da daddare basu wani hiraba sanadin hadarin da ya hadu, daki suka shiga suka kwanta ba a dade ba ruwa ya sauko sosai, haka aka kwana ana ruwa, da asuba malam sukaje sukayi sallah, inna da zainab sukayi acikin gd, haka suka yi koko da kosai shuka karya, bayan sun karya sukayi wanka,..
Bayan sun kan mala komai lokacin gari ya dan sha, kafin suka fito gidin biyar kofar gdn kasancewar garin ba mutane da yawa, don gida daya na da rata tsakaninsa da wani gd,..
bayan sun zauna malam ya bukaci ammar da ya cigaba da lbr sa…
Ammar ya cigaba da cewa bayan na mai dugri mun dau hanyar kaduna, sai dare muka iso kaduna don driver ma na gudu sosai, ko da muka isa garin kaduna, mun sauka a kawo, nan kowa ya fita don ya tafi girin da yazo, ina ina tsaye ni da wani a gefena sai ga mai taxi yazo, yana fadin Abuja Road Magajin, nan mutumin yace nan zaije, take nima na shiga taxi din munyi tafiya mai nisa ina kale2 don yanayin garin yayi kyau sosai, ahaka dai muka iso magajin gari nan mutum ya sauka nima na sauka, ko da na fito na rasa inda zani, hakan yasa nazo masallaci nayi sallah kafin na bar masallaci don na fara jin bacci, kofar wani shago na samu na kwanta don na gaji sosai, kwanana 3 a gurin ganin kar mutanen gurin su zargeni yasa na dau ledata na fara tafiya, nayi nisa sosai kafin naga wani guri mai gine2 na sama ga jama a sosai, daga nesa naga an rubuta “CHE CHENIA MARKET” da manyan harufa, nan nasamu na kutsa, kusa da shagon mai takalma na zauna.
na kwana biyu ina zama a gun har na dawo dan aika a gun, abinda na lura a kwai wani shagon takalma da less da material, saman shagon an rubuta “ZAINAB FASHION DESIGN” a bunda na lura akwai wani alhajin da ke yawan zuwa da yarsa wata kyakyawa na karshe, suna sayan kaya ne ko mai sukeyi ban sani ba, tun da na kalli yarinya naji ta kwanta min a rai ina sonta da kanwa, hakan yasa duk randa zasu zo in sun sai kaya zanje in dauka musu in gaida alhajin ko da babanta zai bani kudi bana karba, sai yayi da gske nake karba, hakan ya mana masa dadi, har yasoma tambayata inane unguwan mu, nan nasoma hawaye ganin haka Alhaji ya kama hannuna muka nufi motarsa, munyi tafiya mai nisan gske, har na fara tsoro ko dan yankan kaine, nan nakama adu’ah neman tsari, mun isa wani unguwan da ba mutane sosai, sai da mukazo kofar wani katon gd mai kyau horn yayi aka bude kofar, gate din, gd ba laifi kam yayi kyau sosai.
Munshiga cikin gd mata kyakyawan mace ta fito da murnanta, tana sannu da zuwa Alhaji, nan ta kalleni, tace Abban Auta ina kasamo wan nan yaro mai kyau haka, Alhaji yace bari mu zauna tukun.
®WHW®
Rash Kardam
[6:40PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Muna isa gd wata mace kyakyawa ta fito, tace sannu da dawowa Abban Auta ya hanya, cikin sakin fuska ya amsa lfylau Alhamdulilah, tace ina kasamo kyakywan saurayi haka, dad yace mushiga ciki tukun, Allah sarki dad gwanin taimako, ko da suka shiga cikin gd abinci ta kawo musu nan Ammar ya faraci daman da dan yunwa ajikinsa, har saida dad ya tausaya masa sosai,
bayan ya sun ci abinci ne dad yace suje falo koda sukaje nan ya tambayi Ammar mai yasa yake kuka da ya tambayesa, san nan ina iyayensa, nan idon Ammar yaciko da kwalla, dad ya rararshesa, Ammar ya basu lbr iyayensa dad saida yayi kwalla ya tausaya masa, kafin yace ya kwantar da hankalinsa zai rikesa, bisa “AMANA” nan Ammar yayi godiya dad ya kaishi dakin da ke waje gefen na masu gadi ya ce ya zauna anan.
Dad ya saya ma Ammar kaya bana wasa ba haka ya cigaba da rayuwa acikin gidansu Auta gashi sun shaku da Auta sosai, a iya zamansa a gd yanda yasamu lbr a gun dad wata rana suna zaune ya soma bashi lbrsa dake sun saba sosai2 dad ya ja shi ajiki,..
Ammar sai da ya kurbi surki mai zaki yaji suga kafin ya ci gaba da cewa barin baku lbr Auta a takaice
Wacece Auta Zee
Asalin Alhaji Al-hasan Kano haifefan dan garin kano ne, zama ne ya kawo su kaduna dake yayi karfi anan yake kasuwancin sa, tun da ya dawo kaduna bayan rasuwan iyayensa , sai ya dibo yan uwansa ya sasu akan dukiyarsa, mahaifiyarsh ita kadai ta haifa yayinda yake da yayu yan uba wato Sani da Isiyaka uwar su daya yayinda Sani shine babba sai Baba isiya ka,
Baba sani yana da yaya 4 Sadiya itace baba sai kabir san nan Anas sai Autarsu Sa’dat sun kasance abin so gun iayensu da kulawa Baban Auta shi ya dauki nauyin karatun Sady ya hada su da Auta gashi jininsu yazo daya baka rabasu ko ina taresuke,.
Baba isiya kuma matarshi daya da yara 2 Fauziya ana kiranta da pinky sai kan warta faima sina kiranta da faty, haka rayuwa tayita tafiya.
Dad ya kasancr mai yawan taimako da son talakawa sabanin yan uwasa da ko kyauta yayi sun rinka mita kenan basa son ganin wani ya rabe shi baran in yana taimaka masa,
tun randa suka san dad ya kawo gdn suka fara hada rai in ko mun gamu zagi da hantara ba wanda ban sha duk in kauda kaina sabida dad ya rikeni da “AMANA” hakan nazamo mai aika a gd kuma wani lokaci mina tare da auta da Bilisu kawarta yar makwabtasu wato yar inspector Abubakar bilki kasancean sunan maman babanta ne shiyasa suka boye sunan ana kiranta da futha wato fatuhatul-khair, ba karamin shiri futha da Zee Auta sukeyiba, haka Ammar yana ji da ita.
Hajiya Aysha itace maman Auta ita kadai dad ya aura tun aurens da yan watanin Allah yabata cikin cikin ikon Allah cikin baizo da wani laulayiba, nan tayita kula cikin koda wata haihuwanta yazo nan ranan nakuda ta kamata basu jima da zuwa asibiti ba ta haifo yan biyunta kyawawa mace da na miji murna gun dad ba’a magana nan suka dawo gd, tun kafin suna na mijin ya rasu ya rage sai mace, mum tayi kuka daga karshe ta hakura ranan suna yar taci sunan zainab zainab wata ta 4 ta kamu da rashin lby, asai bana tashiba basuyi dogon jinya ba Allah ya karbi abusa, tun bayan rasuwansu hajiya bata sake ko bariba sai bayan shekara 5 ta samu cikin Auta nan suka dau son duniya suka daura akan cikin nan bayan wata tara ta santalo yarta kyakyawa nan taci sunan Zainab, haka sukayita rai non xee harta girma.
Tun da na dawo gd Alhaji ya mai dani makaranta nan nacigaba da karatuna ina dawo inyita wasa da Zee da futha, ko muyita karatu haka rayuwa tayita tafiya
Su baba sani basuda birin da yawuce suga na bar gun dad don ba zan manta ba akwai randa suka min sharrin sata ranan nayi kuka kamar raina zai fota.
®WISDOM HAUSA WRITERS.
Rash Kardam
[6:40PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Duk wani abun da zasu min na kanyi, hakuri in jure don ba dansu nake zama ba,
haka rayua tayi ta tafiya har na gama HND a gidan dad na karanta fanni business, yayin da Zee Auta ta gama secondary school dinta ita da Sadiya da futha, ranan murna ba a magana don sai da dad ya shirya mana kayatacen liyafa, bayan mun gama mun dawo zaman gida sai Auta da ke zuwa islamiyya, ni kuma duk wa aiki ina yi duk da cewan sun hana ni yi amma nakan sa kaina wani lokacin.
samun shigan da nayi a gdn shi ya daga wa maikatan gdn han kali har suke ga su da suka dade ba a musu abunda ake min, tun daga ranan suka fara kule2 na hanyar da zan bar gdn.
Baba sani da kawu isiya burinsu yanzu shine tayaya dukiyar dad zai dawo hannun su don kulum samun cigaba ya keyi, kuma ba abunda suka tsana irin yawan sadaka da kyautata wa mutane, acewar su baisan zafin dukiyar sa ba, sun sha zuwa su samesa gameda ya daina yawan rabar da dukiyan sa, yaki, ya ce in dai akan wan nan ne kar su sake tun karansa, tun daga lokacin suka fara kule2 na makircin kawar da Dad.
Basu tashi razana ba sai ran da dad yace musu zan fara aiki, a gurin kuma yanzu zai bani manager a company nin, ko kuma duk wani shiga da fuce kudi yazama ta hannu nane, ko wani kayan da za’a saya duk zai dawo hannu na,
ran da dad ya sanar min bakaramin murna nayi ba har kuka nayi, asai akwai irin su dad a duniya, asai bazan yi maraicin iyayeba, dad yayi ta lalla shina,.
Han kalin su baba sani ya tashi matuka, nan suka fara shawar su jefa dad acikin ruwa nan baba isiya yace tayaya zamu jefasa, haka sukayita shawar wari, har baba sani yace mufara masa baraza ya daura mu a kan dukiyar sa, ko ya bamu in yaki sai muje gd mukashe shi da iyalansa da dan koran da ya daura akan dukiyar, nan sukace gakan za’ayi, tun daga wan nan rana suka soma kiran dad suna masa bara zana, akan dad ya basu dukiyar sa yaki, don har nima a sha yimin barazana akan na bar gdn dad amma naki don da Allah na dogara nan da dad zai rasu ya kiramu ya bani AMANA zee san nan yasanar mana ana masa baraza, amma yaki fadan ko suwaye, bayan da ya fita ne na kirashi a waya na tambayesa da farko ya ki fada min sai da na sanar masa cewa nima ana min baraza na, na basa lbr kafin ya ban lbr komai yace da kar in sanar da xee hankalinta zai ta shi, da daddare suka zo don kashe mu gaba daya cikin ikon Allah ya kubutar da ni da Auta kuma a lokacin taga wayan da suka kashe mata iyaye, dali2 da yasa yanzu na sanar mata kenan wannan shine lbr mu, Malam da inna laure suka dago fiskansu cike da kwalla ga tausayi auta ma kukan take ni kuma hawaye ne, wani na bin wani.
Malam yace Allah ya jikan iyayenku, san nan a duniyar nan har ana samun marasa imani irin wayan nan mutane sun ci AMANA ga bata ZUMUNCI da sukayi ba ko tausayi a ransu sai son duniya, kuyi hakuri da rashi, da sannu Allah zai toni asirin su ya kuma saka muku, Allah ya jikan su muka amsa da Ameen.
Yan uwa amin afuwa na rashin jina kwana 2 waya tace ba charged, kuma ban samu zama ba.
Luv u all my fanz
®WISDOM HAUSA WRITERS
Rash Kardam
[6:40PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Bayan sunyi sallah isha’i suka dan yi hira kasancewar lokacin damina hadiri ya hadu aka soma iska, dole yasa suka shiga dakunan su don bacci, ruwa akayi sosai washe gari da safe bayan sun karya ne, Malam yayi shirin zuwa gona nan Ammar yace zai bi shi suka tafi tare, inna da Auta sukayi aikin gd.
Haka rayuwan su ya kasance acikin kauyen cikin kwanciyan hankali, yau kwanan su 10 kafar Auta har ya warke, Ammar ma ciwonsa ya bushe har yayi bawu, nan yasoma tunanin mafita don zamansu kauyen kaduna sam baiyiba, don marasa imanin nan suna sanin yana cikin kauyen to zasu iya turowa a kashesu baki daya, malam ya samu ya masa baya ni yana so su kara gaba don in mutu nen nan suka samu lbr zasu iya turo wa a kashesu malam yace hakane jiki ba kwari ya dau ko yan kudinsa da ya tara na kayan gonan da ya sayar ya basu yace suyi guziri inna kam da taji zasu tafi har da yar kukanta don sun shaku auta ma tayi hawaye, washe gari alhamis suka fito da ga kauyen nan suka shiga motar zuwa rigiyar malam wani kauye da ke jahar bauchi, a cikin motar suka zauna shiru ba mai magana sai yan motan da suke hira duniya.
Haka har suka iso wani kauye wai shi na bardo, nan yaga ana sauka kawai sai yace bari su sauka gurin nan suka sauka, koda suka sauka gefen rumfunan garin dake bakin hanya ne ya sayo musu fura da nono roba biyu ya ba ma zee ta amsa, tafara sha kenan sai ga hawaye, ammar na ganin haka yace Auta hakuri zakiyi shi rayuwa haka take yau dadi gobe ba dadi mukasance cikin gode ma Allah, sai ya kara wada yar mu cikinta yayi sanyi amma takasa shan nono, wai ita ce yau a titi a kuma kasuwa take cin abu, rayuw kenan Allah ya jikan su dad, ganin taki sha yasa Ammar yakasa sha shima, don baya kaunar ganin zee cikin tashin han kali, nan2 sai yashiga damuwa.
haka suka bar gurin suka dawo gindin wata bishiya suka zauna, lokacin sallah yayi ya nufi masallaci, yayi sallah dake a gefensu yake bayan ya idar ya dawo auta tayi alwala ta shinfuda dan kwalin zanin da inna ta fata ta daura, tayi sallah, haka har dare yayi koda aka watse gashi basu san kowa ba, Ammar ya duba musu gurin wani mai shayi da benci a gun nan ya hada ma auta kwaya biyu yace ta kwanta, haka ta kwanta idonta na zubar da hawaye, tabbas tasan ammar ne kadai ya rike iyayenta da gsky, Allah ya saka masa da dawai niyar da yakeyi da ita, Allah ya jikan iyayenta da nasa Ameen, Ya Allah ka bani abunda zan saka ma Ammar da shi, kuka ne yazo mata marar sauti haka tayi mai isarta daga baya tayi shiru, ammar ko kasance wan benci biyu ne a gun mai shayi ba wanda zai kwanta yasa ya dan zauna ya jingina da jikin falangen gurin shayi haka har bacci ya daukesu.
Cikin dare misalin karfe daya da rabi, cikin bacci Ammar ya rika jin ihu daga nesa tun abun na nesa har ya matso kusa sai auta ma taji ta tashi, ihun yayi yawa gashi gudu sukeyi sai a lokacin yaji ana cewa barawo barawo, yace ma auta ta tsaya kar ta fito jikinta sai bari yakeyi nan ya fita itakuma tana lekawa, aiko yana fitowa sai ga wani tutum da gudu yabi bayan gurin shayi ya gudu, ana haka sai ga mutanen sun yi kansa suka nan suka fara dukansa suna shine barawon, auta na ganin haka tafito da gudu ta na ihu, wayyo Ammar dina ba barawo bane, wayyo dad kuzo ku kuga halin da muke ciki zasu kashe shi kansu tayi gadan2 tana so ta kutsa, da kyar ta samu tashiga dai2 wani ya kai masa duka da dorina kenan ya sauka akan Auta nan tasaki wani razanen kara.
®WISDOM HAUSA WRITERS
Rash Kardam
[6:40PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Wani kara tasaki, sai a lokacin suka kula da ita, take suka haskata da toci sai sukaga macece, wani daga cikinsu yace mai ya kawo wan nan guri, sai da yace tsaya in ga barawo nan tukun don wancan gajeren wando ne ajikinsa, yana haskawa ko ah… ah.. wan nan ba barawon bane to ina yayi, sai dayan yace wan can na da kirar gutun mutum, auta ko sai ihu take, ammar ko motsi ba yayi sanadin dukan da aka masa harda bora, wasu ice haka akayita kwana masa.
A kaduna kuwa sadiya Al’amari abban ta ya daure mata kai don yasaka dukiyar auta gaba sai ci sukeyi, a ko a jikinsu, wata ran kam ma intasoma masa zancen auta ya hauta da fada kenan, haka yasa ta soma zargin wani abu a tare da su,
Wani yammacin asabar sun fito gidansu futha suna tattaunawa akan batun auta da yanda zasu bi al’amarin kenan sai suka hango abban sady, tun daga nesa yasoma wurga mata wani kallon tuhuma, ganin haka yasa tayi sallama ma futha tashiga gd, aiko kamar jira yake yazo ya fara zazzaga mata bala’i akan tafita harkan futha ko ya saba mata, shi baya son kawancen su, ganin su tare ma baya so, sady tace kayi hakuri abba ina tarayya da ita ba dan komai ba sai tun auta ta nan muna tare mun kuma shaku, abban sady yace hungo nan uwaki da autan nace uwaki da auta kar ki kara kira min sunan wayan nan banza mutanen,
nan take idon sady ya kawo hawaye ita kam bazata manta auta ba aminiyarta jininta, anya baba na da imani kuwa ko tausayinsu babu a zuciyarshi ko ya manta dukiyar iyayenta yake wada kansa shi, ya Allah kasanya mana tausayi da imani a zukatan mu Ameen ranan tayi kuka haka ta yini sukuku, sai yamma tayi shirin issalamiyya ta tafi ko da taje nan ta saida wa malaman su akan sutayata adu’ah ta kuma musu bayani ko mai ake ciki, tun daga ranan ya zamana kulum a makaranta bayan an gama karatu sai anyi ma auta da iyayenta adu’ah.
Futha kuwa kwana 2 taji sady shiru nan tashirya ta shiga gdnsu aiko nan sukayi karo da abban sady, tun daga nesa yasoma hararanta, tana isowa kusa yace kee wajen wa kika zo cikin ladabi tace baba kawar Auta ce nazo gun sadiya ne, yace maza ki juya kar na kara ganin lafarki a gdn nan yata batayi kawance da ke ba don ban yarda da kee ba.
ran futha in yayi dubu ya baci haka ta juya gd jiki ba kwari kuma tana tunani akan al’amarin nan,
anya ba hannu baban sady a kisan su abban auta, to tabbas ko ma miye sai na binciko ko da hakan yana nufin rasa raina ne ya Allah ka bayya na gsky.
Muta ne da ke gun duk suka soma watsewa ganin baya motsi gashi sun dakesa ba akan wani laifi ba, gudun shiga Case, auta ko in banda kuka da ihu ba abinda take sai kiran sunan Allah ga idonta har ya kubura yayi ja ga ammar shi da matatce marabansu kadan ne, wayyo Allah na ka taimaka min ka min agaji in ammar ya tafi bani da wanda zan kalla inji dadi, rayuwata zata zama abar tausayi Allah kaine gata na ka tai make ni ammar dina ya tashi, cikin kuka take jijiga Ammar ga hawaye ga majina duk sauka sukeyi, Ammar dan Allah ka tashi kar ka barni ka manta Dad ya baka “AMANA TA” ka tashi ka kula da “YAR AMANA” ka kuka take sosai mai ban tausayi tana ta surutai amma shiri ganin haka yasa takara fasa wani kuka mai ban tausayi wanda ni kaina Rasheedah ban san lokacin da na fara zubar da hawaye ba, gsky Auta da Ammar kun ga jarabawar rayuwa ga wlh Allah sarki auta abun tausayi, Allah yasa ammar dinki ya tashi Ameen.
Jumma’at Mubarak 2 all my muslim sisters n brothers.
®WISDOM HAUSA WRITERS
Rash Kardam
[7:32PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Kuka take sosai ammar ko motsi baiyi ba nan takara jin natsara su baba sani suka jefasu cikin irin wan nan halin, wani bawan Allah ne mai tausayi ya dawo yace bai war Allah daga ina kuke, cikin kuka tace ka taimaka min dan uwana ya tashi shikadai ya rage min an kashe iyayenmu, nan kukanta ya tsananta cikin tausaya wa yace ki tsaya tai mako daya zan miki yanzu ga gidan mai gari can barin je na kirashi da gudu ya tafi ko da yaje ya jima yana buga kofar kafin aka bude, masa, mai gari ya fito suka gaisa nan yasa sai damasa cikin damuwa mai gari ya dauko garensa ko da suka zo har lokacin ammar bai farfado ba, hakan yasa suka daukesa zuwa asibitin garin nan aka bashi agajin gaggawa, bayan sun dan masa treatment ne suka shin fidesa akan yar gadon asibiti, auta ko in banda kuka ba abunda take, bayan ansa masa ruwa mai gari ya musu sallama akan da safe zaizo duba su, auta kasa bacci tayi ga haddiri ya hadu nan akara walkiya da sauri ta haye karamin gadon duk tsoro ya ci kata baran data ga wajen asibitin jeji ne, nan ta kan kame ammar sosai hawayen ta na sauka a akan kirjinshi cikin barci yaji an kan kamesa, a han kali yasoma bude ido yaga duhu da kyar ya iya daga hannunsa yaji auta ne nan kuma yayi kokarin mikewa kansa ne ya masa wani nauyi ga sara masa da yakeyi, a hankali ya shafa kan yaji bandeji ne an daure, sai a lokacin ya tuna mai ya faru hawaye ne yasoma zuba masa shima tabbas yasan suna cikin wani yanayin da Allah ne kadai zai fiddasu.
Auta jin alaman na motsa hannu yasa da sauri ta shafi fiskansa nan taji hawaye a hankali ta daga hannun ta tasoma share masa hawaye tana cewa kayi hakuri Allah zai saka mana kaji kuma Allah yana tare damu yaga halin da muke ciki ba zai bar mu haka ba, nan ya karajin jikinsa ya mutu ga auta da ta kwanta masa ajiki bai san lokacin da ya sauke ajiyar zuciya ba, har azuciyansa yana son auta ko da aure zatayi ba iya bayar ta ga wani ba don bai son wani yaci Amanar da dad ya basa ko in auta tace bata sonsa to dole ya hakura don ba zai takura ta ba, gwanda ya shiga ko wani irin hali ne da ya sata a damuwa.
a hankali ya kara kan kameta a jikinsa wanda sai da itama taji wani shock ya ziyarci jikinta ajiyar zuciya tayi ahaka suka kwana yau kam bacci mai dadi tayi ajikin Ammar wanda rabonta da ta yi tun iyayenta suna da rai, sai da asuba ta mike da ta fiti kofar asibitin in da taga randar ruwa ta diba tayi alwala ta shin fida dan kwalinta tayi sallah,
bayan ta idar ne ta zo da ruwan ammar da kyar ya iya tashi sabida jikinsa yayi tsami tana zuba masa ruwan yayi alwala yana kwance yayi sallah don kansa ya masa nauyi.
Sai da gari ya waye sosai gurin karfe 9:00 mai gari yazo duba sa da yar kununsa a kwanon sha da kosai nan suka gaisa bayan sun gaisa ya ke tambayan su mai ya kawo su gari da har zasu kwana a kasuwa nan auta ta basa lbr ya tausaya musu sosai, nan ya musu sallama akan darana zai zo dubasu auta haka take kula da ammar dan kudin da malam ya basu shi suke yasan abun da ya dan musu su ci, kwanan Ammar uku a asibiti aka sallamesa jikinsa ya warke sai tabo, ko da suka fito a asibiti gdan mai gari ya nufa ya masa godiya san nan yace yana so su kara gaba don yana son cikin birni inda zai samu sana’a yayi da karfinsa, nan mai gari ya ce yanzi kana fita sai garin bauchi shine babban gari, nan yaji yana son garin don ya dade yana jin lbr garin bauchin yakubu ga Addini ka mutunta mutum ga iya karama baki, ga masa waina sai wanda kazaba, nan yayi godiya mai gari ya rakasu suka shiga motar bauchi.
Rash Kardam
[7:32PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Mota su ka shiga, a hankali suke tafiya, haka kurum ya tsinci kansa da farin ciki, tun a hanya yaji yana son garin ya burge shi.
Auta ma haka abun yake tana gefen Ammar ta dan jingina kanta a kafadarsa, haka kurum take jin sanyi a zuciyar ta, nan ta fara tuna irin rayuwan da sukayi abaya lokacin iyayenta suna raye, ku ina zataje a mota suke tafiya mota mai AC ba hayaniya, amma yau gata a motar kasuwa, Allah sarki yarinyan da taso cikin gata da kulawa ya daya tilo yau gata a cikin gararin rayuwa Allah ya kawo masu sauki Ameen.
Karfe goma da minti sha uku, suka iso cikin garin bauchi, driver ya sauke su a waje tashar mota na winti market, nan suka sauka, kowa ya kama gabansa, Ammar ya riko hannun Auta suka bar gurin, titi suka tsallaka suka zo ta gefen stadium akwai dan guri nan suka zauna, kallo daya zakayi ka ga kamanin su auta yanda ya canza sunyi baki ga rama da sukayi sosai.
Sun dade a gurin sosai, amma sun rasa inda zasuyi can yace bari yaje ya nimo musu abinci, tace to gefen gun masu sai da jarida da gyaran mashin ya ga mai sai da shinkafa da wake nan ya saya musu roba biyu da pure water kwaya 2 ya kawo musu, haka suka ci sukayi godiya ga Allah ya mayar wa masu shinkafa ya karbi canji ya dawo, haka suka zauna sai da aka kira sallah, nan ya sake saya mata ruwa tayi alwala shi kuma ya tafi masallacin da ke gefe yayi sallah, bayan ya dawo suka zauna hira ya rinka mata yana bata dariya don ya debe mata kewa sabida yaga damuwa a idonta sosai, haka suka yini har dare agun suka kwanta.
Da gari ya waye sallah yayi yace ta zauna a gun kartaje ko ina zaije ne man abunyi ko da dako yasamu don su rinka samun abunda za suci da in da zasu zauna, haka ko akayi ya shiga cikin kasuwar winti, haka yayi yawo sosai amam shiru ba lbr aiki sai azahar ya dawo yaje ya sayo musu shinkafa sukaci, bayan sunci tace Yaya na anyi nasara kuwa cikin mutuwar jiki yace ina Allah baisa an dace ba, idonta yaciko da kwalla tana shirin yin kuka ya girgiza mata kai alamar aa, yace ko kin manta Allah yana tare da mu bazai barmu haka ba, kuma duk bakin da Allah ya tsaga bazai hana shi abinci da zaici ba.
haka suka sake kai dare nan suka sake kwana.
Washe gari ma haka yafita yayi yawo har ya gaji gashi yan kudinsa sun soma karewa saura dari biyar, yau sai bayan la’asar ya dawo dake ya ba ma Auta naira dari don tasayi abunda zataci ko da yadawo yasamu tana bacci akan yar fallen zanin da ta shimfida tausayinta ya kama shi, Allah sarki auta yau itace tamkar wata tsintaciyar mage gwamma shima namiji ne, idonsa ne ya ciko da kwalla a zuciyarsa yake adu’ah Allah ya kawo musu dauki baisan hawaye yana sauka da ga idonsa ba saiji yayi auta na share masa hawaye itama idonta yaciko da kwalla, tace Yaya na sai dayaji sanyi har cikin ransa, mai yasa ka kuka ban son ganin hawayen ka, in kai kayi hawaye wazai rarrashe ni, kaine mai sani farin ciki, Allah gatana kaine gata na, yaya na waya taba ka karkasa kanka cikin damuwa Allah zai kawo mana mafita yana tare damu kaji, kaman karamin yaro ya daga mata kai, tace kayi min murmushi, ammar baisan lokacin daya murmusa ba, itama murmushin tayi ta rike hannunsa tace Ya Allah kaja kwanan yaya na kabani abunda zan saka masa dashi.
®WISDOM HAUSA WRITER’S
Rash Kardam
[7:35PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Hancin ta ya lakace yace Ameen amma kwanan mu gaba daya, haka suka zauna cikin farin ciki har dare yayi suka kwanta.
Da safe ammar ya sake fita nan ma ya barmata kayan karin kumalo ya fita, nan yayi ta yawon niman aiki da kyar ya samu wani shago zasuna debo kaya daga stored suna kaiwa cikin shago amma ba kullum ba sai randa za a saka kaya a shago ko sun dawo daga sari, haka ya dawo da murna yake sanarmata, nan ta tausaya masa tace Yaya na zaka iya yin dako kuwa kai ya daga mata yace eh kan wata, in dai zamu samu abunda zamuci Alhamdulilah.
Washe gari haka suka tashi kudin su ya kare sai naira hamsin shinkafa ya sayo ma auta ya zauna yasata a gaba taci, tace aa sai dai su ci tare fir yaki don ba zai ishesu dukansu ba, auta taki ci ganin haka yasa ya dau cokalin roba ya fara bata lbr abun dariya yana bata a baki tana ci har ta cinye , ta kalli kwanon tace kai yaya na gashi kasa na cinye kai ya girgiza mata alamar kar ta damu, haka sukayi ta hira har dare,
Futha ce ta fito sanye cikin shiga ta alfarma ta shiga motarta ta nufi makarantar da tafara zuwa, bayan sunyi lectures kenan tafito tana zaune, kiran sady ne ya shigo bayan sun gaisa ta tambayeta kwana biyu tace lfy nan suka taba hira ta hakuri gameda abunda babanta ya mata nan sukayi sallama ta dau ko hanyan gd tun daga nesa ta hango wata sabuwar mota honda ta hadu motar blue kalo daga gidan su Auta tafito wanda yanzu su Sady ne acikin gdn, sai da tazo kofar gidansu ta tsaya don ta karbi lab top dinta da tabada ya duba mata, bayan ta karba ta fito taga wan nan Honda tatsaya dai2 ita nan aka zuge glass wacce ta gani a motar bakara min mamki tayiba da ace itace a wannan motar, pinky ce yar kanini baban Auta wato yar Baba Isiyaka, hy tace mata sai a lokacin ta dawo daga duniyar tunani gaisawa sukayi ya kwana biyi tace lfylau ya school tace Alhamdulilah, sun dayi hira kafin sukayi sallama, futha ta tafi tana tsananin mamaki sosai da sosai pinky ce haka harda mota lalle sun samu duniya tabbas dawata a kasa dole ma tabi didigi haka taja motarta tashiga gida tan tunani kala2.
Can cikin dare wani hadari ya hadu ga iska daya taso sosai, Yaff yaff yaff ruwa da iska yasoma zuba, kan kace me sai ga ruwa ya barke baka dan ba,
nan Ammar suka farka kafin sunimi matsuguni rua ya soma dukan su bakadan ba duk inda zasu fake ankulle nan suka dun kule a gindin shiya ruwa nan dukansu Auta ta kan kame ammar tana yar kuka ga ruwa sai dukar su yakeyi wani tsawa aka sake sosai wanda yasa Auta kara rugume ammar har sai da yaji tsikar jikinsa ya tashi yaso ya ture ta don yanda yasoma feelings, ga wani murdawan da maranta keyi alamar period ga ruwa na dukan su gaka ruwan ya kare akansu tass barin sanyi auta takeyi ga maranta na murda mata gashi ba kayan canzawa haka suka tsuguna a tsugune har gari ya waye jikinsu har ya bushe auta kam mara ke ciwo gada2 ga zazzabi na neman mata mumunan kamu nan hawaye ya soma zuba don tabbas period dinta ne gashi kudinsu ya kare ga pant daya ke jikinta kayan da zata canza ma baba gashi kwananta 2 ba wanka sai yau da ruwa ya mata duka Yasalam!!! Allahuma ajirni fi musibati wa aklifli khairan minha, jikinta yayi zafi sai barin dari takeyi Ammar ko da ya taba jikinta nan take ya rikice ya shiga da muwa gashi kudinsu ya kare ga auta jikinta yayi zafin Innalilahi wa inna ilaihi raji’un yake furtawa a bakinsa.
®WISDOM HAUSA WRITER
Rash Kardam
[7:35PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Jikin auta yayi zafi sosai ga ciwon mara, ammar duk ya rude yarasa me ke masa dadi ga kudinsu ya kare gefen wani shagon daya ga ba a budewa yaje ya kwantarta lokacin gari yayi haske sosai ya cire yar rigansa na janfa ya luluba mata nan yace auta kiyi hakuri barin fita neman kudi ko zan samu sai in saya miki magani kai ta daga masa hannu sa ta riko cikin muryan marasa lfy tace Yaya na Allah ya ka fita sa’a ya amsa da amin, ya fita
Shagon dako yaje yayi sa’a an kawo kaya nan ya yasoma aikin kwasan kaya tun bakwai yagara sai karfe shadaya ya gama nan aka bashi kudin aiki 200 dake kayan ba masu nauyi bane shiyasa, hamdalla yayi yana shirin barin layin masu kayan zai wuce yaji wasu suna neman mai zubar da shara nan yayi aikin ya gyara musu gurin tass suka bashi 50 daya layin ma sun kitashi nan ya fara musu aiki aka soma kiran sallah ya bari da sauri ya ce zaije ya dawo yana fita chemist yaje yasayo maganin mura dana zazzabi yabi yasayo musu shinkafa auta harda tea irin na masu yawo suna hadawa yasa mata da murna ya kama hanya zuwa gunta.
Futha bayan ta huta washe gari tacr ma Sady tana so su hadu akwai abunda takeson sani, nan sady tace zasu acikin Kad poly haka ko akayi da yamma suka hadu bayan sun gaisa futha take bata lbr abunda ta gani Sady tace nima abun ya daure min kai don pinky bakara min busha take ba kuma Abba na nima yace wai ya sai min mota ba a shigo da ita bace ni kaina futha yanda suke bushasha da dukiyar su Auta abun har na razana ni kuma har yanzu sunki yarda ayi binciken akan wayanda sukayi kisan nan da kuma inda Auta take, futha tace kar kidamu sannu a hankali komai zai zama tarihi Allah ya toni asirin duk wannda keda hannu a wannan al’amarin Sady tace Ameen nan suka yi hira gameda karatu har sai magrib suka rabu.
Baba sani ganin Sady da futha suna neman dinkrwa yasa ya baza mata kan tsaro duk inda sady tayi ana biye da ita don kar futha ta gano sirrinsu don bai yarda da ita da mahaifinta ba suna masa shigan sauri akan al’amarin, su baba isiya yanzu abun nema ya samu hankalinsa kwance ke cin kudin da bana saba har in anzo neman taimako gunsa yana ikirarin sunsan wahalar dayayi yasamu dukiyar su asama kawai suka gansa da kudi, kutaya ni ji wai har yana cewa sun san wahalar dayayi, baba isiya har wani yar tumbi yasaka yayi fresh ko mai ya dai2 har ya manta da wani alhaji Al-hassan.
A bauchi kuwa Ammar da murnar sa ya nufo gun Zee Auta ya musu samuwa don shi ko ta kansa bayayi yafiso yaga ita taci kafin sai yaci, yazo tsallaka titi har ya kusa tsallakawa sai ga wani mai mashi ya yanko aguje ji kake kiiiii mai mashin ya shiga da Ammar da sam idonsa ya rufe baya ganin hanya.
Yan gurin nan suka dau salati suna tafa hannu wasu suka yanko da gudu suka zo ba da taimakon gaggawa Allah sarki kowa da irin jarabawar da Allah ke masa a rayuwa kamar yanda Ammar da Zee suka shiga haka wasu ke cikinta kowa da kalar nasa ya Allah ka jarrabe mu dai2 da karfin imanin.mu Ya Allah kabamu Abin da zamu iya Ameen Ya Allah.
®WISDOM HAUSA WRITERS
Rash Kardam
[7:35PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Kiiiii kake ji karar mashin ta tashi sama da ammar nan mutanen gurin duka dau salati, wasu da gudu sukayi gurin, abinci kam duk ya zube, nan mutane sukayi kansa cikin ikon Allah bai ji ciwo ba sai dai ya dan buge kafarsa gefen hanya aka maidashi mutane sai sannu suke masa Ammar na dawo hayya cinsa sai ya hango robar abinci ta fashe maganin kam bai san ida ya yarshi ba, nan take wasu zafafan hawaye suka soma gangaro masa a zuciyarsa yana gode ma Allah daya sa yana da sauran rai in da Allah yaso sai kafarsa ta cire ko hannu yana da kyau a kowani hali ka tsinci kanka to ka gode ma Allah sai ya kara maka, cikin ikon Allah mai mashin ne ma ya dan kurkurje nan ya ba ma ammar hakuri don yanzu fitowarsa bai da ko sisi ajikinsa Ammar yace ba komai haka ya mike ya na din gisawa ya sake zuwa chemist ya sayo paracetamol da da maganin mura na ishirin ya sayo ma auta shinkafa talatin ba ko ruwa nan ya laluba aljuhunsa ya ga biyar hamdala yayi ya sai mata pure water biyar da sauri yana din gishi ya nufi gunta.
yasamu duk ta dawo wani iri dagata yayi yana mata sannu abinci ya fara bata da kyar ta iya ci kafin tasha magani ya maida ta ya kwantar nan yaje yayi alwala yayi sallah bayan ya idar yayi nafila yana gaya ma Allah kukansa kafin ya dawo gurin auta ga yunwa tasoma damunsa sai da yaga bacci ya dan dauketa kafin ya sake komawa cikin kasuwa ya yi sharan yayi sa’ah mai shagon mutumin kirki ne ya basa dari buyu nan ya bashi sauran abinci ammar yayi godia yaci kafin ya sake suwa wani gu ya musu aiki nan ya.samo dari uku nufo hanya.
Tun daga nesa ya hango auta rike da cikinta tana juyi da sauri ya karasa gunta,nan yasoma mata sannu yariketa kuka tasoma masa duk ya rude ya tambayeta mai ke da munta tace cikinta ganin yanda take juyi yasa ya dauketa da sauri ya nufi titi nan rake aka zuna musu ido dake haka ya nufi chemist da ita nan mai chemist ya soma dubata aiko yace Malam period dinta ne zaizo nan ammar ya zare ido yaya zaiyi ba pant ba gun wanka mai chemist ya bata magani tun agun tasha ya dan kwantar ta akan benci sun dan dade don ciwon ya dan ragu sai rashin karfi ajiki nan ya cemasa kudin magani 200 haka ta bashi nan suka mike zasu tafi kenan yaga shini ya bata gun da ta zauna nan ta zare ido yau yaga ta kansa ya zaiyi kenan Yasalam Auta ko tsaban kunya kasa daga idonta tayi sai hawaye nan ta fara Allah ya isa masu baba sani duk sune ummul aba isin sata cikin wan nan hali.
®WISDOM HAUSA WRITERS
Rash Kardam
[7:38PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Ammar gaba daya ya rasa mai ma zaiyi ne sun dan dade agun mai chemist daya ga basu tafi ba ya lura da matsala dake ustaz ne yasha Sunnah ya koshi cikin kulawa yace malam lfy dai ko ammar ya dago idonsa da ya cika da kwalla ya ma rasa mai zai ce, mai chemist yace ya kamata ka kaita gd don tayi wanka ta huta ammar cikin muryan sa na rawa kamar zaiyi kuka yace mu baki ne a garin nan bamu da kowa cikin tausayawa yace ayya sai a lokacin ya lura da yanda jikin auta ya baci nan ya ce masu ammar zan muku taimako daya ga gd na banisa kazo muje gun matana ta taimaka mata da kaya ta gyara jikinta ammar yaji dadi yacd ba matsala nan ya riko hannun auta suka bi mutu min nan gd sa na bayan stadium plat ne ciki da falo sai stored sai kitchen nan ammar ya tsaya daga waje shikuma sukayi sallama suka shiga da auta nan wata mata baka mai dan kyan jiki gata da sakin fuska ta fito tana musu sannu dazuwa cikin harshen fullanci ya mata bayani nan naga fuskan Rahmat ya bayya na tausayi tace yar uwa shigo dake bayinta na falon ne nan ta hada mata ruwan wanka ta kaita bayin shiko mai chemist ya kowa waje gun ammar suka dan fara hira.
Rahmat ta ciro mata sabin pant guda 4 da Alway ko amfani da shi batayi ba ta dauko mata riga da siket daya da dogon riga dake da ka dan zata fi auta ki ba nan ta samata a wata yar jakan biki mai zip da hijab daya da sabulun wanka sinki da na wanki biyu nan ta saka mata riga da siket na eglish wears wanda tasa da hijab mai hannu blue yadin plan tuyobo bayan auta ta gama wanka nan ta bata pant tasa ta bata mai da powder tasha da lip stick kai kar kuso kuga auta nan ta yi kyau abunka da farar mace ga kyau azuciyar rahmat tana yaba kyau irin na auta abinci tabata nan taci sosai ta bata zobo yasha hadi kafin ta dauko jakan ta bata lokacin har ta dauraye mata kayanta sunsha ta nuke tasa mata a hakar tace ki duba waje kice musu kin gama nan auta ta leka tun da tafito ammar ke kallonta sai murmushi yakeyi ga idonsa ya ciko da kwalla rabonsa da yaga auta fess haka tun suna gun su inna laure a kauye yau har yar kyau tayi, auta tazo da sauri tasa hannusa ta share masa kwalla tace yaya na kabar kuka nima zaka sani kuka murmushi yayi yace babyn dad yau kinyi kyau sosai tace ta gode duk abunda sukeyi mai chemist na ganinsu duk sun bashi tausayi nan ta sai dama su sakon rahmat mai chemist yashiga gd ya fito masu abinci sai da su kaci kafin Ammar ya masa godiya auta tafito suka kara gaba. Rayuwa kenan
* * * * * *
Sady abun duniya duk ya isheta yanzu bata isa tafita ba babanta zai dameta gashi yace matukar ta hadu da putha sai ya yanka ta kuma motar da zai bata ma ya fasa duk ita bai da meta ba sai sauyawan babanta anya yana da gsky yake haka yazama dole insan sirrin boye tana cikin wan nan tunanin pinky tazo cikin masu matsatsun kaya da kyar ta ke motsi cab su pinky an samu duniya yanda akeso rawan kai ya karu bare ga mota a hanu….lol… Hira sosai sukeyi anan sady take lbr ta ma pinky sauyin iyayensu pinky kafada tada ga alamar ko in kula cikin isa tace ni ba damuwata bane tunda zanci mai kyau insha mai kyau bani da matsala ga motar da zan shiga ko ina ba sa’ar dazata min raini kin ga ni ba damuwata bace kawai ke ma ki share kizo ayi harka dake sis sady tace ni kyale kyale baya gabana gasky nakeso tafito kuma zanyi iya kokarina pinky tace ae saikiyi ta kai nan tafice tashiga motar ta tabar gdn.
Almarin futha kuwa jaratu tasa a gaba don ta cimma burinta shiyasa ita ko saurayi bata kulawa karatu takeyi ga yawan adu’a Allah ya bayya na Auta ya karesu a duk halin da suke.
Baba sani ko yanzu an waye daga zuwa wan na hotel din sai gdn wacce bazauran shida baba isiyaka holrwar su suke acewarsu Allah ya basu kudi dole suyi abunda ransu keso, Allah ta kyauta ya Allah kar kabamu kudin da baza mu kasheshi ta hanyar halal ba ameen.
* * * * *
Auta dun yitafiya kadan don su koma inda suke zaune bayan sun isa gun ammar yace zai sake komawa kasuwa ko zai sami aiki nan auta ta bata rai tace ka huta ai tau mun samu abunda zamuci kuma gobe ba zamu rasa ba don duk bakin da Allah ya tsaga ba zai hana shi abinci ba nan sukayita hirasu gwanin burgewa daga gani yau suna farinciki ammar yace to kimin afuwa nima naje cikin kasuwa a kwai bayan gidan wanka da akeyi na kudi nima in samu nayi wanka auta tace sai ka dawo Allah ya kare nan ya mike yaje ya biya naira 20 yayi wanka ya fito ya dawo gun autarsa suka cigaba da hiransu.
®WISDOM HAUSA WRITERS
0 comments:
Post a Comment