*Chapter 1*
*GOMBE*
"""Ababban masallacin dake anguwan nan ta masu hali,wato *FEDERAL LOWCOST* Motocine suka cika anguwan Tundaga farkon farata har karshenta,layin mallacin kuwa babu matsaka tsinke saboda yadda motoci suka hada uban gowslow,kana kallon wajen zaka tabbatar da tabbas wani kusane agawannati yake Aure yau,dayake ranar takama Ranar karshen sati ne,wato asabar,Abunda zai baka mamaki,sojojin kasa ne wato army birjit awajen sanye da kakinsu suna mazurai,gefe daya kuma yan sanda ne,suma kamar anyi hayansu,sai gyara parking suke.
Tawagar ango ce tafara isowa cikin hadaddun motocinsu na alfarma Kirar venza2019,sai 306 kirar toyota,607kirar toyota,sai Benz,bayansu kuma motar sojojine,suna tafe da jiniyansu bindigogine ahannunsu da bulalai suna wani zare ido,Abun tsoro,tuni jama"a Aka dinga darewa domin kowa na tsoron ya gifta soja ya fallamai dorina wacce kila sai ya kwana goma yana jinya bai warke ba.
Motocinsu basu gama tsayawa ba,jiniyar motocin mai girma Kwamishinar jahar Gombe tafarayima mutane maraba wato *CP AHMED SIDI NA IYA* Tare da tawagarsa,suna zuwa suka faka motocinsu nan da nan yan sandan dake biye dasu suka hau bude musu motocin suna bayyana,tabbas inda ake biki chan ake,domin manyan mutane ne,suke Fitowa cikin shigata alfarma,dukkansu sanye cikin wasu dakakkun shaddodi gezner suna daukan ido,da hulunansu zannah bukar,suna fitowa basu tsaya wajen mutane ba,suka shiga cikin massllacin bayan an buda musu hanya,yan jaridu kuwa sukayi yamm dasu suna kokarin, sonjin ta bakin kwamishinan ammh masu tsaranshi basu bada damar haka ba,kakkaresa sukayi har ya danganta da cikin massllacin inda waliyan ango da sauran manyan mutane,harda babban limamin masallacin,suke jiransu domin Daura Auren
*JABIR* ya kallesa ganin yadda yawani kishingida kamar yana kwance adakin matarsa yace"Mallam wai bazaka fito bane,kaga fa maigirma kwamishina ya iso,yanzu za"a daura maka ka Aure ka tabbata miji ga *NI"IMATULLAHI AHMED SIDI NA IYA..* "Yafada lokacin daya yana leka kansa cikin gaban motar...
Yafi minti goma bai dagoba kuma baiyi mgana ba, *HAISAM* ya gyara tsayuwa yana fadin"Kaga captain zo muje rabu dashi,Kila bai da ra"ayin isa cikin masallacin ne,mu muje saboda mu muntunta abotaka da kuma zaman tare.."Yafada daidai lokacin da suka Fito daga motar dukkansu,mazaje ne dogaye majiya karfi,kallo farko in kayi musu zaka fahimci tsantsan ilimi da wayewa ya ratsatsu,Kyawawa ajin farko ne,daka kallesu sai kara kallonsu saboda yadda suka dau wanka,cikin wani Ubansu yadi,mai ruwan kasa,wanda yanayin yadda yake yarari kadai ya isa yafadamaka sai da aka tada kai akayi iya mallakarsa, kafafunsu duka sanye da wani Brown din takalmin na fatar damisa,ayayinda kansu ke sanye da hula zannah bukar,kuma dukkansu dasame dressing ne ajikinsu,in ka gansu daga nesa kamar wata daren goma sha daya saboda yadda suke haskawa.
Ganin da gaske suke,basu jira cewarsa ba,suka dumfaru cikin masallacin domin Saura Dan mintocine adaura auren,yan jarida daga nesa suke hangosu,domin sojojin sunyi musu katanga tsakaninsu,to soja babu wargi dole sukayi gefe,Cikin wani takama da aji ya sanya tattausan hannunsa mai cike da gargasa wanda ke daure da wani royal watch mai kyau da yarari, ya bude murfin motar ya zuro kafarsa wacce ta kasance farace,ammh tana da Launin ja,kafar nasa tana sanye cikin wani ubansu Rufaffan takalmim brown colour na fatar damisa,kafar nasa itama tana cike da gargasa domin gayinan yayi kwance luf dashi,ban saki da al"amarin gayen ba,sai da duka jikinsa ya bayyana awaje,bansan sadda biron dayake hannuna ba ya subuce saboda yadda girma da haiba tare da wani kwarjini suka dakeni lokaci daya.
tsarki ya tabbata ga Allah wanda yayi wannan kyakyawan halitar,dogon mutum ne,karkafa mai yalwal Fadin kirji da girman jiki kamar ingarma,fari ne tas,mai Launin ja,Hancinsa har baka yake,mai zagaye da wani bakin Saje wanda ke karamai kwarjini da haiba, kwayan idonsa tamkar wanda aka digamai daimond,saboda yadda yake wani haskawa,Yana da manyan idanu,matsaikata,wanda in ya lumshe su,sai ka zata yayi kari,wa gashin idon nasa,don ko wata mace albarka..,bakinsa dan karami ne,wanda ke dauke da wasu pick din lip masu kyau da burgewa,Kansa yana nannade dawani murdadden bakin gashi kamar wanda yayi kari,Ko fuskarsa badon yana yawan askewa ba,akwai kananan gashi da sukayi mai kwamce,Shima din sanye yake da yadi mai ruwan kasa,irn na abokansa,hatta dinkinshi iri dayane sai dai Shi harda babban riga,Hulan kansa ma irin nasu ne,sai da yadda kayan ya amsheshi dabam ne,Kana kallonsa zaka fahimci mai karfi ne shi,saboda yadda mucsles suke yawo ajikinsa,har ana iya ganinsu,Kana kallon Fuskarsa zaka Fahimci yana da miskilanci da wani irin takama,yana da jan aji,ayanayi yadda yake wasu abubuwa sai ka dauka wani basarake ne,saboda komai cikin isa da iko yakeyinshi,baka iya hada ido dashi saboda yana da bala"in kwarjini babu wanda ya taba kallon tsabar idonshi na tsawon minti biyar ,saboda baiwace Allah yayimai mutane dadama basu iya kallonsa ido cikin ido Saboda yadda kwarjinshi yake tasiri azuciyar mutane.
*CAPTAIN ALIYU ABDULNASEER TAMBARI BUZU* kenan,kuma COMMANDER YAKI,wanda ke jagoranta bataliyoyin sojoji kashi da kashi zuwa filin daka,ko wani kwantar da tarzoma,Wanda ko afagen fama makiya tsoronsa sukeji,matashin Sojan kasa ne wanda ke aiki a barikin Kaduna wato 1division Nigerian Army kaduna,ko abokan aikinsa sun san waye Aliyu Tambari buzu saboda kwazonsa ga aikinsa ko manyansa ma,suna shakkarsa tare da jinjinamai domin kaf bacth dinsu babu na biyunsa ajajircewa da nuna jarumta...Sai da yawani jingina da kofar motar kafin ya dan Saki Fuskarsa ya fara takawa cikin takun nan nasa na isa da takama,sojojin dake karkashinsa sai kokarin karesa suke har ya samu nasaran Shiga cikin masallacin,kusa da Haisam ya zauna,wanda ke zaune kusa da jabir,gefensa kuma *MALLAM LAWAL BATURE* ne kafin kuma *KAWU BALA* dake gefensa shima cikin Shigan kayan alfarma.
An matso domin fara gudanar da Daurin Aure kani ga kwamishina ya kira kwamishinan gefe suka danyi wasu mganganu Tunda kawu bala yaga haka, sai ya sha jinin jikinsa,yana fata wannan karon kada ayi musu gagarumin wulakanci da zasu kasa mantawa dashi,suna dawowa Sai kani ga Kwamishina ya kalli kawu bala yace"Ina waliyan ango su matso kusa adaura aure.."Yafada yana kallonsa batare da wani Tunani ba kawu bala ya matsa yana fadin"Gani,ai inaga basai ka tambaya ba,tunda ko neman Auren wajenka na neman ma Aliyu.."Yafada Shima kai tsaye.
Bude bakinsa sai cewa yayi"waliyin ango nace,ma"ana Waliyi daga *DANGIN MAHAIFINSA* bakai ba.."Gabadaya kawu bala yaji miyan bakinsa ya kafe,dayake mganar bata karfi akeyinta ba,su Aliyu dake gefe basu wani ji,su azatonsu Ana gudanar da Daurin Auren ne,Kawu bala ya kalli mallam lawal kafin yace"Eh to ai mun fadamuku Dangin Mahaifinsa basu akusa,Shiyasa muka gudanar da komai.."Kwamishina ya murmusa kafin yace" *BALA SHEHU AKARAMI* Shine cikakken Sunanka,kuma kaine kwamishinar yada lbrai NA ajahar kaduna,kuma kai yaya kake ga mahaifiyar Aliyu,Tunda kuka gudanar da neman Aure bawani daga dangin baban yaran,kenan ya tabbata da gaske bashi da uba,Balle Asali.."
Arazane kawu bala yace"Haba Ranka yadade wani irin mgana ne,haka baya da uba daga sama ya fado,kaga mubar wannan mganar,adaura Auren Allahbarshi bayan angama sai muyi mgana.."Yafada cikin alamar roko,kani ga kwamishina yace"Sam wannan mgana bamai yuyu bane,bazamu bada Auren diyanmu ga bara gurbi ba,matukar wani daga halin mahaifinsa baizo ba,to an fasa Daura Auren kowa ya watse..'"Ai sai waje ya kaure da hayaniya tawagar Kawu bala sunata maganganu Mallam lawal ya rike kafadan bala alamar lallashi.
Kawu bala yakalli kwamishina yace"kar kayi haka Ranka ya dade ka duba girman jama"an daka tara,dawanda ni na tara,da wanda Shi yaron ya tara,kabari adaura auren nayimaka alqawarin koma miye daga baya sai muyi mgana,don Allah na rokeka..."Yafada harda hada hannu,ammh sai kwamishina ya girgiza kai ya mike,liman dake zaune yana fadin"Subhannallah wai mike Faruwane,kada kubari Shedan yayi Tasiri akanku,yahanaku kullah Alheri mana.."Ammh ina Tuni kwamishina da kaninsa da nasu tawagan sun Fice daga massllacin kawu bala ya bisu da kallo kamar ya zubda da kwallah,babu wanda yake Tunani sai *SUWAIBA* yazataji in tasamu wannan lbrin ta Aliyu mai sauki ne.
Tuni Su Jabir dake zaune suka fara Fahimtar Abunda ke faruwa,tun sadda su kwamishina suka mike,arazane Haisam ke kallon Aliyu wanda yayimai kuri da ido yana kallonsa kafin yace cikin wata murya mai cike da amon tashin hankali..'Haisam meke Faruwane,fata dai ba Abunda nakeji bane ko? yafada yana kafesa da ido,bai samu zarafin bashi amsa ba kawu bala ya kalli jabir yace"Ku sanar da jama"a anfasa Daurin Aure,kowa yakama gabansa..."
DAM!zuciyar Aliyu ta buga Kuri yayima kawu da ido kafin yayi mgana Mallam lawal bature yace"A"a bala,baza'a yi Saurin sanar da haka ba,Duk wanda yake kokarin tonama wani asiri Allah bazai barshi ba,yanzu za"a Daurama Aliyu Aure anan wajen Insha Allahu.."Dukkansu ido suka samai kafin Kawu bala yace"To dawa,lawal?kana ganin fa wulakancin dasukayi mana..?"
Mallam lawal yace yana kallon Aliyu kai tsaye yace" Da..,Da.. *AZEEMA* za"a Daura in ka yarda,saboda babu dadi atara wanan jama"ar kuma ace musu anfasa Daurin Aure,hakan bai dace ba,shiya...'.Zuruf Kawu bala ya mike kafin ya damko hannun lawal yana fadin'Ku zauna mu dawo.."Yafada yana kallon jabir,ficewa sukayi zuwa kofar mallacin,nan suka ga yadda rabin mutanen suka watse,ammh wasu sun tsaya sai sunga kwal uwar daka,gefe kawu bala yajasa kafin ya ciro wayarsa yana fadin"bari na kira Suwaiba..'yafada daidai lokacin dayake kiran ta.
*************
Biki yayi biki,gida babu masaka tsinke,tana zaune *MADINA* ta shigo da waya ahannunta tana fadin" *GOGGO* gashi Daddy ne ke kiranki.."amsa goggo tayi tana fadin"Kila An Daura auren ne,kai Allah na godemaka gadanga yazama magidanci yau.."Tafada tana dariya lokaci daya tana daukan kiran da fadin"Assalamu Alaikum yaya..."dagachan bangaren ya amsa mata da fadin",Suwaiba..."Yadda yakira sunan natane,sai da gabanta ya fadi ta amsa bakinta na rawa kafin tace"Lafiya kuwa yaya? kowani Abun ne ya samu gadanga...? ajiyar zuciya ya sauke kan ya cigaba da zayyanamata Abunda ya faru cikin sauri yace"Za"a Daura mai Aure da AZEEMA diyar mallam lawal yan...."KU DAURA YAYA YANZU NAN DON ALLAH...."Ta fada cikin kuka kafin tacigaba da cewa cikin Fushi.."Ni dana ba Shege bane, yana da tarbiyar da diyarsu bata dashi,ku gudanar da komai haka Allah ya rubutu..."Tana gama fadin haka ta katse wayan tana share kwallah.
Basu tsaya bata lokaci ba,suka koma cikin massllacin sukayi mgana da liman cikin minti kadan Kawu bala ya fito da sadaki ya mika ma liman yana fadin'"Kayima Azeema walicci.."Babu bata lokaci akace amatso za"a Daura Aure,kafin kace me Tuni an Daura Auren *CAPTAIN ALIYU ABDULNASSER TAMBARI BUZU DA AZEEMA LAWAL BATURE* Akan sadaki mafi daraja,nan da nan maroka suka fara Shedan suna fadin"Allah kenan baya tsallake Abun da ya rubuta,Daurin Aure dai ya chanza,maimakon Ni"imatullahi yanzu Azeema ce mai sa"a Domin itace ta kasance mata ga Dan matashin Sojan,Allah kenan komai ya faru da saninka,kuma da izininka.."Suke fada suna shela,tuni waje ya hautsine kowa tambaya fal cikinsa,tun lokacin da tawagar kwamishina suka wuce batare da Dan Daura aure ba.
Captain Aliyu dayayi mutuwar zaune kansa aduke har akagama Daurin Aure bai dago ba,sai jabir ne,ya riko kafadansa yana fadin"Captain kayi ha..."Bai karisa ba yadago kansa idanunsa sun chanza kala jijiyoyin kansa sun Fito radau yace" Sunce baza su bani ba ko? bani da uba ,kamar yadda suke fadi..."Yafada kamar zai kifa saboda yadda kirjinsa ke tasawa,bai kara mgana ba,ya mike da sassarfa ya fice daga masallacin Da hanzari Haisam da jabir suka rufamai baya,yana Fitowa yan jarida sukayi cha suna watsamai tambayoyi wanda suke kara tunzurashi ai yana daga dago kansa ya daka musu tsawa yana fadin"Get Way from my Side..."Yafada afusace yana buga kafa kamar afilin daga,kamar mazari haka sukayi baya suna rawan jiki sojojin dake wajen da hanzari suka kame,ko kallonsu baiyi ba,ya nufi motarsu da suka zo acikinta Ya fada,ko kafin su Haisam su kariso yajata ya fice da wajen dawani mahaukacin gudu,dafe kai Jabir yayi yana fadin"Innalillahi..kada fa Aliyu ya kashe kansa,in yayi irin wannan Fushin fa sai Allah.."Haisam ya damke hannuwansa duka akirji yana fadin"Allah kawai ya kiyaye,ammh ina tsoron Fushin Aliyu kam.."Juyawa sukayi suka koma cikin wajen suna gaisawa da bakin da suka tara,haka suma su kawu bala cikin Farinciki da mura suke gaisawa da mutane suna musu godiya kamar babu Abunda yafaru,yan jaridu ko Haisam ya sallame su dole suka tafi,tunda bazasu samu Abunda sukaso suji ba.
Cikin wani Fushi yake Driving din Allah ne yakaisa *KAGARAWAL* lafiya Da wani banzan taka burki yafaka motar akofar gidansu dake cike da jama"a yan biki cikin Fushi da Wani karfi ya ture murfin motar ya fito yafara taku zuwa cikin gidan jama"an dake waje suka bisa da kallo,Azeema dake kokarin Fitowa zata koma gida,batama kalli gabanta ba,sai ji tayi anyi baya da ita an maidata zauren gidan,Cikin Tsoro Ta bude baki zata yanka ihu ya dakamata tsawa"Ke Shout up..."yafada yana zare mata ido,jin muryansa yasa jikinta yafara zikiri Bude ido tayi tana binsa da kallo yadda naman kirjinsa ke dagawa,ai sai Azeema taji wani Fitsari na neman kubcemata saboda tsoro cikin Tsawa yace"Ina Goggo take...? Dakyar bakinta na rawa tace"Ta..Tana..dakinta..."Tafada wasu hawaye sun zubomata sakinta yayi bayan ya tureta gefe ya wuce fuu kamar kububuwa.,Saura kadan tafadi sai ta ta dafa bango kafin ta tsaya da kafarta,tana ganin ya wuce ta rumtuma da gudu ta fice daga gidan,tana sauke ajiyar zuciya domin daman Duk duniya babu wanda take tsoro irin *YAYA CAPTAIN*
Shiko yana Shiga gidan akayimai chaa ana fadin'Ga angon Ni'imatullahi nan,gadanga kusar yaki,Ba gaba da gaba ba,ko ta bayan sai gwarzo..."Wani haushi ya tokaresa bai bi takansu ba yafada dakin yana fadin"Goggo..Goggo.."Goggo dake cikin daki tayo falo tana fadin"Gani Gadanga lafiyanka kakemin wannan kiran? tafada idanunta sun kada alaman tasha kuka,baiyi wata wata ba,kawai ya zube gabanta yana fadin"Don Allah goggo kifadamin wayeni?,da gaske nidin Shege ne bani da uba,goggo don Allah ki fadamin kota haramtattaciyar hanya kika same...."KAYI MIN SHURU ALI..."Goggo ta katseshi rai bace tana huci kallonta yake yaga yadda ruwan hawaye ke zubomata tace"Ka tashi kafice kabani waje.."Tafada tana nunamai kofa,Tsam yayi yana kallon goggo kan yace"ammh gogggo...'Ka ficemin daa gani nace ko Ali.."Tafada cikin wani Fushin,Baiyi gaddama ba,ya mike tsam yana wani mazari kafin ya kalli goggo kamar zaiyi mgana sai kuma ya fasa kawai sai ya kada kai yafice daga dakin,ya fada nasa dakin bayan ya rufo kofan yanaji kamar ya dauki gidanan akansa ya dinga yawo dashi saboda yadda wani zuciya tare da karfi ke zuwarmai lokaci daya.
Mutane sukayi Tsuru suna kallon kallo,share hawayenta Goggo tayi kan tace"Acigaba da shagalin biki,babu komai..'Tafada kafin ta koma cikin daki,madina da Mardiyya suka kalli juna,suna fatan Allah sa lafiya, *RAMATU* kuwa da diyarta Shalelenta *AZEEZA* Suka kalli juna cikin sonyi gulma ammh babu dama,Ramatu ce keta kunshe dariyarta tanama diyar tata sigina da ido,suna kallon dakin da goggo ta shiga suna Dariya kasa kasa...
_*Topha,kunji fa yadda Abun yake,kanku ya daure,kun samu rashin Fahimta ko? Hhhhhhh haka janafty tace kowani book dinta tafe yake dawani salo na dabam,kuna so,kuna bukata,to cike Tagging dinki da HOT COMMENTS .."Nikuma zan himmatu da kokari wajen baku update..Oneluvs Janaf fans*_
#Comment,share and vote#
#Janafty.....#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of yuong soldier man)_
Wattpad:Janafnancy12
*Hakkin mallaka:Janaf*
*DEDICATED TO MY MOMMAH...,HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘,Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent writer's asso*✏
_Dis NOVEL is not for sale,plz masu bina pc suna tambaya na siyarwane,nawa zasu biya suyi Rigister,So Cool ur mine Aliyu Gadanga is a special gift to my Real Dota RAHMA😘and my mommah shiyasa yazama Free,what are u eating na baka is zubowa kasa,😂Na kudinfa na nan tafe,tunda naga da gaske kuke u what me to become HAJIYA JAMI😂Tanque very much my Real Fans,and a big Tanque to does prople for dere hot comments,Love u Tin Tin😍😘_
*NOT EDITED*💥
*Chapter2*
"""Gidan bikin sai yakoma gidan gulma da tsegumi,sai cecekuce akeyi kunsan mutananmu,sufa basu raina Abun gulma balle wannan dasuke jiran kiris,itako goggo tana daki tana kuka duk lokacin Data tuna kalaman Aliyu saitaji kuka na kawomata,madina ne ta shigo dakin taga halin datake ciki,ita takira mardiya suka zo suna ta bata baki,nan nema take fadamusu Abunda ya faru,dafe kai madina tayi kan tace"Oh mardiya,mutane ba kyau,to ai Shikenan Allah ma ya sakamai da wacce tafi figaggiyar ni"imar ma,don Azeema tafita komai,uwa uba ga hankali da tarbiya"
mardiya tace"Kwarai ma ko goggo,kibar damun kanki,donta Captain ne,lokaci kadan ne,zai warware.."Suka fada suna kokarin kwantar mata da hankali,dakyar tayi shuru kafin ta wanko idonta ta fito kamar ba ita ba,Ramatu ko da Aziza sunyi iya yinsu su Fahimci meke faruwa ammh Basu samu dama ba,shiyasa suka kara gyara zama har sauran tawagan Daurin Auren su dawo kila sasamu wani lbrin daga barayinsu,duk da tasan mallam ko zata mutu bazai fadamata ba,tunda yace tana da rariyan baki..
*****************
Ni'imatullahi tana zaune cikin kaawayenta acikin Shiga ta alfarma sanye take dawani ubansu material mai tsada da yarari black and red an mata wani Fitinanne Dinki ajikinsa kanta kuma an dauremata shi da head baki,fuskarta cikin makeup mai kyau da tsari,Ni"ima gajera ce,bata da tswao ammh tana da kyau sosai domin Farace sosai mai dauke da faffadan Fuska tare da dogon hancinta,tana da jikin mata babu laifi kam ko"ina ya cika,kallo daya zakamata kasan ta fito daga gidan hutu,saboda yadda fatar jikinta ya tsumu ajin dadi,kallon idonta kawai zakayi kafahimci tana da mugun wayewa da budewar idon yan matan zamani sakamakon kaf bayan Primary bata hallarci wata mkranta a Nigeria ba,kasar waje tayi rabi da kwatan Rayuwarta.
Cikakkun kawayenta yan Duniya ya"yan masu dashi,harda diyat gwaannar jahar gwambe mai ci alokacin Falon dai cike da yan gayu na bugawa ajarida,sai shewa ake ana zolayan Ni'ima da fadin Anrigaya da an Dauramata aure Da Captain din nata,kamar yadda take kiranshi,itako sai wani Smiling take,tana wani washe hakoran jin dadi,duk sanda suka ambaci an Daura mata aure da captain dinta,suna cikin wannan Halin ne,wayarta kirar Samsumg gallezy tadauki kara cikin wakan nan U ARE MY LIFE.."Da hanzari ta sanya hannu ta jawota dama tana kusa da itane, LOVELY MUNARI..."Tagani dan tsaki taja don azatonta angon natane Kawartace babbar aminiyarta ma kuwa,wacce fitanta kenan daga falon ta sauka kasa zatayi mgana Da MAMINTA.
Dagawa tayi tana fadin"Ya how far...? Cikin wata murya Munari tace"Swhrt ki sauko kasa yanzu don Allah.."Sororo Ni"ima tayi kan tace"In sauko kasa kuma?uban me zanyi miki in na sauko,kinfa san yanzu matar Aurece ni,so taku daya in zanyi sai da izini in ba haka ba,in Shiga cikin Fushin Allah.."Tafada cikin nuna iya gaskiyarta kenan,Kai munari takama tana kallon yadda falon ya hargitse tun Shigowar Abbah falon da lbrin da suka zo dashi tace"Oh my God..Swhrt kibar mganar nan,ki sauko kiji.."
Tsaki Ni'ima taja kan tace"mtsewww...Bazan sauko ba,in bazaki fadi Abunda ke bakinki ba to rike kayanki,sai kin hauro.."Tafada tana kokarin yanke kiran"Ajiyar zuciya munari tayi kan tace"Yanzu su Abbah suka dawo..,"Da hanzari Ni"ima ta daga tsalle tace"Da gaske,shikenan na zama matar Aliyuna,plz Friend kutayani murna na zama matar my Captain.."Tafada tana dariya gabadaya falon suka saka mata ihu da tafi,Munari ta dafe kai kan tace"Ke baki da hankali wlh,baki iya tsayawa kiji zence,ba to Abunda nakeso na fadamiki su Abbah sun dawo kuma ba"a Daura Auren ba.."
Wani Abu mai Nauyi Ni"ima taji ya tsaya bisa kirjinta cikin wani yanayi tace"ban...ga..ne...ba..?"Tafada cikin rawan murya Munari tace"Haka Abbah yace,an fadamiki an dakatar da Daurin Auren sakamakon haryanzu ba"a ga wani daga dangin mahaifin Aliyu ba,shiyasa Abbah yace bazaya bada Aurenki ga wanda ya tashi gaban mace ba,wanda haryanzu ba"a san asalinsa ba."Ihu kawai Ni"ima ta yanka ko kafin ayi wani Abu ta zube kasa Warwas bata numfashi da gudu kawayenta suka rufu kanta suna Kiran sunanta da hanzari wasu sukayi kasa suka kira mami,wanda tanajin Abunda ya faru ta dora hannu akai,tana fadin"Na Shiga uku ni Hadiza,dama sai da nafada kwamishina wlh Ni"ima bazata iya rayuwa babu Aliyu ba,kada yayi haka,kada ya aikata haka,to gashinan dai Ga Abunda nake gudun nan ya faru.."
Take ta fada tana,kuka,kwamishana na gidan da hanzari aka tarairayeta aka wuce da ita asibiti ba yarda take,ai sai gidan biki yakoma gidan kuka,da gulmagulmace,tuni kawayen Ni"ima suka kama gabansu Munera ce kadai wacce da ita aka tafi asibitin, *FEDERAL TEACHING HOSPITAL GOMBE*kowa yaji ba"a Daura aure ba,sai ya Shiga mamaki yana neman jin dalili,Kafin kaceme gida ya watse sai mutanen daba"a rasa ba,wanda dama sun kasance Shakikai ne,ga kwamishina din da kuma Mami Hajiya hadiza.
Wannan kenan
________________
Sai da Su Kawu suka gama sallaman bakinsu kafin su yi ayari Shida tawagarsa da tawagar angon suka nufi gidansu Aliyun,don kawu yace Sauri yakeyi yau din yakeso yakoma Kaduna,har cikin suka shiga suna gaisawa da mutane Hajiya Umaima mata ga kawu Bala wacce suka kira Da Umma ita ta fito tana fadin"Abban Haisam wai meke faruwa ne? Tundazu goggon yara ke kuka,ga Captain chan ya dawo yana wasu maganganu don Allah wai meke faruwa ne?
Dan mirmishi kawu yayi kafin yace"Bakomai Umaima mushiga daga ciki,mallam Shigo kaima don Allah.."jin haka sai gabadayansu suka dumguma zuwa cikin dakin,Ramatu da Aziza jikinsu haryana kyarma suka rufamusu baya,saboda suna so suji kwakwam,Suna Shiga kawu yasa baki ya kira Gaggo ta fito tana musu sannu da zuwa,Kallonta yayi kan yace"Suwaiba meyasa haka? don Allah kiyi kokarin danne damuwarki,domin kibawa Aliyu kwarin gwiwa,bafa wani Abu dama Allah ya kaddara Ni"ima ba matar Aliyu bace Azeema ce matarsa.."
Da hanzari Hajiya Umaima tace"Bangane ba,da wata Azeema aka Daura aure..'?Kai tsaye yace mata"Diyar mallam lawal,shi ya taimakemu ya fitar damu kunya,da bamusan ya zamuyi da tarin jama"ar damuka tara ba.."Ramatu dake gefe ta zaburo tana fadin"Da wata diyar mallam lawal din aka Daura Aure? badai Diyata bako? na Shiga uku ni Ramatu kowa na raba kanshi da hada zuru"a da mugun iri wanda ba"a son Asalinshi ba,ammh kai..."Ke Ramatu.."Mallam lawal ya katseta cikin Fushi yace"Dake ake mgana,wlh zan mugun sabamiki matukar nakarajin bakin ki cikin wannan mganar,Ba da yarki dakike kirarin itace taki na Aurama Aliyu ba,da Diyar kwarai wacce batagaji tsiya ba na basa AZEEMA.."Da hanzari Aziza ta dago tana kallon mahaifinta lokaci daya taji wani Abu ua tsaya mata bisa kokon rai tun lokacin dataji anfara mganar an Daurama Aliyu Aure kamar kunninta sai yajiyemata kamar Sunanta ake ambata da an Daura mata aure da Aliyu,alokacin wani farinciki ya mamayeta domin tunda tataso anguwa daya Da Yaya captain amtsayinsu na makota takamu da matsanancin sonsa,duk duniya kowani Namiji abanza take kallonsa,babu wanda takeso da buri yazama mallakinta irin Yaya captain koda take wani Abun,saboda Ramatu ne,karta fahimci inda ta dosa,ammh sai kuma gashi Mahaifinta yakira Sunan Azeema amtsayin wacce aka Daurama Aure da Yaya Captain dinta,lokaci daya taji jiri na neman kwasheta,sai da tarike hannun Ramatu kamkam tana rintse ido.
Ramatu ta mike tana fadin"Oho yanzu naji mgana Ai wlh da da yatace yanzu nan zaku warware aure nan domin bazan hada irin da Da"n mace ba mara asali .."Fita kibama mutane waje sakarya mara tunani.."mallam lawal ya katseta yana nunamata kofa Hannun yarta taja wacce ke wani hali tace"Ko bakace ba, zamu tafi,ammh dai an Fadi ba Nauyi kuma duk wanda yahau motar kwadayi karshensa Tashar Wulakanci.."Tafada suna Ficewa.
Ajiyar Zuciya mallam lawal ya Sauke yanajin wani kunya tare da bakin ciki suna dirar mai lokaci daya dakyar ya iya cewa"Don Allah kuyi hakuri da maganganunta haka take sam bata da Tunani wani lokaci.."Mirmishin yake Goggo tayi kan tace"Bakomai mallam lawal Ai ba yau nake tare da Ramatu ba,ai yakamata nasan hallayanta babu komai kadaina biyemata don Allah,mungode sosai Allah ya saka da alheri bazan manta karamcinka garemu ba,ni da gadanga tun zuwana garin nan kake dawainiya dani,tare da gadanga saboda haka Allah ne,kadai zai biyaka Alherinka garemu.."Takarishe kamar zatayi kuka gabadaya suka shiga bata hakuri,nan kawu bala yace su tattaro suzo su koma gida tunda dai biki ya tashi nan akayi mganar tarewar ita Azeema ammh sai kawu yace abari nan da wani lokaci saboda Samun natsuwar Shi Aliyun,shima mallam lawal din yayi na"am da hakan saboda itama Azeeman yanzu take SS1 a babbar sakandiri,Goggo dai bataso ba,taso kawai Azeemar tatare a shashin da Aliyun ya gyarama Ni"ima,tunda nan zata fara zama,kafin yakoma wajen aiki chan kaduna su tafi tare,ammh babu yarda ta iya,domin bata iya tsallake Umarnin yayanta.
Haisam ne zai bi Su Ummah yakoma gida,domin sunyi sunyi Aliyun ya bude kofa yaki,Ran maza fa ya baci Dole yayi sallama da Jabir yabi su Ummh suka damki hanyar kaduna,dashi dasu madina da mardiya,Jabir kadai aka bari,Sai gobe Sunday zai koma Tunda monday akwai aiki,Dakin Goggo yakoma sukacigaba da tattaunawa akan Batun goggo tana nunamai ita tafi jin dadin wannan Auren,domin dama AZEEMAR yar dakinta ne,nan take komai nata ko kafin ma ayi hakan,shi kanshi Jabir sai yaji zuciyarshi tafi Natsuwa da Azeema domin ya santa sosai yarinyace mai hankali da natsuwa gata da ladabi da biyayyah bata da hayaniya ko kadan,Aliyu dai yana daki kwance,so yake yayi kuka ammh yakasa idanunsa ne,suka kada sukayi jajir,jijiyoyinsa kansa suka fito radau,Lokaci bayan lokaci sai ya naushi hannunsa da bango,goggo ko batabi ta kansa, ba saboda tasan halin dan kayanta,Aliyu gadanga zuciyarsa kamar kuturu in yatashi tsiyarsa sai tafita yammah da hankalinsa kafin suke komawa su daidaita.
**************
Azeema Atsorace takoma gida,tayi zaune cikin dakinsu tana sauke ajiyar zuciya data rufe ido tsawar da Yaya Captain yadakamata ke dawomata,sai tawani zabura kamar yanzu Abun ke faruwa,Ganin bata da mafitane yasata tamike tadauki tsintsiya ta share dan tsakar gidan nasu,domin tasani inda inna ta dawo ta tarar da ita batayi ba,sai na lahira yafita jin dadi,ta gama sharan kenan ta kwaso duka kwanukan wanke wanken duka gidan,amadafi tazo wajen wanken wanken nasu ta zube takarisa gindin rijiya ta zura guga ta dinga jawo ruwa sai da tacika botikai hudu,biyu takai Madafi,biyu kuma ta dauki kujera ta kada klin,tafara wanke wanke,tafara kenan taji shigowar inna Da Aziza,ta dago ido tana kallonsu lokaci daya tana fadin"Sannunku da zuwa..."
Inna Ramatu ta kalleta tana hararanta tace"Ke keda sannu,Tunda ubanki ya kashe miki rayuwa ya aura miki wanda ba"asan asalinsa ba,uwa uba gashi mara tarbiya,..."Da hanzari Azeema ta dago tana kallonta gabanta yana faduwa ta bude baki zatayi mgana kenan Aziza tazo ta wuce ta gabanta fuu ta bangajeta harsaida ta Fado daga kan kujeran datake kai,da kallo tabita harta shige daki,kwallah ta tarun mata a ido ta dago tana kallon Inna Ramatu tana fadin"Inna kinga Aziza ko? Tsaki Inna Ramatu taja kan tace"yo in na ganta mezan mata,dakika ga zata wuce meyahana ki kauce ki bata hanya,ai ke da mahaifinki Kwadayi zai kasheku don nasan kwadayin Abun Duniyane yasa ya bada Aurenki ga Dan mace nan..."Da hanzari Azeema ta mike tana fadin"Ni..Ni..Kuma ba.. ba..."Eh dake fa,saboda kwadayin Abun Duniya iyayan wanchan yarinyar sunce bazasu bashi yarsu ba,saboda ba"a san asalin dangin mahaifinsa ba,ammh dayake shashashan uba gareki wanda zuciyarsa tarigaya ta mutu ya daukeki yabada ke,ban damu ba,tunda kece Tunda kema zuciyarki irin ta ubanki ne,da dai yayi karambanin Auramasa Aziza wlh da anyi yakin Duniya na uku.."Tafada lokaci daya tana Shigewa daki,da wani kallo Azeema tabita kafin ta dafe kanta tana hada maganganun Innar in kunnenta yajiyemata Daidai kamar da ita taji inna na fadin A Dauran mata Aure da Yaya Captain,Saurin Dafe kirji tayi tana karanto Duk addu"ar datazo daga bakinta lokaci daya idanunta na zubo da kwallah,runtse ido tayi tana tuna yadda basu shiri sam da yaya captain saboda halinsa na rashin sakin Fuska da walwala uwa uba mugunta yaya captain baya da wasa kwatakwata ko asojojin shi na dabam, ne,nan da nan ta tuna karonsu na dazu,sai jikinta yahau rawa kasa karisa wanke wanke tayi,sai ta wuf ta wanke hannuwanta tafada dan karamin dakinsu gefen katifa ta zauna ta zabga tagumi tanajin kewar mahaifiyarta,domin da"a ce yau mahafiyarta na raye,da kila ta samu kafadan dazatayi kuka,ta lallasheta,ammh yanzu bata da kowa sai Mahaifinta,wanda kuma komai daga barayinsa ya fito,Har abada bazata taba bata kanta ba,bakuma zata watsama Mahaifinta kasa a idoba,duk duniya bata da wanda ya fishi,Share hawayenta tayi kafin tafice takoma ta cigaba da wanke wankenta lokaci bayan lokaci tana kallon dakin inna Ramatu tana share kwallah...
#Comment,share and vote#
#Janafty#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of yuong soldier man)_
Wattpad:Janafnancy12
*Hakkin mallaka:Janaf*
*DEDICATED TO MY MOMMAH..,HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent writer's asso*✏
*Chapter3*
*ASALIN TUSHE*
*MALLAM SHEHU AKARAMI* Sharahararren malamin Addini ne wanda yayi suna abangaren koyar da addinin Allah,Shidin ya kasance Basakawwace ne dan Asalin garin Birnin kebbi,akaramar hukumar kangiwa awani gari da"a kekira Arewa local Goverment,karatu da neman ilimi ya barosa daga garinsu,sakamakon duka mahaifanasa Allah ya amshi kayansa,yayi yawon garuruwa inda yayi karatun Allo har zuwa sauka ya karanta littafai babu adadi kafin Allah ya jehosa garin Zaria.
Agarin na zaria ya samu masaka wajen wani malaminsa wanda ya karisa saura karatun littafai awajensa,sunyi zaman amana tare dashi,Shima malamin ba"arene wato Shima bassakwaceni ,kuma har dangin Shehun yaje,wannan dalilin ne ya saa ya auramasa diyarsa daya tilo Aisha ido,Bayan Aurensu anan zaria suka cigaba da zama,basu dade da Aure ba Allah yayima mahaifin indo rasuwa,baiyi Shekara ba matarsa ta bisa,koda aka raba gado gabadaya dukiyan da gonaki da aka mutu aka barmata duk ta mallakama mijinta Mallam Shehu wanda yagaji mahaifinta ya cigaba da koyar da almajirai karatu daga garuruwa dadama,yakasance mazaunin cikin zaria cityne Akwarbai.
Gonakin sai yadinga Noma dasu,yana hadawa da kiwon Dabbobi domin dogaro dakai,..Bayan Aurensu sai mtsalan wabi ta biyo baya duk ya"yan da indo ta haifa da anyi suna sai sukoma ga mahallicinsu,sai da tayi takwas basu tsaya wa,har sun Fidda rai sai gashi Sun Haifi Bala,wanda basu ma sakaran zai Rayu ba sai gashi ya rayu,Shekaranshi Bakwai Aduniya Indo ta sake haihuwan Suwaiba,wanda tun daganan bata kara haihuwa ba,sai suka godema Allah bayan sun tattara ya"yansu guda biyu da Allah ya basu suka rikesu..
Koda aka haifi Suwaiba bala ya haddace alqur"ani,itama tana tasowa itama Mallam baiyi wasa da karatunta ba,Bala yayi karatun primary sch dinsa awata makaranta mai Suna Zaria acadmy,anan kuma yayi secondary sch dinsa,yana kammallawa ya fada ABU ZARIA inda yake karantar Political Science,Ayayinda Lokacin Suwaiba take SS1 anan Zaria acadmy din,itama kafin asakata mkrantar boko sai da ta haddace Qur"ani tana biya sauran littafi.
ABDULNASEER TAMBARI BUZU.."Wani Buzu ne wanda ya fado garin zaria akuma gidan Mallam Shehu akarami,Domin neman ilimi,Mallam Shehu ya amasheshi hannu bibbiyu Tunda dama yana amsan baki daga wasu kasashen kusa da Nigaria kamar su cameron da Chadi da Niger din,Babu Abunda mallam ya sani nashi sai Shi din mutamin Niger ne,ayanki agadez Sai kuma Sunanshi da suka sani,wajen shakaransa tara tare da mallam Tuni ya Sauke qur"ani yayi haddansa yakoma yanabin sauran litttafai,Shakuwa tare da sabo Tuni yayi da mallam da iyalansa bala da Suwaiba suna kallonsa ne,amatsayin dan'uwa ba almajirin mallam ba,Shiko mallam Shehu akarami yayi Shaku da Abdulnaseer sosai yakuma jarabasa ta hanyoyi dadama inda ya fahimci yana da amana da hankali bashi da mtsala ko kadan,shiyasa yasaki jiki dashi harda harkan Dukiyansa data iyalansa yana da masaniya,sai yazama shalelen malam Domin ma,sauran almajiran da Dan mallam sukemai lakabi,kwatsam batare da shawara da kowa ba Mallam Shehu Akarami ya Daurama Abdulnasser Tambari buzu Da Diyarsa Suwaiba aure Ranar datayi candy dinta Daurin Aure daya hada mutane biyar cur,daga mallam Shehu sai Abdulnaseer din,sai wani Abokin mallam din sai wasu manya daga cikin almajiran mallam din guda biyu,azauren gidan nasa,wanda mallam din da kanshi ya biya sadakin Auren nasu,Abdulnaseer shikanshi baida masaniyar Auren sai da aka kullashi kana kowa yaji,da farko bala ne dayazo Hutun Semister yaso yayi gaddama game da Aure,duba da Aure ba mganar wasa bace,taya ya za"a bama mutum aure batare da sanin asalinshi ba ko sanin wasu daga ciikin danginsa ba,ammh sai Mallam ya tausheshi da cewa lokaci kadan yake jira zasu dumguma dukkansu zuwa chan Niger din domin ganin ahalin Abdulnaseer din,Duk da bala bai wani gamsu ba,ammh sai ya share,saboda yana daraja mahaifinsa bazai iya sa"insa dashi ba,itako indo bata wani Damu ba,domin mijinta yayimata bayani,ita kuma Duk duniya babu wanda take gani da kima da daraja irin uban ya'yanta Shiyasa tabashi goyon baya dari bisa dari..
Abagaren Suwaiba kuwa bata wani ji wani irin ba,lokacin da Mallam yatarasu yake fadamusu,sai ma sunne kai datake tana satan kallon Abdulnaseer din,wanda kwata kwata baya da muni,Fari ne mai kalan ja,dogo ne karkarfan Namiji gashin kansa a nannade kallo daya zakamai kasan buzu ne gaba da baya,yana da kyau na daukan hankali,domin ko a anguwa yana fama da yanmata kai harda zawarawa,ciki harda manya mata wa"inda suka kusa haihuwansa,in suka gansa,kyansa yana Rudansu sukai ma tayi,ammh sai ya taka musu birki,Shima abarayinsa baiji yana kin Suwaibarba Domin bata da muni ko kadan itama doguwa ce,ammh kuma baka ce ita,tana kyanta babu laifi wanda kyan nata mai dauke dawani Sirri ne,sai da wanda yakaremata kallo yake fahimtar haka,Mallam Shi yayi alqawarin gina musu gida su tare nan Filin dake gaban nasu yasa aka tada gini,Ganin haka yasa in akayi abinci sai indo ta umarci Suwaiba data dinga dauka tana kaiwa mijinta adakinsa na zaure,to kusan sha"anin miji da mata,kuma gashi suna son juna,daya nemeta batayi yunkurin hanashi ba tabashi kanta,Ranar da Abun ya faru duk Nuku nukun Suwaiba sai indo ta gane saboda budurci ba wasa bane,ta rude ita da kanta tagasa yarta ammh kuma Abunda ya faru bai mata dadi ba batason mai zatacema Mallam ba,don yana mata fadan barinsu suna kebewa yace yafison koma miyene,in aka kammalla ginin Zasu je chan Niger sukaga dangin Abdulnaseer din in sundawo sai su bashi matarshi koma miye zai faru alokacin babu damuwa..,Indo boyewa mallam tayi bata bari yaji komai ba,balle Ya Fahimci wani Abu,sai dai tayima Suwaibar jan ido,tare da tsoratar da ita,akan tana sake bashi kanta zatayi ciki,kuma in mallam yagani sai ya bata mata Rai,jin haka yasa Suwaiba ta tsorata koda mijin nata yakara nemanta sai tayi gaddama,ammh kusan sha"anin rayuwa,dakuma karfin soyayyar miji da mata,da kanta takai kanta komai ya afku,ammh wannan karan bata bari indo ta fahimta ba,watansu biyu da aure Mallam ya kammallah Shirin tafiya Niger wajen Dangin Abdulnaseer din,sai me Ranar kwatsam Daga mallam ya aiki Abdulnaseer kasuwa da kudade kimanin Dubu dari biyu,yakaima wani abokin kasuwancinsa,zai tafi saro awakai ne,kuma shi ga wannan Tafiyan sai sukayi mgana kan yabashi sakon shi zai je ya siyomai,daman Abdulnaseer ke zuwa,jin haka yasa yabawa Abdulnaseer kudin ya tafi kaima mutumin,Ammh Abun mamaki Tun safe yafita har dare babu lbrinsa,Mallam hankalinsa yatashi yakira Abokin nasa ya tambayesa ko Abdulnaseer yazo,Abunda yabama kowa mamaki cewan dayayi tun safe dayace zai aikosa yake jiransa ammh shuru,hankula fa suka tashi har aka kwana babu lbrin Abdulnaseer Tuni ,Suwaiba ta rasa sukuninta sai kuka takeyi,Abu tun anaganin wasa sai gashi an shafe sati babu lbrin Abdulnaseer duk inda mallam zai saka abincikamai an bincika ammh babu amo babu lbri.
Fadin irin tashin hankalin da wannan Ahali suka shiga bata baki ne,domin Suwaiba bataci bata sha sai kuka,bala ko dayaji,kallan mallam yayi yace"Kagani ko Baba wlh Abun na gudar mana kenan Tun farko nayi Tutsu a al"amarin.."Mallam ya gyada kai yana fadin"Har yanzu jikina yaki yardan Abdulnaseer zai iya aikatamin haka,zuciyata tafi karkarta akan WANI AL"AMARI NE..,Dabam yafaru dashi,ammh babu komai Koma miye Mucigaba da gayama Allah.."
Wata daya kenan Babu lbrinsa tun ana cigiya har akagaji aka zubama sarautar Allah ido,an samu saukin damuwar ta suwaiba,sai da kuma yanzu ciwo ne ya tasota gaba,kullum da zazzabi take kwana,ga shi komai taci sai ta amayar dashi ta rame ta lashe..ganin Babu yaki ci yaki cinyewane yasa Bala daukanta zuwa ABU CHIKA binciken farko aka gano dan karamin ciki na tswaon wata biyu da kwanaki,iya razana bala ya Razana,haka mallam yaji sanda lbrin yazomai,indo batayi mamaki ba sai dai Fargaban Abunda zatafadama mallam takare kanta,haka mallam ya tasa suwaiba agaba yana tambayabta waye yayimata ciki,don shi bai kawo Abdunaseer bane,Suwaiba na kuka tace Abdulnaseer ne,da mamaki Mallam ke kallonta kafin yace mata waye Shaidanta Daga ido tayi ta saukesu kan indo,Mallam dayaga haka sai yamaida kallansa kanta yana tambayanta meta sani game da hakan,cikin kaskastan dakai indo tamai bayanin Abunda yafaru takara da cewa yayi hakuri boyemai datayi,Mallam yayi Shuru yana jinjina al"amarin,Domin basu dawani Tsumi ballatana dabara sai na barma Allah..
Mallam ya kwantarma Da Suwaiba hankali inda yace tayi kokarin kula da kanta da Abunda ke cikinta,Hankalu sunfara kwanciya har cikin suwaiba yakai wata biyar tafara zuwa awo,akuma lokacin Bala ya kamallah degree dinsa harya daura masters dinsa,sai kuma wani karin jarabbawan data bullo musu,domin mutane anguwa suka cha da maganganu na cewa Suwaiba diyar mallam tayi cikin shege,da mallam yaji batun sai da ya kwanta ciwo saboda damuwa,domin baya da ikon kare kansa da yarsa tunda kuskuren nashi ne,shaidun daya daura auren agabansu almajiransa guda biyun tuni suka koma garinsu abokinsa kuwa auren ba dadewa Allah yayimai rasuwa,baya da bakin da zaiyi mgana,karshe sai da fita ta garari indo domin duk inda taje ana tafe zundenta ana yada mata habaicin Yarta tayi cikin shege,Shiko mallam daina ma karatun yayi domin ko almajiran dayake ma karatun sun gudu,Tunda mganar ta fita,bala kuwa Shima lbri har cikin mkranta ana tafe yadawa kanwarsa tayi cikin shege,damuwa tare da tsananin ciwo ya rafke mallam kwance,dama Shine kwarin gwiwansu to shima ya kasa,Alokacin ne,kuma bala ya samu aiki a gidan Radion Nageria kaduna ashashen lbru,lokacin kuma Cikin suwaiba yakai wata na bakwai,Kwanan Mallam bakwai yana jinya jikinsa ya rikice suka daukesa suka kaisa asibitin al madina,sai dai kash kwana daya yayi mallam Shehu Akarami ya amsa kiran mallacinsa,ammh ko da ya rasu yafadama iyalansa kada su kullaci Abdulnaseer domin haryanzu zuciyarsa tana fadamai bada gangan bane ya aikata musu haka,akwai wani boyayye Al"amari,Mutuwar mallam ta girgixa mutane dadama ciki harda indo da bala da Suwaiba,wanda sukayi kuka,kamar zasu mutu saboda rashin bango agaresu,Ranar da mallam yayi bakwai kuma sai ga wata mgana wai Suwaiba ta kashe mahaifinta da bakin ciki,abu goma da ashrin gata da ciki,ga mutuwar mahaifi ga bacewar miji,ga Zunde mutane dawanne zataji,indo ko dama tuni tayi rauni dare daya Hawan jini ya fadeta ta mutu,tsakaninta da mallam kwana 70 ne,topha ta faru ta kare,maraici ya lullube Suwaiba da bala,lokacin yana gabda kammallah master dinshi,shiyasa yazama uba ga Suwaiba,shike lallashinta batare da shawara da kowa ya saida duka kaddarorinsu ya biyama mahaifansu bashi,ganin zaman zaria bazai yuyu dasu ba yasa ya saida harta komai nasu gidan dasuke ciki kadai yabari,dakanshi yahau mota ya tafi garin gombe,inda basu da kowa ya siyama Suwaiba wani dan matsikacin gida da taimakon dilallai,Koda ya dawo yafadama Suwaiba hukuncin daya yanke bata damu ba,saima dadi dataji domin garin zaria ya fitarmata akai kwata kwata,ko fita tayi yara sun dinga binta kenan wasu harda jifa,.
Bala da kansa yadauki kanwarsa yakaita garin na Gombe da kansa,ya damkata hannun makocinta wanda garun gidansu yake ahade wato Mallam lawal bature,wanda ya kasance yana da matar aure daya Fatima,ammh basu taba haihuwa,asa"a Lawal din zaiyi sa"an Bala haka itama matar nasa bata fi sa"an Suwaiban ba,Ganin yadda suka anshi amanar daya basu hannu bibbiyu ne yasa ya zaunar dasu ya karanta musu komai na tarihin rayuwarsu daga karshe yabar amanar kula da Suwaiba da Abun zata haifa awajensu Tunda shi zaikoma ne,Saboda aikinsa da kuma hada kan karatunsa,sunmai alqawarin kula da Suwaiba tare da riketa tamkar nasu,yaji dadi sosai anan ya kwana washegari yayi sallama dasu yakoma kaduna bayan ya jibgemata kayan abinci da kudi harda siyayyar haihuwa suka rabu tana kuka yana kuka,wayyo rayuwa kenan..
Yana komawa yamaida kai ga hada kwalin master dinshi,yana kuma cigaba da aiki a gidan Redio Nageria kaduna,gefe daya kuma yana harka da yan Siyasa tunda yana hira dasu,kuma yana musu tallace tallacen siyasa nan da nan Sunan Bala shehu Akarami yayi Fice kowa ya Sansa,duk bayan sati biyu yake zuwa gombe ganin Suwaiba,ana wannan halin ne ya siyamata waya saboda wata mtsala in tataso basai ansha wata walaha ba,yafadama su mallam lawal da tafara nakuda suyi kokarin kaita asibiti.
Haka akayi Watan biyu da komawa gombe wata ranar jumma"a da yammah tafara Nakuda Allah yasa Fatima na kusa da ita,tabazama waje ta kira mallam,dayake dan sana"ar saida kayan gwari yake,anan kofar gidan,da hanzari ya nemo mota suka kaita asibiti,Suwaiba tasha walaha don sai da ta kwana ta wuni kana ta haifo santalelenta danta mai kama da Ubansa sak,kato dashi wanda yana fitowa Duniya Bala yana karisowa asibitin,lokacin da aka miko masa Yaron kura masa ido yayi,yana ganin tsabar kama dayayi da mahaifinsa Abdulnaseer,yaron ko yana harba kafa,alamar karfi,nan da nan Bala ya rumgumesa yana fadin"Sannu da zuwa Duniyarmu *ALIYU GADANGA...*
#Comment,share and vote..#
#Janafty#....
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of yuong soldier man)_
Wattpad:Janafnancy12
*Hakkin mallaka:Janaf*
*DEDICATED TO MY MOMMAH...,HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘 Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent writer's asso*✏
_*Special Thanks to Hussain80k😝 and HassanATK...Sakallahu Filjannah Dudes😘*_
*NOT EDITED*💥
*Chapter4*
""Kwanan Suwaiba biyu a Asibitin kafin asallamota tadawo gida,Bala yayi Namijin kokari akan Suwaiba domin Duk Abunda uba ke ma da,da Abunda miji zai ma matarsa sai da yayimata shi,mallam lawal da matarsa Fati suma sunyi namijin kokari kan Suwaiba,Fatima nan take wuni sai dare take komawa gida,ita zata sanyama Suwaiba ruwan wanka ta juyemata,kafin tazo tayima Aliyu wanka wanda Sunan da bala ya sanyamai kenan,Suwaiba bata nemi komai tarasa ba na bangaren rayuwa,bangaren yar"uwa kuwa Fatima ta koremata dukkan kishirruwan su.
Kwanan Bala uku agarin Gombe yakoma Kaduna bakin aikinsa,Ranar suna tana zagayowa aka Yankama Aliyu raguna guda biyu,makota da yan"uwan Fatima dana mallam lawal sunzo tayasu murna,dayake suma din yan Asalin Yan gombe ne,Anyi Abun cikin Mutumci da jin dadi,Suwaiba tacigaba da kula da kanta tare da Danta,duk da mutanen anguwa sunata zunde cewa tazo anguwan da ciki ta haifeshi batare da nuna alamun tana da Aure ba,domin ada sun zata Bala ne mijinta,ammh sai daga baya suka Fahimci cewa yayantane ba mijinta ba,duk da haka Suwaiba ta toshe kunnanta bataji bata gani,ta dauki nasihan dan"uwanta daya cemata ta maida hankalinta wajen kula da kanta da Abunda ta haifa.
Aliyu nada Shekara uku aduniya babu inda baya zuwa yayi wayau haryafara Tafiya,alokacin ne kuma Bala yayi Aure da matarsa Umaima yar kadunane Haifaffiyar Kabala ce,mahaifinta shima tsohon dan siyasa ne,tunda shine tsohon mataimakin gwamna a gwannatin data sauka,Akwai girmamawa tsakaninsa da Bala,tun mahaifisu na raye yasan mallam,tunda yace sunyi karatu wajensa,to shigowar Bala harkan Siyasa ne,yasa suka sanjuna,kuma shida kanshi yayimai tayin Auren diyarsa tasa Umaimah,anyi biki lafiya amarya tatare agidanshi dake Anguwan Dosa,gidan yana da girma wanda Bala yadau tsawon lokaci yana ginashi,bayan Aurensu da wata biyu ya dauketa yakaita gombe don ta gana da Kanwarsa Suwaiba,hakika Umaima ta tsausayama Suwaiba ganin inda takoma da rayuwa daga ita sai Da"nta Aliyu wanda yana girma wayonsa da kwazonsa da Karfinsa tare da kamaninsa da mahaifinsa suna kara bayyana,awannan zuwan ne Bala ya sanya Aliyu awata mkranta da"a ke kira MATRIC INTERNATIONAL SCHOOL GOMBE..,Mkrantace mai tsada domin sai ya'yan wane da wane,kowani kusa agwannati ko yan siyasa,Cikin nasara da hazaka Aliyu yafara karatunsa Koda akayimai interview Malaman mkarantan sunyi mamakin kaifin basiran yaron,duk da ance baitaba hallartan mkranta,ammh dayake Suwaiba bata wasa zama take dashi takoyamai Dak da iya Abunda tasani na boko dana Arabi,Nursery 2 aka sanyasa saboda yadda sukaga yaron da kaifin kwakwakwa,kafin Aliyu ya rufe shekara sunansa yayi Tambari a mkranatar nan saboda yadda Allah yayima yaron baiwan karatu Shiganshi Shashen primary yasa sunanshi yakara fitowa domin koda yakeda kankantar shekaru ana zuwa dashi gasan mkranta.
Watan Umaima tara ta haifo santalelen Danta mai kama da ubansa sak,Ranar suna yaro yaci sunan HAISAM,wanda tsakaninsa da Aliyu shekaru hudu ne,bayan shi tazo tayi yan biyu, MARDIYA DA MADINA,Daganan bata kara haihuwa ba, haihuwar Haisam dai Suwaiba bata samu zuwa Kaduna ba saboda mkranatar Aliyu,sai haihuwar yan biyu ne taje kaduna saboda lokacin su Aliyu sun samu hutun mkaranta,sati daya sukayi akaduna kafin Su dawo gombe,Suwaiba tasan yarda take da Aliyu,tun yana yaro,yana da kiriniya da kuma son wasa,ammh bata bari yana Fita,sai dai in zai fita wajene ya zauna wajen mallam lawal,kokuma Fatima tatafi dashi gida,ammh kuma baya zama,da fari ta sanyashi a islamiya anan anguwan ammh sai yaran mkranta suka fara kyamatarsa da kokarim kiransa da wanda bai da uba,Kullum da kuka yake dawowa,yana fadama Suwaiba Abun na damunta,tana tsoron kada su sanyama yaronta wani banzan Tunani,sai kawai ta cireshi ita takoma malamarsa tunda daidai gwargwardo tana da ilimin Addinin harda na boko,sai takoma tana koyar dashi agida,tun yana yaronsa Suwaiba ta fahimci Danta yana da bala"in zuciya gashi tun yana karaminsa yake da bala"in karfi kamar doki,shiyasa take binsa ahankali,Abu dayane yake cimata tuwo a kwayar irin sunan da yan anguwa suka sanyama Danta wai DA'N MACE,tun Abun bai damunta harYafara damunta,shiko Aliyu tun yana dukan yara in sun kirashi da sunan haryakura yafara amsawa,saboda ya yarda shi din Da'n mace ne,ammh kuma macen ta bambamta da sauran mata saboda jajircewanta akan Rayuwar Dan"ta.
Aliyu nada shekara Tara Aduniya Fatima ta samu ciki,wanda ya kasance yana bata wahala,farinciki wajen mallam lawal d Fatima ba"a mgana,ita kanta Suwaibar tana murna da hakan,don ita da Fatima tamkar yaya da kanwace,Saboda laulayin data fama dashi mai zafi ne,yasa mahaifiyar Fatima BABA ADE Tadawo nan gidan tana zaune da ita,tana bata kukawa,duk da itama Suwaiban data gama aikin ta zata rufo gidan tashiga gidan mallam lawal tana taimakama baba Ade dawani Abunda ba"a rasa ba,Cikinta yayi girma sosai kuma yabata wahala,wata tara nayi ta haifo yarta mace santalele da ita,bayan bakar azaban dataci asibiti,wanda Bala shi yayi wannan dawainiyar saboda alherin Mallam lawal da matarsa Fatima garesa dashi da kanwarsa,harta hidiman suna da Kayan babby dana maijego Duk bala yayi su,ranar suna kuma ya yankamata katon ragonta yarinya taci suna AZEEMA..,Sai da tayi arba"in kana Baba Ade takoma gida tabar Fatima nakara kula da yarta,Tare da taimakon suwaiba,wacce tadauki son Duniya ta dorama diyar Fatima,sabida suwaiba na son Diya mace arayuwarta,ammh Allah bai bata ba,sai yabata namiji,Saboda Amintakar dake tsakanin Fatima da Suwaiba ne,yasa Fatima tayima suwaiba tayin Auren mallam lawal,mganar data kawo rudani sosai,suwaiba taki yarda.hartayi ikirarin barin garin gombe,Bala ya shiga mganar yace Fatima tayi hakuri suka cigaba da zumuncinsu,tunda Suwaiba taki,dole Fatima tabar mganar ammh harga Allah tana kaunar suwaiba aranta.
Shekaran Azeema biyu Aduniya Fatima tafara wani ciwo,daga ciwon nono,shikenan sai cancer ciwon Daji,Tun ana ganin abun dawasa har babbar magana tazama babba,mganin gargajiya aka fara ammh Abu yacitura nono sai zagayewa yake,harya harbama dayan ma,Suwaiba da kanta takira bala ta fadamai kan yazo ya taimaki,Fatima koda yazo yaga halin datake ciki sai da ya zubarmata da kwallah,nan da nan aka dauketa zuwa babban asibitin jaha,sai koda sukaje likitoci kin amsanta sukayi,suna ta fada suna fadin sai da ciwo yagama cinyetane za"a kawo musu,bazasu amsa ba,ran Bala yabaci yace adawo da ita gida washegari sai sutafi da ita kaduna,Allahu Akbar Allah yaga Abunda yagani ne,ya takaitama musu wahala Karfe 3:00am na dare Fatima ta karbi kalmar shahada tarasu agaban mahaifiyarta da mijinta mallam lawal bayan ta bayyana amanar diyarta ahannun Suwaiba,wanda Aranar sai wajen sha biyu takoma gidanta,itada Aliyu da Azeema wacce keta kuka,shiyasa ta dauketa suka tafi gidanta takwana awajenta,alokacin mallam lawal ya bugama Suwaiba kofa dayake Bala na nan shi ya fito,nan yake shaidamai rasuwar Fatima,sanda Suwaiba taji sai da ta suma gau,saboda jimami da sabo,Tayi kuka kamar ranta zai fita,babu Abunda take tunawa sai irin sabon dasukayi da Fatima da zaman amanan da sukayi,tunda take da ita bata taba batamata da gangan ba,macece mai hakuri da sanin yakamata,balle mallam lawal dayayi kuka rasa nagartattaciyar mata irin Fatima,ita kanta Azeemar ta fahimci rasuwar mahaifiyarta nata,haka ta wuni kuka,Suwaiba na lallashinta Aluyu ma yasan lokacin da"akayi rasuwar,saboda yana da shekara 12 alokacin Domin har yakammallah karamar primary dinsa sai wucewa gaba,Baba Ade ma takoka domin itakadai ne yarta gashi Allah ya amshi Abunsa,Anayin bakwai Baba ade tatafi da Azeema wajenta,dayake basu da nisa saman anguwansu,shiyasa kullum sai Azeemar tazo wajen Suwaiba,wanda ko Azeema batajeba Suwaiba take wanke kafa taje ganinta Haka kurum Allah ya doramata son yarinyar da tsausayinta,shiyasa komai zatama Aliyu tare take hadawa da Azeema.
Fatima tayi Arba"in da Rasuwa Bala yazo yatafi da Aliyu zuwa kaduna domin hallartar mkarantan daya neman masa Wato COMMAND SECONDARY SCHOOL KADUNA..,Makarantar sojoji dake kaduna,Babu yarda Suwaiba zatayi Tunda Aliyun yanuna yana son mkranatar na Sojojin,dole tanaji tana gani ya hada kayansa yabi kawunsa zuwa kaduna,wanda awannan karon yayan nata yaso tabiyoshi sukoma kaduna ammh suwaiba taki,tace tafi sabawa da Gombe bazata iya barin garinba,shikuma bayason takuramata sai ya rabu da ita,ammh duk Abunda zata bukata sai da ya barmata kafin su tafi,Da shi da Haisam aka sakasu amkranatar dayake anyima HAISAM din jamping din aji shiyasa sukayi Daidai akaratu.
Shekaran Fatima daya da Rasuwa yan"uwan Mallam lawal suka matsamai sai ya kara aure zama hakan bai yuyuwa,Dole tasa ya sake aure da wata yar saman layin dasuke RAMATU,Ramatu Mai awara ne Sunanta saboda awara take soyawa akofar gidansu tana yawan zuwa wajen mallam lawal siyan kayan miya shiyasa suka saba,Ramatu bazawarace tayi aure Allah yayima mijinta rasuwa,ammh bata haihu ba,Ramatu bata da uwa bata d uba,ahannun kakarta take,gabadaya rayuwarta tataso babu kwaba ne,ballatana tsawawartawa,Komai taga dama shi takeyi babu ruwanta,tunkan Auren ta na farko idonta yake abude,irin matanan ne marasa mutumci,da kamun kai,gata bata da kunya sam,ko mallam lawal din ita fara nunamai alamun so,don haka zata dinga aikamai da awara ko yabata kudi bata amsa,da taganshi zata hau sunne kai kamar munafuka,Ko lokacin dayazo da izinin neman amincewarta batayi gaddama ba Ta amince ko wata ba"ayi ba aka Daura aure tatare agidan mijinta,adakin dake gefen na fatima,dayake gidan,gidan laka ne,dan karami mai dakuna biyu da kichen sai dan filin tsakar gida,sai rijiya dake gefe,gidan babu siminti sai dai tarin kasa,ammh dayake lokacin Fatima nada kokarin tsabtaceshi shiyasa sai kasan ta kwanta kamar an daddadeta,.Satinsu biyu suna cin amarci kamar Abun arziki ammh daga Ranar da mallam Lawal ya fadamata zai dauko Azeema ya kawomata ranar basuyi barci ba,don Ramatu cewa tayi bazata rike diyar da bana nata ba wlh,shikuma yace bata isa ba,gata kuwa bazai barma Baba Ade wahala ba,dole tanaji tana gani ya tattarro Azeema ya dawo da ita gidan da zama,Suwaiba bataso haka ba,domin tuni taji lbrin Ramatu bata da mutumci sam,kuma tasani cewa Azeema bazataji dadin zama da ita ba.
Illai kuwa Domin Tunda Azeema tadawo hannu Ramatu take gana mata azaba,duk da karancin shekarunta domin lokacin tana da shekara biyar ne aduniya tayi girma dayake tana da tsawo,gabadaya aikin gidan nan ita keyinshi,da gari ya waye zata jawo ruwa tacika duka botikan gidan,kafin tazo tayi shara,tare gidan gabadaya takoma dakin mahaifiyarta inda yazama wajen kwananta ayanzu,bayan nan takoma kichen ta hura wuta ta sanya ruwan koko ta dama,ta zubama Babanta da inna Ramatu,kuma bata da ikon sha sai Ramatu taga dama,da kananan shekarunta tasaba da wanki na Ramatu da Babanta duk ita ke wankesu,Mallam lawal baya da yadda zaiyi domin kamar Ramatu tafi karfinsa ne,domin yana mgana zata tasomai kamar zata dakeshi,baya da yadda zaiyi sai ya dinga bama Azeema Hakuri,itako ko afuska bata nuna,bataso mahaifinta ya shiga damuwa saboda ita.
wajen datake samun sauki guda biyu,daga gidan Baba Ade sai wajen Suwaiba,wanda tazama tamkar mahaifiyarta,Ramatu tunda ta lura Azeema najin dadi in taje gidan Suwaiba sai ta hanata zuwa,inko taje asace Ranar sai ta kusa kasheta,ko wani Abun amfani Suwaiba tabata to Ramatu zata kwace ta saida,da Suwaiba ta fahimci haka sai ta daina bata sai dai in zatayi amfani dashi taje gidan Suwaiban da Dauka,Suwaiba da hannunta ta sanya Azeema amkaranta awata mkrana dake nan garin gombe G.D.S.S.S GOVERMENT DAY SCIENCES SECONDARY SCHOOL GOMBE,mkrantace mai kyan gaske,saboda tana hade da private ce,sakamakon mkrantar ta masu dashi ne,Tana nan a Federal Lowcost layin ministery of Agric,wanda Ramatu bataso Azeema tashiga mkranta ba,taso tayi ta zama tana mata bauta,ammh sai wannan karan,Mallam lawal ya nunamata bata isa ba,harda islamiya Suwaiba ta sakata,karfe hudu zuwa Shida na yammah asabar da lahadi kuma ta sanyata hadda,wanda in tadawo take zuwa Suwaiban na kara biyamata karatun,wannan dalilin shi yadan samama Azeema salama da takuran Ramatu,duk da haryanzu bata daukemata kowani aiki ba,sai tayi shi kafin tatafi mkranta.
Ramatu nada wata uku da zuwa gidan tasamu ciki,shikenan sai Tsurfa da iyayi ya shigo ciki,Allah ne ma yasa za"a haifi jikin lafiya ta haifi yarta mace mai kama da ita,kuwa Ranar suna lawal ya sakama yarinya suna AZIZA tunda Ramatu ta haihu Azeema ke wahala da ita da yarta,Ko duba kankatarta batayi kamar jaka,itace cin kashin Aziza da cin Fitsarinta,kullum zaka ganta goye da Aziza ko itace uwarta sai haka,Haka Rayuwa tacigaba da tafiya da dadi babu dadi,Azeema na girma kullum wahalarta na karu,bata da wajen jin dadi sai wajen suwaiba,wanda haryanzu Aliyu bai dawo ba,yana chan kaduna wajen Kawu bala,sai dai yana Zuwa lokaci bayan lokaci.
Aziza tafi Azeema jikin girma domin tana shekara goma kamar yar sha biyar,saboda tana da girman gabba,shekaru Biyar ne kwarara tsakaninta da Azeema ammh in kuka ga yadda takema Azeema zakuyi zaton kanwartace takusan ukuma,saboda yadda ta rainata ko agaban waye haka zata dakamata tsawa kamar tsaranta,itako Azeema bata da hayaniya ga hakuri da kawaichi,shiyasa kotayimata wani Abu bata daukan mataki sai dai tafadama Ramatu wacce suke kira da Inna,ammh daga karshe in ma batayi wasa ba ita zataci duka,Gabadaya Ramatu ta lalata Aziza domin ta danneta ta damata arashin kunya da Rashin mutumci,kullum cikin yima yan anguwa take,Azeema bata iya yima Aziza komai saboda tarigaya data raina ta,ko wankinta ita kemata har kuma yanzu ita ke aikin komai agidan,Aziza bata kauda kara suna zaune ita da mahaifiyarta sai dai ta dafa ta basu suci suna zaginta,mallam lawal bai da katabus saboda Ramatu ta zamarmai matar jaraba,har gwara ita Aziza in yayimata mgana tanaji Tunda tasan halinshi bayamata da wasa yanzu jikinta sai ya fadamata,Duk da tanajin Haushinsa acewarta yafi son Azeema akanta,dakuma hudubar mahaifiyarta,Aziza irin yaran nan ne masu shegen kwadayi,tunda ta lura da Abun arzikin da Suwaiba kema Azeema sai takoma shisshigema Suwaiba,ammh sai bata,bata Fuska ba saboda bata mu"amala da yaro mara kunya,uwa uba kuma basu shiri da Ramatu saboda rashin da"anta da kuma yadda take muguntama Azeemar.
Suwaiba saboda kar ace tayi sonkai,sai ta sanya Aziza A mkarantar da Azeema keyi,tare da islamiya ammh duk da haka baisa tafita daga bakin Ramatu ba,kullum bata da Abun zagi sai ita,tanabi gidan suna gidan biki tana fadin tana zaman kanta,don ko danta data haifa ba"a san asalin fa,bashi da uba,kilama dan gaba da Fatiha ne,itako Suwaiba kotakan Ramatu batabi saboda ta fahimci jahalici ke damun Ramatun shiyasa,Azeema kuwa tun bayan barin Aliyu gidan batakara sakashi a idonta ba,wani lokacin ko yazo tana gida tana fama da aiki,kuma baya kwana suke juyawa,Ranar dayazo yakwana itakuma tatafi gidan Baba Ade ta kwana tana dawowa goggo ta ce mata yanzu su gadanga suka koma kaduna,sai dai ta ciji yatsa ammh tana so taga yaya Aliyu taga Shin yakara girma ko yananan yadda yake,yanzu yana fara"a kokuwa haryanzu fuskarnan tasa ba Rahama.
Shiko Aliyu suna kammallah Command sch Haisam ya tafi BUK KANO yana karantar Accounting,ayayinda Aliyu ya fada ABU ZARIA yana karantar Scicology,yaso yatafi NDA ammh sai Kawu bala yace yafara hada Digerinsa First kafin yatafi,Akuma lokacin ne gwannatin datahau mulki ta bayyana Sunan Kawu bala amtsayin Kwamishinar yada lbari ta jahar kaduna,Babu laifi kawu bala yatara Abun Duniya domin yana gudanar da kasuwancinsa bayan aikin gwannatin,kuma haryanzu yana karantama gidan radio Nageria kaduna lbrin Turanci da fassaransu na hausa.
#Comment,share and Vote..#
#Janafy...#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_
*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_
*DEDICATED TO MY MOMMAH..HAUWA .S.ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent Writers Association*✏
_*Assalamu Alaikum janafty Freeking Fans,gawani albishir din danake tafe muku dashi,Ko kuna da lbrin shahararriyar marubuciyar zamanin nan,wacce ta dade aharkan Rubutu,tana fayyace muku,yadda yanayin zamantakewar rayuwar da kullum take,wacce tadade tana haskaka zuciyarku da dadaddan littafanta masu dadi da Fasaha,masu dauke da darussa masu dimbin yawa,kada nacika ku da dogon lbri Ina Nufin NABILANCY LUV(Antyn S&S) wacce tazo muku da wani Salon lbri mai Tafiya da salon zuciyar mai karatu bakowani littafi bane illah...,MAKAUNIYA..(Labarin cin Amanar kauna)kunemi naku kusha karatu domin amfana da Abubuwan ban mamakin dake cikin littafin,Karki bari karka bari abaka lbrin MAKAUNIYA..(Labarin cin Amanar kauna)*_
*Chapter5*
""Cikin Nasara ya kammallah karatunshi yana gamawa ya tafi NDA wato Nagerian Defence Acadamy yayi wata ashirin da hudu ma"ana yayi Short Service kenan,yana gamawa yafito amtsayin SECOND LEUTANET,Tunda Aliyu ya Fito amtsayin Soja gwazonshi da kuma yadda yake Kaunar Abun Aransa yasa,nan da nan yayi Fice kowa ya sanshi,Saboda yana Bama Abu muhimmanci uwa uba kuma jarumi ne,mara tsoro shekaransa daya dawani Abu ya samu karin girma Zuwa LEUTANET,daganan yayi ta samun cigaba tare da karin mikamai Har zuwa yanzu dayake mtsayin CAPTAIN wanda yake karshinshin 1 DIVISION NIGERIAN ARMY KADUNA..
Shekarunsa na haihuwa kimanin 30 kenan,duk inda ake Neman cika da cikar zati da Haiba Aliyu Gadanga ya hadashi,Kyakyawane na gaske,sakamakon kamar dayake da mahaifinsa,in ka gansa akallo farko sai ka yankemai Hukunci dayana da girman kai,saboda mutum ne,mai iko da takama,yana da jinkai,in yana wani Abun sai kadauka yahada jini da Sarauta saboda yadda yake gudanar dawasu abubuwansa,Yana da karancin Fara"a Akan Fuskarsa wani lokacin ya hade Fuska sai yabaka,tsoro sai ka ga yana wani Abu kamar afilin daga,Aliyu gadanga miskili ne na karshe wanda Abokan aikinsa ke masa lakabi da *CAPTAIN A A TAMBARI BUZU..* gashi ya kasance mutum ne dabayason Raini da Sakarci,baya da wasa ko kadan,yana da mugun son Girma kamar gyambo,yana so ka bashi girma koda kai din ka girmesa atakaice dai,yana son Abashi respect na karshe,kana baya da wasa yasan salom mugunta kala,kala,A iya shekarunsa ya fuskacin kalubalen Rayuwa na yadda ake masa kallom mara Uba,wanda ba"a son Asalinsa ba,Shiko Mahaifiyarsa tarigaya datamai duk wani ,bayani,banda Sunan mahaifinshi da yanki daya fito basu san komai nashi ba,bai damu ba,saboda duk Abunda masu Uban zasu takama dashi,toshi ma zaiyi takama dashi harma ya darasu.
Madina da mardiya dukkansu sunyi Auren nan kaduna,sai Haisam dake aiki yanzu da First banka A kano,Sunan GOGGO Yasamo asali ne,saboda su Haisam da suke kiranta da hakan,sakamakon ita din kanwar mahaifinsu ce,sai Shima Aliyun yake cemata haka,har sunan ya bita kowa Goggo,Aliyu mata basa gabansa domin da suna gabansa da tuni ya lalace,don yana matakin farko a jami"a yake samun tayin yan"mata yasani sarai ba saboda komai suke manne masa ba,sai saboda kyansa da ajinsa,Shiyasa baya damuwa,bayajin kunya kartama mace rashin mutum agaban kowaye,Gashi da zuciya ta bala"i,baya da tsoro balle shakka Goggo ce kadai sai kawu ke iya tankwarashi in yayi irin wannan bakar zuciya,baya da bakin da zai Furtama Gaggo Rashin Sanin takamammam dangin mahaifinsa na damunsa,saboda goggo ta kasance wata uwace mai mallakama Danta komai saboda ta inganta nashi rayuwar,yawan nunamata damuwarsa tamkar butulceni agareta,shiyasa koda wasa bai taba nuna mata Abun na damunsa ba.
CAPTAIN JABIR Amini yake garesu ko nace dan"uwa,domin Tun Shigansa,NDA suka hadu,da farko In da Jabir yabiye ta halin Aliyu bazasu taba zama abokai,sakamakon Shi jabir Mutum ne,ma yawan Fara"a da sakin Fuska,uwa uba kuma ga barkwanci,sakamakon Aliyu da yake wani gim dashi Fuskarnan kullum babu alamu rahama,to sanin hali dakuma abota da Allah ya hada shikenan suka zama Aminai,tunda kowa yasan Halin kowa,Suna aiki awaje dayane Anan kaduna,Haka Shima Haisam babu ruwansa,mutum ne Shima mai fara"a Da son lbri sakamom Abokin nasu dayake wani murdadde mai iyamai sai Allah daya hallicesa.
Bayan kowani Sati uku yake zuwa gida,ganin Goggo to duk sanda yazo nan yake ganin Azeema tare da ita,duk da yana so ya tambayi wacece,ammh miskilanci da rashin son Raini yasa yake basarwa sai Goggon ne dakanta take shaidamai Diyar marigayiya Fatima ce tabe baki kawai yayi bai wani nuna wani tsausayi ba,ko yaba mganar goggon mahimmanci,itama sanin halinsa ya satakama kanta dashi,Tun ganin Farko da Azeema tayima Aliyu bayan dadewar datayi bata ganshi ba,Allah ya sakamata tsoronshi,saboda ita arayuwarta ta tsani soja,saboda yadda takejin lbrin Rashin tsausayinsu,to Ranar data ga Aliyun ma da kakinsa ne,yazo gidan Goggo fuskarnan babu Annuri kafarsa sanye cikin wannan katon takalmn nasu,wanda in suka taka ka dashi,ko baka mutu ba,sai kayi jnya mai tsawo,lokacin data ganshi ya shigo dakin goggo,itakuma tana sharemata dakin,goggo na ciki,yana dago labule suka hada ido,ai saboda tsoro batasan sadda tayada Abun sharan ba ta kwantsama ihu ba,Wata razananniyar tsawa ya dakamata yana hararanta,saboda ganin yadda take neman Raina mai,wayau shi da gidansu ya shigo ta faramai ihu,tsawan data kara firgitata ta tsorata sai ga fitsari,shar yana zubowa ta kafanta saboda tsoro,dama Azeema akwai dan banzan Tsoro kamar farar kura,Baki yarike yana kallon yadda take shatata fitsari tana kamkame jikinta,aiko karisa shigowa dakin yayi yana kwanto belt dinshi yana fadin"Bush girl yanzu zaki durkusa ki shanye kazantar dakikayi kuwa..."Yake fada yana Shirin kwanto belt Goggo ta fito tana zabgamai harara,kafin tamaida kallonta kan Azeema taga yadda take rawan sanyi saboda tsoro fada Goggo ta hau gadanga dashi kan yazo ya tsorata mata diya korashi tayi,dole ya fice yana tsaki yaso goggo tabari ya lallasa yarnyarnan,banda iskanci da samun waje kamartane zatayima mutane Fitsari a tsaye,shibaima fahimci shiya firgitata ba,to tundaga ranar Azeema take Tsoron Aliyu wanda take kira da YAYA CAPTAIN,bata yarda tadawo gidan ba,sai da yakoma,Baya zuwa gidansu,ammh yana zama wajen sana"ar baba lawal ta kayan gwari,saboda kamar kawu bala,yake kallonsa ko bakomai yaba da gudummuwa arayuwarsa duk da yanzu yadan manyanta.
AZEEZA tunda Allah yasa ta dora ido kan Aliyu,watarana sun dawo daga mkranta suka ganshi wajen babansu,Azeeza saboda kallo sai da takusa fadi,sai da Azeema ta riketa,kallonsa take bata ko kiftawa Azeema ta tambaya waye wanchan na tare da baba? Azeema ta bata amsa da cewa"La baki ganesa ba,Yaya captain ne fa,na gidan Goggo..."Aziza najin haka gabanta yafadi kardai ace dan Shegen nan ne,mara asali,ammh ko gayen yana da kyau,ya hadu,wasa wasa ranar Tunanin Aliyu bai bar Aziza tayi sukuni ba,Tun tana daukan Abun wasa hartazo ta tabbatar da cewa takamu da son Aliyu,gashi ko mgana basu tabayi ba,saboda yana ganin yarinyar yaji lbrinta bata da kunya ko kadan,shiko baya hulda da marasa kunya yanzunan yarinya tanemi rainashi sai yaci ubanta ko agefen kwalan riganshi,shiyasa koda wasa bai taba sakarmata fuska ba tasha ganinshi baknta na rawa tahau gaisheshi shiko sai yagadama ne ma zai amsa da lafiya lau,daga haka ya gimtse fuska,Wani lokacin yake kawai take tana biyema Ramatun intana zaginsa,saboda bataso ta fahimci halin datake ciki.
Ramatu kuwa ya tsaneta saboda rashin kirknta baitaba gaisheta ba ko zasu bangaji juna kuwa,shiyasa itama bata kaunarshi,duk inda ta zauna bata da mgana sai nashi dana mahafiyarshi,tasha kawo karansa wajen Goggo tama danta mgana baida tarbiya,sai dai Goggo tabata hakuri tace zatamai mgana,ranar data faramai mgana,cema goggo yayi"in batayi hankali ba duk randa ta shiga gonarshi sai ta zagaya anguwanan tana tsallen kwado.."dakuwa goggo tamai tana fadin"Tunda kasata nima zaka iya sakani kenan"Ko ajikinsa saima cema Goggo dayayi"Shi dai bai ce itaba,so karta sa kanta aciki..
Goggo macece mai fada,da shiga Abunda babu ruwanta,indai akan Da'ntane Aliyu,wanda takema kira da GADANGA,Tana da yawan barkwanci da son wasa,shiyasa ya maidata kakarsa,in kaga yadda ake daru tsakanin Gadanga da goggo sai cikinka ya kulle,in yadade baizo ba,tadinga kira tana fadin"Gadanga ko amun yaji ne? saboda kullum da tsiya suke rabuwa,Dakuma yazo ko kwana ba"ayi za"a tsiyace,goggo kenan da Aliyu gadanganta.
Aliyu mutum ne,mai yawan karfin sha"awa shiyasa tunda ya fahimci haka,sai ya rika azumin litini da alhamis,Ammh duk da haka Abu yaci tura sai ya yanke hukuncin fara neman Aure,koda kuwa da yan"matan dake haukan Sonshi ne,yafara neman wata mufida yar kaduna ce,Soyayyarsu batayi nisa ba,suka rabu,sakamakon mahaifinta yace bazai bata shiba,saboda yayi bincike ba"asan asalin sa ba,abun bai dameshi ba ya rabu da ita,bayan ita ya nemi Ummi yar katsina ce Itama itace ke mutuwar sonshi,ita harmgana tayi karfi,su kawu na Shirin zuwa komai ya rushe,bayan ita sai da akayi biyu,duk karatun dayane,Abun ya soma damunshi,duk matsayinshi ace anamai Wulakanci wajen neman Aure ana tozartashi kan baida uba,tun daganan ya watsar da komai ya cigaba da azuminsa kwatsam suka hadu da Ni"imatullahi akaduna wajen Dinner wani abokinsu shima Soja itakuma kawartace ai Tunda ni"ima ta hanga ido,taga Aliyu ta mutu akanshi,sai da tasan yadda tayi kafin tabar kaduna ta kafa gwannatinta.
Ni"imatullahi Ahmed Sidi na iya,diyace ga kwamishar yansanda na jahar gombe,kuma ya'ce daya tilo da iyayanta suka haifa,yar gatace ta karahe,wayayyiyace domin duka digeree dinta harzuwa master dinta ba A Nigeria tayima ba,yar kimanin Shekara ashirin da biyu aduniya,Fara gajera ammh itama babu laifi tana da kyau,Lokaci daya son Aliyu yayimata reshe harda rassa,tun bayabi takanta haryafara saboda yadda take gigitashi da salon soyayyarta,lokaci daya suka afkama juna da soyayyah mai zafi,ba"a dauki wani lokaci ba ya gabatar da kanshi wajen kwamishina zuwan farko duka iyayyan nata sun yaba da zabin diyar tasu ammh sai dai kash,kwamishina na bincikawa sai aka cemasa don makusa Captain Aliyu baida makusa,sai dai makusan guda dayane,rashin takamammen waye mahaifinshi,da kwamishina yaji haka yaso ya butse,ammh sai diyarsu ta nuna,in ba Aliyu ba sai mutuwa,dole aka yarjemai ya turomai magabantashi,kawu bala da mallam lawal sukaje,tun farkon mganar Auren sune jagoran komai har zuwa aka saka ranar Aurensu wata uku,murna wajen Ni"ima ba"a mgana,ta bangaren Aliyu dai laba"asa,donshi babu mai gane yanayinsa.
Da Azeeza taji lbrin Auren da Aliyu zaiyi sai da ta kwanta asibiti saboda firgici da damuwa,Duk iyayanta suka damu,kamar Azeema taji lbri,duk irin diban albarkan da Azizar take mata bata damu,tanajin yar"uwan nata har ranta sabanin ita Azizar datake zaune da Azeemar don bata da yarda zatayi ne,ammah har aranta take jin ta tsaneta batasan dalili ba,kodon hudubar mahaifiyarta akanta ne,ohoabunda kawai tasani bata ma kaunar ganin Azeema cikin Farinciki tafiso ita da uwarta suyi farinciki,itakuma ta dauwama cikin kunci,ayanzu haka shekarun Azeema 20 ayayinda Azeeza take da 15 ammh dayake tana da girman jiki,in akace shekarunta kenan wasu ma basu yarda,dauka suke ita ke gaba da Azeemar.
Ganin gabatowar Biki yasa Aliyu yafara gyaran gidansu,kusan dai Aliyu bawani mai kudi bane,Baya da burin tara arziki,ko yau adinga lbrinsa,amtsayin shi wanine,shidai burinshi ya taimaki kasarsa da lafiyansa da kwazonsa,kodon watarana in ya mutu atuna dashi,yana da Rufin asiri daidai gwargwado,Saboda baidawani dawainiya akansa,goggo ce haryanzu kawu baidaina hidima dasu ba,hatta shi Aliyu,son duk kudadansa,suna kammalle abanki ne,gidan nasu dama dan madaidaicine mai yalwar dan tsakar gida gefe wajen zubda ruwa,sai Famfo,daganan yammah akwai wani daki,ciki daya,nan ne dakin Aliyun,sai daga gabas dakuna guda biyu,daya goggo naciki,daya kuma tana ijiye kayan Abinci da sauran karikice,yana tashi gyaran ya bude dakunan goggo ya hadesu waje daya yayi mata babban falo da Dakuna barci guda biyu da tailot yazubamata kayan more rayuwa sai daga waje yayi musu katon madafin girki,sai barayinsa,dayake buge dakin,yayi ya hade musu Falo da two bedroom da kichen da Bayi,saboda nan zasu fara zama kafin su wuce kaduna,Tsakar gidan ma yasa aka kankare,aka saka interlock,Daga wajen kuma aka fitar da garejin mota,saboda motarsa,baya ma zuwa da ita gomben,saboda ba wajen adanata,yafi hawa motar haya Abunshi,don shifa Babu ruwansa bai dauki Duniya da zafi ba,akayi fenti mai kyau da kayatarwa daga wajenma an gyarashi sosai,tundaga nesa kana hangoshi yana daukan ido..
Tunda biki ya matso yan bani na iya suka damu kwamishina da tsegumin Aliyu,har mgana takai ga kaninshi wanda zai bada Auren Ni"ima,tun kafin Daurin Aure yaso adakatar da mganar,ammh kwamishina yaki yarda saboda yadda mahaifiyar Ni"imar da rike wuta,saboda sanin yadda diyarsu ke mugun Son Aliyu,Ni"ima kuwa tayi rawan kafa,kamar mene,duk da danginta sukaje mata jere,suka dawo suna raina inda Aliyun zai ijeta,harda uwarsa,uwa uba harda anguwan suka raina,sunce ta yaku bayi ce,ma"ana ghetto area ce,Da fari Ni"ima tayima Aliyu mgana,ammh sai ya numata shidin bawani bane,in zata zauna dashi ahaka,Final,in kuma tanaganin tafi karfin nan,To door iz open babu lalle ba dole,shi bazai dau wannan Rainin ba,don baicemata shi wani ne,ba,Shi kawai Sojan Nigeria ne,mai bama kasarsa gudummmuwa.,Dole Ni"ima tai ta bama Aliyu hakuri,domin zaga zaga yayimata,dakyar tashawo kanshi,ya hakura,tasan halinshi sarai baida wasa,shiyasa take kafkafa dashi kada ta balloma kanta Ruwa.
Ranar Daurin aure kiran da Kanin kwamishina yayimai kenan kan su bazasu bada diyarsu,ga wanda baida cikakken Asali ba,Sai yaga Dangin Maihaifinsa,tukunnah inko basu,to sai dai yayi hakuri bazasu basu diyarsu ba,Kwamishina baida yadda zaiyi dashi,dole ya bashi goyon baya,wannan Shine musabbabin Abunda yafaru awajen Daurin Aure,da yadda Daurin Auren yakoma kan AZEEMA, da duk Abubuwan da suka biyo baya...
*Karshen Asalin Tushe*
*Yanzu muka Shiga gabar,ku biyoni don ji yazata kaya gadai gwarzo nan Captain Aliyu Abdulnaseer Tambari buzu,dakuma zaratan matan Azeema,Azeeza,da Ni"imatullah..*
#Comment,share and Vote..#
#Janafty...#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_
*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_
*DEDICATED TO MY MOMMAH...,HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘 Ladingo yar Mutan Niger_
*Intelligent Writers Association*✏
*NOT EDITED*💥
*Chapter 6*
Jabir ya dade dakin Goggo suna hira sai wajen 10:00pm na dare,Goggo taga Aliyu baida niyyar bude kofar shashensa,fitowa tayi da kanta ta isa har kofar shashen tahau bugawa tana fadin"Gadanga kazo,ka bude kofarnan.."kazo ka bude nace ko?goggo take fada cikin fada.
Yana kwance akan Daya daga cikin kujerun Falo,inda Allah ya taimakeshi lokaci da"akazo za"a yima Ni"ima jeren kayanta,hanawa yayi,saboda bazama zasuyi anan dinba,cemusu yayi kada su damu,ko gidanshi na cikin barikin akwai komai,so no need su wahalar da kansu,dayake dama already ya rigaya daya gyara barayinsa nasa bayan ya kawatashi dakayan alatun more rayuwa.
Yanajin Buga kofan Goggo,da maganart,ammh yayi mata banza,yana kwance dagashi sai boxers kadai,babu ko riga ajiknsa,gashin kirjinsa yayi kwance luf dashi,Idanunsa suna lumshe ne,ammah ba barci yake ba,Damuwa tareda bakinciki ke mukurkusan shi,shi yanzu bama ta Ni"ima yakeyi ba,ta makomar rayuwarshi yakeyi,"Waye Mahaifinsa?inda gaske Goggo takeyi shi ba shege bane,to ina mahaifinsa da Danginsa suke? Tambayar da haryau bai samu mai amsamai ba.
Goggo jin Shuru ya sata matsa jikin tagan kofan tana fadin"wlh ko kazo ka budemin,ko in kira gardawa suzo su balle kofan,na shigo har cikin naci maka mutumci,tunda kan mace,gadanga zaka dinga min kyaluwa ina mgana.."Tafada tana kwafa,Ajiyar zuciya ya sauke kan ya mike jikinsa asanyaye,bude lumsassun idanunsa yayi,bansan sadda na Furta subhannallah ba,saboda yadda idanunsa,suka chanza launi,sunkoma red sosai,Jikinsa babu kwari yazo ya murza key din kofar ta bude,bai bi takan Goggo da jabir dake tsaye ba,ya juya yakoma cikin falon yazauna kan kujera,yana kauda kansa,Shigowa dakin Goggo tayi tana fadin"Gadanga..Gadanga..Gadanga.."Saunawa na kiraka.."
Ko dagowa baiyi ba,yace cikin husky voice dinsa"Wai ni Goggo don Allah menayi miki ne?kamata fa yayi ki tsausayamin na rasa,love of my life,ammh kinzo sai fada kikemin.."Yafada yana wani kyabe fuska kamar zai yi kuka,Jikin goggo ne yayi sanyi ta karisa gareshi tana fadin"Yo ai kaine gadanga wani lokacin da ban haushi,ai ni na dauka bazaka wani damu ba,duba da yadda mahaifinta ya tozartaku gaban dubban jama"a,wlh indai kana da zuciya bai kamata kaji dacin Abun ba.."tafada tana zama kusa dashi kansa ya dauka ya kwanta bisa cinyarta yana fadin"koma miye,goggo i Love her,duk da Abunda mahaifinta yayi i knowa Ni"ima tana cikin wani hali yanzu cuz she luv me goggo i swear she can do without me.."Yafada yana damke hannun goggon
Dungure masa kai tayi da dayan hannunta tana fadin"Wai ban hanaka min mgana da wannan yaren Nasaran ba,sai na fara cin kaniyarka tukunnah ko"Tafada tana yar dariya,bai tankata ba ganin haka yasa ta hausha shafa kanshi tana fadin"karka damu kanka Kaji,Allah yabaka mace tagari saliha,na tabbatarmaka Azeema zata zemamaka sanyin idaniya nan gaba,mganar mahaifinka kuwa mucigaba da addu"an gadanga inda rabon sake haduwa,Allah zai hada,ammh ina ji ajikina,Abdulnaseer bai mutu ba yana nan Araye,Ammh inda yakene,ban sani ba,Allah shiya barma kansa sani.."Tafada idonta na cikowa da hawaye,mikewa Aliyu yayi yana kallon goggo kan ya saka hannu ya shafa fuskarta yana fadin"To goggo,in bai mutu ba,yana ina,? ko yan"uwanshi ba wanda zaki tuna,ko yataba fadamiki.."Shuru goggo tayi kan ta sauke ajiyar tana fadin"Gaskiya baitaba fadamin ba,sai dai yana yawan Ambatan Agadez domin yacema mallam ko abaya daga yankin ya fito,ammh kasan Agadaz ba karamin gari bane,kuma shekaru sunja,gaskiya mawuyanci Abune,agano wanda ya sanshi sakamakon babu wata shaida da zata bayyana hakan,..,"Tafada muryanta asanyaye."
mirmishin karfin hali yayi yana kallon jabir dake tsaye yana kallonsu cike da tsausayi,kauda kai yayi yana cije lips dinshi ganin haka goggo ta dafa kanshi tana fadin"Aahhh..Haba Aliyu gadanga kusar yaki,Soja mazan fama,ko filin daka asan takunka,makiya da Abokan gabama tsoronka suke,kaga Saurayi na mamanshi uhmm,kaga Ango Azeema ka.."Saurin mikewa yayi yana dariyan Dole jabir ya tayashi,hanyar bedroom dinsa yanufa yana fadin"Sai da safe Goggo,plz go and sleep,nasan kin gaji dayawa.."ya fada yana fadawa bedroom din ransa bace,babu Abunda yabatamai rai sai kiransa da Angon Azeema da goggo tayi,saboda bacin rai kamar ya kunduma zagi,ammh sai ya tuna goggo ce,ita baikamata azageta ba,uwace,uwa kuma tanada matukar muhimmanci,balle tashi data kasance na mussaman ne.
Goggo batai gaddama ba,ta mike tana ma jabir sai da safe,tasan ko banza ya sauko daga muguwar bakar zuciyar da yahau,barayinta takoma tana yan wakewakenta ko ajikinta,domin ita wannan Aure yayimata daidai,sai alokacin ma ta tuna da Azeemar wanda tun da rana tace mata zata gida,tayi wanka ta dawo ammh Shuru bata dawo ba,bata damu ba sanin halin Azeema da rashin son mutane da hayaniya yanzu haka Rashin sakewan yasata kin dawowa,alwala goggo tayi tazo ta kabbarta sallar,bayan ta sallame issha"i tayi shafa"i da Wuturi,bayan nan ta dukufa rokama Aliyu fatan nasarar rayuwa kafin ta gangaro,kan Allah yayima Aurensu da Azeema albaarka tadau tsawon lokaci tana addu'o'i kafin ta kwanta,zuciyarta fess.
Aliyu yana Shiga bedroom dinshi yafada wanka,ya dade aciki bayan ya Dauro alwala ya fito,yana daure da tawul akwankwansonsa,daya kuma yana kansa,yana tsane ruwa da jabir ya cikaro wanda yayi dare dare bisa lafiyayye gadon dayasha wani ubansu bedsheet,kallo daya yayimai ya kauda kai Aransa yana fadin"Dan iska,ba don Tsohon dan Sandan nan,yayimin cikas ba,ai da yanzu nine bisa gado na ina biyan ladan kudina.."Yafada yana wani Runtse ido,kamar yana Kallon Tanadin dayayima yau din.
Gaban Derressing mirrior din dake Dakin ya isa yana kokarin bude wani lotion na kamfanin OLIVE yana shafawa kallonsa Jabir yayi kafin yace"Hy Dude wai duk wannan Shariyan namiye ne? bafa ni bane kwamishina Ahmed Sidi na iya ba,balle ka huce akaina,kuma Dude wlh Seriously Azeemar dakake kumburi don Ka aureta,yasin tafi Ni"imar taka komai,kai infact ma itace matar Rufin asirinka,don ta rufamaka lokacin da Uban Ni"ima ya tona maka,so Ni banga Abunda damuwa in kayi duba da komai MUKADDARI NE.."yafada yana yar dariya,wani kallo Aliyu ya wurgamai ta madubi baice komai ba,ganin haka Jabir yakara cewa"am wlh Dude ta hadakomai dakake bukata wajen mace,i know kaima aikana ganin yarinya,so quiet da ita,gaskiya kana da sa"a Dude.."Wani Takaichi ya kulle Aliyu baisan sadda ya waigo yana fadin"Nagode Shehi jabiru da Tunatarwa,buh juz give me 5 minutes,.."yafada yana jan Side drower din dake gefen gado,ya fiddo da wani Memo da pen,ya yagi daya ya dora zai fara rubutu Jabir ya kallesa yace"Mezakayi..."ko kallonsa baiyi ba,yace"Sakinta zanyi...!kwalalo Ido jabir yayi kan yace"what are u mad.."?ka saketa,kai Dan iska ne..? yafada yana kama baki,wani dirty look Aliyu ya sakarmai kafin yace"yap,yo ai naga kafini bukatarta,Tunda har ka iya kwatanta tana Abun bukata na more rayuwa gata She iz quit ko?sai na sakar maka ita,tun kafin kafara tunanin binta da Aurena akanta.."yafada yana wani hade rai.
Tsaki jabir yaja kan yace"Buraouban ka,banza kawai sakarta manq,wazai hanaka.."yafada yana ballamai harara,dariyan yake Aliyu yayi kan yace"Kai ne Babban Da'n iska,in ba Da'n iska ba,gaban mijin mace ka hau suffanta ta,ai kai ne banza,ajawo gara kawai.."yafada yana wurgamai takardan da pen din afuska yana fadin"Take ur eyes away from my Wife,i Swear zan iya kashe mutum in yakara suffata Iyalina..yafada cikin kakkuasan murya,yana wani buga kafa
Zabura jabir yayi ya duro daga gadon yana fadin"Me kake takama dashi?Kaki? Kai mallam kamar yadda alluran ke yawo ajikinka,haka take yawo ajikina,ko zamu gwada,billahil lazi sai na barar maka da hakoran gaba,karyan zama Shege kake.."yafada yana hararansa fuskarsa ahade,baya Aliyu yaja yana fadin"Ubanka zanji u already know me ko"?yafada yana wucewa jikin wardrope dakin, yana kokarin budewa,da harara jabir ya rakasa yana fadin"wlh an ma Cuci marainiyar Allah,An hadata da Da"n iskan Soja kawai,ai daka tsaya kaga yadda zan sauyama kammanin.."Dariya Aliyu yayi yana fadin"Sai kaje kafadamusu su kwance auren su auramaka tunda kai ba Da'n iska bane,tunda na lura u are jealous,.'ko kallonsa Jabir baiyi ba ya fada Tiolet,yana kunkuni yana fadin zai zane Aliyu da daddaren nan,shiko yana jinsa yamasa banza,sai ma jallabiyansa daya zura ya Shimfida darduma Ya Tada salla,shiko jabir koda ya fito shima Daure da alwal,shima sallar ya tada,kowa yana nashi ko wajen kwanciya sai da suka buga,harda Ture ture agado kamar wasu yara,dat how Captain Aliyu and captain jabir Art when they are together,kuma basu iya rabuwa da juna,ko cikin bariki suna tare,ammh kuma kowanne yanajin kansa awani Shege ne...
********
"Ni"ima kuwa cikin mawuyacin hali aka kaita Asibiti,likitoci suka amsheta da gaggawa zuwa emargency Sun ci bakar wahala kafin su daidaita numfashinta,domin jninta yayi bala"in hawa,ga zuciyarta ta buga sakamakon wani Abu dataji wanda yayi matukar razanata,kuma zuciyarta ta Firgita da Abun,yanzu koma miye,ayi kokarin ganin An magancemata matukar ana son Rayuwarta ta Daidaita.
Bayanin da likita yayi masa su mami kenan da kwamishina,wanda tunda likita ke mgana,zufa ke ketomai sai yanzu nadamar Abunda ya aikata yazomai,sam baiyi Duba da halin da tilon yarsa zata tsinci kanta aciki ba,kawai yana hango kada yabata rayuwar yarsa ne da zuru"arsu,kallon sa Mami tayi tana Tsiyayan hawaye tace"Kaji ko,Haba Ranka shi dade,tayama za"ayi kafara yanke wannan hukunci batare da ka shawarceni ba,ni da ka kirani dana fadama zakayi kuskure domin Ni'ima bazata iya rayuwa babu Aliyu ba,tana mugun sonshi,tariga data sallama ma kanta yau zata zama matarsa,ammh duk ka ruguza komai,na shiga uku ni Jamila,bani da kowa sai ke Ni"ima tabbas bazan zura ido,kishiga wani hali ba,ni zani gidansu Aliyun dakaina na roke mahaifiyarsa yadawo ya aureki.."Tafada tana mikewa,da sauri kwamishina ya rikota yana fadin"Mamin Ni'ima where are u going? kidawo wannan ba mafita bace,infact ma yanzu aka kirani aka shaidamin basu bar wajen ba,Sai da aka Daurama Shi Aliyun Aure,kinga kenan ko kinje bazasu saurareki ba.."Kallonsa tayi hawayenta na zuba tace"Kaji ko? innalillahi wa'inna Alaihirraju'un wake da karfin gwiwan Tunkarar Ni"ima da wannan mganar,nidai bani dashi,wlh bani dashi.."Tafada tana kuka lokaci daya tana sulalewa daga jikinsa,Rumgumeta yayi yana bubbuga bayanta yake fadin"Banyi Tunanin haka,Sulaiman ne,ya dake kan baza"a Daura ba sai Dangin ubansa sunzo,wlh koni rainq babu dadi,shine ya dage,kuma kinga shine waliyinta bai kamata na tsinkashi cikin jama"a ba.."Dago kanta tayi tana fadin"Ka tsinka shi manq,say what,bakai bane gaba dashi ba,ai gashinan ya zugaka ka aikata Abunda yazo ya damemu,an barmu da wahalan zuciya data sarari,wlh Allah sai ya sakamana kan Abunda yayimana,kuma hakkin Ni"ima bazai taba barinshi ba.."Tafada tana fizge jikinsa,ta fito daga office din tana share kwallah,likita kuwa daman Ficewa yayi ya barsu,dafe kansa kwamishina yayi,kunyar Duniya da Nadama sun kamasa,itako Mami tana fita Munari tataso tana fadin"Mami ya jikin Sweetheart? tafada cikin damuwa,Wani kallon Mami ta watsama yan sanda take kare lafiyan kwamishina,lokaci daya suka fashe,ada sun kasa kunne ne suji mai zatace,hannunta Kawai mami takama suka koma suka zauna kantace"Komai ya dagule Muneera,don likita ya gayamana cewa zuciyar Ni'ima tayi Rauni,gashi kuma jninta yayi bala"in hawa,ceto rayuwarta shine bata Abunda takeso.."Dafe kai Munari tayi kantace"To Mami mai zai hana muje gidansu Soja mu gayamusu halin datake ciki ko Allah yasa zasu Taimaka ya aureta yanzu.."Girgiza kai Mami tayi kan tace"Hmm,ai bakin alkalami yari gaya ya bushe,muneera,kuma dama ance oppourninty comes one in life,ko kinmata,wajen su sukazo nema,kuma muka tozartasu gaban dimbin jama"a,Armm amaganar damuke ma yanzu basu tashi taron ba,sai da aka Daurama Aliyu aure,tayaya kike ganin zasu kallemu in mukaje musu da wannan bukatan,ai banajin zamu samu kyakayawan kallo,saboda mu muka saki damarmu.."Sadda kai munari tayi tana sharan kwallah takasa fadin komai,kawai jinjina al"amarin take,tanq ayyana yadda Ni'ima zata karaji matukar taji Sojanta yayi Aure,Mami kuwa tagumi tazabga,tana Tunanin mafita,Shiko kwamishina bai koma gida ba,sai da aka kawo Ni'ima daki na mussaman domin hutu,Mami ta bishi suka koma gida,don ta tahomata da kayanta da kuma tasaka masu aiki suyi girke tataho dashi.
______________
Azeema bata yi sanyi da jikinta ba,sai da tagama duka aiknta na tsakar gida,kafin takoma ta daura girki Tuwo da miyar kuka,tanayi tana shiga Tunanim yadda makomar rayuwartake,ita gani take kamar amafarki wai itace matar Aure,matar auren ma mata ga yaya Captain? Abun nabata mamaki,ammh sanin bata da wanda zata fadama damuwarta yasa ta ijiye komai gefe daya ta cigaba da aikinta,Ramatu kuwa sau daya ta leko waje,tagani ko Azeema na aikinta samunta tayi lokacin ma tana tsalge,kwafa tayi takoma dakina,tana zaginta ita da Babanta tana fadin"kwadayayyu kawai,watarana sai kwadayi ya kashesu.."itadai ko Tak batace ba saboda inda sabo yaci ace ta saba da Halin Inna Ramatun..
Azeeza kuwa kuryan Daki ta shige ta haye gado tana kuka wurjajan saboda bakin ciki da kishi kamar ya kasheta,gawani tsanar Azeema dayakara tasiri aranta,yanzu ace Tayi shekara da shekaru tana Rainan Soyayyar yaya Captain Aranta,ta wahala akan Sonshi tagama tsara yadda zasu gudanar da rayuwarsu,ammh lokaci daya mafarkinta yatashi abanza,koda Yaya captain zai aure,Ni'ima tayi kuka,ammh zuciyarta bata kusa bugawa ba sai da taji ance Adda Azeema ya aura"Bala"i batajin ko sama da kasa zasu hade zata iya barma Azeema Sojanta,domin tayi alkwarin matukar Tana raye agidan Duniya sai ta Aure yaya Captain koda hakan zaiyi sanadiyar salwartar da rayuwar Azeemar ce ita babu ruwanta,kanta kawai ta sani,Koda Inna Ramatu ta shigo ta ganta tana kuka idanunta sunyi jawur,cemata tayi kanta ke ciwo,jiki na rawa inna Ramatu ta ballo panadol ta bata ta sha takoma ta kwanta lamo tana saka yarda zata wargaza rayuwar Azeema don yanzu ita tafi tsana akan kowa..
Ana kiran sallar mangariba Azeema ta kammallah komai,ta zuzzubama kowa a muhallinshi,tayi alwala tashiga daki takabarta sallah ta idar kenan,taji sallamar Mallam lawal,da hanzari ta fito daga dakinsu tana fadin"Sannu da zuwa Baba.."kallonta yayi sanda take shinfadamai tabarma akofar Dakinsu Baiyi mgana ba,sai da ya zauna yace"Yauwa Azeematu diyar Albarka.."Yafada yana kallon Fuskarta sadda kanta tayi kafin ta mike tatafi randa ta debomai Ruwa cikin wani kofin sulba tazo ta ijiye kafin ta shiga kichen ta daukomai wasu kwanukan sulba na tuwo dana miya,tazo ta ijiye kafin takoma gefenshi ta zauna tana fadin"Baba ga ruwa kasha.."ta fada tana mikamai amsa yayi ya bude murfin ya kwafa kai yasha dayawa kafin yadago ya mikata yana fadin"Alhamdulillah,Allah yayi miki albarka Azeema.."Cikin jin dadi ta amsa da Amin,budemai tuwon tayi,ta zubamai ruwa ya wanke hannu yafaracin Tuwo,wanke hannunta tayi itama tasaka hannu sunacin Tuwon tare,wanda daman ko karfe nawa zai kai baidawo ba,Azeema bata iya cin abinci sai tare dashi,ta riga ta saba tun tana karama,Inna Ramatu tayi bala"in tayi tsiyan ammh duk bataci nasara ba itako Azeeza Abun na cinmata rai,shiyasa take fadin Baban yafison Azeema kuma ba karyabane kowani uba yanason da na gari mai hankali da Natsuwa da tarbiya.
Tsab suka cinye tuwon kafin su wanke hannuwansu,Baba nata santi yana yaba girkin Azeema yana fadin"Uhm,diyar Albarka ta iya girki fa,zan yima mijinki albishir da yagama yin dace indai ta barayin girki ne.."Dariya take,tana jin dadin yadda Babanta ke yabonta tashi tayi ta kwashe kwanunkan takai kichen,bakin rijiya ta nufa zata jawo ruwa ya kwalamata kira yana fadin"Bar zuba ruwanan Azeematu,na hanakin zuwa bakin rijiya da dare,maza ki bari ki zo ki zauna nan mgana zamu yi.."Yafada fuskarsa ba alaman wasa,ganin haka yasa ta ijiye gugan tazo tazauna kusa dashi tana fadin"Gani Baba.."kallonta yayi kafin yayi ajiyar zuciya yana fadin"Yanzu daga gidan Baba Ade nake tace na gaisheki.."Washe baki Azeema tayi tana fadin"Kawata kenan,ina amswa Baba meta baka kakawomin..? Yar dariya yayi yana fadin"Bata bada komai ba,sai gaisuwa,aike yakamata kije ki kaimata."Daganan sukayi Shuru,Dan gyara zama Mallam Lawal yayi yana Fadin"Azeema..."Ta dago ta amsa Tana fadin"Na"am Baba.."Cigaba yayi da cewa'Kiyi hakuri Azeema nayi miki katsalandan na yanke hukunci batare da shawaranki ba,duk da ina da tabbancin Na Isa dake,kuma bazaki taba watsamin kasa a ido ba.."Dagowa tayi idonta ya ciko da kwallah,tace"Baba wacece ni agareka.."Yace'Ke diyatace..."Azeema tace"To meyasa kake cewa haka,Tun tasowata bansan kowa ba sai kai,tun bayan rasuwar mahaifiyata baka barni nayi maraici ba ka wahala dani,kayi hidima dani,niko wacece ni da bazan zama baiwa gareka ba Baba.!koda fansar dani kayi zuwa wata masaurata domin bauta Bazan bijiremaka ba,ballatana,don ka bada Aurena ga yaya captain Da ga Goggo wacce ta kasance makwafin uwa gareni,ashe ko in naki bin umarninka na zama butulu,kuma ban cika y'a ba.."Tafada tana fashewa da kuka.
Gabadaya jikin Mallam lawal yayi sanyi,tsausayi tare da kaunar yarsa,da girmama Kaifin hankalinta suka taru,sukaima yawa,dafa kanta yayi wanda ta cukwikwiyeshi cikin hijabi tana kuka yana fadin"Kiyi Shuru Azeema,dama nasan bazaki bijiremin ba,Tashi ki shiga daki ki kwanta Allah ya albarci rayuwarki,dana Aurenki,Allah kuma yajikan mahaifiyar fatima da Rahama.."Da Amin Amin Azeema take amsawa tana share hawaye.
Inna Ramatu dake tsaye kofar dakinta tanajin duk Abunda suke fadi,taja wani dogon tsaki kan tace"mtsewwwww...Diyar so,an saka miki albarka,nikuma tawa wacce baka so ka tsinemata,dayake kwadayine,kazo kana lallabanta wlh mallam kaji tsoron Allah,ko fifinko dake nunawa kan ya'yanka Allah ya kamaka bazakaji dadi ba.."Ko kallonta baiyi Ba Azeema ta dago tana kallonta ranta na kuna ta shige daki tana fadin"Sai da safe Baba..."Allah ya tashemu lafiya.."yafada yana mike kafarsa ko kallon Inna dake tsaye tana jijjiga jiki bai yi,ba don ya lura sam Ramatu bata darajasa a mtsayinshi na mijinta,ta riga Tagama Rainsa,so take kullum su dinga hayaniya makota naji,shiyasa yake banza da ita,intagaji ta wuce,tunda ita ba karya bace.
#Commet,share, like and Vote..#
#Janafty ce....#
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_
*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_
*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA .S. ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent Writers Association*✏
*Chapter7*
Koda gari yawaye har sukaje massllaci suka dawo,Aliyu bai ko kalli barayin da Jabir yake ba,shima kuma bai tankasa ba,Suna dawo daga sallar asuba Aliyu ya shiga Hada kayansa cikin wata katuwar jakar baya,mai kalan Uniform dinsu na yaki,Jabir na kallonsa,ammh kanzil bai cemai ba,don ya lura sarautar tashi ta motsa,yana ji sanda Haisam yakiraasa suna gulmansa suna dariya,ammh sakamakon yau baya cikin mood din,nunamusu yayi baima san dashi sukeyi ba,ballatana ya tankamusu.
Misalin karfe 8:00am na safe,Wayarsa tana kara tana neman Dauki,ammh Da Aliyu ya dago yagamai kiran,sai ya kife wayar yana sakin Siririn tsaki,shi kadai Jabir yana kallonsa,yana so yagano waye ke kiran Aliyun ammh ya kasa ganowa,mikewa yayi daga kan gado yana mika yace"Dude wai shirin Tafiya ina kakeyi ne?Ko kallonsa Aliyu bai yi ba,illa kokarin zuke zip din jakar dayakeyi Dariya Jabir yayi yana fadin'Haba Dude don Allah warware jaka kada muje bariki ayi damu,kai zaka tsaya shan amarci sai nan da 2weeks zaka dawo bakin aiki.."
Wani Banzan Kallo Aliyu yayimai kafin yace"Ubanka ne zai sha Amarci ko? "Yafada cike da fusata baya jabir ya matsa yana fadin"Ah..No..No maida wukar daga Taimako Allah bada sa"a.."Kada kai Aliyu yayi kafin yace"Better Tunda barikin ba gidan Uban mutum bane,sai ya hanani komawa.."rike baki Jabir yayi yana yar dariya,Shiko Aliyu Tailet yafada Fuskarsa ahade babu alamar fara"a ko kadan,jabir bai damu ba,cos inda sabo yaci ace ya saba da Kala kalan Fuskar Aliyu.
Yana Shigewa Tiolet din ya Sufa zuwa ga wayarsa kirar iphone 9 yana Dauka Daidai kiran nakara shigowa *MUNEERA* batare dawani Tunani ba yadaga kiran ajiyar zuciya Muneera ta sauke kan tace"Hello Captain..."
Kansa Jabir ya shafa kan yace"Ya is captain buh not Captain Aliyu am Captain Jabir how can i help u..."Da Sauri Ni"ima ta karbi wayan tana fadin"Jabir don Allah kamin rai,ka hadani da Sojana,wlh zan mutu in banji muryansa ba.."Tafada muryanta na rawa,cikin alaman jin jiki.
Gyara tsayuwa yayi kafin yace"Am So srry Ni"ima bazan mezancen miki ba,buh u already know Aliyu in yayi inrin wannan kafewar to sai Allah saukowanshi,koda kuketa kira yana gani yaki picking yanzu ma he iz inside d toilet dat why ma na samu daman Daukan kiran,am srry to say buh Abbanki mai kyautama kanshi ba wlh.."Yafada yana cije baki kuka Ni"ima ta fashe dashi tana fadin"Oh ya Allah help me..Na shiga uku wlh zan iya mutuwa indai banji muryan Sojana ba"..Sai dai ko ki mutu..."Jabir yabata amsa Aranshi,yana yar dariya daidai lokacin da Aliyu ya fito daga tiolet daure da wani karamin Towel akugunsa,daya yana kansa yana tsane Ruwan dake diga daga kan nasa,yana ganin jabir da wayansa,ya tsaya cak yana jifansa da wani dirty look,shiko yana ganin haka,sai yayi hanzarin bude wayar a sepeaker,daidai lokacin da Muneera ta amshi wayar tana fadin
"Don Allah jabir do ur best wlh Sweetheart she seriously Sick yanzu haka muna Hopt tun jiya dataji Abunda ya faru,ta samu heartfailure,kabashi hakuri is not her Fuilt,yazo ya ganta ya lallasheta ko tabar kuka,wlh Tun data farfado take ta kuka tana kiran Sunansa plz Jabir..."Jabir yayi kasake yana bin Aliyu da kallo wanda ke rollin din idonsa yana wani cije baki,takowa yayi sai da yakusa gabda jabir kana yace da dan karfi.."Plz Dude tell dem to stay away From me..."Yafada muryansa na rawa,kallonsa jabir yayi sai yaga idonsa yayi ja,jijiyoyin kansa sun mike,Ajiyar zuciya ya sauke kan yace"Kunji ko,plz karku sake kira,sai na nemeku don Allah,kubarsa Abun ya sakesa tukunnah,Ni"ima may Allah (SWA) Shifa u Ameen..."Yana fadin haka ya datse kiran,dagachan bangaren Ni'ima tanajin muryan Aliyu sanda yake mgana,batama gama jin Abunda jabir ke fadi ba,takara tsananta kukanta,kallonta Muneera tayi kan tace"Don Allah Sweetheart kibar kukannan hakanan,kiduba halin dakike ciki,in Mami tadawo ta tarar dake cikin wannan Halin u know bazata ji dadi bako? so plz Wipe ur tear don Allah ba karshen rayuwa ba kenan,kuma da yardan Allah zaki auri Aliyu.."Idonta jawur ta dago tana kallonta kafin tace"Are U sure..."Gyadamata kai Muneera tayi kafin tace"100%Sure Sweetheart..."Share hawayenta tayi kan takoma ta kwanta ta kurama Drip din da"ake sakamata ido tana kallon yadda yake diga sannu ahankali,lokaci daya ta runtse idonta kwallah na zubomata,ta rigaya data sani tayi bankwana da dukkan wani Farinciki Tunda Aliyu ya bar Rayuwarta.
Suko Anasu barayin Jabir na yanke wayar yafada wanka,Shiko Aliyu agurguje ya Shirya cikin wasu riga da wando black and white,kafarsa ya sanya wani bakin takalmi booth,sai kansa ya sanya wata bakar p-cap,ya dau katuwar jakarsa ya rataya yana Daura agogonsa na kamfanin Rado baki ahannunsa,Jabir ya fito,ganin Aliyu atsaye yasa shima ya shirya agurguje,shima yayi shigan Riga da wando,ammh nasa Neavy blue ne,shima jakarsa ya rataya suka dumguma suka fito,makulli Aliyu ya sanya Ya rufe shashensa,suka fada barayin goggo wacce ke kichen tana kokarin hada musu Abun kari,taji sallamarsu Fitowa tayi tana amsawa fuskarta na bayyana farincikinta data ciki.
Ganinsu tsatsaye kuma ga kaya yasa tatsaya Tsurus tana fadin"Lafiyanku naganku da wata uwayen jaka.."Dukawa Sukayi dukkansu Aliyu na fadin"Ina kwana goggo,zamu koma kaduna ne,bakin aiki.."Yafada yana sunkunyar dakai,karisowa tayi tazo tazauna kan daya daga cikin kujerun falo tana fadin'"Kai ku kalleni nan bani son iskanci,ina zaku yanzu da farar safiya,kamar ana koronku,ina fa madafi Tundazu ina kokarin hada muku Abun kari ne,wlh baku isa ba,bazaku barni dashi ba.."Tafada cikin fada,Mirmishi Jabir yayi yana mikewa yace"Kwantar da Hankalinki Goggonmu basai kin bata ranki ba,zamu ci kalacin dakike Shiryamana kafin mutafi,medame dame aka Tanadarmana.."Yafada yana zama kusa da ita.
Washe baki yayi tana fadin"Yauwa Dan Albarka Kunun Shinkafane Sai Fanke danake soya muku,akwai Ruwan Tea wanda yaji citta,sai ku hada dashi.."Tafada tana kallon Aliyu dake duke,Mikewa tayi ta isa garesa tana fadin"Taso taso Gadanga,bar damuwa hakanan,ban hanaku tafiya ba,ammh ku karya tafiya da yunwa babu kyau,tunda gida kuke ba daji ba.."Tana fadi tana rikosa,mikewa yayi yana kallo goggo kafin yace"Karki cikamin ciki goggo,nakaasa jagorantan Bataliyan yaki na gaba.."Sajensa ta shafa tana fadin"Da"n nema kaida yakamata sai sati na sama zaka koma,tunda kana cikin Hutun amarci ne",bata rai yayi yana fadin"Soja baya Daukan Hutu goggo,koda yaushe burin sojan nageria kare dubban rayuwa daya rantsuwa wajen amsan kaki,saboda duk Abunda ya shafi kare hakkin kasata da al"ummata goggo bana jin son jiki a al"amarin...",kansa ta dafa tana fadin"Nasara tana tare dakai Gadanga,insha Allahu sai kasarka tayi alfahari dakai kamar yadda take alfahari da Sardauna.."Amsamata yayi da Amin,kan sukarisa ta zaunar dashi kusa da jabir tana fadin"Bari na kawo muku kalacin."Tafada tana fadawa kichen Jabir da Aliyu suka bita da kallon kauna da tsausayi.
Tana rawan jiki ta jera musu komai,basu ci da yawa ba,ammh goggo sai da ta dura musu kunun shimkafanan cikin wani karamin Flaks,sai Fanke ta zuba musu cikin wani karamar kula ta basu,tana fadin ko ahanya sukaji yunwa su tsaya su ci,amsa sukayi jabir na dariya,shiko uban gayyar yasan hali mirmusawa kadai yayi,sallama suka mata,Aliyu yaba goggo 10k dakyar ta amsa,wai yaya yabata kudi,har waje ta rakosu Aliyu ya Shiga garejin ya fiddo musu da motarsa 4matic baka,Suna kokarim Shigane sai ga mallam lawal ya fito daga gida,da hanzari Aliyu ya dakata bayan ya saka jakarsa abayan motan ya nufi mallam lawal yana dan Sakin Fuskarshi yana zuwa kusa dashi ya rankwafa yana fadin"brka da safiya Baba."Rikosa Mallam lawal yayi bakinsa washe yana fadin"Tashi Tashi gadanga,Lafiya kalau,ya katashi,yakuma kwanan goggonka.."Mikewa yayi yana fadin"Tana lafiya baba,dama zan wuce saboda ankira bakin aiki akwai wata bataliya da zan jagora zuwa yankinnan na zamfara ne,shine nakeson mu shiga kaduna da wuri.."Gyada kai mallam lawal yayi yana fadin"Eh gaskiya to Allah ya taimaka Allah ya doraku bisa kansu,kukuma Allah yayi musu albarka.."Da Amin Amin Aliyu ke amsawa kafin yamikama mallam lawal hannu sukayi musabaha,yana fadin"Zan Tafi baba,..Arrrm *AZEEMA* tacigaba da zuwa mkrantanta both islamiya da boko,in tana bukatar wani tashiga wajen goggo,Don Allah Baba ayi hakuri da yanayin aikinmu sai na dawo sai munsan Abunyi.."Girgixa kai mallam lawal yayi yana fadin'"Ah babu komai Aliyu Fatanmu Allah yabaku nasara,sai ka dawo.."Da haka suka rabu cikin mutumci,yana tsaye har motansu Aliyu ta bace Alayin,kafin ya fara share inda zai basa kayan gwarinsa,yana yi yana girgiza kai in ya tuna tijaran da Ramatu tayi yau da safe,Abun sam babu dadin ji.
*********
*NIGER REPUBLIC*
Awani babban masarautace dake yankin *AGADEZ* Da misalin karfe 3:00pm na silasailin dare ne lokacin adaidai lokacin acikin kayatattaciyar masaraurar wacce takwafa tarihin na tsawon shekaru hamsin da doriya ta mulkan yankin na agadez.,masauratace babba wacce take kunshe da tarihai masu dimbin yawa tunkam zuwan addinin musulunci,Yanzu da ilimi ya yawaita akasamu yan boko suka mulki masarautar ansamu chanje chanje masu dimbin yawa,ciki harda rushe masarautar zuwa na ginin zamani mai kayatarwaa,kana dumfaru masarautar gininta da yanayin tsarinta zai burgesa yakuma baka sha"awa,uwa uba yadda take da uban dakarin yaki da masu tsaronta,masaurautace babba mai cike da bayi da wadanda suka jibamceta.
A babban shashen dayafi kowani shashi girma da kyau da tsari Wanda ya kasance shashin Ranka ya dade maigirma sarki kenan,wanda yake kwance akan makeken wani mulmulallan gadonsa mai kyau da tsari,wanda yaji Shimfidu Na alfarma Adalin sarkin ne da kansa kwance yana barci kamar kullum mafarkin daya saba yine yau ma yakeyin irinshi na yau ma yaso ya bambamta dana koda yaushe domin Fuskar matar hartaso ta bayyana garesa sai kuma yayi Firgigit ya farka daga barcinsa nasa yana salati lokaci daya zufa na ketomai kota ko"ina,Gimbiya FASILA ce yau aturakar ta Sarki da hanzari ta mike tana kallonsa kan tace"Ranka ya dade Allah kara lafiya meya faru ne,naga ka mike afirgice kana salati..? tafada tana kunna hasken dakin wanda ya gauraye lokaci daya.
Kallonta yayi baice komai ba,illah zuro kafafunsa dayayi ya sauka daga kan gadon ya zura wani takalmi mai gashi ya dumfaru wani dan daki da gefe,tabe baki tayi takoma ta kwanta aranta tana mamakin meke damun yallabai ne haka,duk kusan matan nasa ba wacce bata fuskartan wannan mafarkin nasa duk ranar girkinta,in baiyi wannan karon ba,wani zagoyowar zai faru,kuma ko kayi tambayan Duniyan nam baya kulaki ballatana ya baki amsa,Tana kallonsa ya fito Fuskarsa da farin gashinsa na digan ruwa alamar alwarla ya dauro ko kallonta baiyi ba ya isa ga wani dan korido inda wani shimfidaddan cafet yake mai kyau da tsari gefe daya carbi ne,sai daga baya wani cabinet ne,mai dauke da qur"anai da sauran littafai,bai bata lokaci ba ya cire fararan kafafunsa cikin takalmin na sarauta ya isa ga cafet din ya daidai sahu ya tada sallar,sai da yayi raka"a goma sha uku kana ya sallame ya zauna yana lazimi tare yima Annabi salati,aransa yana fatan Allah ya bayyanasa komai miye yake so ya bayyanass masa cikin mafarki Aransa yanaji kamar wani nauyi ne,da hakkin akansa wanda ya rataya awuyansa shekara da shekaru baya saukewa domin da alamun matar dayake ganinta tana bukatarsa cikin mafarkin kuma Abunda yafi daure masa kai yaron dayake tare da ita,wnda kowani lokaci yaron yana so ya iso garesa ammh kuma nisa da tazaran dake tsakaninsu baya barinsu su iso garesu da zarar kuma haske ya bayyana garesa domin ganin Fuskarta sai ya farka daga mafarkin wanda ya dau tsawon shekaru Ashirin da biyar yanayinshi,dayake shi mutum ne mai riko da addini bai yarda da duba ba,babu abunda yasa akayimai ko masu fassaran mafarkin da Ummansa mai babban daki ta sanya ayimai hanata yayi,yace ta barma Allah koma miye Allah zai yayi duhu cikin haske.
Yadade yana addu'oinsa kafin ya shafa gabda gabatowar asuba cigaba da zamansa yayi yana kwaroroma Allah kirari yana kiran anyi kiran sallar farko ya nufi masallaci domin duk sanda yayi wannan mafarkin barci kaurace ma idanunsa sukeyi.,Itako gimbiya fasilatu Tuni takoma barcinta ko ajikinta domin inda sabo sun saba da wannan al"amarin yallabai Adalin sarkin mijin nasu
If the outcomes fulfill you, hold enjoying in} it but in addition strive other 솔카지노 titles to see if there may be a better one. In this fashion, you will progressively slim down your selection to slot machines that have a tendency to give good outcomes. Let’s strive our free slot machine demo first to understand why slot video games are continuing to grow in today’s playing.
ReplyDeleteTo win huge on this recreation, gamers must bring their greatest abilities, technique, and angle when making an attempt their 온라인카지노 luck at beating the machine. Although a number of the} methods for video poker often a|could be a} little complicated, the rewards for understanding and implementing them is nicely worth it. So, go find a penny slot machine and bet 1-cent 5 times in a row. Try the subsequent machine that’s additionally been sitting idle for some time. If this retains occurring for all types of slot machines, then you can to|you probably can} count on it to occur with that casino’s video poker machines. The methods come down to whether you’ll discard or hold certain cards from the dealt first 5 cards.
ReplyDelete