan murmushi yayi gami da shafa farin gemunsa wanda ya sha gyara, yi hakuri mai niimatullah nima ba a son raina na kira ki yanxu ba don nasan kin gaji da yawa, dama xuwa nayi mu yi magana a kan abubuwan da xa a yi a lokacin bikin mu.
langwabar da kaina nayi ni babu abinda xan yi kawai innah ce xata gayyato kawayenta, ni kaga ko kawayen ma ba nida su.
Murmushi yayi to ni dai sai an yi ko baki da su sai kin nemo su duk inda suke, bata fuska nayi xan yi kuka
A'a ni dai ka bar kudinka tausayinka nake ji kaga ka kashe min kudi masu yawa, yau ma ka siya min kayan daki ka bar hidimar haka kada kudinka ya kare mutane su ce wayo nake maka.
Dariya na bashi sosai kina burge ni da yawa idan kika xaro wani zancen, waye xai ce xaki min wayo kin ganki fa yar karama, harar shi nayi ka daina kallona haka idan na tashi girma sai na fika kiba
xaulayata ya rika yi, duk nacin da yayi a kan ya hada min dinner naki yarda, da xa mu yi sallama ya kirgo kudade masu yawa ya bani wadanda baxan iya fadar adadinsu ba kasancewar ban tsaya na lissafa ba sallama yayi min ya wuce gida.
Innah na dankawa kudin ko komawa ta kansu ban yi ba,saboda babu wani abu da zan yi da su, komai innata tana iya bakin kokarinta wajen ganin ta faranta min.
*jeeddahtulkhair😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Zainab Zubairu (Mrs Mustapha Ali Busuguma)*
26
Ban fito ba sai da naji ana kiran sallar asubah, leko da kaina na rika yi ko xan ganshi tsaye yana jirana, A hankali na bude key na fito tarar dakin nayi ba kowa don haka hankalina kwance na koma na xauna, ban kwanta ba sai da nayi sallar asubah, bacci mai nauyi ne ya dauke ni kasancewar jiya ban samu na rintsa ba.
shi kuwa dattijo dakinsa ya koma ya kwanta yana tunanin yadda xai bullowa al'amarin Niimatullah, wani irin kwadayinta da tausayinta yake ji banda haka babu abinda xai hana shi karbar hakkin shi a wajenta, tashi yayi ya nufi bandaki ya yi wanka sannan ya fita masallaci don yin sallar asubah yana idarwa ya nufi dakinta, kwance ya tarar da ita tana ta sharar bacci, a hankali ya taka har ya isa wajen da take, wani kyau take yi masa idan tana bacci, matsawa yayi ya xauna a gefenta yana shafar gashin kanta xuwa bayanta duk abin nan da yake yi bata san a duniyar da take ba saboda baccin da yayi awon gaba da ita, murmushi yayi gami da lumshe ido a xahiri yace ina sonki Niimatullah.
wannan maganar da yayi ita ta farkar da ni daga baccin da nake yi,da sauri na tashi jikina na rawa abinda ya fara fitowa daga bakina shi ne kayi hakuri dattijona, murmushi yayi hannun shi rungume a kirjinsa, menene kika wani xabura kin san dadewar da nayi a nan kina bacci?da sauri na amsa masa da a'a, shafa bayana yayi ki daina jin tsoron babu abinda xan miki da nayi niyyar yin wani abu da ke da tun daxu labari ya sha banban.
kwantar da kaina nayi a kirjinsa ina shafa fuskarsa, na gode dattijona yaushe xaka kaini gida naga innata, tsare ni yayi da ido tunda baki bani abinda nake so ba yaushe xan kai ki gida wani ya ganki ya xaci har yanxu budurwa ce, ki bani dama na xamar da ke matar aure a ranar da kika xama xan kai ki gida.
dan turo baki nayi, yanxun ma ai matar auren ce ni Allah baxan yarda da wannan dokar taka ba, daga kafada yayi tunda baki yarda ba shikenan haka xaki yi ta xama a gidan nan, ko xaki shekara dari baxa ki je ko ina ba muna tare a nan.
kuka na fara yi, dan Allah ka bar ni naje naga innata, dago fuskata yayi wai baki ji abinda nace miki bane Niimatullah?cikin kukan nace naji amma dokar taka ce tayi min tsauri dan Allah kayi min afuwa, murmushi yayi xan miki babyna ai ina sonki amma yanxu dai ki bani dama na nuna miki irin son da nake miki, shafa jikina ya fara yi tare da kokarin cire min kayana da karfi na kwala ihu Allah ka bari na hakura da xuwa gidan, nan da nan naga yanayinsa ya fara sauyawa kokawa muka shiga yi da shi sosai da kyar da magiya na samu kaina, sauka yayi daga gadon yana kallona ina sha'awar ki Niimatullah amma kina ja min rai, duk ranar da kika shigo hannuna xa kiyi baya ni dallah-dallah.
turo baki nayi xan fara kuka me kake nufi da wannan sha'awar ne ni wlh bana so kake fada min, kan gadon ya dawo yana kallona tare da rike hannuna, ina sha'awar hannunki Niimatullah mikewa nayi ina dukan kasa Allah bana so dattijona, murmushi yayi wannan tsallen da kike min ma sha'awa yake bani, cigaba da buga kafata nayi sake dago fuskata yayi komai na jikin ki sha'awa yake bani, kuka na rika ina cewa bana so.
mayafina naja na dauki akwati nace masa sai na tafi gida, ina isa bakin kofar na ji ta a kulle, cike da tsokana yake min magana ki tashi ki tafi ki gayawa innah yadda muka yi da ke,ita ma fada xata yi miki idan da duka ma sai ta hada miki da shi, dawowa nayi na fara yi masa magiya a kan ya daina fada min irin wadannan maganganun, lallashina ya shiga yi daga nan ya fara shafa ni gami da aika min da wasu sakonni, matse ni yayi jikin bango yana mayar da numfahi duk ihun da nayi akan ya sake ni amma yaki sai da ya gama jagwalgwala ni sannan ya kyale ni.
Bayan mun yi breakfast, ya ja hannuna muka tafi bangaren kishiyata a xaune muka sameta ta dora kafa daya kan daya wani irin kallo take bina da shi,ni kuwa ina manne jikin dattijona na dora hannuna a kan kafadar shi saboda bana son na rika hada idanu da ita, waje muka samu muka xauna cike da kulawa yace na gaidata, ban yi masa musu ba na gaida ita, a yatsine ta amsa min gyaran murya yayi sannan ya fara magana.
Alhamdulillah an yi biki lafiya an gama lafiya ga amarya an kawo dakinta don haka hajiya ina kira a gareki ki rike ta amana ki dauketa a matsayin yar da kika haifa kada ki rika yi mata abubuwan da bai kamata ba, kuma idan kika ga xata karkace ki rika yi mata fada, domin diya ce a wajenki, ke kuma niimatullah ki riketa a matsayin mahaifiyarki duk abinda xa kiyi ki rika neman shawarar ta ina addu'ar Allah ya hada kanku ya baku xaman lafiya Allah ya bani ikon yin adalci a tsakanin ku, wani kallo ta dago tayi masa, daga murya tayi ta fara yi masa magana.
kai saurara kaji baxan karbi amanar wannan yarinyar mai kama da karuwai ba dubi fa wai amarya ce amma kalli yadda ta wani rukunkumeka, wannan karuwar xaka bani amana sam baxan karba ba wlh xaman aure taxo yi kowa yaji da kansa, tashi tayi ta bar mana dakin, fuskarsa cike da damuwa ya dube ni kiyi hakuri niimatullah kiyi mata biyayya kinga ta haifeka. gyada kaina nayi alamar eh har ya tashi xamu tafi na saka masa kuka cike da kulawa ya dube ni me yake damunki Niimatullah cikin shagawba nace ni sai ka goya ni baxan tafi da kafata ba, sunkuyawa yayi ya dauke ni a bayan sa ya fito dani ta cikin window ta hango ya dauke ni, ji nayi tana xagina tana aibata mu, shi kuwa ko ta kanta ma bai bi ba, kai tsaye dakina muka wuce muna shiga ya dire ni a kan gado.
kallona ya shiga yi kinga irin halin da nake ciki a gidan nan niimatullah don haka fa na auroki ki share min hawayena ki cigaba da bani hakkina na aure, amma gashi nan kema kina guduna, shafa gashin da ke kewaye a fuskarsa nayi,ba gudunka nake yi ba dattijona dan Allah kayi hakuri ni bana son abin ne gaba daya, rarrashina ya shiga yi yana fada min muhimmancin hakan ga rayuwar ma'aurata da kuma irin halin da xai shiga a duk lokacin da na hana shi kaina, hirar mu muka rika yi cikin farin ciki da annashuwa.
*follow me wattpad @jeeddahtulkhaeer Tijj*
*jeeddahtulkhair😘*
[10/18, 11:22 PM] It'z B Y ebrerheem: 💋💋💋💋💋
*MATAR DATTIJO*
💋💋💋💋💋
*©jeeddah Tijjani*
*Adam*
*(jeeddahtulkhair)*
*follow me on instagram @jeeddahtijjani*
*dedicated to Aysha sammani Alatu (maman kauthar) ina miki murnar samun baby Allah ya raya shi*
*ya Allah ka bawa diyata Aysha yar London lafiya*
25
Dattijo ne ya turo kofar dakin ya shigo sanye yake da farar shadda wadda tasha aiki da farin xare, takalmin dake kafarsa ma fari ya sanya, hularsa ma fara ce, xan iya cewa duk abinda ya sanya a jikinsa fari ne, sanye yake da farin glass a fuskarsa, hannu shi kuwa dauke yake da ledoji wanda baxan iya bayyana abinda ke cikin su ba. kasancewar ta cikin mayafi nake hango shi.
yana murmushi ya karaso wajena, sallama yayi gami da ce min amarya kin sha kamshi, ledojin da je hannun shi ya ajiye a kan side drower sanan ya hau kan gadon da nake, kusa dani ya xauna tare da bude lillibin da ke rufe a fuskata, ni kuwa banda aikin kuka babu abinda nake yi, cikin kulawa yake min magana my niimatullahi meye na kuka, bayan kina tare da mijinki, godiya xamu yiwa Allah da ya cika mana burin mu na xama ma'aurata, kiyi hakuri ki daina kuka haka kowace mace take samun kanta,a kawota gidanta har ta girma ta haifi yaya ita ma ta zama uwa, hada ni yayi da jikinsa tare da cire min mayafin dake sanye a jikina rarrashina ya shiga yi gami da shafa kaina tamkar jaririya, cikin salon soyayya yake kallona, wow!! amaryata kin yi kyau sosai, don ma kukan nan da kika
ya bata min kwalliyata dubi fa har idonki ya fara kumbura.
turo baki nayi to ba innah ce taki biyo ni ba, dariya yayi gami da cewa kiyi hakuri, a cikin daren nan zan kai ki har gidan innah amma ki share hawayenki ki daina kuka tukunna.
handkercheif yasa ya fara goge min hawayen da ya cika fuskata, cike da nutsuwa ya sake kallona tashi mu yi alwala mu yi sallah mu godewa Allah a bisa niimar samun juna da yayi mana.
Hannuna ya kama xai mikar da ni tsaye amma na makale naki tashi, cike da shagwaba nake masa magana baxan tashi ba har sai ka min alkawarin xaka mayar da ni wajen innah yanxu, murmushi yayi tare da kwantar da ni a kirjinsa, xan kai ki babyna tashi mu fara gabatar da sallah sai mu yi magana, alwala muka dauro inda muka yi nafila sannan muka yi addu'a muka shafa.
ledar da ya shigo mana da ita ya dakko, inda ya fara fito min da kayan da ke ciki, kayan kwalliya ne da kayan shafe shafe da kuma sleeping drees na haduwa, daya ledar kuma kaxa ce da kuma fresh milk, cikin nutsuwa ya dakko min kaxar karbi kici babyna nasan kina jin yunwa, gefe nayi da kaina bana ci, dago fuskata yayi me yasa baxa ki ci ba Niimatullah, cikin shagwaba nace masa ance maganin bacci kuke sakawa a ciki, dariya yayi tare da cewa wannan tunanin ki daina yinsa karya aka fada miki, lallaba ni ya fara yi a kan naci kaxar amma naki, tashi yayi ya shiga kitchen ya dakko cup, fresh milk din ya tsiyaya min a cup karbi ki fara sha kinji babyna kurba nayi na ajiy shi a gefe, matsowa yayi daf dani tare da dafa kaina so nake yi ki shanye gaba daya tunda kin ki cin naman na riga na karbi amanar ki a wajen baba hakkina ne na kula da ke my niimatullah, karba nayi na fara sha, kadan na sha na ture hannun shi, bayan mun gama sha ne ya dauki kayan ya tattara ya kai kitchen.
komawa nayi gefe na jingina kaina jikin pillow wani fargaba da tsoronsa ne ya xiyarci xuciyata, tashi yayi ya shiga bathroom jin shi nayi yana wanka daga bisani ya fito daure da towel, ina kallon shi sau daya na sunkuyar da kaina wani kwarjini ya kara min a idona ban taba xaton haka dattijona yake ba. fita yayi sanyo jallabiya fara sannan ya dawo ya xauna.
cike da kulawa yake min magana Niimatullah tashi kema kije ki watsa ruwa, cikin dasasshiyar muryata na amsa masa da nayi wanka tun a gidan innah, cike da xaulaya ya dube ni ki tashi kije kiyi ko na kai ki nayi miki kinga yau dai mu biyu ne babu innah ballantana kiyi min tonon silili.
da sauri na tashi saboda yanxu ina tsoron wasan sa yanxu xai mayar da abin gaske, shiga bandakin nayi na fara watsa ruwa sai da na saka kayana complete sannan na fito, kallona yayi yana murmushi da wannan kayan xaki kwanta Niimatullah cike da tsiwa nace mashi dam da wanne xan kwanta, ni da su na saba kwana a gidan mu, jan kumatuna yayi tare da cewa nan ai ba gidan ku bane nan gidanki ne kuma gidan mijinki abinda nake so shi xa a yi, tashi yayi ya jawo ledar da ya shigo da ita, wata fitinanniyar mitsitsiyar riga ya dakko min tare da cewa, da wannan nake so kiyi bacci daga yau na hana ki bacci da atamfa.
cikin shagwaba na mayar masa da amsa ni Allah baxan saka wannan kayan kafiran ba, matsowa yayi ya rungume ni yana sumbatar goshina, shi nake so ki saka min Allah ko kuma yau din nan mu yi yaki ni da ke.
kokarin xame jikina na shiga yi amma na kasa cikin kuka nace masa, ka sake ni xan saka maka,a hankali ya cika ni na koma gefe ina mayar da numfashi,lumshe idanu yayi yana sake kallona, ki saka min kin ji my Niimatullah idan baki saka min ba waye xai saka min? cikin tsiwa nace ga matarka can ita xata saka maka, tasowa yayi ya matso kusa da ni da sauri na matsa tare da kwala ihu xaunawa yayi yana min murmushi ki daina tsorona ni ba abinda xan miki, da yaga dai ba nida niyyar saka kayan ne ya kyale ni komawa kasa nayi na xauna.
takowa yayi har inda nake ya tsaya daga baya yana min magana ya kamata mu kwanta Niimatullah nasan kin gaji nima na gaji sosai tashi kixo ki kwanta, gyara min gado ya shiga yi, tashi ki kwanta kin ji babyna, makale kafada nayi tare da tambayarsa kai a ina xaka kwana.
shafa gashin kansa yayi a kusa da ke mana, kuka na fara yi Allah baxan kwana tare da kai ba, dariya yayi min tare da cewa kiyi kwanciyar ki da wasa nake yi nima dakina xani na kwanta, kashe min fitilar dakin yayi sannan ya fita ban san ina xai je ya kwana ba.
kwantawa nayi na dade ina mutsu-mutsu kafin bacci ya dauke ni saboda tunanin innata,cikin dare naji tashin numfashi a bayana a xabure na juya don ganin wane ne dattijona na gani kwance ya manna bayana da kirjinsa, muna hada ido ya sakar min murmushi tare da juyo da fuskata sake manna ni da kirjinsa yayi tare da kissing dina, cikin kuka nake tambayarsa meye haka dattijona kai da kace xaka yi bacci me yasa ka dawo xaka hana ni nawa baccin? cike da soyayya yace matukar ban hada jikina da naki ba baxan iya bacci ba niimatullah ki taimaki mijinki ki barni naji dumin ki.
kuka na fara yi masa, kokawa muka shiga yi da shi, cikin shagwaba yake min magana
kiyi hakuri my niimatullah na raya mana wannan daren da muka dade muna jiransa baxan iya hakuri da ke a halin yanxu ba ihu na shiga yi ina kiran innah da kyar na kwace na fada bandaki na mayar da kofa na kulle ina mayar da numfashi.
buga kofar bandakin ya fara yi yana rokona na bude na fito har da dan kukan shi amma naki bude masa, nima cikin kukan na ke bashi amsa Allah baxan fito ba tunda haka abinka yake, kuma gobe da safe xan tafi gida duk abinda kayi min sai na fadawa innata kuma baxan sake kwana a gidanka ba,lallabani ya shiga yi ki fito Niimatullah indai kika fito yanxu xan dauke ki na mayar da ke gida na miki alkawari, kin fitowa nayi duk nacin da yayi min haka na kyale shi tsaye yana ta faman bugun kofa.
0 comments:
Post a Comment