*S*allama take tayi tun daga k'ofar gidan,amma ko tari ba ayiba,ga rana dake dukan kanta...
Banda maik'o babu abunda take,jin ank'i ansawa,yasa ta d'aga allonta dake hannunta ta d'ora akanta,don kare ranar da ta addabeta...
Zuwa can ta sake maimaita yin sallamar,nanma dai shiru aka mata babu amsa....
Hakan ne yasata tsugunawa,ta cire silifanta ta zauna akai kamar mai d'aukan darasi.....
Tun daga nesa dattijon dake tahowa,yake kallonta,sauri ya K'arawa k'afarsa dan tabbatar da zatonsa....
Daf da ita ya k'araso,tare da fad'in *"NANA KHADIJATU*, Uwata me kikeyi a cikin wannan ranar da kowa yake gudunta???"
'Dagowa tayi da saurinta jin muryan mahaifinta dake tsaye,da murnarta ta kalli mahaifin nata tana fad'in "Abba na dawo ina sallama,ba a amsaba shi yasa na zauna anan ban saniba ko ba kowa a gida"....
Banda abunki kuma uwata sai kizo cikin wannan ranar ki zauna kamar an miki dole...
"Tashi maza mu shiga ciki,kar kuma ki sake zuwa ki zauna kinji ko,wannan ai sai wani ciwon ya kamaki"...
Fad'in abban *KHADIJATUL KHUBRA*.....
Hannunta ya kama suka kama hanyar shiga gidan....
Tun daga bakin k'ofar gidan yayi sallama,jin shiru ba a amsaba,yasa abban yaci gaba da kutsa kai cikin gidan had'e da sake yin wata sallamar....
Abunda ya matuk'ar bawa abba mamaki bai wuce ganin da mutum a tsakar gidanba.....
K'arasawa yayi yana k'are mata kallo,kafin ya iya furta ‘’ladiyo dama kina zaune muke sallama,amma amsawa ta gagareki‘’.....
Fuska ta yatsina (tamkar kayan miyan da yaso lalacewa).....
kafin ta bashi amsa da cewa ‘’ina ji sai me??
ko kuwa cewa akayi an ajiyeni ne dan na amsa muku sallama?''......
Ganin zata kunyata shi gaban y'arsa yasa yabar maganar ta hanyar fad'in ''Allah ya kyauta''......
Bud'ar bakin ladiyo sai cewa tayi ''ya kyauta abinda yafi haka''.....
Bai kuma tanka mataba,ya juya yana girgiza kai,ya shige d'akinsa.....
Duk wannan budurin da ake a gaban KUBRA ake,kanta na k'asa sai hawaye dake tsiyayowa daga ciki......
Ganin abbanta ya bar gurin itama ta juya da niyyar barin gurin....
Sai dai muryar ladiyo ta rigata k'arasawa bakin k'ofar d'akin,ta hanyar mako mata mula²n zagi......
Da sauri ta k'arasa shigewa,gabanta na dukan 9²....
Can ku'ryar D'akin ta nemi guri ta zauna,tana jiran gawon shanu....
Cikin d'akin da baida wadataccen haske,take zaune,tayi shiru sai kalle² take tamkar wata bak'uwa,ko wacce ta fara rayuwa inda bata saniba,haka taketa fama ita kad'ai,a haka bacci yayi awon gaba da ita.......
Wani k'ayataccen guri ta hango mai kyan gaske....
Sauri take ta k'arasa gurin,amma duk da haka ta kasa k'arasawa gurin,saima gajiya da tayi......
Haka ne yasata neman guri ta zauna,tana k'arewa gurin kallo ko zata hango inda ruwa yake.....
Rashin ganin alamar ruwa yasata,juyawa ta kalli hanyar da ta biyo.....
hanyace mik'ak'kiya wacce ko farkonta bata ganiba,bare k'arshenta,hakan yasata kifa kanta ta fara rera kukan rashin Madafa....
Tun daga nesa ta fara jiyo hayaniyar mutane had'e da wani daddad'an k'amshi da yasata saurin d'ago kai,tana bin hanyar da hancinta.....
Ayarine na mutane da suke da mayuk'ar yawa suke shirin giftawa ta kusa da ita......
Da sauri ta mik'e tabisu duk da suna kan abun hawa,hakan bai hanata shiga gabansuba,tana fad'in
"Dan Allah ku taimakamin"....
Babu wanda ya saurareta,sai zagayeta da sukayi suka ci gaba da tafiya......
Da gudu² ta sake shiga gabansu,tana rok'onsu.....
Wannan karon kam saboda haushi da ta bawa wasu daga cikinsu yasa su yi mata tsawa....
A firgice,jikinta har rawa yake saboda tsoro take kallonsu,wani k'ato da yayiwo kanta d'auke da bulala yasata fara kuka....
tana bashi hak'uri,d'aga bulalar ya d'aga da niyyar sauke mata a jikinta......
Kafin ya k'arasa ida nufinsa,wata siririyar murya daga bayansa take fad'in kada ka kuskura ka aikata abunda kake k'ok'arin yi .....
Da hanzarinsa ya juya don ganin mai magana,sai dai ganin fuskar wanda yayi maganar yasa shi kaucewa daga kusa da ita,jikinsa na kad'awa tamkar Mazari.......
Kyakykyawan matashi ne ya bayyana daga inda ya kauce,yana sanye cikin fararen tufafi,tafiyarsa cike da k'asaita,har ya k'araso Inda suke.....
Kallon k'aton yayi kafin ya bud'e baki,har ya rigashi cikin ladabi da girmamawa yake fad'in ''tuba nake ranka ya dad'e''......
Hannu ya d'aga masa,ba tare da ya sake yunk'urin yin maganaba,ya juya da nufin barin gurin............
*~_KEEP MOVING 😍😍😍……………_~*
*_REAL SMASHER 🤞🏻😘.._*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*9/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*__________________________*
_Godiya gareki *FATEEY TAMBARIY* tabbas y'an *TIME WRITER'S* muna godiya marar adadi gareki,Allah ya kara baseera,hazaka da kuma daukaka..._
_Ki jima kiyi karko tawan,Allah ya bar zumunci da kauna..._
*__________________________*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣2⃣*
*C*ikin sauri tabi bayansa,tana k`ok`arin tsayar da shi,sai dai hak`anta bai cimma ruwaba…....
Duk da bawai sauri yakeba,haka take binsa tana fad`in *"BAWAN ALLAH* ka tsaya"......
Ganin ta kasa cimmasa,kuma baiyi kokarin tsayawaba,yasa taci gaba da binsa....
Sai dai kamar wanda yake tafiya a cikin iska,haka ta kasa riskarsa,tsayawa tayi,lokacin ne ta hangoshi har ya dad`a mata nisa sosai..…
Zama tayi cike da takaici,gashi ko sunansa bata saniba,a matsayinsa na wanda ya ceci rayuwarta..…
Murmushi ta saki lokacin data tuna cewar zasu sake had'uwa koba wannan lokacinba....…
***************
*LADIYO* dake zaune tsakar gida,wadda tun wucewar *KHUBRA*,take rafka mata kira...…
Jin shiru babu amsa yasata mikewa tayi hanyar d'akin,da niyyar dubawa taga uban me take da har zata kirata tak'i amsawa...…
Shigarta d'akin ta tarar da ida kwance kan dagargazajjiyar tabarmarta,da take kwana kai..……
Ganinta tana bacci ba k'aramin b'acin rai tajiba,Kai ta girgiza,kafin ta koma da baya,tana fad'in da ni kike zancen yarinya...…
K'aton randan k'asa ta d'auka,ta nufi d'akin dashi,bata jira komaiba,ta juyeshi akan *KHUBRA* dake tsaka da dreaming....…
****************
A razane ta mik'e tana duba jikinta da yayi sharkaf da ruwa ga shi duk d'akin ya jik'e ruwan har ya kwanta,a tsakar d'akin...…
'Dagowa tayi ta kalli *LADIYO* dake tsaye tana watsa mata wani mugun kallo...…
Sake juyawa tayi ta kalli d'akin duk wani kaya dake ciki a jik'e yake,saboda ruwan ba kad'an bane...…
Kayanta ta fara tattarawa da niyyar gyarawa...…
*LADIYO* dake tsaye,tana raba ido akanta,ta fizgota tare da wanke mata fuska da mari...…
Gigicewa *KHUBRA* tayi,ta rasa me zatayi,shin kuka za tayi ko kuwa me????
Rashin madafa yasata neman hanyar ficewa daga d'akin...…
Ashar en da *LADIYO* tayi ne ya dakatar da ita,juyowa tayi,cikin ladabi tana fadin
"Kiyi hakuri baba ladiyo,zan gyara gurin ne"…………
''Dan ubanki ni kike fad'awa zaki gyara guri,to billahillaziy baki isaba'' fad'in LADIYO kenan kafin ta d'ora da cewa......
''Maza tun kafin na sab'a miki,ki wuce ki d'ebo ruwa,kin san aiki na nan yana jiranki,kika shigo d'aki kika kwanta ke ga sarauniya koh?''......
Rab'awa tayi ta kusa da ita ta fice,ba tare da ta sake cewa komaiba,sanin irin aikin dake gabanta.....
Tulunta ta d'auka ta kama hanyan rafi,jikinta duk babu dad'i ga kayanta dake jik'e.......
Tafiya take duk kunya ya isheta,saboda surar jikinta dake bayyane ta jikin kayan,duk da bawai banyan ne yake da mutaneba,sai dan kasancewarta mace mai tsanin kunya......
Tana tafe tana tunanin abunda ya faru yanzun,kafin fitowarta daga gida.....
A wani b'arin kuma na zuciyarta tana tunanin mafarkinta,Wanda shi ne kusan zata iya sashi a matsayin silar faruwar komai.......
A haka ta kammala d'iban ruwa,ta sake duk'ufa kan aikin cikin gida,duk da kasancewarta ba mai yawan shekaruba,amma yau da gobe yasata gogewa a fannin aikin gida......
Wuni guda tana aiki,tamkar jaka har kusan almuru ta kai,kafin ta kammala aikin.......
Sai a lokacin ne ta samu kwanciyar hankali,bayan ta je ta watsa ruwa,alwala ta d'auro ta shige d'akinta,da tun fitarta bata sake samun damar komawa cikinsaba sai ynzn.......
***************
Ta jima a tsaye tana kallon yadda k'asar gurin ta tsotse ruwan.....
Haka ta lallab'a ta rab'a gefe ta kabbara sallah...
Kafin wucewar wasu sa'o'i har ta idar....
Kwanciya tayi a gurin duk ta takure guri d'aya......
Sai a lokacin tunanin mafarkinta ya sake dawowa,murmushi tayi,tare da fatan sake ganin fuskarsa ko da a mafarkin ne,duk da dama bata tsammanin ganinsa a zahiri......
*************
Haka rayuwar *KHUBRA* taci gaba da kasancewa,kullum safiyar Allah za taje makarantar allo,daga zarar ta dawo kuma zata fad'a harkar aikace² har goshin maghreb.....
Bata da wajen zuwa,kullum tana gida (kamar daddawa).......
Rayuwarta ita kad'ai,babu k'awaye,bare ta samu abokin shawara......
Babban damuwarta baya wuce rashin zuwa dangin mahaifiyarta,Wanda tun kafin ta girma,shima bawai zata iya tunawa bane.....
Siraran hawayen da suka sakko mata ta goge,tare da tausayawa rayuwarta,irin k'angin da take ciki............
*_~KEEP MOVING..... 😍😍😍~_*
*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*10/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
_Ina matuk'ar godiya da addu'anki gareni,ina kuma jinjina gareki bisa k'ok'arinki Allah ya k'ara basira Doughteeyy *AISHA ISAH (MUMMY'S FRIEND)*......._
*~_#DUK WUYA MUNA TARE DA IZININ UBANGIJI.....~_*
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣3⃣*
*D*a sanyin safiyar wata laraba,tana tafe a hanya,tunanin mutumin da ta gani a mafarkinta ya sake dawo mata,ji tayi duk duniya babu abunda take da muradin gani sama da shi......
Wanda rabonta da shi tsawon sati guda kenan......
Sauri ta shiga yi na ganin ta k'arasa gida,burinta bai wuce tayi aikin da ta saba ta k'are ta kwanta ko zatayi dace a yau tayi katarin ganinsaba....
Da haka ta k'arasa,sai dai me zata tarar,zuwanta gidan ta tarar da LADIYO da wata k'anwarta da tazo daga garin KANO suna zaune cikin rumfa banda shewa babu abunda suke,duk sun cika gidan da hayaniya.... .
Tayi sallama yafi a k'irga,amma cikinsu babu Wanda yayi yunk'urin amsawa..
Haka ta wuce ta ajiye allonta.....
Dawowa tayi har k'asa ta durk'usa ta gaida ASMA'U wacce akema lak'ani da MA'U........
Yatsina fuska tayi,kafin ta kalleta had'e da zabga mata wata uwar harara........
Tsakine ya biyo baya,cikin tsawa take fad'in
''ke ni dallah b'acemin anan gurin,kinibabbiya kawai''.....
Cikin sanyin jiki KHUBRA ta mik'e ta bar gurin,ranta duk a b'ace,haka ta Shiva aiki babu ji babu gani......
*°°°°°°°°°°°°°°°*
LADIYO ce ta buga wani uban tsaki,da yasa k'anwarta MA'U kallonta,tana fad'in ''YAYA ince dai lafiya''.......
''Inafa lafiya,wannan shegiyar yarinya tana gidan nan ina naga kwanciyar hankali'',cewar LADIYO..........
Nan MA'U ta samu dama,ta fara magana da cewa
''YAYA aradu nu kaina na tsani tarinyar nan,da nazoma banyi tsammanin tana nanba,amma yanzun ga wata shawara.......
Me zai hana ki bani ita mu tafi birni,a samamata aikatau,duk wata abunda aka biya sai ina aiko miki da shi,kinga kin huta zaman banzan nan,ke ba sana'aba,ko kuwa ya kikace?''
Ta k'are maganar tata da son jin amsar da za a bata.......
Tunanin maganar MA'U ta shiga yi,zuwa can kuma ta ce
''To amma banda abinki MA'U ta ina zaki tafi da ita ba tare da ubanta ya saniba,ni da bani na haifetaba,dama anamin gorin ko kwai na kasa ajiyewa,kuma na tabbatar ba yarda zaiyiba''......
''Haba YAYA ke kam kamar ba mace ba ko da yaushe aka kawo magana bakya saurin amincewa sai kin kawo suka,shi kenan kinga ai sai kiyi ta zama babu sana'a'' ta fad'a tana had'e fuska,da alama bata hi dad'in maganar da y'ar uwar tata ba........
A'a MA'U baki fahimci me nake nufiba,dolefa sai malam BUBA yasan inda zata,kodama ace an tafi da ita babu saninsa saiya tambaya,kuma yana ganin bani na haifetaba ta ina zai amince da abunda zan fad'a.......
''Shi kenan na gane,amma dai kisan yadda za kiyi ki had'a mata kayanta,a kaita aikatau kema kya samu kifi k'arfin wani abun''.......
Yanzun an daina saka y'ay'a a gaba ana kallonsu,barema ke da babu d'a bare jika........
Ki lallab'ashi akan ni zaki bawa aronta,mijina ne baya nan zata tayani zama,zuwa nan da wani d'an lokaci zata dawo.........
Kinga daga nan sai dai yaji kid'a a magwan.......
Nan suka sa shewa,har da tafawa.......
Wunin ranar haka MA'U ta zauna tanata yiwa LADIYO hud'uba,wanda k'arshe sai da ta amince,akan ko Malam en baya so sai ta aikata........
*°°°°°°°°°°°°°°°*
Kwanakin MA'U uku a k'auyen na KASHIN DILA,tayi niyyar komawa inda ta fito.......
Kayan da KHUBRA ta fito da shi ne ya tabbatarmin da sunyi nasara akan k'udurinsu......
Fuskanta cike da damuwa,haka sukayi sallama,har bakin k'ofar gida LADIYO ta rakosu,tana yiwa y'ar uwarta fatan sauka lafiya......
Nan suka kama hanyan barin garin,mashin d'in achab'a suka hau,daga nan bai saukesu ko inaba sai tashar garin na HAD'EJIA........
Misalin k'arfe d'aya na rana motarsu ta harba kan titi.......
*~#SAFE TRIP KHUBRA...~*
Tafiya ta mik'a,inda KHUBRA dake cikin booth,tsakiyan kaya,tunanin abun duniya duk ya isheta,tana ta sak'a da war-wara bata san lokacin da bacci yayi gaba da itaba.......
*°°°°°°°°°°°°°°°*
Juyowa yayi ya hangota durk'ushe ta kifa kanta,banda kuka babu abunda take......
Cikin takunsa na k'asaita ya k'araso har gabanta......
Bata san zuwansaba,sai k'amshinsa da ta jiyo daf da ita.....
Cikin hanzari ta d'ago,baki ta bud'e da niyyar magana.......
Hannu ya mik'a ya rufe mata bakin,nan KHUBRA ta zaro ido,ganin abunda yake faruwa.....
Da sauri ta cire hannun nasa daga bakinta,cikin damuwa take fad'in
''Me yasa zaka tab'ani bayan ni ba muharramarka bace?''.......
Kallonta yayi tun daga sama har k'asa kafin ya iya bata amsa
''Kin tab'a jin inda akace idan miji ya tab'a matarsa yayi laifi?''......
"Bud'e baki tayi tana k'are masa kallo,ta ina na zama matarsa?"
Abunda KHUBRA bata saniba a fili tayi maganar.......
Cikin b'acin rai da fushi ya fara magana
''Nayi miki k'arya kenan? tunda kin d'aukeni a mak'aryaci,daga yau bazaki sake ganina ba,zanyi nisa da ke,har zuwa lokacin da zaki fuskanci gaskiya''
Daga haka bai sake yi mata magana ba ya juya yaci gaba da tafiya.........
Hak'uri take bashi akan ya dawo,amma ina haka duk kukan da take bai koda sake waiwayeba.......
Kuka mai tsanani ta keyi,tana fad'in dan Allah karka tafi ka barni,ka dawo dan Allah na yarda............
*°°°°°°°°°°°°°°°*
Dai² lokacin da take tsaka da dreaming,suka k'araso birnin KANON DABO gari mai tarin albarka.......
Baccinta take shak'a a Booth sai bakinta dake motsi tana juya kai,hawaye sai layi yake akan face enta......
Har aka bud'e booth en bata saniba,sai da MA'U ta k'araso gurin tana masifar rashin fitowar KHUBRA nan ta tarar da ita tana bacci,mari ta zabga mata,a firgice ta tashi,tana dafe da kuncinta,ta sakko ta shiga jidar kayan,suka kama banyan fita daga tashar.......
Sai lokacin ta tabbatar da cewa abunda ya faru duk mafarki ne.....
fuskanta ta shafa,ruwan da taji ta gogo yasata mamakin inda ta sameshi.......
Dallah ni kina b'atamin lokaci,kin wuce mun tafi ko saina zane miki jiki.........
Cikin sanyin jiki ta ja k'afafuwanta suka ci gaba da tafiya...........
*_~KEEP MOVING.... 😍😍😍~_*
*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*20/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
_Ina mai baku hak'uri na rashin jina da bakuyi,duk da wasu sunsan uzurina na rashin mahaifina da nayi a safiyar litinin, *12/03/2018* ina fatan zaku tayani addu'ar samun dacewa da rahama a gareshi da sauran al'ummar musulmi baki d'aya, rayayyu daga ciki da kuma matattu,Allah yasa muyi kyakykyawan k'arshe......_
*AMEEN...*
*~__________________________~*
*_INNALILLAHI MAA AKHAZA WALAHU MAA A'A'DA WA KULLI SHAI'IN INDAHU BI AJALIN MUSAMMA FAL TASBER WAL TAHTATHEEB..._*
_Ya Allah Kaine mafi sani da abunda ke b'oye,na zahiri,Wanda zai faru gaba,da Wanda ya faru a baya,Allah kayiwa mahaifanmu rahama,gafara,afuwa,ka sadasu da rahamarka......Ameen thumma ameen._
*~_________________________~*
_Ya Allah ina rok'onka da sunayenka tsarkaka,Allah ka dubi halin da y'ar uwata take ciki,ka bata lafiya,ingantacciya mai d'orewa,Allah ka tashi kafad'unta....._
_Wish u a very quick and speed recovery *MY SISI HUBBEEY.*_ 💔
*~_________________________~*
_Kun nunamin karamci a rayuwa,soyyaya,k'auna,Wanda baki ba zai iya jurar furta kalamai garekuba,hak'ik'a ku en masoyane na asali,ubangiji ya biyaku da mafificin alkhairinsa..._
*ONLINE WRITER'S TARE DA READER'S* daga ko wane gida,ina alfahari da kasancewa tare da ku,ina jinjina gareku musamman wad'anda ke cikin wad'annan gidaje....._
*SMASHER & HUBBEY NOVEL GROUP.* 💔❣
*REAL SMASHER NOVELLA GROUP.* 💔❤💘
*A LAUNI HAUSA NOVEL.*💞
*TIME WRITER'S.* 🕙
*WRITER'S ONLY.* 📚📝
*RAYUWAR BASMA.* 🌹
*WRITER'S VILLAH.* 😘😍
*MUSAN JUNA ONLINE WRITER'S.* 💃🏻🤝🏻
*KANAWAN DABO WRITER'S ROOM.* 🤝🏻
*OUR LADIES OUR PRIDE.* ❤
*PRECIOUS FAMILY.* 👨👩👧👦
*BA NI NAYI KAINABA FAN'S.* 💖
_Ina godiya sosai,wacce bata da limit a zuciyana,bisa ta'aziyyan mahaifina,Allah ya bar k'auna..._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣4⃣*
*T*afiya kawai suke ba tare da *KHUBRA* ta san inda suke nufaba,sai kalle² take a haka har suka fito bakin hanya...
Kafi babur suka tare,MA'U ta tak'ark'are ta hau yi masa bayanin rijiyar lemo zai kaisu......
Kud'in da ya yanko mata zata bayar,ta tsaya wangale da baki,nanfa suka tsaya ciniki,yi take kamar ba za a dainaba,d'an adaidata da yaga bazai iyaba,yaja kekensa yayi gaba.....
Duk Wanda za ta tsayar idan taji bai mata yanda take soba sai dai yaja Babur ensa ya k'ara gaba.......
Son kud'i irin nata ya hana su tafiya.......
Sun jima tsaye ba tare da sun samu abun hawaba.....
Ita MA'U son kud'inta da ganin tsada ya hanata ta biya akaisu inda zasu.....
Haka sukaci gaba da jira,yamma na dad'a kunno kai......
'Bangaren KHUBRA kuwa wata azababbiyar yunwace tafi addabarta ga bakinta da ya bushe saboda tsabar k'ishi da ya dameta.....
Rashin sanin abunyi da kuma hali irin na MA'U yasa ta ja bakinta tayi shiru,sai raba ido da take akan hanya......
Ganin tsaiwa bazai kai musuba,da kyashin biyan kud'in motar yasa MA'U juyawa ta kalli KHUBRA,tana yatsina mummunar fuskarta......
Tunda nake a rayuwata ban ta'ba zuwa na b'ata lokaci a tsaye ba tare da samun abun hawaba sai yau da na d'auko MAI BAK'IN JINI......
Jin furucinta na k'arshe yasa jikin KHUBRA dad'a yin sanyi....
Ba tare da ta kalletaba,haka bata ce uffanba.......
''Yanda kikaimin bak'in ciki na rasa abun hawa haka wallahi saina fanshe kud'ina tare da ke MATSIYACIYA Y'AR MATSIYACI''.......
Maganan da ya fito daga bakin MA'U kenan wanda ba k'aramin sosawa KHUBRA rai yayi ba,take hawayen da bata son fitowansa ya b'alle,ita kam da ita ta zaga babu da zai sa ta damu,abunda yafi komai bak'anta mata rai zagin ABBANTA da MA'U tayi....
Ko ganin girmansa batayiba,bare d'aga masa k'afa a matsayinsa na miji ga yayarta.......
Wannan shi ne abunda ya jawo mata ZUBAR HAWAYE.....
Dad'a sunkui da kanta tayi k'asa,ta shiga goge face nata,dan ta tattabata idan MA'U ta san halin da take ciki tana mai iya jibgarta a gurin tamkar kayan wanki......
Sake tsaida wani tayi,babu ko ciniki ta afka tare da cewa ''idan kinga dama kya taho mu tafi.....
Jan k'afafunta tayi ta shiga,duk da haka bata tsiraba,k'arshema sai cikin booth d'in mashin en ta zauna,tun daga kasuwar ta y'an kaba har zuwa unguwan na rijiyar lemo......
**************
Sun is a unguwan ana sallan Maghreb,yana saukesu ta laluba cikin d'an topinta ta zaro masa kud'insa....
Kud'i sosai KHUBRA ta gani ta fito da shi,nan ta tabbatar matar tana da bak'in hali....
Tunani ta shiga yi,na irin rayuwar da zata fuskanta nan gaba,ko yaya zata kaya tsakaninta da MA'U?........
*_Ni ko nace ai KHUBRA bakiga komaiba......._*
*_~Kumin uzuri fan's in sha Allah next page zaizo ba kamar wannan ba..... ~_*
*_Masoya novel ena na RAYUWAR WANI kuyi hak'uri na jina shiru kwana biyu in sha Allah zanci gaba daga inda na tsaya,na gode sosai_*
*_~IYA WUYA MUNA TARE......~_*
*_~KEEP MOVING.....~_* 😍😍😍
*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*21/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AH KAN ABOKIN GABA...*
_ALLAHUMMA ANTA ADHUDHIY,WA-ANTA NASIYRIY,BIKA AHULU,WA-BIKA ASUULU,WA-BIKA UK'ATILU......_
_ALLAHUMMA INNA NAJ'ALUKA FIY NUHURIHIM,WANA-UZHUBIKA MIN SHURIRIHEEM......_
*_~#HISNUL MUSLIM....~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣5⃣*
*B*inta kawai KHUBRA take a baya² har suka k'arasa k'ofar gidan.....
Mukulli ta zaro irin wanda ake kira da (KUBA) en nan ta shiga murd'awa a jikin k'ofan,da kyar ta samu ta bud'e saboda taurin da k'ofan yayi.....
Gidan bak'i k'irin da shi,ga uban daud'a da yayi,kai saika rantse bai tab'a ganin wani abu mai kama da tsintsiyaba.....
Kunna kai tayi ciki ba tare da ta damu da addu'ar shiga gida ba,duk dama dai bana tunanin ta iyata....
KHUBRA dake baya,ta tsaya k'ofar gidan kafin ta shigo....
Sai da tayi addu'ah ta sanya k'afanta cikin gidan,kasancewar mahaifinta yana koyar da ita ilimin FIQHU,AZKAR da sauran abunda ba a rasa ba na zamantakewar duniya......
Bata tarar da MA'U a tsakar gidanba,guri ta samu ta zauna gudun kada tayi laifi,coz ta san yanzun sai ta bi a hankali,tunda tasan halinsu ba k'aunarta sukeba......
Tayi nisa cikin tunani,kan mafarkinta...
Abunda take son fuskanta kan mafarkin ya gazawa tunaninta....
Tashi tayi tana k'ok'arin shiga band'aki danta samu ta rama sallolin da ke kanta,nan ta bar kayan ta shige.....
Ko uzurin da ya kaita bata k'arasaba ta tsinkayo muryan MA'U daga tsakar gida tana surfawa iyayenta zagi....
K'irjinta ta dafe had'e da zaro ido,dan ko ba a fad'a mataba tasan laifinta.....
Addu'ah ta hau yi a zuciyanta,tana me neman tsarin ubangiji tsakaninta da MA'U da kuma zaman da zasuyi nan gaba......
Fitowanta ta tarar da ita tsaye ta rik'e k'ugu kamar wata k'aramar yarinya sai girgiza take.....
Kallo d'aya ta mata ta d'auke idonta a kanta,ta sunkuya ta fara alwala......
''Don ubanki ni zaki mayar mahaukaciya ina magana ki juyamin baya,ko ubanki wannan matsiyacin bai isaba wllh''...
Maganar da ta biyo bayan hucin da take kenan kamar wata KUMURCIN MACIJI.......
K'in magana,duk da kalmomin da tayi amfani dasu sun shigeta,shiru tayi har sai da ta idar da alwalan,sannan ta juya tana bata hak'uri......
Wata uwar harara ta rakata da shi kafin ta figi kayanta tayi cikin d'aki.......
Gajiya da tayi da tsaiwa,ganin ank'i kulata bare ta samu a kirata,kan dole ta nufi hanyan d'akin bakinta na d'auke da addu'ah....
A kwance ta tarar da MA'U,nan ta tsaya tunanin koh wane hali mahaifinta yake ciki a yanzun......
Tsayawan mutum MA'U ta gani kanta cikin sauri ta bud'e idonta,tana zabga mata harara....
Kame² KHUBRA ta fara kafin da kyar ta iya furta
''Dama abun sallah nake so''...
Bata tanka mataba,haka bata tashi ba,saima dad'a rufe idonta da tayi,tana daga kwance kan gadon k'arfe irin na da ennan.....
Ganin tsaiwa bazai kai mataba,ta kabbara sallah daga inda take tsaye.....
Tana sallah tana dafe cikinta da yake ihun yunwa,a haka har ta samu ta idar ba tare da ta kai GA fad'uwaba.....
MA'U kam bacci ne ya kwasheta nan,ba tare da tunanin tashi ta gaida mahaliccinta ba.....
Har bacci ya fara d'aukanta ta tuna da k'ullin kayanta dake waje,cikin hanzari ta fita ta d'auko bata dawo d'akin ba saida ta tabbata ta kulle k'ofar gidan.....
'Dakin ta dawo ta hau bud'ewa,can k'asan kayan ta binciko wani k'ullin leda da ABBANTA ya bata tun jiya....
Bud'ewa ta hau yi,k'uli² ne mai d'an yawa irin wanda ake yinsa da sugar ennan.....
Ci ta fara,kamar wacce ta samu nama,haka ta far masa,sai da taci mai yawa,sannan ta hak'ura ta d'aure ta mayar cikin ledan......
Waje ta sake komawa cikin randa ta d'ebi ruwan da tasan zata iya shanyewa....
Godiya tayiwa Allah,sannan ta koma d'akin ta kwanta a k'asa dai² inda ta idar da sallah.....
Take kuwa bacci yayi gaba da ita......
************
Daf da kiran sallan assalatu ta farka,kasancewar ABBANTA kullum shi yake tashinta idan zashi masallaci sallah da asuba....
Fita tayi ta d'auro alwala,tsakar gidan da duhu sosai,haka ta daurewa zuciyarta tayi sauri ta dawo d'akin.......
Har ta idar da sallan MA'U ko juyin farko batayiba,haka itama KHUBRA batayi gangancin tashintaba.....
Gefe ta koma,ta had'a kai da gwiwa,tana tunanin duniya da makomar zuwanta wannan gari,tasan dai babu komai cikinsa face zallar wahala......
Ganin tunani ba kaimata zai ba,ta shiga karanta AZKAR na safiya,tana zaune har gari ya k'arasa wayewa......
Hijab dake jikinta ta cire ta fita tsakar gida......
Tsintsiya ta d'auka ta hau shara,kafin wani dogon lokaci har ta kammala,sai ga gidan yayi haske daga bak'ar daud'ar da yayi.....
Har tayi wanka MA'U bata san me yake faruwaba...
'Dakin ta dawo,da tunanin ta tasheta ko kuwa......
Tsayawa tayi tana nazarin ta inda zata fara,amma fargaba ya hanata tab'uka komai.....
Kan dole ta hak'ura,ta zubawa sarautar Allah ido......
*************
Sai misalin k'arfe 8:00am ta farka tana ta faman zabga hamma,had'e da mik'a....
Da kyar ta iya tashi tayi waje,ganin tsakar gidan a share tas,ta tab'e baki,ta rarumi buta tayi band'aki,ta jima aciki,tamkar wacce ta sami d'aki,zuwa can kuma ta fito,ta sake d'iban ruwa a bokiti ta koma....
K'arar ruwa kawai kake ji kamar wacce taje suuuu kogi,haka ta shek'ashi a jikinta ta fito,cikin abunda bai wuce minti 5 ba.......
Alwalan ma buji² akayi aka fad'a d'akin.....
Shigarta ta tarar da KHUBRA har ta gyara d'akin tsaf duk ta gyare tarkacen dake cikin d'akin.....
Babu ko sannu bare an gode,saima ladan gaben harara da yatsina da ta shiga yi......
Shiryawa tayi cikin gaggawa,tasa wata atamfa riga da zani,taja gazal a idonta......
Takalminta ta sharfad'a tayi waje ba tare da yin ko da sallan da akayi alwala domin taba......
Babu magana bare KHUBRA ta sa ran ganin abinci tayi waje,tana gaisheta ma ko ta kanta bata biba.....
Ta k'arawa k'afafuwanta mai.......
*_~ALLAH YA SHIRYA.......~_*
*_~KEEP MOVING....~_* 😍😍😍
*_REAL SMASHER🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*22/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾
*APPY APPY BUFDAY*
_Hope your birthday blossoms into lots of dreams come true! May today be filled with laughter and love._
_Happy Birthday and many happy returns of the day._
🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂
*HAPPY BITHDAY 2 U!!*
H B Z
A U
Y A B
A A
T B I
R
A
*(YAYA HAYAT) ADMIN OF ADMINS.......*
_Wannan ranar taka ce,babban Admin mai kundin novels, *WRITER'S* naka *REDER'S* naka,kana k'ok'aree gurin nishad'antar da d'aukacin members enka dake cikin_
*COOL NOVELS GROUP'S 1,2,3,4 & 5, MAKEUP ND KITCHEN GROUP* _Allah ya k'ara 'daukaka,ya k'aro maka shekaru masu albarka,kana mai wadatuwa da imani,kwanciyar hankali........_
_Wannan page en naka ne kai d'aya kayi yadda kaso da shi....._ ✍🏻✍🏻
🍾🍾🎂 *HAPPY BUFDAY WULLNUP ADMIN...* 🎂🍾🍾
*~__________________________~*
*ADDU'AH YAYIN TASHI DAGA BACCI*
_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AHYANA BA'ADA MAA AMATANA WA-ILAIHIN-NUSHUUR..._
_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AFANIY FII JASADIY WARADDA ALAIYYA RUHIY WA-AZINALIY BIZIKHRIY....._
*_~#HISNUL MUSLIM...~_*
*~_________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣6⃣*
*I*ta d'aya zaune tayi shiru,abun duniya duk ya taru ya mata yawa......
Tunanin gida da mahaifinta duk shi yafi damun zuciyanta,ko a wane yanayi yake? Allah shi ne masani......
Ganin babu sarki sai Allah,shi yasa ta bawa zuciyanta hak'uri......
'Daki ta sake komawa,bayan ta tura k'ofan gida,da yake ta san ita kad'ai ke gidan,gudun kuma kada wani abu ya faru......
***********
Tafiya take duk inda ta samu watsa k'afafuwanta take,tamkar wacce zata tashi sama.....
Son kud'i irin nata ya hanata neman abun hawa......
Sai da tsakiyan rana,ganin babu haza yasa ta hak'ura ta nemi keke napep,daga UNGUWAN KURNA zuwa RIJIYAR ZAKI,a ganinta nan ne unguwar masu kud'i,za tafi samun gidan aiki,idan bata samuba kuma,zuwa gobe sai ta nausa cikin gari......
Zafin rana da k'ishi su suka haddasa mata tsaiwa,ta nemi abun hawa,idan yaso sai ta k'arasa,in da ta nufa......
Ta tsayar da masu napep sama da guda goma,amma da sun tsaya suke k'arawa babur en nasu wuta suyi gaba.......
Da kyar ta samu abun hawa,kan neman ragi irin na MA'U......
Yinin ranar yawo ta dungayi gida² take bi a unguwan na rijiyar zaki,kan neman gidan da suke neman Y'AR AIKI.....
Sai da ta sha wahala,kafin ta samu gidan da suka nuna mata suna buk'ata......
Sun gama ciniki kan dubu biyar per month......
Duk iya yinta na su k'ara mata wani abu,hakan ya faskara....
Gudun kada tayi asara gashi wannan d'inma da kyar ta samu,bayan yini da tayi tana GARARIN DUNIYA yasa ta amince,akan zata kawota daga zaran sun gama shiryawa......
Abinci matar ta kawo mata da ruwa mai sanyi.......
Ta gama d'amke cikinta,sannan tayi mata sallama........
Godiya tayi ta tafi da alk'awarin nan da Sati d'aya zata dawo......
***********
Kwance take tana ta faman bacci wanda bata san lokacin da ya d'auketaba,tayi nisa cikin baccinta.......
**************
Tun daga nesa ta hango ingarman dokin wanda akewa lak'ani da KILI ( wato mai fari biyar),kansa mutum ne zaune,cikin farare tas en tufafi......
Matsowa yaci gaba da yi,wanda har sai da yazo daf da ita sannan ne ta iya gane mahayin murmushi d'auke kan fuskansa......
Sai da ya zo gabanta,sannan yaja linzamin dokin ya tsaya.....
Har lokacin tana tsaye fuskanta cike da mamakin ganinsa......
Mutumin daya ce bazai sake dawowaba yau shi ne a gabanta yau.......
Saukowa yayi cikin isa,ya tako har zuwa gabanta....
Cikin wani irin voice da bata tab'a jin irinsa ba tunda take a gaba d'aya tsawon rayuwanta,ta tsinkayo shi yana fad'in
_''Amincin Allah yaci gaba da tabbata agareki''........_
Kasa amsawa tayi saboda tsananin mamaki da yak'i barinta har yanzun......
Hannunta ya kama cikin wani irin salo,ya jata jikinsa.....
_''Haba wifey,ni en ne baki ganeba ko kuwa na zame miki wata sabuwar halitta?''......_
Kuka ne ya kufce mata,jikinta banda rawa babu abunda yake,tsabar tsoro ta kasa magana,sai hawaye dake ta ambaliya a fuskanta.....
Duk k'ok'arinsa da son ganin ta bud'e baki tayi magana abun ya gagara......
Janta yayi ya had'a jikinsu guri d'aya,ganin yanda jikinta yake ta faman b'ari......
Maimakon a samu sauk'i saima k'aruwa da aka samu.........
Kukantane ya sake tsananta,kan dole ya raba jikinta da nasa....
Fuskanta ya kama ya d'ago,tsura mata ido yayi
_''Shin bakiyi farin ciki da ganinaba ne wifey?''...._
Kai ta girgiza masa,alaman
A'a
_''Baby maganafa zakiyi,bana son wannan nodding en''......_
Cikin hanzari ta bud'e baki da niyyan magana
_''A'a,ina mamakin yanda ka dawo gareni ne,alokacin da bantab'a tsammaniba''........_
Fuskanta ya shiga goge mata,yana murmushin jin dad'i......
**********
k'afafuwanta tamkar wacce taje sharan gona,sunyi futu² kamar basu tab'a ganin mai ba.......
Sai murna take na samun gidan aikin da tayi,haka ta sauka a napep en da ya sauketa bakin titi.....
Ta sake ninkawa ta shiga cikin unguwan,a k'ofar gida taja burki,ganin k'ofan a rufe,ta shiga huci.....
Bugun k'ofa ta shiga yi,jin shiru ba a bud'eba,ta shiga dukanta da k'arfi tamkar zata karya.......
************
Cikin baccinta mai dad'i mai cike da mafarkin da a kullum shi ne birinta....
Ta tsinkayo bugun k'ofan da tamkar a tsakiyan kanta ake......
Bud'e idonta tayi,cikin sauri ta mik'e ta nufi k'ofa,har tana had'awa da d'an gudu,wanda saura kad'an ta fad'i,amma haka ta daure ta tunkari k'ofan..........
*_~Uhmmmm ko me KHUBRA zata tarar yau kam.......~_*
*_~KEEP MOVING...~_* 😍😍😍
*_REAL SMASHER 🤞🏻😘_*
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*23/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AR SANYA TUFAFI.*
_________________________
_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY KASANIY HAZAS-SAUBA,WARAZAK'ANIHI MIN GHAIRI HAULIN MINNIY WALA KUWATTA......._
*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣7⃣*
*K*okawa ta shiga yi da k'ofan,wanda da kyar ta samu ta bud'e......
K'ofan na gama bud'ewa idanuwanta sukayi arba da MA'U tsaye,idanunta sunyi jajur dasu kamar garwashi.....
Kamar ance ta kalli k'afarta,ai kuwa nan ta hangi k'afar tayi busu²,dan k'ura da daud'a......
Duk k'ok'arinta na ganin ta kaucewa yin dariya abun ya faskara....
Nan ta fara tuntsirar dariya,kamar kwancen mahaukata.......
MA'U dake tsaye tana jiran a bud'e mata k'ofa,taga ta tsaya tana mata dariya.....
Tsaiwa tayi ta dafe saman gini,tana kallonta,sai dariya take,kamar sabuwar kamu.......
Tsabar mugunta irinta KHUBRA har dafe gefen cikinta take,ita bata matsa daga kan hanya,ta bawa MA'U guri ta wuceba,ita kuma bata tsaida dariyan taba......
Kallonta MA'U taci gaba dayi,ganin abun nata ba na k'are bane,kuma ta rasa me KHUBRAN kewa wannan dariyan a tare da ita,abun ya soma bata haushi....
Ga haushin ta rufe mata k'ofa,sannan ta zo tana mata dariyar rainin wayo.......
Hankad'ata tayi cikin soron,ta shigo tare da maida k'ofa ta rufe.....
Wani gigitaccen mari MA'U ta aikawa KHUBRA da shi,wanda ta jishi,babu shiri kuwa ta had'iye dariyarta.......
Gashin kanta ta dank'a ta jata zuwa cikin gidan,sai zage² take kamar y'ar maguzawa......
Babu zato bare tsammani MA'U ta shiga jibgar KHUBRA kamar ta samu jaka ko ince kayan wanki.....
Tun tana dukanta KHUBRA na iya yin ihun neman ceto har ta koma muryanta ma bata iya fita saboda laushi da jikinta yayi.....
Sai da tayi mata dukan sa'a,sannan ta yasar da ita a gurin ta shige d'aki,ba tare da ta furta ko 'A' ba,zuciyarta kamar zata fito waje saboda haushi.....
KHUBRA dake yashe a k'asa babu,abunda ake iya ji na daga sautin muryanta,banda numfashinta dake fita da sauri²......
Ta jima kwance a gurin,wanda ta gagara koda motsin kirki......
***********
Tun tahowar MA'U da KHUBRA birni,hankalin ABBAN KHUBRA yak'i kwanciya.....
Kullum cikin tambayar LADIYO yake yaushe MA'U zata dawo da ita.....
Amsar dai guda d'aya ce kullum,dazaran lokacin da suka d'auka alk'awari yayi zata dawo da ita.....
Shi kam kullum yana jinta ne,don kuwa ya fuskanci idon MA'U bud'e yake da son nera,tsoron sa d'aya kada su cutar masa da ita.....
Abu sai dad'a gaba yake,LADIYO ta shiga tashin hankali ganin yadda malam en yake neman d'aga mata hankali,har bata so ya shigo ya tarar da ita zaune,yanzun zai dasa mata maganar y'ar tasa mai kama da aljanu.....
Yau ma zaune take cikin y'ar rumfar karan dake bakin d'akin nata,wanda daga nan kana iya hango k'ofar shigowa gidan.....
Zafi duk ya addabeta,daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta.....
Malam buba ya kawo kai zai shigo cikin gidan,da sallama a bakinsa....
Ko amsawa bata yiba ta mik'e cikin hanzari zata bar gurin.....
''Dakata LADIYO,na fuskanci kwanan nan nema kike ki mayar dani wani sha ka tafi''.....
''Ko dai yau ki fad'amin inda y'ata take ko kuma aradu ina mai kai k'ararki gurin MAI GARI''.......
Ido waje LADIYO ta juyo,nan ta shiga bashi hak'uri.....
Saboda LADIYO irin matan nan ne masu d'an karen tsoro,ammafa akwai tsokana....
Idan akwai abunda LADIYO take tsoro a duniyarta kuwa baya wuce MAI GARI ko a ambaci mai bak'in kaya wato ('DAN SANDA).....
Har k'asa ta zube tana masa magiya,akan zata kira MA'U ta dawo da KHUBRA idan ma bata sametaba zata je da kanta ta dawo da ita har gida ba sai maganar ta jega HUKUMA ba.....
Girgiza kai MALAM BUBA yayi,ya juya ya nufi d'akinsa
''Da dai yafi miki kwanciyar hankali''......
Yana fad'a ya k'arasa shigewa ciki.....
LADIYO dake durk'ushe a inda MALAM BUBA ya barta ta d'ago tana dafe k'irji....
Ganin babu MALAM en a gurin tayi wuf ta fad'a d'aki....
Nan ta shiga raba ido kamar shege a rabon gado (yo dama me zai kawo shi tunda yasan bashi da ko allura)?.....
Ita kad'ai ta shiga magana da kanta
_''Ya zama dole nayi aron waya na kira MA'U ta dawo da wannan shegiyar yarinyar mai kamar aljana,tun kafin kashina ya bushe''....._
Ko gama tunanin batayi ba ta zara mayafinta ko riga babu ajikinta,tayi waje......
Bata zame ko inaba sai gidan k'awarta mai suna TABAWA.....
******
TABAWA irin matan nan ne y'an duniya,wad'anda suke da bud'ad'd'en ido.....
Da shigarta ta tarar da TABAWA ta cokalo d'an kwalinta sai zabgawa mijinta rashin mutunci take....
Shi kuwa bawan Allah kansa a k'asa kamar wanda ke gaban uwarsa haka jikinsa sai b'ari yake.....
Bata k'arasa shigowa ba ta tsaya daga bakin k'ofa,tana kallon wannan abun aljabi.....
''Dillah can banza kawai,zaka bani ko kuwa sai na cajeka?
Katabbata idan har na laluba na tarar da kud'i a jikinka,wallahi yau kam babu kai babu cin abinci a gidan nan''.....
Ta fad'a tana hak'ik'an cewa....
Rantsuwa ya shiga yi mata,sai kace d'a da uwa,amma hakan bai sa TABAWA ta yarda ba.....
Rigarsa ta kama ta cukuikuyo shi,ta shiga lalube aljihunansa kaf,sai da ta tabbatar da abunda ya fad'a sannan ta kyaleshi tana fad'in
''Allah ya cece ka''.....
''Amma ba kyaleka nayi ba wallahi,zan ranta maka kud'in cefanen yau,kana samu kayi hanzarin biyana idan kuma ba hakaba,zaka had'u da tijarar da tafi wannan''......
Ita kam LADIYO na nan tsaye tamkar an dasa bishiya,ta lula cikin tunani,har bata san lokacin da mijin k'awar tata ya fita ba......
Dogon ajiyan zuciya tayi,kafin jiki a salub'e ta afko gidan ko sallama babu......
Binta kawai TABAWA tayi da ido
A ranta kuma tana fad'in ko lafiya?
*_~NIKO NACE OHO MUKU.........~_*
*_~KEEP MOVING....~_*😍😍😍
*_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*Viawattpad@realsmasher01.*
*©®2018*
*25/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AR SANYA SABABBIN TUFAFI.*
_ALLAHUMMA LAKAL HAMD ANTA KASAUTA NIHI AS'ALUKA KHAIRAHU WA-KHAIRA MAA SUNI'A LAHU,WA'A'UZU BIKA MIN SHARRIHI WA-SHARRI MAA SUNI'A LAHU..._
*~#HISNUL MUSLIM.~*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣8⃣*
*T*ana nan kwance in da MA'U ta yasar da ita,kamar matacciya,idan ba wai mutum ya kula da yanda chest nata dake shibring ba,za a iya cewa ta jima da mutuwa....
**********
Cikin kwanciyar hankali MA'U tayi kwance kan gadonta,ko kad'an batayi nadamar abunda ta aikataba,bare ta duba taga halin da y'ar mutane ke ciki ba....
Idonta tar kan selling tana nazari kan wannan gidan aiki da ta samu....
Ita kam a nata ganin,da zaran ta samu wani aikin da yafi wannan maik'o zatayi watsi da wannan....
Ko dama ace ba a garin kuwa zatayi aiki ba,ita meye damuwarta,tunda ba ita ta haifeta ba.....
Burinta bai wuce a kawo mata masu gidan rana......
************
Wani uban tsaki TABAWA tayi lokacin da ta kalli LADIYO,da alama tunani take....
Da k'afa ta kai mata hauri...
A firgice LADIYON ta d'ago tana k'ok'arin mai da kallabinta da yake shirin fad'owa....
Jajayen hak'oranta ta bud'e wanda babu abunda ke fitowa daga bakin nata banda wani irin azababben wari,ga su duk sun dafe saboda tsabagen daud'a.....
Kallonta TABAWA tayi tana fad'in
''LADIYO ince dai ko lapia kike irin wannan dogon nazari haka?''.....
''Ke dai bari TABAWA ina cikin tashin hankali wollahi''....
Fuskanta da tsananin mamaki take kallon LADIYON da take koro mata jawabin abunda ya had'o ta da MALAM BUBA akan yarsa......
Dariyar mugunta TABAWA ta hau yi,tana tafe hannunta....
Sai da tayi mai isarta kafin ta saurara,tana k'arema LADIYO kallo,tana tab'e baki....
''Uhmmmm!LADIYO kenan,ni ai a ganina ke kika so,da har kika tsaya MALAM BUBA yake zuba miki irin wannan rashin mutunci,da d'iban albarka haka
Ni baki ganniba,washar da ni,tunda mu ba haihuwa za muyiba,ai gara muyi abunda muke so,kafin dare d'aya suzo mana da maganar k'arin aure''.....
Baki bud'e LADIYO ke kallon TABAWA,da ta tak'ark'are tana koro mata datar......
''Kinga yanzu ba zama ne ya kamacemu ba,abunda kawai za ayi,ki biyo sahuna,mu d'ora daga inda aka tsaya....
Har zamu tsaya ne muna kallonsu,mu tashi a tutar babu,shi kenan munyi ba wan ba k'anin?''.....
Karatun na d'an kama......
"Ina kuma zamu nufa yanzun?"
LADIYO tayi tambayar.....
"Kinga yanzu ba lokacin tsaiwa dogon jawabi bane,idan kina da buk'atar mafita kawai ki taso,bana son dogon sharhi".....
Jiki na b'ari ta mik'e tabi TABAWA a baya,kamar
RAK'UMI DA AKALA......
************
Rashin madafa shi yasa KHUBRA dake kwance,lallab'awa da jan ciki,ta d'ebi ruwa a buta......
Da yake lokacin zafine,ruwan da zafinsa,rana ta gama gasashi....
Haka ta lallab'a ta shige,wanka tayi ta d'aura alwala ko za taji dama²....
Da kyar ta iya mik'ewa tana bin bangon toilet en,ta fito daga ciki,jikinta duk ya mata nauyi....
Haka ta ci gaba da takowa tana d'aga k'afa da kyar,har ta samu ta fito......
'Daki ta shiga da niyyan ta samu ta lallab'a tayi sallah,dan kuwa lokacin har an idar da sallar maghreb......
Ko da ta shiga d'aki da sunan za tayi sallaah......
'Dagowa MA'U tayi,tana K'are mata kallo.....
Cikin tsawa ta hau fad'an da tun d'azun batayiba.....
************
Can cikin wani surk'uk'in hanya suka shiga bi jikin LADIYO sai kyarma yake saboda tsoron hanyan da ko a mafarki bata tab'a tsintar kanta a cikiba....
Bin bayan TABAWA kad'ai take,wacce ita kam ko d'ar bata jin tsoron komai,haka take watsa k'afafuwanta cikin jejin.....
Haka har suka tsinci kansu gaban wata y'ar bukka dake saman wani sand dune hill....
TABAWA da yake tasan kan hanyar yanda ake hawa,haka ta shiga raba k'afafuwanta,har ta ida hawa.....
LADIYO kam ta kasa hawa,sai ta hau sai ta dawo k'asa,jikinta duk ta kurjeshi garin k'ok'arin hawa....
Daga saman dutsen TABAWA ta hango LADIYO yanda take ta faman kaiwa da komawa dariya ta tuntsire da shi,nan ta shiga kokawar komawa k'asa.....
Kokawa suka shiga yi na hawa,in da TABAWA ta rik'e hannun LADIYO kamar wasu k'ananan yara,tana koya mata yanda zata hau,har dai sukayi nasarar hawa saman dutsen.....
Guri suka samu suka zauna kan wasu fatu dake shimfid'e uwa tabarma,suna jiran zuwan mai gurin.....
_KUYI HAK'URI DA WANNAN FAN'S..._
*_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*Viawattpad@realsmasher01.*
*©®2018*
*27/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AH IDAN KAGA WANI DA SABON KAYA.*
_TUBLIY WAYUKHLIFULLAHU TA'ALA...._
_ILBIS JADIDAN,WA'ISH HAMIDAN,WA-MUT SHAHIDAN._
*_~#HISNUL MUSLIM.~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
_Aradu kuna bani dariya fan's en *Y'AR GARUWA* ,labarin nan gaba d'aya yanzun aka fara har hanzun ba ayi komaiba,kuci gaba da biyoni dan jin yadda za ta kasance.... *LUV U OLL.*_ 💔
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣9⃣*
*B*ayyanarsa kawai LADIYO ta gani wanda ba k'aramin tsorone ya cika mata zuciya ba....
Jikinta sai kyarma yake,duk ta firgita,sai neman b'oyewa da take a bayan TABAWA.....
Dariyar da ya kece da ita,wadda ta haddasawa d'an k'aramin forest en amsawa,mai kama da kukan jaki....
Ita ta sake rud'a LADIYO wadda a sanadin hakan har fitsari ta soma,ta mak'alk'ale TABAWA.....
Wata razananniyar tsawa ya mata yana fad'in
''Shiga hankalinki la'ananniya,b'atacciya,duk wanda yazo nan ya tabbata wakilin shaid'an,bama wa muminai aiki....
Idan kin san da sofanen imani a tare da ke maza ki b'ace anan tun kafin yaran shaid'anu su sauke fushinsu akanku''.....
Ya k'arashe maganar yana zare jaajayen idanunsa,masu kama da garwashi......
''A tafiyarmu babu tsoro,bamu san mene shiba bare muyi shi,idan har kin kiyaye wad'annan sharud'a,muna maraba dake yar jakar uba''.....
Ya sake kecewa da wata dariyar da ta fi ta farko....
Ita kam LADIYO yanda yake magana da dariyarsa shi yafi komai tayar mata da hankali.....
Harara TABAWA ta aika mata wadda tasa ta shiga hankalinta,ta zauna sosai,amma da zaka ce mata kyattttttt to kuwa zaka nemeta ka rasa....
Kafin su kaiga yin magana ya tare su yana fad'in
''Bana buk'atar kuce wani abu,nasan abunda ke tafe daku''.....
KEEE ya nuna LADIYO,kafin ya d'ora daga in da ya tsaya....
''Akan mijinki ne da kuma y'ar kishiyarki wacce mahaifiyarta ta rasu''.....
''Me kike so a yi wa mijin naki?
Kina so a kasheshi ne,ko kuwa a rabashi da y'arsa kamar yanda ya rabu da iyayensa, kar ya sake tambayarki in da take,ko kuwa kina so ya koma jin tsoronki tamkar ke kika haife shi?''...
Gyad'a kai tayi cikin farin cikin samun mafita,sannan ta shiga yi masa bayanin abunda take so ayi musu akan MALAM BUBA.....
Haka bokan nasu ya juya yana mai kecewa da dariya ya shige bukkar tasa......
Wasu uban layu ya fiddo ya mik'a mata...
Kinga wannan ya nuna mata wata k'arama daga ciki,zaki sata a cikin matashin kanki da kike bacci (pillow)....
Wad'annan kuma ki samu dai² bakin k'ofar d'akinsa ki hak'a rami ki binne su,idan kikayi haka kuma aikinki ya kammala,sai ki jira kiga mai zai faru''......
Ku tashi ku bani guri.......
LADIYO da shishshigi sai cewa tayi
''MALAM mene ne kud'in aikin nawa?''.....
Tsawa ya watsa mata yana fad'in
''Kaji y'ar jakar uba,mu nan ba a tab'a biyanmu idan mukayi aiki sai bayan aikinmu ya kammala.....
Maza ku bar nan,kada ku sake ku waiwayo''.....
Cikin sauri ko wacce ta suri takalminta suka kamo hanyar barin jejin,ko da wasa babu wacce ta juya,har suka fito daga ciki.....
**********
A fusace MA'U ta mik'e tana shirin dank'o KHUBRA da tayi tsaye....
Ba shiri tayi waje har tana neman fad'uwa du da dama jikintan ba wani k'wari ne da shiba.....
''Da kin tsaya ai y'ar jakar uba,yau da na nuna miki k'aryarki,dan yau na lahira sai ya fiki jin dad'i''.....
Ta fad'a tana huci,sai jijjiga jiki take,uwa wacce take shirin fad'a da sa'anta....
Komawa tsakar gidan tayi,nan ta shimfid'a d'an kwalinta,tayi sallah,ta ci gaba da jiran gawon shanu.....
Sai da ta raba dare a zaune a gurin ba tare da ta motsa ba....
Lokacin da ta tabbatar da LADIYO tayi nisa a cikin baccinta,ta mik'e ta lallab'a....
Gurin kayanta ta dosa d'an ragowar k'uli²n da ABBANTA ya bata shi ta d'auko ta ci,ta sake d'aurewa ta mayar...
Ta d'ebi ruwa ta sha,tayi godiya ga mahaliccinta....
Har ta gama abunda za tayi a d'akin MA'U bata san ta shiga ba.....
Sake komawa ta sake yi ta d'auko zani a cikin kayanta ta fito tare da jaa mata k'ofan....
A inda tayi sallah ta shimfid'a,hijab en jikinta kuma ta cire shi ta lullub'e jikinta....
Takurewa tayi guri d'aya saboda rashin girman hijab en ba zai kai mata ta rufe jikinta gaba d'ayaba.....
A wannan daren sai dai da yake an ce bacci b'arawo ne,amma da KHUBRA zata iya cewa ba zata iya bacciba...
Duk da baccin nata ya kasance rabi² ne....
Sai bayan da tayi sallan Asubah sannan wani nannauyan bacci yayi gaba da ita.......
************
Shigowar MALAM BUBA gida yana ta kwad'a sallama,yaji shiru ba'a amsa ba....
Nan ya shiga kiran LADIYO,jin shirun yayi yawa,ya shiga nemanta lungu da sak'o na gidan,amma ko mai kama da ita bai ganiba bare kuma itan....
Girgiza kai yayi ransa a b'ace yake fad'in
''Duk inda kikaje zaki dawo ki tarar da ni,kuma xa kiyi bayani,wannan iskancin na gaji da shi''.....
Yana gama bambamin fad'an nasa yayi waje......
***********
Kamar yadda ya musu bayani,direct gidan LADIYO suka nufa....
Gidan babu kowa,kasancewarsa haka kuwa da shigowarsu,suka hau dube²,bayan sun tabbatar babu mutum ciki,suka hau aiwatar da nufinsu......
Sai da TABAWA ta tabbatar sun gama aikata komai kamar yadda aka fad'a musu tukun,ta sake d'orata akan hanyar b'ata,wacce su a ganinsu ita ce dai²......
Sannan tayiwa LADIYO sallama,ta nufi hanyar nata gidan,babu fargabar tayi dare bata dawoba,za ta tarar da fad'a......
*********
Sai da gari ya gama wayewa sannan MA'U ta fito daga d'aki....
Kamar kullum cikin al'adunta,tana hamma had'e da mik'a.....
Mutum ta gani kwance,sai alokacin ta tuna abunda ya faru......
Batayi magana ba ta wuce bakin randa,sai da ta cika bokiti da ruwa,ta d'auko shi da k'yaar....
A dai² kan KHUBRA ta d'aga shi ta juye mata shi a kanta....
A firgice KHUBRA ta mik'e tana dube².........
*_~#TEAM KHUBRA...~_*
*_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*Viawattpad@realsmasher01.*
*©®2018*
*28/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'A YAYIN CIRE TUFAFI.*
_BISMILLAH!!_
*ADDU'A IDAN ZA A FARA ALWALA.*
_BISMILLAH!!!_
*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*
*~_________________________~*
_Sisinah ina miki fatan alkhairi arayuwa,ubangiji ta tashi kafad'unki,ina missing enki sosai na rashin kasancewa tare da juna.._
_Wish u a very quick and speed recovery *MY HUBBEEY* ,I so much heart u cweety.._💔💔💔
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*1⃣0⃣*
*T*saye akanta taga MA'U da k'aton bocket,tana ta faman aiko mata da uwar harara....
Mik'ewa tayi tana kama kayan tana matsewa...
Sunkuyawa tayi ta kamo zanin da ta shimfid'a...
Ko kafin ta kai ga d'aukowa MA'U dake tsaye bayanta ta d'irka mata hannunta mai kamar na maza a bayanta....
Lank'washewa tayi a gurin saboda azabar dukan da ya shigeta,ko bata fad'a ba....
Kuka ne ya kufce mata,ta shiga rerawa babu saurarawa...
Kamar mutuniyar arziki haka MA'U ta juya,a bakin randan ta ajiye bocket en ta sake dawowa ta wuce KHUBRA dake faman kuka uwa ranta zai fita...
Sai da ta kalleta kafin ta wuce cikin d'akin,ta d'an jima aciki sannan ta fito...
Hannunta d'aya a goye a bayanta,ta nufo inda KHUBRA take sunkuye ta saka fuskanta a tsakanin laps nata...
KHUBRA da bata san meke faruwa ba bare tasan abunda zai faru nan gaba,sai jin duka tayi ta ko ina yana ratsa jikinta....
K'ok'arin karewa ta shiga yi,amma hakan ya gagara...
Gaba d'aya MA'U ta hanata motsi,ta kama ta nad'eta acikin hijab enta....
K'ok'arin guduwa ta shiga yi,ga MA'U bata daina dukanta ba,ganin azaban yayi mata yawa yasa ta dage ta ingije MA'U ai kuwa nan sai ga MA'U a k'asa timmm....
Da gudu ta nufi hanyan fita daga gidan....
''Kada ki kuskura ki fita daga gidan nan,dan wallahi na lahira sai yafi ki jin dad'i yau,yarinya zaki gane ni kika tura na fad'i''...
Tana daga kwance a inda KHUBRA ta tura ta take koro bayani...
Da k'yar ta mik'e daga gurin tana d'ingishi,haka ta koma d'aki tana duba jikinta...
Hannayenta ta k'urje su,ga d'an yatsanta na k'afa da yake mata rad'ad'i....
MENTHOLATOM ta hau gogawa gurin...
Azabar da yake mata ce ta sata bari babu shiri...
Haka ta kafawa d'an yatsan nata ido,ganin ya soma kumbura ta tabbatar ta samu targad'e...
Dafe kai tayi tana jin rad'ad'in da yatsan ke mata har tsakiyar kanta...
Lallai wannan yarinya koi ja'ira,amma babu komai ta ciji lips enta,
''Zanyi maganinki''
Ta furta ciki².....
*************
Haka ta shige d'aki ko tunanin sallah batayi ba,tana shiga kuwa ta turo k'ofar d'akin nata...
Kwanciyarta tayi take kuwa bacci yayi awon gaba da ita....
K'arfe 9:15pm MALAM BUBA ya nufo gidan nasa,da tunanin ko LADIYO ta ga dama ta dawo?
Tun da ya tunkaro gidan gabansa ke faman fad'uwa...
Bai kawo komai a ransa ba,haka ya shigo gidan,k'ofar dake jingine ya d'aga ya karata a saitin k'ofan...
Juyawa yayi ya shiga da sallamarsa...
Da yake yasan ma koda tana nan ba amsawa za tayi ba,hakan ya sashi wucewa d'akinsa.....
Jiri ne ya fara neman kada shi,da sauri ya dafa wall en d'akin,ya daddafa ya shiga ciki,tun da ya shiga d'akin bai sake sanin inda kansa yake ba......
***********
Lek'owa tayi tana daga soron,jin shiru da tayi,shi ya bata tabbacin bata gurin...
Da sand'a ta shigo ta lallab'a ta kwashe kayanta daga gurin....
Kan wall en toilet en gidan ta kai ta shanya,ta dawo ta nemi guri ta zauna tana jiran gawon shanu,nan ta sake lulawa duniyar tunani...
'Daga labule taga anyi,ai kuwa karaf akan idonta...
zaraf tayi ta mik'e tsaye,tana rab'ewa gefe....
Harara MA'U ta aika mata,ta wuce ta shiga toilet,kamar ko wane lokaci,kafin cikar mintuna biyar har ta fito....
Kallon KHUBRA tayi kafin cikin wata irin murya ta hau fad'in
''Uban meye kike jira a nan?
Ki zo ki wuce ki samo ruwa sannan ki tabbata kin sharemin gidan nan''...
Sum² ta zo ta wuce,haka ta d'auki k'aton bocket en da MA'U ta ajiye,ta jaa silifanta tayi waje...
Lokacin da ta fita rasa ina zata nufa tayi,coz tun da tazo yau ne rana ta farko da ta fara fitowa...
Ta jima tsaye tana tunanin in da ya kamata ta nufa....
Tambaya ta yanke shawaran tayi,amma wa zata tambaya? unguwan shiru,babu kuma masu wucewa....
Haka tayi ta tsaiwa a gurin....
Gajiya tayi da tsaiwan,zuwa wani lokaci har ra fara gumi,haka kan dole tabi ra'ayin zuciyanta..
Gidan dake gefensu ta nufa,sallama tayi ta shiga...
Babu kowa a tsakar gidan,sai wata mata da ta gani tana fitowa daga d'aki...
Da d'an murmushi akan fuskanta ta amsa mata,tana fad'in
''Maraba,k'araso daga ciki''..
Murmushin itama KHUBRAN tayi tana fad'in
''Laa da kin barni ma daga nan''...
Gaidata KHUBRA tayi,kafin ta shiga tambayanta inda zata sami ruwa....
''Laaa kinga ai ba nisa ma,kina fita akwai gida da yake kallon nan,suna da rijiya''-....
Godiya tayiwa matar ta kama hanya ta fice,matar na binta da kallo....
Haka ta shiga gidan,suka gaisa da matar mai kirki,sai jan KHUBRA take da fira,ita kam ta kasa sakin jiki da ita,haka taita kaiwa da kawowa,har ta kammala d'iban ruwan.....
Bayan ta kammala haka ta duk'ufa kan shara,zuwa wanke²...
Lokacin da ta gama tana murna za ta huta,har ta nemi guri ta zauna,MA'U ta lek'o tana fad'in
''To hakima ba zama za kiyi ba,maza duba wancan d'akin akwai kwanuka maza ki tattarosu ki wanke su,idan kin gama kimin magana....
Haka ta shiga tattaro kayan wasuma har sun fara fungi,wani kuwa cikinsa yayi bak'i kamar an shafa kwalta...
da k'yar ta gama wankewa,ko da ta gama haka ta kwashi k'afafunta ta je k'ofar d'akin
''Na gama'' abunda ta iya fad'a kenan...
''To jirani'' MA'U dake d'aki ta fad'a....
Fitowa tayi da uban kaya a hannunta,haka ta watso mata su,ta sake komawa ta d'ebo wasu...
''Ga shinan maza ki tabbatar kin wanke su sun fita tas,dan idanma basu fitaba,zaki sake ne''...
Juyawa tayi tana k'arewa kayan kallo,gasu da uban yawa,ga kuma daud'a,wanda ko kayan d'an goye ba zai nuna musu daud'aba....
Har ta kai bakin k'ofa KHUBRA ta furta ''Sabulun wankin''....
Shigewarta tayi,sai da ta gama b'ata lokaci,sannan ta cillo mata...
Haka tayita gurzarsu,babu iyaka,har dai ta samu ta kammala,lokacin ana kiran sallan ISHAA.....
Ranar gaba d'aya KHUBRA haka ta yini aiki daga wannan sai wancan...
Haka ta tashi jikinta sai kyarma yake,ga ciwo da yake mata,ga tsananin yunwa,ga uban ciwo da kanta yake tamkar zai rabe...
Tashi tayi da k'yar ta tattara kayan da tayi amfani dasu,ta shiga d'akin shirgin nan ta gyara shi,duk da tana cikin wannan halin haka ta share shi...
Ruwa ta d'iba ta shiga ta wanke jikinta,sannan ta d'auro alwala,ta fara jera sallolin da ake binta bashi,dan kuwa MA'U hanata tayi ta motsa ko nan da can...
Tana yi tana ZUBAR HAWAYE,tana rok'on Allah gafara da kuma neman d'auki daga gare shi.....
Ta jima acikin sujudah tana rok'on Allah,kafin ta d'ago tayi tahiya,ta sallame....
Da k'yar ta iya motsawa daga gurin,ta lallab'a ta fito daga d'akin...
'Dakin MA'U ta shiga sai tare kanta take da hannu wanda ke mata barazanar fashewa...
''Dan Allah BABA ki taimakamin da abunda zan ci,wallahi ina tsananin jin yunwa,kuma kaina ciwo yakemun''
Ta fad'a kamar zata fad'i....
''Ke dallah dakata,karki fad'o kaina,dan kina jin yunwa shi ne me?
Malalaciyar kawai,d'an wannan aikin da kikayi kinzo kina min raki''.....
Haka MA'U ta koroto ba tare da ta tausaya mataba...
Kuka ta fashe da ta nemi guri abakin d'akin ta shiga rerawa...
Ashar en da MA'U ta k'unduma ne ya sata tsagaitawa...
Kamar daga sama ta ga MA'U da jakar kayanta a hannu,cillo mata tayi tana fad'in
''Idan zaki iya tafiya bismillah,abincine banga dama ba,kina iya ki nema da k'arfinki sai ki ci......
*_~#TEAM KHUBRA.~_*
*_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*30/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AR SHIGA BAN'DAKI.*
_BIMILLAHI!!! ALLAHUMMA INNIY A'UZHUBIKA MINAL-KHUBSI WAL-KABA'ISI.._
*ADDU'AR FITOWA DAGA BAN'DAKI.*
_GHUFRANAKA...._
*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*
*~_________________________~*
_The hole page goes to masoyana kuma masoya novels en *RAYUWAR WANI* da *Y'AR GARUWA* ,iya wuya ina k'aunarku nima kamar yadda kuke k'aunata Allah ya barmin ku aduk in da kuke..._
*_~#REALLY HEART U GUYS..~_* 💔💔💔
*~_________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*1⃣1⃣*
*T*ana gama fad'an haka ta juya ta shige d'aki,ba tare da damuwan komai a rantaba...
Sai da ta gama cin kukanta sannan ta tashi,ta tattare kayanta da suka zube,ta mai da su ciki..
'Dakin da ta gama gyarawa ta shiga ta sa kayanta daga gefe...
Nan ta takure guri guda tana mai had'a kai da k'afa,tana tunanin wannan rayuwar da ta tsinci kanta a ciki...
Cizon sauro shi yafi takurata,a d'akin haka suke kawo mata farmaki,ga zafi....
Zaman dirshan ta yi bacci ya gagareta,banda koran sauraye babu abunda take,wanda shima da k'yar take iya d'aga hannunta,daga k'arshe ma kasawa tayi,haka ta bar su tanaji tana gani,suke kawo mata farmaki...
Tana daga zaune ta jingina kanta a wall en d'akin,abun tausayi ga jikinta sai faman ciwo yake,ta rasa inda zata sa kanta,saboda azaba kanta kamar zai fad'o haka take jinsa,yanda take ji yasa ta fara cire tsammani da rayuwar duniyar...
Bakinta banda motsi babu abunda yake,da kallo kasan ba abunda take da ya wuce addu'a...
Idanunta a rufe haka hawaye ke layi ta gefen face enta,kukan ya gagareta.....
Da k'yar ta tashi lokacin da taji kiran sallah da asuba tana bin bango haka tayi alwala,ta sake komawa d'akin...
A daddafe tayi sallah daga zaune,ko addu'ah bata samu daman yi ba,wani wahalallen bacci yayi gaba da ita...
**********
Ba shi ya farka ba sai da gari ya gama yin haske,rana harta faso a garin...
Cikin wani irin yanayi na mutuwar jiki haka ya mik'e ya fita,yayo alwala ya dawo,a d'aki yayi sallah ya idar,haka ya zauna yana tunani amma ya rasa mai zai tuna...
A ganinsa akwai wani abu mai muhimmanci da yake son tunawa da shi,amma ya kasa tuna wannan abun...
Badan ya soba haka ya k'yale kansa,yana mai mik'ewa yayi hanyar fita daga gidan....
***********
Har gari ya gama haske rana ta gama haske garin,MA'U bata farka ba,haka itama KHUBRA,Bacci take a wahale...
Sai wajen k'arfe 12:30pm KHUBRA ta farka...
Idanunta take bud'ewa a hankali,duk sun kumbure saboda bata wani samu isashshen bacciba...
Sai da ta gama bud'esu tar,sannan ta mik'e ta zauna,sai da ta zauna ta huta...
Jikinta ba kamar da dare ba,yanzun har tana iya mik'ewa sosai,kantan kuma ta d'anji sauk'insa...
Kayanta ta tattare tana had'asu guri d'aya...
Tunawa tayi da abunda MA'U ta mata jiya kan dole ta mik'e ko dan kar a maimaita irin jiyan,ta d'auka tsintsiya tayi tsakar gida...
Tsaf ta share gidan ta,d'ebi ruwa tayi wanka,haka ta zauna a tsakar gidan,rana sai sake matsowa inda take.....
MA'U ce ta fito daga d'aki tana mik'a,ta nufi band'aki kamar wacce ake tunkud'awa,haka ta fad'a band'akin kamar an cillata,ko addu'ah babu...
Kamar sakkowar ruwan sama haka ta saki fitsarin da shigarta...
Tab'e baki KHUBRA tayi tana daga wajen,fuskarta duk maik'o...
A ranta take fad'in
''Wama ya sani ko ta fara a kwance ne?''...
***********
Tun fitowar ABBAN KHUBRA daga gida bai koma ba,haka ya yaci gaba da rayuwarsa a waje....
LADIYO an shanya baki sai bacci ake,ba ita ta tashiba sai azhur,ba don ta so tashin ba,sai dan cikinta dake ihun yunwa,fun da ta San babu wanda zai bata tana kwance...
Ba tare da tunanin gaida mahaliccinta ba ta shiga neman abunda za taci, rashin komai a gidan, yasata bazama neman MALAM BUBA haka take cilla fasassun k'afafuwanta...
Kitchen ta sake lek'awa neman duniya tayi aciki babu komai cikinsa sai busashshen k'anzon tuwo ta tsinto...
Haka bbau komai ciki bare mahad'i tayi ta garzarsa kamar akuya har ta cinye,sannan ta fito daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta....
Sai bayan ta samu nutsuwa ta zo mata tukun,wani tsoro ya sakko mata,tunanin abunda ya faru jiya ya dawo mata,nan ta tafi duniyar tunani...
''Shin yanzun idan duka wannan abun ya tashi a tutar babu fa suyi yaya ?''
Tunaninta ya tsaya kan da me zata biya kud'in aikin idan har aikin yayi,nan take wani mummunan tsoro ya sake cika zuciyar LADIYO....
**********
Sai da ta gama yauk'inta a cikin d'aki sannan ta fito tana jan k'afa,coz har yanzun ita kad'ai ta san me take ji saboda azabar da yake mata,k'afar duk ta dad'a hawa tamkar kwab'in bread......
A kan KHUBRA ta ja ta tsaya, #50 ta cillo mata cikin tak'ama tace
''Idan zaki iya ki je ki nemo garin kwaki,a shago''....
Ko gama fad'a KHUBRA bata jira tayi ba tayi waje,da hope en ta take tafiya,tana neman shagon da zata siyo garin....
Tayi tafiya mai nisa sosai sannan da tambaya ta samu ta siyo..
Kamar kowane lokaci haka take tafiya,kanta a k'asa,tafiya take har ta kusa da gida...
Kamar daga sama taga an tsaya gabanta..
Da sauri ta d'ago tana kallonsa kamar zai fad'o kanta saboda yanda yake layi....
Hannunsa da wani cukuikuyayyen tsumma,sai dannashi yake a baki...
Idanunsa sun gama rinewa uwa an watsa musu colour....
Wani dariya yayi yana mik'a hannu da shirin damk'ota,yana fad'in
''Y'an mata zo mana''...
Da sauri KHUBRA ta durk'she a gurin jikinta banda rawa babu abunda yake....
Sunkuyawanta shi ya bashi damar dank'an iska,ya sake mik'o hannu zai sake kamota....
Ai KHUBRA kam kan kace mene wannan ta k'arawa k'afafunta wuta,gudu take tamkar taga naman jeji....
Biyota ya shiga yi,yana maganar da ita kam bata san me yake fad'aba....
Gudu take tamkar k'afanta zata cire kan gudu,tana zuwa k'ofan shiga gidan ta daketa da k'arfi tayi ciki,ko tsayawa ta rufe bataiba...
Tai ciki a guje sai d'akin MA'U wanda tana kwance tana jiran dawowan KHUBRA ta ji an fad'o d'akin,kamar an tsikareta ta mik'e tana dafe chest enta....
Cikin tsoro kamar ita tayi gudun ta hau haki tana fad'in
''Me ya faru?''....
KHUBRA ta kasa magana sai k'ofa da take nunawa MA'U....
Ganin tana neman raina mata hankali shiya sata doka mata wata uwar tsawa,data sa jikinta sake ci gaba da rawa kamar an jona mata shocking....
Zuwa wani lokaci jikinta ya jik'e da gumi kamar an watsa mata ruwa....
Magana MA'U ta jiyo daga zaure,hakan ya sata lek'owa ta ga ko waye.....
Mutum ta gani sai layi yake,tana lek'awa ta dawo tana fad'in
''Caarrr uba dama wai abunda kikema gudu kenan,shegiya y'ar bak'in ciki,kin zo kin wuce ko kuwa sai na b'ab'b'laki.............
*_~#Ido na zare ina fad'in ''ina za ta,ba dai gurin wancan d'an magarunba.....~_*
____________________________
_MASOYA *RAYUWAR WANI* INA BAKU HAK'URI NA RASHIN TYPING DA BANYI BA A YAU,COZ KWANA BIYU INA JINA SAI AHANKALI,BANA JIN DA'DI SOSAI,INA FATAN ZAKUYIMIN UZURI.._
_____________________________
*_~#TEAM KHUBRA.~_*
*_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*1/ąpril,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
*ɛɖıɬɛɖ ცყ*
_HAFSAT M.U {rɛąl ɧą℘cყ}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AH IDAN ZA A FARA ALWALA*
_BISMILLAH!!!_
*ADDU'AH IDAN AN GAMA ALWALA*
_ASH-HADU AN-LAA ILAH ILLAH,WAHDAHU LAA SHARIKALAHU,WA-ASHHADU ANNA MUHAMMADIN ABDUHU WARASULUH..._
_ALLAHUMMA JA'ALNIY MINAT-TAWWABIYNA,WAJA'ALNIY MINAL MUTA'DAHHIRIYNA..._
_SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIKA ASHHADU ANLAA ILAHA ILLA ANTA ASTAGHFIRUKA WA-ATUBU ILAIK..._
*_~#HISNUL-MUSLIM~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
_Y'an uwa muna barar addu'ah daga gareku sis ena babu lapia,jikinta ya sake tashi da fatan Allah ya tashi kafad'unta.._
_Wish u a very quick and speed recovery MY HUBBEEY_
*~_________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*1⃣2⃣*
"Dan Allah BABA kiyi hak'uri wallahi d'an shaye² ne,sai neman fad'omin yake a ka d'azunma"...
"Ai wallahi yau ko nemanki zaiyi sai kin fita idan kuma ba haka ba na rantse sai jikinki ya fad'a miki"....
Tsaiwa taci gaba dayi jikinta sai rawa yake...
Ganin tana neman raina mata hankali yasa MA'U ta fice ta nufi d'akin shirginta...
Fitowa KHUBRAN tayi daga d'akin dan tun da taga ta fita tasan ba zasu kwashe ta dad'iba..
Karo sukaci da MA'U ta d'auko tab'arya,a guje tayi waje tana rafka ihuu...
Taimakon da Allah yayiwa KHUBRA lokacin da MA'U ta lek'a bayan ta dawo shi kuma ya juya ya fice yana faman tangad'i,ya nemi hanya yaci gaba gara rayuwarsa...
Tana fita ta tarar babu kowa,wannan shi ya bata sauk'i da ta fita bata ganshi ba tayiwa Allah godiya...
Ta d'an jima a tsaye a waje kafin ta juyo ta dawo da k'arfin gwuiwarta...
Wani malalacin kallo MA'U tayi mata wanda yasa ta sha jinin jikinta...
Kanta a k'asa ta gagara d'agowa...
''Munafuka da ana kije kina k'i yanzun daga wane gidan uwar kike?''
Ko tari batayi ba bare ta amsata,hakan yasa ta mik'o mata hannu tana fad'in
''Bani abunda kika samo''...
Idonta a waje take kallon MA'U
''Wallahi BABA banma ganshiba da na fita ''....
''Gidan wace uwar kika zauna da kika tarar bayanan?''....
''Sai ki wuce ki d'auka wancan abun ki ci''...
Sum² ta wuce ta d'auka tana shigewa d'akin shirgin nata....
Jik'awa tayi haka ta k'asumawa cikinta ko isashshen sugar babu a ciki...
Tun zuwanta garin wannan shi ne karo na farko da wani abu ya shiga cikin hanjinta,baya ga k'uli² da tayi ta k'amusa....
Tsaf ta share wanda ta jik'a, ita kuwa gogar spaghetti ta d'auko ta silala jellop akan idon KHUBRA sai k'amshi take ta sa gaba ta ci iya cinta...
Tana gamawa ko mintuna 10 bata k'araba a gidan tak'arawa k'afafunta wuta....
Sai KHUBRA dake faman gadin gidan ita d'aya....
Tana nan zaune tana fama da sana'ar tata,nan wani daddad'an bacci yayi gaba da ita...
**************
''Please Ki tsaya ki saurare ni my princess,nasan dai dawowan da nayi kike mamaki,ya akayi na dawo,fushi da ke bazai kaimuba..
Wannan kukan kuma bana son ganinki kina min asarar wad'annan precious tears en''...
'Dan murmushi sukama juna...
Kafin yaja hannunta yana fad'in
''Muje muyi fira toh''
Ya shiga janta zuwa wani k'ayataccen garden....
Gaba d'aya gurin ya k'awatu da wasu irin green en grasses,baya ga dogayen bishiyu masu tsananin kyau,gefe guda kuma k'orama ce take gudu ta ratsa ta cikin lambun....
Can daga gefe wasu fararen tattabaru ne suke shawagi daga sama zuwa k'asa suna wasansu,sai kukan tsuntaaye da ya dad'a k'awata shirun gurin...
Akan grasses en suka zauna,basu kai ga saman fararen kujerun dake zagaye da gurin ba....
Kansa ya d'ora akan cinyanta,suna firansu mai ban sha'awa...
Sai wasa take da bak'in suman kansa..
Idanunsa a lumshe kamar mai bacci,zuwa can ya mirgina yana kallon fuskanta...
Ganin kallon ba na k'are bane ta sunkuya dai² fuskansa ta hura masa iska,wanda ya sashi wani ajiyan zuciya...
A hankali ya shiga bud'e eyes ensa da suke brown colour tsakiyansu da wani haske tamkar na mage...
Janyota yayi yana mik'ewa zaune..
Fuskanta ya tallafe da hannu,ya dad'a matso da ita yanda suna jin fitar numfashin juna...
Bai jira komaiba ya had'e bakinsu guri d'aya sun jima haka,kafin wasan nasu ya canja salo....
Sunyi nisa acikin wata duniyar,wanda gaba d'aya KHUBRA a tsorace take da al'amuransa...
Turashi ta shiga yi amma ta kasa breaking abunda ke tsakaninsu...
Saboda rik'on da yayi mata ba na wasa bane..
Kuka ta fasa masa,wanda ya sashi cikata babu shiri,yana kallon cikin idonta..
''Haba wifey me kike nufi kuma,nifa naki ne,kuma ke tawa ce..
Yin haka dai² yake da nuna rashin kulawarki a gareni''..
Ita kam kukanta take babu ji...
Tun yana rarrashinta har abun ya soma bashi haushi...
Mik'ewa yayi a fusace yana shirin barin gurin...
Da sauri ta rik'o hannunsa tana girgiza masa kai...
Fisgewa yayi yana ci gaba da jaa baya..
Cikin wani irin murya ya soma fad'in
''Idan har na tafi daga gareki a yau ba zan sake ko da waiwayowaba...
Wancan lokacin na juyo zuwa gareki,amma wannan karon kada kiyi tsammanin sake ganina''..
''Dan Allah kayi hak'uri ka saurareni''....
Ci gaba yayi da tafiya ba tare da ya saurareta ba bare ya ji me zata fad'a....
************
Cikin wani irin firgici ta farka daga nannauyan baccin da yayi gaba da ita...
Dafe saitin zuciyanta tayi saboda wani irin matsanancin bugu da yake mata...
Tsoro duk ya gama bayyana a tare da ita....
Ta kasa fuskantar komai da ya danganci mafarkin nata,hatta kuwa da fuskansa da ta gani,ta kasa tunawa...
Tashi tayi da niyyan yin alwala,sai dai abunda ta gani ya sata fara kuka kamar wadda ake fitarma da rai....
***********
Duk son duniya irinta LADIYO yau itace taci k'anzo abunda bata tab'a tsammaniba ko da a mafarki...
Gidan ta shiga bincikewa ko zata samu d'an wani abun da zata ci da rana..
Tunda ta fuskanci MALAM BUBA baya gidan yau kam,kuma zaiyi wuya ta ganshi....
Kaf ta gama bincika ko ina amma ko k'wayar shinkafa bata samoba...
Haka ta dawo ta zauna a rumfa,kamar wata mutuniyar Allah....
***********
'Bangaren MA'U kuwa yini tayi neman abun duniya,sai sake cigiyan gidajen aiki take dan ita har ga Allah wancan ya mata arha da yawa...
Shi yasa ta yanke shawaran sake neman wani ko za a dace,amma ina haka ta yini tana yawo a gari....
***********
Duk da bawai yau ta fara ganin hakan a tare da ita ba,haka ta zauna tana kukan...
Coz ta san halin MA'U za ta iya cewa yawon iskanci taje....
Kukan da tagani ba shi ne mafita a gareta ba yasa ta bawa zuciyanta hak'uri,ta mik'e....
Cikin kayanta ta laluba nan ta binciko y'an pieces enta da take amfani da shi tunda bata saba da pad ba....
Tsaf ta gyara jikinta ta dawo ta kwanta kamar ba ita ba.....
***********
Sai bayan Maghreb sannan MA'U ta dawo a matuk'ar gajiye kamar wacce akawa duka haka ta shigo tana raba k'afa..
Da yake yawo ne kuma ita tasa kanta,duk da k'afar da take fama dashi,hakan bai hana mata zuwa yawoba.....
************
Shi kuwa ABBAN KHUBRA tunda ya fice daga gidan yaji bazai iya dawowa gidan ba...
Haka yayi ta zamansa a waje,da yaje kasuwa ma k'odagonsa,bayan ya tashi k'in komawa yayi...
sai dare ya koma gidan,shima sai da ya kintaci lokacin tayi bacci sannan ya nufo gidan.....
*_~#TEAM KHUBRA.~_*
*_REAL SMASHER._*🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*13/ąpril,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AH YAYIN FITA DAGA GIDA.*
_BISMILLAHI TAWAKKALTU ALALLAH WALA-HAULA WALA-QUWWATA ILLAHBILLAH._
_ALLAHUMMA INNIY A'UZHUBIKA AN-ADILLAH,AU'UDALLAH,AU'AZILLAH,AU'UZALLAH,AU'AZLIMA,AU'UZLIMA,AU'AJHALA,AU'YUJHALA ALAYYA.._
*ADDU'AH YAYIN SHIGA GIDA.*
_BISMILLAHI WALAJNA,WA-BISMILLAHI KHARAJNA, WA-ALALLAHI RABBANA TAWAKKALNA._
*_~#HISNUL_MUSLIM.~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*1⃣3⃣*
*T*ana shiga d'akin tayi shirim akan gadon tamkar kayan wanki,irin su MA'U irin matan nan ne da Sam basu da fasali a tsarinsu, bayaga d'an banzan son jiki da take da shi....
Kamar wacce aka mintsina haka tayi saurin mik'ewa tsaye tana raba ido...
Wani durowa ta nufa,daga jikinsa kuma cikin wani d'an sak'o,ta mik'a hannu,poly bag en dake wajen ta janyo ta hau bud'e cikinta,tana fito da kayan dake k'unshe a ciki...
Suphagetti ne da d'an dama dan idan basu fi 10 ba to zasu iya kaiwa hakan...
K'waya d'aya ta d'auka ta nufi hanyan fita daga d'akin,a zuciyanta kuma tana sak'e²,har ta k'idasa ficewa...
*********
Tana zaune ta idar da sallah ta rasa me ke mata dad'i a duniyarta,tunaninma yau kam tama kasa yinsa,duk jinta take kamar wata daban...
Hankalinta gaba d'aya baya tare da ita a wannnan lokaci,tayi zurfi wajen tunaninta,tana son tuno wane garima dangin mahaifiyarta suke?
Shigowar MA'U d'akin shi ya sata dawowa duniyarta babu shiri,cikin wani irin kallo ta jefeta da shi tana mai mik'o mata suphagettin dake hannunta,ba ko bayani ta sa kai ta fice..
Ita kam KHUBRA da ido ta bita dan zuwa yanzun ko dai bata gama sanin halin MA'U ba duka to tabbas ta san mafi yawan kaso daga halayentan..
Cikin sanyinta ta mik'e had'e da zare hijab en dake jikinta,ta fice tana sak'a da warwara...
Har ta kammala bata sake jin ko da motsin MA'U ba,duk da hakan ba bak'on al'amari bane a gurinta,amma sai duk taji kewa na damunta,na rashin wani d'an adam...
Juyewa tayi ta d'auka ta nufi cikin d'akin nata,tana ajiyewa ta juya ta fice...
Hakimar tana kallonta amma ko sannu bare ta sa ran jin wata kalma mai dad'i,haka ta banzatar da ita,mik'ewa tayi ta janyo plask en..
Sai da ta gama k'oshi sannan ta shiga rafka mata kira...
Cikin sauri ta shigo tana sunkuyar da kanta k'asa...
Kwanon ta nuna mata,bata tsaya b'ata lokaciba ta sungumeshi tayi waje,sanin ko ta ce bata ci,kanta zata zalunta...
Sai da ta tabbatar ta tsaftace duk wani abu da tasan tayi amfani da shi kafin ta nufi d'akin shirgi da a yanzun ya zama nata...
Kwanciya tayi cike da son ganin mutumin ta na mafarki,tana wannan tunani har bata san lokacin da bacci yayi gaba da itaba...
**********
Ko da MALAM BUBA ya shiga gidan direct d'akinsa ya nufa yana shiga kamar jiya da k'yar ya iya k'arasawa zuwa shimfid'arsa wanda baima tsaya tunanin ko lafiyaba ya kifa kamar wanda aka hankad'a,take wani nannauyan bacci yayi gaba da shi...
*********
MA'U ce zaune cikin d'akinta,ta rafka tagumi,tunaninta ta yaya zata samu hanyar da kud'i zasu dinga shigo mata,dan kam wannan rayuwa lamarin yana damunta...
Banda sak'a da warwara babu abunda take,zuciyoyinta biyu kowanne tana kawo mata shawaran da a ganinsu shi ne masalaha....
Ta tabbata idan akace zata ta'allak'a ne akan d'an abunda KHUBRA zata samu to tabbas tana cikin wahala,coz ta san halin yayarta da masifar son kud'i _(kunjifa wai kura ce za tace da kare maye)..._
Kafin wani lokaci mai tsayi zuciyarta ta gama rinjayarta,kwanciya tayi tana mai farin cikin samun mafita....
*IN THE MORNING* *******
KHUBRA dake tsaka da shara,ta d'aga kai ta kalli gurin da ta jiyo motsi,tayi matuk'ar mamaki da ta ganta a lokacin da batayi tsammaniba...
''Shin dama tana iya tashi da wuri haka,amma kullum sai ibada ta wuceta?''...
Haka tayi ta tunanin abunda sam bashida wata fa'ida a gareta...
Tana nan tana tunane² har bata san lokacin da MA'U ta gama shiryawaba,sai ganinta tayi ta fito hannunta rik'e da y'ar jakarta wacce akewa lak'abi da *_(JIK'ATA GUMIN HAMMATA)_*...
Hannunta rik'e da leda ta fito tana jaan k'afarta da har yau bata samu an gyaraba...
Naira #50 ta mik'a mata ''ki siyo garin kwaki''...
Daga haka ta wuce ta fice,har tayi nisa ta dawo,KHUBRA dake sunkuye har tsoro abun ya bata dan bata ga lokacin da ta dawo ba,sai magana taji a bayanta....
_''Idan kinga ban dawo da wuri ba kina iya rufe gidan''_
Haka ta shud'a tayi gaba....
********
Ko da ya farka da safe lokacin gari har ya gama haske,rana tana shirin mamaye sararin samaniya...
Istighfari ya shiga yi,coz har aka idar da sallah bai san anayi ba,abunda a iya tsawon rayuwarsa yau ne rana ta farko da yayi rashin sallah a jam'i...
Da matuk'ar k'unar zuciya ya mik'e ya fita don d'auro alwala...
A tsakar gida ya iske LADIYO ta fito banda susar jikinta babu abunda take,kamar wadda tayi wanka da _karara..._
Ta gabanta ya zo zai wuce,cikin rud'ewa dan tasan zai mata fad'an rashin sallah a kan lokaci ne,ta hau fad'in
''MALAM barka da tashi''
Ba tare da tayi tsammanin zai amsa ba...
Yana washe baki ya juyo yana kallonta ''Arrrhhh! hajajju LADIYO an tashi lafiya?''...
Da mugun mamaki ta d'ago tana binsa da ido,sai dai tana yin wani tunani kuma ta waske tana murmushin mugunta _(hak'ansu ya cinma ruwa)_.......
_#PLEASE FAN'S KUMIN UZURI DAN ALLAH NA RASHIN POSTING,UZURI NE YA MIN YAWA,DA YASA KO ONLINE BA NAYI,YAU KUMA NASO YIN TYPING EN BUH CIWON KAI YA HANA NI,IN SHA ALLAH ZA KUJINI ZUWA GOBE,DA YARDAR ALLAH..._
*_~#TEAM KHUBRA.~_*
*_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*16/ąpril,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
*ADDU'AR TAFIYA MASALLACI.*
_ALLAHUMMAJ'AL FIY K'ALBIY NURAN,WAFIY LISANIY NURAN,WAFIY SAM'IY NURAN,WAFIY BASARIY NURAN,WAMIN FAUQIY NURAN,WAMIN TAHTIY NURAN,WA-ANYAMINIY NURAN,WA-ANSHIMALIY NURAN,WAMIN AMAMIY NURAN,WAMIN KHALFIY NURAN,WAJA'AL FIY NAFSIY NURAN,WA-A'AZIMLIY NURAN,WA-AZZIMLIY NURAN,WAJA'ALLIY NURAN,WAJA'ALNIY NURAN,ALLAHUMMA A'A'DINIY NURAN,WAJA'AL FIY ASABIY NURAN,WAFIY LAHAMIY NURAN,WAFIY DAMIY NURAN,WAFIY SHA'ARIY NURAN,WAFIY BASHARIY NURAN,ALLAHUMMAJ'ALLIY NURAN FIY K'ABARIY,WA-NURAN FIY IZAMIY,WAZIDNIY NURAN,WAZIDNIY NURAN,WAZIDNIY NURAN,WAHABLIY NURAN._
*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*
*~________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*1⃣4⃣*
*B*akinta ta wage mai kama da k'ofar gari,hak'oranta kamar an shafa musu d'orawa...
''Lafiya k'alau MALAM''
Tana yi tana kwarkwasa kamar wata tsohuwar y'ar duniya...
Shi dai binta yake da kallo kamar wani wawa,haka ya sungumi buta yayi band'aki..
Ganin haka yasa itama LADIYON ta nemi guri ta k'ame kamar soja tana jiran ganin me zai kuma biyo baya...
Da mamaki take kallonsa yana alwala,mutumin da sallah bata wuce shi a jam'i amma shi ne zai yi sallah da wannan ranar...
Jikinta taja ta shiga band'aki,har lokacin bai bar gurin ba,itama tayi alwala...
Tana idarwa zata shiga d'aki taga ya biyo bayanta,da mamaki ta sake kallonsa,har ya shige d'akintan,ita kuma ta dafa masa baya...
A kan abun sallah ta tarar da shi yana washe mata baki yace
''Yi sauri kisa hijab muyi jam'i''
Ita dai ido ne nata,haka ya jasu sallan har suka idar...
After sun idar,ya shiga bata hak'urin abubuwan da yake mata,kamar wata uwarsa harda saka guiwoyinsa a k'asa....
Su LADIYO an samu abunda ake so,amma can k'asan zuciyanta tunani take akan yau shene shigowarsa ta k'arshe cikin d'akin nata,sai dai ta kasa tunawa...
Jin da tayi ana shafa jikinta,shi ya dawo da ita duniyarta..
Kallonsa tayi cikin mamakin hakan,ta kasa cewa komi...
''Haba uwar gidan MALAM BUBA kice wani abu mana kinyi shiru''
Ita dai binsa take da kallo,shi kuma sai dad'a shige mata yake...
Su LADIYO da jin haka,bata san lokacin da itama ta biyewa MALAM en suka ci gaba da shafar juna,har zuwa MALAM ya samu damar da yake nema a agurinta na cilla k'wallonsa a kwando....
Ihuuu LADIYO take tana fad'in
''Aradu MALAM kasan takan wanga harka,wayyoo dad'i,MALAM ci gaba''...
Hannu yasa ya rufe mata baki,saboda surutun nata ya soma bashi haushi..
Ita kuwa sai dad'a mak'alo shi take,kamar wata k'wad'uwa.... 😂
********
Duk wani aiki da za tayi sai da ta kammala shi sannan ta saka hijab enta..
Fitowa tayi daga gidan tana tafe cikin nutsuwa kamar yanda ta saba,haka har ta isa shagon,ta mik'a kud'in ya bata abunda zai bata,ta sake kamo hanya ta dawo...
Ko da ta dawo gidan babu ruwa sosai,hakan yasa ta fita da bocket tayi ta faman jido ruwa a mak'otansu har sai da ta cika komai dake gurin...
K'ofar gidan ta je ta kulle ta dawo,d'akin MA'U ta shiga ta kwanta a saman gadon MA'U tayi d'ai²,take kuwa baccin wahala ya d'auketa....
*********
Sai bayan komai ya lafa sannan LADIYO ta cika MALAM BUBA ta koma gefe ta kwanta...
Shi kuwa MALAM sai bayan da ya gama biyan buk'atarsa sannan ya tuna inda yake da kuma k'yamar kusantar LADIYON a yanda take,riga kad'ai ya saka ya nufi band'aki yayi wankan tsarki..
'Dakin ya sake dawowa,bai san dalilin da yasa yake jinsa wani iri ba,kamar mara lafiya...
Kud'i ya zaro ya mik'a mata kan ta samu abinda za ta dafa a gidan,karb'a tayi,shi kuma ya juya ya fice daga gidan....
********
Baccinta take ba tare da tunanin komai ba...
Tayi nisa a baccin,ta hangoshi kamar kowane lokaci cikin fararen tufafi,binsa take amma ta kasa cin masa,hakan ya sa ta durk'ushe tana kuka mai tsanani..
Kiransa take HAYATEEY,amma ko waigowa baiba bare ya kalleta....
Hakan da yayi mata shi yasa ta fasa k'ara ta zube a gurin sumammiya....
**********
Can cikin garin SUMAILA cikin wani k'auye ta sauka ta ci gaba da ratsa hanya har ta billo wani farfajiyar guri...
Gidane guda d'aya wanda ba shi da mak'ota ko k'waya...
Tunkarar gidan tayi ta shiga k'wank'wasawa ganinsa a kulle....
Bud'e mata wata y'ar yarinya tayi,tana mai bata hanya...
Murmushi tayiwa yarinyar ta bita suka shiga ciki...
A wani d'aki aka sauketa ta nemi guri ta zauna tana jiran fitowar MALAMIN...
Sai da ta shafe tsawon awanni 4 sannan mutumin ya shigo,daga shi sai dogon riga,duk ta k'udundune ga daud'a kamar ba jikin bil-adam ba...
Zama yayi yana fuskantar ta...
Ta bud'e baki za tayi magana ya d'aga mata hannu,alamar baya buk'atar tace wani abu.....
''Aikinki ba wani mai wahala bane,sai dai ta wace hanya kike so ta dinga kawo miki kud'in?''....
''Koma mene ne MALAM tayi bai dame ni ba in dai zata dinga kawomin kud'i''....
''An gama, sharad'in aikinki idan kika kuskure a cikin aikin da zan baki komai zai juya kanki''..
Tun bai k'arasaba tace
''Na amince''
Ta fad'a tana jiran ganin,me zai biyo baya...
Nan take ta ciro wasu layu da kuma k'ullin garin magani,ya mik'a mata...
''Wannan ya nuna layun,zaki binnesu a tsakiyar hanyan da jama'a suke bi...
Shi kuma wannan k'ullin ya nuna mata garin maganin,za ki barbad'a a bakin k'ofar d'akin da kija san za ta tsallaka....
Ki tabbatar ta tsallaka shi,saboda shi ne cikon aikin ki,zai sa mata farin jini wajen mutane,sai dai babu wanda zai zo da niyyar aurenta,zaki samu mahaukatan kud'ad'e ta dalilinta''......
Jin an ambaci mahaukatan kud'i ta shiga b'are baki,dan murna....
Kud'i ta fitar a jakar tata ta mik'a masa,ta masa godiya ta kama hanya,tare da alk'awarin dawowa...
********
Firgitan da tayi yasa ta farka,ga sautin k'ara da ya ratsa kunnuwanta wanda bata san daga ina yake ba,sai bayan ta farka ta fuskanci inda k'aran ya fito,ashe da tayi kenan ba iya cikin bacci kad'ai tayi ba har a zahiri tayi...
Addu'ah tayi ta mik'e tad'auro alwala,ta jima tana neman sauk'in al'amura daga ubangiji,tare da kariyarsa a gareta...
Sannan ta mik'e,ta d'auki garin kwakinta tayi waje.....
Ko rabi bata iya ciba taji ta k'oshi,hakan yasa ta maida ragowar ta b'oye.....
Tayiwa Allah godiya,ta sake kwanciya,tana tunani kan wannan rikitaccen mafarkinta.....
Da yamma tana kwance a tsakar gidan,maranta taji tana tsunkulinta kad'an² take ta gane abunda yake shirin faruwa da ita,tashi tayi ta kintsa jikinta,ta dawo ta ci gaba da sauron kukan tsuntsaye dake kan bishiyar mak'otansu,haka har akayi sallan Maghre...
Sai lokacin wani tsoro ya ziyarceta,take kuwa ta sake k'ulewa a d'akin MA'U....
**********
Cikin dare sosai ta iso,k'ofar ta shiga bugawa da iya k'arfinta...
Jin bugun yayi yawa yasa KHUBRA ta fito ta bud'e coz ta gane mai bugun,sai a lokacin ta samu nutsuwa....
Duk wani shiri na MA'U ta gama k'udurce a daren ranar zata aiwatar da komai,hakan ne ma yasa ko gidan bata nufoba sai da ta aiwatar da nufinta...
Lokacin gari ya dad'a yin shiru ta fito ta k'arasa abunda za tayi,ta koma zuciyarta wasai,sai kuma jiran ganin abunda zai biyo baya..........
#UHMMM!KU BIYONI DAN JIN YANDA ZA A K'ARKE..
LUV U.....
*_~#TEAM KHUBRA.~_*
0 comments:
Post a Comment