A lokacin da mahmud yaje gida, salma ta tarbeshi kaman yanda ta saba,yaci abinci suna fira amma gaba daya yana tunanin yanda za'ayi ya fada mata, haka dai ya daure yayi na maza ya sanar da ita, amma abun da yayi zata sai bai gani bah, tace alhamdulillah Allah ya sanya alkairi yasa abokiyar zama ce ya baka ikon yi mana adalci, ya amsa da ameen tare da kara son salma, haka aka shirya biki hjy binta ta nemo mai wata yarinyar mai suna bilkisu yar masu kudin gaske anyi biki an kashe naira, amarya ta tare cikin gidanta, suna zaman lafiya ita da salma abun su, tun lokacin da hjy zaliha tazo gidan taga irin yanda suke zama ta kitsa ma bilkisu abubuwa iri2 aiko Tun daka ranan ta canza ta fara yima salma bakaken magana da zagi salma bata taba kulata ba, sai dai ma tace bilkisu mai na miki naga kin canza dan Allah in laifi nayi ya kamata ki fadamin ta daga hannu ta mari salma dallah yimin shuru munafuka, jin muryan mahmud sukai yana fadin bilkisu kije na sakeki saki uku, da sauri salma ta juya tana fadin innalillahi wa inna'ilahira jiun, mahmud wannan wani irin abune haka mai tama zaka mata wannan hukuncin, yace salma bazan zauna da macen da zata ci mutuncin kiba, domin ke nake so bazan bari a wulakanta min ke ba, harga Allah salma bata ji dadin sakin da mahmud yama bilkisu ba, a lokacin da hjy binta ta samu labari tazo tama salma ta tas tace kuma wlh aure nan da sati biyu zai kara, aiko hakan akayi aka aura mishi wata shima dai akan salma din suka kara rabuwa tun daka lokacin suke fadin salma ta mallake shi, tana koran duk wanda ya aura, wannan kenan
MUN DAWO KAN LABARIN
yau aka daura aure, Mutane sun taru domin hjy binta tayi gayya sosai, ango dai kwata2 baya cikin nishad'i, zai iya cewa yau itace ranan bakin cika a rayuwanshi domin an daura mishi mara tarbiya shi yama rasa mai yasa mama ta yarda ta bashi fauziya ba,
Ita kuma gefen amarya tana cikin farin ciki, yau itace matar mahmud abun da take ta burin samu shekara da shekaru yau ya zama nata, ta lumshe ido tare da fadin yau zan nuna maka nawa fagen soyayyar, yau zaka sha zumata, ji take kaman azo a tafi da ita yanzu, ta tashi ta dauko maganin da boka ya bata tayi matsi dashi, tayi murmushi tare da tuna abun da bokan ya fada mata indai ki kai amfani da wannan maganin ya sadu dake toh daka ranan sai yanda kikayi da mahmud, domin duk macen daya sadu da ita zai jita kaman dusa, tace salma saina rabaki da mahmud har abada domin nawa neshi.
Salma anci kwalliya sosai tayi kyau, tasa wani tsadaddan material wanda mahmud ya kuma siyo mata tasa da bikin, gefen ta kuma kanwarta ce hauwa, wanda tazo taya ta zama har a kawo amarya ta wuce, suna dan fira jefi2 hauwa tace niko salma mai yasa kika bar mahmud ya kara aure bayan nasan ba zaki barta ta zauna ba, salma tace hauwa mai kike nufi? Tace naga duk wanda mahmud ya aura kin koresu itama nasan wannan ba barinta za kiyi ba, salma tayi murmushin takaici tace hauwa kenan, kina bani mamaki wlh, tace name ai gaskiya ne abun da yake a zahiri mahmud fah akan ki zai iya komai inba wani abu kika mai ba toh mai yasa zai dinga miki haka, salma tace bana tsafi bana shirka, bana makirci, hauwa tayi dariya tare da fadin toh sai me? Tace KISSA hauwa ta kafeta da ido tare da kuma nanata kalman da salma ta fada kissa, tace ya ake ita kissan hala naki na daban ne, tace a'a kaman na kowa ne, hauwa tace toh koya min mana nima inji ko zan gamsu ita kikeyi, salma tace zan fada miki nan gaba hauwa tace dan Allah ki fadamin yanzu dan na matsu inji, tace na miki alkawari dakai na zanzo gidan ki in fada miki, hauwa tace toh shi kenan, nasan bakya karya alkawari ai, sukayi dariya a dai2 nan mahmud ya shigo salma ta tashi da sauri tare da fadin wlcm my dear dana iya guda da nama, yayi dan murmushi yace toh Ina binki bashi tayi dariya dan ta fahimci abun da yake nufi yayi gefenshi itama ta bishi anan suka bar hauwa tana shs'awar irin rayuwar su, sai dai salma taki fada mata sirrin yayin da ita nata mijin suke yawan samun matsala wannan kenan
Anzo daukan amarya an jera motoci masu tsadan gaske, nan fauziya ta tashi cikin murna da zumudi, aka fita, kai tsaye aka wuce da ita gidan ta, suna shiga suka fara guda da habaice2 suna fadin an kawo wacce zata haifa mana y'ay'a Allah ya rabamu da juya sai ci ana zubarwa, salma dai tana d'aki bata fito ba,.
Hjy binta ta kira mahmud taja mishi kunne akan idan ya saki fauziya toh wlh saiya saki salma itama, dan wannan karan bazan dauka ba, gwara ma ka dawo hankalinka tun wuri yace insha Allah hakan ma bazai faru ba, tace toh saika tashi kaje dan fauziya tana jiranka dare kuma yana yi ya amsa da to, ya wuce.
Yan kawo amarya sun wuce aka bar amarya ta tashi ta fad'a bayi tayi wanka tasa wata rigan bacci wanda dashi ma gwara babu, ta zauna tana jiran mahmud ya dawo, lokacin daya dawo taji shigowanshi nan ta koma ta zauna, shi kuma kai tsaye dakin salma ya wuce, nan ya zauna yana ta faman yi mata kalaman soyayya, tace ka tashi kaje d'akin lanwata tana can tana jiranka, yace korata kikeyi salma? Tace a'a inaso ka zama mai adalci ne kuma kasan yau ranan tane ranan dako wace mace take buri kaga bai kamata mu shiga hakkin taba, fauziya jin ya dade bai shigo bah ta fusata tare da fadin yama raina min wayau ta tashi ta fita tana huci tayi d'akin salma....
Maryam Obam😘
ðŸ’ðŸ’ðŸ’KISSA KO MAKIRCI👹👹👹
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
(Mrs nura kuriga)
35to40
A dai2 lokacin ya fito daka dakin, nan sukai Karo, salma na bayan shi, kallo daya ya mata cikin tsana yace ke wace irin mara hankali ce, zaki fito haka bayan kin san bake daya bace a gidan, salma gaba daya ji tayi ta dauke wuta dan wani azabban kishi ne ya dauketa, wanda yasa idonta ya canza amma saita daure tace dear sai da safe ta rufe kofarta, dan bazata iya ganin wannan takaicin ba, kuka ta sake mai karfi, gaba daya xuciyarta tafarfasa yake, daka ta rufe idonta sai taga fauziya da mahmud ranan barci gagaranta yayi duk yanda taso ta dake ta cire abun amma ta kasa, da dai taga haka ta tashi ta dauko al'qur'an, tana fara karantawa nan ta danji dama2.
Mahmud tunda sukai d'aki shida fauziya ya kasa sukuni dan bai yarda da yanayin salma ba, dan yaga kaman ta dan shiga damuwa, yayin da amarya ta kame a gefe ta daura kafa daya kan daya tana girgizawa amma abun mamaki shi gogan ko kallo bata isheshi ba, ta saki tsaki tare da fadin wannan fah inna biye tashi babu abunda zai faru yau, zai sa inyi asaran magani gashi boka yace sau daya yake bama mutum shi, ta tashi ta nufi mahmud din wanda yake zaune kan kujera yana danna laptop, ta zauna ta gefen kujeran tare da rufe laptop din, ta fara magana tana kashe mai ido haba mahmud dare fah yayi kasan kuma Ina jiranka ya kamata kazo mu kwanta, gaba daya mamaki ya hanashi magana dan bai taba xaton haka ba, tasa hannunta cikin riganshi, yayi sauri ya tashi tare da fadin tir da halinki duk wata mace mai mutunci indai tayi aure aka kawo ta duk rashin kunyanta bata neman namiji sai dai shi ya nemeta, amma ke dubeki wai amarya kenan babu kunya babu komai, ta tabe baki tare da fadin toh miye aciki kuma miye abun jin kunya,ina bukatar ka, dan me bazan nuna ba, kallon tsana da mamaki yake mata, yace lallai sai yanzu na yarda da baki da kunya kuma baki santa ba, inba karuwa ba babu wacce za tayi abun da kikayi a daren farkon ta, dan haka yanzu ni kin samin tantama sai anyi miki test kafin in kulaki, cikin fushi tace mai kake nufi kana nufin ni yar iska ce? Yace waya sani abu a duhu, zama tayi tana hawaye ta rasa abunyi tana tunanin shirinta zai rushe lokaci daya ta kuma tashi tace toh naji na kuma yarda in kace baka yarda dani ba, zaka iya amfani da condom, dan ina bukatar ka, yace fauziya am sorry bazan taba kiba har sai anyi test ya tashi ya koma kan gadon ya kwanta abinshi, ranan tayi kukan bakin ciki tare da daukan alwashi sai ta rama duk abun da mahmud ya mata tare da fadin kai da kanka zaka nemeni, a lokacin zan wulakanta ka zan nuna maka aikin boka, itama dai ranan juyi tayi2 bacci yaki zuwa,
Washe gari tunda mahmud ya nufi masallaci da asuba, bayan an idar da sallah ya nufi dakin salma, ya ganta akan dadduma, nan ta gaidashi ya amsa cikin fara'a yayin da ita kuma take jin kishi dan tana ganin komai ya faru yanzu, ta tashi ta dauki dadduman ta ninke, mahmud yazo yayi hugging dinta yace dear mai yake faruwa, tayi murmurshi tace babu komai, babyna ya kamata ka koma dakin amarya tunda mun gaisa, yace salma korana kikeyi koh? Ta zaro ido tare da fadin ni na isa in kori king dina, wanda duk duniya babu abunda nake son inga ina gani kaman ka, kaine kake sani farin ciki kaine rayuwa na, bana so kona minti daya kayi nesa dani, yace mai yasa toh yanzu kike korana? Tace dear ina sonka banso ka tashi cikin maza marasa adalci indai bazan daura ka akan hanya ba ai bana sonka ta karashe maganan cikin sanyin murya, yayi murmurshi tare dajin dadin kalamanta salma kina sani farin ciki sai yasa koda ina fushi ke daya ce zaki iya sani dariya da nishad'i ya bata fake a saman goshinta tare da fadin ngd dear sannan ya fita, bayan ya koma dakin fauziya ya sameta kwance yanda ya barta, ya girgiza kai ya fara tashin ta, tace mai nene? Yace kinyi sallah ta amsa da eh nayi, amma badan tayi ba dan dai kawai kar yasa ta tashi daka baccin ta.
Salma bayan mahmud yabar dakinta kitchen ta nufa dan ta hada breakfast, cikin lokaci kadan ta gama ta jera a dinning sannan ta koma dakinta, tayi wanka ta shirya cikin wani atamfa dinkin riga da skirt ya mata kyau sosai, ta koma parlor ta zauna dan jiransu su sauko, wajan 10 mahmud ya fito yace dear kinyi kyau mahmud a kullum salma kara kyau take mai, yazo ya zauna kusa da ita tare da kafeta da ido, tayi dariya tace my lafiya? Yace ina kallon halali na ne, tayi dariya tare da tashi zata bar wajan ya janyota ta fado jikinshi, ta fara mai magana kaman mai rad'a tace dear bafa mu kad'ai bane yace sai akayi ya, tayi shuru ba tare data bashi amsa ba, tace muje kayi breakfast ina sister na? Ya gane tana so ne ya saketa daka rikon daya mata dan ya fahimci bata so fauziya ta fito ta gansu a haka, yayi murmurshi tare da fadin tana d'aki, tace go and call her, yace kyaleta zata fito da kanta, tace dear itafa bakuwa ce bata riga ta saba ba, plx ka kirata yace ok my lovely wife, bari in kirata tayi murmurshi ya tashi ya nufi sama, Jim kadan sai gasu shida ita, tasa jallabiya, ko kallo salma bata isheta ba, ta nemi waje ta zauna, salma tace morning sister, kaman ba zata amsa ba, komai ta tuna kuma tace antashi lafiya? Salma tace lafiya qalau, ta tabe baki, salma ta hadama mahmud abinci sannan ta xuba nata, tace sister bismillah kar in xuba miki inyi miki kauro, fauziya cikin isa tace ai dama an saba tunda gida babu, mahmud yace aifa kam yanzu ne naga an shigo gari tunda kin fara neman kudi, ta daure fuska, mahmud yasan ta gaya ma salma magana ne shi kuma, ya bata amsa dai2 da ita, har suka kammala fauziya bata ce komai ba, sai mahmud da salma wanda suke fira jefi2, mahmud yace bari inje office yanzu Zan dawo akwai masu jirana, salma tace ok saika dawo take care, ya tsaya yau daka nan zaki min sallama, tayi dan murmurshi ta tashi ganin ta Mike fauziya itama ta tashi tana huci salma sukai waje mahmud ya wuce, tana shiga falo fauziya ta tareta tace naga kina wani rawan kai toh bari kiji kinga duk wannan abun da yake miki ni nace ya miki dan kar kice ya canza miki dan ya kawo ni, amma da kinga yanda yaban wuya jiya da kin tausaya min yace min baki da dadi kaman dusa kike, salma tayi dariya tace eh toh kin san indai namiji yaji dadin mace bazai barta ba ya fita koda wa yake jiranshi musamman a ranan daya fara saninta, ni nasan da hakan kuma sai yasa nace ya kara aure inda ban yarda ba aida bai auroki ba, so kuma maganan kice ya dinga kulani plx daka yau kice karya kara kulani indai ki kai hakan xan San dagaske ke Zuma ce tana fadin haka ta wuce tabar fauziya da bakin ciki, xan nuna miki ni Zuma ce kuma na isa nan bada dadewa ba.....
Maryam Obam😘
ðŸ’ðŸ’ðŸ’KISSA KO MAKIRCI👹👹👹
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
(Mrs nura kuriga)
40to45
Salma d'aki tayi abunta dan bata son dangin fauziya din suxo su sameta a falo, tana ko yin d'aki bata dade da shiga ba taji shewa da gud'a tare da habaice2 abun ko a jikinta ta kwanta abunta, ta fara bacci taji kaman mutum a kusa da ita, tayi sauri ta farka sukai ido biyu ya sakar mata murmushi tare da fadin wannan irin razanar fah? Ta kasa magana dan ta tsorata dan ita a zaton ta tasa key a dakin kuma ba tayi zaton mahmud din bane, saida ya janyota jikin shi, sannan tayi ajiyan zuciya, shima da kanshi yasan a tsorace take da zaman dan ya shigo yaji irin zage2 dasu fauziya sukeyi suna ganin shi sukai shuru, ta katse mai tunani da fadin yanzu ka dawo? Yace eh ban dade da shugowa ba, tayi murmushi tare da fadin wlcm, ban san zaka dawo yanzu bah gashi ban daura lunch ba am so sorry bari inje inma, yace no barshi na siyo mana gashi nan, ta kalleshi da mamaki tace siyo abinci kuma? Yace nasan yau gidan mutane zasu zo sai yasa nace bari in kawo, tayi dan murmushi tare da sauka a kan gadon ta dauko ledan fried rice ne da garden salad, sai kuma kaza, ta dauko musu drinks cikin fridge din dake dakin, nan suka ci suka koshi..
Su fauziya ana falo ita da kawayenta da yan uwanta, suna cin abinci yayin da ita fauziya din bata abincin take ba, wata daka cikin kawarta mai suna jamila suna kiranta da jamcy, kana ganinta kasan yar bariki ce wacce ta goge a harkan ansha mai fatar nan tayi jawur, tace fauzy ke yanzu a nan zaki zauna kina ganin yayi sama tun daxu ke an barki a nan, fauzy data qumu da bakin ciki ta tabe baki tace jamcy to mai kikeso inyi nan jamcy ta saki dariya tace lallai fauzy, ashe za kiyi sanyi dama akwai abun da xai sa kiyi shuru, tabdi amma kin ban mamaki ina zafin naki? Ina rigiman ki? Fauzy tace jamcy kin san mahmud shine namijin da nake so, ke kin san yanda akayi na shigo komai sai na bishi a hankali kin san dan rainin wayau babu abun daya hada ni dashi jiya sai bakaken maganganu, wai bazai taba niba, sai anyi min test, jamcy tace toh fah mai yake nufi? Fauziya tace abun da kike tunani, jamcy tace toh gskiya sai kinyi dagaske inba haka ba zaki zama yar kallo, dan wannan matar tashi ba'a zaune itama take ba, dan yanda yake sonta ai yayi yawa, wlh gwara ki farka kisan abunyi da ita, fauziya tace karki damu ni yanzu matsalata daya yanda zani wajan malam yaban wani abun, jamcy tace toh gskiya kema kin san wannan abune mai wuya, keda kike amarya ai babu hanyar fita, fauziya tayi dan gajeran tsaki tace ina zuwa tayi sama, kai tsaye dakinta ta shiga ta dauki waya ta kira mamanta, hjy zaliha ta dauka cikin fara'a nan fauziya tasa mata kuka tace lafiya fauziya mai aka miki? Nan ta zayyane ma mamanta abunda ya faru, tace yanzu ma daya shugo yana dakinta Tun dazu, koda ya shigo ko magana bai min ba, yayi wajan matarshi, nan hjy zaliha tace kiyi shuru fauziya karki damu yanzu zan fita zani wajan malam komai ya faru zaki jini, kar ki kara xubar da hawayenki a banza, dan kuka ba naki bane, tace mama kisan duk yanda xa'ayi aban abunda xan mallaki mahmud, sannan a rabashi da salma, hjy zaliha tace an gama bari inje yanzu banso mutane su shigo suji abunda ke faruwa, sai kin jini ta kashe wayan, ta yayibi gyale ta fita.
Kawayen amarya sai wajan karfe goma suka bar gidan, mahmud shida salma suna tare sai dai yaje sallah ya dawo, duk yanda yaso ya sadu da salma taki yarda dan ta nuna mishi bai kamata ba, in sukai haka zasu shiga hakkin fauziya, ganin kaman ya danyi fushi abun da bata saba gani ba a tare dashi, tace dear plx kar kayi fushi dani wlh fushin ka a kaina ba alkairi bane, ya dan juya mata baya, ta juyo ta gabanshi tana hawaye gaba daya ya rude tare da riko ta, cikin tashin hankali yace salma mai yasa ki hawaye, tace ba kai bane, cikin shagwaba, yace sorry my baby, ki daina plz bana so, bana son abun da zai saki bacin rai, tace nima haka yau naga abun da baka taba yi min ba, kayi fushi dani, ban hanaka kaina da gangan ba sai dai gudun kar insa kayi zalinci domin Allah zai kama ka, tunda bani bace dakai, zamu shiga hakkin fauxiya tunda bata yarda kayi hakan ba, kaga gwara muyi hakuri, yayi murmushi tare da fadin na fahimceki salma kuma na gane, bakya taba yin kuskure komai kina yine akan abun da addini ya tsara, ngd ma Allah daya bani ke, tayi dariya cikin jin dadi tare da fadin ngd ina koda yaushe ina godiya da Allah ya bani kai a matsayin miji, domin duk wata mace irin mijin da take son samu kenan, yace waya fada miki? tayi dariya tace abun da yake zahiri ne ai, tace dear ka tashi ka tafi dare yayi dan naji shuru da alama babu kowa, bai musa ba ya tashi ya fita kai tsaye dakin fauxiya din ya nufa, ya ganta a zaune tana waya jin motsin shi yasa tayi sauri ta kashe, kallo daya ya mata ya kauda kai gefe ta tashi cikin isa da gadara tace sai yanzu ta barka kazo, bai kulata ba hakan ya mata xafi, tace anje ana cin amana ta toh wlh baka isa ba yau sai an ban hakki na wlh dan ban san abunda kake nufi dani ba, namiji ya koma mijin tace, yace ki koma ki nemo tarbiya da yanda ake magana da miji, domin mace mai tarbiya ba xatayi abun da kikeyi ba, tace naji bani da tarbiya din, nidai abu daya na sani kaban hakki na, ganin bazai iya da ita ba yasa yayi banza da ita ya kwanta abunshi, nan ta zauna tana ta fadin magana bai tankata ba, haka dai itama ta gaji ta kwanta.
Tunda ya fita sallah sa asuba, ta tashi ta dauki waya ta doka ma mamanta kira, ringing daya ta dauka, fauziya tace wai ina kika shiga tun jiya inata kiranki baya shiga,, tace kedai bari, tunda na fita sai wajan daya na dawo, fauziya tace an dace? Tace eh an dace amma da sharadi, tace name? Yaban na wanda zaki sami mahmud zai fara kulaki Amma yace bazai yi wani tasiri ba har sai kinje da kanki zai baki wanda zaki mallake shi gaba daya, yaji baya ganin kowa sai ke, tayi dariya cikin jin dadi tace an gama yanzu yaushe xan sami wanda ya baki tace anjima zan zo dakai na in kawo miki tace toh sai kinzo amma kixo da wuri tace babu komai,
Wajan karfe goma koh saiga hjy zaliha taxo gidan, a lokacin salma tana falo, ta shigo da sallama salma ta amsa, tare da gaisheta ko kallo bata isheta ba, tayi sama dakin fauziya, tayi nocking fauziya ta bude ganin mamanta yasa ta saki dariya cikin jin dadi domin yau zata sami cikan burinta, bayan ta shigo ta zauna tace ina mahmud din tace baya nan ya fita, nan ta fito da maganin ta bata turare ne, tace kiyi amfani dashi ki tunkare shi zaki sha mamaki, tace mama Kin tabbata xaiyi aiki tace sai yasa yace ki gwada in yayi kije da kanki tace shikenan, tace mai kuka dafa ne dan ban karya ba, tace tashi muje kitchen din muga mai waccan mayyar ta dafa, nan suka fita salma na nan yanda ta barta daxu, hjy zaliha tace samun waje an tura min y'a d'aki ke kin fito falo kina kallo, koh ke ga mai gida, toh bari kiji kin kusa b..... Lokaci daya kuma tayi shuru tare dayin tsaki, ganin haka salma tayi d'aki, nan hjy zaliha aka zauna a dinning aka bude ciki ana kwasan abinci, sai wajan biyu tabar gidan,.
Fauziya tana ta jiran mahmud ya dawo taji shuru to wai yau ina yaje ne banji motsin shiba? Wajan 8 taji an bude gate ta leka ta window taga shine ya dawo da sauri tasa turaran da aka bata, ta zauna dan ya shigo, amma taji shuru tace nasan yana dakin waccan shegiyar, ta tashi tayi dakin basa nan, nan tayi falo tagansu mahmud ya daure fuska dan yana yin shigan da tayi night gown ne sai wani da tasa a sama ana ganin jikinta, yace ke wai yaushe xakiyi hnkali ne, bata ce komai ba sai daura hannunta da tayi akan kirjinshi gaba daya ya fita hayyacin shi, ya riko hannunta yana shin shinawa ta kara makale shi, tace dear yaushe ka shigo yace tun dazu tace tashi muje d'aki kai nake jira, ya tashi tare dayin hugging dinta, salma wani irin jiri ta fara gani dakyar ta iya tafiya d'aki fauxiya tace kadan kika gani, mahmud gaba daya ya fita hayyacinshi baya ganin komai sai fauziya.
Maryam Obam😘
ðŸ’ðŸ’ðŸ’KISSA KO MAKIRCI👹👹👹
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
(Mrs nura kuriga)
50to55
Tana kashe wayan tasa wata doguwar riga, ta dauki gyale, ta fita, tuki take amma gaba daya bata cikin haiyacinta, kai tsaye gidansu tayi, tana shiga tace mmnta taxo su wuce wajan malam, itama ta zira hijab suka nufi wajan malaminsu, sun tarar da Mutane a wajan sai da suka bi layi har yazo kansu suka shiga, yana ganin fauziya ya fara Washe baki, nan suka zauna, yace ya zaku zo ku biyu bayan nace ita daya zata xo? Nan hjy zaliha tace akwai matsala ne sai yasa ka gammu tare, ya daure fuska sannan yace tafita ta basu waje da fauziya zaiyi magana, nan ta tashi tayi waje tana fadin tuba nake, ya kalli fauziya yace ya akayi?? Tace maganin daka bani yayi aiki amma makirar matarshi na rasa mai tamai baya ganin kowa sai ita, yanzu ma tana asibiti ance tana dauke da juna biyu, yayi dariya tare da fadin yanzu mai know kikeso ayi mata? Tace a xubar da cikin domin indai ta haiyu na shiga uku komai nata ne, sannan asa ya tsaneta, inaso asashi ya soni kaman ranshi, na zama komai nace dashi za'ayi aiki a gidan, yace an gama ya taso yazo kusa da ita yana mata murmushi ganin haka yasa ta tamke fuska tare da fadin ya haka kuma? Yayi dariya warin bakin shi ya doketa, yace ta hakan ne kawai Zan baki abunda kikeso, tace bazan iya wannan abun dakai ba ka fadi ko nawa ne Zan baka, yace bana son kudi keee in kin yarda to, in baki yarda ba tashi ki tafi haushi ya kashe ki, nan ta zauna tayi shuru, can tace ta yarda, ya saki dariya nan suka fara aikata zina saboda neman abun duniya Allah ya tsare mana imanin mu, taji jiki sosai yayin da mlm shi kuma abun yamai dadi, nan ya bata magani yace tayi hayaki dashi, sannan ya bata wani turare yace ta feshe duka gidan dashi indai salma ta shaka toh cikin zai zube, sannan ya bata wani kwalli yace tasa indai sukai ido biyu da mahmud toh babu shi babu salma, yace wannan kwallin kar ki kuskura koda da rana daya kiki sawa duk ranan da kika yi fashi toh komai Zai baci, tace toh inya kare fah? Yayi dariya yace bazai kare ba, kullum zaki ganshi a cike, nan tayi godiya ta tashi dakyar ta fara tafiya dan taji jiki, har taxo wajan kofa ya kirata yace duk ranan sati ki dinga zuwa tace toh ta fita tana tsaki, nan taga mmnta tace suje, bayan sun fita tace ya kukayi tace yaban magani tace dakyau kar dai kiyi wasa gaskiya tace hauka nake inyi wasa tabdi da haka har suka karasa gidansu ta sauke mmnta sannan ta wuce gida, har yanzu mahmud bai dawo ba,
Salma har yanzu bata farka ba, mahmud gaba daya ya kasa sukuni, hankalinshi a tashe yake, ya tambayi Dr yakai sau goma yaushe zata farka amsa dai daya yake bashi, bai sani ba amma koda yaushe zata iya tashi, sai wajan karfe uku na rana ta bude ido tare dayin salati mahmud dake gefen gadon bai san ta farka ba dan a hankula tayi salatin, ta hango mahmud a gefenta lokaci daya abun daya faru ya fara dawo mata nan ta saki kuka tare da tambaya maiya faru dani, mahmud yayi sauri ya tashi dan yaji sheshekan kukanta, yace salma dan Allah kibar kuka, ya kamota tare da rungumeta yace salma dan Allah kiyi hakuri nasan na miki laifi babba wlh salma nima na rasa mai yasa nayi haka ji nayi kaman ana turani, am......, tace mahmud badan haka nake kuka ba komai kayi ai matarka ce, ina kuka ne kawai dana ganni a nan ban san maiya faru dani ba, kalamanta yasa gaba daya jikinshi yayi sanyi tare da kara tausaya mata, ya tabbata abun daya faru jiya shiya sata cikin wannan halin amma gudun karta sashi damuwa tace ba abun bane yake damunta, nan ya tashi yace bari ina zuwa, bai dade ba ya dawo tare da driver dasu flaks da kayan tea, nan ya hada mata ya bata tasha, tana sha gaba daya ta amayar dashi a jikinshi, babu abunda yake fada sai sannu, harta gama sannan ya tashi yayi toilet da ita, ya wanke mata jikinta,ya kalleta yace tana da number din hauwa a kai tace eh, ta bashi yasa a phone din driver ya kirata ya fada mata halin da suke ciki, yace ta kawo ma salma kaya, tace toh, nan ya kura mata ido yana kallonta yana murmushi, tasa hannu ta rufe kirjinta, abun ya bashi dariya yace yau ni akema haka, ta dan saki dariya tace naga kallon yayi yawa ne, yace albishirinki tace goro, yace salma Allah ya anshi addu'ar mu, saimu kara gode mai, cikin kosawa taji abun daya faru tace ina jinka, nan yace salma kina da......... Nocking suka ji, yace waye nan yaji muryan hauwa, ya bude tare da amsan kayan ya rufe kofan, yasa mata kayan jallabiya ce, tace ina da me?? Ya matsa kusa da kunnenta yace kina da ciki, lokaci daya wani hawaye ya xubo mata tare dayi ma Allah godiya, yau itace dauke da ciki,
Fauziya tunda ta shiga gidan ta feshe shi da turaran da boka ya bata, jiran dawowan salma kawai take, tayi dan dariya badai ki haiyu anan ba wlh domin ni ya kamata ace na haiyu da mahmud bake ba, tabdi wlh zan iya aikata komai akan inga babu cikin nan.
Dr yazo yaga jikin salma da sauki, yace zasu iya tafiya gida, amma karta dinga d'aga hankalinta, nan ya rubuta mata magani sannan suka wuce, saida suka fara ajiye hauwa kafin suka nufi gida, bayan sun shiga falo nan taji jiri yana neman dauketa tayi sauri ta rike mahmud dan yanda take ganin dishi2 shi kuma gaba daya ya rikice yana fadin salma salma, amma gaba daya bata san yana yiba, fauziya dake d'aki taji maganan shi ta fito da sauri ganin halin da salma ke ciki yasa ta saki dariya tare da fadin ciki sai dai kiga anayi badai ke ki dauka ba, ganin wani ruwa yayi yana xuba daka kafarta da sauri ya dauketa ya kuma fita da ita suka koma asibiti, nan fauziya ta saki shewa burinta ya cika..
Maryam obam😘
0 comments:
Post a Comment