Tana fitowa daga d'akin daidai shigowar haj. Sailuba, idanunta k'yar abakin k'ofar Ammey dan sam bata son had'uwa da kowa wannan shine sa ar aikin ta na yau tana ganin Maryam da bata kula daga inda ta fito ba ranta yai masifar b'aci babu makawa wannan la'a nanniyar yarinyar ta b'ata mata shiri.
Tsawa ta buga mata tace "ke dan ubanki daga ina kike bana hanaki mu a'mala da wadannan matsiyatan ba?"
Da kallon mamaki Maryam ta bi mama wadda tun kafin ta kai karshen maganar ta ta gano kuskurenta tayi saurin fuskewa dan kar ta gano ta, amma duk da haka sai da Maryam ta hango tsantsar tashin hankali atareda maman tata.
"Lafiyan ki kalau mama?"
Kallonta mama ta d'an yi cikin alamun rashin gaskiya kafin ta wuce b'angaren ta cikin tsantsar tashin hankali.
Tana shiga bata bi ta maganar sallar magriba da ake ta kwad'awa a masallaci ba ta zari waya jikinta har rawa yake ta dannawa haj. Zakiyya wacce ita shigarta nata gidan kenan kira da mugun mamaki ta d'aga kiran tana cewa.
" Ya akayine k'awata ko zama banyi ba sai ga kiranki?"
" Na mutu zakiyya, shikenan kuma nawa ya K'are na shiga uku zakiyya da wannan la'ananniyar yarinyar na fara karo wacce boka yace har gwanda naga kowa dana fara ganinta?"
Ta fad'a cikin rushewa da wani fitinannen kuka cikin tashin hankali.
Ita kanta wani irin fad'uwar gaba ne ya rufeto mata agigice tace
"Ke kuwa Sailuba wanne gangancinne yasa kika bari kuka had'u?"
"Cikin kuka tace wallahi nima bansan zamu had'u da itaba kawai ina shigowa mukayi kicib'us"
"Allah yasa bakice zakiyi mata fad'a ba dan gudun kar kija mana matsalar kuma"
"Nayi, sai dai kafin na dire na gano kuskurena nayi saurin fuskewa"
Nan dai suka fara tsara yadda zasu sabunta shirin su tunda wannan ya ruguje.
Ganin yadda maman ta d'aga hankalinta har tayi hanyar d'akin sai kuma ta fasa aranta tace ai kina da kud'i zaki sha kan matsalar, ta juya ta shige d'akin ta batare da wani damuwa ba ta shiga wanka a gurguje tayi wanka ta fito ta kabbara salla bayan ta idar ta d'an yi kwalliya sama sama ta fice, duk suna wajen cin abinci kamshinta ne ya sanar dasu zuwanta, duk suka bita da kallo babu MD awajen duk sai taji babu dad'i dan tun d'azu take ta faman juya labarin da Ammey ta bata nasa tana da tausayi duk da kasancewar ba wai yasha wani wuya na azo agani ba amma rashin mahaifiya ba d'an k'aramin gib'i bane ga rayuwar yaro.
Tana shirin zama Baffa ya dakatar da ita yace taje ta dubo yayanta ko lafiya dan tunda ya shigo bai ji motsin saba, jitai gabanta ya wani buga da k'arfi take abinda ya faru agidan m Bash ya dawo mata sai dai bata da damar yiwa Baffa musu hakan yasa ta fasa zaman ta juya kamar kazar da kwai ya fashe wa aciki tayi waje duk suka bita da kallo yayin da Mama ta saki wani arnen tsaki tsanar yarinyar yana k'ara tasiri aranta, duk suka bita da kallo, basu kawo komai aransu ba tunda sunsan yadda ta tsani MD.
Tana tunkaran wajen bugun zuciyar ta yana k'ara yawaita sai da tashafe kusan 5 mint kafin tayi k'arfin halin kama mabud'in k'ofar ta tura a hankali kamar mai jin tsoron wani abu,
Tunda ya dawo salla yake zaune saman doguwar kujera ya jingina bayansa jikin makarin kujeran idanunsa a lumshe bai tantan ce halin dayake ciki ba abinda kawai zai iya ganewa itace ta cika masa zuciya duk inda zai motsa ta tokaresa.
Jin motsin bud'e k'ofar yasa ya maida hankalin sa wajen k'ofar shima bugun zuciyar sa yana kara yawaita bugu ya wani irin kafe k'ofar yay da kallo, a hankali ta shigo bakinta d'auke da siririyar sallama da k'yar ya iya dai daita kansa ya amsa yana dad'a binta da kallo ta d'an kalleshi suka had'a ido bata san sanda ta galla masa harara ba sai ya saki murmushi ya sani sarai takura ta yayi gashi ita kuma babu hak'uri shi yasa.
Bata san tasowar saba sai tsintar sa tayi agabanta ya dafa kafad'anta "babyna me kike sone kika ja kika tsaya anan ki shigo mana?"
Kallo ta bisa dashi mai kama da harara kafin tace "ni ba babyn ka bace, Baffa ke kiranka yace tunda ya shigo baiji motsin ka ba lafiya kuwa?"
"Inafa lafiya an shake min wuya da mugun k'arfi na kasa koda hadiyar yawu" binshi tayi da kallo mai kama da na tausayi dan sam bata gane me yake nufi ba tace "kasha magani me yake damun ka bross?
"Ke ce, ya bata amsa cikin bazata kece damuwa ta, kece tunani na, kece jina, gani na, walwala na, kuma jin dad'i na, Maryam kece komai na" yafad'a cikin muryan daya mugun karyewa ta daga kai tana kallonsa duk yayi wani iri ga damuwa nan kwance acikin idanunshi
" Kazo muje"
"Kije zanzo yanzu"
"Ni dai Baffa yace k'afa na k'afar ka"
"To jira nayi wanka"
Daga haka bai k'ara cewa komai ba ya haye saman sa da gudu.
Cikin 20 mints ya sauka sanye cikin blue jeans da riga ruwan toka kayan sun mugun amsar sa kunsan farin mutum kuma mai kyau duk shigan da yay amsar sa yake.
Tana can yawon kalle kallen ta a falon taji ya rik'o hannunta binshi tai da kallo yadda yayi mata kyau ga wani fitinannen k'amshi dayake yi ma mugun dad'i, har sukaje bakin falon babu wanda yace da d'an uwansa komai sai itace ma da suka zo bakin falon ta warce hannunta daga cikin nasa ta wuce ciki abinta murmushi ya d'an saki kafin ya rufa mata baya
Duk su Baffa suka bisu da kallo yayin da zuciyar haj. Sailuba kamar zaiyi bindiga tsabar fitina da tsanar ganin Maryam daya Kuma mamaye ta Baffa yace "maman malam daga aike kuma sai najiki shiru?"
Rasa me zata cewa Baffa tayi sai ta d'ago ta dubeshi shima ita yake kallo, kafin ta lalubo abin fad'a yay saurin cewa "sanda taje ina wanka"
"To ku gama cin abincin akwai maganar da zamuyi daku duka"
"Nima Baffa akwai abinda nake son fad'a maka tun kafin kaje wajen Inna kuma naso binka sai bansan katafi ba"
Dafa kanta yay yace kar ki damu wannan zuwan ma sai da Inna tai fad'a sosai na rashin ganinki, laifin mamanki ne da tafiya ya tashi sai ta kawo uzurin da dole ake fasa tafiyan dake shiyasa Nassar kawai Inna tafi sani.
Yay maganar yana kallon haj. Sailuba da tayi wani kicin kicin da rai zuciyar ta nayi mata mugun sak'a.
Shima daga haka ya wuce falonsa Ammey ta tashi ta rufa masa baya dake yau ita ce da girki.
Suna barin wajen ta juyo da niyyar zuba abincin dan har ta k'agu taji neman da Baffa yake mata sai karaf idanun ta suka sauka cikin nasa ya wani yi tagumi ya kafe ta da ido, a ranta tace gaskiya wannan mutumin da bansan shi ba babu abinda da zai hana nace maye ne yadda yake da jarababbe kallon nan.
Azahiri Kuma abincin da zata ci ta d'iba a flat ta mik'e zata bar masa wajen, gane hakan da yayi ne yasa yayi saurin dafe hannunta yana binta da wani marai raitaccen kallo "dan Allah kar ki tafi ki barni"
Ya fad'a kamar zai mata kuka, binshi tayi da kallon mamaki, yayin da shi kuma ya k'ara wani marai raice mata sai ta samu kanta da kasa yi masa musu ta koma ta zauna, shima tsulum ya taso daga inda yake ya dawo kusa da ita "lafiya?"
Tace dashi tana kallon yadda yake wani faman shafa cikin sa d'an marairaice mata yayi yace"yunwa nakeji nima"
Abincin da ta zuba zata ci ta tura masa ta d'auki wani flat d'in yay saurin dafe hannunta yana girgiza mata kai ta d'an kafe shi da ido dan neman k'arin bayani "ki bani mana" ya fad'a yana kallonta ta d'an had'e rai shi kuma ya kafa mata naci sai da ta bashi haka kuma shima yabata suka ci suka k'oshi.
Da alama nacin MD ma kawai zai sa yasamu yadda yake so lol🤣🤣🤣🤣🤣
Maman Islam ce
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Godiya ta musamman gareku masoyan gaskiya hak'ik'a ina jin dad'in yanda kuke min ina ina sonku domin Allah musamman ma ku d'in nan
MAMAN Jani
Ammeyn Sadik
Antyn muhseen
Ya Rahman
Mare
Jidda
MAMAN Abul
Mom Irchad
Ummey Idris yakub
MAMAN sayyadi
Shamsan
Maman sultan
Umm nawaad
MAMAN Raees
Safiya Sopy
Aisha munir
MAMAN jabir
Xeeyyah
Rashida Muhammad
Afra
Fauzi
Ummukurthum
Aishatu k sani
Zainab autar mm
Jannat Aliyu
Barira Aminu
Hykarianeg 17
Ameenatu
Khadija Muhammad
Hafsat Bala kawu
Maman Arif
Ikilimatu D Baraya
Ummu Abul
Mr maimunatu
Aisha ibarahim ummi
Zainab Muhammad sambo
Juwairiyya Lawal
Maman twins
Mama
Khadija Isa Dari
Duk wanda bai ji sunan sa ba yamin afuwan mutara a text fage ina k'aunar ku nima son so fisabilillahi.
Page 33
Tusio tasa ta goge bakinta kafin ta mik'e " ina zaki?"
Kallon yadda ya wani lafe jikin kujeran dining d'in tayi kafin ta wani tab'a baki tace "ina kaji Baffa yace yana son ganinmu?"
Kai ya d'an dafa alamun ya manta sai kuma ya tashi yace "muje" batareda tace komai ba ta mik'e ta wuce yabi bayanta suka nufi part d'in Baffa.
Tun kafin su shiga suke jiyo b'ab'atun haj. Sailuba sai faman bala i take zubawa Baffa wani mugun tsaki MD ya saki har ga Allah ya mugun tsanar matar nan haka nan, abinda ya dad'a d'aure musu kai shine yadda suka shiga suka tarar tana zuba ruwan tujara shi kuma Baffa yana lallab'a ta yana bata hak'uri, da dai yaga abin yak'i k'arewa ne ya dubi Ammey yace.
"Aminatu dan Allah na rok'eki ke ki hak'ura taje tunda ita ban isa da ita ba baza tayi min alfarma koda sau d'aya na sauke hak'k'in ki ba"
Cikin wani irin yanayin da bazaka tab'a iya fassara shiba Ammey tace "ai dama Baffa ni ba matar gida bace 'yar zaman jiran gida bace da kula da gida ko ba haka ba?
Gaskiya Baffa wannan karon bazan yarda ba nima duk abinda zai faru sai dai ya faru amma nataji wallahi haba dan masifa da bala i shekara da shekaru abu yak'i k'arewa nima wannan karon bazan hak'ura ba Baffa sai dai duk abinda zai faru ya faru.
Nan fa Ammey itama ta bud'e wuta ta rik'a zubar da maganganu masu d'aci kunsan ance mai hak'uri bai iya fushi ba to haka ne yafaru ga haj. Amina yau duk irin yadda Baffa yaso rarrashin ta botsare masa tayi.
Dai dai shigowar su MD da suka gama sauraran komai MD ya kafe Baffa da ido kafin yace "Baffa mai yake faruwa ne nakejin abinda ban tab'a jiba game daku?" ya fad'a yana kallon Ammey cikin yanayin da bai tab'a ganinta aciki ba.
"Kamar yadda aka saba ne Muhammad yauma nayi magana ne akan kujeran hajji danake fitarwa duk shekara, Sailuba bata tab'a bari na bawa Amina tabawa wani nata ba sai sau d'aya kuma ni bansan me take da kujeru har guda goma ba tunda ko ta b'angaren mu nike biyama dangi, to itama mai hak'urin yau ta botsare min tace sam bata amince ba itama na rasa yadda zanyi yanzun"
"Kawai kabawa wanda kake ganin yafi cancanta"
"Baza abawa wanda yafi cancanta d'in ba wallahi ko zata mutu wannan kujeru nawa ne dan haka banga wanda ya isa hanani wannan kujeru ba ehe, idan kuma tak'ama ce naga ubanka ma acan k'auye raba kujerun nan yake kamar babu gobe"
"Ni bana harka da jahilai marasa ilimi dan haka bani da lokacin da k'ik'ancin ki*
"Uwar ka ta kabari itace dak'ik'iya baniba dan is...........kafin ta k'arasa taji wani irin fitinannen zafi ya karad'e fuskar ta ta d'ago a firgice dan ganin wanda yayi mata wannan d'anyen aikin sai da ta wuntsula daga kan kujeran ta ganin Baffa ya kafeta da kallo yana huci, yayin da MD ya mai da kansa k'asa cikin tsantsar b'acin rai da wani irin tsanar haj. Sailuba.
Da wani irin tashin hankali ta bar wajen domin wannan ne karon farko da hakan ya tab'a faruwa iya tarihin rayuwar su dan haka abinda yayi matan yai masifar gigitaya ta sani hakan yana nufin aikin ta yana rawa kenan ai kuwa ya zama dole ta sabunta shiri
Tana barin wajen Baffa ya dubi MD yace "Muhammad na fad'a maka ka fita hanyar Sailuba matar nan jahila ce amma bakaji" da mamaki MD yake duban Baffa to shi mai yace dan kawai yace Baffan yayi abinda yake ganin daidai shine ya shiga sangarta?
Da wani irin fushi MD ya bar wajen yayin da duk suka bishi da kallo sai Maryam ma ta rufa masa baya dan sam bataji dad'in abinda maman nata tayiba.
Ammey ma tashi tayi yayin da Baffa itama ya bita da kallo haka dai duk suka watse kowa zuciya babu dad'i Nassar ne kawai ya zauna ya ci ya koshi abimsa ya kama gabansa ya tafi gidansu boy abokansa.
Sanda Maryam ta isa part d'in MD har ya gark'ame k'ofar da key babu irin bugan da batayi ba yai banza da ita kamar baikita ba.
Haj. Sailuba kuwa tana shiga d'aki a gigice ta nemi wayar ta ta kira haj. Zakiyya kamar wata k'aramar yarinya haka take kuka wurjanjan cikin tsantsar tashin hankali ta kora mata duk abinda yafaru.
Sosai ta rarrasheta tace tunda abin haka ne kawai ta shirya cikin satin nan su wuce India can ne za ayi musu aiki mai kyau sun jima suna tattanawa kafin suyi sallama, sai lokacin ta d'an samu sassauci
Maryam kuwa d'akin ta ta koma cikin damuwa tasani cewa Mama bata kyautaba ko kad'an amma Kuma ita meye laifin ta da zai wani rufe mata k'ofa.
Ganin zaman bazai mata ba kawai ta mik'e ta saka mayafinta da niyyar taje wajen Halima ko zata d'an rage damuwa, daidai bakin get suka had'u da Baffa ya hanata fita dole ta dawo gida cikin k'unci.
MD kuwa tunda da yake babu Wanda ya tab'a zagar masa uwa ido da ido sai yau hakan ya masifar k'ona shi da k'yar yasamu ya rarrashi kanshi ya baro falon shi yasa ya kulle kanshi domin a halin dayake ciki baya buk'atar kusanci ga kowa atare dashi.
Ammey kuwa cikin fushi ta koma d'akin ta ranta a masifar b'ace tasha alwashin bazata k'ara yarda Sailuba ta rik'a juya ta ba tunda babu adalci a lamarin itama ya zama dole ta zage ta kwatar wa kanta yanci.
Haka da ranan mutanen suka kwana kowa zuciya babu dad'i da safe da zasu wuce islamiyya hankalinta yana kan k'ofar sa bata taba alamun ya bud'e k'ofar ba, sai ta tab'e baki a k'ok'arin ta nasan yakice tunanin shi aranta tunda shima fushi yake da kowa na gidan.
Sai dai duk irin yadda taso kore tunaninasa aranta hakan yak'i samu sosai tayi sanyi dan ko k'awayen ta na islamiyya sai da suka gane tana da matsala, sanda suke dawowa daga islamiyya shi kuma ya fito daga d'akin dake lokacin an yi kiran Azhar ne sai da ta d'an razana ganin har ya d'an fad'a daga jiya zuwa yau kacal bata kulashi ba ta d'auke kanta, Nassar ne kawai ya gaida shi, ya bita da kallo har tashiga ciki kafin ya juya ya wuce masallaci.
Koda ya dawo shima cikin gidan ya dawo lokacin har sunyi zaman cin abinci banda haj. Sailuba datake d'akin ta tun juya shima wajen ya tunkaro duk suka bishi da kallo har Baffa wanda yay mamakin ganin shi hakan Ammey tafi kowa shiga damuwar ganinsa a hakan.
K'arasawa yayi ya gaida su kafin shima su Maryam suka gaida shi Ammey ta zubawa kowa nasa abincin amma MD da kanta ta fara bashi dan ta riga tasan halinshi muddun yana cikin damuwa baya iya cin abincin sai dai yayi ta fama da tunani tana cikin bashi ya tsinci muryanta tana fad'in.
"Muhammad yakamata ka gane halin wannan matar ina rok'on ka daga yau komai zai faru kada ka k'ara cewa komai ka barta komai lokaci ne dan haka wata rana sai labari" sosai taci gaba da da tausar shi har ya kammala, itama Maryam ta tubure sai da ta bata itama kafin su bar wajen ta bisu da kallo.
Hannunta da Baffa ya kamo ne yasa ta juyo babu wannan walwalan dayaga tana yima yaranta yanzu, ya d'an murmusa yace "haba maratussaliha dan Allah ki saki ranki tun jiya ake fushi dani na takura da yawa" ya fad'a yana murza hannunta dake cikin nashi.
"Ai Baffa na lura baka Sona ko dan ni ba yar uwarka bace shiyasa kake nuna babanci muraran atsakanin mu"
"Dan Allah ki daina wannan batun Amina ta wallahi nima wani lokacin karkiga yadda abin yake damuna kawai dai tashin hankali ne bana so yasa kikaga ina biye mata"
Amma Baffa shekara ashirin sau d'aya ka tab'a bani kujeran nan ban tab'a cewa dan me ba yanzun ma nagane abin ba na K'are nane dan haka wallahi akan wannan komai zai iya faruwa"
"Dole na baki Amina tunda baki tab'a yi min haka ba sai yau dan haka komai zai faru kece da wannan kujeru na bana" nan dai yaci gaba da tausarta har yasamu ta d'an sakko sukaci abincin tare.
Kai tsaye suna fitowa d'akinta ta dosa dan yau tana buk'atar zuwa gidan su Maryam tana shiga suma suna shigowa yi tayi kamar bata gansuba sai da ya k'araso kusa da ita ya d'an dafa kafad'anta ta juyo ta harareshi.
Murmushi ya d'an saki ya sumbaci goshin ta bai ce komai ya juya ya fice daga d'akin ta raka shi da ido kafin ta juya tacigaba da shirinta.
Taku ce
MAMAN ISLAM
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Page 34
Cikin atamfa riga da sket kamar ajikinta aka dinka rigar tsabar yadda tayi mata d'as a jikinta, bata wani yi kwalliya mai yawa ba duk kuwa da yadda take da son kwalliyar, mayafin da ya dace da kayan ta dauka ta saka ta saka takalmi mai mugun tsini Allah yayi mata son takalma masu tsini ta fito d'as abinta.
Dukansu juyowa sukayi suka kafeta da ido ba k'aramin kyau tayi ba,kasa daurewa MD yayi sai da ya taso ya d'an matso kusa da ita yace,
"Bakiyi kyau ba" dan hararan sa tayi tace " ai daman badan kai nayi kwalliya na ba bare ka kushe" murmushi yayi tare da mata gwalo domin yasan taji haushi ai kuwa ta k'ufula ta wani had'e rai, ta juya ta wuce d'akin Ammey karab sai a idon mama da ta fito zata fita jitai wani irin fitinannen tashin hankali yakawo mata farmaki da k'arfi tace "ke gidan uwar wa zakije ne" ta fad'a tana kafe Maryam da wani irin kallo.
Ba Maryam ba hatta MD da Nassar sai da suka zabura suka zuba mata ido, ita ko Maryam babu wani shakka ko tsoro tace "haba Mama wallahi har kin bani tsoro irin wannan ihun haka kamar aradu?"
Wani irin tuk'uk'i ne ya tokare haj. Sailuba ta kafe Maryam da wani shegen kallo zuciyar ta yana suya yaushe Maryam ta sami damar fad'a mata magana haka lallai in batayi wasa ba wata rana sai Maryam ta zageta anata haukan tunanin kenan.
Amma azahir cewa tayi "ni nake ihun bab? wai ma tukun me zakiyo ad'akin matar nan bana hanaki mu a'mala dasuba?"
"Hummm mama kenan ai duk randa babu ke dole itace uwata, ko baki tab'a tunanin hakan bane? kuma kadafa ki manta mama ba a raba hanta da jini mun riga mun had'u babu yadda zakiyi tunda ta haifa kin haifa dole ne itama ta sarara agidanna dan Allah mama ki daina irin wannan abun bashi da amfani ko kad'an haba"
Fashewa kawai haj. Sailuba tayi da kuka saboda tsabar tashin hankali da bak'in ciki kasa yi mata magana tayi har ta shige d'akin Ammey tana kallon ta.
MD kuwa wani irin annushuwane ya kamashi sanda Maryam ke fad'awa haj. Sailuba magana wani arnen murmushi kawai yake saki, yana ganin Maryam ta shige d'akin Ammey ya k'arasa kusa da haj. Sailuba yace "hajajju makkatu me kike tunanin zai faru duk ranar da wannan yarinyar tagane cewa ke ba uwarta bace uwar rik'o ce?
Ya zakiji lokacin da tasan cewa mahaifiyar ta kike sawa tanawa cin mutunci da wulak'anci
Me zai faru idan tasan cewa ba dan Allah kike rok'on taba kina rik'on tane saboda wani banzan dalili naki mara amfani?
Hhhhhhhhhhhh kad'an kika gani Sailuba domin Allah baya bacci"
Babu kunya haj. Sailuba ta kuma fashewa da kuka tana kallon MD kafin tace "hummmm Muhammad kenan na maka alk'awarin bazan bar hakan yafaruba sannan kuma ina Mai farin cikin sanar dakai cewa komai ya kusa zuwa k'arshe rayuwar Maryam zaiyi wulakantar da babu wani rayuwa da zata kai tata lalacewa zata bi maza zata yi shaye shaye zata yi sata zata zama abin kwatance da misali na miyagu da munanan halayya"
Sosai gabansa ya fad'i da jin furucin ta domin yasan zata aikata fiye da hakama jiyai hankalinsa yai masifar tashi ya dubeta da tsantsar b'acin rai yace "Allah ya fiki yafi waninki Sailuba kuma duk abinda kike tak'ama dashi insha Allah hakan ki bazai cimma ruwaba"
Wata shegiyar dariya ta saki tace "zaka gani zaka kuma tabbatar muzuba nidakai shege ka fasa" daga haka tayi waje hankali a tashe.
Sosai maganganun ta suka tsaye masa rai sai dai kamar yadda yake tsaye wajen yiwa Maryam Adda a ya zama dole ya k'ara zage damtse.
Maryam kuwa tana shiga d'akin Ammey ta rufeta da fad'a akan maganganun da taji tana sakarwa haj. Sailuba tace mata koba komai matsayin uwa take awajen ta dan haka ta rik'a sanin irin maganan da zata fad'a Mata.
"Nifa Ammey indai akan kune babu abinda zaki fad'a min na fahimta matar da bata da lokacina sai na gantali kullum tana tafe a hanya ita ba kasuwanci ba ba komaiba, ai wallahi duk laifin Baffa ne da yasake mata haka dayawa shiyasa take iskancin ta son Rai"
"Ungo nan Ammey ta yiwa Maryam tace "idan har da gaske kina ganin mutunci na kamar yadda kika fad'a to kada ki sake kinji ko?"
"Naji Ammey, ina Baffa shi nazo nema"
"Lafiya kike neman Baffa?"
Bata b'oyewa Ammeyn komai ba ta fad'a mata tana son bawa baban k'awarta jarine ya fara sana a, sosai hakan yayiwa Ammeyn dad'i arai taji dad'i ya kasance yarta tana da zuciyar tausayi dan haka Ammeyn ce da kanta ta bawa Maryam dubu d'ari tace "gashi idan Kuma bai isaba kimin magana sai na k'ara miki?"
Rungumeta maryam tayi tace "na gode Sosai Ammey na Allah yaja da rai ta sumbaci Ammeyn tayi waje da sauri tana fad'in saina dawo"
Sosai Ammey ke jin dad'in yadda yarinyar ta soma sakewa da ita ta rage wannan d'an banzan yawon dayake sanyata fargaba da damuwa musamman idan haj. Sailuba ta dawo taga bata nan ko zata kwana basata tuhumeta taji inda taje ba.
Tana fita suka gabza wani uban karo da MD ai kuwa taji zafi sosai shima haka duk suka dafe wajen suna kallon juna kafin Maryam ta galla masa harara ta wuce tana sosa goshinta.
Da sauri yasha gabanta ya tsaya yana d'an diddira k'afa irin na shagwab'a yace"ni Allah Allah Allah sai ki bigeni kuma ki wuce babu hak'uri ni sai na rama" yadda yayi maganar dole abin yabata dariya batasan sanda ta saki murmushi ba tace "sorry"
Daga haka ta wuce kuma shan gabanta yayi yace "ina kuma zaki?"
"Gidan su Maryam ta bashi amsa dan har ga Allah sauri take ta tsai da baban Maryam yau baifita nema ba dan haka yakamata taje akan kari
"Wanda kike siyayyar nan awajensa?"
Ta tsinci muryarsa tana shirin fita "Eh shi"
Ta bashi amsa tana ficewa da sauri ya bita ya rik'o hannunta yana kallon ta tace "dan Allah yaya sauri nake sai batamin lokaci kake"
"Muje mana naganshi idan ya cancanta da amanar da kika bashi saiya cigaba da kula da su idan Kuma ba haka ba sai na amso ko?"
Sanin cewa sunyi maganar da Ammey yasa bata musa masa ba suka jera suka shiga motar yaja suka bar gidan.
Maman Islam ce
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Page 35
Saida tasa kashi suka biya wani spermaket ta d'an musu siyayya, dan Allah yasani hakanan Allah yasaka mata tausayin iyayen Maryam, saboda yak'i nin su da kamewar su hakanan sun iya babun su, dan malam Abdullah mutum ne jajir tacce tsayayye, akan iyakansa bai yarda da zubar da daraja da kimar gidansa ba, haka kuma baya daukar raini ko kad'an dan haka hatta iyalinsa suna shakkar sa saboda sam bai yarda da wulakanta kai ko zubda mutunci ba.
Yadda suke shiga cikin lungunan unguwar yasha mamakin yadda Maryam tasan wajen dan koshi dayake namiji bai tab'a yowa ta area dinba sosai ya rink'a binta da kallo yana mamakin ta.
Sai yanzu yake gane asalin halinta mai kyau ne irin na mahaifiyar ta wancen halin na aro ne wanda aka d'ora ta akai bisa wani dalilin mara tushe da makama.
Ita duk wannan kallon dayake binta dashi sam bata kulaba dan hankalin ta yana kan wayar ta suna chat da Halima sai yanzun ta d'ago dan taga ko sunkai inda ta kwantato masan ai batasan sanda tasaki kara ba ta maida hankalin ta kanshi ganin suna shirin taka wani k'aton dutse, shima da sauri ya taka burkin da sai daya janyo hankalin wasu daga cikin masu wucewa dake cikin unguwa be.
Harara ta galla masa kamar idanunta zasu fad'o tace "to kasheni ka huta tunda ka gaji da ganin rayuwata"
Murmushi ya d'an saki kafin ya d'an shafi fuskar ta yace "ina son ki princess dan Allah ki soni my happiness" hararan ta kuma masa kafin ta d'auke kanta yasa hannu ya kuma juyo da fuskar nata saitin sa ya kafeta da ido,
."dan Allah ki kalle ni nasan zaki yadda da abinda nake fad'a miki har zuciyana ne" bata musa masan ba ta d'an kalleshi na kamar 1 mint take taji ta fara d'an tsuma tsuma tasoma k'ok'arin kwace fuskar ta amma ya hanata damar hakan da sauri ta runtse idonta dan bazata juri kallon wannan fitinannun idanun nasa ba.
Murya na rawa tace ni kaina ya k'age ka sakar min fuskana, kuma ka daina yimin wannan kallon mayun" murmushi ya d'an saki kafin yace "indai akanki ne baby ki kirani lasan ma ba maye ba da da yadda zanyi na tsaga jikina na sakaki da tuni na jima da yin hakan na huta' dan Allah baby karki gujeni, idan kika gujemin hakan yana nufin abubuwa da yawa ciki harda rayuwana"
Yanayin da yayi maganar yasa dole ta kara bud'e idanunta akanshi yadda taga idanunsa sun koma ba k'aramin tsoratata abin yayi ba sunyi wani irin mugun ja ga wani kyalli kyalli alamun ruwan hawaye ne suka kwanta masa aciki, wani irin tausayin sa ne ya kamata tace
"Zaka iya aurata koda ace bana sonka?
Sosai maganar ta ya dakeshi, zaka iya aurata koda ace bana sonka?
ya sake maimata tambayar a zuciyar sa kenan akwai wanda take so Kennan tunda bata son shi?
Wani irin ajiyar zuciya ya sauke kafin yace
"Baby wa kike so?
"Babu"
Ta bashi amsa atakaice sannan ta d'ora da fad'in ba kaine kakori muhseen ba yaron dayake masifar Sona kamar zaiyi hauka tundaga ranan yake masifar tsorona bama kaiba ko a hanya ya ganni wallahi canja hanya yake"
Sosai maganar ta ya masa zafi a zuciya amma sai ya daure tunda shine mai nema dole ya sauke duk wani zafin ransa gefe ya nemi masalaha
"Kina son muhseen d'in?
Ta tambaye ta cikin tsantsar zafin rai dana zuciya.
"Ni babu wanda na tab'a jin ina so arayuwata shima muhseen d'in saboda nacinsa da rashin zuciyar sa yasa na tausaya masa na fara kulashi" baisan sanda ya wani fisgeta ta fad'a jikinsa ba ya wani k'ank'ame ta atare suka sauke wata irin ajiyar zuciya kafin yasoma magana cikin sanyin da shi kansa baisan zai riskeshi a wannan lokacin ba yace
"Na amince baby zan aureki koda ace bakya sona nasan dole wata rana zanyi nasara zan mallake ki KE DA ZUCIYAR KI"
"Ya jima yana zubar mata da sak'onnin da suka cunkushe masa zuciya suka hanashi sukuni, bai tab'a sanin da akwai rayuwa irin wannan ba rayiwar da zaka kasa katab'us ka kasa sukuni ba sai da ya had'u da jarrabar SO wanda ya hanashi sakat yake sanyashi kasa baci cikin dare ya kasa runtsawa tsawon dare ya zubda hawaye ba adadi duk asanadin SO"
Tun bata fahimtar maganganun sa har ta fara fahimta sanadin da jikinta yayi sanyi bata san da cewa akwai ranan da MD zai iya kallon idanunta ya furta mata tsadaddun kalamai irin wannan ba musaman idan tayi tunanin yadda suke da shi.
"Bross muje na tsaida bawan Allah yanata jira" tayi maganar cikin sanyin jiki dan kalaman sa sun mugun kashe mata jiki sai da ya sumbaci goshin ta da idanunta da suka fi komai d'aukan hankalin sa kafin ya saketa ya tada motar suka k'arasa gidan su Maryam d'in.
A mota ya tsaya ta shiga kamar yadda ta zata Abban yana nan yana jiranta kamar yadda ta nema Umma ce tayi mata shimfid'a ta kawo mata ruwa da lemo, sai da ta gaida su sannan ta sanar musu ai tare suke da yayanta Abba yace "kuma kika barshi awaje kai wannan yara Allah ya shirye ku da rashin wayo"
Ya fita ya shigo da MD duk da kasancewar basu dashi amma yayin gidan kad'ai zai nuna maka mutanen gidan suna da tsananin tsabta, sosai suka gaisa da su kafin Maryam tayiwa Abban bayanin dalilin zuwansu, hakan ba k'aramin dad'i yayi wa Abban na ya zauna yayiwa MD bayanin duk abinda aka sai mata da kud'ad'en da take kawowa harda shanu da yaje can garinsu yasai mata da yake shi ba d'an garin bane.
Yanayin sa kawai yasa MD yaji hankalinsa ya kwanta da shi dan haka suka d'anyi shawarwari akan abubuwan nata yace "tunda shanun sun kai har guda goma kuma duk Yan k'anana wanda basu fara haihuwa ba kawai asai na mijin sa kamar guda biyar a had'a sai abada kiwo ga wanda ya amincewa.sannan gidajen kuma anemi yan haya masu mutunci da amana asaka su aciki"
"Nima tun farko shawaran da nayi da ita kenan tace in dakata tukun" murmushi MD yayi yace "kasan yar k'auye ce babu abinda ta sani sai k'auyanci" shima Abban murmushin yayi yace " banda abinka d'ana ai k'auye tushen kowa ne shima MD murmushin yayi suka ci gaba da tattanawa, sun jima a gidan har sanda Maryam ta dawo suka suka shige d'aki dake sanda sukazo bata nan Umma ta aike ta.
Umma ce ta lek'a tacewa Maryam ta fito zasu wuce sai da zasu tafi sannan Maryam ta kawo k'udin da Ammey ta bata ta mik'ewa Abba tace
"Abba gashi nan ka nemi wata sana ar ka fara Allah ya taimaka.
Tsabar mamaki Abba kasa magana yayi gashi kuma ta toshe duk wata hanya da zai mata godiya sai addu'ar da yay ta zuba Mata har suka bar gidan
MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Page 36
Suka shiga mota ya tada suka bar wajen saida suka d'an yi nisa da tafiya kafin ya d'an juyo ya kalleta " enye enye ashe yarinyar tana da hankali, to nima aban jarin mana"
Murmushi kawai tayi tasan tsokanar ta yakeyi dan haka ta d'auke kanta suna cigaba da chat da Halima wacce take zaman jiranta a gida.
"Ko bazaki baniba?" Ya sake tambaya, hararan wasa ta d'an yi masa ta dauke kanta tana d'an murmushi.
Haka dai yai ta janta da hira har suka koma gida kai tsaye d'akin ta ta wuce shima fat d'in sa ya nufa dan duk sun gaji.
Ita kam tana shiga falon ta tadda Halima tana zaman jiranta hararar wasa tayi mata tace " to hajiyata shanyar taki ta bushe Allah badan gobe zan koma ba da tuni nayi tafiyata"
"Sorry dear gidan su name sake mukaje bamu tadda taba har sai da muka jira ta dawo"
"Naji kina jam u kedawa?"
"Tare da bross mana" wani irin waro ido Halima tayi tace "kedawa?"
Kunsan fa Halima bata da masaniyar shirin Maryam MD domin bata da yawan surutun mara dalili.
"Ai kinji abinda nace kema neman zance ne kawai irin naki"
"Ai abunne dole yabani mamaki yadda baku shiri da bross kuma kice tare kuka fita ai kinsan dole mamaki yamin illah"
"Humm wai kinsan ma wani abu kuwa?"
"A'a"
"Wai sona yake karkiga yadda yakemin naci kamar bashi ba duk ya wani susu ce"
"Ke dan Allah dena fadaymin dama ba babanku d'aya ba?"
Ta fad'a duk idanunta awaje tsabar mamaki
"To ni tsabar tsorata ranan da yace yana sona ihu na dinga zunduma masa nayi tunanin kwakwalwan sa ne ya tab'u wallahi"
Jinjina kai Halima tayi tace "haba wallahi wani lokacin nakan zauna nayi tunanin yadda Ammey take ba wata babba ace ta haifi kamar bross da ace kece akace yarta babu wanda zai yi mamaki ammafa bross abin yana d'aure min kai, ke amma kinsami dami akala wallahi na miki murna bross ai miji ne na yaw........
"Ke dalla rufewa mutane baki zaki fara halin naki babu fullstop ba qommer nace miki ina son sane da zaki wani fara yyyyyyyy murya kamar ta yan China"
Harara Halima ta galla mata tace "ank'i a rufe banza mara mutunci ai dama inka shekara dubu bakaga mutum ba tambaya halinsa ni zakiwa iskanci koda yake ni na kawo kaina bari nay tafiyana"
"Jeki mana seme dama duk kin isheni kin saka min ciwon kai"
Sai da sukayi halin naau da suka saba duk had'uwa kafin su daidaita su hau zance na gaskiya da gaskiya, wannan halin nasu tun suna yara suka taso fashi Halima surutu ratata Maryam kuma fad'a.
Sun jima sosai Maryam ta fad'awa Halima gaskiya itafa bata son MD Halima tace "karki damu yar uwa wata rana zakiso shi har kiyi kishin sa kawai dai mudage da addu'ar Allah ya zab'a mana abinda yafi alkhairi amen"
Sosai Halima tabawa Maryam shawarwari masu kyau yayin da sukayi sallama dake hutunsu ya kare zata koma schl itama Maryam d'in sati mai kamawa zata koma.
Tsakanins Maryam da Halima akwai so da k'auna akwai yarda da amana akwai shak'uwa mai tsanani wanda yasamo asali tun suna yan yara alokacin basa rabuwa kullum suna tare ay fad'a a shirya kullum basa gajiya da dambe da f basa b'oyewa junanau duk wani abu har kawo wannan lokacin.
Name sake d'in ta kuwa k'awance ne irin na makaranta sannan babu abinda tasani akanta banda mahaifinta da tasan mai k'udi ne dan har yanzuma bata bata damar zuwa gidansu ba dan Maryam bata jan mutum ajiki sai ta gama karantar waye shi, itama dai bata da wani aibi tana da kirki ga kamewa wanna neyasa Maryam k'ulla kanwace da ita har takai ga tafara temakonta.
Bayan tafiyar Halima Maryam tayi wanka ta fito duk a dining room ta samesu har Baffa sai mama da har wannan lokacin bata dawoba, kujeran kusa da Baffa ta jawo ta zauna suka sakashi atsakiya ita da Nassar yayin da Ammey tata kujerar ke kallon ta Baffa "ke uwar taki bata fad'a miki inda ta tafi ba yau gashi har anyi issha?"
Dan yamutsa fuskar ta tayi itama yawon na mama yana mugun damunta tace "zai wuce gidan waccen haj. Zakiyyar ni bata fad'a min inda zata"
Kwafa Baffa yay cikin b'acin rai kafin yace komai MD ya shigo wanda gaba d'aya kamshinsa ya cikasu kujeran dake kallon ta Maryam ya ja ya zauna ya wani kafeta da ido ko kunyar su Baffan bayaji.
Tana ganin haka ta wani tsare gida yayin da Baffa yace "zamu yi magana daku keda Sailuba idan ta dawo a yawon nata"
Had'e rai Ammey tayi amma bata tanka ba yayin da Maryam ta sunkuyar da kanta k'asa tak'i yarda koda wasa ta kalli inda MD yake shikam ko ajikinsa ya fitineta da kallo yana cin abincin sa, bata wani ci abin kirki ba saboda yadda ya takurata ta mik'e , Ammey ta dubeta tace "ya haka baby banason fa zama da yunwa"
Had'e rai tayi tana hararan MD k'asa k'asa tace "k'oshi nayi ne" daga haka bata jira cewar suba ta bar wajen, duk suka bita da kallo, shima MD kad'an ya k'ara ya mik'e direct d'akinta ya wuce ilai kuwa ya sameta tayi d'ai d'ai asaman gadonta da ice cream tana faman sha sam bai ma kula da abinda takeyi ba sai da ya buga uban sufa ya fad'a kusa da ita sannan ya kula da kayan sanyin da take sha k'ala bai ce mata ba ya zare robar a hankali ya kai saman frich ya aje ya dawo ya kuma kwanciya tareda d'ora kansa saman kafafunta a wani firgice ta kai idanunta saman fuskar shi idanunsa ma shi a lumshe suke take jikinta ya kama wani irin rawa cikin tsantsar tashin hankali da rawan murya tace me mey meye ha ka ni fa ban a son is Kan ci tayi maganar a rarrabe tsabar tashin hankalin data shiga, wani muskilin murmushi ya saki yace
Muje zuwa daga
MAMAN ISLAM
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Gaisuwa ta musamman gareku hazikai kuma jajurtattu a kungiyata
Princess Aisha
Miss flower
Maryam H
Allah ya kara muku juriya da hak'uri. Allah ya kara had'e kanmu first class mu dad'e muyi k'arko 💃🏿💃🏿💃🏿💃🏿
Page 37
"Nine d'an iskan princess?" Ya fad'a yana kallonta ko k'ibtawa bayayi had'e rai tayi tareda fashe wa da kuka maimakon ya saketa kamar yadda take buk'ata sai kawai ya rungumeta take zuciyar ta yayi wani irin mahaukacin buga ta fara k'ok'arin tureshi amma ina k'arfin ba d'aya bane.
"Na tsaneka" ta fad'a cikin kuka sakinta yayi a firgice yace "ni d'in baby ni Muhammad dinki kike cewa kin tsana?"
Harara ta galla masa da idanunta da suka koma launin ja ta murgud'a masa baki ta fice daga d'akin tayi d'akin Ammey wacce itama bata d'akin ta fat d'in Baffa.
Bata jima ba Ammey ta shigo hannunta d'auke da Leda da kaya aciki Nassar na biye da ita yana mitar ta hana Baffa siya masa ways.
Da kallo tabi Maryam wacce ta takure waje d'aya asaman gadonta, kana kallonta kasan akwai abinda yake damunta "Ammey zoki zauna dan Allah muyi magana" tayi saurin katse Ammey tun kafin tayi mata tambayar da bata da amsa,
A hankali Ammey ta tako kusa da Maryam tasamu ta zauna ita kuma tayi saurin d'ora kanta ajikinta tana sauke ajiyan zuciya sannan tace "Ammey zan iya auren MD?" ta fad'a kamar yadda ta tab'a jin m Bash ya kirashi da sunan
Gaban Ammey ne yai masifar fad'uwa a d'an razane ta dubeta tace "waye kuma hakan?" Ganin yadda tayi saida tai mugun bata dariya kafin tace "Muhammad dinki nefa MD nima abokansa naji suna fad'a shine na d'ana" ta fad'a tana b'oye face d'inta ajikinta.
Wani irin sanyi Ammey yaji har batasan sanda ta rungumeta ba tace "zaki iya mana baby me zaihana ai bazaki tab'a samun kamar saba kamilin mutum managarci wanda yasan darajanki"
"Oh ji Ammey saboda shi d'in na wajen kine kike irin wannan zuzuta shin?"
Dariya Ammey tayi ta lakace mata hanci tace ba haka bane baby ai d'ana d'aya ne tamkar da dubu nasan shi nasan halinshi yana da halin kwarai zakiji dad'in rayuwa da shi domin yana da kyautawa"
"Shikenan Ammey tunda kema kin amince da nagartar sa naji na amince zan aureshi kamar yadda ya buk'ata amma fa na sanar dashi cewa bana sonshi hasali ma ni ban tab'a jin sonsa araina ba kamar yadda babu son kowane d'a namiji a zuciyana, to yace yaji ya amince shikenan magana ya kare" daga haka ta mik'e dan fita daga d'akin Ammey ta bita da kallo har ta fice ba k'aramin farin ciki ta tsinci kanta aciki ba duk da cewa maganar ta na k'arshe bai mata dad'i ba.
Ba k'aramin mamaki tasha ba ganin har lokacin MD yana d'akinta akwance ya wani yi mata d'are d'are asaman gado kafeshi tayi da ido tana k'arewa baiwar ubangiji kallo MD ba k'aramin mai kyau bane ta ayyana hakan cikin ranta.
A hankali ta k'arasa rufe k'ofar ta tafi cikin sand'a tana lek'a fuskar shi ya kuwa fisgota da k'arfi ta fad'a kanshi ta bud'a baki zata zunduma ihu yayi saurin toshe mata bakin da hannunsa, tashi yai ya zauna itama ya zaunar da ita suna kallon juna yadda tayi wani tsuru tsuru da ita abin yaso bashi dariya sai kawai ya murmusa baice komaiba ba sai faman kallonta yake.
Yadda yake faman kallonta ba k'aramin takura ta yayi ba ta wani had'e rai tana tura baki bakin ya sumbata ta wani zaro idanu tana kallonsa da k'yar tace "Allah saina fasa aurenka idan kanamin irin wannan abun"
"Yi hak'uri my happiness na daina, amma kisani iya hakan ma ba k'aramin kokari nake ba princess sonki yamin illah bansan lokacin da sonki yayi min irin wannan kamun ba yabi jinin jikina ya mamaye JININA ba dan Allah ki zauna dani koda bakya sona zanfi samun nutsuwa idan kina kusa dani" daga haka bai jira cewar ta ba ya sumbaci goshin ta ya sauka yafice daga d'akin, binsa tayi da kallo kafin ta saki murmushin dabata san ko na menene ba asarari Kuma tace "maye kawai" sai kuma ta shek'e da dariya tana buga cinya.
Cikin sauran kwanakin hutunsu ba k'aramin hanata sakat MD yayi ba tun tanajin haushin sa har ta fara sabawa ya masifar nanuk'e mata duk inda zata sai ya bita matuk'ar yana gida idan ya fita office kuwa kafin ya dawo tana samun kiransa fiye da ashirin tun tana jin haushin sa har ta daina saima wani mugun shak'uwa da yafara shiga tsakaninsu sosai ta fara kamuwa da son MD batare da tasan hakan ba ita dai tasan cewa muddun yana nesa da ita ta rik'a kewar sa in yana kusa da ita kuma tana samun nutsuwa da farin ciki bata gajiya da daddad'an kalaman shi masu sanyata nishadi.
Cikin haka hutunsu ya kare suka koma makaranta karatu suke babu sauk'i kasancewar suna shekaran su na k'arshe hakanne yasa Maryam bata da sukuni har rama ta somayi duk da kasancewar tana samu temako daga MD dan shima idan baku manta ba saida ya fara karatun likita kafin ya koma ya zama soja.
"Na fad'a miki kiyi hak'uri ta k'arasa karatun kafin na tarwatsa komai"
"Bazan iya ba boka itace fa ta wargatsa min shirina na shekara ashirin da d'aya shirina na tundaga ranan haihuwar ta har zuwa yau boka badan ina tsoron rayuwar kurkuku ba da wallahi da hannuna zan kashe ta kamar yadda ta kashe min farin ciki na"
Shi kenan tunda kince haka amma kada kiyi kuka dani duk abinda yafaru ki kuka da kanki kasancewar idanunta sun riga da sun rufe tace taji ta gani kuma ta amince.
"Boka ana gama mata aikinta nima nawa yasamu kamar yadda muka alk'awarta"
"Ke zakiyya burinki zai cika kuma Deedah bata da irin halin ki gaskiya tana da wankakken zuciya amma fa wannan buri naki ba makawa zai cika sannan kuma komai zai wargatse"
Maguguna ya had'a musu tare da fad'a musu yadda za ayi kamar yadda aka saba sosai taji dad'in shirin su na wannan lokacin.
Suna fitowa haj. Zakiyya ta dubeta tace "maganar mu na zuwa India?"
"Yana nan amma ba yanzu ba sai komai ya kammala sai kawai nayi b'atan dabo aneme ni arasa koya kikaga?"
Suka shek'e da dariya haj. Zakiyya tace Allah k'awata kinsan takan tsiya kina ta sha'aninki hankali kwance"
"Inafa kwanciyar hankali buri bai cika ba ai CIKAR BURINA shine kwanciyar hankali na"
Haka suka tafi suna hiransu na mugun abu har suka cimma inda suke faking idan sunzo
Wannan karon zuwan bazata Baffa yay musu sai ganinsa kawai sukayi ranan ma Sailuba taje yankan busa dan tafiyar su yana ta matsowa kai ranan Baffa ba k'aramin ruwan tujara ya zubar ba ya addabi Ammey da fitina wai duk laifin tane da bata sanar masa abinda ke faruwa.
Cikin b'acin rai Ammey tace "kaga malam kada ka isheni ni nake aurenta da zan samata ido?
Tsayama da zakace haka naga agaban kama ficewar ta takeyi kataba cewa dan me saini daka raina zakasa agaba da bala i wallahi nagaji kar ka k'ara sakani a shirgin ku da matarka matuk'ar kana son zaman lafiya a tsakaninmu idan Kuma tashin hankalin kake so nima na iya"
Daga haka ta bige zaninta tabar masa wajen cikin b'acin rai, shima yasani k'ureta yayi shiyasa ta zage yau take mayar masa da martani.
Muje zuwa
MAMAN ISLAM CE
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Page 38
"Dad dan Allah ka taimaka min na rasa yadda zanyi na fad'awa yarinyar nan irin son da nake mata gashi saura sati biyu mugama karatun mu kasan tare zamu gama dan Allah dad kayi min rai"
Wani mugun kallon Abba AL HASSAN ya jefawa d boy kafin yace "kaga Kamal ka fita daga idona na rufe karaba ni da wannan shed'anin yaron dan wallahi ko mata sun kare a duniya bazan bari ka auri wannan yarinyar ba yayanta da kake gani ba k'aramin aljanin mutum bane bashi da mutunci ko kad'an d'an iska kamar mai gani har hanji duk sanda kayana suka shigo saya yajamin babbar asara"
Fashewa da kuka d boy yayi dan har ga Allah yana masifar son maryam ga Dad d'in sa idan yakafe akan abu shegen taurin Kaine dashi.
Mahaifiyar sa ya kalla yana kuka sosa yace "mammy dan Allah kisa baki dad ya barni da wacce nake so"
"Uwata ce ita da zatasani yin abinta banga dama ba dagakai har Maimunan wallahi sai na had'a ku naci kaza kazanku" ya antayo musu wani zagi mai rai da lafiya.
Take ran haj. Maimuna ya b'aci ta kasa daurewa tace "ka daici naka uban me na maka kaji nashiga maganar ku bare ka dagamin hankali tsabar neman fitina kasan bazaka tab'a min in k'yale kaba wallahi tunda kai mutumin banza ne mara mutunci kawai"
"Iyayen kine marasa mutunci yar marasa tarbiyya wadda batasan girma da martaban na gaba da ita ba"
"Iyayen kadai sune iyayen banza suna kallon d'an su yana hark'allar miyagun k'wayoyi amma basa iya tab'uka komai tur da iyaye irin naka wallahi, ni kuwa iyayena sun bani tarbiyyan da har ka gani ka yaba kuma ka aure"
Nanfa rigima ta balle harda mare mare dan haj. Maimuna bata ragawa Abba AL HASSAN ko kad'an tunda ta fahimci tantirin d'an duniya ne ga zagi nacin mutunci.
Cikin fushi d boy ya fice yabar musu gidan yana hawayen bak'in cikin wannan halin na iyayen sa wanda ko kunyar idanunsa basaji idan fitinar su ya motsa.
Tun bayan da ta shige d'akin ta Baffa bai karajin d'uriyar taba ya tabbatar da fushi tayi, maganar gaskiya yana mugun tsoron fushin Amina dan bata iya fushi ba idan tayi masa fushi yana matuk'ar shan wahala.
Yana shirin tashi yabita har d'akinta haj. Sailuba tana shigowa fasa tashin yayi ya koma ya zauna ya kafeta da ido, ganin irin kallon dayake binta dashi yasa ta d'an sha jinin jikinta sai ta wayance da fad'in
"La Baffa yaushe ka dawo irin wannan dawowa haka babu sanar wa? sannu da zuwa" nan dai tahau masa borin kunya.
Shi kam k'ala baice mata ba kafeta kawai yay da Ido hukunci yake mata da haka, yayin da ta rasa yadda zatayi, sai da ya tabbatar da yagama sanyaya mata jiki sannan yace.
"Waye naki agarin nan da har kullum bakinan me kike fita yi ko me kike nema wanda baki sameshi anan gidan ba?"
Shiru tayi ta kasa magana sai faman rarraba ido take yayin da Baffa yaci gaba da cewa "maganar gaskiya Sailuba wannan shegen yawon gantalin naki ya isheni haka idan kuma baki gyara ba zan d'auki mummunan mataki akanki"
Hak'urin munafurci taita bashi har da kukan k'arya kafin yace ya hak'ura sannan ya d'ora da fad'in "tunda gobe weekend ne ki sanar da Maryam ta shirya zamu wajen Inna"
A mugun firgice ta d'ago tana duban Baffa yayin da maganar boka yafara kara kaina cikin kunnen ta kamar yanzu yake fad'a mata kar ta sake ta yarda Maryam ta had'u da Inna domin akwai babbar matsala ga had"uwar ta tasu domin Inna zaya ruguje musu komai ta yadda har abada bazasu tab'a nasara akanta ba kamar yadda har yau har gobe suka kasa akan Nassar domin akwai dafa in datake bashi yake sha.
"Lafiya wai me kike nufine Sailuba da hana maryam kusantar mahaifiya ta idan ke kin gujeta so kike yata ma ta guje rabon Maryam da taje garin nan tunda aka yayeta sai dai idan Innan ce tazo ta ganta so kike ki raba yata da mahaifiyata be?"
Cikin dauriya da k'arfin hali tace "a a Baffa ni wacece da zan raba baby da Inna naga nima Innan nan uwatace dan Allah ka daina yimin irin wannan bahaguwar fahimtar"
Nan dai ta kalalleme shi da dad'in baki har ya sauka daga fushin daya dauka sannan ta wuce d'akinta da tarkacen da tazo dashi daga wajen bokanta.
Karfe shida daidai ta dawo daga makaranta a mugun gajiye ga d'an banzan yunwar da ta kwaso tsabar yunwar har wani jiri jiri take gani ta fito a motar ta tana had'a hanya, shima MD shigowar babu dad'ewa wanka yai ya fito ya hango ta tana takawa kamar mai koyon tafiyar murmushi ya d'an yi kafin ya taka a hankali zuwa inda take ya d'an hura mata iska a fuska a d'an tsorace ta juyo dan bata ji zuwansa kusa da itaba tsabar bata nutsuwar ta jarrabawan yau ya azabtar da su fiye da tunanin mai tunani.
Kallonsa tayi da lumsasun idanunta wanda tsabar yunwa yasa suka wani d'an shige "me yafaru happiness naganki haka?"
"Yunwa" tace dashi tana dafe cikin ta da ya isheta da k'ugi "ayya baby muje ciki maza Ammey tagama tuwon dare" da sauri ta kalleshi "Allah tuwo tayi? kasanfa ina son tuwo sosai" d'an murmushi yayi danshi tsokanar ta yakeyi yayi zaton irin Nassar ce itama batason tuwo kamar sa.
"Tsokanar ki nake Baffa kawai Ammey tayima"
" Ai kuwa nima tuwon zanci yasin" ta wuce kanta tsaye dining room d'in, saida ta fara had'a ruwan zafi ta gasa cikin ta kafin ta bud'e tuwon Baffa da Ammey tagama shiryawa gwanim ban shi'awa ta d'auki malmala tasa aflat ta zuba miya ta soma ci a nutse, duk da bak'ar yunwar dake damunta hakan baisa ta rud'a kanta tayi irin cin yunwar nan ba, Ammey da ta shigo dan daukar abincin Baffa tsayawa tayi tana kallon Maryam dake aikawa da tuwo batare da tasan cewa Ammeyn tazo wajen ba, sai data k'arasa wajen Maryam ta ganta tayi wani wuri wuri da ita can kuma tace "wallahi Ammey bross ne yace kinmin tuwo"
"Na tambaye kine?"
Ta fad'a tana wurgawa MD harara wanda yake gefe yana d'an murmushi wayarsa a hannu yana faman daddannawa, bata k'ara magana ba ta d'auki d'an kwandon data jera abincin tayi waje MD ya dungure mata kai yace" da so kikai ki had'a ni da uwata ko?"
Bata ce komai ba sai harara data galla masa taci gaba da cin abincin ta sai data jita daidai kafin ta mik'e tana hamdala tawuce kai tsaye d'akinta ta nufa wanka tayi ta yo alwala tayi sallar la 'asar da ya k'wace mata tun a hanya ta jima tana addu'o'i kafin ta kama karatun Al qura ani mai girma da fita tasoyi d'akin Ammey ganin lokacin magriba ya karato yasa bata fitan ba ta jima tana karatun kafin a kira magriba tayi addu a ta tashi kawo sallar magriba bata bar wajen ba saida tayi issha Nassar ya shigo da murnan zasu gidan yayar Ammey wacce take sonshi "Adda zaki?"
Harara ta aika masa tace "bazani ba d'an rainin hankali da dani kuke zuwa?"
Nan dai ya fitineta da hiran anty shamsiyya wacce suke kira da momma har dai ya ja arayinta tace itama zata cikin farin ciki ya daka tsalle yay waje kaiwa Ammey labari, itama ba k'aramin dad'i hakan yayi mata ba ko ba komai anty shamsiyya zatasan cewa ansami cigaba kenan.
Ita ko Maryam Nassar yana fita ta mik'e ta wuce d'akin Mama mamaki ne ya kamata ganinta cikin damuwa ta k'arasa ta kwantar da kanta saman kafad'ar ta tace "Mama lafiya na ganki cikin damuwa ko baki da kud'i ne?"
Wani k'ululu ne ya tsayewa haj. Sailuba jin tambayar da Maryam tayi mata, amma sanin cewa ita ce silar d'ora ta akan hakan yasa tace mata "eh kina dasu ki bani?" Girgiza mata kai tayi tace "ai tunda naga yanzu Baffa ya bud'e miki bakin aljihu fiye da kima yasa na daina tambayar sa k'udi domin nasan cewa idan kina dasha nima inada shi kuma wanda kike bani ma yanzun baya isana saboda wani saurayi danayi d'an talakawa ne sosai shi nake kashewa" da gayya tayi mata wannan zancen dan son gane asalin gaskiyar batun MD dayace wai maman ta uwar ta bata ki taga ta saida mutuncin ta ba,kimar tafa tak'amar kowacce budurwa mai ji da son kara Martaba da kimar ta har zuwa gidan aurenta.
Ga mamakinta ta kuwa bud'ar bakin mama sai cewa tayi "ni dai duk abinda Zaki aikata kada kisake ki kwaso ciki ki rik'a amfani da matakan kariya"
A matuk'ar firgice Maryam take kalloan haj. Sailuba jikinta har rawa rawa ya soma dan tsabar mamaki kasa magana tayi saima tunanin da ta soma aranta na "anya wannan uwa tace kuwa?"
Da k'yar ta iya ce mata daman nazo ne dan Allah Mama ki barni naje garin da momma take Nassar yace kwana d'aya kacal zasuyi dan Allah......katseta Mama tayi cikin sauke ajiyar zuciyar samun mafita na kaucewa tafiyar ta da Baffa zuwa wajen wannan jarababbiyar tsohuwar tace "sai kun dawo" mik'ewa tayi k'udin da takawo mata sai da ya girgiza ta ta amsa yau ko godiyar batayi mata ba ta fice kai tsaye d'akin Ammey ta nufa har MD ma yana can ta mik'ewa Ammey k'udin ta fashe da kuka tace "wai mama ce take cemin duk abinda zanyi kada na d'auko mata ciki anya uwata ce kuwa dan Allah Ammey ki fad'a min itace ta haifeni?"
Ita kanta Ammeyn ba k'aramin girgiza tayi ba musaman da suka k'irga k'udin miliyan d'aya da dubu d'ari da hamsi itama Ammeyn fashewa tayi da kuka ta kasa magana ganin haka MD ya kasa cewa komai ya rungume maryam yana rarrashin ta ransa na masa wani irin suya sun jima a haka kafin Ammey ta janyo maryam daga jikin MD ta kasa magana saima sabon kuka daya kwace mata.
0 comments:
Post a Comment