Afia kuwa tana Isa sashensu a palo ta tadda NURU da farhat na zaune Kamar ko yaushe farhat na jikin NURUn suna kallon cartoon din SpongeBob ta tsaya cak tana kallonsu hawaye nason ciko idanuwanta Amma ta danne sbd tanajin zuciyarta na karyewa na abinda tayi din sbd ta Kara NURU Dan biyan buqatarta Wanda idan daga baya bayan sun koma akaji auren NURU da Imran za'a iya daukan hakan amatsayin cin amanar MALEEK datayi tunda yanzu Anneti taji cewar MALEEK zata aura..
Cikin yanayi na sanyi NURU ta dago Jin mutum a tsaye akansu ta kalleta da idanuwanta dasukai laushi sbd ciwon Kai datake ji kadan kadan ta bude baki ahankali tace da sanyin murya tace"
Afia lafiyanki k.....Bata qarasa maganar taba afian ta qaraso hawayen cikin idanuwanta na gangaro ta rungume NURUn tana rintse ido batareda tace komaiba.
Shiru NURUn tayi itama dukkanin jikinta na sake yin sanyi Jin saukan hawayen afia akan bayanta dake bayyane ta cikin doguwar riga Mara hannu.
Sun Jima ahaka kafin NURUn ta dago afia tana kallon idanuwanta dasukai jajir ta saki wani sanyayyan numfashi tace"
Menene yafaru??
Kasa kallonta afia tayi ta juyar da Kai gefe tana hawayen cikin idon suka sake gangarowa kafin ta dago ta zubawa NURU idanuwanta cikin sanyin murya da nadama tace"
NURU idan Baki saniba ayau inason kisani ke din wata babbar bangarene na rayuwata nida farhat,
Ina Jin araina tamkar yanda nakejin farhat sbd na dade da Baki matsayi na 'yar uwar uwa daya uba daya,
NURU wlh kisani duk duniya banajin zanyi Abu Dan kawo cutatarwa gareki Dan haka nake roqonki dakimun uzuri karki zargeni da komai idan har kikaji wata magana ta bullo Miki daga Anneti duk da nasan sirrine da bazata futarba ita kanta saidai koma yayane Ina roqon alfarmarki da kadakice komai duk tsanani kada kifada komai duk abinda akace kice eh sbd hakan shine zai bani lokacin kawo gyara tsakanin dad da mum Dina Wanda kinfi kowa sanin wannan shine burina a duniya and you promise to support me akan hakan right??
Tsit NURU tayi tana kallon afia din kaman wata sokuwa sbd ita anan Bata gane komaiba sbd zancen duk a baibai yake bayan hakan ita menene nata wane matsayi take dashi da afia zatace tashigo cikin zancen komai akace tace eh,to menene zata cewa eh din??
NURU Zaki taimakemu mu dawo da mahaifiyarmu nida farhat??
Cikin tsoro da mamakin shiga huruminda ba nataba ta kalli afian da idanuwanta sukai jajir ta gyada Kai ahankali batareda ta iya bude Baki tayi maganaba sbd Jin abin take yayi Mata nauyi kaman bazata iyaba sbd Jin kamar ba zancenda zata shiga bane.
Zamewa tayi gefen NURUn data shiga tunani haka kawai ta kwanta tareda Dora kanta kan jikin farhat dake jikin NURUn itakuma da hakan duk su duka biyun suka shiga tunani.
****
Tsaf kaleeb yaga sauraron saqo me girma da jekadi tazo dashi idanuwansa nakan makekiyar TVn data kusa cike Rabin bangon palonsa zaka dauka baya sauraronta Amma tsaf yagama Jin komai ya jinjina Kai Yana sake juya zancen cikin ransa da tunaninsa.
Jekadi menene halaye munana da kyawawa na NURULHUDA??
Ya qarfin nutsuwarta da biyayyarta?
Ya qarfi da girman son duniyarta take?
Sake zubewa qasa jekadi tayi cikin girma da tabbacin abinda zata fada Kai tsaye tace"
Allah ya qarawa Kaleeb Nisan kwana da lafiya.
NURU negestati ce wadda zance komai nata da yardar Allah yayi abisaga tsarin da kake son Matar MALEEK ta kasance,
NURU jikace Kuma 'yar asalin amintaccin bayinka da kakanta da mahaifinta,
NURU baiwace me biyayya tareda da'a wadda takaita ga samun ribar zaman rayuwa,
Anneti ce da kanta tayi zabin NURU tazaman Matar aure ga MALEEK wadda zan bada rayuwata akan Anneti Bata yanke komai akan garaje Wanda wannan halin na zurfi da tsaftataccen tunanin daukarsa tayi daga cikin halayen girmanka da adalcinka ya kaleeb.
Jinjina Kai yakuma Yi tareda kallonta wannan karon ya bude Baki cikin gamsuwa da zallar cikar ikonsa yace"
Ahada dukiyar neman auren MALEEK UBAYD zuwaga mahaifinta tareda saqon 'yantawa ga dukkanin zuriarsu tareda tukuicin zuwa gizah ga dukkanin ahalin Dan halartar auren 'yarsu.
Sake zubewa jekadi tayi tana miqa tsagwaron godia da kirari tareda fatan nasara da tarin aduoi ga wannan aure harta fice tanayi cikin tsananin farin take da wannan aure sbd har cikin ranta Allah yasanya Mata kaunar NURU take Kuma fatar cigabanta Wanda tun zuwanta ta yaba takuma Yi tunanin kyawu da halaye na gari irin na NURU matuqar ta zama negestatin MALEEK to ko Bai auretaba wata Rana to tabbas saita zamana negestatinsa datafi matansa daraja a zuciyarsa saigashi abin yazo alokacinda Babu zato ba tsammani Dan haka ko minti biyu Bata qaraba aka fitarda saqon kaleeb take aka fara hada dibbin dukiya da tarin zinarai masu nauyi da daukar ido Wanda yasa take maganar ta fito filin Allah zancen auren ya bazu Kamar wutar daji wasu Basu tabbatarba Saida aka Kai dukiyar gidansu NURU yakasa dauka take aka sauya musu muhalli acikin qanqanin lokaci gari kuwa ya dauka tako Ina zancen akeyi wasu na qaryatawa wasu kuwa mamaki da firgici ya hanasu yadda.
Padima dake zaune bakin kofar dakin da aka jere dukiyar neman auren NURU dakuma Wai MALEEK UBAYD Wanda sunansa kawai sukeji kaf delah din Nan kila idan ba kakansaba sai wasu qalilan ance Babu Wanda ya taba ganinsa koda cikin sa'a ne.,
Sam Bata yardaba da wannan zancen tafi yarda da cewan wani dai acan gizah zai auri NURUn Amma badai MALEEK ba Dan kuwa har abada ko ita datake gaban NURU akomai Bata taba kawosa cikin rantaba bare NURU sokuwa wannna masarautar delah ta boyewa su abal ne amma tasan tsohon da take negestatinsace zai aureta Kuma a iya saninta ba ace musu maleek ba da akazo daukarsu negestati.
Kallonta amminsu tayi lokacinda ta fito dayan dakin riqeda hannun meryam daketa tsalle tsalle da farin ciki me tsanani tun jiya da akace Mata zasuje inda zasuga NURUnta.
Da mamaki ammin tace"
Padima tun jiya kin kasa dogon motsi kin kasa kin tsare kofar dakin Nan bayan kinsan Babu Wanda zai shigo gidan Nan idanma sata kike gudu ki kwantar da hankalinki Mana idanma tambaba kike na waye NURUn zata aura ai zamuje saimu tabbatar sbd muma munkasa yadda da abin al'amarin yazo mana a wani irin girmame saidai koma wane munsan wannan babban cigabe da abin farin ciki ga NURU sbd aure abune me girma dazai tabbatarda darajarta.
Qala padima Bata samu cewaba dan kalma daya acikin zancen ammin Bata fahimta ba babban burinta da damuwarta yanzu shine su tafi gizah din tasamu ganin NURU taji komai daga bakinta shine kawai zai Bata kwanciyar hankali tanaji meryam na fada Mata amed na kiranta waje harso shida tayi kamar batajitaba qarshe korata tayi da wani mugun kallo dayasa meryam din tafiya gurin ammi tana waiwayen padiman sbd ganin yau ko gyaran dogon gashinta batayiba Wanda kullum sai tayi gyaransa Kamar wani sarki.
Daga waje Kuma amed ganin Bata fitoba harya gaji da tsayuwa ya juya ya wuce Yana cewa"
Kome Zakiyi wlh sai anci dukiyar Nan Dani sbd rabona ya koka aciki Dan kuwa nasan yanzu tunda Zaki tafi gurin NURU a gizah dukkanin burinkanki kinsamu damar cikasu wlh maqalewa yanzu nafara Miki mutu ka raba komai Zaki samu taredani zamu cisa.
****
Zaune yake cikin makeken palonsa na quryar sashensa Wanda bayan masu gyarawa Babu Wanda yataba shigarsa ciki Koda kuwa mahaifiyarsace.,
Kyawu da tsarin palon kawai ya isa sanyaka lissafinda bazaka iya kaiwaba musamman sbd komai na sassansa na daban ne Dan zamowarsa MALEEK.
Akaro na biyu ya sake wani boyayyan numfashi Yana sake lumshe fararen idanuwansa dasuka Dan sauya sbd ciwon Kai me qarfi daya damqesa lokaci daya da kaleeb yakirasa ya sanar Masa da aure za'a daura Masa da negestatinsa abisaga umarni dakuma roqon alfarma da neman cika biyayya daga mahaifiyarsa da Bata taba neman wata alfarma daga garesaba ataqaice wannan ne Karo na farko data yanke hukuncin wani Abu akansa tun bayan rasuwar mahaifinsa Yana qarami.
Kaleeb ya sanar dashi an aika komai ankai qarshen komai jibi za'a daura auren Wanda har zancen ya fita shin tayaya zai musa wannan auren da yarinyar datake tamkar 'yar cikinsa Dan kuwa idanma lissafin yaje daidai afia zata girmeta Koda da shekara biyune ko daya.
Ta Yaya aure zai shiga tsakaninsa da wadda yakewa kallo daya da farhat qanqanuwar yarinyar da batafi shekara gomaba.
Wayarsace tayi haske tana vibrating ahankali ya bude idanuwansa ya kalla wayar ahankali yaga sunan Mr Omar akai dauke Kai yayi tareda mayarwa ya rufe tsawon lokaci ahakan kafin ya bude idanuwan daidai Mr Omar nasake Kira sbd sanin MALEEK dakyau da yayi yasa yake iya kwatanta mintunan sake Kira na biyu idan yayi na farko cikin sa'a kuwa ya daga batareda yace komaiba.
Da sauri cikin girmamawa da kaucewa dogon bayani da MALEEK bayaso yace"
Barka da hutawa MALEEK.
Dama 'yan media ne sukeson yada zancen...um..um..maganar auren ko za'a sirrantane?duk Wanda ya fitar Kuma mu dauka mataki akansa.
Kai tsaye yace"
Aure Yana boyune???
Jin haka yasa mr Omar cewa"
Allah ya huci zuciyar MALEEK.
Kashe wayarsa yayi ya ajiye tareda Miqewa yayi ciki Dan kuwa kila Babu me sake ganinsa sai gobe idan kaleeb ya iso daura auren Dan yasan zancen yanzu cikin awanni kadan zai bazu koina musamman NEGES da tun jiya yake son ganinsa Amma baya cikin mode dinda zai iya ganin kowa.
Yana daf da shigewa breaking news din auren THE KING OF DELAH GIZAH MALEEK UBAYD ya sauka acikin cikin qatuwar TVn dake palon ya juyarda idanuwansa ahankali zuwa kan time sai kawai yashige sbd Dama yasan media jira kawai suke abasu tabbacin zancen gashinan mintuna uku da zancen harsun sake breaking news.
*******
Qarfe shida na yamma daidai lokacinda zancen auren ya fita adaidai lokacin Anneti tayo aike me qarfi na daukar NURU zuwa wani kebantaccen sashe dake cikin sashenta Wanda Babu Wanda yasan inda aka Kai NURUn har afia kuwa Dan Koda aka tafi da ita afian na bacci Dan ko daki ba'a Bari Takoma ba daga Palo Dan haka Koda afia ta tashi da mummunan labari biyu daya Bata mummunan shock taci Karo na farko tun a waya tasamu labarin auren mahaifinta ta fito a rude saikuma tasamu labarin kebe NURU Wanda kowa yace baisan inane aka kebetaba.
Wayar dad dinta ta nema arikice tafara Danna Masa Kira Bata shiga hannuwanta dukkaninsu rawa suke da qafafunta tana sake Danna Kiran dad dinta Kiran Imran sai shigowa wayarta yakeyi na kakkautawa tana kashewa Dan ayanzu batasan ma a Ina kanta yakeba ta zari takalmi tayi sashen Anneti saidai tana shiga bata samu ganinta ba sbd Wai tana hutawa Bata fitowa lokacin dawowa tayi a haukace ta nema numbern kaleeb ta Danna Masa Kira shima Bata samu damar magana dashiba Yana cikin dakin hutawarsa.
Ji take kamar ta Ari hauka sbd so take tasamu bayanin abinda tagani take kumaji idan zancen datayine aka dauka da gaske take ake Shirin auren tun anan.
Palo tadawo ta zaune tana neman rusa kuka sbd idanuwanta dasuka kada sukai jajir ta dafe kanta dake neman tarwatsewa.
Wayartace tayi ringing a zabure ta wawuro wayar tana dubawa sai jikinta yayi wani irin daskarewa sbd tsananin sabon firgici da mamakin data shiga sbd ganin sunan""
MUM" baro baro akan screen dinta sai kawai jikinta ya saki tana kallo wayar na ringing harta tsinke Bata iya dagawa Dan kuwa rabon data ji mum dinsu shekarunma batasaniba tun bayana tafiyarta sai yau Wanda tasan dalilin Kiran baya wuce labarin auren dad dinsu data gani a duniya.
Zubewa tayi kan kujera tareda sake kuka Mara sauti tanajin wani zafin mum dinta da duk itace silar watsewar farin cikinsu" i hate you mum"takeson cewa Amma zuciyarta na hanata saidai wani irin zafin mum din takeji,
Babban baqin cikinta biyu ta rusa rayuwar NURU bayan tasan yanda sukeson juna da Imran hakama Imran ta rusa Masa farin ciki uwa uba me gaba daya bazata iya yadda ta karbi wata ba mum dinsuba amatsayin matar dad dinsu Dan haka Dole zatasan yanda zatayi ta Raba wannan auren ko an hadashi sbd kowa yasamu abinda yakeso.
***
Duk wani gyara da shiri na musamman anfara yiwa NURU shi atake da aka zo da ita Wanda Kuma kala Babu Wanda yake cewa ga duk tambayoyin datake musu sbd ita tsoro da firgici abin yake Bata Dan batasan meyake faruwa duk ta daga hankalinta musamman dataga ire iren gyara na musamman da ake Mata tamkar wata sarauniya Wanda Kuma ta tabbatarda wannan Shirin na aurene kokuma na Shirin kaiwane ga NEGES,to kenen gurin NEGES dinta datake negestatinsa za'a kaita..wasu irin hawayene masu matuqar zafi suka ciko idanuwanta tuno komai ya ruguje kenan daga yanzu a rayuwarta.
DELAH GIZAH ta dauki babban amo na jama'a manyan qasashe da dauloli dabam dabam hadda turawa da larabawa na nesa Dana kusa sun cika gizah damqam shiyasa tsaro da matakai harsunyi yawanda ko matso na Wasa basayi sbd atake zakayi ta bakin ranka sbd matakan tsaron ba dama musamman idan washe gari tayi ranar daurin auren kenan matakan saisunfi tsananta dan kuwa ko yanxu bashiga ba fita a gizah idanba na manyan baqinsuba na daurin aure.
Anneti duk wani farin ciki tana cikinsa musamman datai ido biyu da kyakkyawar fuskar NURU wadda cikin kwana biyu kacal ta sauya sbd tsananin gyara daya maidata tamkar asalin sarauniyar gizah musamman har wani sheqi fatarta keyi tuni tasake bada odar dasa sabon gyaran ciki Wanda zaibadu damar janyo zuciyar MALEEK gareta daga sun kusantu.
Washe gari jekadi na isowa tareda iyayen NURU dasu padima acikin tawaga ta musamman ta kaleeb Wanda Yana shigowa gizah aka rufeta gabaki daya ba shiga ba fita sai bayan daurin aure da qarfe biyun Rana.
Guri na musamman aka sauke iyayen NURU wainda suketa fama da padima da zazzabi me qarfi ya rafketa reras Banda some some Babu abinda takeyi daqyar suka samu tayi bacci kafin sukaci abincin alfarma fiyeda kala goma suka koshi aka kawo kayan Shirin abal dinsu ya shirya masu tafiya dashi suna jira yafito suka nufi can bangarenda za'ayi daurin aure yabar amminsu da sallar nafila tana zuba adduaoin a daura auren Nan lafiya yasa idan akai auren sai mutuwa NURUnta.
Meryam Kuma a zaqe take dataga NURU wadda Babu me ganinta kaf sai mijinta idan tafara fitowa daga maboyarta Wanda wannan al'adarsu ce.
Qarfe biyu aka daura auren UBAYD MALEEK M KALEEB da NURULHUDA ABAL YONAS akan sadakin darhaman zinare Wanda dubban daruruwan hamshaqan duniya suka shaida a masarautar delah gizah dakeda kafaffen tarihin.
Daurin auren yasamu 'yan farin ciki da Yan sabanin hakan da masu burika daban daban akansa Dana alkhairi Dana sharri.
Maganar aurensa ita ta batarda maganar rabuwarsa da matarsa data fara bulla.
Har yamma tayi lis afia Bata cikin cikakkiyar nutsuwarta Dan haka tanajin saqon fitowa da MUSHRAH(bride/sabuwar Matar sarki/amarya)yagama bazuwa a cikin delah gizah ta shirya cikin qarfin hali da danne damuwarta ta shirya tsaf cikin shigar alfarma ta li'ilitinta tafito Dan zuwa miqa gaisuwarta datake al'ada dakuma Dole Dole ga duk wani Wanda ke cikin masarautar delah gizah fitowa Kai gaisuwa ga duk MUSHRAn NEGES wato amaryar sarki.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_💖💖💖
_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_
_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
*_Mamuhgee 21_*
Tunda aka fito da ita taga sauyi me matuqar girma da mamaki sbd tsaro da girman da ake Bata kamar za'a bauta Mata yasa taji hankalinta ya ninku gurin tashi da firgici saidai sbd a rufe take Babu me iya ganin hakan gashi takasa Jin komai daga bakin kowa bare ta tabbatarda abinda yake faruwa Abu daya data tabbatar shi shine tabbas yau gurin NEGES dinta za'a miqata Wanda hakan yasa idanuwanta masifar cikowa da hawayen tausayin kanta dana im harma Dana afia da farhat dinta da zasu rabu gashi har abada Bata ikon sauya wannan ikon akanta.
Kai tsaye babban sassan MALEEK UBAYD aka nufa da ita Wanda shine yakeda ikon fara ganinta kafin tafito kowa yaganta Dan haka suna Isa tangamemiyar kofar gurinsa masu tsaro suka bude musu sbd tsananin tsaro da securities din gurin masu Kama da samudawa anan kowa ya tsaya daga ita sai jekadi suka shige aka rufo har lokacin Babu kala jekadi Bata ce ba shiyasa batama San da ita ake tareba bare tasan inda suka shigo.
A kofar palonsa na karshe Wanda dagashi saina hutawarsa sai master bedroom dinsa Dan haka daganan jekadi taja gefe ta tsaya cikin bawa NURUn girma tace"
NURU gaki a kofar shiga gurin uban gidanki Kuma mijinki na halak malak Wanda shine zai budeki kafin kifito al'ummar gizah nason sheda ganinki wato mace me sa'a.
Da haka tayi baya ta fice daganan Takoma can farkon shigowa jiran fitowar NURU din.
Kasa motsi tayi daga inda take tsaye sbd firgicinta daya koma zallar mamaki Dan kaman Bata fahimci me jekadin tagama fadaba ta wuce.
Saitaji kaman tace aure?
Girgiza Kai tayi ahankali tareda sauke Numfashi sbd sanin ba hakan bane itada samun arzikin daukar igiyoyin auren wani sai Allah tunda harta rasa igiyoyin auren im tasan aure gareta sai rabo me qarfi Dan tuni take cikin radadin hakan har lokaci da rayuwar data samu a Paris ya mantar da ita komai yanzu Kuma qaddararta tadawo gareta Dan haka ba gudu bare tsira.
Ahankali ta tura tareda saka Kai cikin qofar da jekadi ta 'dan bude Mata ba dukaba sbd takaitawa NURU aikin bude qofar Wanda badan kofar MALEEK bace itace zata bude Mata ita har qarshe.
Wani irin sanyin AC ne Dana wani qamshi data sani suka fara tarbanta ta maida kofar ta rufe ahankali har lokacin fuskarta arufe take.
Tunda ta iso tsakiyar palon ta tsaya cak batareda ta qara taku ba sbd bugun zuciyarta daya qaru Yana fita da qarfi Dan zuwa yanzu tagama tabbatarda qamshin datake ji musamman data iso tsakiyar palon taji yasake gauraya gurin.
So take ta yaye fuskarta taga inda take sbd firginta daya sake dawowa Amma ba hali sai kawai qafafuwanta suka hau rawa da dukkanin jikinta dama gashi ko abincin kirki tadaina ci kwana biyun sbd tsoro da shakkun datake ciki na abinda yake faruwa
Hannunta dake tsananin rawa ta daga ahankali ta shafo fuskarta dake lullube taji zufan tashin hankalin turaren MALEEK datakeji tako Ina na shiga hancinta take ta lalubo kujera ba shiri sbd jirin dayake Shirin dibarta ta ta zauna akan kejeran cikin rudewan rasa abin,
Dauke wuta tayi atake sbd Jin kusada mutum ta zauna batareda tasaniba rintse ido tayi cikin tsananin tashin hankalin rashin sanin meyene Wai yake faruwa da ita ta yunqura da sauri zata tashi taji anriqe hannunta ta tsaya cak tareda saurara abinda takeji na qamshin MALEEK zuciyarta na harbawa da qarfi kaman zata faso kirjinta.
Lullubinta taji an yaye ahankali Wanda yasata yin qasa da kanta tareda rufe idanuwanta sbd koma wanene bazata iya kallonsa Kai tsaye ba tunda shugabantane.
Tsit gurin yayi Babu wani motsi Babu wata magana tsawon mintuna shida ahakan kafin ya miqe ahankali har lokacin kayan daurin auren ne ajikinsa dasukai Masa matuqar kyau suka sake boye manyancinsa tareda bayyanarda asalin kyawunsa abun Kamar almara Amma har wani kyalli yakeyi Wanda ake cewa na anganci.
Ciki ya wucewarsa batareda yace komaiba,
Har lokacin Bata dagoba saidataji shigewarsa ta bude fararen idanuwanta ahankali ta dago Amma takasa bin inda yabi Koda kallo ne,
Hannunta daya Kama ta dago ahankali takai hancinta gabanta yasake wani irin faduwa,
Duk Wanda ya yaye fuskarka daga fitowarka wankan boyo shine yakeda Kai da ikonka Kona aure Kona negestati,
MALEEK???
MALEEK???
Toshewa kanta yayi gabaki daya Bata fahimci komaiba ta miqe har lokacin qafafunta na rawa ta fito dama wannan al'adace Kuma ancikata tunda ya yayeta.
Tana fitowa kallo daya jekadi Tai Mata ta hangi tsagwaron rudu da firgicewa atareda ita da hanzari ta qaraso gurinta cikin kulawa da girma tayi qasa da murya tace"
Ki nutsu kada ki daga hankalinki taron mutane ne keson ganin MUSHRAn MALEEK.
Cak ta tsaya tareda waiwayowa ta kalli jekadi da idanuwanta da zuwa lokacin tuni hawaye suka fara gangaro musu kenen dai ta tabbata maleek ne hancinta da wasi wasinta yazama gaskia.
Da sauri jekadi ta Kara gabanta ta boyeta tana cewa"
Allah ya taimaki mushrah wannan ba girmanki bane bayyanarda hawayenki agabanmu Dan Allah ki kwantarda hankalinki
Allah kuma ya huci zuciyarki da salama idan bazaki iya ganin kowaba ayanzu ko zamu rakaki gurin iyayenki dasuka zo kifara mgana dasu wannan sakone daga Kaleeb Kuma Yana Tayaki murnar tareda sanyawa aure albarka.
Ita gabaki daya batasan lokacinda kuka yazo mataba ba shiri jekadi ta nufi sashen Anneti da ita Wanda yafi kusa daga Nan din suna zuwa Anneti tace akaita kuryar dakinta abarta ta huta tukuna dama zataji abin wani iri tunda batada masaniyar komai.
Take aka sanar kowa ya tafi NURU tana hutawa bazata samu damar fitowaba yanzu Wanda hakan yasa kowa yafara mamakin irin sa'a da gata tareda daurewa da NURUn ta samu na take al'ada tun aranar farko.
Afia ma Bata datazo yau da mamaki Takoma sashensu sbd Bata samu damar ganin NURU ba sbd dolen Dole abarta ta huta tasamu nutsuwa Wanda itakuma tasan NURU na buqatarta yanzu sbd tayi Mata bayanin kada ta tayarda hankalinta idan sun bar Nan komai zai koma daidai zata samu Imran dinta.
Kuka tayi sosai batareda tasan Kona meneneba itadai yanzu iyayenta dataji suna kusa takeson gani Dan sune zasu Mata bayanin komai ta fahimta.
Sai dare lis ta fito cikin wasu kayan dabam da aka kawo Mata akasa tayi wanka ta sauya ta fito dukkanin abindake jikinta qyalli yakeyi tundaga kayan dake jikin nata har zuwa wata siririyar diamond necklace dake wuyanta ta daqyar ta iya cin abinci tareda Anneti suna gamawa Ana kawo Mata farhat data rikice musu kwana biyu na rashin ganin NURU din tana ganin NURU ta fallo da gudu itama NURU sai lokacin taji Dan damar abinda takeji ta rungume farhat din cikin samun nutsuwa tace"
I miss you sweetie.
I miss you more my Lewa ohhh Anneti tace ke mamanace yanzu bazaki taba tafiya kibarniba kaman mum ko??
Wani dum NURUn taji takasa dagowa ta kalli Anneti dake jinsu hakama takasa bawa farhat amsa ita Tama rasa kunyace ta kamata kome?
Riqeda hannun farhat din suka fito daga sashen Anneti jekadi da sauran mabiyanta uku na bayansu suka nufi gurin iyayenta farhat nata yaba kyawu da sauyawar datayi itadai gabaki daya tafiyar kawai take hankalinta baya tareda ita abubuwa da yawane suke yawo cikin kanta wainda suka girmi tunaninta.
Suna Isa dukkaninsu jekadi daga waje suka tsaya daga ita sai farhat suka shiga bayan an wangale Mata kofar tana shiga aka rufe abal da amminsu dake zaune a Palo suka kallo qofar atare fuskokinsu na bayyanarda wani yalwataccen farin cikinsu daya kasa boyuwa itama kasa motsawa tayi sbd kasa gasgata mafarki take kokuwa gata ga iyayenta bayan wasu shekaru take idanuwanta suka ciko da hawaye suna Shirin gangarowa meryam data fito daga gurin padima tana ganin kyakkyawar halitta a tsaye cikin palon ta tsaya cak taqare Mata kallo ta tabbatarda NURUntace a guje tayo kanta tana Kiran sunanta NURU ta ware Mata hannu tareda dauketa cak suka qanqame juna tana jero Mata yarensu Wanda farhat ce kawai batasan me take cewa NURUn ba.
Daqyar suka saki juna kowanne farin cikinsa yakasa raguwa ta qaraso gurin amminta ta rungumeta tareda riqo hannun abal dinta cikin yare da muryarta me sanyi tace"
Abal ubana nagari nayi kewarku fiyeda komai da kowa nayi farin cikin ganinku cikin lafiya da wadata.
Murmushin farin ciki me sauti abal yasaki Yana dafa kanta yace"
NURU 'yata tagari munyi farin cikin ganinki cikin koshin lafiya da nustuwar rayuwa,
Bamu taba farin rayuwaba irin Wanda Kika bamu ayanzu na aurenki da muka gani cikin ahali me girma da daraja.
Amminsu kuwa sbd farin ciki takasa cewa komai sai kallon 'yarta takeyi cikin tsananin so da kauna tareda alfahari Wanda yasa NURUn Jin nauyin iyayenta musamman da abal ya dauko maganar auren yana Mata nasihar hakuri da nutsuwa tareda tawakalli daya santa dasu Kuma yake qara Jan hankalinta dasu akan ta rungumi wannan aure da hannu bibbiyu.
Cikin mamaki ta kalli ammi tace"
Ammi Ina padima?
Ajiyar zuciya ammin tasaki tareda Dan satar kallon abal din kafin ta kalli kofar dakin da padiman ke ciki tace"
Tana can akwance batada lafiya sosai gobema inshallah zamu koma gida sbd aje can abal dinku yasamu maganin Bata Wanda zaiyi Mata tunda ciwon na jiri ne.
Subhanallh"NURU tace cikin damuwa da kulawa kafin ta miqe ta nufi hanyar dakin bayan ta kalli farhat dake maqale da ita tacewa ammi ga farhat Nan su gaisa
Ammin tajawota ta Dora kan cinyarta tana tambayarta tana lafiya?
Tana Isa dakin tashiga Kai tsaye padima dataji zuwan NURUn tasake sassake jiki tana maqale murya tareda qaro nishin ciwonda babusa hadda hawayen da tun safe suka kasa tsaya Mata na abinda ya tsaya ya danne zuciyarta.
Da sauri NURU ta qaraso bakin gadon tana kamo padiman tana Kiran sunanta cikin tsananin kulawa Tama dungumota gabaki daya tana cewa"
Padima meya sameki bayan yau Ina cikin tsananin farin cikin ganinku ku duka.
Marairaicewa padima tayi itama tana rungumo NURUn cikin muryar datayi laushi ta ciwo tace"
NURU nayi tsananin kewarki wadda bantaba sanin haka nake kaunarkiba Saida Kika tafi nakasa nutsuwar zuciya,
Wlh NURU nayi kewarki fiyeda zato ga amed ya yaudareni yace yafasa aurena Amma tsoro yahani fadawasu abal Wanda hakan yasa suka tsangwameni"""kuka tasake Mara karfi sosai tana sake shigewa jikin NURUn tace"
Nidai NURU bansan ya zanyiba mutuwa kawai nakeson Yi sbd itace daidaini,
Dan Allah NURU ki yafemun abinda nayi Miki wlh nayi nadama tunda gashinan Naga ishara irin wadda bantaba tsammani ba.
Cikin mamaki NURU ta share Mata hawayenta tana cewa"
Kidaina kuka padima duk wannan yariga ya wuce Kuma shi amed kansa yayiwa sbd Allah zaibaki Wanda yafisa Inshallah idan har kin tsarkake zuciyarki.
Wasu sabbin hawaye tasaki tana satar kallon kofa tace"
NURU bazan taba daina kukaba sbd kuka yaganni.
Da tausayawa NURU tace"
Kidaina fadar hakan padima.
Padiman zatayi mgn saiga amminsu tashigo wadda takasa zama Jin sun Dade aciki tsaf hankalinsu Bai kwanta da kebewar NURU da padima ba Dan haka Bata Bari padima tasake mgn ba ta janye NURU suka fito inda ta zauna tsakiyar iyayenta suna sake zantawa Kamar kadasu tafi goben jintake Kamar tabisu kosu bita musamman Meryam wadda takeda burin dauka duk tayi aure Amma yanzu Kam ko ita Bata gama tantance matsayintaba bare harta dauko wani ya zauna a qarqashinta.
Saida jekadi taga lokacin kaita gurin maleek yayi tashigo ciki ta sanar musu tayi bankwana da iyayenta bayan anshigo da tarin kayan arziki anjere musu daga Kaleeb da Anneti sai babbar kyautar MALEEK wadda ko ciki baa shigo da itaba saidai idan sun Isa gida akai musu.
Dazata fice harda hawayenta padima ta riqo hannunta tana hawaye qasa qasa tace"
NURU ki taimakeni Banda lafiya mutuwa zanyi idan Ba'a nemamin magani ba ciwon zuciya me qarfi nake fama dashi tunda dadewa kullum bana iya bacci ki taimakeni ki tafi Dani ki nemamin magani NURU.
Kallonta NURU tayi a Dan tsorace tace"
Tun yaushe padima shine Baki fadaba idan yayi tsanani wani Abu yasameki fa?
Kallon abal tayi cikin damuwa da kulawa tace"
Abal meyasa ba'a fadamunba ko a wayane da anfadawa jekadi ta fadamun ta waya wannan ciwon ba abun Wasa bane zantambaya afia Inshallah zamu tafi da padima.
Wani mugun kallo ammi tayiwa padiman data bushe idonta ba wani alamar qarya ko yaudara atareda ita abal ya hade fuska tsaf yace"
Kije NURU Allah ya albarkaci rayuwar aurenki ya Hana duk wani Wanda beda fatan alkhairi sa'ar rabarki,
Padima bazata bikiba kowane irin ciwone zamu nema Mata magani Inshallah.
Kallon padima NURU tayi tana Bata hakuri ta ido da cewa tayi hkr Inshallah ta Mata alqawarin dawo da ita hannunta ta nema Mata lafiya idan nasu abal din baiyiba.
Da haka aka wuce da ita tabarsu suna binta da addua suka wuce ciki Babu Wanda yaceda padima dake tsaye idanuwanta sunyi jajir zuciyarta na wani irin zafi da harbawa.
Kai tsaye sashensu datake dasu afia aka maidata sbd saqon maleek daya Isa gurin jekadi ta hanyar Anneti cewar basai ankar NURU gurinsaba yau din gobe zasu koma,
Tana Isa ta tarar da Afia zaune tagama hada musu kayansu tsaf sbd suma dad ya sanar cewa gobe zasu koma dama amatse take dasu bar Nan din sukoma Kota samu kanta tayi tunanin abinda yakamata.
Tsayawa tayi daga bakin kofa tana kallon afia da duk damuwa da sanyin jiki ya bayyana atareda ita taji tausayinsu su duka ya dawo Mata sbd tafi kowa sanin burin afia akan dawo da mahaifiyarta gidan MALEEK gashi yanxu su duka qaddara ta bullo musu ta inda basa zato.
Qamshin NURUn daya cika gurin yasata dagowa sukai ido biyu kowa yakasa motsawa suka tsurawa juna ido kafin Afia ta taso ahankali ta qaraso gaban NURUn ga mamakinta saitaji afia din ta rumgumeta tana cewa"
Thank God you're back NURU nayi kewarki.
Mamaki yasata daskarewa batareda tace komaiba ko motsawa.
Afia kuwa tarigada tasan zaman aure ko rayuwar aure tsakanin NURU da dad dinta bamai yiyuwa bane har abada Dan haka Bata sawa ranta damuwaba Dan duk duniya Babu Wadda dad dinta zaiso idan ba mum dintaba Dan haka tasan shima idan har aka koma Babu wani maganar aure dazaibi hakama NURU tana komawa Imran yadawo bazata yarda ba Imran zataso komawa Dan haka ta daure tacire damuwar komai aranta.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_💖💖💖
_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_
_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN qNUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
*_Mamuhgee 23_*
Abdul-rahman (sudais) is a young boy who's so passionate about putting the Holy Qur'an into memory. Please help this little boy grow his YouTube channel *ABDUL-RAHMAAN* you got nothing to lose in sha Allah thank you and Jazakumullah khair🙏🏻
https://youtu.be/WWIGq5Jbtb0
Do subscribe please
****************
Kodata fito kasa zuwa dakin farhat tayi sbd gabaki daya kafafunta sunyi sanyi toilet dinma tana fitowa ta zube kan gado a kife tana sauke ajiyar zuciya a jejjere Dan Kamar har lokacin tanajin dumi da softness na hannunsa akan mararta.
Bude kofar da akaine yasata Dan juyowa ahankali taga afia ce ta tashi zaune da sauri tana cewa"
Princess tadawo.
Dariya afia tayi tana qarasowa ta aje shopping bags din dake hannunta tace"
Harkinji sauki kenan?
Waskewa NURU tayi da cewa"
Eh" tajawo kayan tana budewa Dan mantar da kanta tunanin abinda yafaru din.
Duk abinda take buqata afian tasiyo Mata ta tashi ta tattara kayan tasa musu su a inda suke aje kowanne tayi sallah tazo ta zauna suna duba wani sabon Francie's program na likitoci da lawyers tareda engineers a laptop.
Sai la'asar lis tayi wanka ta sauya cikin White three quarter da farar top me laushi ta fita tayi dakin farhat afia tabi bayanta da kallo sbd kusan kome NURU tasaka kyau yake Mata inama ace Imran dinta tafara aura dashine zata more rayuwa sbd yanda yake Sonta Amma dad dinta bazata taba samun so agaresaba har abada sbd mum ce kawai a zuciyarsa.
NURU na shiga dakin farhat ta taddata itama sanye da fararen qananun Kaya tana jiranta har ta fidda kayan drwing din Nan suka baje suka fara.
Sai bayan magriba suka gama
Farhat ta dauka da gudu taje nunawa dadynta ya duba Masu idan sunyi daidai Amma bayanan kusan so uku tana komawa bayanan ta karba wayar NURU ta saka numbernsa dake cikin kanta ta Kira Bai dagaba tukuna ta hakura anan dakin sukai sallarsu suka kunna cartoon suka baje abinsu adakin suna kallo Saida lokacin cin abincinsu na dare yayi suka fito zuwa dining suka zazzauna sukaci suka koshi suka shige anan dakin farhat NURU tayi barci Bata koma nasu ba Dan dama hakan takeyi wani lokacin.
Qarfe goma Sha biyu da mintuna ya nufo dakin farhat din wadda kusan kullum idan haryana gida saiyazo ya dubata da daddare sbd qarancin shekarunta musamman yau dayasan saitayi nemansa sbd zanenta yaduba Mata Dan haka ya nufa dakin Kai tsaye ya bude yashigo tareda rufe kofar har zai kunna wuta gudun kada ya tadata yasa Bai kunna dinbaya qaraso bakin gadonta tareda zaunawa bakin gadon ya Kai hannu yakunna bedside lamp kadan haske ya 'dan bayyana yana waiwayowa yaganta itace kwance abakin gadon farhat na quryar gadon ya sauke sahirtaccen numfashi Yana kallon kayan baccin jikinsu itadai farhat komai iri daya riga da guntun wando royal blue bacci suke duk su duka hankali kwance.
Dan qara rage hasken wutar yayi sbd kaman hasken zai damesu yajanyo musu bargo ya lullubesu ko Gama janye hannunsa baiyiba NURU tasa kada ta yaye lullubin Dan dama Bata cikason rufaba cikin bacci.
Fuskarta yayiwa kallon minti biyu ya dauke Kai tareda Miqewa ya nufi hanyar ficewa harya taba kofa zai fita saiya tsaya tareda Dan rufe ido ya bude tunanin Dole wani daga cikin masu aiki zasu tadasu da asuba yasashi dawowa yasake Jan bargon ya rufa Mata saidai Yana dauke hannu takai hannu cikin baccin zata yaye yakai hannu zai danne hannuwansu suka sauka atareda nashi akan nata Wanda Kai tsaye yasata bude manyan idanuwanta dake cikeda bacci ta dagosu.
Kasa yadda tayi da abinda tagani tasan mafarkine kawai take Dan haka saita juya hannunta tasanya tafin hannunta tana sake tattaba hannunsa Dan Jin tsananin taushinsu ta lumshe ido baccinta na fizgarta har lokacin tafin hannuwansu na hade.
Dan sarquwa yayi da yawu kadan yasaki Dan qaramin tari Mara dogon sauti Wanda yasata bude idanuwanta duka da qarfi tareda zaburowa daidai motsawar farhat sai yayi saurin dafeta Takoma kwance sbd kada ta tada farhat ga farhat din da surutu zata iya jeho wani zance akan hakan.
Kallonsa takeyi face to face akaro na farko a rayuwarta zuciyarta na harbawa a tsorace yayi Mata kallo daya da idanuwansa da yau suka shiga daidai cikin nata take taji jikinta ya sake gabaki daya sai kawai ta sake a jikinsa ya hadiye wani mugun yawu a maqogaransa Wanda yasata kallon moqoshinsa sbd yanda Adams apple dinsa yayi sama yayi qasa ta maqoshin nasa.
Miqewa yayi tsaye yaraba jikinsu sbd asthma dinsa dayakejin kaman zata tashi ya juya ya fice adakin yabarta kwance Bata iya ko daga hannunta sbd mutuwar jiki saidai ido databisa dashi cikin wani irin yanayi na kunyane ko na menene ta Bata saniba illa dai Abu daya data tabbatar ayau shine kyawun da Allah yabasa Wanda ko rabinsa 'yayansa Basu daukoba cikin yama manyanta kenan...daganan baccinta ya watse har kusan asuba Bata samu baccinba gashi gobe tanada zuwa makaranta Dole ta rintse idanuwanta Dan tayi baccin Kona Dole ne.
Qarfe shida ta farka ta sauko gado tashiga toilet tayo alwala ta tada farhat sukai sallah ta fice.
Tana shiga dakinsu ta tada afia sallah kafin ta fito ita ta fice zuwa kitchen aikin breakfast.
Tana gamawa ta jere a dining takoma daki tayi wanka tashirya cikin black riga da wando ta doro doguwar kimono fara akai ta daura black scarf me kauri tafito sukayi breakfast itadasu afia da farhat suna gamawa kowa yaje ya dauko jakarsa suka fito.
Da Mr Omar suka fara cin Karo tsaye jikin motar dazasu tafi da ita makaranta tareda sabon driver cikin girmamawa yana Dan taudasa harshe cikin sakin fuska yace"
Gud morning Mrs MALEEK.
Gud morning princess.
Kallonsa AFIA tayi Jin abinda yace itadai NURU sidadawa tayi ta wuce Jin kalmar tamata girma ta shige mota tana kunna wayarta da Imran yahanata sakat da kira saigashi tana kunnawar kiransa na shigowa ta dannata silent tana Dan kallon gefen Mr Omar dake tsaye idanuwansa kuwa quru akan wayarta tana juyowa ya dauke Kai Yana cewa"
Adawo lafiya.
Suna barin gidan ta sauke ajiyar zuciya tareda daukar wayar data kusa katsewa cikin sanyi da rawar murya na rasa abin cewa da damuwa tace"
Hello im ka......da wata gigitacciyar ajiyar zuciya ya katseta yana cewa"
NURU labarin aurenki Bai kasheniba duka ya kashe rayuwata gabaki daya amma rashin daukan wayarki zai kashenine sbd.....
Da siririyar murya tayi saurin katse zancen da cewa"
Kariga kasan komai Im tayaya zan iya daukan wayanka yanzu inajin tsoron hakan.
Kasa danne abinda yakeji yayi cikin wata wahalalliyar murya idanuwansa na cikowa da hawayen zafi da ciwon da zuciyarsa kemasa ya bude Baki dakyar yace"
NURU shin da gaske kin auri MALEEK sbd wlh nakasa ji nakasa yarda da komai inason ji daga bakinki Dan kuwa nasan nikadaine a zuciyarki nakasa yadda da hakan NURU na.....
I'm sorry im bansan mezan iya cewaba Amma dai koma menene gskiyan shine aure dai andaura Wanda Koda bada son Rainaba Dole zan kiyaye dokan aure Dan Allah im kayi hakuri komai yafaru ne kaman daga sama,nasani kana tsananin Sona haka Nima Ina......shiru tayi Idanuwanta na cikowa da wasu irin hawayen karyewan zuciya sbd Jin sautin kukansa dake fita ahankali cikin karyewa da zuciyarsa keyi taji zuciyarta ta karye itama hawayenta na gangarowa takasa karasa mganar ta kashe wayar sbd kukansa reras dake ji cikin qaramin sauti.
Kasa cewa komai afia tayi tanajinsu sbd tausayinsu datakeji musamman im Wanda tafi kowa shaida irin so me girma dayakewa NURUn.
Farhat kuwa riqo hannun NURUn tayi tana kallon hawayen daya gangaro Mata tace"
Aunt NURU meya samu uncle Imran din Naga kina kuka.
Dauke kanta tayi tana goge hawayenta da tissue ta Dan qaqalo murmushin yaqe tace"
Ba komai kafiyansa kalau he's just missing you princess farhat.
Murmushi tayi tace"
kema Yana missing naki ko??
Shiru sukayi Babu Wanda yasamu damar cewa kalaba har suka Isa aka ajeta suka wuce Dan su sunada Dan nisa.
Suna isa makarantar Kai tsaye ladies washroom ta nufa ta nutsar da kanta tareda bude kanta kwakwalwarta tasamu damar haddace abinda take nanatawa kanta na cewa tanada haqqin auren wani akanta yanzu dokar Allah na kanta.
A dauki mintuna aciki kafin ta samu 'yar nutsuwa ta gyara fusakrta ta fito tana duba wayarta dake ringing ga mamakinta saitaga numbern ta Ethiopia ce Kiran daga gidane kenan da hanzari ta dauka tana tafiya cikin sa'a kuwa padima ce cikin tsananin farin ciki tace"
Hey padima hw are you??
Dif padima tayi sbd batasan abinda NURUn tafada meyake nufiba tana danne baqin cikinta tayi kasa da murya cikin tsananin damuwa tace"
Nuru kina lafiya kuwa?
Ya gida?
Yasu farhat?
Lafiya kalau kowama Yana lafiya,yayasu abal da meryam Ina ammi?
Sake qasa da murya tayi tace"
Lafiyansu kalau nuru.
Kefa padima kina lafiya dai ina?Kuma Yaya jikinki?
Antabo Mata inda take jira sai kawai takasa riqe kukan 'dacin ran datakeji tsawon kwanaki cikin qaramar sheshekar kuka tace"
NURU wlh bansamu saukiba Ni kilama ciwon ajaline abun yamin tsanani Kuma Babu wani magani dasu abal ke bani hasalima haryanxu fushi sukeyi Dani tun kan maganar cikin Nan da Babu nidai Dan Allah NURU kitaimekeni inason gyara rayuwata sbd Nima na faranta ran iyayenmu.
Sanyi jikin NURU yayi ta danyi shiru na seconds kafin ta sauke numfashi me zafi asanyaye tace"
Padima kidaina kuka Inshallah Zaki samu lafiya bazan Bari wani Abu yasamekiba da yardan Allah,
Yanzu Ina makaranta idan nakoma gida zanyi shawaran zuwanki na tambayi AFIA muji idan da hali sai jekadi takawoki Nan anemamiki lafiya.
Da qaramar muryar kuka tace"
Ngd sosai NURU Dan Allah kadaki manta ayi magana da wuri kada abin yayi qarfi fiyeda da.
Tana kashe wayar tafara tunanin Yaya zatayi yanzu da wannan sabuwar damuwar Kuma,da haka ta shiga class.
Qarfe biyar saura suka dawo amatuqar gajiye Dan ko zama batayiba ta aje Jakarta ta tareda zare kimono dinta ta nufi dakin farhat dan wanka take tsananin buqata da fitsari dayake neman matsarta gashi AFIA tarigata shiga toilet bazata iya jiraba.
Tana Shiga dakin farhat bata ciki Kai tsaye ta tube tareda janyo qaramin towel din farhat ta daura tafada toilet.
Ajiyar zuciya ta sauke lokacinda ruwa masu dumi suka sauka jikinta sbd yau Bata zauna sosaiba sbd zuwanta biyu kotu yau ga damuwar padima data Imran Amma yanzu taji sauki komai datayi wankan Nan.
Farhat yau da zazzabi tadawo daga school sbd bayan drwing din da jiya aka bawa kowa yayo yau games sukayi ita tana cikin masu football Wanda yadata haki da yawa Amma sbd ba qura asthmanta be tashiba saidai ta kwaso zazzabi me qarfi Wanda tun a school tayi collapsing aka Kira MALEEK Koda suka Isa ta farfado Amma Kam tanajin jin zazzabi sosai siadai yanzu zazzabin ya sauka gabaki daya saitasamu bacci ya dauketa Dan hakane yasa Koda suka dawo gida da ita ganin su afia basanan yasa yatafi da ita samanshi yanzu ta balcony daya hango dawowarshi saiya daukota ya dawo da ita dakinta danta samu kulawa gurinsu afian sosai.
Fitowa tayi tana gyara zaman towel din farhat dayayi Mata kadan tana sauke ajiyar zuciyar nustuwar data samu tana qarasowa tsakiyar dakin taganshi tsaye bakin gadon da farhat ke bacci wata mummunar razana tayi ta damqi towel din da qarfi Jin zai sabule Mata ta sake dagowa da sauri ta kallesa cikin tsananin tsoro.
Tsabar rudewa rigarta dake gefen gadon ta nufo da sauri zata dauka kafin ta iso yabar gurin batareda yabari ta qaraso gurinba ya fice dakin gaba daya Dan towel din ko Gama rufeta baiyiba sbd qanqantarsa.
Zamewa tayi bakin gadon farhat tana kallon kanta tareda dafe goshinta tanajin wani irin yanayi na damuwa.
Zarar kayanta tayi ta fice da sauri ta fada dakinsu ta Sanya kaya tayi sallah ta zauna gefen afia batareda tace komaiba ta zurfafa tunanin wani Abu dayakasa fita cikin ranta afia na lure da ita Amma batace Mata kalaba.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_💖💖💖
_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_
_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
*_Mamuhgee 22_*
Washe gari tunda safe sakon Anneti na gayyatarsu cin abincin safe tareda ita ya iso musu suka shirya dukkaninsu itadai jekadi dama tunda safe tazo da kayanda NURU zata saka tana Palo takasa ta tsare Dan kuwa komai daya danganci NURU yanxu saiya biyo ta gurinta kafin ya isa gun NURUn.
Da kanta tashirya farhat kafin itama ta shirya cikin doguwar royal gown dinsu me adon golden stones da sequence rigar ta tafine straight shiyasa ta fidda shape din tudun qirjinta zuwa shafaffen cikin har fadin hips dinta saidai adon sequence ne ya 'dan boye bayyanar shape din nata Sosai Sosai Amma duk da hakan yafito sai wuyan rigar dakeda Fadi sosai ta Sanya qaramar siririyar sarkar gold ta doro gyalen rigar akanta ta rufe gashinta dake daure Yana qamshin turaren hayaqin da akai Masa ta fito afia nabinta da kallon yaba kyawun datai Wanda duk be daga Mata hankaliba tunda dai duk abanxane suka fito jekadi na bayan NURU sai sauran masu Binsu suna bayansu kawunansu duk a soke kasa.
Afia ce ke kokarin janta da firar karatunsu da tun shekaran jiya yakamata su koma Amma Basu komaba itama NURUn abin sai lokacin yafado Mata musamman da tafara zuwa Court itama afian tana zuwa asibiti sama sama sbd karatun nasu.
Tun kan su qaraso aka sanarda zuwansu suna isowa suka tararda askarawan maleek kusan guda shida a sassan Anneti din afia na gani tasan dad dinsu na ciki ita Kam NURU batasaniba tunda Babu abinda tasani anan din Dan haka Babu tunanin komai dayazo Mata suna isowa aka wangale musu qofa Ana yiwa NURU gaisuwa ta musamman kafin aka juyo akaiwa AFIA da farhat suka shige.
Suna shiga palon farko duka sauran Yan rakiyarsu suka tsaya anan dagasu se jekadi suka wuce har cikin asalin palon hutawar Anneti suna shiga jekadi ta zube qasa cikin bada girma tace"
Allah yaqara MALEEK kyakkyawar zuciya data fuska,barka da fitowa.
Da hannu kawai ya amsa tareda juyowa Jin muryar AFIA na gaishesa cikin girmamawa itama.
Farhat kuwa kusadashi ta zauna tareda riqe hannunsa tana cewa"
Good morning Daddy.
Da sauri jekadi ta Raba gefen NURU data kusan sanqamewa a tsaye sbd shammatarta da abin yayi Sam ko kadan ko qamshinsa batajiba batama taba saka ran zata ganshi ananba.
Kallon afia yayi da idanuwansa masu haske cikin sautinsa na kamewa ya amsa Mata tareda cewa"
Kuna lafiya?
Gyada Kai tayi tana cewa"
Yes Inshallah.
Ahankali NURU ta tako ta qaraso ciki ta tsaya ta gefen NURU cikin sanyin murya batareda ta kallesa ba kanta na 'dan qasa tace"
Barka da fitowa.
Tsit gurin yayi kafin ya dago ahankali itama ya kalleta Wanda yayi daidai da fitowar Anneti tasaki murmushin ganinsu ta nufi hanyar dining room tana cewa"
Farhat zo ahau table cin abinci Afia zokiyi serving Dina.
Dan kallon NURU afia tayi ta sauke idanuwanta akan budaddiyar gaban rigarta daya bude sosai Dan idan har ba shedan ne yake Mata gixoba tana hango saman nonuwar NURUn kadan ta juya ta wuce tana Dan waiwayowa harta shige dama farhat ita tuni tashige.
Dauke idonsa yayi daga kanta tareda Miqewa baice komaiba ya wuce ciki.
Ajiyar zuciya ta sauke a boye sbd idan har akwai abinda yafi takura da firgici tashiga sbd taji idanuwa akanta saidai Babu tabbacin nasane Kona afia.
Kokarin zama takeyi taji Anneti takira sunanta tafasa ta nufi hanyar dining room din a sukwane tana Dan sauke Kai tana shiga Anneti ta nuna Mata kusada ita ta qaraso ta zauna kirjinta na bugawa sosai sbd duk wannan abin wani iri takejinsa Yana Mata nauyi sbd zuwan komai lokaci daya.
Afia ce tayi serving kowa Nan suka hau cin abincin Babu me mgn musamman itadai gabaki daya bataci abinda ya wuce Loma hudu ba sbd amatuqar takure take.
Maleek ne yafara tashi ya fice kafin Anneti saisu daga baya suna fitowa tuni aka fitarda komai na tafiyarsu suka dunguma zuwa ainihin fadar NEGES inda yayiwa NURU kallon tsaf kafin ya kalli MALEEK Dan kuwa yatabbatarda NURU bazatayima sa'ar afia ba Amma maleek ya aureta.
Yanaga Dole akwai dalilin dayasa MALEEK auren wannan yarinyar wadda akace asalinta ma 'yar bawan kaleeb ne,
Idan har da akwai dalili saiya bincika yaji Dan kuwa wannan karon bazai dagawa MALEEK qafaba Dan Bai shirya sauka mulkiba ya bawa MALEEK kujerarsa Dan haka zai binciki asalin ita yarinyar da zuriarta dole baza'a rasa abinda zaiyi amfani dashiba daga ciki ya rusa maleek gaba daya saiya mallaki kejeran da hujja.
Kyauta me girma yayiwa NURU tareda su afia kafin aka fito da NURU sai alokacin kowa yaganta 'yan jaridu kuwa sukaita dauka wasuma a sace suke daukar hotunan hadda maleek batareda sun saniba.
Kayan aure da aka bawa NURU Dole saidai aka barsu anan a hannun jekadi data riga yanxu tadawo gizah sbd sassan NURU daza'a fitar a tsara itace zata zauna Dan duk lokacinda NURU zataxo tananan Dan haka kayan acan sassan NURUn za'a ajesu.
Har airport jekadi ta rakasu tana sake jaddadawa NURUn wasu bayanan na cewa wannan aure ba saki ba warwarewa,aurene daya qullu har abada Dan haka ta nutsu ta rungumi abinda Allah yabata ta riqe da kyau tareda kiyayewa Banda Kuma yarda da kowa sbd za'a iya biyowa ta gurinki a cutatar da maleek.
Itadai saurare take kawai Dan batamasan wane turn rayuwarta zata daukaba daga yanzu Kuma.
Harsuka shiga jirgi suka miqa tana cikin tunanin yanda zatai rayuwa agidan amatsayin matar dadynsu afia gashi haryanxu bataga wani Alama daya nuna afia bataji dadin abinba ta bangare daya ga Imran datasan yanacan Yana jiran dawowarsu batasan me zatace masaba ya fahimta.
Sai dare sosai suka sauka motocin daukarsu suna airport jiransu Mr Omar sai wani rawar jiki yakeyiwa NURU Wanda yasa MALEEK yimasa kallo daya ya nutsu ya daina aka barta cikinsu afia kamardai yanda suka Saba tun ada.
Suna isowa gida su mum Sarah suka tarbesu suna zubewa yiwa MALEEK barka da dawowa Kai tsaye ya wuce samansa bayan ya amsa musu da hannuwa.
NURU suka jiyo sunawa barka da dawowa taredasu afia wadda tayi gaba sbd sai yanxu taji tasamu nutsuwa harwani ajiyar zuciyar nutsuwa take sakewa farhat mum Sarah takama hannunta suka nufi dakinta Dan wanka da hutawa.
Koda NURU tashigo daki afia harta shiga wanka Dan haka itama a qage ta cire kayan jikinta ta dauko towel ta daura tana warware gashinta afia ta fito tana gama warwarewa ta nufi toilet din tashige ta sakarwa kanta ruwan zafi tana rufe ido itamadai kusan dawowa gidan yabata nustuwa.
Tana fitowa ta Sanya kayan bacci ta saka jallabiya akai tayi sallolinta tana gamawa ko ruwa Bata nemaba ta cire jallabiyar ta haye gado ta shige bargo sai bacci Wanda afia tuni tayi nata baccin.
Washe gari sai guraren 11 dukkaninsu suka fito kowanne a shirye Banda farhat da har ankaita school sukuma sai zuwa gobe zasu fara zuwa.
Kai tsaye dining suka nufa suka zauna breakfast afia na fadawa nuru suna buqatan zuwa shopping sbd kusan turarukansu da mayukansu dasu shower creams dinsu duk sunyi qasa gashi ita tana buqatan wasu books na karatunta data siya tun last month sun iso ankirata tazo ta karba.
Ruwa NURU Tasha ta aje cup din tana cewa"
I also need some books zanbincika idan munje.
Miqewa tayi ta nufi daki tana shiga wayarta na ringing ta qarasa ta dauka cikeda mamaki da tsoro ganin Imran ne me Kiran ta ajiye wayar tareda kifewa hankalinta na neman tashi,
Me Imran keyine dazai kirani bayan nasan yariga yasan abinda yafaru.
A musulunce a al'adance duk laifine me girma Amma duk da hakan zatai magana dashi tafada Masa Dole hakuri zasu dauka haka Allah yaso Babu aure atsakainsu.
Tana daukan wayar tana tsinkewa sai kawai ta ajiye tareda kashe wayar gaba daya ta nufi closet dinsu ta janyo dogon pencil jeans da riga doguwa har qasa saidai daga qasan a tsage take har cinyoyi Wanda yasa ake Dan ganin jeans din idan tana tafiya ta janyo veil ta daura harta dauki wayarta sai ta fasa ta ajiye ta juya ta wuce.
Afia Dama a shirye take suka fito afia da kanta zataja motar yau suna sako qafafuwansu waje NURU ta tsaya cak wani tunani Yana fado Mata na sanin yanzu fa ita Matar aurece batada ikon fita kona kanta.
Waiwayowa afia tayi ta kalleta tana cewa" lafiya Kika tsaya?
Numfashi NURU ta sauke tana basarwa kada afia tagano dalilinta saita riqe gefen cikinta tana Dan yamutsa fuska kadan tace"
Marata tana ciwo inaga period Dina zaizo kije Bari nakoma na kimtsa najira zuwansa Dan kowane lokaci zaizo.
Da wani irin kallon mamaki afia tace"
Amma ai ba lokacin period dinki bane.
Sake yamutsa fuska tayi tace"
Eh ba lokacinsa bane Amma inaga abubuwan da akaita banine a gizah dama tun can sunata sani ciwon ciki.
Kallon mamaki da tsoro afia Tai Mata takasa cewa komai sai kawai ta juya tana cewa"
Shikenan ki koma Ni zanje nadawo.
Juyawa tayi Takoma ciki tana shiga Palo tana ta sauke ajiyar zuciya ta nufi daki ta cire rigar ta sauyo da qarama Mara kauri tabar wandon ta nufi kicin direct Dan aikin abincin Rana Kota samu abinyi dazai hanata zaman tunani.
Tanayi su Fana da mum Sarah na tayata harta gama tafito ta jera a dining tana baro dining din saiga farhat andaukota daga school tun daga Palo tana shigowa tace"
Aunt NURU yau akwai drwing dazamuyi babba na _Eiffel tower_ competition ne inason nazama 1st.
Yes yes sweetie Inshallah zamuyi shi babba me kyau Wanda zaisa ki cinye afterall who's gonna help you drw????
Da qarfi tana tsalle tace"
Our beautiful Aunt NURU.
Hmmn that sounds like a bribe sbd bantaba Jin kince our NURU ba saidai kice your NURU to yau kenan kinyadda keda afia.
Suna qarasawa kofar shiga palon kurya farhat na cewa"
No not afia,Ina nufin me and my dad since you are his wife now.
Tsit NURU tayi sakamakon hada ido datayi da maleek dayake saukowa tayi saurin dauke kanta tana riqo hannun farhat wadda ta kwace tayi gurinsa tana cewa"
Daddy barka da fitowa.
Kama hannunta yayi Yana nufar hanyar dining Yana cewa"
Hw is daddy's little princess?
alhmdlh dad but today I have.......kallonta yayi cikin nustuwa yace"
Go and freshen up first kafin kizo naji menene.
Da gudu tayi ciki tabarsu tsaye sai alokacin NURU tadan gyara tsayuwa tana rage murya qasa qasa tace"
Barka da fitowa.
Kai kawai ya gyada Mata ya nufi dining Wanda yasata Dole binsa Dan serving tunda dai Babu kowa agurin.
Zama yayi taqaraso cikin Jin nauyin kayan dake jikinta musamman dayake kujeransa tana seti da inda take tahowa tamafi Jin kunyar rigar dake jikinta din sbd Ana ganin yanayin kalar bra dinta fara ta ciki sbd transparent ce Amma ba sosaiba Dan Bata tana tunanin har lokacin Yana gidaba.
Tana qarasowa tafara serving dinsa cikin nutsuwar Dolen data tattarowa kanta.
Tana gama zuzzuba Masa ta nufi kicin ta hado drink dinda tasan yanasha tareda ruwa masu sanyi Amma ba sosaiba takawo ta aje tareda zuba Masa drink din a cup ta Dan dago kadan ta kallesa zatai magana ta rude ta kasa sbd kallon dayayi Mata yasata neman rudewa hartana neman fada Masa Bata saniba Saida ya tareta da hannunsa daya Wanda ya ba tsammani ya sauka daidai kan shafaffen cikinta daga ita harshi da saida suka kalli juna ya dauke Kai Yana kamewa tareda janye hannunsa tayi saurin juyawa tabar gurin jikinta na neman sakewa sbd duk duniya Babu Wanda yataba taba mararta sai yau gashi abin kamar na tsautsayi batasan yaushe rigarta tadan dagaba Dan kuwa direct taji saukan dumin hannunsa akan skin dinta da gudu taqarasa daki ta nufi toilet da gudu sbd har wani fitsari fitsari takeji na shiga rudu.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_💖💖💖
_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_
_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
*_Mamuhgee 24_*
Saida safe dukkaninsu sukasan farhat batada lafiya Koda suka Isa dakinta tana zaune jikin dad dinsu Yana zaune bakin gadonta sanye da black jallabiya ta maza me tsananin taushi sai kyallin maiqo takeyi alamar ta masu abun duniya ce.
Itace agaba ashigowa kafin Afia Amma tana ganinsa tayi slow afia ta wuceta tana qarasa dayan gefen ta farhat din ta zauna tana cewa"
Gud morning dad,
Farhat bakida lafiya bamusaniba mum Sarah ke fada Mana yanzu da safen Nan.
Dago fuskarsa yayi dake fayau dinta sai wani daukan ido take ya kalleta da idanuwansa Wanda itama daidai shi ta sata kallo suka hada ido tayi saurin sauke idonta muryarta da wani irin salon sanyi dabata saniba tace"
Barka da safiya.
Har lokacin kallonta yakeyi
Tasake dagowa ta saci kallonsa suka sake hada ido sai kawai tunanin ganin dayayi Mata jiya da daddare kusan Babu komai a jikinta take wata matsananciyar kunya ta mamayeta batasan lokacinda ta rufe idoba ta fita da gudu Kamar karamar yarinya.
Da mamaki afia ta dago ta kalli kofar kafin ta juyo ta saci kallon dad dinta da bataga alamar ma yasan da NURU tashigo bare tace kofar yake kallo ta maida kallonta kan farhat tana cewa"
Sorry baby aunt NURU taje Sanyo kayane sbd batasan dad na Nanba ta taho da sleeping dress ajikinta shine Takoma ta sauyo nasan kin matsu tazo gurinki ko baby?
Gyada Kai farhat din tayi tana kwantawa jikin afia din tace"
Afia I saw mum yesterday a school dinmu she was there before I fainted......
Da sauri AFIA ta dago ta kalli farhat din tareda kallon dad dinsu da sauri shima saidai ko Gama juyowa batayiba ya miqe ya fice kamarma baiji me farhat taceba afia tabi bayansa da kallo kafin tadawo da kallonta kan farhat cikin mamaki tace"
Baby dagaske Kinga mum?
Gyada Kai tayi tana kallon afia din tace"
Eh naganta tazo kafin ta iso gurina I fainted daganan shikenan saidai Naga dad kawai.
Wani yawu afia ta hadiye kafin ta ta danne mamakinta da farin cikinta tana miqewa tace"
Ok baby Bari naje naturo Miki NURU tazo tayi Miki wanka da brush saita Baki abinci akwai abinda zanyi yanzu na gaggawa ok baby.
Wucewa tayi ta fice da sauri ta nufi dakinsu ta janyo doguwar riga tasanya akan kayan baccin jikinta ta dauki wayarta da sauri ta fice ta nufa library dinsu Dan Yin waya.
Doguwar kimono NURU ta doro akan kayan jikinta na bacci kafin ta wuce ta nufa kicin ta hadawa farhat Dan guntun breakfast sharp sharp ta dauko a qaramin faranti ta nufa dakin tana adduar Allah yasa ya fice.
Ganin baya dakin yasata qarasowa da wuri ta ajiye tray din tana cewa"
Sweetie kiyi hkr bamu San bakida lfy ba,jiya ma anan nayi wanka Amma banluraba sbd hankalina yatafi wani gurin dabam na......kasa qarasawa tayi tana sake tunano abinda yafarun sai kawai ta sauya zancen da sakin qaramin murmushi tana cewa"
Ok sweetie muje ayi brush kizo ga breakfast sai asha magani.
Tayar da ita tayi suka nufi toilet din suka shige.
Harsuka gama komai har wanka da Shirin farhat din kafin suka fito zuwa nasu dakin itama NURU tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga suka fito Palo ta kunna Mata cartoon takoma ciki tayi Shirin makaranta tazo ta fice har lokacin afia Bata shigowaba tanacan.
Tsaye take cikin libry din idanuwanta sunyi jajir sbd tsananin baqin cikin dake mamaye da zuciyarta ayanxun datake waya da mum dinta cikin tsananin sanyin murya da sarewa tace"
Haryanxu Babu 'yayanki acikin ranki kenan?sbd wani burinki na duniya mum kike fadar haka? Tayaya kike tunanin dad zai iya rayuwa ahaka for how long kikeso yayita jiranki?mum please ki......
Cikin iko da muryarta me taushi ta katse afia da cewa"
Zandawo wa MALEEK Amma ba yanxuba haryanxu akwai abubuwan dake gabana,afia kinada naci akan zance daya koyaushe bayan nace Miki zandawo Amma ba yanzu ba idan akwai abinda yafi cancanta yanzu dakiyi shine ki raba maleek da yarinyar daya aura Kuma tabar gidan gabaki daya sbd matuqar tananan koya saketa bazan iya dawowaba infact inason sauyin gida tunda harta zauna a wannan gidan koba komai idan haryanzu kunason aikinta zaku iya zama da ita acan Amma dai Ni Kam a sauyamin gida musamman farhat da lalurorinta sunyi yawa yau ciwo gobe lafiya....
Cikin mamaki,takaici da baqin ciki daya Gama kashe afia tabude Baki tace"
Mum shin akan abindake gabanki kika watsar da 'yayanki musamman Yar qanqanuwa Kamar farhat harkina cewa lalurarta yayi yawa?
Ciwone fa atareda ita Wanda Allah ne ya Dora Mata ba ita tadorawa kantaba, badan NURU ba da yanzu dukkanin mu munshiga wani hali and now kina cewa akoreta?a koreta kokuma mubita can mu zauna kenan kin yafemu?
Mum inasonku keda dad duka saidai I'm sorry to say this to you yau nafi son dad ayanzu fiyedake da duk wani tunaninki Dan kuwa koba komai shi yasan haqqinmu 'yayansa akanshi Yana bamu Dan haka mum tunda haryanxu Bakida mijinki da yayanki aranki inaga zaifi idan na karbi hakan na runguma nakuma amince Dan kuwa na tabbatarda dana amince da hakan tuntuni da bazan cutatu hakaba,
Na lalata rayuwar mutum uku sbd hope din Zaki dawo saidai Ashe mafarkinane kawai....hawayen baqin ciki me tsanani ne suka gangaro Mata ta kashe wayar da qarfi tareda wurgi da ita sbd Jin mum din na cewa"
Afia ke yarinyace haryanxu bazaki ganeba Dan haka please don't call again idan Baki shirya daukan abubuwan dazan fada mikiba.
Kuka me qarfi ta sake tareda daukar wayar taqara kwadawa da qasa tana qoqarin sulalewa qasa cikin kuka taji hannuwan dad dinta duka biyu ya riqota Yana kallon kyakkyawar fuskarta ya girgiza Mata Kai ahankali ya bude Baki cikin muryarsa me nutsuwa da dadin sauti yace"
AFIA MALEEK karki manta ke 'yar maleek ce jikar kaleeb our beautiful and brave lioness and you know wat thats means right princess??
Da jajayen idanuwanta ta dago ta kallesa zatayi mgn yace"
Ya Isa haka banason Jin komai all I want from you shine ki maida hankali akan karatunki ki Gina career dinki da kanki.
Sakinta yayi tareda juyawa zai fice saikuma ya dakata batareda ya juyoba ya bude Baki wannan karon cikin cikakken iko da bada umarni cikin sautinsa me daidaita nutsuwarta yace"
Wannan shine Karo na karshe daza'a Kuma maganarta acikin gidan Nan.
Karo na karshe.
Gyada Kai tayi tana sawa ranta batada uwa araye daga yau itama sbd dukkanin inda take tunanin mum dinta yau ta kai limit Dan Bata taba daukar uwa zata iya yafe har yayanta ba datake ikirarin Bata buqatar farhat sbd tacika ciwo, wannan kalmar ta rusa duk wata sauran hope datake dashi akan mahaifiyarsu.
Fitowa tayi tana shigowa Palo ta tararda farhat zaune apalon tana kallon cartoon cikin walwala abinta tana ganin afia din tasake murmushin farin cikin ganinta tana cewa"
Afia bakije makaranta ba kina inane tun dazu?
Aunt NURU ta tafi ta dauka kintafine.
Kasa magana afia tayi tausayin qanwarta me tsanani na shigarta har batasan sanda hawaye suka ciko Mata idoba suna gangarowa ta qaraso ta zauna gefen farhat din tareda rungumeta jikinta tanajin tsananin so da kaunar yarinyar tareda tausayinta,tayaya uwa zatace Bata buqatar 'danta sbd wani ciwo na harbawa da Allah ya sako Masa,
Ta Yaya mum dinsu zatace Bata buqatar farhat?
Kamar farhat din tasani saita lafe jikin afian batace komaiba hawayen afian Bata sauka kan jikinta sun Jima ahaka kafin Afia ta zame tareda Miqewa yayi daki ta rufe kanta tana wani irin kuka me ciwo da baqin cikin rayuwa,
Babu abinda Allah be basuba najin dadin duniya sai rashin uwa tagari da soyayyar uwa da Basu samuba kwata kwata,
Suna cikin ni'imar dukiya me yawa,
Mulki na sarauta me girma,uba nagari da soyayyarsa,ilimi na Boko Dana addini,kyawun jiki Dana fuska taredana zuciya daidai gwargwado Amma uwa Basu samu komai daga garetaba bayan dawainiyar daukan ciki da haihuwa duk cikinsu Babu Wanda yayi shekara yanashan nononta take zaresu tabarwa masu aikisu sune komai nasu tayaya zasu qarar da soyayyar uwa.
Sai yamma NURU tadawo tun apalo ta sake tabbatarda farhat ta warware Dan da gudu ta tarbeta suka fada kan kujera cikin murna take bawa NURU labarin yau dad yafita da ita Amma Basu dadeba suka dawo.
Miqewa NURU tayi tana cewa"
Iyye yau Daddy ya kyauta Mana sweetie taje yawon datake so.
Duk da haka fa aunt NURU alqawarin mu Yananan fa dakikace Zaki kaini yawo har wani qasa daban.
Hanyar daki suka nufa tana cewa"
Eh banmantaba saina gama karatu idan zanje Vegas attaching papers Dina na Gina career Dina dake zanje Inshallah sweetie.
Tsalle tasaki tana cewa"
Yes yes my Lewa
Suna shiga daki afia na zaune tayi wanka sanyeda gajeran wando da shimi tana aiki da laptop tana ganinsu ta sake fuska tana cewa NURU"
Welcome baby.
Thank you princess"NURU tace tana zare kayan jikinta tana fadawa Afia zancen dasuke da farhat suna dariya.
Wanka tayi tazo yayi sallah ta Sanya qananun kayan Shan iska itama tasha coke daya ta Dan kwanta sbd ta Dan gaji Kuma batajin yunwa Dan taji snacks a wani coffee shop.
Tana bacci wayarta tadauki ringing afia dake zaune ta kalli wayar saitaga sunan padima.
Murmushi tasaki sbd tasan padima abakin NURU Amma Basu taba gaisawaba Dan haka ta dauka Kai tsaye tareda cewa"
Assalm alaikm padima ānichī gini inidēti neshi? (ya kike ya gida/hw are you doing and family).
Tsit padima data Kira da Dan qungun kukanta tayi Jin muryar afia wadda takeda tabbacin itace 'yar maleek da ake fada Dan haka saita Dan saita murya cikin girmamawa da kulawa da sautin muryarta daya tabbatarda tayi kuka tace"
Lafiya kalau alhmdlh li'iliti.
Ya karatu da hidima?
Murmushi me sauti afia tayi tace"
Ba hidima saidai karatu shima munatayi inshallah munkusa gamawa, NURU na bacci yanzu saidai ko Zaki sake Kira anjima kokuma idan ta tashi saina fada Mata ok?
Dan kame kame padiman tafara tana cewa"
Eh baza'a tada ita bane yanzu da magana zamuyi me mahimmanci ne?
Kai tsaye afia tace"
Aa baza'a tashetaba yanzu dai lokacinda ta tashi dakanta kokin manta Matar maleek ce?
Koma yayane bazan tashetaba saita tashi da kanta matuqar ba lokacin sallah bane kawai ya isa yasa na tasheta sai idan dad ne dakansa yake nemanta which kuma is not possible for now dai.
Wani Abu padima taji yataso Mata kamar zata ashararo ashar ta danne tana cewa" Sabala ibilis cikin ranta.
Wato NURU har matsayin nata yafara kaiwa haka tun wuri.
Jin shiru yasa afia cewa"
Ko da akwai matsale ne a gida?
Kifadamun zanyi maganan da ita idan ta tashi.
Shiyafi komai sauki 'yar maleek padima tafada cikin ranta tareda sauke wani wahalallen numfashi tana karye murya zuwa rawa rawar son kuka tace"
Dama nafada Mata maganar rashin lafiyan danake fama dashine abin yafara tsanani anyi magani anan gida baiyiba shine tace zata kaini Inga likita anan ko za'a dace.
Da mamaki a bayyane afia tace"
Anan Kuma?
Tun yaushe ne ciwon?
Tsawon shekara"padima tafada tana hawaye.
Gyara zama afia tayi tana cewa"
Shekara daya ciwo ajiki shine NURU Bata taba fadaba.?
Menene matsalar?
Ciwon zuciyane yanzu nakai Ina amai da tarin jini wani lokacin.
Innalillahi padima meyasa bakuje ko English hospital na can ba.
Shiru padima tayi tana hawaye da shehekar data sake bawa afia tsoro tafara Mata tambayoyin akan yanda takeji da kalar jinin datake gani tana nazartawa da 'dan nata ilimin na likita da Bata qarasa zamaba.
Girgiza Kai tayi cikin jimami da tausayawa tareda tsoro tace"
Padima this is serious yakamata kiga likita cikin gaggawa gaskia.
Kuka padiman tasake fashewa dashi tana cewa"
Bansan Yaya zanga likitaba Dan Allah li'iliti ki taimakeni NURU takasa taimakona banason na mutu yanzu.
Ki taimakeni ki kawoni gurinki ki kaini gurin likita Dan Allah.
Shiru afia tayi ciki rasa sanin abinyi Nan take Sadai koma menene batada ikon kawo padima Nan take Dole saidai NURUn ce zatace akawota tukuna akawota din sbd kawo mutum Kai tsaye gidan MALEEK wani aikine Dan kuwa sai ankaita gizah an tantance kafin akawota gidan MALEEK Wanda yanzu Kam NURU ce kawai takeda ikon kira gizah tafada tanason akawo Mata padiman.
Ajiyar zuciya ta sauke tareda nutsuwa cikin son fahimtarda padiman tace"
Kiyi hkr padima Inshallah Zaki samu lafiya Amma yanzu dai Ni inshallah zan nema appointment na babban likitan da Zaki gani anan Amma maganar zuwanki zanyiwa NURU magana idan ta tashi saita Kira inda za'a kawo ki anan din.
Nagode sosai Allah yaqara girma ina gaida NURUn idan ta tashi.
Katse wayarta tayi tareda wurgi da ita tana jerowa daga afia din har NURU zagi sbd Sam sunqi hawa yanda takeson suhau su rikice da tausayinta yazama basa tunanin komai saina tausayinta tasamu Isa qasar.
##MAMUH#
0 comments:
Post a Comment