Wai me yake faruwa Nabeel? Wallahi nima ban sani ba, domin munyi waya da Abbah yace mun ya fito daga gida ya taho, bayan dana iso naga bai zo ba nakira wayarsa bata shiga na d'auka matsalar network ne shiyasa banyi wani abu ba, ga Adnan ma wayarsa gaba d'aya akashe.
Shiru sukayi Ra'eez yace dama nasan da wuya mu kwashe da sauki a wannan shari'ar, domin da manyan mutane abun ya had'o dole sai mun hada' da 'Yan sanda amma amintattu.
Rafeek yace tabbas zargin da nakeyi ya tabbata, Ra'eez kaje ka samu Alkali ni nasan suna buk'atar ka, ina so kayi amfani da wannan damar ka k'ara samun wani abu, nasan dole Alhaji M. Sanda yayi wani abu, kuma k'arya ne ace Fawwaz baya k'asar.
Ra'eez yace wallahi na ganshi. Jabeer yace yanzu ya zamuyi? Jinjina kai Ra'eez yayi yana fad'in zanyi magana da abokina inspector Hamza nasan zai taimaka mana, kome ake ciki bazamu bari Fawwaz ya bar k'asar nan ba, dan nasan ayanzu suna gab da fitar dashi, dole muyi wani abu matukar muna son a kammala shari'ar cikin sauki.
Ra'eez yace haka za'ayi, yanzu bara naje wajen Alkali, Jabeer kai da Nabeel kuje abi maku diddikin layin Abbah da Adnan, kafin nan Yaya yaje wajen Inspector Hamza sai kuyi magana dashi dole muna buk'atar 'yan sanda saboda kada a cutar dasu Abbah. Kai suka jinjina gaba d'ayansu.
Wucewa yayi ofis d'in Alkali yayinda Alhaji Mansur suke zaune a mota shida Kawun Jabeer suna tattaunawa.
***
Wallahi Alhaji dole na sara maka, sai yanzu na yarda da maganar ka, tabbas kai d'in kwararre ne, amma abinda ban gane ba, gashi dai kace Adnan kawai za'a sace sai kuma gashi Alhaji Sulaiman bezo kotu ba, kuma alamu sun nuna zai zo d'in saboda sunce ya taho.
Murmushi Alhaji M. Sanda yayi yana fad'in kana wasa dani Alhaji Barau, na fad'a maka duk wani wanda naga zai kawo mana tasgaru a wannan tafiyar zanyi komai dan na kaudashi.
Bayan tafiyarka jiya na zauna ina wani tunani, nasan dole sai an buk'aci ganin shugaban makarantar su Fawwaz, gashi kuma bamuyi wata magana dashi ba hakan yasa zuciyata bata amince abarshi ba, hakan yasa na turama Lucky kwatancen gidanshi nace shima a d'aukemunshi idan ya fito zai taho kotu, yanzu haka suna wajen su Lucky nace sujirani a kammala shari'ar kafin a aiwatar masu, dan yanzu idan aka kashe su wata sabuwar shari'ar ce, kaji yanda nayi dashi.
Jinjina kai Alhaji Barau yayi yana fad'in yanzu kam hankali na ya kwanta, abinda ya rage na kira Ra'eez na siyeshi domin yayi watsi da shari'ar.
A'a kada kayi haka Alhaji Barau, na fad'a maka zuciyata bata kwanta da wannan yaron ba, k'wazonshi yayi yawa, basirarsa baiwace daga Allah, kuma nasan bazai tab'a amincewa da cin hancinka ba, dan haka ka barshi kada kayi abinda zaisa ya gane ko kai waye, dole sai yana da shedu sannan zai gabatar da shari'ar, kuma jibi ne za'a kammala komai, dan haka ka barshi, idan yazo ma ka k'arfafa masa guiwa. Alhaji Barau yace shikenan nagode.
Kwankwasa k'ofar da akayi tasa yayi saurin kashe wayar, izinin shigowa ya bada hakan yasa Ra'eez ya shiga. Bayan ya zauna Alhaji Barau yace sannu da kok'ari Ra'eez, gaskiya kana kokari akan wannan shari'ar, shiyasa ma na kaita zuwa alhamis saboda ka samu damar kammala sauran shedun ka, maganar Fawwaz kuma idan har yana da laifi dole a maidoshi.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in nagode Alhaji, nasan ai saboda nine kayi haka kuma naji dad'i. Alhaji Barau yace haba ai bakomai, abinda nakeso da kai ka tsaida hankalin ka ka samo cikakkar hujja dan bana so mutane suga gazawarka musamman da shari'ar take tsohuwa, gara ace kayi nasara zaifi.
Kai Ra'eez ya jinjina yana fad'in insha Allah. Tashi yayi yana fad'in nagode zan tafi. Alhaji Barau yace ka kula da kanka.
**** ****
Kada ka damu Rafeek, wannan abu ne mai sauki, ina tabbatar maka ayau zan kama Fawwaz, nasan Iyayen shi sun killace shi agida suna jira lokacin tafiyarsa yayi sannan su fiddoshi ya tafi, nasan dan wasa yanzu bazamu ganshi ba, amma nasan wanda zansa ya fiddo manishi cikin sauki.
Rafeek yace nagode Hamza, sai maganar su Adnan, tabbas nasan sune sukasa aka kamasu, amma na tura su Brr. Jabeer suje abi mana diddikin layinsu.
Hamza yace bara nakira amintattun ma'aikata na dole wannan aikin yana buk'atar sirri saboda kasan yanzu duniyar babu gaskiya zasu iya siye masu matattar zuciya acikin mu, shiyasa sai amintattuna kad'ai zan d'auka domin na saba fita dasu irin wannan aikin sirrin.
Rafeek yace yanzu waye kake tunanin zai iya fito da Fawwaz? Murmushi Hamza yayi yana fad'in akwai babban abokinsa d'an uwan su Maid'akina ne, nasan yanda zanyi ya fito mana dashi.
Hamdala Rafeek yayi yana fad'in nagode abokina. Hamza yace haba bakomai, insha Allahu komai zai tafi lafiya lau, kuma zan tsaya har sai an tabbatar da gaskiya.
Wayar Rafeek ce tayi k'ara, yana dubawa yaga Jabeer, saurin d'auka yayi. Jabeer yace Yaya gaba d'aya layinsu a waje d'aya ya dena aiki, sai dai kuma alamu sun nuna wajen da yabar aikin waje ne da yayi nuni da b'oyayyan waje dan ba cikin gari bane.
Rafeek yace shikenan ku taho zamu san yanda za'ayi. Hamza yace ya dai? Fad'a masa abinda ya faru yayi. Murmushi Hamza yayi yana fad'in sace su akayi, idan kuma har abinda aka duba gaskiya ne to zamu duba daga inda layin ya tsaya dole suna ata wajen. Rafeek yace nagode. Sallama yayi mashi ya tafi.
**** ****
Dan Allah Sweetheart ki nutsu, idan akabi komai a sannu babu abinda zai faru. Zama Momin su Marwan tayi tana goge idonta, kallon Yaronta tayi tana fad'in wallahi kashe shi zasuyi, kasan kuwa dokar k'asar saudiya? Ni na rasa wannan abu na Marwan, shida yake india bansan ya akayi yaje saudiya ba, duk da nasan yana fad'a mun yana kasuwanci a Madina amma be fad'a mun zeje can ba.
Gyara zama saurayin yayi yana fad'in to dama baki san Marwan yana dillacin kwayoyi ba? Momy tace wallahi ban tab'a sani ba, idan nasani taya zan barshi, dan Allah *Nuress* idan kana da mafita ka fad'a mani.
Murmushi Nuress yayi yana fad'in gashi kuma gobe zan koma, kuma gaskiya ni bani da wanda na sani a Madina, tunda Alhaji zai dawo gobe ki barshi yazo nasan abun zaizo da sauki tunda sune masu k'asar.
Ajiyar zuciya tayi tana jawo wayarta tace bari na turama Khalil kud'i yace mun kud'inshi sunyi k'asa, nima ba kud'in gareni ba tunda duk na kwashe su nayi wannan siyayyar gashi kuma asara ta sameni, jira nake Alhaji ya dawo ya k'ara mani jari dan duka kud'in account d'ina bazasu wuce million goma ba.
Matsowa Nuress yayi yana shafa mata baya yace kada ki damu Baby komai zaizo da sauki, tunda Alhaji ya warke daya dawo kud'inshi zasu dawo.
Murmushi tayi tana kok'arin tura kud'i, tsaf Nuress ya haddace code d'inta. Bayan ta gama ta mik'e tana cire sark'ar zinarinta dan tunda suka dawo daga unguwa bata samu cire kaya ba ta samu wayar an akama Marwan hakan yasa hankalinta ya tashi.
Durowa ta bud'e ta d'auko wani akwati, bud'eshi tayi saiga wasu sarkokin da abun hannu hada zobuna duk na gwal, maida wadda ta cire tayi ta rufe akwatin da mukullinshi ta maida mukullin inda yake.
Koda ta juyo sai taga Nuress ya juya mata baya da alamu baisan abinda takeyi ba dan hankalinshi yana kan waya. Abinda bata sani ba ta cikin wayar yake kallonta.
Sunanshi ta kira hakan yasa ya juyo. Nuress yace Baby kije kiyi wanka naga jikin ki duk yayi sanyi. Murmushi tayi tana fad'in zanyi amma kad'an zo ka sakani nishad'ani sai nayi wankan da hujja. Murmushi yayi yana fad'in yanzu kuwa, ai gara nayi na bankwana tunda anjima zan bar gidanki zuwa gobe na wuce.
**** ****
Wai abokina dan zaka koma waje shine ake kullen ka? Fawwaz yace wallahi ba haka bane, kasan na fad'a maka abinda ya faru lokacin muna sacondary, to ashe munafuki Adnan yaje ya fad'ama Iyayen yaron da nake fad'a maka na yanka da wuka, shine fa aka maido shari'ar babbar kotu, yanzu haka nemana akeyi shi ne fa Dady yace komawa zanyi bazan sake zuwa Nija ba.
Milo yace yana da gaskiya, domin idan ka tsaya nan dole a kama ka, amma haka zaka zauna har lokacin tafiyar ka yayi bazaka d'an shana da budurwarka ba? Fawwaz yace gobe ne fa tafiyar kuma inaji jirgin safe zanbi.
Milo yace gaskiya zanyi kewa, amma ya kamata kazo muje kayi na bankwana. Fawwaz yace gaskiya Dady yace kada naje ko ina, kuma idan na fita dole zai gane.
Milo yace motata bakin glass ne, ka fara fita kashige zan biyoka daga baya kaga babu wanda zai san tare muka fita. Fawwaz yace shikenan, amma dole zaka k'ara mani wannan kayan. Milo yace baka da matsala. Dariya sukayi ya tashi, wayarsa ya aje yana fad'in nan zan barta kada Dady ya kira.
**** ****
Wallaji Oga munyi iya binciken mu bamu samu komai ba, har mun wuce inda wayarsu ta dena aiki amma babu abinda muka samu, kuma bamuga kowa wanda zamu iya zargin wani abu ba, shiyasa muka dawo ko zuwa gobe sai mu canza waje.
Gyara zama Hamza yayi yana fad'in ba sai kun canza waje ba, dole suna nan inda kukaje, ba k'ananan b'arayi bane shiyasa basu bar wata alama da za'a iya ganesu ba, dole sai munsa basira a aikin kafin mu kamosu, dan haka ku barshi sai gobe sannan mu koma.
Sara mashi yayi kafin yayi waje. Wayarsa ya d'auka yana fad'in ina jinka Milo, toshikenan kayi yanda nace dan bana so ya zargeka, gamu nan zuwa kawai ka nuna baka san komai ba. Nagode.
**** ***
Ra'eez tashi muci abinci kaji. Tashi Ra'eez yayi yana dafe kai. Jabeer yace jarumta zakasa aranka insha Allahu komai zaizo da sauki, idan suna tunanin wannan abun da sukayi sunyi nasara to hakan zai jawo masu fitina, domin Allah baya barin azzalumai, idan ka bari damuwa ta kaika k'asa shikenan zasuyi galaba akan mu.
Kallonshi Ra'eez yayi yana fad'in wallahi aikin shari'a ya fitar mun akai, dama can saboda d'aukar fansa na tsaya na karanceshi, amma ina kammala wannan shari'a to zan kammala ta tare da aikina, wallahi Jabeer bazan iya ba, aikin lauya aikine na halaka.
Kada ka sare Ra'eez. Saurin juyowa sukayi jin magana daga bakin k'ofa. Alhaji Mansur ne tsaye yana kallonsu. Duk'ar da kai Ra'eez yayi.
Shigowa yayi yana fad'in wannan fa somin tab'i ne, duk da ma shine mai wahalar domin kafin akai k'arshen shari'ar kowa zaisan matsayinsa, dan haka kadena damuwa yanzu haka Fawwaz yana hannun Inspector Hamza.
Cike da farin ciki Ra'eez ya d'ago kai yana kallonshi. Kai ya jinjina yana fad'in Rafeek ya kirani ya tabbatar mani da haka, kaga komai zaizo da sauki. Jabeer yace amma naji dad'i, sai ka matso muci abincin yanzu.
Murmushi Ra'eez yayi ya matso yana fad'in ko yanzu ma akoma kotu. Dariya Alhaji Mansur yayi yana fad'in banda cika baki fa. Ra'eez yace Allah Abbah naji sauki yanzu, sai dai hankalina yana wajen su Adnan da Abban Nabeel, bana so ta silata su rasa rayukansu.
Alhaji Mansur yace Hamza ya tura amintattun yaranshi, duk da sunje basu samu komai ba amma gobe zasu koma, bazasu tab'a kashe su yanzu ba, nasan zasu jira zuwa jibi kafin nan kuma insha Allahu an kwatosu. Ra'eez yace Allah yasa.
Wayar Alhaji Mansur ce tayi k'ara, yana dubawa yaga Bala bakanike, murmushi yayi yana fad'in ko har an kammal gyaran motar? 'Daga wayar yayi. Bayan sun gaisa Alhaji Mansur yace Bala an kammala ne? Daga can Bala yace wallahi yanzu haka aikin nakeyi, kasan motar ta dad'e a aje dole sai da na fiddo komai dan tayi kura sosai, amma kuma injinta lafiya lau yake, to bayan da na fito da kujerun motar sai na samu wani tsohon flash, shine nace bara na kiraka na fad'a maka.
Alhaji Mansur yace flash kuma? Saurin gyara zama yayi yana fad'in Bala kana ji na ko, ina so ka samu abinda zaka saka mani shi, ka jira ni nan da mintuna zan kira ka, ina so yazo lagos daga nan zuwa gobe. Kashe waya yayi yana fad'in Allah amin.
Ra'eez yace Abbah lafiya? Murmushi yayi yana fad'in Ra'eez gaskiya tana ta kok'arin bayyana kanta, kasan Bala ya tafi da motar Alhaji zai dubata, shine yace mun a k'asan kujera ya tsinci wani tsohon flash, duk yanda akayi ajiyar Marigayi ce, Alhamdulillahi Allah mungode maka, dole nayi waya a samu wanda zai taho lagos ya kawo manashi, badan ma bana so wani abu ya faru ba da ko amotar haya sai a d'oroshi, amma bari nayi waya da abokina shine shugana 'yan Union.
*** ****
Ka kwantar da hankalin ka Mr. Kallah babu abinda zai faru, ina fatan baka fad'ama Alhaji Marusa komai ba dan kaga daga ciwo ya tashi? Mr. Kallah yace ban fad'a masa ba amma dole na damu Alhaji Barau, tsohon sirrin mu da yayi shekara da shekaru fa akeson bankwad'owa taya hankalina zai kwanta.
Alhaji Barau yace kada kamanta fa mune kotu, Alhaji M. Sanda bazai tab'a bari asirinmu ya tonu ba, kai tun daga can sama muna da k'afa taya kake tunanin asirin mu zai tonu, kai dai kawai sai kun dawo goben, ka gaishe mani da 'Yallab'ai Marusa. Dariya sukasa ya kashe wayar.
**** ****
A zabure ta tashi daga kwancen da take ganin sakon daya shigo wayarta, hannu tasa ta murtsike idonta ta d'auka ko bacci takeyi amma tabbas zahiri ne.
Gaba d'aya ta rikice, taya aka amsar mata makudan kud'i har haka, gashi kuma acikin bankin aka amshe su, dole tasan a volk room ne kad'ai za'a iya amsar wad'annan kud'in domin tasan acan take amsar kud'i masu yawa. Suman zaune tayi, wasu hawayen tashin hankali ne suka zubo mata lokacin data kalli balance d'inta, ita da take da kusan million takwas dan d'azu ta turama Khalil kud'i amma yanzu itace take da dubu d'ari biyar.
K'arar sakon daya shigo mata ne yasa tayi saurin dubawa. Ido ta tsura ma sakon tana karantawa a hankali.
*Nasan da ciwo aci amanarka, amma ciwon mai sauki ne idan akayi duba da abinda mutum ya aikata, nasan baki san koni waye ba shiyasa kika fara tarayya dani, ni kuma sanin da nayi maki ne yasa nashigo rayuwar ki, ina fatan hakan zai zama darasi agareki idan kina da sauran Imanin da zaki iya koyon darasin. Nuradden Hambali, 'Dah ga Shehu Hambali Rigacukum zariya, ko ahaka na barki nasan ya isheki ki tuna komai, kinci amanar mahaifina wanda hakan ya jawo ajalinsa, kin wulak'antani akan nazo neman taimakon kud'in da zan kai Mahaifina asibiti, duk da kece silar jefashi halin da yake amma kika tozartani, tun daga ranar na d'auki alk'awarin tozartaki, na tausaya maki shiyasa na rage maki na cefane, kada kiyi tunanin nemana domin zakisha wahala kuma hakan zai kaiki ga mutuwa ma, ki gode Allah daya baki basirar zab'en akwati mai kyau na ajiyar gwalagwalai, na barki lafiya. Ur's Nuress.*
Wurgi tayi da wayar cikin tashin hankali ta bud'e durowa, ihu ta saki ta zube tana wani irin kuka, tabbas Nuress ya gama da ita, bayan da ya mayar da ita tamkar matsarsa, ta siya masa gida da mota, duk hakan be ishe shi ba sai da ya aikata mata cin amana.
Runtse ido tayi a hankali ta furta *Shehu Hambali*
****
Shine saurayinta na farko arayuwarta, tana kaduna yana zariya amma haka yake zuwa wajenta, sunyi soyayya sosai, kasancewarta mai idon cin naira yasa ta tasoshi gaba, shi kuma yana sonta shiyasa baya iya mata gardama, a hankali ta rik'a tatseshi, kafin asa masu rana duk wani abu nashi sai da ta cinye, bayan ansa masu rana akazo had'a lefe tace ga irin wanda takeso, beda kud'i sai gidanshi na gado, dole ta sashi ya raba gidan biyu ya siyar da rabi tace zatayi maleji tasan bayan aure zasuyi kud'i.
Ana saura sati d'aya bikinsu ta had'u da Alhaji Marusa, cikin k'ank'anin lokaci labari ya canza, aranar d'aurin aure Shehu da abokansa suna zaune sukaji an d'aura da wani bashi ba.
A asibiti ya kwana, kwananshi ukku aka sallamoshi, yana zuwa gida ya iske amaryarsa, domin tun acan Kawunsa yasa aka d'aura da diyarshi, ana dawowa kuma aka siya mata komai ta tare.
Yayi kuka har ya gaji, tun daga ranar ya kamu da ciwon zuciya, sau d'aya ya tara da matarsa rabon Nura yashiga, ga talauci, ana haka ya samu labarin inda Karimatu take a Lagos, haka ya wanke kafa yaje, sai dai wulakancin da tayi masa ko kare bazai d'auka ba, tunda ya dawo ya samu littafi ya rubuta tarihinsu, haka yacigaba da rayuwa cikin kunci, duk da matarsa tana kula dashi.
Bayan shekaru Nura ya tasa, tunda ya taso haka ya iske Mahaifinsa babu lafiya, zuwa lokacin basu da komai, ga ciwo, ganin zai mutu suka kaishi asibiti, makudan kud'in aikin da za'a mashi ya tada hankalinsu, haka yazo d'akin Mahaifinsa yana duba takardun gidan ya siyar ayi masa magani.
Littafin daya iske yaja hankalinsa ya karanta. Yayi kuka har ya gaji, a washe gari yaci bashin kud'i ya nufi Lagos, duk da bayanin da yayi mata besa ta tausaya mashi ba, haka ta wulakantashi tasa masu gadi suka masa duka suka wurgoshi waje.
Kafin ya dawo sai zaman makoki ya iske, ta silar haka Mahaifiyarsa ma ziwon zuciya ya kasheta, yasha wahala hakan yasa ya taso da niyar d'aukar fansa. Dole tasa ya siyar da gidan gadonshi yaje ya sayi kaya masu kyau ya koma Lagos da zama.
A hankali ya fara bibiyar Karimatu, wata rana ta fito daga wani Mall suka had'e, shine ya amsar mata kayan ya kai mata mota, tunda ta ganshi ta mace akanshi. Wannan ne silar had'uwarsu, yana sane ya maidata kamar matarsa duk da ba hakan yaso ba, zafin dake ranshi yasa ya biye mata, tayi masa hidima a ciki hada gida da mota, a yau daya kammala aikinsa sai yaji duk wani kunci ya bar zuciyarsa, haka yabar Lagos.
Ajiyar zuciya ta saki mai k'arfin gaske bayan data gama dogon tunani, wato shiyasa Nuress yashigo jikinta har haka kenan, ta aminta dashi hatta da aiken banki shi take turawa ko nawa ne zai karb'o mata kuma be tab'a mata sata ba, ma'aikatan bankin duk sun sanshi dan tace masu k'aninta ne shiyasa da ta aikeshi da check matuk'ar akwai sa hannunta suke bashi kud'i, to ya akayi ma tasa hannu a check d'in? Dole sai idan satar fasaha yayi mata.
Wani sako ne ya sake shigowa wayarta, saurin dubawa tayi... *Nasan zakayi mamakin yanda akayi aka bani kud'i ba tare da sa hannun ki ba, to idan baki sani ba yanda na iya sa hannun ki ko ke bazaki nuna mun iyawa ba, wannan dalilin ne yasa na iya saka hannunki, ada nayi tunanin na cira ta Atm, sai naga bazan ciresu alokaci guda ba, shiyasa na shirya tafiya da rana saboda na samu naje banki, sai kuma naci sa'a aka gama komai na bar bankin kafin kisan anyi, na barki lafiya.*
Wani irin ihu ta saki data tuna abinda yayi mata, da sauri Mai aikinta tashigo, ganin halin da take ciki yasa tayi saurin kiran masu aiki maza, kafin suzo ta sume, dole suka d'auketa zuwa asibitin su.
*** ***
Wai ina Fawwaz yaje ne? Ammi tace tun bayan da abokinsa yazo har ya tafi yana d'aki kwance dan naga lokacin da abokin ya tafi sai dai ban shiga d'akin ba dan nasan baya son takura.
Amma ai nakira wayarsa tana k'ara kuma be d'auka ba, jeki duba mani d'akin, ko kuma muje ma. Turuss sukayi ganin baya d'akin, saurin tura k'ofar band'aki yayi amma baya ciki, hankali tashe ya d'auki wayar Fawwaz yana duba sunan Milo, sai dai babu lambarshi babu alamunta.
Zama yayi zufa tana keto mashi. Ammi tace wai lafiya Alhaji? Kallonta yayi yana fad'in burinki ya cika kin barshi ya fita saboda akamashi dan bakiso yabar k'asar.
Ammi tace mekake fad'a haka, nice zan barshi ya fita? Tomeyayi ma da za'a kamashi? Tsaki yayi yafice daga d'akin.
Wayar Lucky ya kira, yana d'agawa yace Lucky Fawwaz ya fito, inaso ka kokarta ka dawo dashi gida tun kafin aganshi, ka duba gidan hutawarsa kuma ka bincika inda yake zuwa bana so asamu matsala.
Kashe wayar yayi yana huci.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
4⃣3⃣
Haka Alhaji M. Sanda yayi ta zagaye a d'akinshi sam ya kasa kwanciya, duk bayan mintuna sai ya kira Lucky amma amsar d'aya ce ba'a dace ba, dole tasa ya hak'ura ya kwanta ranshi a b'ace.
**** ****
Milo kaga abinda nake fad'a maka ko, nace maka Dady yace kada na fita amma kace na fito gashinan an kama mu, gara kai nasan sakin ka za'ayi ni ko kamani zasuyi zuwa kotu kuma kashe ni za'ayi.
Milo yace yanzu meye amfanin b'oyewar, ko ka tafi idan aka gano kana da laifi ko birnin sin kaje kotu tana da ikon maido ka, shawarar da zan baka kawai kaje ka fad'i iya abinda ka sani zaifi maka.
Hawaye ne suka zubo ma Fawwaz yace yanzu Milo kaine kake bani shawarar naje akashe ni? Dafashi Milo yayi yana fad'in ka fahimce ni abokina, wallahi ban tab'a jin na tsani rayuwar da nakeyi ba sai yanzu, tunda ka bani wannan labarin hankalina ya tashi, ayanzu da ka fad'a mani shari'ar da za'ayi sai nayi nadamar abubuwan dana aikata, kuma insha Allahu daga yau na bar shirmen da nakeyi, shaye-shaye kuwa dole zan barshi domin shine yake samu aikata sauran laifukan.
Kwanciya Fawwaz yayi yasa kuka. Matsowa Milo yayi yana rarrashinsa tare da kwantar masa da hankali.
**** ****
Wajen k'arfe goma motar su Alhaji Marusa ta shigo cikin gidanshi, masu aikin gidan ne suka zo suna masa sannu da zuwa, Mr. Kallah ne ya bud'e mashi mota ya fito tare da sandar da yake dogarawa, duk ya rame sai dai yayi haske.
Har cikin falonshi suka rakashi shida Alhaji Barau dan shine ya d'auko su. Ruwa Mai aikin gidan ta kawo masu, bayan ta aje ta duk'a tana sake gaishe su tana tambayar mai jiki.
Alhaji Marusa yace ina Hajiya fa na kira wayarta akashe? Mai aikin tace ai Hajiya bata da lafiya jiya sai wajen k'arfe d'aya muka dawo daga asibiti dan tace bata son kwana acan shine aka sallameta amma tana can kwance tana cikin ciwo ko magana batayi sai kuka.
Alhaji Marusa yace meya sameta ne? Wallahi ina aiki kawai naji ihunta, kafin nazo na iske ta suma, haka na kira sauran muka kaita asibiti, sai dai lokacin data farfad'o tasa kuka tana fad'in wayyo kud'inta tana kuma kiran sunan Nuress.
Alhaji Marusa yace to Allah ya kyauta, idan na huta na shiga. Da sauri Alhaji Barau yace ba haka za'ayi ba, kana ji fa tace tana ambaton kud'i hada sunan namiji, ke wanene Nuress? Wiki wiki mai aikin tayi da ido.
Alhaji Barau yace magana zakiyi dan musan abinda yake faruwa, domin daga bayanin ki na fara fahimtar bakin zaren gara ma ki fad'i abinda kika sani ko nasa a kulle ki.
Mr. Kallah yace wai Alhaji Barau ina ruwanka, wannan fa maganar cikin gida ce. Alhaji Marusa yace barshi yacigaba nima naji ina son naji komai. Mr. Kallah yace kasan fa ba wata lafiya kake da ita ba meyasa zaka damu kanka.
Alhaji Marusa yace muna jinki. Kai a k'asa ta fad'a masu waye Nuress har zamanshi a gidan bayan tafiyarsu da irin alak'ar da sukeyi da Hajiya, sai dai batasan abinda ya had'asu ba.
Mamaki sosai ya kamasu Alhaji Barau, Alhaji Marusa kuwa murmushi ya saki yana fad'in ashe dai maganganun da ake fad'a mani gaskiya ne nine ban yarda ba, lallai Karimatu kin cika butulu, koda yake dama ai nasan za'a rina dama can butulu ce ita, shikenan tayima kanta domin ni mace bata isa ta sani damuwa ba, abu d'aya ne zan rasa nashiga tashin hankali shine kud'i domin sune nasa araina fiye da komai, ko Marwan da naji yaki tsayawa yayi jinyata banji haushi ba, domin dama can ban sasu araina ba dan nasan zasu iya sani ciwon kai.
Mr. Kallah yace baza'ayi haka ba Alhaji, yakamata kaji abinda ya faru domin ka taimaka mata, muna can fa take fada maka kayanta sun salwanta, kaga kila shima yaron yaudararta yayi.
Tsaki Alhaji Marusa yayi yana fad'in wallahi babu abinda zan mata, kai na saketa ma saki ukku tazo ta barmin gidana bana buk'atar ta ayanzu.
Alhaji Barau zeyi magana sukaji an saki kuka, ganin Hajiya sukayi ta shigo tana takawa da kyar, dama daurewa tayi jin ya dawo tazo tayi masa sannu da zuwa.
Cikin sauri ta shigo tana fad'in Alhaji ka rufa mani asiri, wallahi zan shiga damuwa idan ka rabu dani, duk tarin kud'in da kake bani ban tab'a tunanin siyen kadara ba, abu d'aya nasan ina tarawa sune gwalagwalai, sai kuma kud'ad'e da nake ajewa a banki suma na kwashe su na saro kaya gashi nayi asara, sauran kud'in kuma an sace su da gwalagwalai na, ga Marwan jami'an Madina sun kamashi da kayan kwayoyi yana can dama jiran dawowar ka nakeyi, dan Allah ka rufa mani asiri wallahi sharrin shed'an ne, gaba d'aya Nuress ya takaitani.
Shiru sukayi suna kallonta da jin irin abinda take fad'a. Alhaji Barau yace to a ina za'a samu shi Nuress d'in? Cikin kuka take fad'in nima ga sakon daya rubuto mani nan, ashe d'aukar fansa ce ta kawoshi waje na......
Tsab ta fad'a masu abinda ya faru. Shiru wajen yayi sai sautin kukanta. Alhaji Marusa ne yayi gyaran murya yana fad'in wallahi da zanga wannan yaron sai nayi masa babbar kyauta, wannan yaro shi ake kira da d'an halak, kuma yayi dai-dai, to bari kiji, wallahi babu wanda zai b'ata lokacinsa wajen tayaki nemoshi, kema yanzu ba anjima ba zaki bar mani gidana, suturarki kad'ai zaki d'auka amma ko mota bazaki d'auka ba wallahi, taimako d'aya zansa direba ya kaiki tasha zan baki kud'in mota kitafi, dama bakizo da komai ba.
Ihu tasa tana fad'in Alhaji kodan Yaranmu da suka girma kada kamun haka wallahi zan gyara, idan ma ka sake ni naji ka barni nayi zaman yarana.
Tsaki yayi yana fad'in ni yanzu yaro d'aya nake dashi domin nasan Marwan tashi ta k'are dan saudiya hukuncin kisa suke ma duk wanda suka kama yana siyarda miyagun kaya, ni ko wallahi bazan b'ata kwabo na wajen amsoshi ba, shima Khalil idan ya dawo to, idan kuma ya zauna acan zan cigaba da kula dashi.
Alhaji Barau zeyi magana yayi saurin tashi yana kwalama direba kira, kallonta yayi yana fad'in na baki mintuna ashirin, idan baki shirya ba zaki tafi haka. Jiki na rawa tayi saurin tashi dan tasan halinshi.
Haka taje ta had'a kayanta kusan akwati bakwai, sai kuka takeyi, Nuress ya cuceta, amma tasan alhakin Hambali ne, ashe dama irin wannan rayuwar zata risketa, yau kusan shekaru talatin da wani abu tana cikin jin dad'i amma rana d'aya komai ya tafi, sam bata tab'a tunanin ta gyara gidansu ba, batayi tunanin ta taimaki wani nata ba, asalima bata cika zuwa gida ba, sai tayi shekara bata leka ba, idan taje ma bata wuce kwana biyu, shima har ta baro gidan bata cin komai na gidan, gashi yanzu zata koma can da zama.
Haka ta fito masu aiki suka d'aukar mata kaya sai kuka takeyi. Dubu hamsin Alhaji Marusa ya bata, Mr. Kallah ya ciro tubu talatin ya k'ara mata yana bata hakuri, Alhaji Barau kuwa wajen ya bari yana yamutsa fuska.
Bayan sun tafi Mr. Kallah yace Alhaji ya za'ayi da Marwan? Alhaji Marusa yace Allah yaji k'ansa, yanzu ta Khalil nake kuma kada ku sake tuna mani dashi. Mr. Kallah yace kada kace haka.... Hannu ya d'aga mashi yana fad'in dan Allah.
Kai Mr. Kallah ya jinjina yana fad'in muje ciki kayi wanka ka huta zamu wuce. Hannu ya mik'a masu yana masu godiya. Alhaji Barau yace zan wuce dan tun d'azu Alhaji M. Sanda yamun waya yana nemana sai munyi waya. Godiya yayi masu suka wuce.
**** ****
Ido awaje Alhaji Barau yake kallon Alhaji M. Sanda jin abinda yake fad'a. Hannu yasa ya goge zufar data zubo mashi yana fad'in Lucky d'in yace basu ganshi ba? Alhaji yace har yanzu babu labari.
Gyara zama Alhaji Barau yayi yana fad'in ana wata ga wata, nasan dole su Ra'eez ne zasu sa a d'aukeshi, yanzu ya zamuyi? Alhaji yace nasan Fawwaz bazai tab'a amsa laifinsa ba, kai kuma ina so kayi saurin yanke hukunci da zaran Fawwaz yaki amsa laifinsa shikenan magana ta wuce, domin dole jawabinshi ne kad'ai zai tabbatar da gaskiya, nasan kuma bazai fad'i gaskiya ba, kaga babu Adnan, babu Alhaji Sulaiman, kuma su kad'ai ne suka san gaskiya, kai ko suna nan basu da hujja ahannu iyakarta abaki, kotu kuma da hujjar zahiri take amfani, sannan kuma basu kai su ukku ba.
Ajiyar zuciya Alhaji Barau yayi yana fad'in hakan ma yayi kuma yasa naji sauki, gara ma Fawwaz d'in yaje kotun hakan zaisa kowa ya yarda dashi tunda bazai fad'i gaskiya ba.
Alhaji yace magana ta wuce, anjima zanje na duba Alhaji Marusa, bazan sake damuwa akan a nemoshi ba, mubarshi yaje kotun ba shikenan ba. Alhaji Barau yace haka ne. Sallama yayi mashi ya fita.
**** ****
Rumaisa leka naji ana sallama. Fitowa Rumaisa tayi tana amsawa, cike da mamaki take kallonta. Murmushi Raheena tayi tana fad'in K'anwarmu ko na koma? Murmushi Rumaisa ta saki tana fad'in kishigo mana.
A falo ta zauna, fita tayi ta kawo mata ruwa tana fad'in sannu da zuwa. Raheena tace kin ganni ko azahar ban bari tayi ba, dole tasani fitowa tun d'azu ma naso zuwa naga safiya tayi da yawa shiyasa na daure har shabiyu tayi.
Rumaisa tace amma Yaya besan zaki zo ba ko? Raheena tace shine ma silar zuwana, kwana biyu idan nakirashi baya d'auka, duk da nasan yana kan aiki ne amma ko beje ba ai sai muyi waya ko.
Murmushi Rumaisa tayi tana fad'in sosai kuwa. Mama ce tashigo da sallama, saurin risnawa Raheena tayi tana gaisheta. Amsawa Mama tayi cikin sakin fuska, fita tayi ta basu waje.
Ganin sunyi shiru Rumaisa tace Aunty bara naje na d'ora abincin rana kada na bar Mama da aiki, kiyi kallo kafin na gama. Tashi Raheena tayi tana murmushi tace haba muje muyi aikin tare. Rumaisa tace ki barshi zanyi. Wucewa tayi tana fad'in Allah tare zamuyi. Fita Rumaisa tayi tana mamkin karfin halin Raheena, dole haka suka had'u sukayi aikin, Mama kuwa tausayin Raheenar ma takeji.
**** ****
Shiru sukayi suna jiran fitowar likita daga d'akin gwajin da aka shigar da Ummu, Ra'eez addu'a kawai yake Allah yasa Ummunsa ta samu sauki. Jabeer ne ya dafashi yana fad'in insha Allahu zata samu sauki.
Fitowar likita yasa su saurin tashi. Hannu ya mik'a ma Alhaji Mansur suka gaisa. Kasa hakuri Ra'eez yayi yana fad'in an dace likita? Zama yayi yana murmushi, gaba d'aya suka zauna suna kallonshi.
Takardar da take hannunsa ya kalla yana fad'in da farko zan fara da godema Allah, domin shine mai kwantarwa kuma ya tayar, Alhamdulillahi Allah shine abin godiya, yau kam Allah ya kawo mana saukin al'amauran da suka shige mana gaba, acikin mutane goma da aka d'aukesu a wannan asibitin a shekarar 2008 tare da Hajiya yau Allah ya nufa itama ta samu lafiya kamar yanda biyar daga cikinsu tuni an sallamesu.
Cikin farin ciki Ra'eez ya zube k'asa, goshinsa ya kai yana mai sujudar godiya ga ubangiji. Gaba d'ayansu kallonshi sukayi cike da tausayi. 'Dagowa yayi yaje ya rungume likita yana hawaye.
Alhaji Mansur yace ai babu sauran kuka kuma sai farin ciki, gaskiya nayi matuk'ar farin ciki, likita babu abinda zamuce maka sai godiya kai da Alhaji Usman, hakika kun bada gudummuwa akan Hajiya Bilkisu, Allah ya saka maku da alkhairi.
Zama Ra'eez yayi yana fad'in amin Abbah, wallahi na rasa bakin godiyar ma. Likita yace ai kayi abinda akeso, domin wannan sujadar da kayi ta wadatar, sai kuma aje ayi sadaka.
Jabeer yace wannan kam kullun cikin yinta akeyi, amma dole ta yau ta zama ta musamman. Alhaji Mansur yace ya jikin nata yanzu? Likita yace babu abinda yake damunta yanzu sai rashin kwarin jiki, ina ganin nan da juma'a zaku iya tafiya da ita, dalilin da yasa nace zan riketa anan nafison ku kammala wannan shari'a hankalin ku zaifi kwanciya, kafin nan ta k'ara warwarewa.
Ra'eez yace yanzu zamu iya ganinta? Kai likita ya d'aga yana fad'in kaje ka ganta idonta biyu. Hannun Jabeer yaja sukayi waje da sauri. Murmushi Alhaji Mansur yayi yana fad'in bawan Allah, koba komai yanzu zaiji sanyi a ziciyarshi. Likita yace sosai ma.
A hankali ya tura k'ofar d'akin, Ummu tana kwance tayi saurin tashi tana kallon Ra'eez, cikin sauri yaje ya shige jikinta yana sakin kuka. Rungumeshi tayi itama hawaye suka zubo mata, duk da iya abinda ya faru alokacin da Malan Sani yazo kawai zata iya tunawa amma tasan tabbas wani abu marar dad'i ya faru da Abbun Ra'eez.
Shigowar Alhaji Mansur yasa suka nutsu. Zama yayi yana fad'in Ra'eez kai da zaka kwantar mata da hankali shine zakasa mata kuka. Murmushi yayi yana goge idonshi.
Kallon Ummu yayi yana fad'in sannu Hajiya Bilkisu, Allah ya k'ara lafiya yasa iya wahalar kenan. Murmushi tayi tana amsawa, tana son ta tambayeshi amma kawaici ya hanata.
Kamar yasan abinda take tunani yace abinda nakeso dake kisa aranki kome ya faru muk'addari ne daga Allah, nasan akwai tarin tambayoyi a zuciyar ki, amma ki sani yanzu ne kika warke daga ciwo, kuma ciwonki yana buk'atar natsuwa domin abu ne daya had'a da kwakwalwa, dan haka ki adana tambayoyinki insha Allahu ranar juma'a idan muka koma gida zakiji komai, amma inaso kisa jarumta aranki, sannan ki godema Allah bisa baiwar da yayi maki na baki lafiya da yayi.
Kai ta jinjina tana kok'arin maida kwallar idonta. Tashi yayi yana fad'in bara naje Alhaji Kamal yana jira na, Ra'eez ku dawo gida dawuri saboda an kawo wannan sakon na Kano ina so mu bincikeshi. Kai Ra'eez ya d'aga.
Tashi Jabeer yayi yana fad'in bara na koma wajen aiki kai ka zauna anan. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in nagode. Haka suka fita suka barsu, gyara zama Ra'eez yayi yashiga bama Ummu labarin karatunshi.
**** ****
Yauwa kana ji na ko, kada ka bari su b'ace maka gani nan zuwa, inaso kayi amfani da hankali kasan manyan 'yan fashi ne zasu iya gane kana binsu, shikenan gani nan zuwa.
Cikin mintuna ashirin Hamza ya isa bayan gari, da sauri d'an sandan ya fito daga inda ya b'oye. Hamza yace yauwa sannu Hassan ina ne suka shiga? Hassan yace cikin wancan lungun naga sun shige, sai dai su biyu ne kawai.
Hamza yace kai da sauran ku biyo ta baya, ni kuma zan shiga ta gaba amma kuyi ahankali. Su ukku suka zagaya ta baya yayin da Hamza yawuce ta gaba.
Ruwa suka watsama Adnan wanda yake a sume saboda tsab'ar kishir ruwa da wahalar d'aurin da akayi masa, Abban Nabeel yana d'aure a saman kujera cike da tausayin Adnan, saboda sunfi bashi wahala shi a zaune yake kan kujera yayin da Adnan yake d'aure atsaye, sannan shi Abbah ana bashi abinci da ruwa amma basa bama Adnan.
A firgice Adnan ya farka yana sakin ajiyar zuciya. Abbah yace haba bayin Allah wace irin zuciya ce da ku, idanshi Ogan ku beda d'igon Imani da hasken musulunci ai ku musulmai ne, meyasa zaku biye mashi bazaku bama wannan Yaron ruwa yasha ba, ko babu abinci ai zai iya rayuwa da ruwa.
Dariya d'aya daga cikinsu yasa yana fad'in idan baka sani ba kome mukeyi Oga Lucky yana kallon mu a gidanshi, ko baya zaune yana zuwa zai kunna yaga abinda ya faru, idan ma mun kashe kemarar zai gane, dan haka bazamu b'ata aikin mu ba saboda kud'i muke so.
'Dayan zeyi magana yaji saukar k'asan bindiga akanshi, k'ara ya saki ya zube a sume, rarumar bindiga d'ayan yayi amma Hamza yarigashi kwad'a masa sanda, fad'uwa yayi yana nishi, saurin shigowa su Hassan sukayi, kama su sukayi suka d'aure suka fita dasu.
Saurin kwance Adnan da Abbah Hamza yayi, sai dai tuni Adnan ya faad'i saboda babu kwari ajikinshi. Ruwa Hamza ya d'auko ya kamoshi, saurin amsa yayi ya fara sha, yana gama sha ya fara amai. Abbah yace muyi saurin barin wajen nan domin Ogansu zai iya zuwa dan yana ganin duk abinda akeyi. 'Daukar Adnan Hamza yayi sukayi saurin barin wajen.
**** ****
Ra'eez goge flash d'in kafin ka saka shi nasan yayi kura, Ra'eez yace Jabeer wurgomun gashinan gefen ka, d'aukowa Jabeer yayi yana fad'in bara muga ka iya kwallo.
Murmushi Rafeek yayi yana fad'in duk wanda yayi makaranta ai ya iya buga kwallo sai dai matsoraci. Wurga masa Jabeer yayi yana dariya, hannu Ra'eez yasa zai cab'e sai dai bezo a dai-dai ba sai ya fad'a k'asan gado.
Alhaji Mansur yace lallai Ra'eez beyi kwallo ba. Ra'eez yace Allah mugunta yamun. Jabeer zeyi magana wayar Rafeek tayi k'ara, saurin d'auka yayi ganin Hamza.
Saurin tashi yayi yana fad'in amma mungode Hamza, shikenan kayi yanda kace, bana so akaishi asibiti subi bayanshi, shikenan nagode sai mun had'u goben.
Zama yayi yana fad'in Allah maji rokon bawansa, su Hamza sun samu kama b'arayin da suka sace Adnan da Abban Nabeel, yanzu haka Adnan da Abban suna gidanshi ana bama Adnan taimako dan yaji jiki.
Gaba d'ayan su sukayi hamdala. Alhaji Mansur yace Jabeer kira Nabeel ka fad'a mashi dan hankalinsu ya kwanta, kai ma kira Sameer ka fad'a masa.
Bayan sun kirasu Rafeek yace d'auko flash d'in mu duba. Lek'awa Ra'eez yayi sai yaga ya shige ciki, tasowa yayi yana fad'in sai kazo ka d'aga katifar a d'auko. Murmushi Jabeer yayi yana fad'in Ra go kawai.
Alhaji Mansur yace Rafeek kama masu naga yau shiriritar tasu ta motsa. Tashi Rafeek yayi yana murmushi ya kama mashi suka d'age katifar.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
4⃣4⃣
Bayan ya d'auko flash d'in har za'a maida katifar Ra'eez yace wallahi Abbah mutanan Da akwai su da dabara, tun kwanaki dana d'aga katifar nan naga wata loka a jiki amma ban bud'eta ba.
Da sauri Alhaji Mansur ya taso yana fad'in ina lokar take? Ra'eez yace gata nan ajikin gadon hada mukullinta ajiki da gani babu komai ciki tunda ba'a cire makullin ba.
Saurin lek'awa Alhaji Mansur yayi yana fad'in ku k'ara d'age katifar. Hannu yasa ya bud'e, jawowa yayi saiga ajiyar da Abbu yayi ta flash daya adana sirrikanshi.
Da sauri ya d'auko yana fad'in ikon Allah, lallai yau muna da sa'a, garinya da ka ga lokar baka d'aga ba? Ra'eez yace wallahi lokacin sauri nakeyi shiyasa ban bud'e ba, tun daga lokacin kuma ban sake tunawa da ita ba.
Sakin katifar sukayi gaba d'aya suka zo domin ganin abinda yake ciki. Jabeer yace wanne za'a fara sawa? Alhaji Mansur yace ku fara saka mana wanda aka samu yanzu kamar zamufi samun abinda muke so. Sakawa sukayi gaba d'aya suka natsu.
***
Ajiyar zuciya suka saki lokacin da ya k'are. Hawaye ne suka saukoma Ra'eez a lokacin daya gama jin bayanin Abbunsa, dan daga k'arshe Abbu ya d'auki kanshi yana fad'in wannan sheda ce ta haramtattun kaya da Alhaji Marusa yake shigowa dasu, ko da bana raye ina fatan wannan sheda zata riski adalin Alkali domin a yanke ma masu laifi hukunci dai-dai da abinda sukayi.
Jinjina kai Alhaji Mansur yayi yana fad'in wato wannan shine abinda ya jawo suka kashe Alhaji Maiwada, domin Abubakar ya fad'a mani sun gano abinda Malan Hassan yasa a gidan Alhaji Marusa shine suka kashe shi, jin yace Alhaji Maiwada yaga komai shine dalilin da yasa suka kashe shi suka d'auke kamfutarsa atunaninsu sun b'atar da kowace sheda basu san Allah yafisu ba.
Rafeek yace su hud'u ne manyan cikinsu kuma manyan masu laifi, Adebayo da Umar sune k'ananan masu laifi, sai sauran 'yan dabarsu.
Jabeer yace wato sun had'a kai an kashe Abbu sai suka d'ora Adebayo amatsayinsa, shi kuma Alhaji Barau bayan tsohon Alkali ya sauka sai ya d'orashi amatsayinsa, shi kuma Umar ya hau matsayin Adebayo, haba shiyasa yanzu ake shigo da abinda akaga dama saboda sune keda abun.
Alhaji Mansur yace kunna d'ayan mu gani.......
Bayan ya k'are suka kashe, mayar da flash d'in sukayi cikin jaka. Hamdala sukayi Alhaji Mansur yace shari'a tazo k'arshe, wannan karon mune masu matsayi domin mune masu abun nunawa, Allah sarki Naseer, Allah yaji k'ansa ya kyautata makwancinsa, domin yayi abinda akeso, dan wannan shedar tashi tafi komai muhimmanci, ko ita kad'ai muke da ita basu da hanyar da zasu iya k'aryata zargin da ake masu, ko da kotun da tafi kowace kotu shiririta da rashin iya aiki za'a kai shari'arsu ina mai tabbatar maku dole a yanke masu hukunci, haka zalika ko akwai shugaban k'asa acikinsu k'arewar kud'i da matsayi dole hukunci ya hau kansu, dan haka dole muyi magana da Alhaji Kamal a daren nan kafin gobe.
Rafeek yace gaskiya Naseer yayi jarumta, amma Abbah a shawarata a fara gabatar da shedar Naseer, bayan da kowa yasan masu laifi idan za'ayi shari'ar su sai agabatar data Abbu.
Alhaji Mansur yace wannan haka yake, Ra'eez wannan aikin ka ne, dole ka saka wad'annan shedun a mizanin da kowa zai k'ayatu da shari'ar, dan haka kasa tunani irin naku na lauyoyi ka tafiyar da shari'ar yanda zata k'awatu.
Ra'eez yace insha Allahu Abbah. Tashi yayi yana fad'in Malan Sani komai yazo k'arshe, domin daga gobe ya gama kwanan gidan yari insha Allah, zan kwanta Rafeek ka gaishe da mutanan gidan.
Tashi Rafeek yayi yana fad'in zasuji Abbah, nima tafiya zanyi ina so naje wajen Hamza kafin nawuce. Alhaji Mansur yace ka masa godiya. Sallama yayi masu ya wuce d'akin da yake kwana.
Tashi sukayi suka raka Rafeek, bayan ya tafi suka kulle gidan suka dawo ciki. Wanka Ra'eez yayi kafin ya kwanta, bayan Jabeer ya fito ya kwanta yana kallon Ra'eez da yake waya k'asa-k'asa.
Murmushi yayi ya juya baya yana fad'in gulmamme wayar ma baza'ayi da k'arfi ba. Kyaleshi Ra'eez yayi yana fad'in Pretty kikace Raheena tazo? Rumaisa tace ai naji dad'i da kace bazaka zo cin abincin rana ba Yaya Jabeer yazo ya kai maku asibiti kai da Ummu zakuci, bakaga yanda ta b'ata rai ba, abincin ma kasa ci tayi dole ta tafi.
Murmushi yayi tana fad'in daga gobe ai zata gane dalilin da yasa naki karb'ar soyayyar ta, idan tana da hankali bazata sake nemana ba. Rumaisa tace wallahi na kosa a gama wannan shari'ar mubar garin nan.
Ra'eez yace kinsan gobe Kawu a gida zai kwana fa. Rumaisa tace da gaske? Ra'eez yace insha Allahu, domin a gobe zamu nemi ayi shari'arsa dasu Alhaji Barau.
Rumaisa tace Allah ya tabbatar, aikuwa gobe azumi zanyi. Ra'eez yace muna tare kenan, nima azumin zanyi, kinga zamuyi shan ruwa mai dad'i. Murmushi tayi suka cigaba da firar su.
Bayan daya kashe wayar ya lek'a fuskar Jabeer yana fad'in kayi hak'uri na hanaka bacci abokina. Tsaki Jabeer yayi ya tureshi yana fad'in dalla matsamun marar kunya.
Dariya Ra'eez yasa yana fad'i. Haushi kakeji kai baka da abokiyar fira. Jabeer yace Allah tausayin Raheena nake, ina tunanin yanda zataji idan tasan asalin kalar Mahaifinta. Ra'eez yace hakuri zatayi, shiyasa nace ka aureta hakan zai rage mata zafi, kaga.... Saurin juya masa baya Jabeer yayi ya rufe kunnuwanshi yana fad'in sai da safe. Dariya Ra'eez yasa yana fad'in Allah ya kaimu.
***** *****
*Safiyar alhamis a kotu*
Duk da kasancewar shari'ar ta bama mutane haushi amma hakan be hana suka dawo ba domin suji yanda za'a k'are. A sannu kowa ya shiga kotun suna jiran zuwan Alkali.
Bayan da Alkali yazo kowa ya samu nutsuwa, sai dai Alkali sam baya cikin natsuwarsa, tunda Lucky ya fad'a masa an kama yaranshi kuma an tafi dasu Adnan hankalinsa yake tashe, gashi Lucky yace bazai zauna ba shima guduwa zaiyi, hakan ne yayi masifar tada mashi hankali, dan ko sauran abokansa bai fad'amawa ba dan yasan suna iya barinshi tunda shine ya zamar ma dole yazo kotu.
Magatakarda ne ya tashi ya sake karanto shari'ar da za'a gabatar. Bayan ya zauna Alkali ya d'ago kai yana fad'in Brr. Ra'eez muna jiranka, da fatan wannan karon kazo da cikakkar sheda.
Fitowa Ra'eez yayi yana fad'in nazo dasu ya mai shari'a, kamar yanda kowa ya sani a ranar talata an buk'aci kotu da ta kawo Fawwaz M. Sanda domin ya amsa wasu tambayoyi wad'an da suka shafi wannan shari'ar da akeyi, sai dai bayan da aka je kiransa sai akace baya k'asar wanda na ja da hakan sai aka buk'aci dana tabbatar da shedar yana cikin k'asar nan, alokacin bani da wannan shedar, amma ayanzu ina so kotu ta bani dama domin na gabatar da ita.... Kotu ta baka dama.
Hamza ne yayi ma su Hassan alamu hakan yasa suka fita, ba'a jima ba sai ga Fawwaz sun taso shi agaba duk ya fita hankalinsa, duk da babu wanda ya tab'ashi amma tashin hankali ya hanashi sakat.
Gyara zama Alkali yayi kirjinsa yana dukan ukku-ukku, gaba d'aya zufa ce take zubo masa, amma duk wanda ya kalleshi sai ya d'auka yayi murna da hakan, saboda ba'a gane komai ta fuskarshi.
Bayan da Fawwaz ya shiga ya tsaya sai Ra'eez ya tako kusa dashi.
Ra'eez... Kotu zata so taji cikekken sunan ka.
Sunana Fawwaz Muhammad Sanda.
Ra'eez... Malan Fawwaz ko zaka fad'a mana yaushe ka dawo k'asar nan.
Fawwaz... Zanyi wata d'aya dana dawo.
Ra'eez.... kenan dai baka sake komawa ba? Kai Fawwaz ya d'aga yana fad'in E.
Ra'eez... Malan Fawwaz ko zaka iya fad'a mana sunan makarantar da kayi wato secondary da shekarar da ka gama, da kuma abokan ka wad'an da bazaka iya mantawa ba.
Fawwaz... Kings college nayi, na kammalata a 2008, manyan abokaina kuma guda biyu ne, Sufwan da Adnan, sai dai Sufwan ya rasu.
Ra'eez... A cikin 'yan ajinku ko zaka iya tuna *Farouk Ahmad Ringim*?
Fawwaz... Shiru yayi yana mazurai, can kuma yace gaskiya na mantashi domin shekarun da yawa.
Ra'eez... Naseer Sambo Jarmai fa?
Fawwaz... Nifa mutane biyu kad'ai na iya rik'ewa saboda sune manyan abokai na, sauran kawai ana gaisawa wasu ma ko magana bamayi.
Ra'eez... Murmushi yayi yana fad'in shikenan bara na tuna maka su, Farouk shine abokin fad'an ka lokacin kuna aji shidda, a binciken da nayi hakan ta faru ne silar wata yarinya mai suna Minal wacce ta kasance budurwa a wajen Farouk, bayan ka ganta kaji kana sonta hakan yasa ka nemi daya bar maka ita, shi kuma ya nuna besan haka ba, wannan shine silar rikicin ku dashi, shin ko zaka fad'ama kotu abinda ya faru a ranar da kukayi fad'a na k'arshe wanda Adnan ne ya raba ku?
Fawwaz... Zufa ce ta fara keto mashi, kallon mutanan kotun ya farayi ko zaiga Dadynsa. Runtse ido yayi yana tuna maganar da sukayi da Dady ana gobe za'a saceshi.
*Fawwaz abinda nakeso da kai ka sani, koda Allah yasa dole sai kaje kotu ina so ka tsaya akan maganar da zan fad'a maka, duk yanda za'ayi kada ka sake ka amsa laifinka, domin ita kotu da hujja ukku take amfani, na farko idan aka samu shedu mutum ukku, na biyu idan aka sami hujjar zahiri kamar ace hujja ta vedio, na ukku idan wanda ake zargi ya amsa laifinsa. Ina so ka sani ayanzu Adnan da Alhaji Sulaiman ne kawai suka. san abinda ya faru kaga kuwa su biyu ne, sannan basu da shedar da zasu iya nunawa saboda mun konata, kai ka d'ai ne zaka iya bada k'ofar a kamaka da laifi, dan haka ina so duk yanda Brr. zai maka tambaya ka nuna baka san komai ba.*
Ajiyar zuciya Fawwaz ya saki yana kokarin tattaro jarumta, kallon Ra'eez yayi yana fad'in gaskiya ni bani da wani abokin fad'a a makaranta, duk wanda yasan mu yasan mu ukku ne, bama shiga harkar kowa bare har muyi fad'a da wani, kuma ni bana soyayya a makaranta.
Ra'eez... Jinjina kai yayi yana fad'in shikenan zaka iya tafiya. Ajiyar zuciya Fawwaz ya saki shida Alkali kafin ya koma ya zauna.
Ra'eez... Ya mai shari'ar ina so kotu ta bani dama domin nayima Alhaji Sulaiman tsohon shugaban makarantar kings college tambaya.... Kotu ta baka dama.
Ra'eez.... Kotu zata so taji sunan ka da kuma bayani akan tsohuwar makarantar ka.
Sunana Alhaji Sulaiman, na rik'e matsayin shugaba amakarantar kings college wanda tuni na aje aiki.
Ra'eez... A shekarar 2008 an samu gawar d'aya daga cikin d'alibanka a bayan gari, shin ko zaka iya fad'a ma kotu abinda ka sani.
Alhaji Sulaiman.... Ajiyar zuciya yayi yana jin wata irin kunya, kallon yawan mutanan kotun yayi kafin ya duk'ar da kai yana fad'in da farko ina so na fara neman yafiyar Iyayen Farouk Ahmad, domin na aikata masu laifi mai girma, duk da bani da hannu cikin kisan da akayi masa amma ina da sa hannu a wajen lullub'e gaskiya.
A shekarar 2008 a ranar alhamis da misalin k'arfe 5:15 na yamma, a ranar ina zaune a ofis na samu waya daga Alhaji Muhammad Sanda wato tsohon Alkalin kotun nan wanda ya kasance Mahaifin Fawwaz, bayan mun gaisa yake fad'a mani yana so nayi masa alfarma, idan har nayi masa haka zai bani mak'udan kud'i, to alokacin kunsan zuciya da kwad'ai, jin yawan kud'in da za'a bani yasa na amince da abinda ya fad'a.
Anan yake fad'a mani Yaronshi Fawwaz yayi fad'a da Farouk tsautsayi yasa ya yankeshi da wuk'a har hakan ya jawo ajalinsa, ayanzu haka yana bayan makarantar wajen band'akuna yana so nayi kok'ari kafin kowa yaga gawar a fitar da ita, hakan ne zaisa babu wanda zai zargi komai tunda ba'a makarantar aka ga gawar ba, kuma lokacin tashi yayi.
Duk da na jinjina abun amma tuna yawan kud'in yasa banyi tunanin komai ba kawai na amince, haka naje da mota ta dan bana so nasa wani ya tayani aje a tona asiri, koda aka ganni nayi cikin makaranta babu wanda ya damu acikin masu aiki saboda sun san nine sunyi tunani zagaye nakeyi.
Haka naje na d'auki gawar nasata a mota na bar makarantar, sai da gari yayi duhu kafin naje na wurgar da ita na bar wajen, tabbas zuciyata taji babu dad'i domin na aikata babban laifi, amma tunda na amshi kud'i a hannu sai na manta da komai, tabbas nayi nadamar abinda na aikata, kuma ina neman alfarmar wannan kotu data sassauta mani akan hukuncina.
Ina da ja ya mai shari'a. Brr. Bajinta ne yayi saurin tashi, risnawa yayi yana fad'in ya mai shari'a nine lauyan Alhaji M. Sanda, ina so kotu ta bani dama domin na kareshi abisa sharrin da Alhaji Sulaiman yake son yayi masa.
Ajiyar zuciya Alkali ya saki dan besan Alhaji M. Sanda yayi magana da Brr. Bajinta ba. kai ya jin jina yana fad'in kotu ta baka dama, amma zaka iya jira Brr. Ra'eez ya kammala tambayoyinsa.
Komawa yayi ya zauna yana fatan nasara. Gaba d'aya kotun ta d'auki hayaniya. Bubbuga tebur Alkali yayi kafin akayi shiru. Hannu yasa yana gyara glass d'insa ganin abinda yake faruwa a cikin kotu. Alhaji Kamal ne ya shigo shida wasu mutane guda biyu, hakan yasa wasu daga cikin kotun suka tashi domin su basu wajen zama.
Ajiyar zuciya ya saki yayin da cikinsa ya fara kad'awa, meya kawo Alhaji Kamal kotu kuma bayan shima Alkali ne? Hannu yasa ya d'auki kofin ruwan da yake kusa dashi yasha, gyara zama yayi yana fad'in Brr. Ra'eez kacigaba.
Ra'eez... Murmushi yayi yana fad'in Alhaji ko zaka iya fad'ama kotu dalilin da ya hanaka halartar kotu a ranar talata bayan kuma kace zaka zo?
Alhaji Sulaiman... Tabbas nayi niyar zuwa kotu domin nazo na fad'i gaskiya, kuma aranar na shirya na fito daga gida domin halartar kotu, sai dai ina barin gida wasu mutane suka tare ni, tunda na tsaya suka fiddo ni ban sake sanin abinda yake faruwa ba sai da na farka na ganni a d'aure ni da wani yaro wanda shima yana da alak'a da wannan shari'ar domin shine abokin Fawwaz da yake magana wato Adnan, tun alokacin na gane dalilin kamo mu, an azabtar da Adnan yanzu haka yana can ana masa magani dan cikin ikon Allah 'Yan sanda suka ceto mu yayin da suka samu sa'ar cafke mutane biyu daga cikin b'arayin.
Ra'eez... Mungode Alhaji zaka iya tafiya, ya mai.... Saurin tashi Brr. Bajinta yayi yana fad'in ya mai shari'a ina so kotu ta bani dama domin nayi magana akan abinda Alhaji Sulaiman ya fad'a. Da sauri Alkali yace kotu ta baka dama.
Mamaki ne ya kama mutane, gashi dai Brr. Ra'eez be kammala tambayoyinsa ba amma an bama wani dama. Ra'eez kuwa murmushi yayi ya koma gefe yana kallonshi.
Matsowa Brr. Bajinta yayi yana fad'in Alhaji Sulaiman naji bayanin ka, sai dai kada ka manta kotu tana amfani ne da hujjar zahiri ba ta baki ba, shin ko zaka iya nuna ma kotu hujja akan cewa Alhaji M. Sanda ne ya saka aikata abinda ka fad'a.
Alhaki Sulaiman... Gaskiya bani da wata hujja domin lokaci ne mai tsawo, kuma banyi tunanin d'aukar wata sheda ba saboda nasan bazata mun amfani ba, amma tabbas shine yasani wannan aikin.
Brr. Bajinta... Baka da hujja Alhaji Sulaiman, domin duk wanda yake cikin kotun nan da wanda yasan tsohon Alkali da wanda besanshi ba kowa yasan irin adalcinsa, kuma wannan abun daka fad'a zai iya yuwuwa wasu ne suka biyaka domin kazo ka b'ata masa suna tunda gashi ka kasa gabatar da hujjar abinda ka fad'a, ina rokon wannan kotun da kada tayi amfani da abinda Alhaji Sulaiman ya fad'a. Nagode.
Matsowa Ra'eez yayi yana fad'in Alhaji zaka iya tafiya, ya mai shari'a ina so kotu ta bani dama domin na gabatar da mutanan da suka sace Adnan da Alhaji domin nayi masu tambayoyi.
Dammm gaban Alkali ya fad'i, hannu yasa ya sake d'aukar ruwa yasha, abun goge fuska ya ciro ya goge zufar data sauko masa, da kyar ya sauke ajiyar zuciya yace kotu ta baka dama.
Zuwa yanzu mutane sun fara mamakin Alkali, domin gaba d'aya ya fara rasa nutsuwarshi sai gyaren zama yake ga ruwa da yake yawan sha yana goge fuska.
Bayan da suka tsaya agaban kotu kowa ya natsu yana kallon su.
Ra'eez... Kotu zata so taji sunan ku.
Sunana Gali Haruna... Ni kuma sunana Zubairu Garba.
Ra'eez... Gali ko zaka iya fad'ama kotu dalilin dayasa kuka kamasu Adnan da Alhaji?
Gali... Hakanan muka kamasu domin muna so a bamu kud'i amma babu wanda yasa mu.
Ra'eez... Ai ban tambayeka waya saka ba, kawai dalilin sace su na tambayeka, kenan kaine shugaban ku ko?
Gali gaskiya ba nine shugaba ba bansan inda yake ba dan babu wanda yasan gidanshi a cikin mu iya abinda na sani kenan.
Ra'eez... Zubairu zaka iya fad'ama kotu wanda kuke ma aiki?
Zubairu... Babu wanda muke ma aiki kawai muna neman kud'i ne.
Ra'eez... Shikenan zaku iya tafiya. Ina so kotu ta bani dama domin na gabatar da sheda ta k'arshe.... Kotu ta baka dama.
Jabeer ne ya tashi ya fara had'a kayan da zasu haska domin kowa ya gani. Tunda Alkali ya fahimci abinda suke shirinyi hankalinsa ya tashi, kafin su gama yasha ruwa kusan kofi ukku, sai goge zufa yake yayin da cikinsa yake buk'atar agajin zuwan band'aki, haka ya daure gudun kada ya tona kanshi.
Shiru kotun tayi yayin da kowa ya zuba ido yana jiran a kunna. Hannu Ra'eez yasa ya kunna nan take aka hasko fuskar Fawwaz alokacin da suke fad'a da Farouk. A zabure Fawwaz ya mik'e yana shirin barin kotun, da sauri jami'an tsaro suka cafkoshi, ladabtar dashi sukayi kafin yayi shiru.
Dede lokacin da ya yanki Farouk da wuka da zuwan su Adnan har suka bar wajen. Hannu Ra'eez yasa ya kashe kallon.
Salati akasa gaba d'aya kotun. Wani babban mutum da yake zaune a baya yasa hannu ya goge hawayen da suka zubo masa, tun ranar Talata da yaronshi yaje masa da labarin shari'ar su Farouk yayi alkawarin zuwa domin yaji yanda shari'ar zata kasance danshi ya cire rai da neman adalci a mutuwar Farouk saboda afarko ma beyi niyar neman hakkinsa ba bare kuma yanzu, kawai yazo ne domin yaga wad'an suka tado da wannan shari'ar, sai gashi zuwanshi yayi amfani domin Allah ya nuna mashi wanda ya kashe mashi babban 'Danshi da idonshi.
Bayan kowa yayi shiru Ra'eez yace ya mai shari'a iyakar abinda zan gabatar kenan, ba sai nace wani abu ba, domin nasan adalcin wannan kotun ne, saboda duk abinda zan fad'a idanuwan kowa sun gani, ina fatan wannan kotu zata bima Farouk hakkinsa, sai magana ta gaba akan shari'ar Naseer Sambo Jarmai. Nagode.
Duk yanda Alkali yaso ya daure kasawa yayi domin jikinsa ya jik'e da zufa, gashi cikinsa yariga ya kad'a bazai iya daurewa ba dole sai yaje band'aki.
Cije baki yayi cikin dauriya yace kotu zataje hutun rabin awa, kafin nan kotu tana buk'atar da a killace Fawwaz da sauran masu laifi. Kottt!!!
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:41 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne, Naira 200 kacal, ka tura Mtn card ta wannan lambar.. 08147669770, sai kayi screen shot ka tura ta whatsapp a wannan lambar ta k'asa, idan kuma transfer zakayi sai ka tuntub'e ni ta whatsapp a wannan lambar. 08028525263.*
4⃣5️⃣
A sanyaye mutumin yabi bayan d'ansa suka fita, kai tsaye wajen Ra'eez wanda yake tare dasu Alhaji Mansur suna magana ya nufa.
Sallama yayi tare da mik'a ma Alhaji Mansur hannu suka gaisa. Kallonshi sukayi dan basu fahimceshi ba. Kallon Ra'eez yayi yana fad'in barka dai Brr, nasan baka sanni ba, sunana Alhaji Ahmad Ringim, Asalina d'an kano ne, kuma nine mahaifin marigayi Farouk, agaskiya nayi farin ciki da wannan shari'a, na dad'e da fidda ran nemawa Farouk adalci, sai gashi ranar talata Yaro na yazo mani da maganar shari'ar hakan yasa nace zanzo wajenka domin naji wanda yayi silar tado da shari'ar.
Alhaji Mansur yace Allah sarki, ashe dai wad'an da aka zalunta suna da yawa, sannu Alhaji insha Allahu komai yazo k'arshe, kuma ayau zakaga yanda za'a yanke ma azzalumai hukunci, muje can mu zauna na fad'a maka yanda akayi.
****
K'arar burkin mota yasa mutane suka maida hankalinsu inda ya fito, tsayawa sukayi suna kallon Alhaji M. Sanda ganin ya fito daga mota tamkar wanda aka wurgo, ganin yanda mutane suke kallonshi yasa yayi kok'arin dai-daita kanshi.
'Yan jarida ne sukayo kanshi hakan yasa yayi saurin shigewa kafin su k'araso, dole tasa suka hakura kowa yana jiran d'aukar rahoto.
Alhaji Barau ne ya fito yana sharce zufa yana kok'arin d'aure wandonshi. Cak ya tsaya yana kallon Alhaji M. Sanda yayin da gabanshi yayi wani irin fad'uwa.
Jiki a sanyaye ya samu waje ya zauna yana kokarin shan ruwa, sai da ya gama sha kafin ya goge fuskarshi yana fad'in Alhaji sannu da zuwa.
Ajiyar zuciya ya saki yana fad'in Alhaji Barau me nake shirin ji haka? Brr. Bajinta ya kirani ya fad'a mani halin da ake ciki, duk yanda naso abun ya kasance amma naji ana niyar kai bango, a jiya na shiryama Brr. Bajinta duk yanda zaiyi sai gashi yana fad'a mani wai an kawo irin shedar da muka k'ona a wayar wannan yaron, Alhaji Barau lokacin mu fa yayi, inaji ajikina bamu da sauran mafita matuk'ar aka samu d'ayar shedar da yaron ya d'auka.
Ajiyar zuciya Alhaji Barau ya sauke yana fad'in wallahi Alhaji kaina ya d'aure, yanzu haka saura mintuna a koma kowa yana jiran ayanke hukunci, babban abinda yafi d'aga mani hankali ganin Alhaji Kamal tare da wasu mutane wad'an da nake kyautata zaton daga chamber suke, kasan kuwa abinda yasa Alhaji Kamal ya iya baro ofishinsa kasan babban dalili ne.
Gyara zama Alhaji M. Sanda yayi hankali tashe yace ba dai an kai maganar sama ba? Alhaji Barau yace wallahi bansani ba, amma idan zaka tuna Alhaji Kamal shine Baristan Alhaji Maiwada, sannan acikin wannan vedion da muka kona ta wayar Naseer akwai maganar da mukayi ta yanda za'a kashe Alhaji Maiwada, gaskiya jikina yayi sanyi.
Ajiyar zuciya Alhaji M. Sanda ya sauke yana fad'in su Alhaji Marusa sun san da wannan maganar? Alhaji Barau yace babu wanda na fad'amawa, sun san dai maganar shari'ar Fawwaz kuma na fad'a masu komai zaiyi dai-dai tunda an kama su Alhaji Sulaiman.
Kallon agogo yayi yana fad'in yanzu dai lokaci ya tafi, abinda nakeso da kai kada ka yanke ma Fawwaz hukuncin kisa. Saurin kallo shi yayi. Kai ya jinjina yana fad'in nasan lokacin da yayi kisan shekarunsa sun kai ya amshi hukunci saboda alokacin zeyi shekara 18, kaga kuwa hukunci ya hau kanshi, amma za'a iya juya abun, kace shekarunsa 14 kawai ya shiga makaranta ne da wuri, kaga hukuncinsa bazaiyi dede dana baligin mutum ba, idan kayi mani haka zanji dad'i.
Alhaji Barau yace abu d'aya zakayi, sai dai ka b'oye takardar shedar haihuwarsa hakan ne zesa kowa ya yarda. Ajiyar zuciya ya saki yana fad'in babu damuwa dan bazasu tab'a gano inda take ba, kawai kayi yanda nace, su Alhaji Marusa kuma ka barsu a kammala wannan shari'ar sannan.
Kai ya jinjina yana fad'in bara na koma lokaci yayi. Alhaji M. Sanda yace zan zauna anan bazan iya fita ba, kome kenan idan kowa yashige zan fice dan bana son had'uwa da 'yan jarida.
***
Hannu Alhaji Ahmad yasa ya goge hawayen da suka zubo masa, sosai ya jinjina rashin imani irin nasu Alhaji Barau. Kallon su yayi yana fad'in wannan shi ake cema Allura ta tono galma, lallai wannan shari'ar abun so ce, domin d'aya bayan d'aya za'a warware komai, nagode sosai Alhaji Allah ya biyaku da alkhairinsa.
Alhaji Mansur yace amin, ku tashi mu koma gashi can ana shiga. Tashi sukayi suka wuce. Rafeek ne ya fito daga mota, Jabeer yace yauwa gashinan ma ya dawo. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in kasan abinda nake tunani kenan hakan yasa kaji nayi shiru tun d'azu. Jabeer yace ai tunda Abban Nabeel yace za'a samu nasan za'a samu.
Mik'a mashi takardar Rafeek yayi yana fad'in sai da naje na tayasu kafin Allah yasa aka binciko file d'in, ai gaskiya Allah na sammu. Amsa yayi yana fad'in sannu Yaya. Murmushi yayi yace yauwa.
Sameer ne da Nabeel suka k'araso wajensu, gaisawa sukayi suna tambayarsu Adnan da jiki. Sameer yace da sauki dan ya farfad'o, muna ta sauri kada a kammala ashema yanzu za'a koma. Jabeer yace muje gashi can Babban Alkali ya shiga. Dariya sukasa kafin suka wuce.
***
Tsit kotun tayi kowa yana jiran hukuncin Alkali. Bayan daya gama rubuce-rubucenshi ya d'ago yana fad'in kotu taji duka bayanin da aka gabatar mata, bisa manyan hujjojin da aka gabatar ma wannan kotu ta gamsu da cewa Fawwaz Muhammad Sanda shine ya kashe Farouk Ahmad, wanda yayi amfani da wuk'a wajen kashe shi.
Sai dai anan kotu zatayi duba da abubuwa guda biyu, na farko kotu zatayi duba da yanayin shekarun Fawwaz alokacin da yayi kisan kafin ta yanke masa hukunci, na biyu kotu zata kalli yanayin yanda akayi kisan, domin kisa kala-kala ne, akwai kisan da akeyinsa da niya, akwai kuma kisan tsautsayi.
Idan akayi duba da yanayin yanda Fawwaz yayi wannan kisan zamuga cewar zuciya ce ta d'ebeshi, domin ba daga zuwanshi ya yankeshi da wuk'a ba, sai da suka fara kokowa kafin tsautsayi ya ratsa har ya yankeshi da wuk'a, sai na biyu, wannan kisan anyishi a shekarar 2008, alokacin Fawwaz yana da shekara 14, idan akayi duba da yanayin shekarunsa zamu ga cewar be kai shekarun girma ba, domin Mahaifinsa ya tabbatar ma kotu an sakashi makaranta da wuri shiyasa ya kammala ta a k'ananun shekaru, dan gaka kotu zata zartar da hukunci.
Saurin tashi Ra'eez yayi yana fad'in ya mai shari'a ina neman alfarma, inaso kotu ta bani dama domin akwai abinda zan gabatar ma kotu. Langwab'ar da kai Alkali yayi alamun k'osawa da maganganun Ra'eez, ganin kallon da ake masa yasa yayi saurin amincewa.
Murmushi Ra'eez yayi ya fito yana fad'in ya mai shari'a wannan takarda ce ta haihuwar Fawwaz wadda aka samo a cikin file d'insa na makarantar daya kammala secondary d'insa, idan akayi duba da wannan takardar haihuwar za'aga cewar alokacin da Fawwaz yake aji shidda yana da shekaru 18 ne, hakan kuma yayi dai-dai da lokacin daya kashe Farouk, abisa tsarin addinin musulunci duk namiji mai wannan shekarun ya isa ya d'auki hukunci domin yashiga shekarun baligi, sannan kuma ba a wajen da sukayi fad'an ya samu wuk'ar ba, dama can yazo da ita, kunga kenan dama yazo da niyar kashe shi, zamu iya cewa wannan kisa bana ganganci bane, kisa ne da aka shiryashi kafin ayi, bisa wannan hujjar nake so kotu tayi amfani da ita wajen yanke ma Fawwaz hukunci dai-dai da laifinsa. Nagode.
Mik'ama Magatakarda yayi shi kuma ya mik'ama Alkali. Jiki a sanyaye ya amshi takardar yana dubawa. Tabbas takardar haihuwar Fawwaz ce, kuma duk wanda ya ganta zai tabbatar cewar bata k'arya bace.
Ajiyar zuciya ya sauke, shikenan babu sauran wata hanya domin duk wasu shedu sun tabbata dole ayanke ma Fawwaz hukunci. Kallon gefen dasu Alhaji Kamal suke zaune yayi, ganin shi kad'ai suke kallo dole tasa yayi gyaran murya yana fad'in kotu ta gamsu da wannan shedar, dan haka zata yanke hukunci.
Abisa hujjojin da aka gabatar ma kotu kwarara, wanda suka tabbatar da Fawwaz shine wanda ya kashe Farouk, abisa kundin tsarin mulki na k'asa, sashen kisa, amfani da makami ko wani abu, wannan kotu mai albarka ta yanke ma Fawwaz M. Sanda hukuncin d'aurin rai da rai agidan yari, sannan Iyayen shi zasu biya diyyar Farouk ga mahaifansa idan sun buk'aci hakan.
Sannan kotu ta yanke ma Alhaji Sulaiman da Alhaji M. Sanda hukuncin d'aurin wata ukku a gidan yari ko kuma tarar naira dubu d'ari biyu saboda an kamasu da laifin taimakawa wajen b'oye gaskiya.
Mutanan da aka gabatar ma kotu cewar sun kama su Alhaji Sulaiman kotu bata gamsu da hujjar da aka gabatar mata akansu ba, dan haka take umartar da a koma a sake bincikensu a tabbatar da hujja kafin a sake kawo su.
Annan kotu ta kawo k'arshen wannan hukunci, zaku iya d'aukaka k'ara nan da wata ukku idan kuna buk'atar hakan.
Ihu Fawwaz yasa yana kuka yana kiran Dady, saurin rik'eshi akayi aka fita dashi. Tashi Ra'eez yayi yana fad'in ya mai shari'a sai shari'a ta gaba akan Naseer Sambo Jarmai.
Runtse ido Alkali yayi ya bud'e yana fad'in kotu ta d'age sauraron wannan shari'ar zuwa ranar litinin idan Allah ya kaimu. Kottt!!!
Gaba d'aya mutane suka tashi kowa yana fad'in shari'a tayi, haka kowa ya jinjina ma Ra'eez, sannan sun k'ara jinjina adalci irin na Alkali.
Alhaji Barau kuwa ta kofar kotun yayi saurin ficewa dan yasan 'yan jarida zasu iya rutsashi.
Suna fita Nabeel yaja Abbansa zuwa mota dan yasan 'yan jarida suna iya rufeshi da tambaya, ayanda yaga jikinsa yayi sanyi yasan dole yana buk'atar hutu, hakan yasa yasashi mota suka bar kotun, ko su Ra'eez sai dai yayi masu waya.
Brr. Ra'eez wane irin farin ciki kake ciki da Allah ya baka sa'a kayi nasara a wannan shari'ar? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in ina mai cike da farin ciki domin yau Allah yasa Iyayen Farouk sunga yanda aka yankema wanda yayi silar mutuwar d'ansu hukunci, duk da shari'a ce tsohuwa amma yau Allah yasa an kammala ta, har Allah yasa a cikinta an samo wata hanya da zata kaimu ga samo gaskiyar wata shari'ar.
Brr. Ra'eez ya kake gani akan shari'ar da za'ayi ranar litinin? Insha Allahu itama muna saran nasara. Nagode. Saurin wucewa yayi dan a matuk'ar gajiye yake.
****
Wai Alhaji wane hali ake ciki naga tunda ka dawo kotu wajen Alhaji Barau kake kwance anan baka sake cewa komai ba. Ajiyar zuciya Alhaji M. Sanda ya sauke yana fad'in ko dai muyi nasara ko kuma suyi nasara, yanzu haka an tabbatar cewa Fawwaz shine ya kashe Farouk.
A zabure Ammi ta mik'e tana dafe kirji idanuwanta awaje, kallon Alhaji tayi tana fad'in amma ba haka kuka fad'a mani ba. Runtse idanuwanshi yayi ya bud'e, sosai sukayi ja. Kallonta yayi yana fad'in ban d'auka abun zai kai haka ba shiyasa na b'oye maki, amma yanzu dole kiji komai.....
Kuka kawai Ammi takeyi da tagama jin abinda ya faru, kallon Alhaji tayi tana fad'in yanzu shima kashe shi zasuyi? Garinya saboda b'oye laifin Fawwaz zaku kashe wani, haba Alhaji.
Saurin tashi zaune yayi yana fad'in saboda irin haka yasa na b'oye maki, ki sani zan iya yin komai domin farin cikin Fawwaz, dan haka ban fad'a maki dan kiyi mani wa'azi ba, na fad'a maki ne dan naga babu amfanin b'oyewar. Tashi yayi ya shige d'aki.
Zubewa Ammi tayi hawayen bakin ciki yana zubo mata, ashe dama Alhaji zai iya kisan kai akan son da yake ma Fawwaz? Lallai biri yayi kama da mutum, gashinan Fawwaz yayi kisa an kamashi, idan bincike ya tsananta shima dole akamashi, lallai wannan shine abun kunya Uba da 'Dah sunyi kisan kai.
Yana shiga d'aki wayarsa tayi k'ara, saurin d'auka yayi ganin Brr. Bajinta........
Salati kawai Alhaji M. Sanda yake bayan da ya gama jin yanda shari'ar ta kasance, zubewa yayi saman gado jikinsa yana rawa, a sanyaye yace yanzu shikenan an tafi dashi? Brr. Bajinta yace wallahi dole ne tasa Alkali ya yanke wannan hukuncin, domin idon mutane suna kanshi, ga bak'i da nagani a kotun, Alhaji sai dai hakuri kawai, idan kuma zaka d'aukaka k'ara shikenan.
Jinjina kai yayi yana fad'in shikenan, amma bazan iya zaman gidan yari kona wuni d'aya bane bare har wata ukku, kawai zan biya tara nagode. Kashe wayar yayi ya fara neman Alhaji Barau, tsaki yayi jin wayar a kashe. Hannu yasa ya dafe kanshi yana jin d'akin yana juya masa, tabbas idan har suka bari aka gabatar da shari'ar Naseer asirin su zai tonu, tunda har suka iya gabatar da wannan vedion dole suna tare da d'ayar. Kwanciya yayi hawayen bakin ciki suka zubo mashi.
**** ***
Sannu da zuwa Alhaji bansan ka dawo ba sai da Raheena take fad'a mun kana kwance a falo taga kamar baka jin dad'i. Tashi zaune yayi yana fad'in Hajiya ina cikin tashin hankali kawai kitayani da addu'a.
Zama tayi tana fad'in menene ya faru kuma? Hukuncin kisa ya tabbata akan Fawwaz, domin an tabbatar da shine yayi kisan da nake fad'a maki, yanzu haka na yanke masa hukuncin d'aurin rai da rai agidan yari, wallahi kunyar Alhaji M. Sanda nakeyi shiyasa ma na kashe wayata domin shima hukunci ya hau kanshi.
Jinjina kai Momy tayi tana fad'in gaskiya akwai tausayi, amma kadena damuwa, shima fa tsohon Alkali ne, waya san yawan mutanan daya yanke ma hukuncin kisa, wasu ma ratayesu akeyi wasu a jefesu wasu kuma a harbesu, damme zaka damu kanka kamar ka aikata wani babban laifi, abune a fili, dole sai da kowa yaga hujja kafin ka yanke hukunci, kuma ma wannan hukuncin arabuce yake, kana tunanin da ace shine a matsayinka akace d'anka yayi kisa zaice kai abokinsa ne bazai yanke masa hukunci ba? Kada kamanta nasan awajen hada 'Yan Jarida, da ace baka yanke hukuncin daya dace ba ina mai tabbatar maka da yanzu ka amsa kira daga sama, dan haka ka kwantar da hankalin ka bana so wani abu ya same ka, Allah ya basu hak'urin rashinsa.
Murmushin takaici yayi yana kallon Momy, batasan sirrin da yake k'asa ba da bata fad'i haka ba, amma zai bita ahakan dan baya so ya tashi hankalinsu. Jinjina kai yayi yana fad'in nagode Hajiya, muje ki had'a mun ruwan wanka.
*** ***
Ai na d'auka bazai iya yanke ma Fawwaz hukunci ba, domin naga lokacin da Alhaji M. Sanda yazo wajenshi lokacin da aka fito hutun rabin awa, na tabbata alokacin ya shirya masa abinda ya fad'a.
Ra'eez yace ai Abbah shiyasa muka dage sai da aka binciko mana takardar haihuwarsa, domin nasan irin haka zata iya kasancewa, ajiya Yaya yayi magana da Abban Nabeel, shine yayi mana jagora domin samo takardar, duk da ansha wuya saboda shekarun da yawa, amma kasancewar ana adana duk wasu takardu na 'yan makarantar yasa aka sameta.
Alhaji Kamal yace dole a gobe zanje Abuja domin ranar litinin za'a k'aro mutane, kafin nan dole asa masu ido gudun karsu gudu, hatta shi shugaban Kwastam d'in da mataimakinsa duk asa masu ido saboda suma sai an hukuntasu.
Alhaji Mansur yace ai naso ya tsaya yayi shari'ar Naseer da ayau sai dai suyi kwanan takura dan dole a akamasu, amma bakomai Allah ya kaimu litinin d'in.
Alhaji Kamal yace amin. Wato abinda ya bani mamaki da kace mani an samu flash d'in a motar Alhaji Maiwada, abun tambaya nan shin dama Naseer ya kai mashi flash d'in ne ko kuma ya akayi?
Alhaji Mansur yace kasan a labarin da Malan Sani ya bamu, a daren da za'a kashe Naseer da Alhaji Maiwada sun had'u da Naseer yana kokarin shiga wajen aikinsu da gudu har suka kusa tureshi, anan ya tsaidasu yace biyoshi akayi, hakan yasa suka taimaka mashi, dalilin da yasa Malan Sani yace wannan yaron shine Naseer saboda ya fad'a masu sunanshi, kuma da suna maganar kisan Farouk da akayi sai Naseer yace masu abokinsa ne, kaji dalilin da yasa Malan Sani yace wannan yaron shine Naseer, kuma da aka samu flash d'in a motar na fad'ama Malan Sani sai yace tabbas aranar da suka d'auki Naseer a kujerar baya ya zauna saboda Alhaji Maiwada baya zama baya.
Alhaji Kamal yace bara mugani idan zan iya had'a kan labarin..... A hasashe na, bayan da Naseer yaje gidan su Fawwaz sai ya iske su Alhaji Marusa suna tattaunawa akan kashe Alhaji Maiwada, bayan daya gano shugaban kwastam suke nufi shine dalilin da yasa Naseer ya nufi ofishin su domin ya bashi wannan d'auka da yayi, kafin ya kai sai aka tura mashi mutane kamar yanda Adnan ya baku labari yaji ance aje a kashe shi har an anshi hotonshi, ganin an biyoshi sai tsoro ya kamashi, bayan da suka taimaka mashi sai yayi tunanin kada ya bada flash d'in a inda be kamata ba domin kaga ai dare ne bazaiyuwu ya iya gane Alhaji Maiwada ba, bayan da suka ajeshi sai yaga dacewar ya b'oye flash d'in a motarsu saboda ya tsorata kada abiyo bayanshi bayan tafiyarsu, ina ganin wannan shine dalilin samuwar flash a motar Alhaji Maiwada.
Jinjina Alhaji Mansur yayi mashi yana fad'in aiki ga mai k'areka, wani abun sai ku tsofaffin lauyoyi, wannan hasashen naka tamkar kana wajen akayi, domin ya tafi dai-dai, tabbas babu ja hakan ce zata kasance, kuma ba kowa bane yasa hakan ta kasance sai Allah, domin ya riga daya tsara komai, kuma Alhamdulillahi gashi nan yau yayi mana rana.
Alhaji Kamal yace Allah yajik'ansu da rahma, mu kuma yasa mucika da imani kuma yasa a kammala wannn shari'ar lafiya, amma fa Alhaji sai kace ma su Ra'eez su kula, domin ayanzu suna gab'ar rikici domin zasu faraucesu tamkar tsohon zakin daya shekara babu abinci, abinda nake gani kada Ra'eez ya aje wannan flash d'in a wajenshi.
Hannu Alhaji Mansur yasa ya ciroshi yana fad'in Alhaji ina ganin ka tafi dashi wajenka hakan zaifi, duk da mun rarraba shi a wayoyin mu amma nafison a k'ara samun wani awajen ka.
Alhaji Kamal yace shikenan Allah ya bamu ikon tabbatar dashi, ya kuma kare kowa daga sharrinsu. Alhaji Mansur yace amin ya Allah.
*** ***
Daga duba Adnan wajen Ummu suka wuce, ganin yanda jikinta yayi sauki yasa Ra'eez yace abarshi su tafi da ita, Alhaji Mansur ya kira ya fad'a mawa hakan yasa yace su taho da ita. Sosai sukayima matar da take kula da ita alkhairi da godiya, haka sukabi duk 'yan wajen da akhairi, har bakin mota likita ya rakosu suka tafi cike da murna.
Gaba d'aya gidan ya hargitse da murna, Maman Labiba da Mama sun saka Ummu a tsakiya kamar zasu goyata, bayan koke-koke suka zauna akaci abinci, aranar kamar ana biki haka gidan ya kasance.
Madu kasa zaman waje yayi haka yashigo ciki akayi murnar dashi. Suna zaune saiga Ladi dan Madu ya aika yaro ya fad'a mata, zama tayi tana ta farin cikin samun lafiyar Uwar d'akinta.
Gaba d'aya sai abun ya dawo ma Ummu sabo, sosai tayi kuka. Bayan da suka dawo sallar isha'i suka zauna a falo Ummu tayi wanka tasa kaya sai ta fito tamkar ba itace tayi hauka ba, sosai tayi kyau, sai dai har yanzu akwai damuwa a fuskarta, duk ta kosa a fad'a mata abinda ya faru.
Gyara zama Alhaji Mansur yayi yana fad'in Bilkisu inaso ki bani aron hankalinki, na lura idan ba'a sanar dake abubuwan da suka faru ba bazaki tab'a samun nutsuwa ba amma ki dubi girman Allah kada kiyi abinda zai dawo da ciwonki, nasan dai zuwa yanzu kinsan cewar Allah ya amshi Alhaji Maiwada, sai dai bakisan sauran abubuwan ba, dan haka yanzu zan sanar da ke komai......
0 comments:
Post a Comment