Driver gudu yake amma mahmud gani yake kaman baya tafiya, gaba daya ya tsorata da yana yin salma, suna isa asibitin aka kuma yin emergency da ita, nan Dr ya shiga ya fara dubata mahmud sai kaiwa da komowa yake, Dr ya dauki wajan 30mnt kafin ya fito, ya kalli mahmud yace saika godema Allah yanzu ta dawo haiyacinta, yace Dr cikin fah?? Hope babu abunda ya sameshi?? Dr yace eh babu abunda ya sami cikin sai dai tana bukatar bed rest, inba haka ba cikin zai iya fita, nan yayi ma Dr godiya sannan ya nufi d'akin da aka canza mata, ya sameta a kwance ga wata nurse tana gefenta, bayan ya shiga nurse din ta fita, ta sakar mishi murmushi, ya kamo hannunta tare da fadin ya jikin naki? Tace da sauki, yace kiyi hakuri babyna yana baki wahala koh? Yanda yayi maganan abun ya bata dariya, nan ya zauna tare da ita har wajan 10 tace yaje gida, ya mata wani irin kallo yace in tafi in barki dawa? Tace nurse zata dinga kula dani, yace a'a babu inda zani ina tare dake, tayi murmushi tace plz dear ka tafi kaga babu wani abu dake damuna, na warke kawai hutu nake bukata, yace shikenan amma sai dai in kira hauwa taxo ta kwana dake ban yarda ki kwana da nurse kawai ba, tayi dariya tace toh shikenan,
Kai tsaye gidan hauwa din suka nufa, dama ya kirata ya fada mata zasu zo su dauketa tace babu komai mijinta yana lagos ta fada mishi, bayan sun dauketa yace bari suje gida ta dauko ma salma kaya sai driver ya dawo da ita, hakan koh akayi sunje gidan babu kowa a falo hauwa taje d'akin salma ta kwaso mata kayan sawa da sauran abunda take bukata ciki harda wayarta, sannan suka koma asibiti ita da driver, driver ya taya ta diban kayan sukai ciki dashi sannan ya wuce, hauwa ta kalli salma tace wannan abun kaman wani almara kin tafi lafiya kuma kin dawo jiki babu dadi, salma tayi dariya tace ikon Allah kenan babu yanda bazai iya ba, jarabawa ne, hauwa tace hakane Allah dai ya sauke ki lafiya ta amsa da amin, da hauwa da nurse suka kwana da salma komai take so sai dai a mata basa bari tana wani motsi mai karfi domin har yanzu ruwan nan yana fita.
Mahmud kwanciya yayi a falo, can ya tuna da wayoyinshi a dakin fauziya yayi tsaki sannan ya tashi ya nufi d'akin, tana nan daka ita sai wata riga na bacci iya cinyanta, suka hada ido ta sakar mishi murmushi, lokaci daya yaji komai nashi ya tsaya, shima ya mayar mata da martani, ganin haka yasa taji dadi domin abunda take so ta samu magani yayi aiki, matsawa yayi kusa da ita yayi hugging dinta, gaba daya ya gigice, ji yayi kaman ana tsungulinshi nan suka shiga soyayya, tun daka lokacin gaba daya yaji fauziya ta shiga ranshi har yake ganin ta fiye mishi salma, amma wani gefen na zuciyanshi na karyata hakan, washe gari har wajan 12 suna ta bacci abunsu gaba daya fauziya ta kashe wayanshi,.
Salma ta tambayi hauwa mahmud yazo kuwa dan itama tasha bacci, tace a'a bai zo ba, abun ya bata mamaki tace anya lafiya kuwa? Har karfe daya tayi bai shigo ba, tace bani wayana in kirashi ta kira a kashe, tace anya lafiya, wayanshi a kashe mahmud kuma baya kashe waya, duk ta rude, tace hauwa dan Allah ko zaki gida kiji koh lafiya, tace salma ki kwantar da hankalinki dan Allah, ki kira driver dinshi kiji, nan ta doka ma driver kira, ya dauka tare da gaidata ta amsa tare da fadin oga fa Kuna tare ne? Yace yana cikin gida dazu na shiga naji shuru bai fito ba dan ko sallan asuba yau banga ya fito ba, sai madam tace min yana bacci yace wai ya gaji yana son ya huta, nan salma taji gabanta ya fadi ta kashe wayan, ta kalli hauwa tace hauwa ki kira min Dr ya sallameni, hauwa tace akan wani dalili salma? Tace hauwa barin fauziya da mahmud hatsari ne ki duba fah har yanzu bai zo ba kuma ko waya baiyi ba yaji ya jikina, na kira ance yana bacci wai ya gaji, hauwa tayi shuru tare da tausaya ma yar uwarta tace toh ko Kin je gidan mai zaki yi, ba gwara ki zauna a nan ba ki sami lafiya, tace hauwa baki San wacece fauziya ba, fauziya makira ce wlh ina tsoran makircinta, hauwa tayi dan murmushi tace salma kenan, har akwai macen da zata baki tsoro keda ake jin tsoranki kin mallake miji, ganin hauwa ba zata fahimce taba yasa tayi shuru, gaba daya ranan mahmud bai zo asibitin ba, hankalin salma yayi mugun tashi, ta tashi daka kan gadon nurse tace madam lafiya ina zaki ko toilet zaki shiga, tace mata eh, nan ta taya ta sauka a hankula sannan ta shiga toilet din, tayi alwala, taxo ta zauna tana sallah tana kuka tana rokan Allah ya kare mata mijinta tun wajan biyu ta fara sai da takai wajan uku tana yi, data sallame, nurse din tace madam sannu gaskiya kina burgeni yanda bakya wasa da sallah salma tayi dan murmushi, ta tashi ta koma gado ta taimakon nurse din ta kwanta tana ta Istigfari, bacci barawo yayi gaba da ita.
Mahmud harga Allah ya manta da salma, gaba daya baya ganin kowa sai fauziya ta hanashi fita ko nan da can, salma ta kira ta kira amma sai dai fauziya taita danna mata busy, harta hjy binta itama ta kirashi amma fauziya taki bari ya gani balle ya dauka, ta zauna dashi daka tace kaza yace mata toh an gama,
Yau satin salma daya a asibiti, babu mahmud babu dalilinshi, koda yaushe salma na gayama Allah kukanta, cikin ikon Allah wannan ruwan ya daina zuba, duk ta rame, hjy binta tazo asibiti da kanta ta sami salma a zaune ita da hauwa, ta mata tatas tace kin shanye min d'a inna kirashi baya dauka baya zuwa waje na, to wlh baki isa ba, babu abunda salma take sai kuka, nan hauwa tace hjy kiyi hakuri wlh itama rabonta da mahmud yau wajan kwana bakwai kenan, nan hjy binta tayi shuru, can tace karyan banza muna fukai wlh zanyi maganinki, ta fita fuuuu, tana mota tana tunani ko dai gaskiya aka fada mata domin inta kira fauziya itama bata dauka, sai rannan data dauka tace tana gidansu ta tambaye ta mahmud fa tace yana gida, da haka har driver ya karasa da ita gida, mahmud ko ya koma saniyar tatsa dan fauziya ansan kudi take a hannunshi kaman hauka, har gida ta gani tace tana so ya bata kudin ta siya,
Yau salma ta cika kwana goma sha daya a asibiti, Dr ya bata sallama, yace ta dinga kiyaye wa, tace toh, ta kira wayan mahmud a kashe nan tace suje su hau taxi, hauwa ta fita ta samo mai taxi suka kwashe kayansu suka sa a ciki, kai tsaye gidan suka nufa, babu kowa a falo, har yanzu tana jin kalan abun da taji ranan data shigo falon, tana ta furta innalillahi wa inna'ilahira jiun......
Maryam obam😘
ðŸ’ðŸ’ðŸ’KISSA KO MAKIRCI👹👹👹
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
(Mrs nura kuriga)
60to65
Har suka haura sama sai data shiga dakinta taji dai2, nan hauwa tace bari inje in hada miki wani abu kici, tace toh, nan ta sauka tayi kitchen, bayan hauwa ta fita salma ta zauna tana kuka tare da tambayan kanta mai tama mahmud, wata zuciyar tace baki masa komai ba, aikin fauziya ne, nan tayi sauri ta kawar da tunanin dan bata son ta gasganta abunda zuciyarta take fada mata,lokaci daya ta share hawayenta tare da fadin koma mai nene addu'a shine magani,
Mahmud ya shigo gida dan yau ya fita suna da meeting, yaji motsi a kitchen ga kamshi dake tashi, nan yayi kitchen din amma sai yaga ba fauziya bace, yace hauwa, yaushe kika zo? Ranta a bace tace dazu, tace salma fa? Tace tana d'aki, nan yayi sama, har hauwa ta gama ta dauka takai mata farfesun kayan ciki ne, da teba miyan ogbono, tace tashi kici, salma ta tashi tare da daukan kayan cikin ta fara ci, tace kaman Kin san abunda nake so inci gashi yayi yaji, hauwa tayi dariya tace mai ciki an bani da kwadayi yanzu wannan ne yayi yaji, tace eh sosai yajin yamin dadi, nan suka fara fira can hauwa tace mahmud ya shigo kuwa? Tayi shuru tare da kallon hauwa taci gaba da cewa dazu ya shigo kitchen nace kina d'aki, salma ta 'kago murmushi tace eh ya shigo yace min bari ya dawo, shuru tayi tare da tunanin toh mai yasa mahmud bai zoba bayan ta fada mai ina d'aki, ganin shurun yayi yawa hauwa tace bari inzo in wuce gida, salma tace kai mai yakon ki bari in dan kara warkewa tace ai kin warke yau gida zani, nan ta tashi ta dauki kayanta tace toh sai min yi waya, Allah ya kara sauki ta fita,
Mahmud yazo zai shiga d'akin salma suka hadu da fauziya tasha wannan kwallin nata, ta fara mai fari da ido, gaba daya ya rikice ya bita, duk da zuciyanshi nason ganin salma din amma ya kasa shiga ya rasa mai yasa, fauziya tabbas ta tsorata da dawowan salma, domin tunda suka dawo ta gansu ta window din d'akin ta, amma abu daya take jin dadi inta tuna cikin salma ya xube, tace yanzu inna bari ta haiyu ta sami namiji aina bani komai ya koma wajanta, tayi dan murmushi tace akan kudi zan iya komai wlh, .
Har gari ya waye mahmud bai zo wajan salma ba, abun ya dameta sosai amma babu abunda take sai addu'a dan daran jiya batayi bacci ba, sallah take tayi, Sai wajan asuba ta samu tayi bacci, shima mahmud din yana son zuwa wajanta amma ya kasa ya rasa dalili, sun fito suna breakfast shida fauziya amma gaba daya hankalinshi na wajan kofar salma yana son yaga koh zata fito ya ganta, fauziya ta lura da hakan, tace lallai zan dauki mataki gaskiya kafin abu ya lalace, ta kalleshi tace ya kamata yau kaje gidan mama ka gaidata yace toh an gama bari in gama sai inje, hakan koh akayi yana fita, itama ta fita, gidan malaminta tayi babu kowa dan haka kai tsaye ta shiga, fuskanta a daure ta zauna yace lafiya kuwa? Tace ina lafiya abu yana so ya lallace, yace ina zuwa nan ya buga kasa, yace kai karya ne ya kuma bugawa, ya hargitsa tare da fadin ya zaku min haka wannan karya ne, ya hargitsa yakai sau biyar yana fadin karya ne, tace wai mai yake faruwa ne, yace cikin bai zube ba, tace what kar ka raina min wayau mana, kana nufin duk aikin da kayi baiyi ba, toh wlh da sake kullum kasa ina ta faman zuwa duk sati kana tabani da wannan kazamin jikin naka amma kace cikin bai zube ba, ya daka mata tsawa cikin murya mai karfi lokaci daya tayi shuru yace ke yarinya karki fadamin maganan banza wannan cikin ko mai zaki a kanshi bazai fita ba, in kika matsa zaki iya rasa rayuwarki, kuma daka yau karki kara zuwa nan inko kika sake zuwa saina sa aljanu sun illata min ke tunda baki da kunya baki San mutunci ba, duk rashin kunyan fauziya ta tsorata musamman yanda taga kwayar idonshi ya canza daka fari zuwa jaaa, yace fita kiban waje da sauri ta tashi tayi waje kirjinta na dukan uku3,
Mahmud bai dade da fita ba, ya dawo, domin babu abunda yake son ya gani kaman salma, dan ko gidan mama din bai jeba, yana dawowa kai tsaye d'akin salma yayi ya ganta a zaune tana kwalla, lokaci daya yaji jikinshi yayi sanyi, ya kira sunanta cikin sanyin murya, salma, tayi sauri ta waigo sukai ido biyu gaba daya yaji kaman an cire mai wani abu, ya nufeta tare da tsugunnawa a gabanta yana fadin salma nayi miki laifin da ban San da wani kalma Zan baki hakuri ba, dan Allah salma ki yafe min wlh ni kaina ban San abunda yake damuna ba, kwana biyu da suka wuce kullum na kasance cikin kasala, wanda bana iya aikata komai, dan Allah ki yafe min, tayi sauri ta toshe mai baki tare da fadin miye haka, dan Allah ka tashi daka wannan tsugunnan kana sani ina jin wani iri, yace salma bazan tashi ba har sai kin yafe min, tayi dan murmushi tare da fadin baka min komai ba inma kamin na yafe maka, nayi ma kaina alkawari bazan taba yin fushi dakai ba, yayi murmushi tare da tashi yayi hugging dinta, yace Zan iya magana da babyna ta d'aga mai gira alaman eh, yasa kunnenshi akan cikinta yana fadin baby hi, how are you, hope you are ok, talk to dady my baby say hi to dady, dariya salma ta saki, ya taso yana kallon ta cikin so da kauna ganin kallon da yake mata yasa ta rufe fuska yayi murmushi nan suka shiga farantawa juna rai,
Fauziya tana fita, ta kira hjy zaliha tana kuka tana fada mata abun daya faru tace rabu da dan iskan, kina ina yanzu muje wajan wani malamin gari da yawa tace ki fito bakin titi zanzo in daukeki mu tafi, tace toh nan ta yayibi gyale ta fito, kai tsaye gidan wani mlm suka je, inda yake zaune a wani daji saida suka ajiye mota sukai tafiya mai nisa a kafa, bayan sun karasa babu abunda kake ji sai kukan tsintsaye fauziya tace nifa tsoro nake ji, hjy zaliha tace karki damu babu abunda xai faru, suna tsaye bokan ya bullo, fauziya ta rike hannun mmnta, ya saki dariya yace ya akayi, hjy zaliha zata fara magana yace dakata nasan maiya kawo ku, ya kwashe da dariya yace wannan cikin bazai fita ba,tace toh yanzu miye abun yi? Babu wani hanya? Ya kwashe da dariya yace hanya daya ne shine ki bar maganan wannan cikin, ki nuna kina so komai zai miki zan baki wani abu da zaki dinga murzawa komai kika tambaya zai baki, tace toh nan ya bata wani abu kaman gyad'a guda daya amma yana da dan girma suka wuce, ranan sunyi sunturi gidajan malamai amma ance cikin bazai fita ba sai gidan wani boka da suka je shine yace cikin zai fita amma aikin da xa'a mata akwai tsada tace babu damuwa ko nawa ne zan biya, nan yace zata bada 3 million, tace yanzu babu a hannuna amma gobe zan kawo, nan suka tashi suka wuce da nufin gobe zasu dawo.. Hmmm muje zuwa dan jin ko fauziya za tayi nasara.
Maryam Obam 😘
ðŸ’ðŸ’ðŸ’KISSA KO MAKIRCI👹👹👹
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
(Mrs nura kuriga)
65to70
Sai wajan 9 fauziya ta dawo gida, kai tsaye tayi dakinta bata ga mahmud a ciki ba, nan ta kirashi a waya bai dauka ba, tayi shuru tana dan nazari kar dai ace wannan dan iskan ya lallata komai, dana shiga uku, ta kuma doka mai kira yasa mata busy, tace na shiga uku wlh ya bata komai ni yake kashe ma waya, kai tsaye tayi dakin salma tana bugawa, mahmud yazo ya bude cikin bacin rai yace wai ke mahaukaciyar inace? Tace dole ka fadi haka, dama kana nan shine na kiraka kaki daukan waya ko, toh wlh ni nafi karfin wulakanci sai dai kama waccan mara zuciyar, yace keee kisan abunda zaki dinga fadamin inba haka ba wlh ranki zai baci, tace ya baci din mana babu abunda ka isa kamin wlh, yace haka kika fada koh? Tace eh yace ok kije gidanku saina neme ki, ta saki dariya wlh babu inda zani baka isa ba wlh, ai gidan nan na shigo kenan sai dai kai ka fita ka barshi wlh,kuma ina nan kaida kanka zaka kawo kanka yayi murmushi tare da tsaki ya koma dakin salma yasa key ya barta tana ta hauka, salma gaba daya ta tsorata dan bata san tashin hankali ko kadan, ya kalleta yayi murmushi tare da fadin dear ya naga kin canza? Tace dan Allah ka tafi wajenta wlh ban san rigima plx, ya daure fuska, ganin haka yasa tace kayi hakuri ban fadi haka dan in bata maka rai ba, yace toh karki karamin maganan inje wajanta, tace insha Allah babyna, salma gaba daya ta tsorata da kalaman fauziya, tace dole in kara dagewa da addu'a,
Fauziya tana yin d'aki ta kira hjy binta ta fada mata abunda mahmud ya mata da wanda yayi da wanda baiyi ba duk ta fada mata, dama tana fushi dashi yaki zuwa wajanta wajan sati daya kenan, tace kiyi hakuri gobe zanzo gidan da safe tace toh sai kinzo tana kuka,ranan fauziya bacci gagaranta yayi ta kosa gobe yayi taje wajan mlm a xubar da cikin salma.
Hjy binta karfe bakwai ta dira gidan mahmud, lokacin basu tashi daka bacci bama dan sai da suka kai asuba suna sallah kafin suka kwanta, fauziya ta fito ta rungumeta tana kuka, tace yi shuru ina mahmud din? Tace yana dakinta basu fito ba, ta haura sama ta fara buga dakin tana Kiran sunan shi, yayi sauri ya farka, yace salma ta canza kaya da sauri dan rigan bacci ne a jikinta tayi sauri tasa jallabiya, sannan ya bude kofar kai tsaye dakin ta shiga tana sakar mishi harara, tace sannu shanyayye, ta kalli salma tace kin shanye min d'a baya ganin kowa sai ke, kin raba ni dashi kwata2 baya zuwa wajena yanzu harta office Kin hanashi zuwa toh wlh baki isa ba, daraja daya kika ci shine kina dauke da jikana a jikin ki da yau wlh baki kwana a gidan nan ba, mahmud yace dan Allah mama kiyi hakuri wlh ba laifin salm...... Dallah yimin shuru karka cemin komai ai dama ita bata laifi, kai da ita Kuna ta wulakanta min y'a toh wlh ka fita daka ido na, gwara ka dawo cikin hayyacinka wlh, tun kafin inyi mugun saba maka, kazo ka makale mata kun bar min y'a ko oho, duk ta rame sai zalintan ta kake wlh mahmud Zan saba maka indai kaci gaba da haka, ta fita fuuuu yabi bayanta yana bata hakuri kun San tsakanin d'a da uwa, tace babu komai fauziya tana nan ta labe tana jin abunda suke fada, tace ya jikin salma din? Yaji dadin tambayan da tayi cikin jin dadi yace da sauki, tace kar dai ka bari ta dinga abubuwa Mai wahala tunda baiyi kwari ba, yace toh mama na gode, ta wuce, Fauziya dake labe tace kambu wlh da sake wato itama tana son cikin dukanku zanyi maganin ku wlh, hjy binta bata dade da fita ba itama fauziya ta fita,
Mahmud a ranan salma tace ya kamata yaje office dan ya kwana biyu a gida, bai musa ba yace babu damuwa, yace baya son inya fita tace za tayi wani abu da kanta ta zauna kar baby dina ya samu matsala, tayi murmushi tace shikenan babu damuwa sai ka dawo, ya bata fake sannan ya fita,
Fauziya taje banki ta cire kudi, ta nufi wajan mlm yau ko biya ma mamanta ba tayi ba, ta wuce ita daya, bayan taje ta bashi kudin yace ta koma gida nan da sati daya cikin zai xube cikin murna ta wuce, ba tayi gida ba wajan mamanta tayi, ta sameta tana kallo, ganin fauziya din yasa ta Washe baki tace Tun daxu inata jiranki amma shuru, fauziya tace ai har naje ma daka can nake, tace kaji yar albarka, yanzu ya akayi tace yace nan da sati daya zai xube, hjy zaliha ta washe baki tace yauwa kinga inya xube kowa ya huta, ke naji ma har yanzu shuru ta tabe baki tare da fadin bari in wuce gida, ta fita.
Salma bayan mahmud ya fita, tayi dariya tare da fadin bari inje in daura mishi abinci tunda naji sauki inna biye mishi babu abunda zan dinga yi, gwara inyi in sami lada, tayi kitchen ta daura abinci, fauziya ta dawo taji kamshi na tashi kai tsaye tayi kitchen din tace munafuka dama kece, salma tayi banza da ita nan ta matsa kusa da ita takai mata duka a ciki nan ta fadi tana wash Allah innalillahi wa inna'ilahira jiun, ganin haka yasa tabar kitchen din tana fadin kadan kika gani,
Mahmud tunda ya fita yaji gaba daya hankalinshi bai kwanta ba, ya dawo gida Tun daka waje yake jin kauri da sauri ya shiga gidan, yaga hayaki a kitchen yana fitowa da sauri yayi kitchen din ya fara tari ya kashe gas din yaga salma a Kwance nan ya kuma rudewa ya dauketa yai waje da ita, driver ya shiga suka kama hanyar asibiti yana ta fadin yi sauri driver yana ta gudu, tazo zata tsallaka yayin dashi kuma ya kasa tsayar da motar ya bigeta, nan mahmud ya saki Salati, jini gaba daya jikinta, nan matar da suke tare ta saki ihu mahmud yazo yace ta shigo suje asibiti, dakyar ta yarda ta shiga sukai asibiti dukan su emergency akayi dasu, yayin da yarinyar ko numfashi ba tayi ita kuma salma gaba daya ta fita hayyacinta.
Maryam Obam😘
ðŸ’ðŸ’ðŸ’KISSA KO MAKIRCI👹👹👹
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
(Mrs nura kuriga)
70to75
Mahmud ya shiga cikin tashin hankali, har rama yayi na lokaci daya fuskan shi tayi fayau, hada kanshi yayi da bango yayin da zuciyarshi take bugawa, gefe daya kuma ga matar da suka bigema yarinya tana ta faman ihu sun kashe Mata y'a,yayin da driver kuma gaba daya komai nashi ya tsaya dan yana tsoran kar ace yarinyar ta rasu, gaba daya suna cikin tashin hankali, dukansu suna son suga Dr ya fito ya musu bayani,.
Fauziya tunda ta bige salma tayi d'aki take a tsorace yanxu idan wani abu ya sameta fa? Tace ni na aikata mata hakan nasan Mahmud bazai barni ba, nan ta fito tayi kitchen din amma babu salma babu dalilinta, kai tsaye dakinta tayi shima dai bata ciki, nan ta kuma tsorata tayi waje, tana tambayan security salma ta fita ne? Suka ce eh oga ya dauketa kaman a sume take nasan dai asibiti Suka tafi, nan tayi gida da sauri tare da fadin na shiga uku, nan tayi d'aki ta dauko key din mota tama rasa ina zata sai yawo take a titi, daka karshe ta yanke bari taje gidan hjy binta, nan ta nufa bayan tayi parking ta fito tana kuka, nan hjy binta ta fara tambaya lafiya kuwa Fauziya mai ya faru? Nan ta fara shargo mata karya salma ce tana ta nemana da kokawa naki kulata ganin haka shine tazo zata janyo ni shine ta zame ta sume, ni yanxu ina tsoran ta farfado ta kullamin sheri wajan Mahmud, tace ni na tureta, nan hjy binta ta kumbura tare da fadin wato tana bakin cikin wannan cikin koh tana so ya xube dama naga take takenta bason cikin take ba wlh, nasan magani tayi tasha dan karta dauka yanzu Allah ya kamata ya bata shine take son ta zubar min da jika toh wlh idan cikin nan ya zube wlh saina sa an daure min ita harda iyayenta kaji yarinyar banza mara mutunci, tashi muje asibitin.
Dr dai shuru har yanzu bai fito bah, Mahmud dai yana nan a tsaye tun dazu ya kasa zama, wani gefen kuma yana tunanin mai yasa salma taki Jin magana na nace kartayi komai amma taki ji, yanzu gashi taja ma kanta matsala wani hawaye ya xuba a idonshi ya furta a hankali salma ina sonki, I can't live without you, mai yasa kika ki jin magana na why salma??? Jin an taba shi yasa ya waigo hjy binta ce cikin bacin rai amma ganin tilon dan nata na hawaye yasa gaba daya jikinta yayi sanyi, tasa hannu ta share mai tare da kamo shi ta zaunar dashi lokaci daya yasa kanshi a kafadanta yana kuka kaman karamin yaro, nan hjy binta ta tsorata, Fauziya kuma babu abunda zuciyarta keyi sai bugu, hjy binta tace Mahmud mai ya sami salma din? Tace har yanzu Dr bai fito bah mama ina tsoran kar in rasa salma ina sonta, hjy binta tace haba Mahmud kaji ance ma zata mutu ne? Ka daina wannan maganan kaji, yace mama wlh a cikin wani yanayi muka zo asibitin nan, ina cikin tashin hankali, nan taita bashi baki tare da mishi nasiha, ita kuma babu abunda take sai Allah yasa kar cikin ya zube domin tana bala'in son cikin, matar dake gefe itama ta zabga tagumi tana jiran taji lafiyar yar tata,
Wasa2 sai da Dr yayi kusan awa biyu kafin ya fito, gaba daya Suka tashi badda Fauziya da tsoro ya dameta, Mahmud yace Dr ya jikinta? Dr yace muje office nan duka Suka bishi harda driver, bayan Dr ya zauna ya kalli Mahmud yace gaskiya you are very lucky, matarka na abubuwa wanda basu dace damai ciki ba, sai dana fada maka karta dinga yin abu mai wuya amma Ka barta tana yi, hjy binta ta katse shi da fadin yanzu maiya sami cikin? Yace cikin na nan, sai dai kuyi mata addu'a ta haiyu lafiya, hjy binta tayi ajiyar zuciya tare da furta alhamdulillah, Fauziya jin haka taji kaman ta shake hjy binta dan takaici dan taga yanda take wani zakewa akan cikin, Mahmud yace Dr yarinyar nan fah? Hjy binta Tace wace yarinyar nan ya bata labari Dr yace eh munyi iya kokarinmu sai kuyi addu'a domin har yanzu bata farka ba, nan matar nan ta saki kuka tare da fadin nashiga uku sun kasheta, hjy binta Tace haba baiwar Allah ki daina fadin haka miye amfanin kukan addu'a xaki mata, ta kalli Dr Tace zamu iya shiga yace eh, nan sukai emergency din, salma tana kwance amma idonta biyu tana kallon sealing, yayinda yarinyar ita kuma ansa mata oxygen, saman kanta ansa plaster da kafanta na hagu, alaman ciwo taji a wajan, Mahmud wajan salma ya nufa, ya kira sunanta a hankali tare da rike mata hannu, hawaye ya zuba a idonta, yace ya jikin? Ta amsa cikin sanyin murya dasauki, nan ta hango Fauziya da hjy binta gabanta ya fadi, hjy binta ta matso tare da fadin kinci sa'a cikin bai xube ba da wlh sai kinje freezing keda iyayenki Mahmud yace haba mama bakya ganin halinda take ciki, tace yimin shuru, kana nan tana maidaka wawa baka San abunda kake ba, taso ta zubar da cikin ne Allah ya nuna mata iyakar ta, nan salma ta saki kuka, tace kaji makira koh, ai baki kuka ba sai kinyi kuskure kin zubar da cikin nan sannan zaki kuka, tayi tsaki ta fita Fauziya ma tabi bayanta, nan Mahmud ya zauna yana ta bata hakuri tare da fada mata wata rana sai labari, ta kara hakuri akan duk abunda mama zata mata, tayi dan murmurshi tare da fadin nasha fada maka, komai mama tamin babu komai mahaifiyata ce, ta isa tamin komai, yayi murmurshi yace nagode salma Allah ya saka miki da alkairi, nan ya tashi yaje kan yarinyar nan yana dubata yana fadama salma abunda ya faru lokaci daya yayi shuru tare da kara kurama fuskan yarinyar ido yana tuna inda ya Santa, salma dake kwance gaba daya idonta na kanshi tana mmkin irin kallon da yake ma yarinyar gashi yana mata magana yayi shuru, lokaci daya yayi murmushi, ya dago kai sai a sannan ya tuna salma na wajan kuma yaga tana kallon shi.......
Maryam Obam😘
ðŸ’ðŸ’ðŸ’KISSA KO MAKIRCI👹👹👹
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
(Mrs nura kuriga)
75to80
Suka hada ido da salma yace salma nasan wannan yarinyar, tace a ina?? Yace tana yawan zuwa office dina kwanaki daka baya na daina ganinta, tunda na ganta naji kaman tana naiman taimako Amma Allah baisa na taba tsayawa naji mai take nema ba, salma tace Allah sarki komai ai sai Allah ya nufa, Allah ya bata lafiya sai kaji matsalanta inna taimakawa ne a taimaka mata, ya amsa da ameen, nan ya kira driver yace ya kwantar da hankalinshi insha Allah zata tashi babu abunda zai sameta, driver yayi ajiyan zuciya tare da fadin Allah yasa oga hankalina ya tashi sosai ban taba bige ko kaza ba amma na fara da buge mutum, Mahmud yace idan Allah yasa abu zai faru babu mai hanashi, dan haka kayi imani da hakan, yace hakane oga ngd, nan Mahmud ya zaro kudi ya bashi yace ya siyo musu abinci, ya amsa cikin ladabi ya fita,
Mahmud yana tare da salma har driver ya dawo yarinyar bata farka ba, Mahmud ya cire nasu da drinks, sannan yace ya dauka yaba ma matar nan itama, nan ya amsa da to ya fita, Mahmud ya bude fried rice ne, da kaza rabi a ciki, da garden salad, nan ya fara ba salma tana ci harta kochi, sannan shima ya samu yaci, bayan ya Gama ya kalleta yace salma ta amsa da na'am, yace mai yasa kika shiga kitchen bayan nace kar kiyi aikin komai? Tace kayi hakuri Mahmud bayan ka fita ne, nace bari inje inma abinci dan naji jikina da sauki kuma na gaji da zama waje daya, ina cikin aikin.... Tayi shuru yace inaji tace ban San maiya faru ba kuma sai dai na ganni a nan, shuru yayi yana kallonta kaman yana son gano wani abu, can yace salma dan Allah daka yau koda mun koma gida ban son ki kara yin wani abu da kanki, inaso kimin alkawari, Tayi shuru tana kallonshi, tace insha Allah bazan kara yiba, har sai na warke sosai, yace no koda kin warke bana son kiyi komai har sai kin haiyu, ban San matsala, tayi dariya tare da fadin shikenan koda yaushe ni mai bin umarninka ce, yayi murnushi tare taba mata hanci, jin motsin yarinyar nan yasa sukai saurin waigawa da sauri, Mahmud yayi wajanta da sauri ya danna wani abu ja, ko minti biyu ba'ayi ba saiga Dr ya shigo dasauri, nan ya fara dubata ganin numfashinta ya koma normal aka cire mata oxygen din, Dr yace mata ya jikin tace da sauki cikin sanyin murya, yace inane yake miki ciwo? Ta nuna mai kanta, yace kiyi hakuri a hankali zai daina, ya kalli Mahmud yace jikin da sauki sai dai ciwon da taji shine yake damunta, nan Mahmud ya godema Allah ganin ta tashi kuma ance jikin da sauki, Dr yasa a fitar dasu daka emergency asa su cikin wani daki, salma tace a kaisu na mutum biyu ita da yarinyar kar a raba su, hakan koh akayi, lokacin da aka fito dasu za'a kaisu dakin driver da mmn yarinyar suka taso a tsorace ganin yarinyar idonta bude tana dago hannu tana mika ma mmnta yasa driver yaji dadi tare dayi ma Allah godiya, tana rike da hannun mmn sukai dakin, nan mmn ta saki kuka tana fadin ya jikin naki? Ta amsa dasauki, tasa hannu tana share mata hawaye tare da fadin aina warke kin sha naki maganin? Ta amsa da eh nasha, salma taji sun bata tausayi, tace mama kiyi hakuri Dr yace babu komai dake damunta yanzu ciwon jikinta ne kawai, shima insha Allah zai warke da wuri, matar da waigo tana kallon salma tace Allah yasa hakan ita daya gareni sai yasa na shiga damuwa ina tsoran in rasa ta, sai a sannan Mahmud yayi magana yace insha Allah babu abunda zai sameta,
Kwanan su hudu aka sallame su, a dan kwanakin da sukayi salma ta fahimci matar kaman tana da wani ciwo, tana yawan shan magani, in bata shaba yarinyar zatai ta mata magana tasha, gashi bata San shiga cikin dakin wanda ako da yaushe zaka ganta a waje, sai anyi dakyar zata shigo ta rakube wajan gadon yarta, suna hada kaya salma tace mama yanzu dai sai kuxo muje gidan mu, idan kuka kimtsa sai a kaiku gida, nan matar tace a'a babu inda zasu sun gode, saida mahmud ya shigo ta fada mai sannan yayi mata magana shine ta yarda, driver ya dibi matar ya fara tafiya dasu sannan ya dawo ya kwashi su salma, dakin baki driver ya kaisu, koda su salma suka je gida fauxiya bata nan, nan Mahmud ya bada kudi a kawo musu abinci, ba'a dade ba driver ya kawo, ya bashi na matar yace ya kai mata sannan yayi sama dana hannunshi, ya tarar salma bata dakin ya daiji kanshi sabulu a nan ya gane tana toilet, ya xauna bai dade ba ta fito, ido ya kura mata yana kallonta, tayi murmushi tace wannan kallon fah, dariya yayi ya tashi ya kamo ta sannan ya xaunar da ita akan kujeran dake dakin, yace bana hanaki yin komai ba, tace mai nayi yanzu tare da xare ido, yace wa yace kije ki wanka da kanki? Tayi dariya mai sauti tare da fadin ai wannan ba aiki bane, yace to daka yau shima bana so kina yi, ni zan dinga miki, Ta kalleshe suka hada ido, tayi sauri tayi kasa da kanta tana dariya, nan ya tashi ya dauko ledan abincin ya bude sakwara ne da miyan egusi, yaji ganda da dry fish, ga wani kamshi dake tashi, dayan ledan kuma farfesun kayan ciki ne, kafin ya gama budewa harta dauki sakwaran Ta fara ci, dariya yayi tare da fadin babyna yasa bakya wasa da abinci itama dariyar tayi taci gaba daci, har Ta koshi sannan ta ajiye, yaje ya dibo mata ruwa a wani bowl ta wanke hannu, ta kalleshi tace yasu mama suma an kai musu? yace eh tace bari inje in duba su, yace a'a ki zauna ki huta anjima sai kije bata musa ba ta zauna nan ya xauna da ita yana ta bata kulawa har bacci ya dauketa, sannan ya fita.
Salma sai wajan 4 ta tashi, alwala tayi, sannan tayi sallah, kai tsaye dakin baki tayi taga kofar a bude ta shiga, taga matar da yarta, suna zaune akan kujera sunyi wanka sun sa kayan data basu, da fara'a tace sannunku suka amsa da yauwa nan salma ta tambayi yarinyar miye sunanki mmnki taki fadamin yarinyar tayi dariya tace ai bata fada, tace sunana salamatu, salma tayi dariya tace lah sunan mu daya, yarinyar tace to yanzu xaki sa mamana ta fara jin kunyan ki, salma taci dariya, salma ta kalli mmn da tayi shuru tana musu dariya, tace mama a wani anguwa kuke? Nan tayi shuru, yarinyar tace bamu da gida duk inda muka samu anan muke kwana, salma tace kaman ya? Mmn tace ke ban San surutu, yarinyar tayi shuru salma tayi dan murmushi tare da fadin mm yanzu dai saiku xauna a nan idan ta gama warware sai ku tafi bata musa ba tace babu komai, jin muryan Mahmud yasa ta tashi ta fita dan taji security na mishi sannu da zuwa, ta fito tana mishi murmushi da sauri ya karaso wajanta yayi hugging dinta sannan sukai ciki, a falo suka xauna nan take fada mishi abunda ya faru, shuru yayi na wani lokaci kafin yace inaga mu basu kudi su wuce, salma tace a'a ina so in san ko su waye su, ina son ka taimaka musu, yace salma idan na basu kudi aiya isa, no need ki san kosu su waye, tace dear plz wlh suna ban tausayi kar ka hanani in san labarin su, plz yace owk Allah ya taimaka, fauxiya ta shigo falon babu sallama sai sakin tsakin da tayi tare da fadin mayya, kwadayi dai mabudin wahala, Mahmud cikin fushi yace ke wace irin mara tunani ce, tace eh bani dashi sai waccan yar iskan data dauko cikin wani tace naka ne,yace keee fauxiya kije na sakeki saki daya kuma ki jira takardan kotu akan shegenta min d'a, tace wlh ba........ Kafin ta karasa magana suka ji muryan hjy binta tana fadin dakyau ya waiga cikin tsoro.......
0 comments:
Post a Comment