Jin yanda yake sake rintse hannunta dake cikin nashi ne ya sanya tayi saurin kallonshi, suka had'a ido tayi saurin saukar da nata 'kasa tana motsi da bakinta, so take tayi magana amma saboda tsabar kwarjinsa ya sanya takasa, sai kawai ta cigaba da kallon gefe guda tana jin yanda yake shafa tafin hannunta a hankali a hankali, lokaci 'kankani taji duk jikinta yayi sanyi idanunta suka soma lumshewa da alamun bacci a tare da ita, kanta ta dora jikin murfin motar tana takure jikinta hade da runtse idonta gam! wannan abin da yake mata sam bata so wani ya gani a cikinsu khalifa dake gabansu, Allah ma yasa hirar da sukeyi ta dauke musu hankali da yake rashida akwai saurin sabo duk garin da suka wuce sai ta tambayi khalifa sunan garin shi kuma ya fada mata tare da cikakken bayani.......Yana kallonta ta takure jikinta a jikin murfin mota idanunta a rufe, sai ya sake matsawa jikinta sosai ta bude lumsassun idanunta da suka soma sauyawa bacci ne ko meye oho! a hankali ya kamo ha'barta ya d'ora kanta kan kafad'arshi kana ya zura hannunsa 'kar'kashinta ya ri'ke 'kugunta sosai ya matso da ita jikinsa ya ri'ke da kyau!! Rintse idonta ta sakeyi tana sauke ajiyar zuciya gabanta na d'an fad'uwa kad'an-kad'an! Kamshin turaran jikinsa ne yayi masifar tafiya da imaninta abinda ya sanya ma kenan ta sakeyin luf a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, jikinta ya soma shikawa bacci na fizgarta mai dad'i......Jin shirun tayi yawa ne ya sanya Khalifa d'an juyowa yanayi masa magana, sai kawai idanunsa ya gane masa abinda ke faruwa, Abokin nashi ya gani ya wani yi la'kas! dashi hankalinsa kacokan na kan Wasilan da bacci me nauyi ya dauketa a jikinsa, shi kuma ya kurawa fuskarta ido fuskarshi dauke da wani munafikin murmushi.....Khalifa ya danyi gyaran murya yana fad'in "Kaga yanzu mun wuce gaidan! garinsu Alhaji Yunusa mutumin nan dake kawo mana shanun sallah." Ya dago kanshi yana kallon khalifan yana ya mutsa fuska yace."Nagane shi koba wannan madamfarin mutumin ba? kasan akwai sallahr da ta gabata nasa shi ya kawo min shanu irin wanda nake sadaka dasu, ya kawo marasa lafiya cikin guda goma uku ne suka rayu naji ciwon abinda yayi min shiyasa na daina siyan shanu a gurinshi." Khalifa yace." Nima tuntuni munyi hannun riga dashi dama ai nine na had'aku dashi ko?" Gyad'a kanshi kawai yayi ya sake gyara zamanshi wanda hakan ya sanya kanta ya sauka a kirjinsa a maimakon kafadarshi, gyara ta yay sosai ya tallafeta da hannunshi guda.....Khalifa ya kalleshi shima ya kalleshi sai yayi mishi nuni da Rashida da bakinshi, basarwa yayi ya nunawa Khalifa shi ina ruwanshi da wata rashida! Abinda basu sani ba kuwa shine ba rashida ba har su Garba sun d'an hango abinda ke faruwa basarwa kawai sukayi......Murmushi kawai Khalifa yayi ya juya yana mamakin abokin nashi, idan ance masa yana son yarinyar sai yace ba hakaba gashi lokaci 'kan'kani duk ya wani susuce a cikin mota.
Kuluwa ta fito daga cikin d'akinta hannunta rike da wani 'kullin kaya, wanda zanin da aka d'aure kayan yayi da'kal-da'kal da daud'a, ta nufi inda Uwani ke sunkuye da wata 'katon baho a gabanta, wacce ta cika ta da kayan wanki ta zuba klin da sabulu a hannunta tana cud'awa! Kuluwa ta dire 'kullin kayan dake hannunta tace"Uwani idan kin gama wankin dan Allah ki d'an sa'be wa 'kananan yaran nan kayansu tuntuni nake so nayi wanki bani da sabulu kina dai kallo kwana biyu gidan sai a hankali yanzu Kawunki baya fita komai ya rinca'be mana." Uwani ta d'ago kanta cikin tsananin wahala da gajiya tace"Kuluwa kinga dai sabulun nan banawa bane na mutane ne dan Allah ki bari a wankewa mutane kayansu ya fita wai me yasa duk sanda zanyi wanki sai ki kwaso min kayan yara kice na wanke alhalin kin san sabulu da omo ba nawa bane nima aikatau nakeyi a biyani."
Da jin abinda Uwani ke fada sai Kuluwa ta fusata ta soma sirfa mata masifa da fad'in wallahi duk sanda ta sake yi mata musu kan abinda ta umarce ta dashi to sai ta bar mata gidanta." Uwani dai ta cigaba da gurxar wankinta bakin ciki duniya kamar ya kasheta, tun safe take wankin jama'a har yanzu bata karya kummalo ba, ko da yake sai ta g
ama wankin ta kai sannan zata samu kudin da zata siyi abin karin dashi dan tuntuni Kuluwa ta daina bata abin kari a gidan, da daddare kawai take bata abinci shima d'an mitsitsi idan towo ne kuwa sai ta lakata mata 'karshen kwasa cikin kwano wanda yaro 'karami ma yaci ba zai isheshi ba.
Tana gurxar wanki hawaye na 'kokarin su'bce mata, wannan wace iriyar masifa ce take cikinta? tayi dana sani tayi nadama tayi da ace abinda ya wuce zai dawo baya data yi gaggawar gyara kuskuranta, wannan wuya da take sha tasan duk itace ta jawowa kanta, Allah ya kawo musu dauki ita da 'yarta ya had'ata aure da mai kudi mai mu'kami amma sabida hange da mummunar kaddara ta dinga zugar 'yar tata ta kashe auranta, yanzu wa gari ya waya? wahalar da take ciki a yanzu ta wuce wacce taci a baya, a gidan Kawunta ana bata abinci taci ta koshi anan kuwa sai dai ta nema ta ciyar da kanta, Kawu Madu sallamamman namiji ne mijin tace sai abinda kuluwa tace ayi a gidan yake yi shiyasa duk abinda yake faruwa da rayuwarta baya tofawa, tun bayan tafiyarsu Wasila da kwana uku Kuluwa ta soma gallaza mata kyara! da hantara! da masifa! da kuma horan yunwa! ganin hakane ya sanya Ta nemi Inna Tabawa tana kuka take shaida mata halin da take ciki, itama Tabawar ta tausaya mata sosai sai da bata da yanda za tayi tunda itama talakace, sai kawai ta bata shawarar kan cewar ta kama sana'a sai ta rike kanta, saboda ba komai ne yake sanya Kuluwa nayi mata rashin mutunci ba saboda tana bata abinci ne." Uwani tace"Dama can baya nayi sana'ar wanki indai zan samu anan to wallahi zanyi na rufawa kaina asiri." Tabawa tace"Kada ki damu idan Allah ya kaimu gobe kizo gidana mu tafi cikin gari Unguwar amare zamu mubi gidajen mutane idan suna da wankau su bamu." Uwani tace"To shikkenan."
Aikuwa gari na waye wa Ta shirya ta tafi gidan tabawa, suka dauki hanyar cikin gari.......gida biyar suka samu wanki aikuwa Uwani ta zage ta wanke musu kayansu ta shanya musu tsaf suka biyata kudinta, ranar sai yamma suka dawo gida, Uwani ta bawa Tabawa kudi cikin kudin da samo ta 'boye sauran a jikinta......Tun daga sannan Uwani ke zuwa unguwar amare tana musu wanki watarana kuma ta d'oro kayan saman kanta ta tawo dashi gida sai ta wanke su bushe tsaf sai ta kai musu su bata kudinta.
Da 'kyar Rashida ta iya gane hanyar gidan ta dinga nunawa Garba hanya yana bu ta cikin kunyar gonakin mutane gwajab gwajab din da motar take ya sanya ta bud'e idanunta tana d'an motsawa, sai kawai taga duk rabin jikinta a jikinshi, yayin da shi kuma yayi wani irin zama a cikin motar kamar wanda zai kwanta yayi hakan ne domun taji dadin yin baccin a jikinsa........Da sauri ta mike zaune tana gyara xamanta had'e da gyara mayafinta ta d'ora saman kanta.......Ya mi'ke zaune sosai yana ya mutsa fuskarsa, hakuri kawai yake yi amma wannan kwanciyar da tayi a jikinsa ta ya mutsa shi, sosai ya d'an saci kallonta sai yaga tana hamma! da alamun baccin bai isheta ba, sai kuma ya mutsa fuska takeyi cikinta ne ya soma 'kullewa yunwa na sasakarta dama 'ka'ida ne idan tayi bacci ko yayane ta farka sai taci abinci.......Jikinta ne ya soma rawa, ta dinga zare ido tana mutsu mutsu ta rasa ya za tayi a yaron dake cikinta yana mata wani irin motsi da zillo tare danno mararta kamar me shirin fitowa waje, cikin rawar murya tace"Rashida ina kayanmu suke."? Rashida tayi saurin juyawa tana kallonta ganin yanda idanunta suka kad'a ne ya sanya ta gane yunwa takeji da sauri tace" Suna bayan mota." Still murya na rawa tace"To sai kizo ki dauko min kin san dai cewa nayi ki rike min a hannunki saboda zan iya bukatarshi cikin ko wane irin yanayi me zai sanya kisa a cikin akwati.'' Rashida tace."Yi hakuri anti Wasila ai mun kusa sauka." Tsaki taja tana motsa bakinta.....Ya kalli Rashida cike da kulawa yace."Menene."? Tace." 'kwai dafaffe ne Bitan ta bata shine tace na ri'ke mata a hannu na ni kuma wallahi na manta nasa a cikin jakar kayanmu gatacan a bayan motar." Shiru yayi kawai ya juya bayanshi da kanshi ya kinkimo jakar kayan nasu ya d'ora saman cinyarshi ya zuge zif din jakar ya soma dubawa.....Nan ya d'auko daurin leda yaluwa da dafa
ffan 'kwai a ciki kusan guda ashirin, a jikinta ya d'ora ledar ya mai da zif din jakar ya zuge kana ya maida ita inda take ya gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Gashinan karkiyi kuka gama naga shi kike shirin yi." Shiru tayi masa ta cigaba da kokarin kwance ledar.......Kar'ba yay ya kwance mata ya d'auko d'aya ya soma 'bare mata , ya mi'ka mata ta kar'ba da sauri gutsira biyu tayi masa ta cinye.....Tana kallon hannunshi dake kokarin 'bare mata wani, Haka dai yayi ta aikin 'bare mata kwai tana taunewa sai da taci guda tara sannan ta hakura ya mi'ka mata ragowar ruwan swan din da yasha d'azu ta 'karba tana sha tana lumshe idonta sai yanzu taji dama dama a jikinta.
Uwani na tsaka da shanya kan katanga taji tsayuwar mota, dake katangar bata da tsayi sosai ana hange na waje kafin ta ankara taga Rashida ta fito daga cikin motar Wasila ma ta fito da sauri ta ajiye rigar dake hannunta ta nufi cikin dakin da take kwana mayafi ta dauko tayi hanyar fita tana kokarin yafawa a jikinta, a soro sukayi kicibus da Rashida sai ta rungumeta tana fad'in "Rashida sai yau kuka tunani dani ko? ke da waye a cikin mota ina Wasila ya jikin nata."? Rashida ta dinga kallon mahaifiyarta ta ganinta gaje gaje yayi masifar daga mata hankali, Wasila ta shigo ta gansu sai itama ta shiga bin Uwanin da kallo jikinta sharkaf da ruwa......Gashi duk tayi wani wujuga wujuga da ita. Uwani ta rumgume Wasila tana hawaye tace" Yarinyar nan kullum dake nake kwana nake tashi a raina Alhamudullihi jiki yayi kyau masha Allahu ga cikin ki ya girma dama ai nasan mutukar kun koma gaban mai allo zai kula daku mutum ne shi mai tausayi kuma yana kaunarku." Wasila da Rashida suka shiga binta da kallo jin abinda take fad'a kan mai allo wai yau Uwani ce ke yabon mai allo lallai duniya.
Gidan suka shiga gabad'ayansu, Wasila ta dinga bin gidan da kallo ko ina kaca kaca da kazanta iri iri ga wani wari na tashi da alama shaddar gidan ta cika tana bukatar agaji warin yayi yawa.....Ta dinga bin mahaifiyarta da wani irin kallo na tsantsar tausayi da jin kai. a hankali tace"Uwani wannan wane irin 'kuraje ne a jikinki? dubi yanda fatar jikinki ta kod'e kinyi wani iri duk kin rame."! 'Kwallah ta cika kwarmin idon Uwani tace"Ku mu shiga ciki babu komai." Bin bayanta sukayi suna mamaki tabbal akwai abunda ke faruwa da mahaifiyar tasu.........Kuluwa ta fito daga dakinta kirjinta daure da dadd'aud'an zani!!! kanta babu d'ankwali tamkar hammatar d'an iska yayi wani cibiri cibiri dashi dan saboda tsabar dauda gashin kan nata har ya soma d'aukewa da kanshi wani guri da a kwai wani gurin babu.....Ganinsu Wasila yasa tasha kunnu tana fad'in "Ku kuma yaushe kuka zo."? Wasila tayi saurin kauda kanta daga kallonta dan ji tayi tsigar jikinta na tashi kallon gashin kanta ya sanya mata tashin hankali amai na taso mata....Rashida tace" Yanzu muka zo Baba mun same ku lafiya."? Kuluwa tace "Lafiya lau ina fata dai yau zaku juya domin dai muma bamu da abinda zamu baku koda yake dai ga uwarku nan na neman kudi zata iya daukar dawainiyarku." Babu wanda yace mata ta tafasa ballanta ta sauke suka shige dakin ina Uwani ke zaune tana jiran shigowarsu......Nan suka tarar da ita a zaune a gefen wata guntuwar tabarma ta zabfa tagumi! Wasila ta dinga bin dakin da kallo daki sai kace zai rufta ya durkushe gashi babu labule babu ledar kasa sai wata guntuwar tabarma wacce take nuni da cewar nan ne makwancin mahaifitar tasu.....Kwallah ta zubo mata murya na rawa tace"Uwani wannan wace irin rayuwa kike ma'kaskanciya, wannan d'akin da kike ciki ya ru'be wallahi saura kad'an ya rufta bakya tsoro watarana ya rufta dake."
Uwani na hawaye tace"Ya zanyi Wasila! Ya zanyi? nice na cuci kaina na kuma cutar daku na tabbata da kina gidan Alhaji Ahmadu da duk wannan wahalar bamu shigeta ba, nasan da tuni munfi karfin gurin zama da ci da sha da suttura, na cuci kaina na cutar daku Ubangiji Allah ya yaye mana wannan masifa."!!! Ganin tana kuka sai suma suka fara kuka ta goge hawayenta tana fad'in "Idan dan kunga ina kuka kuma kukeyi to na daina yi sai kuyi shuru." Wasila ta goge fuskarta tana kallonta.....Uwani a nutse
ta soma basu labarin wahalar da takesha a gidan da yanda kullum take cin ruwa sai kace agwagwa.
Wasila tace"Ai dole sanyi ya kamaki Uwani wannan wace irin masifa ce ace kullum mutum na cikin ruwa dubi fatar jikinki ta kod'e ta bushe ga wasu kuraje marasa kyawun gani sun feso miki a jiki.
Uwani tace"Wai sunanan ina sha musu magani da ai sunfi haka yawa a jikina." Wasila ta shiga girgixa kanta tana tunanin yanda za tayi ta kubutar da mahaifiyarta daga wannan ukuba.
Uwani ta kalli Rashida tace"Wai waye ya kawo ku a mota ne."? Rashida tace"Alhaji Ahamadu ne mijin aunti Wasila." Da sauri ta kalli Wasilan tana neman karin bayani......Rashida itace ta shiga fada mata yanda al'amura suka faru.....Uwani ta dinga washe bakinta tana fad'in "Alhamdullhi Allah nagode maka daka amsa adduata kullum.burina mutumin nan ya dawo garemu naji dadin wannan zuwan naku kuma yau zanyi bacci harda munshari." Wasila tace"To sai ki sauya kaya kije soro ku gaisa dan da kunya a shigo dasu wannan 'kazamin gidan." Uwani ta mike da sauri ta bude jakar kayanta ta dauko atamfar data rage mata dan duk kayan da tazo dasu Kuluwa ta sace taje ta siyar, sai dai kawai in ta fita taga kayanta a jikin mutane idan ta tambayesu sai suce kuluwa ce ta siyar musu shaddar wasila ma data sace gidan ma gari ta kai suka siya.........Suna kokarin fita daga cikin gidan Kawu Madu ya shigo gidan yana washe bakinsa hannunsa rike da kud'i sabbin 'yan dubu dubu kar kar dasu......Kuluwa yake kwad'awa kira ta fito daga d'aki da saurin gaske dan har zaninta na 'kokarin fad'uwa ta rike da kyau! tana fad'in "Malam ya akayi ne." Yace."Ki fito kizo ki dangwali arziki ki barshi ashe yarinyar nan Wasila matar babban mutum ce, ikon Allah yafi gaban wasa! Kuluwa kinga uban kudin da mijinta ya bani yana waje shi da abokinsa sunzo cikin wata 'karuwar mota kamar jirgin sama."! A d'amauce! Kuluwa tayi hanyar waje tana tafiya kamar zata kifa 'kasa saboda sauri! Kwata kwata ta manta a halin da take ciki babu dankwali da riga daga ita sai daurin kirji.....
Littafin na kudi ne....!
Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah What'spp numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*64*
Da sauri Uwani ta tare bakin 'kofar fita tana kallon Kuluwan cikin mamaki tace"Haba Kuluwa dubi yanayin da kike ciki babu suttura a jikinki kanki babu dankwali sannan kuma kike 'kokarin fita haka gaban siriki karfa ki manta mutumin nan babban mutum ne kamar yanda Kawu ya fada miki idan kin fita haka ai kin zubar mana da kima da mutunci ." Kuluwa ta hau ya'ke tana washe baki tace"Wallahi duk na manta babu riga a jikina Uban kudin dana gani hannun Malam su suka gigitani amma bari inje in sanyo riga ku jirani dan Allah." Da sauri ta koma cikin gidan jikinta sai rawa yake.....Wasila da Rashida suka bita da kallon mamaki matar mayyar kudi ce duk ta fita daga hayyacinta.....Kawu Madu kuwa na tsaye sai dariya yake yana ta dangwalar miyau a hannunshi yana lissafa kudin hannunshi, kamar zautacce ya kalli Uwani yace."Uwani kudin nan dubu hamsin ne wallahi! kai masha Allahu gaskiya naji dad'in zuwan mutumin nan Uwani ashe haka Allah yayi wa 'yar arziki amma saboda baki da hankali kika kashe mata aure, saboda kina mata bakin ciki, waye ya fada miki yanxu ana wasa da auran irin wad'annan mutanan? ai duk abinda ya faru ya fad'a min yanzu kafin na shigo sai ku godewa Allah da Allah yasa ya mai da auran dan da bai mayar da auran ba to da kun cutar damu wallahi dan wannan arzikin sai da mugani a nesa amma yanzu ko banza nasan zamu dinga samun zakka a kai a kai! idan Allah ya nufa ma wataran sai da kawai naji ance na fito an biya min kujerar makkah." Kawu Ya 'kare maganar tashi yana dariya had'e da gyara babbar rigarshi yana sake gyara xaman kudinshi a aljihu........Kuluwa ta karaso cikin wata kod'ad'diyar atamfa da wani ya mushashshen mayafi da duk ya tattare saboda tsabar yaga jiya da yau wai nan sune karshen adakarta, sai wani washe baki take ta kalli Uwani tace"Ai haka yayi ko."? Uwani dai shiru tayi dan bata da abince wa sam ma bata so Kuluwa ta bisu gani take zata iya yin wani abun na rashin hankali ita kuma bata so yanzu mutuncinsu a zube a gurin Ahmadu......Kawu ne yay gaba suka biyo bayanshi
A babban soron gidan suka tsaya Kuluwa sai l'eken kofar gidan take dan Kawu cewa yayi su tsaya anan zai shigo dashi Kuluwa duk ta 'kago sai d'aga kai takeyi tana lekawa.....Wasila taji tamkar ta gaura mata mari shin wai ita wannan matar wace irin mata ce mara kintsi da kamun kai.? 'Kamshin turaranshi ne ya bakuncin hancinsu gabad'aya, Uwani ta gyarq lullubinta hade da sunkuyar da kanta 'kasa kunyar hada ido take dashi sosai, Ita kam kuluwa fad'i take "Sannunku da zuwa Alhaji sannuku." Ahmadu da Khalifa suka samu gefe suka tsuguna a nutse aka fara gaishe gaishe, Ahmadu ya kasa tantance mahaifiyar matar tashi duk da ya ta'ba ganinta sau d'aya amma dai baya tunanin Kuluwa itace saboda yanda ta za'ke da yawa sai banbad'anci takeyi tana musu hirarraki Mikewa sukayi a tare Khalifa ne ya fara yin gaba shi kuma ya tsaya yana gyara rigarshi, kuluwa ta tsura mishi ido Kudi ya fito dasu daure a kyaure ya mi'kawa Wasila dake gefanshi a hankali yace."Ki bawa Momy ko." 'Kin 'karba tayi Kuluwa tayi wuf ta kar'be kudin tana washe baki da fad'in "Ai kunya ba zata bari ta kar'ba Alhaji Mungode kwarai Allah ya tabbatar da alkairi ya baku xaman lafiya." Uwani da Wasila ba suji dadin Abinda Kuluwa take ba, sai basu da yanda za suyi da ita......... Kuluwa da Kawu har bakin mota suka rakosu suna musu godiya da fatan alkairi, jama'ar garin sun taru suna mamakin irin bakin da Kawu Madu yayi, sai bayan motarsu ta 'bace daga gurin ne Kawu ya shiga yi musu bayani cewar Ai sirikin sa ne mutumin dake auran 'yar gidan Uwani 'yar 'kanwarshi.....
Uwani cikin gidan ta koma ta shiga daki ta had'a tagumi hawaye takeyi sosai takejin kewayar 'yayan nata amma ko babu komai zamansu a gidan Ahmadun sai yafi mata kwanciyar hankali fiye da su zauna a wani guri itama ta yarda mutumin nason 'yarta dan da baya sonta da bazai mayar da ita ba duk da tarin laifin da tayi masa.
Bayan azuhur suka sauka gajiya gami da jiri da zaman mota suka taru sukayi mata yawa, dan da kyar ma ta iya fitowa daga motar kafafunta duk sun sage sunyi tsami! Tana dan ya mutse fuska t
a rike hannun Rashida tana kokarin zama gefan shuke shuke! Ya fito daga cikin motar hannunshi rike da babbar rigarshi, Garba ya kar'bi rigar da wayoyinshi, hankalinshi na kansu yaga tana matse fuska cike da kulawa yace."Lafiya menene."? Shiru tayi mishi." Ya kalli Rashida yace."Ku shiga ciki mana karki bari ta zauna anan." Rashida ta kama hannunta suka soma tafiya, 'kafarta ta dama ce ta ri'ke ta kasa takuwa, ta rintse idanunta tana salati, dama tun a cikin mota takejin yanda cikin ke tattare mata yana dunkule mata guri guda, kwallah ta cika mata ido bakinta na rawa tace"Rashida 'kafana d'aya ta ri'ke gefan marata ya daure." Rashida tace"Ki daure anti wasila zaman mota ne yaja mu shiga ciki ka zauna sai in matsa miki kafafun naki." Yana tsaye suna magana da Garba yaga sun tsaya sai ya sallami Garba ya nufi inda suke.......Rashida na ganinshi tace"Wai kafarta ciwo take." Yace"Subahanallahi! to me ya jawo hakan."? Rashida tace "Nima ban sani ba watakila kuma zaman mota ne." Ya kalli Wasilan yaga tana kuka tana kokarin zama kasan gurin......Yace."Kada ki zauna anan mana tashi mu shiga ciki ki samu kiyi wanka sai ki kwanta ki huta."
Shiru tayi ta'ki tanka masa bala'in haushinsa takeji a ganinta ba kowa ne ya jawo mata wannan masifar ciwo ciwon ba sai shi.....Ganin tana had'a zufa a gurin rana na dukanta yasa ya sunkuya ba tare da yayi shawara da ita ba ya dauketa cak daukar jira jirai yayi mata ya nufi cikin gidan da ita......Duk da halin da take ciki sai da taji wani iri kunyar ma'aikatan gidan duk ta rufe ta tasan dai dole idan wasu ba sugani ba wasu zasu gani Uwa uba ga 'Kanwarta Rashida, rufe idanunta kawai tayi ta 'boye fuskarta cikin 'kirjinshi.....Rashida tabi bayansu tana sinne kai fuskarta dauke da murmushi sosai mutumin yake burgeta saboda irin kulawar da yake bawa 'yar uwarta.
Hajja tace"Subahanallahi! me ya faru haka."? Yace"Zaman mota ya sanya kafafunta tsami ta kasa tafiya dasu." Hajja tace"Aifa dama zaman mota ma ga mai lafiya babu dadi ballanta ga mai ciki sannu Wasila ka shiga da ita ciki tayi wanka sai suci abinci su huta.'' Baice komai ba ya shige da ita bedroom dinshi, kai tsaye bad ya kwantar da ita ya nufi toliet.
Mikewa zaune tayi a hankali tana d'an mikar da kafafunta wacce tafi takura mata da ciwo ta dan tasa kad'an! ta rintse idonta tana kiran sunan Allah can taji zillo a cikinta ta bude idanunta da sauri tana sauke ajiyar zuciya, yanzu zai isheta da kusurkusur a ciki idan ba abinci taci ba babu zaman lafiya.....Fitowa yay daga toilet din yana tattare hannun rigar dake cikin shi tayi saurin dauke kanta ya 'karaso inda take ba tayi aune ba taji ya dauketa, da sauri ta kalleshi ya d'aga mata girarshi guda, dauke kanta tayi tana zumbura baki kamar zatayi kuka itafa wannan za'kewar da yake a kanta sam baya burgeta taga sai wani rawar jiki yake mata tasan dai ba komai ya sanya shi yake mata hakan ba sai dan tana dauke da cikinshi.....A hankali ya dure ta tsakiyar bandakin yana mata wani munafikin kallo ya dora hannunshi a wuyanta, tureshi tayi ta jingina da bango (garu) gabanta ne ya soma faduwa, Ya sake matsowa kusa da ita, sai kawai ta saka kuka tana ture kirjinshi, cikin taushin murya yace"Wanka zanyi miki ba wani abu ba, ke kuka baya miki wuya ko."? Cikin nauyin baki da yanayi na gajiya tace"To ka barni mana nayi da kaina da can kaine kake min?" Ya shiga kallonta yana girgiza kanshi, yace." Daga yau nake so duk wata d'awainiya taki ta dawo hannuna ni mutum ne mai tausayin masu lalura irin taki, insha Allah mutukar ina gida zan dinga dauke miki dukanin laluranki har Allah ya saukeki lafiya."
Shiru tayi tana kallonshi anya kuwa zata amince da wannan dad'in bakin nashi? itafa tafi tunanin saboda cikin sa da take dauke dashi ne yasa yake rawar jiki a kanta.......Saukar hannunsa taji a bayanta yana kokarin zuge zuf din rigarta, ta dinga tureshi tana hawaye hakan be dameshi ba sai da ya cire mata kayan jikinta tas, ya kurawa cikinta ido da yayi kurcici a mararta, wata kwallah ce ta ciko a idanunsa, ya tsuguna gwiwa bibbiyu 'kasan toilet din ya dinga sumbatar cikin yana shafashi da hannunshi, Wann
an k'wallar dai da yake ta 'boyewa sai da ta sauka, yay gaggawar gogewa, tana kallonshi taji ya dan bata tausayi, dan janye jikinta tayi ta matsa gefe tana zum'bura baki.....Ya sake binta yana rike hannunta duk jikinsa yayi sanyi wani irin masifaffan son yarinyar yaji yana bin dukanin ilahirin jikinsa......A hankali yaja hannunta suka isa inda kwamin wanka yake ya dauketa ya shiga da ita cikin ruwan da ya had'a, ido jawur yake kallonta yana jin wani masifaffan fleening na taso mishi, soso da sabulu ya dauka ya shiga cud'a mata jikinta yana sakin ajiyar zuciya, kamar kwai yake ta'bawa haka yake cud'ata sai da ya tabbatar ya wanke ta tas kana ya dauki towel mai kauri ya nad'eta a ciki......Daukar ta yayi ya fito da ita ya zaunar gefan gado.....Vasilin ya dauko ya nufi inda take zaune, warware towel din ya shiga yi ta rike towel din mirya na rawa tace"Ni ka bari shafa mai ai bai da wuya zan shafa da kaina." Girgiza kansa yay saboda idan yace zaiyi magana cikin halin da yake ciki zai iya tona asirin kanshi, ya kar'be towel din daga hannunta ya aje gefe guda, a hankali ya haye bed din ya raba 'kafafunshi ya sanyata a tsakiya ya shiga shafe mata jikinta da vasilin din, girman nonowanta da yanda suka sake kumburi da bun'kasa shine yake gigitashi yake d'imauta shi ya dinga kokarin daurewa duk dan kar ya nuna zulamarsa a fili al'amarin ya gagara bai san sanda ya jefar da vasilin din ba ya sanya hannuwanshi duka biyun kan nonowan ya shiga lailayasu yana jan nipples din tare da sauke masifaffiyar ajiyar zuciya...... Da sauri ta mi'ke zaune tana kuka tana kare jikinta da blanket ta dinga watsa masa harara tana share hawaye......Hannu ya d'aga mata yana so yayi magana sai kuma ya fasa, jiki a sanyaye ya sauka daga bed din ya bude wardorve ya dauko mata riga da zani na atamfa (vilsco) ya mika mata muryarshi a 'kasa yace."Kar'bi ki sanya." Hannunta na rawa ta kar'ba saboda bata so tayi musu yace zai 'kara kusantarta, yana mi'ka mata kayan ya kama hanya ya fice daga d'akin hankalinshi a masifar tashe.
Da 'kyar tasa kayan tayi kwance a bed tana siyayyar da hawaye sam bata jin zata iya sakewa dashi kamar da a yanzu babban burinta bai wuce ta rabu da cikin dake jikinta lafiya ba............Bacci ne ya fara fizgarta sam yanzu bacci bayayi mata wahala, mussaman yanzu da ta samu daki mai cike da 'kamshi da sanyin na'urar sanyaya guri, bacci mai nauyi ya dauketa.
Jin shuru bata fito ba ya sanya Hajja tace Rashida ta shiga dakin ta gani ko lafiya? Rashida na shiga ta tadda ta kwance a bed tana bacci, murmushi kawai tayi ta fito tace "Hajja bacci takeyi." Hajja tace tace"Koda naji ai shuru din tayi yawa, to ga abinci can ke sai ki zuba wanda zai miki kici idan ta tashi sai taci nata." Rashida tace"Nagode hajja." Daining din ta nufa domin cin abincin.
Ahmadu kuwa kai tsaye ke'bantaccan gurin hutawarshi ya nufa dake bayan gidanshi, yayi kwance kan wani irin gado mai kamar lilo yana lilashi idanunshi a rufe abin duniya yayi mishi yawa, ada da bata kusa dashi yana daurewa amma kuma yau din nan da ya kusance ta yaji hankalinshi ya tashi sosai wanda har baya so ya sake shiga gidan ya ganta gudun aikata abinda baiyi niyya ba, ya kuma lura da yarinyar kamar tana tsoranshi yanda take zabura idan ya kusanci jikinta tilas dama hakan ta faru a tsakaninsu tunda rabuwa ce sukayi ita dashi mara dad'i! amma dai shi yanzu babu sauran wani 'kulli a cikin ranshi ya amince da tubanta kuma yana so suyi zama na kwarai zaman da kowane ma'aurata keyi, ammafa ya zauna yayi tunani da nazari hakan ba zata kasance ba har sai yayi kokarin dauke idonshi daga kanta, ba zai yuwu ba ace daga dawowarta ya fito da zulamarshi a fili dole ya dinga dauke kansa yana kuma nuna mata ba wannan ne ma'kusudin abinda ya sanya ya dawo da ita gidanshi ba, da wannan shawarar ya mike ya nufi cikin gidan dai-dai lokacin da ake kiran sallah la'asar.....Hajja da Rashida ne zaune a palon suna kallo suna hira ya shigo sannu yay musu ya nufi bedroom dinshi hajja tace"Yana da kyau idan ka shiga ka tasheta tayi sallah barcin yamma bashi da dadi ko kad'an Mafi akasarin masu ciki kuma sunfi s
on irinshi." Yace."Kwarai kuwa Hajja annabi ma ya hanemu da yin bacci tsakanin azuhur da la'asar bari na tasheta yanzu."
Yana shiga dakin ya tarar da ita ta tashi idanunta na kallon rufin dakin....Ya karaso kusa da ita cike da kulawa yace."Ki tashi kiyi sallah ina fatan 'kafar naki ya daina ciwo."? Daga masa kanta tayi yace."To alhmdullhi." Toilet ya nufa ta bishi da kallo tana ayyana abubuwa da yawa a kanshi ya fito daure da alwala ya fice daga dakin, a hankali ta sauko daga bed din ta nufi toliet din bakinta ta wanke sannan ta d'aura alwala ta fito, sallahr ma da kyar tayi saboda yana take jin wata shegiyar yunwa idanunta har rufewa sukeyi saboda rawar jiki wuyanta da hijab din da tayi sallah ta fito tana rarraba ido a palon......Hajja da Rashida na daki suna sallah sai shi kad'ai ne kan kujerar daining yana had'a abinci ya hangi fitowarta, had'a ido sukayi ta dauke kanta jikinta babu kwari ta nemi kujera ta zauna, ya gama had'a abincin cikin plate ya dauko a nutse ya kawo mata inda take, ba tayi musu ba ta 'karba ta dora saman cinyarta ta fara ci da bisimillah a bakinta ya kawo mata ruwa da lemo ya aje gabanta ya juya domin komawa daining din ta bishi da kallo tana mamakin yanda ya zama wani silent babban mutum mai kudi da shekaru gami da tarin ilimi na boka dana isilma shine ya mayar da kanshi bawa a gurinta, mamaki take sosai sai kuma wani sashen zuciyarta ke fad'a mata cewar "Duk wani abu da zai miki shi a yanzu yanayi miki shine saboda d'anshi ko 'yarshi da kike dauke dashi amma da babu cikinsa a tare dake kallo baki isheshi ba sai dai idan jarabarshi ce ta kawo shi. Girgixa kanta tayi kawai tana adduar Allah yasa ta sauka lafiya tagani zai cigaba da hidima da ita ko kuwa.
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book na barki da Allah! Kema kika karanta baki biya ba na barki da Allah! Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*65*
Koda ya kammala cin abincinshi sai ya mike a nutse ya nufi bedroom dinshi yana tafiya tamkar wanda 'kwai ya fashewa a ciki, shi kad'ai yasan abinda ke damunshi, hakika dawowarta gidan nashi na barazana da lafiyarshi dan tun suna cikin mota yake ta fama da joystick dinshi yana hanata aikata abinda takeso dan duk abinda yake daurewa yake yi a yanzu dai idan ba samu yayi ya rage damuwa ba to tabbas dai ya san yau da 'kyar idan zai iya rintsawa........Wanka yayi ya shirya cikin yadin kashmir d'an gasken milk colour mafi akasari kayanshi farare ne bai fiye sanya abu mai duhu ba duk da ya kasance farin mutum, ya tsaya gaban mudubi yana gyara wuyan rigarshi kana kuma ya dan gyara saisayayyar sumarshi ya daura agogo a hannunshi, turaranshi mai dadin kamshi ya fesa ya fito palo hannunshi rike da hularshi yana gyarawa, Tunda ta daga kanta sau daya suka hada ido dashi ta mai da kanta 'kasa gabanta na fad'uwa, ganinshi tayi tamkar sabuwar hallita kamar wanda aka 'bareshi a akwali (sabo) yayi wani fresh dashi fatarshi tayi luwai luwai annuri sai sauka yake kan kyakykyawar fuskarshi.....Hajjah tace"Au na d'auka yau d'aya zaka zauna a gida tunda matar gidan ta dawo sai ku tattauna a tsakaninku amma naga ka shirya zaka fita." Ya danyi gyaran murya yana d'ora hular a kanshi yace."Ba zan jima ba zan dawo insha Allah akwai ba'kin da zanyi zamu had'u dasu can gest house d'ina dan already ma yanzu suna can suna zaman jirana." Hajja tace"To Allah ya kiyaye a dawo lafiya." Rashida tace"Yayana Allah ya tsare." Ya amsa cike da kulawa. Ya d'an saci kallonta dai-dai lokacin data d'ago kanta suka had'a ido dashi, murmushin sa mai tsada ya sakar mata yana d'an d'aga mata girarashi guda kamar dai yanda ya saba, tayi gaggawar mayar da kanta 'kasa kamar bata so tace"Adawo lafiya." Bai tsammanin hakan ba sai yaji dad'i sosai yace."Amin amin." Ya nufi kofar fita, tsintar kanta tayi da binshi da kallo har sai da ya fita sannan ta mai dauke kanta tafiyarshi ma abar kallo ce komai nashi a nutse yake ya cika namijin da ko wace mace zatayi sha'awar aure amma ita har yanzu tana shakku a kansa dan tana jin tsoron ta sake sakin jikinta dashi wani abun ya had'asu na kuskure yazo ya saketa ko yaci mata mutunci amma itama tana hango tsantsar son da yake mata a 'kwayar idonsa.
A can gest house din nashi Khalifa ne tare da Alhaji Muktari daura dan takarar governor jahar katsina ya kawo masa ziyara tare da dashi da mu'karrabansa, dake jam'iyarsu daya shiyasa suke zumunci kuma kusan halinsu yazo d'aya da juna, Alhaji Muktari ya ta'ba zama governor a jahar katsina yanzu yana so ya maimaitane yana kuma so ya karya al'kadarin governor dake ci a jahar tasu mai suna Engineer Haruna Haruni mutum ne mugu wanda yake mulki bisa zalinci halinsu d'aya da mai girma governor Lawan Rabo governor dake ci a jahar kano, duk wani 'kulla 'kulla gami da cuta da zalinci tare sukeyi dan duk abinda Lawan Rabo yayi a jahar sa to lashakka Haruna haruni shima sai yayi a tashi jahar, Wannan dalilin ne ya sanya Alhaji Muktari zuwa gurin abokin nashi domin su shawarta abubuwan da zai amfane su ya kuma amfanin al'ummar jahohinsu...............Tunda Governor Lawan Rabo ya samu labarin zuwan Alhaji Muktari garin sai ya dami kanshi, sosai ya kira Abokin nashi ya shaida mishi abinda ke faruwa, Haruna Haruni yace." Nasan ba zai bar garin ba tilas sai shigo ku gaisa kada ka nuna masa komai kamar yanda suke abunsu a lullube muma zamu bisu a haka, ai yanzu ya'ki d'an zamba ne muke kan kujearar mulki sai munso wani zai hau ka daina tayar da hankalinka kan komai kuma Amadu ya daina firgitaka, komai fa na hannuka a yanzu koda Amadu ne ya cika za'be sai munyi juyin mulki ballantana kuma muna da mai matacciya wannan maimai d'in ko sun so ko sun'ki sai munyi idan zaka shigo katsina ka shigo a shirye domin tilas ma a wannan karon mu kauce hanya mubi matasan yaran nan a sannu su samo mana 'kananun yaran da zamu bawa mai matacciya yayi mana aiki a kansu, tabbas dai nasan baka mance abinda ya faru ba a shekaru uku da suka gabata." Lawan Rabo ya sauke ajiyar zuciya yace."Tilas shawararka ita
ce abun dauka a gaskiya yanda naji dad'in wannan kujerar zai yi wuya na barta kai tsaye kai ni ko da d'an da na haifa za'a bu'kata zan iya badashi tunda dai nasan ai ba gama haihuwar nayi ba.'' Haruna haruni yace."Haka ake son cikkaken namiji jarumi me a'kida, kada ka damu idan Muktari ya shigo fadar gomnati ka kar'beshi hannu biyu zamu 'bullo musu ta bayan fage, mulki dai sai dai suga anayi insha Allah duk jama'ar da suke dashi sai ta dusheshe ranar za'be mune zamu lashe." To Wannan maganganun da sukayi ne ya sanya Governor Lawan Rabo kwantar da hankalinshi kamar tsumma a randa, ya tabbatar suna da ya'kinin akan cewar mutukar bokan da yayi musu aiki da 'kuk'onan kawunan yara yana nan a raye cikin duniyar to sun tabbata sai sun watsa shirin su Amadu da Muktari
Amadu na isa gest house din nashi Alhaji Muktari ya soma tsokanarshi da fad'in "Da har ina cewa bari mu tafi tunda dai mu gaisa da Khalifa ya isa kai sai ayi maka uziri tunda kana tare da Uwargida." Amadu ya zaune kan kujera yana murmshi hularshi ya cire yana kallon Khalifa yace."Nasan wanda ya fad'a maka cewar ina tare da Uwargida" Khalifa yace."Nine na fad'a mishi da kayi zamanka ma yayi maka uziri ko bakaji abinda yace bane." Murmushi yayi yana girgiza kanshi yace."Uwargida bata da 'koshin lafiya me kuke tunanin za'ayi."? Alhaji Muktari ya bashi hannu suka tafa suna dariya a tare Yace."Yana da kyau dai muje na dubata kafin na wuce, dan Khalifa yanzu yake shaida min an samu 'karuwa to Ubangiji Allah ya raba lafiya." Amadu yace."Ameeen ya rabbi, yace." Khalifa ya fad'a maka na samu 'karuwa shi bai fad'a maka tashi 'karuwar ba.''? Alhaji muktari ya kalli khalifa da son jin 'karin bayani." Khalifa yasa dariya yana kallonshi shima Amadu yace."Shima iyalinshi juna biyu gareta." Alhaji Muktari ya shiga girgiza kanshi yana kallonsu da fad'in "Gaskiya mutanan nan bakwa wasa." Khalifa na dariya yace."Bama wasa ko dai baka wasa Alaji matanka biyu 'yayanka shida ai kaine shugaba gwara mu da mace daya muke zaune." Alhaji muktari ya dan tura hularshi 'keya yana gyara zamanshi yace." Ai mata biyu shine jin dad'i Alaji sai ranar da kukayi zaku gane haka.'' Amadu dai murmushi yake yace."Duk mutumin dake da mace biyu bashi da kwanciyar hankali Alaji bana jin zan iya had'a mace biyu a gidana in dai ba Allah ne ya 'kaddara ba."
Khalifa na d'auke da murmushi a fuskarshi yace."Ni kam ina tsammanin had'a mata biyu anan gaba dan gaskiya ina da ra'ayin yin hakan." Alhaji Muktari ya bashi hannu suka tafa.....Amadu kuwa kallonshi yay da mamaki a fuskarshi yace."To tunda ka tona asirin ranka sai na fad'a mata kasan ni da Hafsa akwai amana ba zan yarda kaci amanarta ba."
Khalifa yasa dariya yana fad'in "Kafi tsuntsu gudu dan Allah! haka kawai Allah da annabi sun halasta min ace kada nayi, Kasan Allah idan lokacin aurena yazo dole ne Hafsa tayi hakuri dan ina da wannan niyyar." Amadu ya dinga girgiza kai yana kallonshi, shi kam a nashi ra'ayin bai son had'a mata biyu ko sama da hakan a ganinshi duk damuwa ce mutukar matarshi zata dinga dauke mishi dukanin laluranshi bai damu da lallai sai yayi wani auran ba koda kuwa ya samu mulki a nan gaba.
Tattaunawa suka shigayi da sabbin tsare tsaren da zasuyi mutukar Allah ya cika musu burinsu akan abinda suke nema mutukar sun samu nasarar d'arewa kujerar mulki to babu shakka Al'ummar jahar kano da katsina zasuyi farin ciki zasu ga sauyi ta ko wanne 'bangare
Misalin 'karfe tara da rabi na dare suka fito daga gest house d'in Alhaji Muktar yace yana so ya duba Wasila kafin ya koma dan gobe da asubah yake so su wuce, To dan kar ya watsa masa 'kasa a ido ne ya sanya ya amince da bukatarsa, saboda baya son abinda zai sanya girma da mutuncinsa ya zube a idonshi, baya so suje gidan Yarinyar tayi wani abun wanda zai nuna babu jituwa a tsakaninsu domin har yanzu ya lura da ita bata wani saki jikinta ba sosai.
Goma shaura motarsu ta shiga cikin gidan garba nayi parking ya fito cikin sauri ya bude musu kofa suka fito, tare suka nufi cikin gidan dukaninsu harda khalifa.
Rashida ce ita kad'ai a palon tana kallo Hajjah tuni ta shige daki ta
kwanta dan tanayin sallah isha'i take kwanciya, Wasila kam bata jima da barin palon ba itama wanka ta shiga tayi ta kwanta dan har yanzu jikinta bai dawo dai-dai ba akwai sauran gajiyar hanya
Rashida ta mi'ke tsaye tana musu barka da zuwa, ta gaishe su a nutse tana kokarin shigewa Har zai yi mata magana sai kuma yaja bakinshi yayi shuru ya kalli Abokan nashi a nutse yace."Bari na fito da ita." Khalifa yace"Kada kayi wannan dad'ewar da ka saba." 'Karamin tsaki yaja ya yana girgiza kanshi ya tura kofar dakin ya shiga wanda yayi dai-dai da lokacin da ta fito daga toilet jikinta daure da towel iya cinyarta.....Sallamar dake dauke a bakinsa ce ta gagara fitowa, da kyar ya janyo dauriyarshi da jarumtarshi ya shiga dakin, 'Dan tsayawa tayi tana kallonshi tana turo bakinta gaba, shiyasa ta'ki shiga dakinsa ta gudo nata ashe bata tsira ba yazo zai takura mata, 'Bata fuskarta tayi ta wuce a hankali taje ta zauna gaban mirror tana bud'e man shafawa
Bayanta ya tsaya yana kallonta ta cikin mudubin tana shafa mai a hankali tana shafawa a hannunta, ba tare da yace komai ba ya sanya hannunshi cikin vasilin din ya soma shafa mata sassan jikinta, jin saukar hannunsa a jikinta ya sanya ta sauke ajiyar zuciya me tafe da tashin tsigar jiki, hannunsa ta cire wanda yake kokarin cusawa cikin towel din ta sake daure kirjinta dashi, bai ce mata komai ba, ya dan rankwafa a hankali ya d'an ja 'kafafunta ya soma shafa mata vasilin din a cinyoyinta da kafafunta.......Ido ta tsira mishi yayin da kanshi ke 'kasa, taji wata 'kwallah na kokarin zubo mata daurewa tayi ta dauke kanta da sauri lokacin da ya dago ganshi, bayan ya gama shafa mata vasilin din, Ta mike tana sake rike daurin towel din a kirjinta wardrobe ta nufa ya bi bayanta, kayan bacci masu taushi ya dauko ya rike hannunta a hankali yake kokarin kwance towel din, tasa kuka tana tureshi, ya mi'ka mata kayan da fad'in "Kiyi gaggawar sanyawa tunda baki so nasa miki akwai 'baki na jiranki a palo abokina ne yazo duba jikinki.'' Cikin rawar murya tace" Ni ka fita to nasa kayan zan fito yanzu." Harararta yayi yace."Meye abinda zaki 'boye min a jikinki ? wai ke dan Allah yaushe zaki daina wannan 'kauyancin ne? Shiru tayi mishi ta nufi bed da kayan a hannunta, zama tayi gefan gado ta soma zura dogon wandon tana kare cinyoyinta da towel, shi dariya ma take bashi wallahi, yay tsaye a kanta har ta gama sanya kayan ya mi'ka mata 'katon hijab d'inta na sallah tasa kana ya nuna mata hanya da hannunsa......Gaba tayi yabi bayanta haka suka fita palon.
Alhaji Muktari ya kalleshi a lokacin da suke karasowa inda suke yace."Ashe dai da gaskiyar khalifa shiyasa kafin ka shiga ya tuna maka.'' Amadu yayi sauri bagarar da zancen dan baya so ta fahimci inda zancen nasu ya dosa, shi baiga wani dad'ewar sa a ciki ba sa'ido ne kawai irin na khalifa.
Ta gane khalifa, d'ayan ne bata gane ko waye ba, a nutse ta zauna kusa da mijin nata ta shiga gaishesu, Alhaji Muktari ya shiga mamakin 'kan'kanuwar yarinyar wai itace matar abokinshi Yo ai wannan za tayi sa'ar babbar 'yarshi Sa'adatu, babi shakka dole abokin nashi yace bashi da sha'awar 'kara wani auran saboda yasan yana da wacce zai mori 'kuruciyarshi da tsufanshi.
Cikin kulawa yake amsawa ya dan tsokanta ita kuma sai sunkuyar da kanta take kunyar mutumin takeji sosai ganin kamar ma ya girmi mijin nata, Wanda sam ba haka bane Alhaji Muktari sa'an Amadu ne dan shima baifi shekaru arba'in da biyar ba , kawai dai dan yayi aure da wuri ne kuma yana da jikin girma ba kamar Amadu da bai da 'kiba ba, Tana zaune tana sauraransu suna hira duk ta 'kosa ta bar gurin ta d'an muskuta a hankali zata tashi, Ya ri'ke mata hannunta ba tare da ya kalleta ba ya juya suka cigaba da magana da Khalifa, tamkar zata fashe da kuka haka ta kalleshi to meye amfanin zamanta a gurin bayan sun gaisa ba sai ya kyaleta taje ta kwanta ba......Kirane ya shigo wayar Khalifa sai lokacin suka san dare yayi sosai sha d'aya da rabi Hafsa taji shuru bai dawo ba ta kira wayarshi, Ya mike da sauri yana kallon agogonshi, yace"Ashe dare yayi sosai sha d'aya da rabi yanzu." Duk sai suka mi'ke tare Alhaj
i Muktari yace."To Uwargida kuma amarya xamu tafi Allah ya 'kara sauki ya kuma saukeki lafiya insha Allahu muna nan zuwa ni da iyalina duk ranar da kika haihu." Tace"To Allah ya kawo ku lafiya mungode." Ta kalli khalida da yayi gaba hankalinshi duk yayi gida tace"A gaishe min da Afnan da momynta." Yace."Zasuji insha Allahu.......Ta dauka zai musu rakiya sai taga ya tsaya bakin kofa yana fad'in To Alh sai munyi kenan a sauka gida lafiya nagode da ziyara insha Allah nima ina nan tafe." Khalifa yace."Wai kana nufin daga nan zaka tsaya."? Yace."Meye a ciki to akwai gajiya a tare dani ina so huta ne." Khalifa yasha jinin jikinsa, ya kalli Wasila dake tsaye a kusa dashi yabi ya rike mata hannu gam kamar wacce zata gudu.....Yace." 'Kanwata ina fata baki mance abinda Dr Aliya ta fad'a miki ba ko." Wasila tayi jim!! Tana nazari sai kuma ta kalli Khalifan jikinta a sanyaye ta daga kanta.' alamun bata mance ba........A ranar da akayi mata d'aurin mahaifa Dr Aliya ke shaida mata cewar dole ne ta nemi wata hanyar domin biyawa mijinta bukata mutukar ana so cikin jikinta ya zauna lafiya to banda yawan sex da ayyuka masu tsauri, a lokacin da Aliya ke yi mata wannan jawabin sam bata d'aukeshi da mahimanci ba saboda tasan bata da aure lokacin, To da yake duk a gaban khalifa tayi jawabin yasa yanzu ya sake tuna mata kuma ta gane inda ya dosa, tabbas kuwa dole ne tayi taka tsantsar dan tayi bala'in sanin waye Amadu idan ya hauta ya dunga suburbud'arta mancewa yake da kowa da komai a lokacin shi dai burinshi kawai bukatarsa ta biya........Hannunta ya rike zugwi zugwi! ya nufi bedroom dinshi da ita, ya mai da 'kofar d'akin ya rufe da key, sai sannan ya sakar mata hannu, jikinta babu kwari ta nemi gefan gado ta zauna, shi kuma ya nufi toilet domin watsa ruwa.
Ya fito daure da towel ya ganta zaune tana gyangyad'i Gyaran murya yay ta zabura da sauri ta bud'e idonta tana kallonsa, gabanta ya fad'i ras! ganinsa daure da guntun towel! da sauri ta haye bed din ta ja blanket ta rufe jikinta har fuskarta, ita kam ko me zaiyi ba zata bari ya hau kanta ba gani take idan ya sa mata wannan 'katuwar abar tashi zata iya haihuwar dole....Ganin razanar da tayi ya bashi mamaki sai kawai ya girgiza kanshi ya bude sif ya dauko jallabiya da gajeran wando yasa a jikinshi, kana ya nufi ke'bantaccen gurin da yake ibadarshi, kafin ya isa kira ya shigo wayarshi ya dauka yana dubawa Khalifa ne, Yace."Dama dazu ina so nayi maka bayani to babu dama gaban Mutane.....Khalifa ya fad'a mishi sharud'an da Likita ta fad'a kan Wasilan ya cigaba da cewa ko za kayi kar ya wuce sau d'aya dan kar ka wahalar da yarinyar mutane kuma ka wahalar da d'an dake cikinta......Yace."Okey shine naji kuna magana da ita d'azu kuna wani 'boyewa."? Khalifa yace."Meye abin 'boyewa nifa zumud'in da naga kana yi ne yasa na tuna da maganar kai ma kanka ko ba'a fad'a ba ai ka d'aga 'kafa! A hasale yace."Kai kaga ki likita tace ko bata ce dama ni banyi niyyar yin komai ba dan haka sai da safe." Kashe wayarsa yay ya ajeta yana jan tsaki ya nufi kan dadduma......Khalifa kam nashi 'bangaran dariya yasa dan ganin yanda lokaci 'kankani zuciyar abokin nashi ta hasala....Wasila kam tun tana rawar jikin ta daina dan bacci me dad'i ne ya dauketa cikin bargonshi mai cike da kamshin turarirrkanshi masu dad'in 'kamshi da kashe jiki.
Littafin na kudi ne!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys
*66*
Nafila yayi raka biyu bayan ya idar da sallahr sai ya bude al'kur'ani mai girma ya karanta iya yanda ya sawwa'ka ya jima hannunsa a sama yana addua sannan ya rufe da fatihatulkitabi ya shafa a fuskarshi, a nutse ya mike ya nufi bed din ya xauna yana kallonta bacci take sosai kuma daga ni tana jin dadin baccin a hankali yaja bargon ya shiga ya kwanta kusa da ita tare da d'an jawota jikinshi ya d'ora hannunshi 'kasan mararta yana shafawa a hankali a hankali bakinshi na motsawa da alama addua yake yi a nutse ya tofe musu jikinsu bakid'aya kana ya ja bargon sosai jikinsu ya rufe idanunsa yana adduar Allah ya taimakeshi bacci mai nauyi ya daukeshi, cikin ikon Allah kuwa baccin ya daukeshi, kuma baccin da ya jima baiyi Irinshi ba.
Wajejen karfe hud'u shaura na asubah ta farka da wata matsananciyar yunwa, jiki na kyarma tayi yunkurin mi'kewa, yay gaggawar rike ta idanunsa ya bude ke kyace dama ba bacci yake yi ba, Amadu bashi da nauyin bacci ko kad'an, a hankali yace."Menene."? Shiru tayi tana mutsika idanunta, sai ya mi'ke zaune yana me cire bargon dake jikinsu ya sanya hannunsa guda a jikinta ya shafa wuyanta, babu alamun zazzabi a jikinta, Yace."Menene? ko zakiyi wani uzirin ne? muryarta na rawa tace"Yunwa nakeji." Yace."Yunwa."? Daga kanta taji hawaye na kokarin zubo mata, Yace."Dama baki ci abinci ba kika kwanta."? "Naci dama duk dare ina tashi naci abinci." Ya shiga girgiza kanshi a hankali ya mike ya sauka daga bed din ya fita daga dakin
Kicin ya nufa yayi dube duben shi babu abinci sai kawai ya jona kettle ya dora ruwan tea yana tsaye yayi ya juye mata a cup ya nufi dakin dashi, lokacin ta fito daga toilet daure da alwala dan an soma kiran sallah." Ya aje tae din kam bedside yana fad'in "Ga tea nan babu abinci a kicin din wallahi." Zumbura bakinta tayi ita me zatayi da wani tea banda ya sata jin wata yunwar, Fita tayi daga dakin Yabi bayanta kicin ta nufa, ya tsaya bakin kofar kicin yana fad'in "Ki koma ki kwanta bari na tashi hajja sai ta sarrafa miki wani abun." Girgiza kanta tayi tace"Kawai tana baccinta sai a tasheta tayi girki nima zan iya." Shiru yay yana kallonta tana kunna gass cocar, Shi da kansa yayi alkawarin daukar dukanin laluranta baiyi tsammanin harda shiga kicin ba, a lokacin da suke tare a can baya bai santa da wannan cin abincin ba yanzu dai yafi tunanin cikin da take dauke dashi ne ya sanya ta, kicin din ya shiga ya kar'be tukunyar hannunta wai zai d'ora mata abincin......Tausayi ya bata ta kar'bi tukunyar taje ta zuba ruwa ta tazo ta dora tukunyar gefanta ta bude taga lafiyayyar miya wacce taji nama zu'ku zu'ku.....Sai kawai ta bud'e sto ta dauko supargetti guda d'aya, yay daurin kar'bar taliyar a hannunta, ta rike tana girgiza mishi kai tace"Ka barshi zan dafa babu wuya fa." Ya d'an tsira mata idanunsa itama shi take kallo tana sake jin wani irin yanayi a jikinta gaskiya ta lura ya mato akan sonta, da girmanshi da komai ya dinga biye mata da dukanin abinda take so.....Yace."Kin tabbata zaki iya." Daga kanta tayi yace."Okey bari nayi wanka da alwala na wuce masjid.'" ya wuce ta bishi da kallo tausayi tausayinsa take ji a cikin ranta.
Tana tsaye taliyar tayi ta tsaneta kana ta juye cikin fulas ta dauka ta nufi daki dashi, lokacin har yayi wanka ya sanja jallabiya hannunsa rike da cazbaha, sai kamshi yake ta matsa mishi hanya shi kuma ya fita ba tare da wani yace da dan uwanshi komai ba.
Kicin din ta koma ta dauko plate sannan ta samu wani abu ta zuba miyar a ciki ta dawo dakin ta zauna kasan kafet a nutse ta zuba abincin ta soma ci sai da taci ta koshi sannan tayi sallah ta koma ta kwanta, bacci na fizgarta taji shigowarshi.......Ta bud'e idonta a hankali tana kallonshi lokacin da yake kokarin karasowa kusa da ita......Zama yayi gefanta a nutse yace."Tashi zamuyi magana." Ganin babu wasa a tare dashi yasa ta mike xaune tana wasa da hannunta.....Cikin kulawa ya kalleta yace"babu gaisuwa ko."? Ta dan kalleshi da gefan ido sai taga ya tsirawa jikinta ido, kanta ta sunkuyar a hankali tace "Ina kwana." Ya amsa da sakakkiyar fuska kana yace."Ya kwanan boy." Shiru tayi yace."Kamata yayi ma kafin mu fara magana na fara gaisawa dashi." ba tace masa komai ba, dan janyota jikinsa yana laluben jikinta, hannunsa ya d'ora saman mararta yana shafawa, ta dinga jin hucin numfashinsa a fuskarta, rintse ido tayi gabanta na faduwa tsigar jikinta na tashi, ya d'ora bakinshi saman goshinta tare da fad'in "Allah yayi miki albarka." Ta bude idanunta dake rufe tana kallonshi, mikar da ita yayi zaune yace"Yanzu hankalina ya kwanta na duba yarona yana da kyau ma muje kuga Dr insha Allah." Ba tace komai ba tana dai kokarin gyara rigarta, sai da ya tabbatar ta samu nutsuwa kana ya kalleta a nitse yace."Wane guri kika tsaya a karatun ki na al'kur'ani da hadisai nasan dai kinje isilamiyya ko.'? Taji gabanta ya fad'i! ta kalleshi idanunta na kokarin kawo ruwa, ina suka ga gatan da zasuyi karatu....Shiru tayi masa tana wasa da yatsun hannunta, Yace."Koda yake dai yanzu ku kin fad'a min ga inda kika tsaya bai da amfani tunda dai ba tilawa kikeyi ba, yanzu ki shirya ko ince ku shirya keda kanwarki insha Allahu kullum da asubah zamu dinga zaman karatu dani daku zamu fara tun daga fatiha da izinin Allah zamu sauke al'kur'ani mai girma mutukar kun bani had'in kai! Idan kin san ba'ki kin iya karatun al'kurani da sauran litattafan addini insha Allahu karatun nasara (boko) ba zai miki wuya ba zan d'anko muku mai muku lesson kafin ki haihu sai ku koma makaranta ko bakya so."? Yafada yana kallonta cike da kulawa......Hawaye ta share murya na rawa tace"Ina so mungode." Yace." Kin kammala secondary skul ko." ? Shiru tayi kunya duk ta isheta, ya sake maimaita tambayarshi, da kyar tace "Tunda muka fad'i jarrabawa muka daina zuwa." Yace."Okey duk ba wani abun bane insha Allah zakiyi karatu mutukar kin mai da hankalin ki ni kuma zan tsaya miki da yardar Allah." Hawaye taji sun zubo mata a fuskarta, tace"Mungode Allah ya saka da alkairi." Sai ta fashe da kuka harda shashsheka, rungumeta yayi sosai yana rarrashinta tare da shafa kanta, tayi luf a jikinshi tana sauke ajiyar zuciya.....Ya dago ta daga jikinshi yana goge hawayen fuskarata yace."Ki rabu da wannan 'kawar taki wacece sunana? bata da kirki duk wani lalacewa da rayuwarku tayi da ita da kuma rashin gata wanda baku dashi amma insha Allahu nine zan zama gatan ku in dai zaki zauna dani da tsarkakkiyar zuciya abinda ya faru a baya ya wuce a gurina na yafe miki insha Allah Allah ya yafe mana gabad'aya." Hannunsa cikin nata tace"Dama tuntuni mun rabu da Camas! nagane ita ke zugani ina yin wasu abubuwan marasa kyau tunda abun nan ya sameni ta gujeni ta gudu da kudina kusan miliyan biyar har yanzu ban san ina take ba."
Yace."Duk abinda kikace ta aikata miki zata iya domin nima na nemi taimako a gurinta lokacin da muke neman ku kafin kuje gurin mai allo, yarinyar ta'ki ta bani cikakken bayani 'karshe ma sai ta daina d'aga waya ta idan na kira." Girgiza kanta ta shigayi tana mamakin halin dan adam ko a mafarki idan ance mata Camas za tayi mata haka ba zata yarda ba sai gashi babu shakka mutum abin tsoro ne.
Yace."Je ki kira Rashidan mu fara zaman karatun yanzu." A hankali ta sauka daga bed din ta fita daga dakin, Ya dauke idonsa bayan fitar ta yana girgiza kanshi, yana jin zai iya sadaukar da farin cikinsa da duk wani jin dadinsa mutukar yarinyar zata samu walwala da farin ciki.
Lokacin da ta shiga
dakin, Hajja na zaune kan dadduma da carbi a hannunta ita kuma rashida ta idar da sallah tana kwance kan daddumar bacci na kokarin dauketa.......Ta samu guri ta zauna a nutse suka gaisa da Hajja tana tambayarta jikinta, Tace jiki da sauki alhamdullihi." Rashida ta mike tana mutsika idanunta suka gaisa tace"Kizo zamuyi karatu." rashida ta mike tare da zura hijab dinta suka fita daga dakin, hajja kuwa ido tabisu dashi haka kawai take tausayawa yaran.
Palo suka taddashi zaune kan katuwar dadduma gabanshi da al'kur'anai da kuma sauran litattafan addini........Ya bawa ko wacce al'kur'ani guda d'aya ya umarce su bude 'kasa, zasu fara daga fatiha ne.
Ko wacce ta bude nata a nutse yayi bisimillah ya soma karatu cikin nutsuwa da 'kira'arshi mai kyau da dad'in saurare, nutsuwa sukayi sosai suna saurarashi, sai da ya maimaita musu fatiha da fala'ki da nasi sau uku sannan yace su karanta masa yaji." A tare sukayi bisimillah suka soma karatun cikin nutsuwa, ya dinga sauraransu har suka kammala, yaji dadi sosai yanda ya biya musu haka sukayi, yace su rufe alkur'ani suka, Ya dauki littafin ahlari yana dubawa, a nutse ya soma karanto musu yana musu bayani dalla dalla bayanin jinin haila da hukunce hukuncensa bayanin janaba itama da hukuncinta shuru sukayi suna sauraranshi, dan wani gurin idan ya fada kunya ce take rufesu sai suka lura shi bai damu ba karatunsa yake yana so su fahimci abunda yake so su fahinta, bayan sun kammala karatun sai ya sallami Rashida ya mai da hankalinshi kan Wasila tana zaune jikinta duk yayi sanyi bata ta'ba tsammanin yana da ilimi irin hakaba sai taji ya sake yi mata wani kwarjini a idonta, A nutse yace" Wasila meye banbanci a cikin wankan haila da janaba niyya iri d'aya ake ko kuma ta bambamta."?
Ta dan kalleshi a nutse tace"Akwai bambamci mana." Yace."Kiyi min bayani sosai." Tace"Niyyar wankan haila daban niyyar wankan janaba daban amma duk wankan iri d'aya ne." Yace."Meye janabar meye kuma haila."? d'an tura baki tayi tana mi'ke kafafunta ita tagaji da wannan tambayoyin yace."Idan baki min bayani ba zan dauka baki da ganewa da saurin fahimta."
Tace"Janaba itace "Kamar mutum yayi rayuwar aure da mijinshi to janaba ta hau kanshi sai yayi wanka wanda ya zama farillah kamar yanda annabi ya koya mana."
Yace."Na gamsu da wasu bayanan naki sai dai kuma har yanzu baki fayyace min meye janaba ba da yanda zan fahimta kince rayuwar aure ni dake yanzu haka rayuwar aure mukeyi ina so ki fahintar dani shin rayuwar aure wace iri? Kamar zata fashe da kuka tace"Kamar yaya."? Yayi murmushi yana kallonta a nutse yace."Kamar yanda nayi miki bayani." shuru tayi mishi yace."Nasan rashida ta fiki gane karatu bari na kirata tayi miki bayani kuma mutukar tayi miki bayani abinda nake so ku fahimta sai nayi miki bulala! ita kuma nayi mata kyauta.'' mi'kewa yake kokarin yi ta rikeshi tana kuka "Ni wane bayani zanyi to bayan nayi maka bayanin abinda na fahinta! Ni kar ka kira rashida me ta sani a cikin abinda kake fad'a ai har gwara ni nafi ta fahinta." Ya koma ya zauna yana dariya, yace."Ai saboda nasan kin fita fahintar ne yasa na sallameta ke nace ki zauna kiyi min bayani, to gashi kin kasa min bayani gamshashshe wanda zai sa na gamsu."
Hawaye ta share tana zumbura baki, gashi ta rirrike masa riga kusan ma rabin jikinta duk yana jikinsa, Cikin kasalalliyar murya yace."Tashi muje ciki ni nayi miki bayanin yanda abin yake, in yaso bayan na gama sai ki fahimci yanda janaba take a kan mutum." Shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya, ya dan janyeta daga jikinsa yana kokarin mikewa ta rikeshi! ita bata so ya kira Rashida ai abin kunya ne ma ya tambayi rashida yanda janaba take! Shima dama wasa yake yi......Yace." bakya jin kunyar wani ya fito ya ganki haka kina kuka kamar kankanuwar yarinya."? Tace"Dan Allah kada ka kira Rashida wallahi na fahimta." Yace."Nima da wasa nakeyi ai, ai nace muje d'aki na nuna miki ko." Sauka tayi daga jikinsa ta koma gefe guda tana ya mutsa fuska......Girgiza kanshi yay ya mi'ke a nutse yana fad'in "Kinbi kin nukurkusa min jikina yana tsami! kizo kiyi min tausa." Kallonshi tayi kawai ya wuce bedroom dinshi Yana shiga ya cire jallabiyar jikinshi ya kwanta bed yana rintse idanunshi, da so samu ne ya samu ko dan romantic ne ya samu yayi to amma sam baya son takurawa yarinyar zai dai cigaba da daurewa Allah yasa zai iya............Bacci me nauyi ya daukeshi ita kuma ta zauna a palon saboda tana jin tsoro ta shiga dakin yayi mata wani abun, Hajja da rashida suka fito daga dakin.........Dai-dai da lokacin da Rabe ke shirya musu daninng, Wasila na kallonsu suka nufi daninng din tayi zamanta a inda take har suka kammala suka isketa Hajja tace"Lafiya baki karya ba ko bakijin dadi ne."? Tace"Hajja kafin asubah naci abinci bana jin yunwa yanzu sai zuwa anjima nasan zan nemi abinci." Hajja tace" To shikkenan ki dai dunga ci kina koshi domin ki samu kuzari da kwarin jiki duk da nagani baki wasa da cin abinci." Rashida tace"Ai hajja wannan baby nasan kato ne anti wasila fa kullum cikin cin abinci take babu dare babu rana." Hajja tasa dariya tana fad'in "Ai lafiyace ta jawo haka ana so mai ciki ta dinga cin abinci sai kiga ta haifi yaro lafiyayye mai ban sha'awa." Wasila dai murmushi tayi kunyar hajja take, sai ma ta mike ta nufi daki tana murmushi ita kanta tasan dolene ta haifi katon d'a dan ganin irin abincin da take narka sai kace jaka.......Kusa dashi taje ta kwanta a hankali ta d'ora kanta kan kirjinsa tana lumshe idanunta, sai taji saukar hannunsa a bayanta, tayi yunkurin mikewa ya riketa sosai! idanunsa a rufe! sai tayi luf a jikinsa tana sauke numfashi, jin baiyi mata komai ba yasa ta saki jikinta sosai bacci ya dauketa a jikinshi.
Littafin na kudi ne!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*67*
To haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya cikin kwanciyar hankali gami da samun nutsuwa, sosai Amadu ke kula da Wasila ita da abinda ke cikinta, sunje asibiti likita ya tabbatar mishi da lafiyarta data yaronshi, yanzu itama ta saki jikinta sosai dashi tana zama suyi hira sosai in yana gida kuwa ta dinga kwanciya kenan a jikinshi daga tace wannan sai tace wancan Hajja da Rashida suyi ta kallon drama dan wataran ma idan sukayi wani abun hajja barin gurin takeyi, Rashida ma tayi ta jin kunyarshi tana mamakin yanda yayarta ta samu sake a gurinshi take zuba sangarta gami da shagwaba iya yanda take so shi kuma yana biye mata.......Idan suka zo zaman karatu da asuba ma sai sun gama rungume rungumensu kafin Rashida ta fito, dan wani sa'in idan wasilan ta rikitashi baya iya yi musu karatu me tsayi zaije ya kwanta yace sa had'u da daddare, to ka yaje ya kwanta haka zata bishi ta nan'ika da jikinshi, dole sai ya marmatsata sannan hankalinsu ke kwanciya ita dashi, akwai ranar da yaso ya sadu da ita ta hanashi, gashi ya kai 'kolulowa gurin bukata idonsa jawur ya fita daga d'akin, tayi kwance a bed tana hawaye, ita tsoronta Allah tsoranta annabi kar garin jin dad'insu yaronsu ya samu matsala, shiyasa bata so yace dole sai yayi sex kawai dai su tsaya iya romantic din har Allah yasa ta haihu........Ranar fushi yayi da ita ya shirya yayi ficewarsa harkokinshi, sai bayan tara da rabi na dare ya shigo gidan lokacin ita da Rashida ne a palon zaune suna kallon wani india film Rashida tayi mishi barka da zuwa ya amsa cike da kulawa yana tambayarta hajja tace"Taje ta kwanta.....bedroom dinshi ya nufa, yana jiyo muryarta nayi mishi sannu da zuwa, ya'ki amsawa, ta mike a hankali dan cikin nata ya fito sosai yanzu zama take da 'kyar ta mike da kyar tunda yanzu cikin ya kai watanni bakwai, bayanshi tabi wanda tana murd'a kofar dakin taji a rufe, ta tabbata key ya sanya, jikinta a sanyaye ta dawo ta zauna kusa da 'yar uwarta idanunta na kawo ruwa, wannan alamun da ya nuna ya nuna mata fushi yake da ita.....Rashida tace"Anti Wasila akwai abinda ke faruwa tsakaninki da Mijinki dan naga alamu tun a gurin karatu." Tace"Wane alamu kika gani.'? Tace"Yanzu fa ya shigo Kinyi mishi sannu be amsa ba, anti Wasila Allah kina 'kure hakurin mutumin nan sai bashi wuya kike nasan laifin naki ne wallahi." Cike da mamaki take kallonta tace"Har kike rantsewa laifina ne."? Rashida tace"Eh mana ni dai tsayin wata biyu da nayi a gidan nan banga abinda mutumin nan yayi miki na 'bacin rai ba kullum.cikin kyautata miki yake yi yana rarrashinki da kula dake, kinga kuwa dole nace laifinki ne." Shiru tayi tana nazarin maganar 'yar uwartata, babu shakka tsayin wata biyu da sukayi a gidan idan tace ga laifinsa tayi masa sharri kullum cikin tattashinta yake watarana ma abinci shike bata a baki, ta haye jikinsa tayi ta nu'kur'kusa bai ta'ba gajiyawa ba, tabbas laifi daga gurinta yake,
Ta kalli rashida a nutse tace"Nasan dai ke me hankali ce rashida idan na fad'a miki dalilin da ya saka yake fushi dani zaki daina ganin laifina, a gabanki komai ya faru kuma a gabanki likita ta gindaya min sharad'ai, kinfi kowa sanin irin 'bakar wuyar da nasha kafin wannan cikin na jikina ya zauna, duk wani 'kokari inayi masa domin na biya mishi bukatarshi duk hakan bai isheshi ba dole sai ya kwanta dani ni kuma ina tsoron wani abun ya faru dani da yaron dana ke dauke dashi a mahaifata." Rashida tace"Lallai anti Wasila dama saboda wannan matsalar ne yasa kike ta bashi wahala, gaskiya kin zalince shi wallahi ai itama likitan ba tace kar ayi ba cewa tayi a dinga d'aga 'kafa, tun a lokacin da cikin yake 'karami take wannan maganar to yanzu kuma ya girma ni ina ganin babu abinda zai same ki da yaron dake cikin ki kawai dai dan kin kasa kwantar da hankalinki ne yasa kike ganin kamar wani abu zai faru dake."
"Gaskiya Rashida bana jin zan iya amincewa da bukatarshi dan ni 'kadai nasan irin 'bakar wuyar da nake ci babu ciki ma ballanta yanzu da wannan cikin ai nasan mutuwa zanyi kawai yayi hakuri Har Allah yasa na haihu.'' Rashida tace" Ni wallahi bana so naga kina 'bata masa rai duk sai
naji babu dadi dan Allah ki bashi hakuri anti."
"Ki kyaleshi zai huce da kanshi, ni ba zan iya wannan bita zaizai d'in ba, sai ma ya d'auka na damu dashi ne." Rashida ta 'bata rai! ta tsani halin taurin kai irin na 'yar uwarta wallahi, kawai dan taga yana sonta ne shiyasa take masa wulakanci ita sam ba taga aibu ba dan ta bashi hakkinsa rana daya yayi ai ba laifi bane.
Wanka tayi ta shirya cikin kayan bacci ta nemi gado ta kwanta tana jiran shigowarsa kamar yanda ya saba, ko mai dare idan ya dawo koda tayi bacci sai ya tashe ta akwai wani Ice cream da yake siyo mata mai dad'i sai tasha shi take samun nutsuwa, yau tana tunani ko ya siyo ko bai siyo mata ba, tana dai jiran shigowarshi d'akin.......daga zaman jira bacci ne ya d'auketa, ba ta tashi farkawa sai kusan d'aya da rabi! ta kwanta da tunanin Ice cream dan har mafarki tayi ta mi'ke zaune tana dube dube a d'akin wai ko ya shigo ya tarar tana bacci ya aje mata duk ta gama dube dubenta bata ga komai ba, ranta ya 'baci sosai ta riga ta kwallafa ranta dashi dan tayi masifar sabo da shan Ice cream din, bude kofa tayi ta nufi d'akin nashi, har yanzu kofar a rufe take......Yana 'kokarin mikewa daga kan dadduma yaji alamun ana ta'ba 'kofar dakin, a nutse ya karasa bakin kofar ya murza key din dake jiki kofar ta bud'e ita ya gani tsaye tana cikin rigar bacci iya gwiwa mai hannun shimi cikinta ya fito sosai dake rigar irin me kwanciya a jiki ce, kanta babu hula sai dai gashin kanta daure yake cikin katon ribbon, Ya d'an bita da kallo babu yabo babu fallasa yace."Menene."? Kamar zata fashe masa da kuka tace"Ina Ice cream din."? Yace."Ajiya kika bani da zaki tambaye ni Ice Cream yau ban shigo dashi ba." Tayi narai narai da ido tana shirin yin kuka, kofar dakin yake kokarin rufewa, tayi saurin shiga dakin tana kalle kalle......Ya nufi bed ba tare da yace mata komai ba ya zare jallabiyar jikinsa daga shi sai boxer ya haye bed dinshi yaja bargo ya rufe jikinsa.......Ta jima tsaye a dakin tana sha'kar bakin ciki kafin tace"Kaine fa kayi al'kawari kace kullum zaka dinga kawo min tunda babynka yana so da kasan ba zaka cika al'kawari ba da baka d'auka ba." Yanda ta fad'i maganar zaka gane a kufule take dama ance zuciyar me ciki a kusa take.....Yana jinta yayi mata shuru, yana lumshe idonsa, Girgiza kanta tayi da tayi niyar fita sai kuma ta fasa tinkis tinkis ta karasa bakin bed din ta tsaya babu zato yaji gunjin kuka a tsakiyar kanshi, kuka take sosai hawaye na zuba a fuskarta, ya mike zaune da sauri yana kallonta, hannunta ya rike ta fuzge tana cigaba da kukanta, ya 'mike da sauri ya lalubi jallabiyarshi da ya cire ya zura da sauri ya kama hanyar fita daga dakin, idan akwai abinda ya tsana a duniya to bai wuce kukanta ba, ya kan rasa tunaninshi gabadaya idan yaga tana kuka da damuwa, Ice cream dinta na mota, 'bacin ran da yake dauke dashi ne ya sanya bai shigo mata dashi ba, bayanshi tabi dai-dai lokacin da taga ya bude kofar palon ya fita, sai tayi tsaye a tsakiyar palon tana jiran dawowarshi
Ya shigo hannunsa rike da ledar Ice cream din ya ganta tsaye a tsakiyar palon, kai tsaye inda take ya nufa ya mi'ka mata ledar Ice craem din babu kunya ta sanya hannu ta 'karba tana tura baki ta juya zata barshi a gurin, ya rike hannunta na dama, ta juyo tana kallonshi, Hausawa suka ce me nema baya fushi, dik yanda yaso daurewa kasawa yayi kawai sai ya tsinci kansa da rungumeta a jikinshi yana shafa gashin kanta, a hankali ya talfo fuskarta yana so ya hada bakinshi da nata, ta dan kautar da fuskarta, harshensa ya sauka kan ha'barta sai kawai ya shiga tsotsa ha'barta da kumatunta da le'bunanta, tsigar jikinta ta shiga mi'kewa, kafafunta ne suka shiga kyarma ta dan ture fuskarshi tana so ta bar gurin ya matseta sosai dan har sai da tayi 'yar 'kara, shaf ya manta da cikin jikinta saboda hankalinshi baya tare dashi, harshensa ya zura bakinta ya shiga tsotsa yana lumshe idanunsa, itama rintse idanunta tayi ledar hannunta na 'kokarin fad'uwa 'kasa! daurewa takeyi amma ta kasa kawai sai ta yar da ledar hannunta ta sarkafo wuyansa da hannuwanta tana wani irin rawar jiki ta shiga shan baki
nshi, tana lumshe idonta, tayi bala'in missing din bakinshi da yawunsa mai za'ki da gamsawara, sosai suke sucking din junansu, har dai suka gagara tsayuwa ya zauna kan kujera ya dorata a cinyarshi, suka cigaba da sucking din bakin junansu duk sun wani gigice sun ma'kal'kale junansu.
Littafin na kudi ne...!
Kika futa da book din nan keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*70*
'Dumin jikinta da kuma yanayin yanda take shafa jikinsa ya sanya jikinsa ya mutu bacci me dad'i ya daukeshi, a hankali ta d'ora hannunta kan nasa dake 'kasan mararata sai taji ya sake janyota jikinshi ya rike kugunta cikin jikinta yayi wani irin zillo lokaci guda mararta tayi mata wata irin dam'ka! rintse idonta tayi tana cize bakinta ta kasa motsawa kawai saboda bata so ya tashi a baccin da ya daukeshi......Ta jima tana jin ciwon mara kafin a hankali a hankali yayi sauki! sai da baccinsa yayi nisa sannan tayi dubara ta zare jikinta anashi ta gyara mishi bargon jikinsa kana ta fita daga d'akin
Palo ta tarar dasu Rashida suna hira ta dan zaune a hankali tace"Rashida had'o min tea ba zan iya zaman dainnig din nan ba." Rashida ta mike da sauri tana fad'in "To anti Wasila.'" Hajja ta kalleta cike da kulawa tace"Sannu kinji ko ai yanzu tilas kiyi ta jin sauyi iri iri a jikinki tunda ciki ya tsufa sai dai fatan rabuwa dashi lafiya."
Tace"Wallahi kam hajja ni kadai na san abinda ke damuna duk dare da kyar nake bacci ga ciwon kwankwaso." Hajja tace"Dama ai me ciki komai na jikinta ciwo yake ciwon kwankwaso kuma dole ne gabobinki ne suke budewa insha Allahu idan kika zo haihuwa ba zaki sha wuya ba." Tace"Allah yasa Hajja."
Rashida ta 'karaso hannunta rike da madaidaicin cup da tea a ciki sai plate wanda ta hado mata da soyayyan dankali da kwai. 'kasa ta sauka ta dan mike kafafunta ta soma kur'bar tea din tana had'awa da dankalin.
****
*Camas! tare da Usaini dillali*
Malam Usaini dillali yayi nasarar damfarar Camas kudin manya manyan filaye guda uku kud'in sun kai kimanin miliyan shida da rabi dan bayan kudin Wasila har da nata tasa a ciki kusam miliyan biyu usaini yayi mata roman baka inda yake cewa kafin shekara kudin filayen zasu kai miliyan goma ko fiye da haka, duk ya bata dakardun gaibu ya gudu ya bar gari dama ba'asan daga inda yazo ba..........Camas ta zama tamkar mahaukaciya lokacin da taje taga filayenta wani attajiri yana aikin gina gidan gona dashi, ihu! ta dinga kurmawa tana zagin masu aikin gurun wai filayenta ne waye ya basu damar ta'ba mata.....Tana wani irin huci! ta d'auko musu takardun filayen tana nuna musu, duk suka kar'ba suna dubawa, sai suka kwashe da dariya sunayi mata kallon mahaukaciya, babban cikinsu yace."Amma ke jahila ce wallahi wane shegen ne ya fada miki wannan takardar fili ce? hahaha! takardun wuta da ruwa ne saboda dakikiya ce ke baki fahimci abinda aka rubuta a jiki ba." suka dinga dariya suna kallonta........Wayarta ta dauko a fusace! take neman numbar husaini sai dai kiran duniya sai ace mata layin ma baya aiki kwata kwata, ta sharce gumin dake goshinta ta kallesu daya bayan daya tace''Idan kun san wata baku san wata ba, 'yan sanda zan kira muku sune zasu rabani daku shegu tsinannu barayi." Daya daga cikinsu yace."Zaki ci ubanki yanzu." Waya ya ciro ya kira mutumin da ya sanyasu aikin......Minti goma sai gashi cikin wata arniyar mota, ya karaso gurin yana me neman karin bayani, kawai tsaurin ido na Camas! sai ta hau kund'uma masa ashar har tana 'kiransa 'barawo mutumin ranshi ya baci da sauri ya kira *Anti daba* yace suje da ita su tuhumeta a inda yay sata idan ta'ki fada musu su ragargajeta! Tun a gurin suka dinga kwada mata mari suna haurinta da kafafunsu, sosai ta tsorata ta dinga kuka tana bawa mutumin hakuri yace."Ai sai kin fada musu inda naje nayi sata." Camas hankalinta yay masifar tashi ta dinga kuka tana data sani, haka dai *Anti Daba* suka tasa kyeyarta har ofis dinsu.
****
Cikin kaya marasa nauyi ya fito palo yay bacci har ya gaji, baccin da ya jima bai yi irinshi ba.......Kai tsaye daining ya nufa dan da wata irin yunwa ya tashi daurewa yayi yayi wanka gami da sallah sannan ya fito palon , hankalinta a kanshi lokacin da ya fito palon sai ta fara yunkurin mikewa Rashida tace"Anti Wasila ki koma ki zauna ki fada min abinda kike so sai nayi miki." Girgiza kanta tayi tace"Aikin lada zanyi Rashida." Hajja da rashidan suka bita da kallo lokacin da ta nufi inda yake wanda su sai lokacin ma suka san ya fito palon
Har ta'karaso inda yake idanunsa na ka
nta, ya dan sassauta fuskarsa yana yi mata wani irin kallo wanda kana ganinsa kasan na tausayi ne.
A hankali tace"Ya jikin."? Sai ya tafi tunani shaf ya manta plan dinshi, da sauri ya dan ya mutsa fuska yace."Yanzu kam alhmadullhi." tace"Ka jima kana bacci dan har nayi tunanin tashinka kaci abinci kasha magani gashi lokacin shan maganin ya 'kure biyar ta kusa."
Ya aje cokalin hannunshi yana kallonta a nutse yace."Gwara ma da baki tasheni ba dan da kin tasheni mybe ki 'kara min wani ciwon ne tunda kin san bana so a tasheni ina bacci.'
Tace."Eh nima tunanin da nayi kenan."
Ya cigaba da kokarin zuba abincin, cikin nutsuwa ta kar'bi plate din tana kokarin zuba mishi ta hada masa komai ta tura gabanshi.
Yace."Allah yay miki albarka." Cikin zucci ta amsa, tana goge hannunta da tissue yace."Sai ki 'karasa ladanki ko." Ta kalleshi tana son karin bayani.
Girarsa ya daga mata fuskarsa da murmushi me kayatarwa, tayi kasa da kanta tana dan murmushi ta gane abinda yake nufi sai kawai tayi niyyar barin gurin, yace."Idan baki bani da hannuki ba to ba zanci ba."
Ta juyo tana kallonshi cikin shagwaba tace"Bafa mu kadai bane a palon." Yace."Eh nasani tunda kina jin kunya dauko abincin muje daki.'" Makale kafada tayi tace"ka bari idan anjima sai na baka yanzu dai kaci wannnan da kanka."
Ya wani lumshe idonsa yana mata shu'umin kallo yace."Idan anjima ba abinci nake so ki bani a baki ba, wani abu nakeso ki bani." Tace"Koma meye nayi alkawari kai dai kaci kasa magani." Yace."Kince Kinyi alkawari ko."? Daga kanta tayi alamun E yace."To zo ki zauna gabana naci abincin ina kallon fuskarki.'' Dariya tasa tana kallonshi, tace"Idan na zauna kusa da kai ba zakaci abinci sosai ba idan ka gama ci na dawo.'' Da murmushi a fuskarsa yace."A ganinki idan kina kusa dani zan kasa cin abinci ko? baki sani ba xaman ki a kusa dani shine zai sanya na cinye abincin ba tare da nasani ba." Kujerar daning din ta gyara ta zauna tayi tagumi tare da tsira masa ido tace"Shikkenan gani na zauna amma minti biyar na baka ka cinye abincin gabanka." Yanda ta fad'i maganar ya bashi dariya yace."ki dai 'kara minti biyar su zama goma abincin fa nada yawa." Murmushi tayi tace"Tom na kara minti uku." Yace." Okey." Agogon hannunshi ya d'an duba biyar da minti da minti biyu......Sai yay bisimillah ya fara cin abincin da sauri da sauri yana had'awa da lemo Dariya take kunshewa ganin yanda yake cin abincin hannu baka hannu kwarya wai baya so lokacin ya cika bai cinye abincin ba...........Ya d'ago kanshi suka had'a ido lokacin ya cika bakinshi da abinci me cike da ganyayyaki ga nama dariya take tana nuna bakinsa da hannunta 'kasan ha'barshi kan gemunsa duk miya! ta dinga kyalkyala dariya tana kallonshi......'Bata fuska yay da sauri ya kalli agogon hannunsa yaga biyar da kwata....Kallonta yay da sauri! itama tayi saurin kallon agogon hannunta, biyar da minti goma sha shida, Still dai da mirmushi a fuskarta ta d'aga masa hannunta mai daure da agogo tana nuna masa lokaci,
'Bata rai yay yace."Agogonki na latti." tace."Agogona dai-dai yake tafiya kai ka 'kara minti hud'u kan mintinan dana baka dan haka al'kawarinmu ya rushe. Murmushi yay wanda ya tsaya iya la'bbanshi ya mika hannunsa yana kokarin daukar tissue tayi saurin cirowa tana goge mishi bakinshi dai-dai inda ya 'bata a gurin cin abincin.....Kunyace ta rufe ta ganin yana mata wani irin kallo ta juya zata bar gurin......Hannunta ya rike yana me narkar da kwayoyin idanunsa cikin nata.
Taji wani irin yanayi a jikinta, a duk sanda zai mata irin wannan kallon nashi takan ji tamkar wani mayen son shi a cikin zuciyarta.
Mairairaice fuska yay ya mai da kanshi karamin yaro ya wani kankance murya yace." Ina so ki zama mutum mai cika alkawari kan abinda kika al'kawaranta, kada kice min komai kece kikayi min al'kawarin zaki bani du abinda na nema idan naci abinci yanzu kuma kice min alkawari ya rushe."
Yanayin yanda yake kallonta da kuma yanda yake magana kasa-kasa yasa ta fahimci inda ya dosa, sam dazu bata gane abinda yake nufi ba sai yanzu da ya nuna mata zahiri......Jikinta a sanyaye tace"To ai baka da lafiya.
" Ya dan kalleta cike da bege gami da tsantsar sha'awa yace."Duk cutar dake damuna dana kusance ki za tayi nata guri ke dai kawai ki bada kai bori ya hau."
Gabanta na fad'uwa tana d'an kallon gefansu Hajja tace"Tom na amince amma dan Allah kada kayi min da karfi kuma sau daya za kayi." Da sauri yace."Haba!! ai nasan duk abinda ke faruwa ba zan mayi da kaina ba kece zakiyi abinki yanda kike so."
Cike da rashin wayo tace"Yawwa dama ni bana so ka dunga buguna da karfi bana so wani abu ya same ni da abinda ke cikina." cikin rauni gami da tsoro take maganar
Yaji wani irin tausayinsa na ratsashi, hannunta ya rintse a cikin nashi yace."Ki kwantar da hankalinki bbu abinda zai sameki keda yarona lafiya zaki haihu, kuma nace miki yanda kike so zakiyi sai dai idan kingaji na taimaka miki."
Ajiyar zuciya ta sauke tana kallonshi.
Da kyar ta iya cin abincin dare saboda tsabar fargaba motsi kadan gabanta sai ya fad'i! bayan sun gama cin abincin suna kallo a palo shi lokacin ma baya gidan ya dan fita, Ta mike a hankali tana kallonsu Hajja da rashida tace"Hajja zan shiga na kwanta yau bacci nakeji." Hajja tace.''Nima yanzu zan tashi dan har na fara gyangyad'i. Allah y bamu alkairi." Rashida tace"Lallai wallahi ku tsaya ku 'karasa kallon film din nan yayi kyau sosai." Hajja da Wasila babu wanda ya kulata kowanne da abinda ya dameshi.
Ta jima zaune a gefan gado tana tunani ko kawai ta rufe kofarta ko ta gudu dakinsu Hajja tunda ta lura yana jin kunyar biyota dakin....Wani bangare na zuciyarta yace."Ki daure kiyiwa mijinki biyyaya ki samu aljanna kika sani ma ko zaki haihu ko bazaki haihu ba ko ki mutu da cikin a jikinki." Xuciyarta ta karye hawaye ya shiga zubo mata
Jikinta a sanyaye taje tayi wanka ta kimtsa jikinta tsaf sai kamshi turarrika take ta kwanta tana jiran shigowarshi....
Cikin baccin da ya soma daukarta taji alamun shigowarsa dakin....Idanunta ta bude tana kallonshi ya nufi toilet tasan wanka zaiyi.
Ya fito daure da babban towel ya tsaya gaban mudubi yana goge jikinshi......faffad'an bayanshi ta tsurawa ido tana kallo ta lumshe idanunta tana sauke zazzafar ajiyar zuciya.........Motsin zamansa taji a kusa da ita ta bude idanunta, cike da kulawa yace "Baki bacci ba." ? Dan d'aga masa kanta tayi tana kokarin mikewa zaune Yace."Ki koma ki kwanta mana." ta koma ta kwanta gabanta na dan faduwa tace"Kasha maganinka ko." Kallonta yay sai kuma yayi saurin cewa"Zan dai sha yanzu kafin na kwanta." Ya manta da wani magani dan bashi ne a gabansa ba, ashe ita hankalinta na kansa.
Ya mike ya fita daga dakin, mintina goma ya dawo...... Paracetamol kawai ya 'balla ya watsa a bakinsa ya kora da ruwa, ya aje gorar ruwan saman fridge ya nufi bed din......Tana kallon zuwanshi sai ta rintse idanunta tana takure jikinta.
Bargon ya dan ja a hankali ya shiga ciki idanunta ta rufe dai-dai lokacin da taji hucin numfashinsa a kusa da ita.........Hannunshi ya sanya ya d'an juyo da ita suna fuskantar juna........Ya sanya dan yatsansa kan le'banta na 'kasa yana shafawa a hankali.
Shuru tayi duk kuzarinta yakare, cikin kunnanta ya kira sunanta, taji wani irin yarrrr a jikinta.
A hankali ya cire mata rigar jikinta ya kai kanshi kan cikinta ya sumbata tare da fad'in Allah yay maka albarka yarona." Wasila na jinsa nata magana da dan cikinsa kamar me magana da mutum, mamaki gami da tausayinsa ne ya kamata ta lura yana masifar son abinda ke cikinta tun bai iso duniya ba.
shafa sassan jikinta ya shigayi yana sa harshensa yana lasar sa'ko da luko na jikinta yana aika mata da wasu zafafan kesses masu hargitsa lissafi! wani irin rawa jikinta ya shigayi tsigar jikinta ta soma mikewa kamar dai koda yaushe jikinta ya mutu sosai ta saki jikinta ya dinga jagwalgwala iya son ranshi dan babu inda bai tsotsa ya lashe ba a jikintajagwalgwalata romantinc sukeyi irin wanda basu ta'bayin irinsa ba, cikin jikinta bai hanasu aikata komai ba, Amadu ya aikata komai cikin nutsuwa dan ita ya barwa fagen tayi iya yinta mai gudun kada ciki ya samu matsala sai gashi ta manta dashi, tana biyan bukatar ranta, sai da tayi iya yinta sannan ya shi ya soma nashi cikin nit
suwa tana taimaka masa tare da shashshafa sassan jikinsa, duk sun rikice sun had'a zufa fatar jikinsu sai mannewa takeyi guri guda, kusan tare suka samu gamsuwa suka rungume junansu suna sauke numfashi.
Littafin na kudi ne!
Kika futar min da book keda Allah! kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*71*
Can 'bangaran su Uwani kuwa, tun bayan tafiyarsu Wasila sai ta dan samu sassaucin cuzgunawa daga gurin Kuluwa, ta daina kyararta tunda ta gane tana da amfani, shi kansa Kawu Madu din lallabata yake yi wai su shirye suje ga gidan Wasilan tunda basu ta'ba zuwa ba, Uwani ta shiga tunani kan maganarshi tana jin tsoron daukarsu suje garin ganin gida suje su jawo mata abin kunya tasan ba komai ne yake d'awainiya dasu ba sai kwadayin abin duniya, kawu madu kullum cikin naci yake da dai ta gaji sai tace "Shikkenan zasuje amma sai karshen wata, kuluwa tamkar ta zuba ruwa a kasa tasha saboda murna da farin ciki.
***
Sosai *Anti Daba* suka sa'bawa Camas kammani saboda ta kasa kawo musu shaida gamshashshiya wacce zata nuna musu da cewar ita d'in me gaskiya ce, kwanta biyu a hannunsu suka saketa bayan sun mata kashedi mai tsauri kan kada ta kuskura ta kara zuwa filayen nan tace nata ne duk ranar data sake zuwa to sai sun mata dukan mutuwa......A jigace ta fito bakin titi inda tayi parking din motarta ta nufa, wayam! babu ita a gurin, ashe ranar saboda tsabar rud'ewa a jikin motar ta bar key din, kuma akan idanun wasu matasa, aikuwa tana bada baya suka dauke motar, sai yanzu ta tuna abinda ya faru tsugunawa tayi bakin titi rana na dukanta ta dinga kukan bakin ciki, sai da tayi ta gaji ta samu babur ta hau government house ta nufa.
******
Yau dai basu samu damar zaman karatu ba dan basu tashi da wuri ba, Rashida ma gajiya tayi da zaman jiransu ta bar gurin, basu fito palo ba sai takwas saura, lokacin Hajja da Rashida har sun karya suna zaune suna hira...... Kai tsaye inda Hajja ke zaune suka nufa a nutse suka gaisa Wasila sai sinne kai takeyi kunyar hajja takeji sosai, barin gurin tayi ta nufi daning shi kuma ya zauna suna magana da Hajjan.........Suna break fast ta d'an kalleshi sai akaci sa'a shima ita yake kallo, kasa tayi da kanta, ya gane duk sanda take son yi masa magana kunya na hanata, yace."Akwai abinda kike bukata ne."? Ta dago kanta a hankali tace"Ina so ka dan bani waya ta ina so mu gaisa da Kawu duk da dai bani da numbar wayar Kawu Habibu wacce zata sadani dashi nasan baza'a rasa a gurinka ba.'
Murmushi yayi yana goge bakinsa yace."da akwai numbar Kawu Habibu a wayata sai da kwanaki nayi ta kiran wayar baya dagawa nasan fushi yake dani kan abinda ya faru.'' A hankali tace"Kawu Habibu fushi ne dashi nima bama shiri sosai munfi yi da mai allo." Wayarsa ya mika mata yace."Ki duba sunanshi nayi serving da Habibu garko."
Wayar ta amsa tana budawa taga hotonsu ita dashi a fuskar wayar hoton da hafsa ta daukesu lokacin da suka zo hoton yay masifar kyau......... 'Dan kallonshi tayi hankalinsa na kan karamar wayarsa yana dubawa, ta dauke kanta tana sauke ajiyar zuciya bata ta'ba tsammanin haka yake da saukin 'kai ya mai da kansa karamin yaro duk dan saboda farin cikinta.
Tayi ta kiran layin Kawu Habibu gashi dai tana shiga amma bai dauka ba, Ta dan kalleshi sai taga yayi murmushi, a nutse yace."Mutukar fa zai ga numbarta ce ba zai dauka ba har yanzu nima kunyar hada ido nake dashi nasan abinda nayi ban kyauta ba amma ai na bada hakuri kuma ya cancanta a yafe miki ko." Cikin wani irin yanayi yake maganar.......Sai taji tana jin zafin Kawu Habibun meye abin ri'ko da daukar gaba, ai itace mai laifi tunda duk abinda ya faru itace ta jawowa kanta itama yanzu ta daina ganin laifinsa bisa ga sakin da yay mata ta wani gefan ma farin ciki take da hakan ta faru tunda gashi tayi hankali tasan inda yake mata ciwo.
Rau-rau tayi kamar zatayi kuka tace"Kawu Habibu haka halinshi yake kayi hakuri." Yace."Nine zan bashi hakuri ai kada ki damu duk sanda Allah ya saukeki lafiya zan daukeki muje har gidanshi na bashi hakuri ai tunda ina sonki babu abinda ba zanyi ba." Hawaye suka zubo mata ta tsira masa ido tana kallonshi ta rasa wane irin so yake mata! Yace"Ke kam bakya gajiya da koke koke goge hawayenki." Ya mika mata tissue kin kar'ba tayi tana shashsheka, hannunta ya rike ya mikar da ita suka nufi dakinshi.
Rungumeta yay ya rarrasheta tayi shuru kana ya bud'e wata drowar dake gefan gadonshi ya dauko mata wayoyinta da
jakarta, cinyarta ya aje mata yace."Ki duba kiga abinda baki gani ba sai ki fada min."
A hankali ta bude jakar tana dubawa komai nata data sani na ciki ga sabbin kudinta nan na sadakin auranta da sauran tarkacenta a ciki ta aje jakar tana kokarin kunna wayar, ya kar'ba ya kunna mata.
Numbar Kawu Habibu ta dauka a wayar tata ta soma kiranshi, aikuwa ya dauka duk suka cika da mamaki.
Muryarta na rawa tace"Kawu Ina kwana" Ya amsa yana tambayar wacece.''?
Tace."Kawu nice Wasila." Tana ji ya sauke ajiyar zuciya yace."Wasila ya kuke ina fatan kunanan lafiya ko? ina mijin naki."?
Ta dan kalleshi yana zaune yana jinsu, tace"Kawu gashinan kusa dani yana jinka." yace."Masha Allah." Tace"Kawu dan Allah kayi hakuri ka daina fushi nice fa mai laifi dan Allah ka yafe masa kamar yanda mai allo ya yafe masa."
Kawu Habibu yace."Wasila ni tuntuni na yafe masa abinda ya faru kawai duk sanda na tuna sanda yazo gabanmu yace ya sakeki raina yake 'baci sosai, amma ni bana rikon mijinki." Tace"To Kawu me yasa idan ya kira wayarka baka dauka."
Shuru yayi tace"Kawu kayi hakuri magana ta wuce nima nayi alkawari insha Allahu bazan sake baku kunya ba." Yace."Masha Allahu dama haka nake so naji."
Amadu ya kar'bi wayar daga hannunta, a nutse yay sallama Kawu Habibu ya amsa cikin mutumci suka gaisa da juna, Kawu Habibu kunyar abinda yayi masa taso ta hanashi magana, inda shi kuma Amadu ya nuna masa komai ba komai bane ya kuma tabbatar masa da cewar abinda ya faru a baya insha Allahu ba zai sake faruwa ba a gaba..........Kawu Habibu yaji dadin maganarshi sosai da sosai dan yanzu babban burunsu shi da dan uwansa shine yarinyar ta zauna a dakin mijinta.
Mika mata wayar yay bayan sun gama ta karba tana fad'in "Kawu dan Allah idan ka koma gida ka bawa mai allo wayar ina so mu gaisa dashi." Kawu Habibu yace."Insha Allahu idan na koma gida zan bashi yanzu haka nayi tafiya wani gari zan kuma kwana biyu acan sai dai na koma din." Tace."To Kawu Allah ya dawo da kai lafiya." Ya amsa da "ameeen." Sukayi sallama cike da kaunar junansu..........Ajiyar zuciya ta dan sauke kanta a kasa, yanzu tana masifar kaunar kawunanta saboda ta gane yanxu sune gatanka........Hannunsa taji cikin nata yana saka mata wani abu, ta dago kanta tana kallonshi, tana kuma kallon hannunta, wasu takardune guda biyu ya saka mata cikin hannunta........Kallonshi tayi tana neman karin bayani.
Yace." Kada kice komai ni nayi niyya kuma idan nayi kyauta ba'a cewa dani dan me? na jima da mallaka miki wasu kadarori nawa tun ranar da na amshi budurcinki na mallaka miki rumfunana biyu dake cikin kasuwar sabon gari, naki ne a halin yanzu halak malak, tun daga ranar dana mallaka miki kawowa yau din nan duk wani abun da aka samu na cinikayya suna cikin asusuna, insha Allah zamuje a bude miki account zan sa miki kudinki a ciki, bayan wannan kuma akwai sabuwar motar dana siya miki tana can gareji a ajiye, yanzu ki rike key d'in a hannuki." Ya mi'ka mata key din motar yana murmushi.
Hannunta ne ya shiga rawa, ta rasa ma abinda zatace masa sai kawai hawaye ya 'balle mata, rungumeta yay tsam a jikinsa yana shafa bayanta, cikin shashshekar kuka tace"Nagode mijina Ubangiji Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana Allah ya rabaka da sharrin masu sharri Allah ya bamu zaman lafiya da zuria masu albarka." Ya dinga amsawa yana dan bubbuga bayanta a hankali.
****
Cikin ikon Allah da hukuncinsa komai na tafiya dai-dai a zamantakewar auransu, ta samu nutsuwa dashi ya samu nutsuwa da ita, yayin da karatunsu na al'kur'ani yayi nisa sosai yanzu sun wuce izifi ashirin tunda kullum sau biyu yake musu kari, bangaran littafan addini kuwa sun wuce matakin su ahlari da fikhu yanzu manyan littafai yake musu irin su Minhajil musulum zaduzjaujen Ismawi balaga......bangaran ilimin addini Wasila da Rashida ba'a cewa komai sai godiyar Allah.
Cikinta ya shiga wata na tara, lokacin kuma ciwuka suka tsananta yau ciwo gobe ciwo haka dai take daurewa duk sanda bala'in ya isheta sai ta shiga daki taci kukana ta koshi.............Gashi baya xama a gida sosai kusan kullum sai sun fita da jama'arshi yawon campain, wani sa'in ma
kwana sukeyi ko kuma su dawo cikin dare lokacin ta dade da yin bacci, ga Rashida ta soma zuwa makaranta abun dai duk babu sauki ta kowanne bangare wani lokacin hajja itake zama tana debe mata kewa idan kafafunta sunyi tsami ta matsa mata a gaskiya babu abinda zata ce da matar sai dai addua.
Akwai ranar da Anti Kubura ita da yaranta suka zo gidan suka tarar da Hajja na matsawa Wasila kafafunta duk sai suka shiga mamaki mai tsanani yanzu kamar hajja ke aikin matsar kafa.....Anti Kubura ta kufula ranta yayi masifar 'baci ta kalli Wasilan shekeke tace"Wato asiri da surkullen naku na fulani ya dawo kan baiwar Allah wacce bataji ba bata gani ba, kawai saboda tsabar rashin arziki ki mike kafafu ki sanyata matsar kafafu shin itace tayi miki cikin da zaki dinga sata aikin wahala? ke ko kunya bakiji ba." ! Hajja tace"A'a kubura nice nasa kaina ba itace ta sani ba, to idan ma itace ta sani laifine dan na matsa mata kafafunta ai lalura ce! bana son irin abinda kikeyi kubura." Hajja ta karashe maganarta cikin jin rashin dadin abinda tayi.....Suhairat da takeji kamar taje ta turmushe Wasilan ita da cikin jikinta tace"A'a Hajja wallahi da sake! baxai yiwu ba idan suna cin 'kasa to su kiyayi ta shuri! asirinsu da surkullansu ba zaiyi tasiri a kanki ba, shi da Yaya Amadu da yaga zai iya sai yaje yayi, amma kamar wannan mara gata da galihu ta saki a gaba kina mata matsar kafa! ai bata isa ba idan ita bata san darajarki ba to mu mun sani."
Wasila ta soma kokarin mi'kewa ta bar musu gurin......Hajja ta dan rike hannunta tana mata sannu, hawayen dake kokarin zubo mata ta mayar ba tace komai ba tabar gurin, tana jin Suhairat na zaginta da kiranta 'Yar iska jahila mai bin maza." Wannan kalmomi sunyi mata ciwo sosai, kawai ta kwanta kan gado ta shiga kukan bakin ciki da takaici! Illar ka aikata mummunan abu kenan bata ta'ba zina ba amma gashi anzo har cikin gidanta ana kiranta da karuwa me bin maza...
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*alliya:
'Yr Bngr Sys
*72*
Bayan shigar Wasila d'aki Hajja ta shiga yiwa anti kubura da Suhairat fad'a kan abinda sukayi bai dace ba suzo har gida s suna zagin matar gida......... aikin matsar kafafu itace tasa kanta ba wai Wasilan ce ta sanyata ba, tace mutukar idan kun san tashin hankaline zai kawo ku to ku daina zuwa dan kun san idan Amadu yaji ba zaiji dadi ba bana kaunar abinda zai 'bata masa rai kamar yanda baya kaunar abinda zai 'bata min rai! Ke suhairat ki iya bakinki wallahi naji kina kiranta karuwa a gidan ubanki tayi karuwancin? to wallahi kika sake Amadu yaji wannan maganar zai iya daureki kuma wallahi ba zance masa dan me ba tunda bakinki ne ya jawo miki." Da jin abinda Hajja take fada sai kawai anti kubura ta fashe da kuka tana fyace majina tace"Haba Hajja ashe kudi yafi zumunci kada fa ki manta ni dake uwarmu daya ubanmu daya, Amadu kuwa bake ce kika haifeshi ba dan mijinki ne amma kike kokarin za'barsa akaina shikkenan nagode."Anti kubura ta karasa maganar tana mikewa, tsaye suma Suka mike ransu a 'bace! Hajja tace"Yanda kika dauki al'amarin ni ba haka na daukeshi ba Kubura nagode kwarai yau ni kikewa gurin haihuwa ko babu komai." Anti kubura ta kad'a kan 'yayanta suka fita daga gidan ransu a tsananin 'bace! Hajja kuwa sai da ta matse hawaye kafin ta mike ta shiga cikin daki.
Rashida da ta dawo gidan duk sai ta gansu wani iri babu cikakkiyar walwala alhalin ba haka ta tafi ta barsu ba, sai da suka ke'be da 'yar uwarta take tambayarta abinda yake faruwa, Wasila na hawaye take fada mata irin zagi da cin mutuncin dasu Suhairat da mahaifiyarta suka zo sukayi mata.
Rashida ta fusata sosai tace"Wallahi anti Wasila da ina gidan sai na rama mi ki wannan ai rashin mutuncine da iskanci su shigo har cikin gidanki suna zaginki na rantse da girman Allah duk ranar da Suhairat ta sake zuwa gidanan ta zage ki sai na nuna mata wacece ni sai ta futa da fashashshan baki." Wasila tace"Ki kyaleta rashida tayi na farko tayi na karshe nima na dauki al'kawarin kan duk ranar da ta sake zuwa taci min fuska cikin gidana sai ta gane bata da wayo...........
To Yau ma bai shigo gidan da wuri ba sai kusan sha biyu da rabi na dare lokacin tayi bacci har ta gaji dan wajejan takwas ta kwanta yanzu kwanciyar ma wuya take mata sai tayi ta juye juye da zarar bacci ya dauketa bata minti talatin sai ta farka, jin shigowarsa dakin ya sanya ta mike zaune......Yace."Baki bacci ko jikin ne.'? Girgiza masa kai tayi, yace."Okey bari nayi wanka ko." ba tace masa komai ba ya nufi toilet, tana zaune ya fito ya kimtsa jikinsa ya fita daga dakin
Minti biyar ya dawo hannunsa rike da ledoji guda biyu ya aje kasan kafet ya bude fridge ya dauki lemo da ruwa........Lokacin da yake kokarin zama kasan kafet ne ya fahimci damuwa a fuskarta, ya kalleta cike da kulawa yace." Menene? Hawayen da take 'boyewa suka su'bce ta soma kuka da shashsheka
Yaji duk wani annushuwa da farin cikin da ya shigo dashi ya dauke, jikinsa na kyarma ya zauna kusa da ita yana me rungume kafadunta da hannunsa....."Kiyi shuru ki fada min abinda ke damunki bana son wannan kukan naki." Abinda yake fada kenan yana goge mata fuska da hannunshi.
Kwanciya tayi a jikinsa tana cigaba da kukanta. Hankalinsa yay masifar tashi ya dinga rarrashinta da kalamai masu sanyi,da kyar tayi shuru yace."Kukan da kikeyi bai da amfani saboda yana sa hankalina tashi ki fada min abinda ke damunki."
A hankali tace"Meye tsakaninku da Suhairat."? Sai ya shiga tunanin wacece ma Suhairat? can ya tuna yarinyar anti kubura ce kanwar Hajja. Yace."Kanwata ce me ya faru.''?
Ajiyar zuciya ta sauke tace"Ai kai baka da wa ko 'kanwa." Yace."Eh hakane ita suhairat din yarinyar kanwar Hajja ce anti kubura."
Tace."Kace mata kada ta sake zuwar min gida tunda ba alkairi ne yake kawota ba."
Ya danyi shuru yana mamakin maganarta, cikin nutsuwa yace "Kince ba alkairi ke kawota ba sai ki fada min abinda ya faru dan na fahimci dama keda ita tuntuni kunsan juna."
Tace."Idan na fada maka abinda ya faru ranka zai 'baci watakila ma ka dauki tsatstsauran mataki akansu har ita anti kuburan, fad'ar maganar bata da amfani tunda ba alkairi ba
ne, dalili kenan da ya sanya nace ka hanasu shigowa inda nake dan mutukar suka sake zuwa suka zagi iyayena sai na rama.".....Ranshi yaji ya 'baci jin abinda tace Yace."A gaban hajja kukayi wannan shashancin."? Mikewa tayi daga jikinsa tace"Nifa kar kaga laifina nasu ne dan bar musu gurin ma nayi saboda abinda ya dameni shi ya dameni."
Yace."Shikkenan tunda bakya so su shigo miki gida zasu daina shikkenan ko?" Babu kunya tace"Eh." Yace."Sauko kici abinci." Tabi ledojin dake gabansa da kallo, a hankali ta sauka ta dan mike kafafunta shi kuma ya shiga bude ledojin manya manyan kaji ne gassasu wanda sukaji hadi sosai sai kamshi sukeyi.
A nutse suke ci suna dan hira yana bata labarin irin nasarorin da yake samu ta 'bangaran siyasar shi, yanzu babu local goment din da basu kai ziyara ba kuma ko ina sukaje cike da nasara suke dawowa, al'amarin siyasar dai ya dauki zafi sosai da sosai ta inda ko ina ka zaga a fad'in jahar kano zance Amadu Musa ake da fatan Allah ya bashi mulkin jahar kano a hannunsa, pastes dinshi sai yawo suke a titi kasuwanni gami da jikin gidajen mutane, gabakidaya al'ummar jahar kano sun gaji da mulki Lawal rabo sauyi kawai suke bukata a jahar tasu.
Sosai taji dad'in irin nasarorin da yake samun ta 'bangaran siyasarsa dan har sai da fuskarta ta nuna alamun jin dadi ta dinga yi masa addua gami da fatan nasara akan dukanin abinda ya sanya a gaba.........Da kyar ta yunkura ta mike tsaye ya dan bita da kallo lokacin da ta nufi toilet sai ya mai da hankalinshi kan abincin dake gabanshi......brush tayi ta tsuguna tana fitsari dan yanzu haka takeyi bini bini fitsari kuma idan ta tsuguna ba wani na kirki takeyi ba.?
tana tsarki taji wani abu me yauki na biyo hannunta bata damu ba dan tun da cikinta ya tsufa take ganin abubuwa iri iri, da kyar ta mike tsaye tana cije baki ji Tayii kasan mararta yayi mata wata irin dam'ka! salati tayi ta dan rike kofar toilet din tana mai da numfashi.
A hankali ta lalla'bo ta fito lokacin baya dakin sai ta kwanta kan bed tana lumshe idonta......Bacci ya soma fizgarta taji motsin shigowarsa ya shiga toilet yay brush ya fito ya kashe fitila yaje ya kwanta kusa da ita......Kamar dai zai daure sai ya kasa hannunsa yasa ya dan janyota jikinsa yana shafa bayanta da gashinta
Gabanta ya shiga faduwa tana addua Allah yasa kada yace wani abu dan yanda take jin ciwo bata jin zata iya wani abun.....Aikuwa dai abinda yake nufi kenan dan sai kesses yake mata tare da kokarin sabule mata rigar jikinta.
Cikin sanyin murya tace"Dan Allah kayi hakuri yau cikina ciwo yake." A marairaice yace."Nayi kokarin yin hakan nakasa ki daure nayi koda sau daya ne hankalina zai kwanta." Shuru tayi masa, ya cigaba da wassaninsa da sassan jikinta yayin da take sake jin ciwo na tsantsanta a gareta ta dinga cije bakinta tana kokarin daurewa, lokacin da ya shigeta wani irin murd'a da dam'ka mararta tayi ta rirrike damtsansa tana salati! shi kuwa ai baya ma cikin nutsuwarsa dan duk sanda zai jishi cikin wannan gurin yakan manta da hankalinsa.....Jin kamar an 'kara mata ni'ima ya sanya ya kwarkwance ya dinga buga sambatu yana bugunta sam ya mance lalurar da take tare da ita.
Kuka ta dinga yi tana masa magiya ya rabu da ita, lokacin yake kara kuzari da karfi kukanta na kara ingixashi kan abinda yake yi............nishi ta dinga fitarwa sama-sama yaron dake cikinta yana dunkulewa guri guda yayinda mararta take mata wata irin dam'ka tana murd'a mata!! "Wayyo Allahna ka kawo min agaji kada na mutu na shiga uku abinda nake gudu sai ya faru."! sambatun surutun da take kenan! ya rufe mata bakinta yana sake bugunta da karfi shima yana daf da kawowa ne shiyasa ya rasa nutsuwarsa...........Jikinta ne yayi lakwas duk wani kuxari nata ya kare sai idanunta suka hau lumshewa tana shiga ganin bibbiyu cikin idanunta.
Sai da ya tabbatar da duk ya fitar da abinda ke mararashi sannan ya hakura, aikuwa yana zare jijiyarshi wani irin jini ya ambulo daga jikinta.......Yaji saukarshi kan cinyarshi, cikin gaggawa ya kunna fitila dakin yay haske kawai sai yaga idanunta suna kafewa tana jawo nunfashi da kyar ga jini sai ambulowa yake daga
gabanta.
Salati ya sanya a d'imauce ya sauka daga bed din, yay dira dira sai ya dawo bed din a gigice ya dauki jallabiyarsa yasa da gajeran wando.....Hannunsa na kyarma ya dauki wayarsa ya kira Dr Nasir yace gashinan zuwa hospital dinshi emagency........Garba ya kira a waya yace maza ya fito da mota.......Yay gaggwar maida wayar aljihunsa ya tarairayota jikinsa sai rawa yake yaga tayi lakaf komai nata ya daina aiki! Kawai sai yaji ya tsinke da al'amarin cikin gaggawa ya fita daga dakin ya kira Hajja a gigice ta fito ita da rashida suka shiga dakin.
Rashida na ganin halin da yar uwarta take sai ta fashe da wani irin kuka tana fad'in "Anti Wasila kada ki mutu ki barni wayyo na shiga ukuna." Rirrike hannunta tayi tana kuka, ita kuwa hajja ba yarinya bace ganin babu kaya a jikin Wasila ya sanya ta fahimci abinda ke faruwa, wato rashin hakurinsu yasa sun jawowa kansu matsala, na'kuda mai tafe da jini ai hadari ce sosai.
Da sauri ta umarceshi wanda yake tsaye ya rasa yanda zaiyi da ya sani yake yafi dubu....Tace"Ka dauko mata kayanta ka sa mata muje asibiti." Sai sannan ya dawo hayyacinsa ya nufi wardrobe cikin saurin gaske.
Rashida ce ta sa mata kayan shi kuma ya dauketa a hannunshi suka fita daga dakin........Garba ne ya tukasu zuwa asibitin dr nasir yayin da jikin wasila ya sake rikicewa sai salati takeyi tana yin wani irin nishi wanda kana jinsa kasan tana cikin halin ciwo........Amadu addua kawai yake mata hankalinsa duk ya tashi lokacin ita kuma ta dinga rirrike masa hannunsa tana wani irin murkususu a jikinsa.
Littafin na kudi ne....
Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*73*
A mutukar galabaice aka shiga dakin haihuwa da Wasila, Dr Nasir da wasu narses biyu suka rufu a kanta har sai da suka samu nasarar tsayar da jinin dake zuba daga jikinta, lokacin kuma ta daina duk wani yunkuri da takeyi duk karfinta ya kare bata gane wanda yake kanta, Dr Nasir ganin halin da take ciki na baraxana da rayuwarta ya sanya ya fita daga dakin da sauri, nan ya iskesu a tsaitsaye Amadu sai zurga zurga yake a gurin hankalinsa a tashe.
Dr yace."Yallabai muje ofis zamuyi magana." Amadu ya juyo yana kallonshi, ganin yanayin fuskar dr din ya sanya jikinsa yin sanyi sai kawai yabi bayanshi yana mi'kawa Allah a'lamarin.
Dr Nasir yace"Yallabai yarinyar nan ta galabaita sosai dan duk wani karfinta ya kare, ba zata iya haihuwa da kanta ba kayi hakuri ka sanya hannu yanzu mu shiga idata tiyata." Wani irin gumi ne ya shiga yanko masa, idanunsa sunyi jawur ya karbi takardar dake hannun Dr din jiki a sanyaye ya sanya hannu ya aje takadar yana me dafe kansa Dr ya mike a hankali yace"Yallabai ka kwantar da hankalinka insha Allah za'ayi nasara." Kanshi na 'kasa har dr din ya fita daga ofis din bai dago ba dik ya rasa yanda zaiyi yana ganin kamar rashin hakurinsa ne ya janyowa yarinyar shiga wannan matsala........Hannu yasa ya goge gumin fuskarshi ya mike ya fita daga ofis din da sa'bulallan jiki.....Hajja da rashida na ganin yanayin sa ai duk hankalinsu ya tashi,Rashida kam kuka tasa tana adduar Allah ya raba 'yar uwarta da wannan wahala da take ciki.
Dr Nasir na komawa dakin sai yaga nurses din sun rufu a kanta, tun kafin ma ya fadi abinda ke bakinsa daya daga cikinsu tace"Dr insha Allah zata iya haihuwa da kanta dan gashinan yaron ya soma fitowa sai da babu karfi a jikinta wanda zata taimaki kanta."
Dr nasir yace."Alhamdullhi kuyi mata duk wani kokari da kukeyi mu gani idan bata haihu ba nan da minti goma za'ayi mata Cs domin ceto rayuwarta.
yana gama maganar sai ya fita daga dakin yaje yana shaidawa Amadu halin da ake ciki hannunsa ya daga sama yana rokon Allah ya sauketa lafiya.
To cikin ikon Allah Wasila ta dan samu karfi da kuzari a jikinta ta dan dunga taimakawa kanta gurin yin nishi yayin da su kuma narses din suke mata dabaru irin nasu, har Allah yasa kan babyn ya soma fitowa sai kawai suka yanke shawarar yankata domin rage mata wahala guri daya suka yanka, aikuwa tana yin wani yunkuri babyn ya fito tare da mahaifarshi.....Lokacin taji wani irin sanyi duk wani ciwo da takeji ya dauke da kyar ta kalato miyau ta hadiya ma'kogwaronta ya bushe kamas.
Cike da farin ciki narses din suka shiga gyara babyn suna kwarzanta kyawun yarinyar gata katuwar gaske tamkar ba haihuwar fari ba.........Wasila na jinsu sama sama tsabar wuya da galabaita ta hanata motsa koda d'an ya tsanta ballanata ta bude ido taga abinda ta haifa.
Da saurin nurse ta fita cike da walwala da farin ciki ta samesu sunyi jugum jugum da sauri tace"Dr ta haihu yanzu an samu baby girl." Dr Da Amadu suka mike da sauri sai suka soma rige rigen shiga dakin Amadu sai washe baki yake kamar gonar audiga.......Ita kam rashida zubewa tayi a gurin tana sujjadar godiya ga Allah.....Dukaninsu suka shiga dakin, muryoyinsu ya sanya Wasila dan bude idonta tana kallonsu dishi dishi taga sai murna da farin ciki sukeyi suna dariya, rintse idanunta tayi tana ajiyar zuciya tabbas sai yau tasan tazo duniya ashe haka mahaifiyarta tasha wuya kafin ta haifeta.......Dr Nasir ya kalli Amadu dake kokarin zuwa gadon da take kwance yace."Yallabai ina ganin dole ayi mata karin jini saboda ta zubar da jini da yawa." Yace."Dr ayi komai idan da hali ma za'a iya daukar nawa idan zaiyi dai-dai da nata." Dr Nasir yace." okey to zan gwada yanzu."
Kusa da ita ya tsaya yana dan kallon fuskarta lokaci kankani ta rame duk tayi zuru zuru, ya kama hannunta ya rike cikin nashi, idanunta ta bude tana kallonshi, a hankali yace."Sannu." Kanta ta daga mishi ta maida idanunta ta rufe.........Hajja da Rashida suka karaso gurin suna mata sannu ba tare data bude idanunta ba ta daga musu kanta.....Hajja ta kalleshi da fadin "Gaggawa ta sanya bamu dauko komai ba dole aje a dauko mata kaya t
unda na jikinta sun baci." Yace."Bari na koma gidan yanzu." Hannunta ya saki da sauri ya fita daga dakin........Suna tsaye ita da rashida nurses din suka fito daga wani daki sun shirya baby tsaf da ita cikin kayan sanyi tana kamshin turare me dadi.....Hajja ta sanya hannu ta karbeta sai washe baki take tana musu godiya........daya daga cikin narses din ta tsaya kusa da Wasila tana mata magana......bude idanunta tayi tana kallon narse din da kyar tace."jiri ne kawai ke damuna sai bacci." Nurse din tace"To bari na taimaka miki muje toilet na gyara miki jikinki sai ki kwanta kafin Dr ya shigo." Daga kanta tayi narse din ta kama hannunta suka mike tsaye a hankali a hankali suka nufi toilet din dake cikin dakin.......ma dai-daicin ruwan dumi narse din ta hada mata ta zaunar da ita a jikin ruwan kana ta samu towel mai tsafta da wani ruwan d'umin tana dan danna mata jikinta.........Fitowa tay daga toilet din wanda yayi dai-dai da shigowarsa dakin hannunsa rike da ledoji Hajja tace"Yawwa kayan ne ko."? Yace."Sune Hajja ina take.'? ya fada yana rarraba idanunsa a dakin....Hajja tace "Tana bandaki." Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya dan tsaya kusa da rashida yana le'ka fuskar babyn tashi.....Hajja ce ta karbi kayan hannunsa ta mikawa nurse din ita kuma ta kar'ba ta daukar mata riga da zani na atamfa da pants da audiga guda biyu, ta juya da sauri ta koma toilet din
Rashida ta mi'ka masa babyn tana murmushi tace"Yayana kamarku daya da yarinyar na dauka ma zata dauko kammanin anti na saboda wuyar data bamu kafin tazo duniya." Murmushi yayi ya karbi yarinyar yana kallonta yace."naji dadi da tayo kammanina rashida nima ai nasha wuya kafin na sameta."
Rashida na cike da farin ciki tace"Ubangiji Allah ya rayata ya bawa mamanta lafiya." Ya amsa da "ameen lokacin da yake kara bakinsa kunnan yarinyar yana mata hud'uba gami da kiran sallah.
Ganin nurse din ta fito da ita daga toilet din a kimtse gashi tana tafiya da kafafunta sai ya sauke ajiyar zuciya yana sake godewa Allah da ya sanya komai yazo cikin sauki.......Dr ne ya shigo yace." Yallabai zamuje yanzu a dauki jinin." Sai yay gaggawar mikawa rashida babyn dake hannunsa suka fita daga dakin tare da dr din.....Rashida da hajja suka nufi gadon da Wasila ke kwance suna sake yi mata sannu, kai kurrum take iya daga musu bakinta ya mutu murus har yanzu tana tuno irin bakar wuyar da tasha acikin awannin da suka gabanta, rashida ta dan zauna kusa da ita a hankali tace"Anti wasila baki dauki babyn ba." idanunta ta bude a hankali take kallon rashidan da babyn tayi murmushi a hankali tace "Rashida yarinyar na kama da babanta ko."? Rashida tasa dariya tana kallon Hajja tace" Eh mana nida hajja ma haka muka ce." Murmushi ta sakeyi ta rufe idanunta a hankali tace"Allah yayi mata albarka." Rashida da hajja suka amsa da "ameeen"
Bacci me nauyi ne ya dauketa wanda tana baccin dr yazo yayi aikinshi ya gama ya fita Amadu kam fita yayi harabar asibitin ya dinga kiraye kirayen waya yana shaidawa 'yan uwa da abokanan arziki karuwar da ya samu.
Karfe bakwai na safe Khalifa da matarshi suka shigo asibitin..........Khalifa ya dauki babyn ciki da farin ciki yake mata addua da fadin Afnan ta samu 'yar uwa dama kullum maganarta yaushe momynta zata siyo mata kanwa."
Hajja da rashida suka saka dariya ya kalli Wasila dake dan murmushi yace "Sannu Wasila Allah ya kara lafiya kin iya haihuwa gaskiya kin biya mu tunda kika iya haifo mai kama damu." Murmushi tayi cike da kunya ta sunkuyar da kanta kasa, hafsa ta zauna kusa da ita tana mata sannu da jiki hafsa tayi sha'awar yarinyar wasila taji inama itace ta haihu ita yanzu cikinta watanshi hudu da sauran lokaci.
Bayan sun koma gida misalin uku na rana sai ga mutanan garko Inna hajara da bitan da kuma matar kawu Habibu mai suna Saratu, mai allo ne yace maza maza suzo su gane masa abinda aka samu kafin yazo.......Su Wasila sunji dadin zuwansu sosai, nan inna hajara da bitan sukaga irin daular da Wasilan ke ciki dukaninsu mamaki suka shigayi babu shakka ba karamin mutum yarinyar ke aure ba, lalacewa sukayi gurin kalle kalle a gidan har gariba tayi gashi mai allo y
ace su koma da wuri, Aikuwa Wasila tace ba xasuyi tafiyar dare ba sai da su bari sai gobe.....Inna hajara tace"Wai ni jama'a gidanan ba'a ganin fad'uwar rana ne? nifa tunda na shigo gidanan nake ganin yanayi daya baka gane ya yanayin gari ya yake wai ashe har magariba tayi bamu sani ba oh."
Rashida ta dinga mata dariya tana fad'in "Nima lokacin da nazo gidan haka nayi ta sai da nasaba tukkuna nake ganewa idan lokacin sallah yayi zakiji kiran sallah ko kuma ki kalli agogo."
Ina hajara tace"Yo duk cikinmu waye ya iya agogo ai kina sake baki sanar damu lokaci ba." Wasila dake zaune kusa da bitan tana shayar da babynta nono tace"Nifa Inna ba zaku koma da wuri ba dukaninku zaku zauna sai anyi suna nayi ar'ba'in tukkuna."
Inna hajara tace"Ashe dai baki da hankali wasila yo ai idan wasu suka gamu rud'u rud'u sai su dauka kwadayi ne ya zaunar damu yanzu ma dan dare yayi ne shiyasa da tuni mun tafi." Wasila tace"Dan girman Allah inna ki zauna ko bitan ku taimaka min." Bitan tace"Idan banda abinki wasila wannan baiwar Allah na zaune tare dake tana iya bakin kokarinta a kanki ai idan muka zauna sai taga kamar mun raina kokarinta ne." Hajja dake kokarin 'karasowa inda suke tace"A'a bitan ni bazance komai ba wallahi ni kaina zanfi jin dadi ace wata daga cikinku ta zauna tare damu har yarinyar nan tayi ar'bain." Bitan tace"To sai dai ko Hajara amma dai sai abinda malam yace Hajja tace"malam ba zaice komai ba insha Allahu.
Koda Amadu ya dawo gidan ya tarar dasu Inna hajara sai yaji dadi sosai ya shiga har inda suke suka gaisa a mutunce yana tambayarsu mutanan gida da malm mai allo, sukace kowa lafiya lau malam yace ayi maka barka kafin yazo.....Yace."Insha Allah gobe zan sanya Garba yaje ya daukoshi domin yazo yaga abinda aka samu.
Kafatanin ma'aikatan gidan babu wanda bai shigo yaga baby ba, dukaninsu suna cikin farin ciki mussaman Garba da Abdulhadi aranar Amadu yayi musu kyatuttuka duk domin farin cikin da suka nuna bisa ga 'karuwar da ya samu.
Wasila taga gata da kulawa gurin Hajja da inna hajara babu abinda takeyi sai aukin bacci idan kuwa kaga baby a hannunta to nono zata sha yarinyar na tsakanin hannun Hajja da inna Hajara watarana kuma rashida itake rainonta idan tana gida......Malam da Kawu Habibu sunzo sunga baby sun sanya mata albarka sosai nan Amadu ke shaida musu sunan yarinyar Fad'imatu sunan mahaifiyarshi kenan.....Malam da kawu suka sanya mata albarka da adduar Allah ya sanya ta zama mai taimakon addinin musulunci.
Ranar suna Wasila ta fito tamkar wata amarya taci gayu sosai da wani uban les Hafsa ce ta dauko mata me make up tayi mata kwalliya sosai ta shiryata hannayenta da kafafunta sun sha jan lalle wanda yayi masifar kyau yayi jawur abun sha'awa, gold din dake jikinta kuwa abin kallo ne dan ana ya gobe suna ya shigo mata da kayan barka ita da baby set din akwatina shida shida makil da kaya iri daban daban wasu a dinke wasu kuma ba'a dinka ba ga uban gold kirar dubai da ya siya mata har kala uku yari da sar'ka da zobuna da abubuwan hannu ko ina na jikinta walwali yake yi.....Hafsa ta gayyaci kawayenta manya mata su kansu sai da suka raina kwalliyarsu ganin kwaliiyar mai jego din ta mussamance.......Zeey da Suhairat kam kasa zama sukayi a cikin gidan tsabar bakin ciki da yayi musu yawa ko wacce ta silale ta gudu ba tare da mutane sun fargaba.
Amadu kam tun da safe kafin ya fita da yaga kwalliyar matar tashi hankalinsa yay bala'in tashi ganin tamkar an 'bare ta daga leda tayi wani 'bul-'bul ta cika ta batse tayi uban kwarjini irin na jego sai daukar ido takeyi, kafin ya barta ta fita daga d'akinsa sai da ya latsata iya son ransa ya tsotsi bakinta ya tayar wa da kansa hankali mutuka, sai da taga yana kokarin shige gona da iri ne yasa tasa masa kuka tilas ya kyaleta jikinsa na kyarma ya shiga goge mata fuska wai baya so ta 'bata kwalliyarta, da kyar ta samu ta kufce daga hannunsa, aikuwa bata sake komawa dakin ba har ya fito tana jinsa suna magana dasu Hajja taki fitowa daga daki sai bayan ya fita daga gidan ne ta fito ta cigaba da hidima da mutananta.
******
Bayan suna da kwana biyu gida ya dawo normal
Hajja da Inna hajara suna zaune a palo bayan sun karya Wasila na cikin daki tana kimtsa kayanta irin wanda ta samu masu uban yawa turaman atamfofi babu adadi ga uban kudin da bata san iya adadinsu ba, dan abokananshi kyauta kudi suka dinga yi mata wanda takasa irgasu ballanta tasan adadinsu, shi kansa khalifa kyautar kusan dubu dari biyu yayi mata tare da sit din akwati cike da kayanta dana baby Zahra......Ya shigo dakin cikin farin yadi anyi masa dinki irin na zaman gida, idanunsa sakaye da farin gilashi, tana ganin ya shigo dakin sai gabanta ya fad'i! ciki ciki ta amsa sallamarshi tana dan gyara kafafunta, ya karaso ya zauna kusa da ita yana nani'karta, kamshin turaransa ya bugi hancinta, ajiyar zuciya ta sauke lokacin da taji saukar hannunsa a bayanta yana tattare gashin kanta daya sauka a bayanta, kafad'arta ya rike sosai ya matso da ita jikinsa murya a kasa yace."Laifin me nayi ne aka daina shigowa gaishe dani da safe."? Dan turo bakinta tayi gaba! Ya sanya dan yatsansa kan le'banta na 'kasa yana shafawa cikin wani irin salo, kallonshi tayi da idanunta da suka dan soma sauyawa, ya dan daga mata girarshi guda daya da munafikin murmushi a fuskarshi.........ta mai da kanta kasa gabanta na faduwa kadan kadan......Cikin wata irin murya yace." To tunda ke kin kasa zuwa inda nake ni gani nazo kin san hausawa nacewa garin masoyi baya nisa duk inda kika shiga kika 'boye sai na biki." Shuru tayi masa ba tace komai ba, ya sanya hannunsa ya tallafo fuskarta suka kurawa junansu ido.....Wani irin zallan sonta ta dinga hangowa cikin kwayar idanunsa, ta dinga kallon kyakyawar fuskarshi wacce annuri ke sauka akai a take taji wani masifar kaunarsa na ratsa ilahirin jikinta.....Lumshe idanunta tayi gabanta na wani irin bugawa da karfi da karfi.....Tana jin sanda yake lasar le'bunanta yana dan tura harshensa cikin bakinta ta wani makale a jikinsa tana sake ri'keshi a jikinta, harshensa dake wasa dashi saman le'bunanta tayi gaggawar sarkafoshi dana ta shiga tsotsa da sauri da sauri tana shafa wuyanshi da saisayyar sumar kanshi...........
Littafin na kudi ne.......!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Wasap numbar
*07084653262*alliya:
'Yr Bngr Sys
*74*
Inna Hajara ce ta murd'a 'kofar dakin hannunta rike da baby zahra dake kukan yunwa tashinta daga bacci kenan tun bayan wanka safe da akayi mata bacci ya dauketa shine ta tashi tana kuka.....Inna hajara na fad'in "Ai dolene ki tashi da yunwa 'yar nan....kasa k'arasa maganar tayi ganin Amadu zaune a kusa da Wasila tayi fi'ki fi'ki da ido shi kuma ya sunkuyar da kanshi 'kasa kunyar duniya ta isheshi Allah yasa ma sunyi gaggawar sakin junansu lokacin da sukaji muryar Innan, to amma dai duk da haka inna hajara sai da ta fahimci wani abu tunda dai ai ita ba yarinya kankanuwa bace." A'lamarin ya bata mamaki sosai dan dukaninsu suna zaune a palo sam basu ga sanda har ya fito daga dakinshi ya shiga dakin ba, Karasawa tayi tana dan gyara fuskarta tace"Kar'beta ki bata nono kada ta soma wannan kukan nata kin san ba zakiji da dad'i ba." A sabu'le ta kar'bi yarinyar tana kokarin fito da nono.....Ya mi'ke tsaye yana dan gyara gilashinsa, ba tare da yayi kuskuran kallon innan ba yace."Inna antashi lafiya ya kwanan su Fad'ima." Inna Hajara itama dake ta iya duniyan ci sai ta maze kamar bata gane komai ba tace"Lafiyarsu kalau Alhaji ga Fad'imatu nan tayi wayo tubarkallah.'" Dan mirmushi yay yace."Allah yayi mata albarka." Inna ta amsa da "ameen." Yana fita daga dakin Inna hajara ta zauna kusa da ita fuskarta murtuk!!!! tace"Wallahi duk sanda na sake gani ya shigo dakin nan kin sakar masa fuska ya ta'baki sai ranki ya 'baci kwana tara da haihuwa har kin soma sakarwa miji jiki ke wace irin 'kwad'ayayya ce ne? ashe baki da wayo Wasila! ashe kin mance irin wahalhalun da kika sha kafin ki haihu shine sabida rashin kamun kai zaki saki jikinki har ya shigo yana tatta'baki ko."
Wasila ta kama kuka tana kokarin kare kanta Inna Hajara tace"Rufe min baki ni bana son shashancin banza da wofi! kefa da kanki kike fad'a min anyi miki d'inki a matuncin ki to har yaushe ya warke da zaki komawa miji shashasha mara wayo kawai."
Cikin kuka tace"Wai Inna me kika shigo ki kaga munayi kawai sai faman fad'a kike min ke baki shigo kinga munayin wani abu ba."! Inna Hajara ta kai bayan hannunta ta make bakinta tace"Dan Ubanki yarinya xaki mayar dani." Wasila ta kame bakinta tana hawaye.....Inna Hajara ta cigaba da sababi tana fad'i na shigo dakin na ganku makale da juna kuna tsotsa tsotse sannan ki raina min hankali."! Da sauri ta sunkuyar da kanta 'kasa tana mamaki ashe duk gaggawar sakin junansu da sukayi sai da ta gansu kai Inna hajara muguwar 'Yar sa'ido ce........Inna hajara tayi 'kwafa cike da takaici tace"Wallahi zan saka ido sosai a kanki duk ranar da na kara ganin kin sakar masa jikinki har kuna rungume rungume da tsotse tsotse to a ranar zan tattara nawa nawa nayi tafiyata tunda ke kin zama mara kamun kai da rashin kintsi.......Har yaushe akayi abun ? guri duk a d'anyace baiyi kwari ba amma saboda rashin hakuri irin naki ki biye masa ya cuceki a banza a wofi."!!! Cikin kuka tace"Ni Inna abar maganar dan Allah naji shikkenan zan kiyaye dan Allah kada ki tafi." Tsaki Inna hajara taja tace"Ai bana magana biyu na sake gani da idona sai dai ki nemeni ki rasa a gidanki." Tana gama maganarta ta fita daga dakin ranta dik a bace
Wasila kuka taci ta 'koshi ta share hawayenta tana cigaba da shayar da babynta tana tunanin abinda ya faru tsakaninsu itama fa ta hango wautarta gaskiyar Inna hajara haihuwar fari tayi, ya kamata ace ta kame kanta a guri guda gudun azo a haifi dan da bashi da ido tasan ita dashi duk basu da hakuri a wannan fagen, gashi kuma bata so Inna hajara ta tafi tilas ne ta kama kanta ko ya shigo ta daina sakar masa fuska, wannan ce sha'awar data yankewa kanta.
Hakance kuwa ta kasance kwata kwata Amadu ya daina ganin walwalarta ko ya shiga dakin ta dinga dauke dauken kai kenan idan ya zauna kusa da ita sai ta sauya guri idan ya dame ta tasa masa kuka tace dole sai ya bar dakin.....Abun da takeyi ya dinga bashi mamaki sosai ya soma jin haushinta yana dai daurewa ne, kawai baya so ya nuna mata fushinsa, ya kuma lura da yanda Inna Hajara ke zurga zurga a dakin duk sanda ta ganshi ya shiga da safe, dama da safe kawai yake
shiga kafin ya fita da daddare baya dawowa da wuri kafin ya dawo sunyi bacci sai ya wuce dakinsa kawai, shi ba yaro bane tsaf ya fahimci akwai saka hannun Inna hajaran gurin abinda Wasilan ke masa duk sai yaji zaman matar a gidanshi ya isheshi tunda ba abun arziki take sa'kawa ba.
*****
Yau kwanansu ashirin da shida kenan har ta soma sallah dan jinin biki da wuri ya dauke mata, tana kwance tana bacci dama 'ka'ida ne idan tayi wanka ta karya sai ta kwanta tayi bacci dan cikin dare ba sosai takeyi ba baby zahra na yawan tashi shan nono.........Cikin shirin fita ya fito daga dakinshi yana sanye da shadda fara 'kal da ita wacce kana ganinta kasan me tsada ce d'inki hannu ne na 'bakin zare wuya da hannuwa sai yay amfani da 'bakar Hula (dara) 'yar gasken mai gashi gashi a jikinta agogon dake hannunsa na dama shima 'baki ne na fatar damisa takalman kafarshi masu gidan ya tsa suma ba'kake sosai yayi kyau tamkar wani sauri dan shekara ashirin da takwas......Suka gaisa dasu Hajja da Inna hajara ya nufi dakin nata, Inna hajara idanunta a kansa tana so tagani idan taga ya jima bai fito ba tabi bayanshi.
Yana shiga dakin ya tarar da ita tana bacci tana sanye da wani material roba roba dinki riga da siket ne dama can kayan sun matseta ballanta yanzu da ta sake cika da cikowa irin ta haihuwa......A hankali ya isa bakin gadon ya d'an tsaya a kanta yana 'kare mata kallo.....Cikin baccinta ta dinga jin 'kamshin turaransa, bud'e idanunta tayi sai taga inuwarshi tayi saurin daga kanta tana kallonshi.
Mi'kewa tayi zaune tana mutsika idanunta, a hankali tace"Ina kwana."? Ya amsa babu yabo babu fallasa......mikewa tsaye tayi tana d'an jan rigarta da duk ta tattare tayi sama, ya bita da kallo tana kokarin wuce shi ya tari gabanta.
Sai ta 'bata fuska tana kallonshi......Shima fuska a 'bace yace."Me yasa kika sauya halinki? wane dalili ne ya sanya duk sanda na shigo dakin nan kike 'bata rai idan na zauna kusa dake ki sanja guri idan na rike hannuki ki saka min kuka meke faruwa dakene."?
Murya a sanyaye tace"Babu komai." Ya had'e ranshi sosai yace."Bana son 'karya ki fad'a min dalilin da ya sanya kike gudana ko zugaki akeyi ne."? Tayi saurin kallonshi......Yace." 'Kwarai kuwa ai da ba haka kike ba cikin 'yan kwanakin nan kika sauya d'abi'u dole ne nayi zargin ko zugaki ake."
Sai ta tsargu! ta dinga kallonsa tana son tayi magana! Sam bata so ya zargi Innarta dan tana so ya cigaba da ganin mutuncinta kamar yanda yake gani ba zata so ya gane cewar Inna Hajara ce ke zugata ba........Tace"Ni babu wanda yake zugani kawai dai ina ganin kamar be dace ba ace muna had'uwa a d'aki ni da kai saboda banyi ar'bain ba."
Ya dinga kallonta yana mamakin maganarta akwai kuruciya da rashin wayo a tare da ita, wannan maganar da takeyi sam bata da tushe ballanta makama kuma ba tunaninta bane, yasan innarta ce ke zugata.
A d'an kausashe! yace." A cikin wane littafin addini ki kaji ance dan mace ta haihu shikkenan ita da mijinta sai ranar da tayi ar'bain? wannan magana da ki keyi irin ta jahilai ce ba'ace dan kin haihu shikkenn sai ki dinga gudun mijinki ba! Ni ba yaro bane na kuma gane abinda kike gudu shiyasa nace wannan abinda ki keyi ba tunaninki bane zugaki akeyi kuma duk me zugaki zata kaiki ta baro ne Ko yau idan nayi ra'ayi zan iya shigowa d'akin nan na kwana tare dake dama ba'ace lallai ki kwana da wata ba ni zan iya kula dake da yarinyata." Yanda yake maganar ne yasa ta gane ranshi a 'bace yake sosai to itama ranta ya 'baci sosai jin yana 'kokarin cin fuskar Innarta a gabanta zuwa yanzu ta gane ya gane cewar Inna hajara ce ke zugata.
Murya na rawa tace"Inna Hajara kake kira da jahila kada ka manta fa a matsayin uwa take a gurina tunda kanwar mahaifina ce." Idanunsa tsaye a kanta yace."Ni da bakina kinji na zageta ko na ambaci sunanta nace da ita jahila." ? sunkuyar da kanta tayi tana kokarin mayar da kwallar dake kokarin zubo mata Tace."Ai ka gane itace shiyasa kake kokarin fad'a mata ba'kar magana a gabana to meye laifinta ai gyara kayan ka baya hana sauke mu raba." Murmushin takaici ne a fuskarsa ya bud'e baki kenan zaiyi magana zuruf Inna Hajar
a ta turo 'kofar d'akin ta shigo kafad'arta sa'be da baby zahra tana fad'in ''Kina ina ne Wasila zo maza kar'beta ki bata nono kada ta fara wannan kukan nata." Duk suka juya suna kallonta tana tsaye a bakin 'kofar shigowa..........Jikinta ne kuma yayi sanyi ganinsu kamar suna cikin 'bacin rai dan ta lura da Wasilan ma kamar kuka take, sai tayi maza ta juya zata futa tana fad'in "A'a Alaji ashe baka fito ba." Yay saurin 'karasawa inda take yana fad'in "Yanzu zan fito Inna bani ita mu gaisa." Ya mi'ka hannunsa ya 'karbi yarinyarsa Inna ta bud'e 'kofar dakin ta fice da sauri duk kunya ta isheta.....Hannunsa ri'ke da babynsa suka 'karasa inda take tsaye tana shashshekar kuka
Littafin na kudi ne!
Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
07084653262
*BINTA UMAR ABBALE*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
[8/24, 9:55 AM] .: 'Yr Bngr Sys
*75*
_Assalamu alaikum barkan ku da safiya da fatan kun tashi lafiya ya gida ya yara? madallah Jiya na fita anguwa tun safe ban samu nayi typing ba sai bayan na fita ne na kawo muku uzirina afuwa👏🏻 da yawa daga cikin ku nasan zasu dauka wani abu daban to nasan wad'anda suka san wacece binta baza su dauki rashin yin typing dina da wata manufa ba, amana d'aya ce kamar yanda na d'auki alkawari kuma na karbi kudin ku #600 domin ku dinga samun update na 'yar banga sau biyu a rana, to ku sani a cikin ku akwai wad'anda nayi wa uziri suna da yawa, kuma a rayuwa dole sai kayiwa d'an uwanka uziri mutum ba kullum yake samun abinda yake so ba, tinda na fara typing na 'yar banga ban tsaya ba ko hutun sallah ban tafi ba kullum sau biyu nake har 'yan normal gruop suna surutun hakan, ban ta'ba tsallake kwana biyu banyi typing ba inayi iya bakin kokarina duk domin na sauke nauyin dake kaina, Ni ina kokarin rike amanarku amma kuma wasu daga cikinku suna cin amanata to wannan be dameni ba saboda nasan kansu sukewa, watarana zan tashi bani da chaji watarana zan tashi bani da lafiya ko yarona, kunga typing ba zai yiwu ba, dole sai da nutsuwa nasan dai wad'anda suka san wacece binta zasu bada shaida a kanta ban kar'bi kudinku dan nayi wasa da hankalinku ba duniya dole sai kayiwa dan uwanka uziri, saboda haka dik sanda aka ga banyi typing ba to a fara tambayar lafiya tukkuna kafin aji bayani na, ku kar'bi uzirina kamar yanda nake kar'bar uzirinku...................Assalamu alaikum🙋🏻♀️_
Yana isa inda take tsaye sai ya rike hannunta ya jata suka zauna kan gado, baby Zahra ya d'ora mata a cinyarta cikin murya mai taushi yace."Ki bata nono kinga tana kuka bana so naga momyna na zubar da hawaye."
Ma'kale kafad'a tayi tana goge fuskarta cikin shagwaba tace"Uhm!Uhum! wato momyka ko? to nima ai momyna ka 'batawa rai." Ya rike kafad'arta yana dan sansana wuyanta a hankali yace."Ayi min afuwa nima Inna Hajara mamana ce kuma kema ai kin san duk abinda na fad'a akanta hakane yanzu gashi data shigo kin tabbatar da maganata ko."? Shuru tayi masa kunyarsa takeji sosai.....Murmushi yay yana dan daga mata girarshi a hankali yace."Ai naga kin fara sallah saboda haka yau dakin nan zan kwana dan kwana biyun nan kokari da hakuri kawai nakeyi sha'awarki zata kasheni." Cikin wani irin voice ya'karashe maganar.
Kallonsa takeyi tana d'an zum'bura bakinta tace"Ni wallahi A'a so kake ka sake farke gurin bayan kasan sai da aka yanka ni." Ya wani marairaice fuskarsa yana mata shu'umin kallo yace."Ai naji Likitarki tace gurin ya had'e ranar da mukaje asibiti."
Hawaye ta share tana sake zu'baro baki gaba tace"Eh duk da ya had'e ai amma tace sai anyi wata uku sannan wani abu zai faru." Jikinta ya sake shigewa ya d'ora ha'barshi kan kafad'arta tare da zura hannunsa ya ri'ko kungunta ya rike sosai yace."Kina so na mutu kenan wata uku da kike magana tamkar shekara uku ce a gurina ai ni yau ma bazan iya hakura ba yanzu kafin na fita zanyi saboda nasan innarki zata hanani shigowa da daddare." Yana maganar yana cusa hannunsa cikin rigarta
Zabura tayi baby zahra dake hannunta ta kusa fad'uwa yay saurin riketa yana dan kallonta yace.''Baki da hankali zaki yar min da momy ko."? Tana tureshi daga jikinta tace"To ka daina ta'bani ko kuma in maka ihu! Inna Hajara ta shigo taga abinda kake." Sai yasa dariya yana kallonta yace."Idan kin min ihu! Inna Hajara ta shigo taga abinda nake meye a ciki dama ni nafi so ta gani itace zataji kunya bani ba."
Shiru tayi masa tana kokarin fito da nono domin bawa baby dake dan kuka......Taimaka mata yayi suka fito da nonon a tare, gabakid'aya idanunsa suka rufe ganin lafiyayyan nonon nata ya cika sosai gashi a tsaye nipple din ya sake tsukewa saboda tsotso, ya sauke ajiyar zuciya me zafi a hankali ya dora hannunsa saman brest din yana shafawa tamkar wani maraya ya d'ora kanshi a kafadarta......Wasila abu biyu ne suka dameta Yanda yake shafa fatar saman brest dinta shine ya sanya ta shiga wani irin hali gashi baby zahra ta kama nipple din tana ta tsotsa, sai tsigar jikinta ta dinga tashi duk ta rasa yan
da zatayi sai mutsu-mutsu takeyi tana dan tureshi yana sake makaleta a jikinsa.....Kuka tasa masa tana fad'in "Dan Allah ka bari wallahi babu dad'i."
Ya bud'e jajayen idanunshi da suka 'kankance yana kallonta kwata kwata ji yay bakinsa yay nauyi ya kasa magana a take jikinsa ya shiga kyarma wani irin sanyi ya dinga ratsa shi.
Tunda taga ya shiga wannan yanayin sai gabanta ya tsananta fad'uwa domin tana gane duk sanda yake cikin tsananin sha'awa jikinsa rawa yake.
Baby Xahra ya kar'be daga hannunta ya ajiyeta gadonta dake gefe, tana kallonshi yana kokarin 'balle botiran rigarshi da links....Sai tayi yunkuri barin gurin yay gaggawar rike hannunta.
Bakinta sai rawa yake takasa magana....Murya a hard'e yace."Ki taimaka min na samu stysifiend ba dole sai na shiga wannan gurin ba tunda kince da matsala ke kin san irin dubarar da zakiyi min ko."? Yana wani lankwashe kansa yake maganar.
A tsorace take kallonsa bakinta na rawa tace"Fita fa zakayi ka shirya tsaf kuma sai kace wani abu ni dai dan Allah ka mayar da rigarka ka tafi inda zakaje."
'Dan 'bata rai yay yace."Wai meyasa ne duk sanda zance miki ga abinda nake so sai kinyi min gardama meye a ciki dan kinyi min dabaru na samu biyan bukata kin san bana neman mata ko? kuma ke kadai ce matata to ki sani wannan halin naki zai iya janyowa na sake aure dan ni mutum ne mai yawan bukata da kuma san soyayya da kulawa."
Jin maganar aure yasa ta soma kuka tana kallonshi tace"To ai inayi maka kokari duk sanda zaka zo da bukatarka ina kokarin ganin ka samu gamsuwa ko ranar da zan haihu ma hakane ya faru, yanzu kuma ai haihuwa nayi ba sai ka hakura nayi ar'bain ba." Kansa ya dafe cikin 'bacin rai yace."Ba zakiyi abinda na umarceki ba." Matsawa tayi gefe tana goge fuska...."Ni dai ka bari nayi ar'bain." ! Yaji kamar ya kwad'a mata mari! Yarinya mai shegen taurin kan tsiya wai meye manufar ar'bain d'in nan da malam bahaushe ya tsira! Tsaki! me kar'fi yaja ya mi'ke tsaye yana maida botiran rigarsa ya d'auki hularsa da gilashinsa da ya aje ya sanya, ya kama hanya ya fita daga dakin ba tare da ya kalli inda take tsaye ba.
Yana fita ta nemi gefan gado ta zauna tana kuka ita tsoro takeji kada Inna hajara ta fahimci wani abun na faruwa a tsakaninsu ta tafi kwata kwata bata so ta tafi shiyasa kuma tana jin tsoransa kada yazo ya danneta ya lalata mata d'inki duk da likitan tace gurin yayi normal amma ai baiyi wani 'kwarin kirki ba.
Inna Hajara ce kadai a palo ita hajja ta shiga daki domin daura alwalar sallahr walha to tana ganin wucewarsa ba tare da ya ko kalli inda take ba sai jikinta yay sanyi a hankali ta mike ta nufi dakin Wasilan.....Ta tarar da ita xaune tana kuka. Zama tayi kusa da ita a hankali tace"Goge hawayenki." Wasila ta goge hawayenta tana sunkuyar da kanta.....Inna Hajara tace"Ni banzo da niyyar na kashe miki aure ba Wasila, na lura mijinki bashi da hakuri ko kad'an, ni kuma ke nake tausayawa saboda irin wahalhalun da kika sha kafin ki haihu Uwa uba akazo aka yanka ki aka d'inke kamar 'kwarya, dole a sanya ido sosai a kanki domin ingantuwar lafiyarki! Bayan haka kuma dole ne kafin ki komawa miji sai an gyara miki jikinki domin haihuwar da kikayi duk wata ni'ima da kike dashi babu nida a tunanina ma ina so idan zan tafi gida muje tare dake can in gyaraki sosai da sosai to amma tunda naga take taken mijinki to zan tattara nawa nawa na tafi dama akan dole nake zaune a gidan, bana so yazo ya dinga jin haushina ko ya fahimci cewar nice nake hanaki biya masa bukata."
Tun kafin Inna hajara ta 'karasa maganarta ta rike hannuwanta tamau! tana kuka sha'be!sha'be! "Wallahi Inna ba zaki tafi ba sai nayi ar'bain sai kace wata mara gata da galihu! ai haihuwar fari nayi kuma koda zanyi haihuwa goma a gidanan kina da damar da zaki zo ki zauna tare dani tunda ina cikin gidan.....Inna nasan abinda nakeyi nima bazan yarda ya haike min ba kawai ya cuceni bayan ban gama dawowa dai-dai ba, na amince zan jure ko wane irin fushin da zai dauka dani nasan idan ya gaji zai daina.."
Inna hajara tace"A'a Wasila ni bazan so kullum ki dinga kwana da tsiniwar Allah da mala'ikunsa ba, kibi mijinki sau da '
kafa kiyi masa biyayya kan abinda yake so ni dai na fad'a miki yau yau zan tafi dan naga kamar haushina yake ji to zai dawo ya tarar na bar masa gidansa.
Wasila ta dinga kuka tana bata hakuri Inna Hajara ta rufe idonta ruf ta fita daga dakin domun zuwa ta had'a kayanta.......Hannunta na kyarma ta d'auki wayarta ta shiga kiransa.....Lokacin yana cikin company sa tare da ma'aikatansa yaga kiran wayar tata ya'ki dauka har yanzu haushinta yake ji
Ta kira ya kai sau biyar bai dauka ba sai kawai ta aje wayar ta fito palo tana goge fuskarta tasan haushinta yake ji shiyasa bai dauki wayarta ba, tana fitowa palo ta tarar Inna hajara da hajja suna fafatawa, Inna Hajara taurin kan tsiya ne da ita ta'ki sauraran hajja hannunta ri'ke da jakar kayanta ta kama hanya ta fita Wasila tabi bayanta har wajen harabar gidan......Garba ya iso gurin da sauri ya karbi jakar kayan hannunta shi baiyi tunanin wani abuba saboda ya dauka inna zata tafi gidane....Can parking ya nufa da jakar kayan ya fito da mota har inda suke tsaye Inna hajara ta bude ta shiga tana 'bata rai! Wasila kallonta kawai takeyi domin ita har ta gaji da magiya da bata hakuri, tana tsaye har garba yaja motar suka fita daga gidan, ta girgiza kanta ta juya domin komawa ciki tana kokarin mayar da hawayen dake so ya zubo mata.
Tana shiga ta tarar da Hajja a tsaye a tsakiyar palon itama tana cikin alhini na tafiyar Inna hajaran Tace"Wasila kodai wani abu akayiwa hajara ne irin wannan tafiya haka da gaggawa, kuma na lura kamar dai ranta a 'bace yake."!
Ta d'an d'auke hawaye a hankali tace"Haka kawai ta tubure wai gida zata tafi babu abinda akayi mata."
Hajja ta zauna kan kujera jikinta a sanyaye tace"To ai shikkenan Allah ya sauketa lafiya." Ta amsa da "ameen tana kokarin shiga d'aki.
****
"Haba Uwani wai dan Allah tun yaushe nake miki magiya kan ki kaimu muga d'akin yarinyar amma kin'ki kaimu kullum nayi miki magana sai kice zamuje to sai yaushe zamuje? kada fa ki manta da cewar kwanaki dani dake mukayi lissafin watannin cikin yarinyar har ki kecewa cikin ya isa haihuwa nace watakila ma ta haihu to kinga yana da kyau muje muga halin da ake ciki." Kuluwa ce zaune a gaban Uwani take wannan maganar cikin 'kas'kantar da kanta.......Uwani ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Kuluwan kamar ba itaba wai yau an wayi gari Kuluwa nayi mata magana cikin kalami mai dad'i lallai duniya kenan.
Tace"Kuluwa ba wai bana so muje bane gaskiya bana so muje gidanan kiyi wani abu da zai sanya kima da mutuncinmu ya zube mutumin nan ba karamin mutum bane kuma kinga mu sirikai ne dole mu kama girmanmu ke kuma kuluwa baki da girma sai na jiki idan kin amince cewar xaki kiyaye kuma zaki nutsu sosai to shikkenan sai mu shirya idan Allah ya kaimu dani dake da Kawu da kuma su Inna mai waina muje muga abinda yarinyar ta haifa."
Cikin kwantar da kai Kuluwa tace"Haba Uwani wallahi bazan aikata abin kunya ba zan kula sosai bazan baki kunya ba insha Allahu." Uwani tace"Shikkenan to yanzu zan tashi na shirya na nufi gidan Inna Tabawa domin na shaida mata halin da ake ciki." Kuluwa tace"To hakan yayi bari idan na sauke abinci sai na d'an d'umamaki ruwan wanka kafin ki tafi kiyi sai kinfi jin dad'i." Mikewa tayi ta nufi kicin........Uwani tabi ta da kallo cike da mamaki.
0 comments:
Post a Comment