Rayyan ya ba shi amsa da "Eh".
"Ok ku mu je ku kai Ni". Yafaɗa yana miƙe wa tsaye da hanzari
Tare suka fice suka shiga motar Suhaib, Rayyan ne ya ja su zuwa asibitin.
Suna isa ɗakin da aka kwantar da RAUDHA, Daddy yayi saurin ƙarisawa wajen ta, zama yayi ya ɗaura tafukan hannayen sa biyu saman fuskar ta yana shafa wa, ji yake yi tamkar yayi ta kurma kuka sabida tsananin tausayin ɗiyar sa. Wai yau RAUDHA ce kwance cikin wani hali na taɓin hankali, duk a sabida sakacin su
Lumshe idanu yayi yana sake sauke wa akan kyakkyawar fuskar ta, wanda ya rame sosai, sai haske da ta sake yi, barci take yi har yanzu sabida alluran barcin da aka yi mata. Ahankali Daddy ya saka hannun sa ya ɗauke hawayen da ya silalo masa a kuncin sa, sannan ya juyo yana kallon su yace, "ina ne Office ɗin doctorn dake duba ta?"
"Daddy bari in Kai ka". Rayyan yayi saurin faɗar haka
Gyaɗa kai kawai yayi yabi bayan sa
Shi kuma Suhaib ya koma kusa da ita ya zauna a gefen gadon, ya riƙe hannun ta ɗaya wanda akayi mata ƙarin ruwa aka cire.
Wajen mintuna ashirin da fitan su Daddy kafin suka dawo, dayake magriba tayi, sai suka wuce gaba ɗaya masallaci, har bayan sallan isha'i suna nan a asibitin, har sannan kuma RAUDHA bata farka ba, dole suka taho gida suka bar ta cikin kulawar likitoci, tunda dama asibitin ba kasafai suke barin mutane suna kwana da mara lafiya ba. Daddy ya so ya kwana amma sai su Rayyan suka taushe shi akan ya koma gida, tunda shima yana buƙatar hutu a wannan lokacin
Sai da suka mayar dashi gidan sa, kafin suka wuce su ma, da zummar gobe Suhaib zai kawo mishi Haneep da Farida, sai su gaisa tunda yau basu samu sun haɗu ba.
A taƙaice ranan Daddy be iya runtsa wa ba, kwana yayi a zaune yana nema wa ƴar sa samun lafiya daga wurin mahaliccin mu.
Washe gari tare suka taho da Farida gidan Daddy ɗin, anan suka gaisa, Daddy ya amshi Haneep yana ta faman mishi wasa, sosai soyayyar yaron ya shiga ransa, kuma ya tausaya mishi da rashin lafiyan da yake yi, yayi masa addu'a sosai kafin ya miƙa ma Farida shi, sannan suka fito suka nufi asibitin, daga can Rayyan ya wuce wurin aikin sa.
Wajen awanni biyu da zuwan su, sannan ne RAUDHA ta farka, amma kuma gaba ɗaya ta rikita su da koke-koken ta, kuka take yi sosai tana surutu kamar zautacciya, ba ma ta gane wanda ke kanta
Sosai tashin hankali ya sake bayyana a wajen Daddy da Suhaib, sun rasa ya zasu yi, har kuka sai da Suhaib yayi, shi kuma Daddy sai faman sharan ƙwalla yake yi, musamman da ya riƙo ta yana faɗin, "shi ne Daddyn ta, tayi shiru". Yana rarrashin ta
Sai tahau zagin sa, daga ƙarshe ta soma ɓaɓɓaka masa dariya tana tokarin sa da ƙafa, wai sai ya sake ta ta hau saman silling
Da gudu Suhaib ya fice yana sharan hawaye
Itama Farida dake riƙe da Haneep ta zauna a gefe tana kallon RAUDHA dake jikin Daddy, bata san sanda hawaye yayi ta kwarara a saman fuskar ta ba, sabida tsantsan tausayi
Hauka tuburan RAUDHA take yi, an rasa yanda za'a yi da ita, tunda tuni Suhaib ya kira likitoci sun duƙufa akanta
Ƙiri-ƙiri Daddy ya ƙi fita a ɗakin koda suka buƙaci su ba su wuri
Yanda suka ga hankalin Daddy yayi ƙololuwar tashi, dole suka tausaya mishi suka bar shi a cikin ɗakin, haka suke iya yin su wajen taimaka wa RAUDHA, sai da suka yi mata alluran barci sannan suka samu lafiya, amma ta karaɗe ɗakin da waje da ihun ta
Daddy kasa jure wa yayi ya faɗi ƙasa a sume, ai nan hankalin su Suhaib ya sake tashi da jin abinda ke faruwa
A wani ɗakin aka kai Daddy aka soma ba shi taimakon gaggawa, sosai jinin sa ya hau, ga shi yana buƙatar hutu, dole suka yi masa alluran barci don ya samu ya huta ko jinin sa zai sauka
Abun tausayi idan ku ka ga Suhaib, ya hana kansa sukuni duk ya tsangwami kan sa, shima ba don jarumta da ƙarfin hali ba; da tuni ya zube, sai Farida da ke ƙarfafa masa gwiwa tana masa nasiha akan ɗaukan ƙaddara. tabbas haka Allah ya so ƙaddaran RAUDHA ce, dole wannan ciwon sai ya same ta, sai dai su yi wa Allah godiya tare da roƙon Allah ya taƙaita abun haka.
Wajen awanni uku Daddy yayi a kwance, sannan ya farka. duk yanda likitoci suka so ya zauna ya sake huta wa a ɗaura masa drip amma yaƙi, nan ya soma buga waya ya hau yi mata cuku-cukun yanda za'a yi a fita da ita Abroad, sai dai basu samu ba, tunda ko wani ƙasa ance a dakata da zuwa, shi kansa Nigeria an rufe, dole Daddy ya bar ta anan asibitin, sai dai ya samu an yi masa hanyar likitoci ƙwararru waɗanda za su iya kula da RAUDHA
Abun ka da ma su kuɗi, a washe gari sai ga likitocin sun iso, nan aka duƙufa wajen duba RAUDHA, sosai take samun kulawa wajen likitoci, sai dai kamar ma ƙara haukan take yi, domin ciwon ci gaba yake ba baya ba, ta kai yanzu ɗaure ta ake yi a jikin ƙarfen gadon, sabida idan ta tashi daga alluran barcin da ake mata, ta rinƙa hauka kenan tana fashe-fashen kayan ɗaki, ko kuma tayi yinƙurin guduwa dole sai an kamo ta, har kayan jikin ta take yagawa, sai dai a sauya mata wani.
Bazan iya misalta muku halin da bayin Allan nan suke ciki ba, har wani rama suka yi sabida tashin hankali, babu abinda su Daddy da Suhaib suke yi sai dana-sani, dana-sanin barin RAUDHA cikin shaye-shaye, ga shi yanzu ta haukace suna ji suna gani, kuma kuɗin su be iya ba ta lafiya ba, babu yanda za su yi yanzu sai bin ta da addu'ar samun lafiya, wuni kuwa cikin yin ta suke yi, duk idan suka zo asibitin nan sai sun zubar da hawaye
Gefe ɗaya ma Rayyan duk ya shiga matsanancin damuwa sosai, duk a sabida ciwon RAUDHA, sosai yake matuƙar ƙaunar ta, ko barci ba ya iya yi sabida tunanin ta, da shi ake yin duk wani zirga-zirga na neman maganin ta, ya kasa hankalin sa gida biyu, a hankali shima a tsaye yake rame wa duk a sabida damuwar da ya ɗaura wa kansa.
Yanzu haka dole aka mayar da RAUDHA asibitin mahaukata tunda abun yafi ƙarfin asibitin, an ware mata ɗaki daban a matsayin ta na ƴar gata, sai dai su Daddy su je can su riƙa duba ta, su kansu likitocin ma su kula da ita daban ne aka ajiye mata.
Wasa-wasa sai ga RAUDHA ta shafe watanni huɗu a asibitin mahaukata, tana fama da mugun ciwon da ba ya baya sai dai gaba, kullum-kullum gaba ciwon nata yake yi ba baya ba, duk wani magani an yi mata amma har yanzu ba'a dace ba, ba'a taɓa samun ranan da aka wayi gari an samu nasarar ci gaba wajen samun lafiyan ta ba, sai dai gaba abun yake yi, da sarƙa ake ɗaure ta, abun mamaki kuma sai da safe a zo aganta a kwance. likitan da ke duba ta sosai yake mamaki idan ya zo ya ganta a kwance tana zaune tayi ta ɓaɓɓaka masa dariya.
Yau ma kamar kullum a kwance ya ganta, sai dai kuma abun mamaki a saman cilling ya hange ta tana ta kwasan dariyan dake fita tamkar na mutane goma, ga shi ɗakin yayi duhu sosai sai uban sanyi tamkar ƙanƙara
Da sauri likitan ya kunna wutan ɗakin yana me mamakin "ta ya ɗakin zai yi duhu bayan yanzu yamma ne ba dare ba?"
Can ya hange ta a sama tana yawo tana wannan dariyan me ban tsoro. Da sauri ya bar ɗakin don kiran sauran ƴan uwan sa
A time ɗin ne Daddy da Suhaib suka zo duba ta
Nan likitan yayi kiciɓis da su, sai ya miƙa musu hannu suka gaisa sannan ya kai su office ɗin sa ya ajiye su, sai ya fita ya bar su suka koma tare da wasu Doctors ɗakin da RAUDHA take ciki
Har a time ɗin tana saman tana shawagi tana wannan mahaukacin dariyan da yake karkasuwa da yawa, suna shigowa ta kallo su da idanuwan ta masu tsananin haske tamkar an ƙara musu haske, har wani walwali suke yi kamar an kunna tocila
Sosai likitocin suka tsorata da wannan al'ajabin, har za su koma sai ɗayan ya dakatar da su
Kamar ƙiftawar ido sai ganin ta suka yi ta koma ƙasa a yashe, gashin kanta ya rufe mata fuska duk ya barbaje
Shi babban likitan shi ya ƙarisa gaban ta ya yaye mata gashin kanta, sai dai da alamun ba ta numfashi, duk inda yakamata ya taɓa don jin tana numfashi amma alamu sun nuna ta sume ne, dama ta saba haka, sai tayi wajen kwana biyar tana barci, ko kuma ta dena numfashi gaba ɗaya, hakan na basu mamaki, amma basu alaƙanta hakan da komi ba, tunda gashi result ɗin su na nuna musu ƙwaƙwalwan ta ta samu matsala sakamakon ƙwayoyin da take sha, kuma koda yaushe suna mata gwaje-gwaje amma abu ɗaya suke gani, duk maganin da zasu ba ta still dai babu ci gaba.
Sake ɗaure ta suka yi da sarƙan, kafin suka soma aiki akanta, bayan sun gama suka fito daga ɗakin, likitan ya nufi Office ɗin sa da su Daddy ke ciki, yana shiga ya sake ba su haƙuri da zaman jiran sa da suka yi, sai da suka sake gaisawa sannan ya soma musu bayani, kamar dai ko yaushe babu wani ci gaba da ake samu
Gaba ɗaya ransu duk a matuƙar damuwa suke sauraron likitan, kullum abu ɗaya yake faɗa musu, duk kuma hanyan da zai kawo yace a gwada, idan an gwada ɗin abu ɗaya ne babu sauƙi, gashi kuma babu yanda za'a yi a fitar da ita wani ƙasan, nan kuma asibitin yana ɗaya daga cikin asibitin da yafi ko wanne ƙwararrun likitoci na masu hauka, da ba don haka ba da tuni sun sauya mata wani wajen, su yanzu har sun fawwala wa Allah komi, sabida kullum babu ci gaba
Ajiyan zuciya likitan ya sauke yana kallon su, sai da ya ɗan ja fasali kafin yace, "sai dai Ni akwai shawaran da nake so in baku idan babu damuwa".
"Menene likita? Ka faɗa ko wani shawara ne idan har hakan zai kawo samun lafiyan ɗiya ta, muna maraba dashi". Cewar Daddy da tsantsan damuwa a maganar sa
"Eh to Ni dai a haƙiƙanin hange na da nayi, ciwon ɗiyar ka ba na asibiti bane gaskiya, duba da yanda kuke ta wahala da ita, mu ma kuma muna yi wajen treating ɗin ta, amma kuma har yanzu babu ci gaba, sai kuma abinda ke ɗaure min kai a tattare da ita, musamman idan na je inda take, hakan yasa nayi tunanin tabbas ciwon ta akwai yiwuwar shafan aljanu a tattare da ita, ba wai zan ƙaryata cewa ƙwaƙwalwan ta be taɓu bane a sabili da shaye-shayen da take yi, tabbas hakane, sai dai kuma idan har akwai aljanu a jikinta, to, tabbas babu ta yanda za'a yi maganin da muke mata ya warkar da ita, duba da yanda aljanu suna irin hakan a jikin Mutum, zasu lafe su hana tasirin duk wani magani a jikin ta, haka za'a yi ta wahala da ita a kasa gane meke damun ta, ya kamata a gwada na Islamic tunda an kasa dacewa anan ɗin".
Daga Suhaib har Daddy zuba ma doctor idanu suka yi suna sauraren sa, har sanda ya dire bayanin sa babu wanda yayi yunƙurin magana, gaba ɗayan su sun tafi ga tunanin abinda ya sa tun farko ba su yi wannan tunanin ba.
[3/19, 10:08 AM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Isma'il Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON THIRTY SEVEN*
_______📖 Sun daɗe a wajen likitan yana musu bayani, har yayi musu hanyar wani babban Malami dake garin Zaria, kuma sun amince zasu gwada ɗin ko Allah zai sa a dace.
Sai da suka duba RAUDHA kafin suka bar asibitin.
A cikin kwana biyu har an gama shirye-shiryen yanda zasu tafi da RAUDHA zuwa Zaria, tunda an rigada an sanar wa malamin kuma ya ce a kawo ta, gaba ɗayan su zasu yi tafiyan har Farida, tunda dama gida ne zasu koma shiyasa zasu tafi gaba ɗaya
Rayyan ya so ya bi su, sai dai yanayin aikin sa bazai bar sa ba, dole ya haƙura ba don ya so ba.
A jirgi suka isa Zaria, gidan Daddy suka sauka inda anan ne Malamin zai zo ya riƙa duba ta, bisa alfarman da Daddy ya nema a wajen sa, (Chemist) cibiya ce babba suke da shi a Zarian, wanda aikin su ne cire ma mutane aljanu
A ranan da suka zo, a ranan ne Malamin da zai duba ta shima ya iso gidan, a time ɗin RAUDHA na barci ne sabida alluran barcin da aka yi mata daga can asibiti, saboda samun sauƙin tahowa da ita
A tare da Daddy da Suhaib suka raka sa ɗakin da aka ajiye RAUDHA, sai da ya nemi abubuwan da yake buƙata wajen su, sannan ya zauna ya saka mata magani a cikin kasko, ta yanda idan har tana da aljanu dole zasu bayyana kansu idan turaren ya shiga hancin ta
Ilai kuwa, ana saka wa sai ta farka a firgice, gaba ɗaya zubo musu idanu tayi tana kallon su tamkar zata cinye su, sabida yanda ta waro idon nata waje, sai yamutsa fuska take yi tana cije baki
Malamin ta kafa ma idanu, wanda shima ita yake kallo, nan da nan idanun ta suka soma sauya kala zuwa ja, sai ta kawar da kai ta koma ta kwanta batare da ta sake ko motsi ba
Su dai su Daddy suna zaune akan sofa suna kallon ta, ko wannen su ya buga tagumi
Ajiyan zuciya Malamin yayi kafin ya kalli su Daddy yace, "tabbas yarinyan ka tana da aljanu a jikin ta, da alamu dai manya ne, saboda duk wanda na saka mishi maganin nan, dole ne su tashi a lokaci ɗaya su bayyana kansu, amma kuma ita ba haka ba, sai dai ta yanda ta farka ɗin nan, da kuma yanda idanuwan ta suka sauya kala, to, tabbas tana tare da su. Insha Allahu zamu fara aikin mu nan ba da jima wa ba idan abokan aikina sun zo, zamu fara mata ruƙiya ne su fara bayyana kansu, sannan mu san abun yi".
Suhaib da Daddy jinjina kai suka yi alamun gamsuwa.
Suna nan zaune Sai ga wasu Maza su kusan biyar sun shigo ɗakin
Malamin kallon su yayi yace, "su zauna su soma karatun".
Gaba ɗaya zama suka yi suka zagaye RAUDHA da har yanzu tana kwance idanu a rufe taƙi motsawa
Karatu suka soma yi da ƙarfin muryan su. sun daɗe suna karatun amma RAUDHA bata yi wani motsi ba, su kuma basu fasa karatun ba, sai da suka ɗau kusan mintuna talatin suna karatu kafin ta soma wani irin gurnani har yanzu idanun ta a rufe, hakan yasa suka sake dage wa suna sake ɗaga murya, nan da nan ta soma ihu tamkar wani ƙaton gardi, kukan yana fita ne kashi-kashi wanda baza ka gane na mutane nawa bane, kukan kawai take yi bata motsa ba, kuma idanuwan ta a rufe
Sai malamin ya tashi ya matso kusa da kanta, ya soma yin wasu addu'o'i yana tofa mata akai, yayinda sauran mutanen suka ci gaba da karatun Alqur'ani da iyakan ƙarfin su, idan suka zo wasu ayoyi na jinnu sai suna maimaita wa kafin su wuce
Addu'o'in da Malamin ke tofa mata, shi yasa ta buɗe idanunta da suka sake matuƙar girma tamkar ba nata ba, sun sauya kala zuwa kore, jajja-jajja, sai kawai ta soma ɓaɓɓaka dariya nan da nan ta tashi tayi sama tana shawagi, take ta tsaga wani uban ihu da ya razana su gaba ɗaya, ba su kaɗai ba gaba ɗaya gidan sai da ya amsa sabida ƙarar ihun nata. Babu shiri Daddy da Suhaib suka miƙe tsaye suna zazzare idanu sabida tsoron da ya shige su, ai nan suka soma addu'a jikin su na rawa, ga shi babu daman fita sabida Malamin sai da ya saka aka kulle ɗakin
Malamin kallon abokan aikin sa yayi, yayi musu nuni su ci gaba da karatun, yayinda shima ya ci gaba da karanto addu'o'i waɗanda zasu saka su bayyana kan su
Kuka ta soma yi sosai a wannan lokacin, sai dai babu hawaye amma gaba ɗaya idanun nata sun sauya kala, ko ɗigon fari ba'a gani, sai shawagi take yi a saman tana wani irin tururi tamkar ana dafa ta, hayaƙi sai fito wa yake yi a jikin ta
Karatun su ke yi, ita kuma tana ƙara yawan ihun nata, gaba ɗaya ta cika ɗakin da kuka ko karatun nasu ba'a ji.
Malamin sosai ya gane aljanun masu taurin kai ne akanta, sabida duk yanda suka yi karatun, sun ƙi yin magana sai kukan da suke yi, daga ƙarshe ma sai taci gaba da ɓaɓɓaka dariya, idan ta gaji kuma sai ta koma kuka, sun shafe wajen awa biyu ana abu ɗaya, sai daga baya da suka ji ayoyi na ƙona su, sun ji azaba na ratsa su sosai wanda baza su iya jure wa ba, sai ta faɗo ƙasa da ƙarfi ta kurma uban ihu, cikin ƙaton murya na gardi take cewa, "ku dena ƙona mu, ku dena ƙona mu, ku dena ƙona mu". Abinda take ta ambata kenan, har muryan ma ta koma tana faɗa ahankali sabida tsaban wahala
Gashi sun ƙi dena karatun
Sai ta koma kuka da hawayen ta tana roƙon su sosai
Nan malamin ya ba su daman dakata wa, sannan ya soma tambayan su "su wanene akan ta?"
Amma sai taƙi yin magana ta kafa wa Malamin idanu, idanun ta na zubar da hawaye
"Baza ku yi magana bane?" Cewar Malamin yana kallon ta shi ma
Sai ta ɓarke da dariya me fita muryoyi da yawa, nan ta miƙe da gudu tayi bakin ƙofa ta soma jijjiga ƙofan, kankace me ta kusa cire ƙofan, domin har ya ɓanɓaro tana shirin cire shi, nan suka yi kanta suna riƙe ta, tana bizgewa tana ihu, duk ta gama bibbige su
Su Daddy babu inda jikin su ba ya rawa, yau sun ga tashin hankali.
Daƙyar suka riƙe ta suka dawo da ita cikin ɗakin, haka suka soma kici-kicin kwantar da ita don su danne ta, amma sun kasa, sai ta fara zagin su tana musu gargaɗin "idan basu sake ta ba, sai ta halaka su"
Malamin ganin dai tana son fin ƙarfin su, sai ya ɗauki waya yayi kiran wasu daga cikin malaman su, sannan ya kalli Daddy yace, "idan da hali ku ƙaro mana mutane, sabida tana ƙoƙarin guduwa ne, kuma tabbas idan har ta fice a ɗakin nan da akwai matsala".
Jikin Daddy na rawa, ya umarci Suhaib ya kira masu aikin gidan maza su shigo
Dasauri ya fita ya kira su, sai ga su kusan su shida sun shigo
Nan Malam ya saka su duk suka taru wajen kwantar da RAUDHA, amma sun gagara, gaba ɗayan su sun kai su goma sha biyu kenan, amma sun gagara kwantar da RAUDHA ƙasa, ihu kawai take yi tana fizge-fizge, duk wanda ta samu ta mazge shi
Karatu suka ci gaba da yi suna danne ta tana kuka da ihu. Ba su yi nasaran kwantar da ita ba sai da wasu daga cikin malaman suka shigo, kusan su huɗu ne, Malamai ne su ma masu cire aljanu, tare suka dage daƙyar suka danne ta a ƙasa, suka hau karatu babu ji babu gani, sosai suka wahalar da ita, kukan ma wani irin kuka take yi tamkar na mage, gaba ɗaya tayi yaushi sai fitar da huci take yi, amma tsabar taurin kai taƙi magana.
Wani magani malamin ya samu ya fesa mata, take ta sandare tamkar ranta ya fita, sai kuma ta fashe da sabon kuka tana buɗe idanuwan ta daƙyar, ta hau roƙon sa wai "za su fita".
"Ƙarya kuke yi mugaye azzalumai, uban me tayi muku da kuka shiga jikin ta, ku ka wahalar da ita har haka, tsawon lokaci kun haukatar da ita, shin ku wasu irin mugaye ne, na ce uban me tayi muku ne?" Yaƙarike maganar cikin tsawa
Cikin kuka tana nishi tace, "wlh babu abinda tayi mana, kawai muna son ta ne, tayi mana ne shine yasa muka shige ta".
"Tayi muku? Dama akwai wani abun da ya haɗa jinsin mutum dana aljanu ne?"
Tari ta soma yi babu ƙaƙƙauta wa, gaba ɗaya idanuwan ta sun gama juye wa, sun ƙara tsananin ja har babu kyan gani
"Shin zaku sanar damu ne meyasaka kuka shige ta? Ko kuwa sai mun ci gaba da gana muku azaba?".
Shiru tayi taci gaba da tarin ta, yi take yi babu ƙaƙƙauta wa
Malamin kaɗa kansa yayi, kafin ya kalli sauran ya ce, "ku ci gaba".
Nan da nan suka ci gaba da karatun Alqur'ani, shima yana ci gaba da addu'o'i
Atake anan taci gaba da kuka tana shirin bige su ta gudu, haka suka danne ta sosai suka hana ta tashi, kuka take yi sosai tana ihu, har da su majinu, ta jigata iya jigata sai ta hau zagin su tana faɗin, "wlh idan basu sake ta ba, sai ta kashe su". Amma ko sauraron ta basu yi ba. Sun shafe tsawon lokuta suna karatun, kafin ta soma ba su haƙuri akan zata yi magana, amma malamin ya hana su dakata wa, sai da ta sha baƙar wahala ta sake yin yaushi sosai, ta yanda duk wani taurin kanta sai da suka yi maganin shi, kafin malamin ya saurare ta ya ce, "to ina ji zaku faɗa dalilin da yasa kuka shiga jikin ta ne ko kuwa sai na ƙona ku gaba ɗaya na kashe ku? Shin ku nawa ne ma ajikin nata?"
Cike da tarin wahala cikin wani irin babban murya tace, "muna da yawa a jikin ta, kuma Ni ne mijin ta, Ni na fara shiga jikin ta, sannan sai na jawo ƴan uwana su ma suka shiga jikin ta".
Jinjina kansa Malamin yayi kafin ya ce, "har ma ka zama mijin ta kenan, sannan saboda tsaban mugunta sai ka jawo ƴan uwanka suka shiga jikinta don ku cutar da ita ko?"
Girgiza kai ta soma yi tana hawaye, sai tayi shiru taƙi magana
"Ina jin ka zaku yi magana ne ko sai na ƙona ku?"
"Zamu yi Malam, zamu yi". Tafaɗa cikin mawuyacin hali tana juya idanuwa
"Kar ku sume mana anan, ina sauraron ka yi magana".
Shiru tayi tana rufe idanuwan ta tamkar ba ta numfashi
Malam ya sake watsa mata wani farin magani
Sai ta buɗe idanunta, sun koma fari a yanzu ɗin tamkar nata, cikin siririyan muryan ta da ya gama dishewa tace, "Daddy". Idanun ta akansa
Ai da sauri Daddy ya nufo wajen shima yana kiran sunan ta
Malamin ya dakatar da shi yana faɗin, "ba ita ba ce, suna son Raina mana hankali ne, ku muci gaba da karatun".
Karatun suka ci gaba da yi, sai ta soma kuka, sai da taji azaba kafin ta ce, "kuyi haƙuri don Allah, wlh baza mu ƙara muku taurin kai ba, duk zan faɗa maka abinda ya sa muka shiga jikin ta".
"To ina sauraron ku".
"Tun farko abinda ya fara jan hankali na akanta sabida ba ta ibada, sannan tana shigan banza, tana barin kanta a buɗe, shine yasa na kamu da sonta, kuma na shiga jikin ta, sai na jawo ƴan uwana muka shiga, sannan sai suka ɗaura mana aure dani da ita".
"Shin kai Musulmi ne ko kafiri?" Malamin ya sake tambayar sa
"Ni ba kafiri bane, amma ba mu Sallah, kuma tunda muka shiga jikin ta mu ke hana ta yin Sallah, tunda dama ba ta yi sai ta ga dama, wannan dalilin ne muka sake mayar da ita me wasa da Sallah, daga ƙarshe muka rinjaye ta muka hana ta Sallah".
"To tun yaushe kuke jikin ta?"
"Mun daɗe sosai, tun tana ƙarama".
Malam ya ce, "kenan duk ku kuke saka ta shaye-shaye har kuka samu damar haukata ta ko?"
"Wlh ba mu bane, amma dai mun san mun ba ta gudunmuwa, ko tana son bari sai mu hana ta, mu riƙa saka ta tana son sha koda yaushe".
"To yanzu meyasaka ka aure ta bayan kasan babu aure a tsakanin mu da ku?"
"Ai na ce maka ina son ta ne, tayi min ne".
Malam ya ce, "to yanzu zaku fita ne ko kuwa kun samu wurin zama ne baku da ninya?"
Shiru tayi tana ci gaba da hawaye
"Ina magana kuna ji na, muna son ku fita a jikin ta, ku bar ta ta huta tunda kun rigada kun azabtar da ita".
"Malam wlh ina ƙaunar ta, ita matata ce".
"To shine yanzu na ce ka sake ta ku fita a jikin ta, tun kafin in azabtar da ku".
Shiru tayi taƙi yin magana.
.
_To ya za'a kaya, shin za su bar ta ko kuwa?_
[3/19, 1:25 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Isma'il Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*HIKIMAR FARILTA SALLAH*
_An farilta sallah domin a cikin ta akwai godiya ga Mani'imcin sarki jalla Ta'ala, wanda yake shi ne macancancin godiya da yabo, kuma shi ne kaɗai muka keɓe shi da ruku'u da sujada. Ba wani mahaluki da ya dace da wannan. Idan wata masifa ta sami mutum yakan yi maza ya fake da Allah ta yin Sallah, kamar dai yadda Allah yayi umurni a cikin suratul Baƙara, aya ta 45 da cewa:_
_"Kuma ku nemi taimako da yin haƙuri, da Sallah"._
_Ganawar da bawa yake yi da Ubangijin sa a cikin Sallah ita ce bauta wadda take ƙarfafa zumunta tsakanin bawan da Ubangijin nasa. Ubangiji kuma yana yi wa bawan baiwar darajar samun kusanta da shi. Hikima ce kammalalliya da aka farilta sallah, don kuwa ta yin Sallah ne ake kankare wa bawa zunubai, muddin dai ya yi sallah yadda ake so._
_An ruwaito cewa annabawan da suka wuce, ko wannen su yana da Sallah da yake ibada da ita. Sallolin suna da lokatai biyar; asuba, azahar, la'asar, lokacin faɗuwar rana da na isha'i. Ashe za mu lura cewa Allah ya tara wa Annabi da al'umma tasa sallolin dukan annabawan da suka gabata._
_Allah ya sa mu dace._
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON THIRTY EIGHT*
_______📖 Daƙyar Malamin ya samu Sa'a suka amsa za su fita, shima sai da ya gama gana musu azaba sosai sannan ne suka ce za su fita, ta hanci suka fice, sai faman atishawa take yi, daga baya kuma ta hau barci babu ji babu gani
Malamin sallaman mutanen yayi, sannan ya soma magana da su Daddy daga shi sai su, anan ya soma ba su shawara akan yanda za su kula da tarbiyyan ta, sabida ya kula kaso saba'in cikin ɗari duk laifin su ne, inda ba ta shigan banza da duk hakan bata faru ba, ita ta soma janyo hankalin su gare ta, kuma ga shi daga ƙarshe ita tasha wahala. Sosai yayi musu nasiha tare da shawarwari, sannan kuma ya ce za su riƙa zuwa ana amsar mata magani don ba zama za'a yi, ko wani lokaci za su iya dawowa idan har ba'a ci gaba da nema mata magani ba, don ya kula taurin kai ne da su, ya san ba su yi nisa ba, tun daga nan ya fara ba su magunguna da za tayi sirace da shi, sannan ya ce musu "idan sun ga ta tashi hankalin ta be da wo ba, dole za su mayar da ita asibiti saboda aci gaba dana asibiti, tunda dama ƙwayoyin da tasha sun birkita mata ƙwaƙwalwa, dalilin aljanun ne har yanzu ana magani babu ci gaba
Sosai suka yi wa Malamin godiya, har waje Daddy ya raka sa tare da ɗumbin alkhairai da ba ya faɗuwa.
Suhaib na ɗakin da RAUDHA take kwance ya tasa ta gaba yana ta kallo, har Daddy ya dawo shima ya zauna kusa da shi, tsawon lokaci suna ahaka idanuwan su akanta, kafin Daddy yaja numfashi yace, "tabbas mun aikata babban kuskure tun farko, ga shi son zuciya ya saka mun yi wasa da tarbiyyan ta, soyayya ya rufe mana idanu daga Ni har kai mun kasa wa Baby tarbiyya irin ta addinin musulunci, duka laifin mu ne, kuma insha Allahu daga yau za mu gyara, Allah mun gode maka da ka taƙaita abun haka".
"Gaskiya ne Daddy, laifin mu ne gaba ɗaya, sabida son da muke ma Sweetheart yasa ba ma hana ta, shiyasa ta tashi bata san bari ba, duk abinda take so shi take yi, ga shi abinda ya faru daga ƙarshe, Allah ka yafe mana". Suhaib yafaɗa yana share hawayen sa
Daddy hannu ya saka yana buga bayan sa tare da ba shi baki. Sun jima a ɗakin ba su tashi ba, har sai da aka kira sallah tukunna suka fito suka tafi masallaci, bayan sun saka su Saude su zauna a ɗakin da RAUDHA take ɗin.
Bayan sun dawo ne ta farka, sai dai yanda take yi ne suka gane da akwai matsala har yanzu, dole suka ɗauke ta suka yi da ita asibiti, anan aka sake duba wa aka gane har yanzu tana da matsala a ƙwaƙwalwan ta, amma kuma ba wani sosai bane, don ba sai an dangana dana asibitin mahaukata ba
Duk wani abinda Yakamata an yi mata, daga ƙarshe aka ba ta gado har zuwa sanda za ta warke.
Haka rayuwa taci gaba da gudana, inda RAUDHA tana kwance a asibiti tana amsar magani, kuma ana kan mata na Islamic, da sannu-sannu suka soma ganin sauyi a gare ta, tunda har tana iya gane su tana banbance su, sai dai magana ne ba ta yi sai dariya, to an dai ci gaba da yin mata magani har zuwa sanda ta shafe tsawon watanni biyu a Hospital ɗin, kafin ta samu lafiya.
Su Daddy sun yi murna matuƙa sai godiyar Allah suke yi
A zaman ta a Hospital ɗin, zuwan Captain Rayyan sau uku yana duba ta, shima don babu time ne aiki na hana sa zuwa sosai, amma da Suhaib ya kira sa ya sanar masa samuwar lafiyan ta har za'a sallame su, ya ji daɗi sosai, sai dai babu damar zuwa ya duba ta, haka yayi mata fatar alheri suka rabu.
Koda suka koma gida an dai ci gaba da yin mata magunguna don ba'a zauna haka nan ba, tun ba ta saba wa har ta saba, ita da kanta take yin kayan ta, irin su sirace, shafa magani a jiki, shan zuma, shan wannan da wannan duk ta saba
Sosai RAUDHA ta sauya gaba ɗaya tamkar ba ita ba, duk da dama ba ta da hayaniya sosai, amma yanzu ta sake zama so silent, wuni tana maƙale jikin Daddy ko jikin Suhaib, haka za su zauna su yi ta mata hira ita kuma tana murmushi, har su gama hiran na su, daƙyar take iya yin magana sau ɗaya ko sau biyu
Kayan sakawan ta, gaba ɗaya Daddy ya saka an kwashe, an sauya mata da sababbi, dogayen riguna duk aka siyo mata, sai kuma irin Pakistan ɗin nan riga da wando, tunda dama bata iya shigan Hausawa ba shiyasa ma be haɗo mata da atamfofi ba, amma ƴan kanti da Arabian gown duk su aka siyo mata.
Itama Ramcy sosai take zuwa duba ta, tunda ta ji labarin dawowar ta, har waya suna yi yanzu
Farida ce me kula da ita sosai, sai da ta sake samun lafiya sosai da sosai sannan Suhaib ya tarkata suka koma Abuja
Dayake ana hutun Corona babu school sai zaman gida, haka rayuwan taci gaba da gudana har sanda aka shafe kusan shekara ɗaya da samuwar cutar, sannan aka soma buɗe makarantu anan Zaria da sauran garuruwa, wasu ma garin sun daɗe da buɗe wa, don haka itama RAUDHA ta sanar da Daddy tana son koma wa school, sai dai tace ba ta son zaman Abuja tafi son Nan kusa da Daddy, tunda shima yana gida ba ya zuwa ko ina
Da ya nemi ra'ayin ta akan school ɗin da zata shiga
Sai ta ce masa tana son abroad ne
Da sauri Daddy ya kalle ta ya ce, "haba Baby taya zan bar ki ki je wani ƙasa karatu bayan kin san halin da ake ciki yanzu? Ga kuma halin da kika shiga a baya, ki zaɓi dai inda kike so anan don ba na son kiyi nesa dani".
Shagwaɓe fuska tayi ta hau buga ƙafa a ƙasa tana hawaye
Janyo ta yayi jikin sa ya hau rarrashin ta, sai da ya ga taƙi haƙura, don daga ƙarshe saka mishi kuka tayi, sosai yake ƙaunar ta, domin soyayyar ta bazai iya bari yana gani tana neman abu ya hana ta ba, sai yace mata, "yi shiru to, faɗa min wani ƙasa kike so ki je umm Baby na?"
Cikin shagwaɓa tace, "Daddy Saudia zaka kai Ni, can nake so sabida in koyi addini sosai, tunda ka ga ban iya komi ba, ka ga idan na je can zan shiga school ɗina, sannan zanna riƙa islamiyya sosai a can".
Washe baki Daddy yayi yana sake rungume ta ya ce, "iyeeeee ashe Baby na ta girma haka? Ashe kina da wayau? Good dear gaskiya naji daɗin zancen ki".
Dariya ta ƙyalƙyale dashi cike da farin ciki itama
Nan Daddy yayi ta nuna farin cikin shi, kafin yayi mata alƙawarin zai nema mata insha Allahu idan har an dace, tunda a time ɗin ba kasafai ake bari fita Abroad ba, su ma can ɗin ba sa bari a shigo musu ƙasa.
Koda Daddy ya sanar da Suhaib shima yayi murna sosai, sai dai kuma ba su so tayi nisa da su har haka ba, amma kuma sun san can ɗin zai fi nan, tunda zata je ta nemi ilmin addini ne, kuma can shine garin musulunci, ta yiwu idan ta dawo ma ta zama wata Malama Sheikhiya, hakan da suke tuna wa shi ke saka su jindaɗi sosai.
Babu jima wa Daddy ya soma mata cuku-cukun fitar da ita zuwa Saudia, sai dai ba'a saki hanya ba har yanzu, dole Madina zata tafi tunda can anfi barin mutane zuwa, Saudia kuwa ko ƴan zuwa hajji an hana su zuwa.
Da labarin tafiyan ta ya iske Rayyan, ya shiga wani hali sosai, har faɗa sai da yayi wa Suhaib wai "akan me za su tura ta wani ƙasa bayan sun san halin da take ciki? Kuma yanzu sai su ƙara barin ta tayi nesa da su?"
Sosai Suhaib yayi mamakin faɗar Rayyan ɗin, har dai ya ce, "wai Dude ko dai akwai abinda kake ɓoye min ne a game da Baby?"
"Kamar ya fa?" Cewar Rayyan ɗin
"Ina nufin faɗan yayi yawa, ko matar ka ce sai haka ai".
"Ok kana nufin Ni ban isa inyi mata faɗa a matsayin yayan ta ba ko?"
"A'a ba haka nake nufi ba, ina.."
Cike da ɓacin rai Rayyan ya tari numfashin sa da faɗin, "haka kake nufi mana, Ni ban isa da ita ba, kana son ka nuna min banbanci tsakani na da ku, tunda har ku kun yarda Ni kuma asuwa da zan hana ta".
"Haba Dude wlh baka fahimce ni bane, meye na zafi haka abinda be kai ya kawo ba?".
Ƙitt ya kashe wayan
Sosai Suhaib ya sake mamaki da halin da Rayyan ya nuna masa, ya san shi ba mutum bane me yawan ɗaukan zafi akan abu, idan kuwa ka ga fushin sa, to, tabbas ba abu bane ƙanƙani, har yana mamaki da kasancewar sa ya zaɓi soja, domin kuwa ko kusa aikin be kamace sa ba, yana da sauƙin hali sosai, idan har ba ka ƙure sa ba ne, to shine zaka ga ainihin waye shi, a nan ne zai nuna maka haukan sa tuburan.
Sake kiran sa yayi, daƙyar ya amsa call ɗin, sosai Suhaib ya ba shi haƙuri
Shi kuma a lokacin shima ya sauko kaɗan, don ba kaɗan yayi fushi ba, har yanzu baƙin cikin tafiyan RAUDHA wani ƙasa ne ke nuƙurƙusan shi
Anan suka shirya har suna taɓa hira kafin su kashe wayan, aran Suhaib dariya kawai yayi ya ce, "uhmmm idan tayi tsami ma ji".
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
Komi na tafiyar RAUDHA ya gama kammaluwa
A washe garin ranan da zata tafi haka Ramcy ta zo ta wuni mata har zuwa dare, sannan ta tafi.
Washe gari Daddy da Suhaib da ya zo don yin sallama da ita, su suka kai ta har airport, sai da tayi ta kuka kafin ta yarda ta shiga jirgin
Ahaka suna ɗaga mata hannu har jirgin ya tashi, sai da dukan su suka share ƙwalla kafin suka juya suka shiga motan su, suka bar wajen ko wannen su cike da kewar RAUDHA.
.
_muna miki fatan alkhairi RAUDHA, sai mu ce sai kin dawo._
_Nima zan tafi hutu har sanda RAUDHA zata dawo._ 🥴🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️
[3/19, 8:47 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Isma'il Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON THIRTY NINE*
_______📖 *AFTER FOUR YEAR'S.*
Gaba ɗaya haraban airport ɗin ya cika maƙil da jama'a, ciki kuwa har da ƴan jaridu waɗanda suka zo domin samun rahoto, sabida zuwan Jikan Sarkin American da zai bayyana a ƙasar ta mu
Sai dai kuma jami'an tsaro sun hana kowa shiga cikin haraban airport ɗin, har ta da ma su zuwa ɗaukan ƴan uwan su, sai dai suka faka motocin su daga can nesa
Suhaib na ɗaya daga cikin mutanen wajen, yana tsaye jikin motan sa yana jiran saukar jirgin, sosai idan ka kalli fuskar sa zaka ga bayyanuwar tsantsan farin cikin da yake ciki a wannan ranan, saboda dawowar ƙanwar ta sa.
Koda jirgin ta gama sauka sai mutane suka fara fito wa, can na hango wata kyakykyawar cikakkiyar kamilalliyar budurwa tana sauko wa, a ƙalla shekarun ta bazai wuce 24years ba, tsananin kyauwun ta da hasken ta sai da duk wanda ke haraban wajen idan har idanuwan sa sun sauka a kanta sai ya kasa ɗauke ido a wajen ta, a zuciyar sa yana sarkake Allah da yayi wannan kyakykyawar halittan
Tana sanye da doguwar rigan abaya baƙa ce, daga saman gaban rigan har ƙasa an saka kalan ruwan ƙasa, sai aka bi wajen da kwalliyan stones masu tsananin ƙyalƙyali me ban sha'awa, ta yane kanta da ɗankwalin abayan, sai ta toshe idanunta da wani faskeken baƙin Glasses da ya sake ƙawata farar fuskar ta, sak idan ka ganta tamkar wata balarabiyya sabida shigan ta da yanayin ta, baza ka taɓa cewa ita ɗin ta haɗa jini da bahaushe ba, Bahaushen ma Bazazzage.
A hankali take taka matattaƙalan benen, wanda hakan yayi matuƙar ƙosar da matashin saurayin dake bayan ta, shi ɗin yana sanye da riga da wando baƙaƙe ne ma su tsananin kyau da tsada, ya saka rigan sanyi ja me hula, wanda hakan yasa ya rufe kansa da hulan, tare da saka faskeken Glasses a fuskar sa, wanda ya ba shi damar ɓoye fuskar sa gaba ɗaya. Sosai ya ƙosa da ya bar wajen tun kafin asirin sa ya tonu, shi ɗin mutum ne da ba ya son mutane bare kallo, shiyasa ya zaɓi ɓoye kansa batare da an yi talla da shi ba.
Ta Geben ta ya raɓa ya wuce, hakan yasa ya ɗan bige ta har wayan hannun ta ya so kubce wa, sai dai tayi saurin tare wa tana ɗago kai tabi bayan sa da kallo, wanda shi tuni har ya ƙarisa sauka kan benen ma
Dogon tsaki taja, ahankali ta furta, "Useless".
Tsakin nata kaɗai yaji, don haka ya juyo don ganin wacce har ta samu damar iya masa tsaki. Akan kyakykyawar fuskar ta ya sauke, sai kawai ya ware idanun sa sosai yana kallon ta
Ita kuwa a time ɗin ma ta mayar da hankalin ta kan wayan ta tana latsa wa, har tazo ta wuce sa batare da ta sake bi ta kansa ba, ba ma tasan Allah yayi ruwan tsakin sa ba
Be dena kallon ta ba, har sanda ta ɓace wa ganin sa, sai kawai ya saki numfashi da sauri da sauri, kasancewar tun tozali da ita da yayi ya ɗauke numfashin nasa, be taɓa ganin yarinyan da ta tafi da imanin sa kamar wannan ba, duk kuwa da cewa ya ga ƴan mata bila adadin waɗanda suka fi ta kyau da komi, amma shi dai wannan ɗin ta daban ce a wajen sa. Yana tsaye ya kasa motsawa a wajen har sai da good 5 minutes ta shuɗe, sannan a hankali ya taka ya bar wajen yana sake rufe fuskar sa da hulan kansa, inda ya ga tabi nan yabi amma kuma ko me kama da ita be gani ba, hakan yasa ya nufi wajen ƴan Taxi ya hau ɗaya suka bar wajen.
🌐🌐🌐
*RAUDHA* na fita wajen airport ɗin, ta hangi Yayan ta mafi soyuwa a birnin zuciyar ta, da sauri ta ƙarisa wajen sa sai ji yayi an rungume sa
Wani irin farin ciki ya sake kama sa ganin ƙanwar ta sa rungume da shi, ai nan da nan shima ya rungume ta yana me sake nuna farin cikin ganin ta
Ita kuwa sai faɗin "I Miss You so Much Yaya". Take yi, bakin ta ya ƙi rufuwa sabida tsaban murna
Ɗago kanta tayi tana kallon sa, cike da washe haƙora tace, "Yaya ina Daddy be zo ba?"
"Baby Daddy yana gida, Ni kaɗai na zo ɗaukan ki". Suhaib yayi maganar yana shafa kanta shima bakin sa har kunne
Har zata yi magana sai wasu maza biyu masu uniform a jikin su, suka ƙariso mata da Trollys ɗin ta da tasaka su ɗauko mata
Ganin su da akwatin sai Suhaib ya je ya buɗe musu Boot suka saka mishi, sannan ya biya su suka bar wajen, shi kuma ya buɗe mata gaban motan ta shiga, ya zaga ya shiga suka bar wajen.
A cikin mota surutu RAUDHA ta dinga yin masa yana biye mata, tamkar ba ita ba domin ta sauya sosai fiye da da, duk da a yanzu ɗin ba ta yawan surutu ga kowa idan ba da su ɗin ba, har yanzu halin ta na nan na rashin sabo da mutane
Shekaru huɗu kenan ta shafe a ƙasar Madina, abubuwa da dama sun sauya a tattare da ita, duk wani halin ta mara sa kyau ta dena gaba ɗaya, tunda ta je karatu kawai ta saka a gaba, bata da aiki sai karatu sai research akan addinin ta, kafin ta shiga makarantar islamiyya sai da ta shafe kusan shekara da zuwan ta, a time ɗin ta gama sanin wasu abubuwa sosai a addinin ta, sannan daga baya ta shiga islamiyya, makarantun da ta shiga guda biyu ne duk islamiyya, idan ta je boko ta dawo sai ta wuce can wani Islamic school, sai dare take koma wa gida, da weekend ma school ɗin da take zuwa daban ne, babu nisa da inda take zaune
Lokaci ƙanƙani RAUDHA ta gama sanin komi sabida ta saka abun a ranta, dama ga ta da ƙwaƙwalwa, a lokaci ƙanƙani tayi suna sosai a ko wani school da take yi, musamman ma boko.
Su Daddy suna kawo mata ziyara akai-akai, kuma sun ji daɗin yanda take mayar da hankali fiye da tunanin su
Kankace me harshen ta ya gama juye wa irin na larabawa, larabci a bakin ta kamar ruwa, sosai take son harshen shiyasa duk abinda zata yi, tafi son tayi magana da harshen larabci akan ko wani yare, sabida school ɗin da take yi ana karatu ne da English and Arabic
Sometime tana tambayan su Daddy idan suka zo mata ziyara, akan su taho mata da Ramcy, sosai take kewar ta, yawan tambayan ta da take yi ne, Daddy har ya yanke shawarar tambayan mahaifin ta, idan har zai bar ta taci gaba da school, shi kuma zai biya mata makaranta ta koma can wajen RAUDHA ɗin, amma kuma sai Baban Ramcy yace be yarda ba, shi ba ya son ɗiyar sa tayi nesa da shi, hakan ya sa Daddy ya yanke shawaran biyan mata taci gaba anan A.B.U Zaria, kuma akayi Sa'a Baban ta ya amince. Sau uku tana zuwa kai wa RAUDHA ziyara, wani lokacin idan Suhaib zai je sai ta bi shi, wani lokacin kuma Daddy ke tafiya da ita. Itama dai taci gaba da school ɗin ta anan kamar yanda Daddy ya alƙawurta zata yi, yanzu haka kusan watanni bakwai da gamawar ta, har an saka mata rana yanzu saura wata ɗaya bikin ta.
🌐🌐🌐
Suhaib na yin parcking motan, RAUDHA ta buɗe ta fito, cike da zumuɗi ta nufi hanyar cikin gidan
Suhaib na mata dariya yana faɗin "baza ta jira sa ba ta tafi?" Amma ina ba ma taji sa ba, burin ta kawai ta isa ciki ta haɗu da Daddyn ta
A hanya duk ta gama gaisa wa da wasu daga cikin ma''aikatan gidan. Suna mata murnan kammala karatu, ta amsa su cike da farin ciki. Su kansu sun yi mamakin sanja war RAUDHA. Bata bi ta kansu ba ta shige da gudun ta da ya zame mata jiki
Ai kuwa Daddy na zaune a parlour'n ƙasa, yana ganin ta ya miƙe yana mata waƙa yana dariya
Da gudu ta ƙarisa gare sa ta rungume sa tana faɗin, "Daddy na Ni kaɗai! Daddy na da yafi na kowa".
Still dariya yake yi yana cewa, "na'am my dear daughter, Ina miki murnan kammala school ɗin ki lafiya, Allah ya miki albarka".
"Ameen Daddy". Ta amsa shi tana sakar mishi peck a kumatu kamar yanda larabawa suke yi, bakin ta a washe
Time ɗin ne Suhaib ya shigo, bayan sa ma'aikata suna jaye da akwatunan ta, ajiye wa suka yi suka bar wajen, yayinda su kuma suka zauna akan sofa suna ƙara gaisa wa tare da tambayan ta school da inda ta baro
Nan ta washe baki tana ta zuba musu surutu tamkar an kunna rediyo, gaba ɗaya ta haɗa su ta matse idan ta rungume wannan sai ta rungume wancan, tana faɗa musu missing ɗin da tayi nasu, tana tsakiyan su ne tana zaune
Su kuma bakin su ya ƙi rufuwa saboda murna, sai biye mata suke yi, sai da aka kira sallan magriba sannan ta tashi ta nufi ɗakin ta, su kuma suka wuce masallaci.
Tana shiga wanka ta soma yi, komi tana yin sa ne cike da kewa, sai rera waƙan "i miss You home" take yi. Sallah ta soma gabatar wa wanda ake bin ta, sannan ta ɗaura da magriba, ta saka riga da wando ma su santsi da kwalliya ta fito
A Parlour ta tarar da su zaune suna jiran ta, tana fito wa Daddy ya ce, "su hau kan dainning su ci abinci"
Zama suka yi suka ci abincin, sannan suka koma Parlour tana ta ba su labaran da ya ƙi ya ƙare, sai kuma daga baya ta soma raba musu tsaraban da tayi musu, har da nasu Farida da yaran ta biyu, Haneep da Abdullahi da ta haifa kusan shekara biyu da rabi, suna kiran sa da Abdul kasancewar sunan mahaifin Farida ne, yanzu yaran sun ta so kansu ɗaya ne tamkar ƴan biyu, har Abdul ya fi Haneep wayau yanzu sabida halin laluran da yake fama da shi, Suhaib be taho da su bane sabida akwai school na yaran, zuwa gobe weekend za su zo, ranan Lahadi kuma su koma gaba ɗaya har Suhaib ɗin.
Anan suka shantake har kusan ƙarfe 11:30pm. Kafin suka je suka kwanta.
Washe gari da wuri sai ga Ramcy ta bugo musu sammako, kasancewar har yanzu RAUDHA akwai ta da son huta wa, shiyasa idan ta kwanta tana kai wa 11:00am bata tashi a barci ba, idan har ba Lectures take da shi ba to tana wuni ne a kwance da safe, sai da rana zuwa da dare wannan kuma time ɗin karatu ne, ya rigada ya zame mata jiki har yanzu bata fasa ba.
Ramcy bayan ta gaisa da su Daddy sai ta wuce ɗakin RAUDHAN, anan ta ganta shame-shame tana barci, zama tayi ta soma tashin ta
Koda RAUDHA ta tashi, ganin Ramcy a gaban ta, ai da sauri ta rungume ta suna murnan ganin juna, ko wacce cikin su cike da kewar ƴar uwan ta, har da ƙwalla suka share
RAUDHA tace, "ana haƙƙan ishtaƙtu laki ya jamilaty".
Dariya Ramcy tayi tace, "Besty kin manta ne, nan fa ba Madina bane".
"Ya Salam naseetu wlh, ana asif".
Murmushi Ramcy tayi tace, "again?"
Dafe goshi RAUDHA tayi, sai kuma ta kwaɓe fuska tace, "sorry Besty na rigada na saba, sai kin yi haƙuri dani".
Ramcy zata yi magana, sai wayan RAUDHA ta soma ringing na waƙar larabci me daɗi
Hannu ta saka ta ɗauki wayan tana murmushi tun kafin ta kai ga duba wa, domin ta san mutum ɗaya ne ta saka mishi wannan ring ɗin. Peacking tayi ta kara a kunne, sai ta narke fuska tace, "nayi fushi Ni dai".
Murmushi kaɗai Ramcy take saki idanun ta akan RAUDHA ɗin, sosai take tsananin burge ta da yanda ta sauya gaba ɗaya, sauraron ta take yi duk da ba ta jin abinda wancan yake faɗa, har ta gama bata ɗauke ido akan ta ba
Hakan yasa RAUDHA da ta cire wayan daga kunnen ta ta ɗage mata gira tace, "lafiya! Kallon fa?"
Still Murmushi Ramcy ta saki tace, "kina tsananin burge Ni ne, ta yanda kika iya tafiyar da soyayyar ki da Ƙalbin ki (dayake haka take ce mishi, kuma har su Daddy babu wanda be san hakan take kiran sa da shi ba, sai dai babu wanda ya san shi har yanzu), ko a mafarki idan wani yace min zaki riƙe soyayya irin haka, zan ƙaryata shi, domin kuwa na fi kowa sanin wacece ke akan yanda kika riƙe so".
Murmusawa RAUDHA tayi tace, "ai ada ne ba yanzu ba, yanzu ke ma ba ga shi ba har an kusa a shafa fatiha? Bigaddin nazri anil waƙti, (komi da lokacin sa)"
"To yaushe ne zaki nuna mana shi, har yanzu kina min rowan shi na rasa meyasa?"
Lumshe ido tayi tana buɗe wa akan Ramcy, kafin tace, "ƙariban jiddan". Sai kuma tayi murmushi tace, "sorry Besty, a mean very soon".
"Ok Allah ya Kai mu".
"Kin san naji daɗin yanda za'a yi bikin nan naki dani? Tabbas da ina school ne dole sai na ajiye na dawo".
Ramcy tace, "wa ya isa yayi min aure babu Besty kusa? Ai wlh da bazan taɓa aure ba in dai har sai nayi aure ne kafin ki dawo, dole na saka aka ɗaga".
"Hal haƙƙan? A mean really?" Tayi saurin sauya zancen tana ɗaura hannun ta a goshi
Ramcy na dariya tace, "yeap I'm sure, but Nima dai dole zan koya larabcin nan ko dan mu riƙa yi, tunda muna baki wahala".
Dariya itama RAUDHA tayi tace, "ai na dawo da sannu zan rage kar ki damu".
Daga nan hira suka ci gaba da yi, har time ɗin da Farida ta zo, sai lokacin RAUDHA ta miƙe ta shiga wanka tayi tafito, ta shirya cikin farar jallabiya me hula, ta saki hulan a bayan ta, sai ta ɗaura wani hulan daban
Parlour'n ƙasa suka sauka, inda acan suka haɗu gaba ɗaya ana ta hira, sosai RAUDHA ta maƙalƙale su Haneep tana ta musu wasa, musamman Abdul da ya fi surutu. Sosai take tausayin Haneep sabida rashin lafiyan sa, ko magana be cika yi ba, idan ya zauna ya dinga zilalar da miyau kenan, gaba ɗaya gaban rigan sa sai ya jiƙe, a rana sai a sauya masa kaya babu adadi sabida ɓata wa da yake yi, ga shi ko maganar sa ba ya wani fita sosai, hannun sa ɗaya kuma ashanye duk da yana iya sarrafa shi, wai Nan ma don an ta magani ne.
Anan Ramcy ta wuni sai dare ta tafi gida, sai gobe zata dawo tunda za'a shirya wa RAUDHA partyn murnan kammala karatun ta.
[3/21, 12:10 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Isma'il Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*TARIHIN FARILTA SALLAH*
```An farilta sallolin nan biyar ne gabanin ƙaura, watau hijira, da shekara ɗaya da rabi. Sallah ce kaɗai ibadar da aka farilta ta a sama a daren Isra'e, kamar dai yadda aka ruwaito a hadisin nan na Anas. Da farko an umurce shi da Sallah guda hamsin ne; da sannu aka dinga rage su har suka zama biyar a bisa roƙon da shi Manzon ya yi wa Ubangijin sa. Da suka zama biyar, sai Allah ya ce masa su biyar ɗin nan, dai-dai suke da hamsin.
Malamai da yawa sun yi bayanin yadda sallar ma'aikin Allah, mai tsira da aminci, take gabanin Isra'en.
Wasu malaman sun ce, "Gabanin Isra'e, babu wata sallah wadda aka farilta sai sallar dare (Ƙiyamul lail) wadda aka umurci ma'aiki da yin ta ba da iyakataccen lokaci ko adadi ba, kamar yadda yake a suratul Muzzammil, ayoyi huɗu na farko:
"Ya wanda ya lulluɓe! Ka tsayu domin yin Sallah a cikin dare (duka) face kaɗan, rabin sa, ko ka rage abu kaɗan daga gare shi, ko ka ƙara kansa... Ma'aikin Allah ya kasance yana yin sallar a kashi biyu cikin uku na dare ko a rabin sa ko kuma sulusin sa. Musulmi suka dinga yi tare da shi kamar shekara guda har suka gaji; daga nan sai Allah ya shafe ta don jin ƙan su.
An ruwaito cewa sallar da Musulmi suke yi gabanin tafiyar dare suna yin ta ne kafin faɗuwar rana da kafin ketowarta kamar yadda yake a sallah littafin Almanhalil Azb. Gabanin ƙaurar Annabi zuwa Madina raka'o'in sallah bibbiyu ne, bayan ƙaura ne suka zama hurhuɗu, illa magriba da ta kasance raka'a uku, ita kuma sallar subahi ta tsaya a kan biyu saboda dogon karatun da ake yi cikin ta. Buhari da Ahmad sun ruwaito daga Nana A'ishah cewa, "an farilta sallah raka'a bibbiyu, bayan ƙaura ne aka mai da ita raka'a hurhuɗu, amma an bar sallar tafiya a kan raka'a ne bibbiyu, sai sallar magriba ita ko da ma raka'a uku-uku ce."
Allah ya sa mu dace.```
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON FORTY*
_______📖 Daga airport kai tsaye Zaria me Taxi ɗin ya wuce da shi, can cikin tudun jugun; gonan ganye. A bakin tanƙamemen wani baƙin gate aka sauke sa, ya fito ya saka hannu cikin aljihun sa ya fiddo kuɗi, kuɗin irin na American ne, sai ya kalli me Taxi ɗin sannan ya kalli kuɗin, guda biyu ya zara ya miƙa masa batare da ya ce komi ba
Me Taxi ya tsaya sakaka da baki yana kallon sa, sai kuma ya ce, "bawan Allah ban san ya zan yi da wannan kuɗin ba, kana gani wannan ai ba na Nigeria bane".
Sai a time ɗin ya sauke hulan kansa, fuskar sa ta bayyana duk da ba duka bane, kasancewar akwai Glasses. Murmushi yayi cikin harshen sa da be gama iya hausan ba ya ce, "I know, but ka amsa idan ka sauya dana Nigeria 10k ne".
Zaro ido drever'n yayi, sai kuma ya washe baki cike da murna ya saka hannu ya amsa, nan ya soma mishi godiya
Sai dai shi murmushi kaɗai yayi ya juya ya nufi bakin Gate ɗin, hannu ya saka ya tura small door ɗin dake buɗe
Me gadi dake zaune saman benci kusa da Gate ɗin, ya kara rediyo a kunnen sa idanuwan sa a rufe. jin ƙaran buɗe Gate, firgigit yayi ya miƙe yana nufo sa, be gane sa ba sai da ya iso gaban sa, sai ya washe baki ya ce, "ranka ya daɗe kai ne?"
Murmushi yayi masa, ya gyaɗa masa kai
"To ai an tafi ɗauko ka, baka gansu bane?" Me gadi ya sake faɗa cike da fara'a
Still Nan ma gyaɗa masa kai yayi, yayi hanyar gidan zai bar wajen
Biyo sa me gadi yayi yana mishi barka da zuwa, har bakin ƙofan shiga parlour'n ya rako sa, sannan ya juya
Shi kuma ya buɗe ya shiga, babu kowa a cikin parlour'n sai t.v dake aiki, ƙamshin daɗi ya cika ko ina, tsaya wa yayi a tsakiyar parlour'n yana bin ko ina da kallo, har hotunan dake cikin parlour'n na mutanen gidan, tare da iyayen sa da kakannin sa, murmushi kaɗai yake zuba wa yana ci gaba da taka wa zuwa cikin parlour'n.
A time ɗin ne wata matashiyar budurwa da a ƙalla baza ta fi 21years ba, ta fito daga kichen tana yarfe hannayen ta, ganin sa sai ta kwatsa ihu tana kiran sunan sa
"Yaya Zulain".
Juyo wa yayi yana kallon ta, sai ya sakar mata murmushi yana buɗe hannayen sa alamun ta zo
Da gudu ta ƙariso cikin tsananin murna ta rungume shi
Ihun ta shine ya fito da mutanen gidan, Abba da Momy da kuma Sharif. ganin Zulain rungume da Sharifa, gaba ɗaya sai suka yo wajen sa suna me nuna murnan su da ganin sa
Nan shi kuma ya sake ta, ya bi su bayan ɗaya yana rungume su cike da fara'a
Abba na murmushi yace, "amma kuma yanzu Drever'n da na aika tare da bodyguard ɗina, suka kira Ni akan ba su ganka ba har yanzu, ashe kai ga ka har ka iso gida, ta ya ka gane hanya da ka taho kai kaɗai?"
Dariya Zulain yayi yace, "Abba kenan, ba fa yau na saba zuwa ba, kasan ba na son mutanen wajen su gane Ni, that's why na ɓoye fuska ta na fito na hau Taxi ya kawo Ni".
Momy tace, "ai kuwa kayi kyan kai wlh, Ni ban san ma wanda yake kiran su ba, nan muka zauna a gaban t.v muna jiran mu ga an haska ka, amma muka ji shiru, ashe kai kayi musu wayau ne ka gudo".
Dariya suka yi gaba ɗaya, kana suka zauna suna sake gaisa wa, Abba na tambayar Iyayen Zulain ɗin da mutanen can ƴan uwa
"Abba kowa lafiya, suna gaishe ku sosai da sosai".
"Masha Allah muna amsa wa".
"Sharifa tashi mana ki kawo masa Drinks, kin zauna kin wani maƙale masa". Cewar Momy tana kallon Sharifa da ta shige masa
Buga ƙafa ta hau yi kana tace, "Um um Momy! Ba ga Yaya ba ya ɗauko masa, Ni ba na son jirga wa kusa da shi".
Sharif hannu ya saka ya buge mata baki yace, "a aike ki ki aike Ni, ina wasa dake ne?"
Zumɓura baki tayi tana shirin kuka
Zulain ya saka hannu yana shafa mata kai yace, "oh sorry my dear sister, Kar ki biye masa kiyi kuka bar sa ko?"
Tsamm Momy ta tashi tana cewa, "Ni bari in tashi in ɗauko maka".
"Tun farko ma da hakan kika yi, da baki ɓata bakin ki ba, kin san halin Sharifa tunda ta ga Zulain ba kuma sauran aiki". Abba ya faɗa yana murmushi
Sharif yace, "Ai Abba ƙyale ta Ni ne maganin ta wlh, in sake ganin an saka ki ki ɗauko wani abun ki ƙi".
"Kai da baka ɗauko ba, ina ce ai duk halin ku ɗaya?" Momy tace hakan sanda ta dawo ta ajiye babban Plet a saman Centre table, janyo wa tayi ta matso da shi gaban Zulain ɗin, sannan ta koma ta zauna
Sharif dai be ce komi ba, sai saka hannu da yayi yana zaba wa Zulain Coke a cikin glass Cup
Abba ya ce, "mun yi magana da Yaya yace min zaka ɗan jima ko?"
"Yes Abba, Coz anan zan yi hutu na gaba ɗaya ma".
"To Masha Allah, ka ga ai ka za ga dangi sosai wannan karon, da waɗanda ma suke min ƙorafin ba su sanka ba duk zaku je su sanka, ga Sharif nan tunda shima ya dawo hutun sa gaba ɗaya sai ku riƙa zuwa tare".
"Abba nima har da Ni". Cewar Sharifa cike da zumuɗi
Hararan ta Sharif yayi yana cewa, "wa ya saka bakin ki?"
Momy tace, "ka ji ka dai, to idan bata raka ku ba, ai ina ce duk sammakai da kai da shi ɗin, tunda kaima babu inda ka sani a dangin, dole ita zata nuna muku ko ina ku shiga".
Gwalo Sharifa tayi masa
Shi kuma yayi ƙwafa yana ɗaukan wayan sa ya ce, "wlh Momy duk ke kike saka wa yarinyan nan tana raina Ni, amma babu komi zan yi maganin ta".
Daga Abba har Zulain murmushi kawai suke musu
Hira suka ɗan taɓa, kafin Abba ya ce su tashi su tafi masallaci ana kiran sallah.
Ba su dawo ba, sai da aka yi sallan isha'i, inda suka zauna a dainning suka ci abinci, sannan suka dawo Parlour suka dasa hira, sai wajen goma suka watse, Zulain da Sharif suka wuce ɗakin Sharif ɗin, sai da Zulain yayi wanka ya sauya kaya sannan ya hayo kan gadon, sai dai tunda ya rufe idanuwan sa ya kasa barci, illa fuskar RAUDHA da ya bayyana masa, gaba ɗaya ya rasa sukunin sa sai faman tunanin ta yake yi, yana fata Allah ya sake haɗa shi da ita, sosai yarinyan ta hana sa sukuni har ya rasa me ke damun sa, daƙyar ya iya samu barci ya ɗauke sa, sabida ba ƙaramin gajiya ne a jikin sa ba.
Abba Ƙani ne wajen mahaifin Zulain, haifaffun nan Zaria ne, inda Mahaifin Zulain karatu ya kai sa can American, anan suka haɗu da ƴar Sarkin American ya aure ta, kuma suka ci gaba da zama a can, ɗan su ɗaya suka mallaka a duniya wato Zulain, idan ya samu hutu suna kawo sa nan wajen Abba yayi mishi hutu, har zuwa yanzu da ya girma yana aikin sa a can, sai dai yanzu ɗin be cika zuwa sosai ba sai idan ya samu hutun shekara.
Abba babban mutum ne a nan Zaria, kuma ɗan siyasa ne wanda ya ci jiya yana cin yau, kuma yana fata gobe ma a dama dashi a ƙasar, yanzu haka shi aka tsayar a takarar mataimakin Gwamnan Kaduna, yaran sa uku, Hauwa'u me sunan Maman Abba, suna kiran ta Aunty Mimi, tayi aure har da yaran ta biyu, sai Sharif da yanzu yake aiki a Abuja, shima yanzu haka an saka mishi rana, sai kuma Sharifa da yanzu ne take aji na biyu a A.B.U Zaria
Tun farko ita Allah ya ɗaura mata ƙaunar Zulain sosai, shiyasa take shige masa sosai har suka saba matuƙa, idan ta samu hutun school can American take zuwa tayi hutun ta, hakan ya sa suka sake shaƙuwa fiye da tunanin mutum, har wasu suna musu kallon akwai soyayya a tsakanin su, ba su san cewa shi Zulain yana mata kallon ƙanwa ce kaɗai, shi a rayuwa babu ruwan sa da mata idan har ba ƴan uwan sa ba, sai dai ya taɓa yin soyayya da daɗe wa, har ya so ya auri yarinyan, sai dai Allah be yi ba ta mutu, yarinyan dangin sa ce a can American, kuma Christian ce, tunda dama itama har yanzu mahaifiyar sa bata musulunta ba, to su a wajen su babu komi idan har ya auri ko wace irin yare ce.
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*SATURDAY*
Yau ce ranan da za'a yi wa RAUDHA partyn kammala karatun ta. Gaba ɗaya gidan an yi masa decorations, sosai ko ina yayi kyau gunun sha'awa, a bayan gidan a cikin Garden ɗin wajen za'a yi, sosai wajen ya matuƙar haɗuwa, ga shi an kashe kuɗi, komi green and red aka sanya a wajen.
Zuwa ƙarfe 04:00pm. Har mutane sun soma zuwa gidan, duk da ba wasu gayya ne a kayi ba, domin dai RAUDHA bata da ƙawaye illa Ramcy kaɗai, sai ita Ramcy ɗin da ta gayyaci ƴan gidan su, sai kuma Daddy da Suhaib su ma da suka gayyaci mutanen su na nan Zaria kaɗai, ciki kuwa har da Abba za su zo da su Sharif, tunda dama Abba abokin Daddy ne, tare suka yi Siyasa kafin Daddy ya fita, jam'iyyar su ɗaya, ta dalilin hakan ne Sharif da Suhaib suka san juna har suka zama abokai, to abokan takan nasu tayi ƙarfi ne sanda Sharif ya koma Abuja da zama yana aiki, shiyasa suka ci gaba da zumunci sosai.
.
_More Comments more page, idan har babu Comments da zai faranta min, to tabbas na ɗau hutu domin baza ku ji Ni ba._
[3/21, 12:36 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:*✍️
_Nafisat Isma'il Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON FORTY ONE*
_______📖 Biri da wando ta saka me santsi Light orange, ƙasan wandon me fela ne sosai, sai ta saka top fari iya gwiwar ta, me kwalliyan stones, sannan sai ta naɗa blue ɗin ɗankwali a kanta, wanda ya fito mata da gashin ta ta ƙasan ƙeya, Light makeup tayi da ya fito da tsantsan kyawun ta, kai Masha Allah duk wanda ya ga RAUDHA wannan lokacin bazai so ya ɗauke idanun sa ba, ta haɗu iya haɗuwa sai wanda ya gani, takalmin da ta saka me tsinin gaske ne cover me igiya, kalan Light blue da farin Socks a ciki, sai tashin ƙamshi take yi irin turaren nan na Arabian
Ramcy dake zaune saman sofan ɗakin ta, sakin baki tayi tana kallon ta
Sai da RAUDHA ta matso kusa da ita, ta sanya hannun ta ta shafa fuskar ta tana murmusawa. Sannan a time ɗin Ramcy ta rufe bakin ta bayan ta dawo da tunanin ta jikin ta
"What happened Besty?"
Gwauron numfashi Ramcy ta sauke kafin tace, "ban san me zan ce bane wlh Besty, haɗuwar ki yayi yawa. Masha Allah gaskiya ki gode Allah".
Murmushin ta me kyau ta saki kafin ta lumshe ido ahankali ta furta, "Shukran Lak, linazhab".
Da ido Ramcy tayi mata magana, "wai what?"
"Let's go".
Miƙe wa Ramcy tayi tana gyara zaman gyalen ta, itama tayi shiga ne cikin baƙin yadi me santsi, ɗinkin doguwar riga, duk da kasancewar ta baƙa but sosai tayi kyau matuƙa, kasancewar an yi wa rigan ado da jan zare sai Stones, kuma tayi amfani da jan ɗankwali ne sai farin gyale.
Fita suka yi, inda tuni an gama taruwa su kaɗai ake jira a wajen. A hanya suka haɗu da Farida ta zo kiran su, sai suka tafi tare, itama kanta sai ya ba kwalliyan RAUDHAN take yi
Ita kuwa sai murmushi take saki me fid da sihirtaccen kyawun ta, tana takun nan nata ɗai-ɗai me ban sha'awa, kasancewar bata yafa gyale ba, shiyasa duk inda jikin ta ya juya ana ganin komi ta yanda take sarrafa jikin ta.
Tun doso wan su wajen sai idanun mutane kawai ya koma kanta, hakan yasa wasu da hankalin su be kai kanta ba, sai duk suka kallo wajen
Tana tsakiyar Farida da Ramcy ne, suna taho wa wajen
Nan da nan aka soma tafi sabida sanar wan da MC ke yi na zuwan ta, nan ya soma koɗa ta yana kambama ta
Ita kuwa idanuwan ta na kan su Daddy da ta hange su, su ma suna mata murmushi, Suhaib har da ɗaga mata babban yatsan sa alamun tayi zam-zam. ita kuwa ta saki murmushin nan da ke ƙara wa fuskar ta kyawu.
"Kai man juyo ka ga wata halitta don Allah". Cewar Sharif da yayi maganar a hankali kusa da kunnen Zulain dake waya ya karkace kai
Juyo wa yayi kuwa, yana shirin hararan sa sai idon sa suka sauka kan RAUDHA dake tafiya zuwa wajen zaman ta, take anan komi nasa ya tsaya illa idanun sa da ya lumshe ya sake buɗe wa akanta, yana son tabbatar wa kansa itan ce ko kuwa?. Maganar Sharif ya sake dawo da shi hayyacin sa
"Ni wlh da na san S. Makamashi yana da ƙanwa irin wannan, ai da tuni ita na nema, me zai kai Ni zuwa waje gida be ƙoshi ba".
Shiru Zulain yayi don hankalin sa be gama dawo wa kan Sharif ba, bare ya tantance me yake faɗa, idanun sa ƙyam akan RAUDHA har ta zauna ta yanda yanzu yake ganin fuskar ta sosai. A take ya saki wani irin ajiyan zuciya yana sake lumshe ido
A tare Sharif da Mom ɗin sa da suke waya, suka je ho masa tambaya the same
Buɗe idanun sa yayi yana kallon Sharif da ya tsaya kallon sa shima, sai kuma yayi saurin kara wayan a kunnen sa sosai yana faɗin, "Mom zan kira ki letter please". Ya Yi saurin katse wayan be jira cewar ta ba, nan ya sake mayar da idanun sa kan RAUDHA gaba ɗaya ya mayar da hankalin sa gare ta, sosai yaji daɗin ganin ta da baki ma bazai iya furta wa ba, har wani sakin murmushi yake yi batare da ya sani ba
Sharif dake faman kallon sa baki sake, ya jinjina kansa ya ce, "cab ɗijam.. Kar dai har ta sace maka zuciya daga kallon farko?"
Zulain be kalle sa ba don ba ya son abunda zai gilma ga kallon kyakykyawar nan, amma kuma sai ya ɓata fuska yana kumbura shi irin maganar Sharif ɗin fa ya fara isar sa
Murmushi kawai Sharif yayi be ce komi ba, ya mayar da hankalin sa shima ga abinda ake yi.
A lokacin RAUDHA ta miƙe ne tana speech da muryan ta me daɗi da ya karaɗe wajen. Sosai duk mahalukin dake wajen ya mayar da hankalin sa gare ta cike da sha'awa. Har ta gama aka soma mata tafi Raf.. Raf... Raf
Sannan sai Suhaib ya amsa ya sake ma kowa godiya tare da yaba wa ƙanwar sa, da nuna irin tsantsan ƙaunar da yake mata. daga nan kuma Daddy ne ya amsa shima ya soma yabon ta sosai, da abun mamakin da ta ba su, tare da nuna wa mutane tsantsan alfaharin da yake yi da ɗiyar sa
Haka ake ta tafa wa cike da tsananin burge su da suka yi, don sosai iyalan suka burge kowa. Haka dai aka ci gaba da gudanar da partyn cike da sha'awa, inda daga baya MC ya kira RAUDHA domin ta taka
Murmushi kawai ta soma zuba wa, domin har yanzu ƙaunar ta da rawa yana nan, sai dai yanzu ba kamar da ba, duk da a yanzu ta koyo irin rawan larabawa ne, ko tana yi zaka ka bata cika yin irin na nan ba saboda ya zame mata jiki na larabawan. Tashi tayi ta fita ta soma taka wa a hankali tana dariya bakin ta ya ƙi rufuwa
Nan Suhaib ya taso ya soma taya ta
Yanda yake rawan ne sai da ya ba kowa dariya, sai tafi ake musu
Ita RAUDHA ta saka a sauya musu, don ta kasa yi sosai sabida waƙar Hausa ce, sai ta ce a saka mata na Laraba wa, ai nan ta soma taka wa irin nasu sosai, sai shima Suhaib ya biye mata suna yi tare, har da riƙe hannu irin na laraba wa yanda suke yi
Sosai yanzu ɗin Suhaib yafi ba wa kowa dariya, kowa ka gani wajen nishaɗi yake yi.
Lumshe idanu Zulain yayi saboda tsantsan wani farin ciki da yake ziyartan sa, sosai yarinyan ta matuƙar burge sa fiye da tunanin mutum, nan da nan ya ji soyayyar ta me tsananin ƙarfi ya kama sa. Har wani buga tagumi yayi da hannu biyu yana bin ta da kallo.
While sauran samarin, abokan Suhaib duk haka ne a wajen su, kowa fatan sa ya dace da mallakan kyakykyawar balarabiyyan nan.
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
Wata farar mota ce ta shigo cikin gidan a wannan lokacin, ahankali motan take tafiya har zuwa inda akayi parcking motoci, kamar mintuna biyu da tsayuwar motan aka buɗe ƙofan, sai dai wanda ke ciki be fito ba, illa ziro fararen ƙafafuwan sa dake cikin baƙin sandal Shoes da yayi waje
Daga inda yake duk da akwai tazara sosai da inda ake partyn, amma kuma hakan be sa tattausan waƙar larabawan dake tashi a wajen kasa ratsa masa kunnuwa ba, take anan ya lumshe idanun sa cike da jin daɗin waƙan, kamar shuɗewar mintuna biyar ya buɗe su yana aza idanun sa kan wayan sa dake saman cinyan sa, ɗauka yayi ya soma dubo Numban Suhaib da yayi masa serving da Dude yayi kira
While Suhaib na filin rawa yana tiƙan rawa tare da RAUDHA, sai yaji wayan sa na ruri, dasauri ya saki hannun ta yana zira wa cikin aljihu ya ciro wayan, ganin sunan Dude a screen ɗin wayan na yawo, sai nan da nan fara'an sa ya ƙaru, matsawa yayi gefe yana answer call ɗin ya kara a kunne, "Dude".
"Surprise! Gani a cikin gidan ku".
Waro ido Suhaib yayi, "haba don Allah".
Murmushi yayi shi kuma yace, "ka zo ka gani, ina nan wajen parcking space". Daga haka ya katse wayan
Da sauri Suhaib yayi hanyar barin wajen
Inda RAUDHA ta kira sunan sa
Juyo wa yayi yana kallon ta. Ta ɗage masa gira akan "ina zai je?"
Nuna mata yayi da hannu wai "yanzu zai dawo".
Ta marairaice fuska kafin ta juya ta nufi wajen zaman ta. A lokacin ne aka soma bata kyaututtuka.
🌐🌐🌐
Suhaib na isa wajen parcking space, Rayyan dake mota ya fito yana rufe wa. Rungume juna suka yi cike da tsananin murna, kafin kuma su saki juna suna cafe hannayen su ko wanne baki a washe
"Dude wlh ka shammace Ni, nayi tunanin ba yanzu zaka dawo ba".
Murmushi Rayyan yayi yace, "dama wannan week ɗin zan shigo, but sai naga dacewar shigowa yau ɗin tunda naga yau ce ranan ƙanwar ta mu, sai in Taya ta murna".
Dariya Suhaib ya saki yana ƙara ba shi hannu suka cafe yace, "gaskiya ka kyauta, Daddy zai yi farin ciki da zuwan ka, to ya Uncle da Ammee, da su Faruk?"
"Alhmadulillah duk suna gaishe ku, akwai babban surprise ma, but bazan sanar maka ba sai muna gaban Daddy".
Murmushi Suhaib yayi yace, "ok mu je to, mun tsaya a nan".
Jan hannun sa yayi suka nufi cikin gidan. Har sun kusa ƙarisa wa wajen taron sai wayan Rayyan tayi ƙara, ogan sa ke kiran sa don haka yace ma Suhaib "yayi gaba zai zo". Wayan ya ɗauka suka soma magana. Daga inda yake yana hango taron mutanen, inda fitilu masu haske suka haske wajen, kasancewar duhun magriba ta gabato, a time ɗin ma shirin tashi suke yi.
Yana gama wayan sai ya nufi wajen, a time ɗin har wasu sun soma barin wajen sabida an gama.
Tuni itama RAUDHA taja hannun Ramcy sun shige gida.
While su Daddy sun tsaya suna sallama da mutane.
Ƙarisawa Rayyan yayi wajen Suhaib.
🌐🌐🌐
Kai tsaye ɗakin RAUDHA dake sama suka wuce, anan suka zube kan kujera kowa na faɗan gajiyan da ya sha, sai kuma Ramcy ta tashi tana faɗin, "oh na bar su Aunty Nafeesa a waje, kuma sun ce min tafiya za su yi, ina zuwa bari inje".
RAUDHA tace, "miƙo min wayan ki, but kar su tafi yanzu zan sauko sai mu gaisa, in yaso drever ya mayar da su, but ke nan zaki kwana ko?"
Dariya Ramcy tayi tana zaro ido, "No ai nima tafiya zan yi zuwa anjima kaɗan, sabida Baba na gari kuma sai da yayi min gargaɗin in dawo, ina tunanin ma zamu tafi tare kawai da su ne".
"Ok mu je to sai mu yi sallama". cewar RAUDHA tana miƙe wa tare da wayan ta dana Ramcy dake hannun ta
Ramcy kuma ɗaukar jakan ta tayi suka fice.
RAUDHA tafiya take yi tana latsa wayoyin, kasancewar tana son tura pictures and videos ɗin da Ramcy tayi mata ne a wayan ta, kuma tana son tura wa *Ƙalby* a yanzu ɗin.
Sai da suka fita waje, kafin suka haɗu da su Amarya da Aunty Nafeesa suna shirin shigowa
Anan RAUDHA tayi musu godiya sosai, inda tasaka masu aiki suka kwaso musu kayan party ɗin. har wajen motan da za'a tafi da su ta raka su, kasancewar gaba ɗaya an gama watse wa, wasu sun wuce masallaci.
Su sun shiga mota, ita kuma ta tsaya da Ramcy suna ɗan Surutu, har sanda ta gama tura wa kafin ta miƙa mata wayan. Sai da ta jira suka tafi tana ɗaga musu hannu kafin ta juyo cikin gidan. Da ɗan tazara tafiyan, ahankali take taka wa tana latsa wayan ta, inda take karanta text ɗin da Ƙalbyn ta ya turo mata, tana sakin murmushi cike da nishaɗi, har sanda ta iso cikin gidan, ta hau Lifter ya wuce da ita sama. ɗakin ta takoma ta shiga Toilet tayi wanka kafin ta ɗauro alwala, kayan ta ta saka farar less mara nauyi tamkar yadi, doguwar riga akayi mata fitet amma me guntun hannu, sai ta tufke gashin ta ta saka hula Robber ja, ta ɗaura Hijab tayi Sallah, sai da ta gama ta cire ta ɗauki wayan ta tafito parlour'n sama, anan ta haɗu da Farida da yaran ta tana buɗe musu Chocolates suna sha
"My guys how far?" RAUDHA tayi maganar tana murmushi bayan da ta ƙariso wajen su
Nan suka tashi suka nufo ta, sai ta soma ba ma Abdul hannu suka cafe, sai kuma ta miƙa wa Haneep da ya miƙo mata nasa yana dariya da zilalar da yawu
Murmushi tayi ta saka nata hannun cikin nasa, sannan ta sumbaci goshin sa ta ce, "My Daddy , I love you so much".
Washe baki yayi cike da murna, cikin muryan sa da ba ya fita maganar sosai ya ce, "I lobi u Baby".
Shima wai yayi irin na Suhaib da yake kiran ta Baby
Sai suka saka mishi dariya daga ita har Farida dake kallon su
"Wow My Daddy wa ya koya maka faɗan suna na?"
Abdul yayi saurin cewa, "Aunty ai yaji Daddy na faɗa miki ne, kuma yanzu yace mu kira ki, sai ya ce miki i love You Baby, shi ne shima ya faɗa, but be iya sanar da ke sauran ba".
Murmushi RAUDHA tayi ta shafa kan Abdul tana faɗin, "kai kuma me wayau ga shi ka faɗa".
Ya washe baki yana tsalle
Still murmushin tayi; tayi musu peck a kumatu, sanan ta shafa kansu, ta miƙe tana kallon Farida tace, "Aunty bari in zo".
Tashi za su yi su bi ta, sai Farida ta riƙe su tana ce musu "su zo ta gama ɓare musu biscuits and Chocolates ɗin".
RAUDHA tuni ta bar wurin, ta Steps ta nufi ƙasa, a hawa na biyu ta tsaya ta shiga parlour'n don duba Daddy, don tasan baza su wuce suna nan ba dukan su. Tana shiga wani ƙamshi ya doki hancin ta, lumshe ido tayi tana buɗe wa, tabbas kamar ta taɓa sanin me turaren nan, kamar ta taɓa jin sa a wani waje, amma aina? Wurga idanu ta soma yi cikin parlour'n. Can ta hangi mutum saman kujera, sai dai bayan sa take hanga tunda kujeran da ya zauna a kai ya juya wa ƙofa baya ne
Kamar ta wuce sai kuma wani zuciyan nata ya bata umarnin zuwa ta ga ko waye, domin dai tana ji a ranta ta san koma waye ne, kuma farin sani tunda turaren sa ya tabbatar mata da hakan, amma kuma ta kasa tuna inda ta sani. Takowa tayi ta nufo wajen
Kasancewar bata da takalmi a ƙafafuwan ta sai Socks, shiyasa Rayyan be San da zuwan ta ba, ya ƙuƙe sai kallon zafafan hotunan ta da ta turo masa yake yi, yana zuba murmushi
Gab ta kusa isa wajen, inda ƙiris ya rage ta hangi abinda yake yi a wayan, sai ya juyo da sauri, sabida ajikin sa sai da yaji kamar da mutum a wajen, kuma take yaji ƙamshin turaren ta ya bugi hancin sa.
Haɗa idon da suka yi, sai ta tsaya cakkk tana bin sa da kallo, ƙure sa da idanu kawai tayi ta kasa tunanin komi
Haka zalika shima idanun ya zuba mata, yana kallon ta cike da tsantsan ƙauna a idanun nasa, tare da tsatsan kewar ta gami da muradin ta cikin ransa. Komi nata ya sauya fiye da Da, ta sake girma da tsananin kyau.
[3/23, 3:29 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Isma'il_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*SHAR'ANTATTUN SALLOLI*
```A dukan mazhabobi sallolin da aka shar'anta sun kasu kashi biyu ne, farilla da nafila. Amma shi kuwa Abu Hanifa ya ce uku ne: farilla, wajiba da nafila. Ita farilla ɗin ta kasu biyu.
_1. Farlu aini._ Wannan ita ce sallar da take kama baligi kansa, ba wani da zai iya ɗauke masa yinta, kamar dai su sallolin nan biyar da sallar juma'a.
_2. Farlu kifaya._ Ita ce sallar da take kama baligi, amma idan wani ɓangare na mutane suka yi ta, ta faɗi ga sauran jama'a, misali sallar jana'iza. Idan sashin mutane kuwa ba su yi ba, jama'a duk sun yi laifi.
A mazhabar Abu Hanifa wajibi kashi biyu ne:
_1. Wajibi don kansa-_ watau abin da wajabcin sa bai dogara akan wani abu daban ba, kamar sallar wuturi da sallar idi da sujadar tilawa.
_2. Wajibi don wani abu-_ wannan shi ne abin da wajabcin sa yake dogara ga wani abu daban, kamar sujadar rafkannuwa da raka'o'in ɗawafi da bakantacciyar sallah da ramakon sallah wadda ta ɓaci. Watau, sujadar rafkannuwa ba ta wajaba sai don rafkanar wani abu a cikin sallah. Su kuma raka'o'in ɗawafi ba sa wajaba sai don ɗawafi, bakantacciyar sallah ma ta wajaba ne saboda bakance. Ita nafila kuwa ramakon ta bai zama farilla ba sai da ɓacin tun farko.
A mazhabobin maliki da shafi'i da Hambali nafila ita ce duk abin da yake ba farilla ba. Watau, abubuwan da Hanifawa suke ɗauka wajibi ne don kansu, a wurin sauran mazhabobi suna cikin sunna ko mustahabbi sabida cewa wajabcin ba don zatin su ba ne, illa dai sabuban da aka ambata.
Ita nafila ɗin an kasa ta gida biyu:
_1. Nafila mu'akkada,_ watau wadda aka ƙarfafa sunnancin ta, kamar su sallolin idi da wuturi da raka'o'in ɗawafi, waɗanda Hanafawa suke kira wajibi.
_2. Nafila wadda ba mu'akkada ba,_ watau wadda ba a ƙarfafa sunnancin ta ba, kamar su nafilolin da ake yi gabanin azahar ko bayanta, da waɗanda ake yi gabanin la'asar da bayan magriba da kuma gabanin isha'i da bayan ta.
Allah yasa mu dace.```
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON FORTY TWO*
_______📖 Yanda take jin wani iri da kallon ƙwayar idanun sa, hakan yasa tayi saurin ɗauke kai daga kallon sa, a lokaci ɗaya ta taɓe baki don bata yi tunanin shi ɗin zata gani ba, tun barin ta Abuja rabon ta da shi, sabida koda ya zo Hospital gaishe ta sanda tana jinya, ba ta sanin kowa. Sosai ya sauya mata fiye da tunanin ta, ba don ta sanshi sosai ba baza ta iya gane sa ba, ya sake ƙiba da ya ƙara masa kyau matuƙa, ga haske da ya sake wanda kowa ya kalle sa zai san hutu ya zauna masa, ya sha aski da yayi masa kyau ya sake fito da shi, kasancewar ba hula a kansa, yana sanye cikin faran gezna shara-shara, har Singlet ɗin da ya saka a ciki ana gani. Yanzu bata san meyasa ba, kaso sittin a cikin ɗari na daga tsanar da tayi masa a baya, yanzu kuma sai taji babu shi, ya ragu sosai.
Juya wa tayi zata bar wajen, sai ta tsinkayi muryan sa da yasa ta sake tsaya wa cakk, zuciyarta ta na wani irin bugawa da ƙarfi, sakamakon sunan da ya kira ta da shi. Dasauri ta juyo tana kallon sa
Shima idanun sa akanta suke, sai ya saki murmushi ya sake cewa, "pretty babu gaisuwa?"
Waro idanuwan ta waje tayi, sosai zuciyar ta take tsananin bugawa a yanzu ɗin, domin kuwa the same sunan da Ƙalby ɗin ta yake kiran ta da shi ne, ita in ba ma makuwa tayi ba, muryan sa na mata shige da muryan sa. Ji take yi tamkar tace ya sake maimaita sunan, sai kuma tayi dauriya tana kau da idanun ta daga kallon sa, ta sake juya wa tayi hanyar ɗakin Daddy.
Da kallo Ray ya bi ta da shi, yasan sarai abinda ke cikin ranta, don haka tuni ya saki murmushi zuciyar sa cike da farin ciki.
Har ta kusa ƙule wa, sai Suhaib da ya shigo yanzu ya kira sunan ta. juyo wa tayi tana kallon sa, sai kuma ta tako tana faɗin, "Yaya ina kuka shiga, ina neman ku? An ce kaima kana nema na".
"Eh Baby, dama Dude ne ya zo musamman don taya ki murna, shine na ce bari in Kira ki ku gaisa. Dude ga Baby ɗin; ko kun gaisa?" Suhaib ya sauya akalan tambayar nasa ga Rayyan yana kallon sa
"Yaya mun gaisa". RAUDHA tayi saurin faɗar maganar idanun ta kan Suhaib tana murmushi, tana juya wayan hannun ta
Murmushi shima yayi ya ce, "ok mu je mu zauna to, yanzu Daddy zai shigo ya sauka downstairs raka baƙin da yayi ne".
Gyaɗa kanta tayi, suka nufi inda Rayyan ke zaune, Suhaib ya zauna gefen sa, ita kuma ta zauna can kujeran dake kallon nasu, zata yi magana kenan taji shigowar message a wayan ta, ɗagowa tayi tana karanta wa
_"Pretty kin Yi matuƙar kyau fiye da ko yaushe, har kin saka naji na ƙosa na mallake ki a matsayin matata, wlh pretty ina son ki, ƙaunar ki zai zauta Ni, ji nake yi kullum kamar ana ƙara min wutan ƙaunar ki a raina, I love You so Much my pretty"._
Murmushi kawai take zuba wa, sabida sosai message ɗin yayi mata daɗi. Itama sai ta soma typing don mayar masa da reply.
Ray dake hira da Suhaib, hankalin sa na gare ta, ta ƙasan ido yake kallon ta, ta yanda babu wanda zai fahimci yana kallon ta.
Tun tafiyan ta ƙasar Madina, hankalin Rayyan ya tashi matuƙa, gani yake yi gaba ɗaya ya gama rasa ta, shi da yake burin da zaran ta samu lafiya, ya bayyana mata ƙaunar da yake mata, sai gashi wai zata tafi karatu, hakan ya saka sa damuwa tsantsa. Haka ya danne wa ransa yaci gaba da al'amuran sa, sai dai ya rasa ta ya ya zai samu gana wa da ita ko da ta waya ne kamar yanda yake tura mata saƙo, tunda tuni ta dena amfani da wayan ta, anan Abuja ma ta bar shi, kuma da ta tashi tafiya sai dai aka siya mata wani, ga shi ba shi da Numban ta, ya rasa ya zai yi ya samu, ba ya son tambayan Suhaib kar ya zargi wani abu.
Ahaka dai Allah ya basa Sa'a, inda watarana suna zaune suna hira da Suhaib ɗin, ya ce "ya ara masa wayan sa zai tura wani abu" to anan ne ya lalubo Numban ta na can yayi saurin kofe wa.
Tun daga ranan Ya samu damar waya da ita, da fari text ya soma tura mata, ita kuma lokacin da ta gani, ta sha mamaki kasancewar yayi mata bayanin shine Masoyin ta da ke tura mata text a baya. Ta so ta share sa, sai kuma mamakin abun ya ƙi barin ta, tambayan da ta soma masa, "shin aina ya ƙara samun Numban ta? Kuma taya ya san ba ta ƙasar Nigeria?"
Shi kuma be bayyana mata komi ba, sai ya ce mata "duk inda take a faɗin duniya, idan har yana numfashi, to tabbas sai ya lalubo ta, ƙaunar da yake mata ya wuce tunanin ta".
Hakan sai ya saka ta shiga tunani tsantsa, tana tunanin shin wanene shi? Aina ya santa? Tunani kala-kala take yi a kansa. Kuma tun daga ranan bata sake mishi reply ba, duk da kuwa tana karanta saƙon sa, sosai yake saka ta tunani duk idan ta gama karanta saƙon sa, sabida kalaman sa ba ƙaramin taɓa mata zuciya yake yi ba, da haka ya soma kiran ta wai "yana son jin muryan ta". Tun bata ɗauka, har dai ta soma ɗauka, inda ta sha mamaki, domin kuwa muryan sa sak yayi mata kama da wanda ta sani, sai dai ta rasa aina? Koda wasa bata taɓa kawo cewa Captain Rayyan bane, to taya ma zata yi tunanin hakan bayan ta san ba sa shiri, ya tsane ta itama ta tsane shi, ita ta manta da shi ma tuni.
Haka rayuwan taci gaba, inda Rayyan be ƙasa a gwiwa ba wajen yin nasaran sace zuciyar RAUDHA, sai dai fa ya sha matuƙar wahala, domin sai da ya dage da gaske, da jure duk wani wulaƙanci nata kafin yaci nasara, don da farko ma har block ɗin sa ta koma take yi, sai ya sauya sim ya sake neman ta. Sosai take mamakin naci irin na mutumin da bata ma sanshi ba.
Kusan shekaru biyu da zuwan ta ƙasan, sannan ta amince ta karɓi soyayyar shi, don tuni ta saba dashi fiye da tunanin mutum, tabbas RAUDHA tana da wuyan sha'ani, babu wanda yake iya shiga jikin ta ta daɗi, tana da wuyan sabo, idan kuma ta saba da kai, tana baka yardan ta ne ɗari bisa ɗari, idan tace tana sonka, to tana son ka ne har cikin zuciyar ta.
Sun saba sosai matuƙa, koda yaushe suna tare maƙale a waya ko a chart, idan tana school zata ijiye duk wani soyayyar sa a gefe, shima haka idan yana aiki be cika takura mata ba, ahaka dai rayuwan taci gaba, inda sosai RAUDHA ta tsunduma a soyayyar Rayyan batare da ta san waye shi ba, kuma bata taɓa tambayan sa don ta sani ba, ba wai don ba ta son sani ba, a'a, sai don shi be bayyana mata kansa ba, ita kuma jan aji da miskilanci irin nata, ya hana ta tambayan sa, musamman ya buɗe sabon account na facebook suke charting, ko su yi a WhatsApp da Numban sa personal, Wanda don ita kaɗai yake amfani da shi, ko kuma su yi ta inbox message.
Haka rayuwan taci gaba da gudana, har sanda ya nemi ta tura masa hotunan ta, sabida yana matuƙar kewar ta yana son ganin ta. Anan ne tayi masa maganar itama tana son sanin shi, tana nufin ya faɗa mata komi a kan sa. Amma sai yayi mata daɗin baki inda ya ƙi yin mata duk abinda ta buƙata. Ita dai ta tura masa pictures ɗin ta, kuma bata sake tambayan sa ba tunda ta lura ba ya son ya nuna mata kanshi ne, har ga Allah ta yarda dashi ɗari bisa ɗari, kuma tana ƙaunar sa, ta saka a ranta ko waye shi zata iya auran sa. Dama akace duk wanda be taɓa soyayya ba, idan har ya tashi yi ba ya ɗaukar ta da wasa, tabbas haka ne a wajen RAUDHA, domin mahaukacin so take yi wa Rayyan, gaba ɗaya ta ɗau yardan ta ta ba shi, a cikin duk wanda ya san ta babu wanda be san labarin sa ba, su Daddy tuni sun san da irin ƙaunar da take mishi, sun buƙaci ganin sa amma sai tace musu watarana zasu gansa kamar yanda shima yake sanar mata, itama hakan ta sanar musu, sunan sa kawai ta gaya musu, inda yace mata sunan sa Muhammad. Yayi mata alƙawari duk sanda ta gama karatun ta, idan ta dawo Nigeria za su haɗu.
🌐🌐🌐
Shigowar Daddy ya saka RAUDHA ta ɗago kai tana kallon sa, sai kuma ta ajiye wayan tana tashi ta nufe sa tana kiran sunan sa
Tarban ta yayi yana murmushi, inda ya shafa kanta ya riƙe hannun ta suka dawo suka zauna a inda ta tashi
Anan Rayyan ya gaishe shi, ya amsa cike da fara'a yana tambayan sa aiki kafin ya ce, "nayi mamaki, wai yaushe ka shigo ƙasar?"
Dayake tuni an sake musu sauyin wajen aiki, dama shekara uku za su yi a Abuja, sai su dawo Kaduna inda anan ne dama yake aikin sa, to sun samu hutu sai ya tafi ƙasar su Bayelsa, sai yau ya dawo, kuma ya hana kansa sukuni sai da ya shigo Zaria don ganin muradin ransa.
"Daddy yau na shigo".
Jinjina kansa Daddy yayi yace, "Weldon Captain kana ƙoƙari wlh, ya mutanen gida, ɗazu muna magana da Mahaifinka sai kuma muka katse akan ana jiran sa, zamu yi waya anjima, kuma ka ga hidima ya mantar dani ban sake kira ba, shima be kira ba".
Murmushi Rayyan yayi yace, "lafiya ƙalau suke, amm. Uncle babban surprise ne da shi, duk da ban yi tunanin zai sanar maka ba, ya bari zuwa Friday, Coz ranan Saturday za su shigo gaba ɗaya".
"Haba dai? Are You serious?" Daddy ya faɗa cikin fara'a
"Yes Daddy".
Take anan shi da Suhaib suka nuna matuƙar farin cikin su
Ita dai RAUDHA tana jin su bata ce uffan ba, sai faman taɓe baki take yi tana kallon Rayyan da shima ke kallon ta ta ƙasan ido
"Baby kina ji Uncle ɗin ku zai zo, baki taya Ni farin ciki ba?"
Yaƙe tayi tace, "Daddy I'm so happy, Allah ya kawo su lafiya".
"Emeen Baby".
Hira suka ci gaba da yi. Inda RAUDHA ta bar su tana ta faman latsa wayan ta, don bata san ma me suke cewa ba.
Sai ga Farida itama ta shigo ta zauna cikin su, lokacin su Abdul duk sun barci.
Ba su tashi ba sai da aka kira isha'i.
Bayan sun dawo suka yi dinner a parlour'n ƙasa, inda Rayyan yace musu zai wuce, don shi be damu da tafiyan dare ba, kasancewar sa jami'in tsaro
But Sam Daddy ya ƙi barin sa, dole yace masa sai ya kwana, in yaso washe gari sai ya tafi da wuri
Be musa masa ba kuwa, anan ɗin ya kwana, washe gari zuwa ƙarfe 08:30am. Yayi sallama da su ya tafi, ya so ganin RAUDHA sai dai be samu dama ba, domin dai tana can tana barci, kuma ba ya kyautata zaton zata iya tashi yanzu don yasan halin ta sosai.
Sai ƙarfe 12:40am ta farka kuwa.
Zuwa dare su ma su Suhaib suka wuce Abuja, inda suka bi jirgi.
[3/23, 7:33 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
𝐑𝐀𝐔𝐃𝐇𝐀
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
𝐌𝐀𝐋𝐋𝐀𝐊𝐀𝐑: ✍️
𝑁𝑎𝑓𝑖𝑠𝑎𝑡 𝐼𝑠𝑚𝑎'𝑖𝑙 𝐿𝑎𝑤𝑎𝑙 𝐺𝑜𝑚𝑎.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
𝐅𝐄𝐄𝐍𝐀𝐇 𝐖𝐑𝐈𝐓𝐄𝐑'𝐒 𝐀𝐒𝐒𝐎📖
®Ɗ𝚊𝚢𝚊 𝚝𝚊𝚖𝚔𝚊𝚛 𝚍𝚊 𝙳𝚞𝚋𝚞💪✓
𝗝𝗜𝗞𝗔𝗥 𝗟𝗔𝗪𝗔𝗟𝗜 𝗖𝗘✍️
𝗪𝗮𝘁𝘁𝗽𝗮𝗱: 𝗨𝗺𝗺𝘂𝗗𝗮𝗵𝗶𝗿𝗮𝗵👈
\𝗙.𝗪.𝗔📚/
𝐑𝐀𝐌𝐀𝐃𝐇𝐀𝐍 𝐌𝐔𝐁𝐀𝐑𝐀𝐊𝐇🤲🏽🕌
2021.
.
𝗡𝗢𝗧 𝗘𝗗𝗜𝗧𝗘𝗗 ___________________________📗
𝗦𝗘𝗔𝗦𝗢𝗡 𝗙𝗢𝗥𝗧𝗬 𝗧𝗛𝗥𝗘𝗘
_______📖 Washe gari ƙarfe 11:00am. RAUDHA ta tashi, bakin ta kawai ta wanke ta ɗauraye fuska ta fito Parlour, part ɗin Daddy ta wuce, sai dai bata same shi ba, sai ta tambayi ɗaya daga cikin ma'aikatan dake gyara Part ɗin, suka ce mata "ya fita ne"
Ɗakin ta ta koma ta ɗauki waya ta kira sa, nan yake sanar mata "ya fita, but bazai daɗe ba zai dawo". Sake fitowa tayi da wayan a hannun ta, inda ta kira ɗaya a cikin masu aikin ta bata umarnin kawo mata Breakfast ɗin ta saman
Bata jima ba kuwa ta haɗo mata
zama tayi saman dainning tana ci tana latsa wayan ta. Kamar shuɗewar mintuna ashirin sai wata acikin masu aikin ta shigo take sanar mata tayi baƙi. maimaita kalman baƙin tayi a fili, idanun ta kan ƴar aikin, sai kuma tace, "su wane ne?"
"Ranki ya daɗe wasu samari ne su biyu".
Shiru RAUDHA ta sake yi zuciyarta cike da mamaki, kafin kuma tace, "ok CE musu su jira Ni, ki sauke su parlour'n ƙasa".
"To ranki ya daɗe". Tayi maganar cikin girmamawa tana juya wa don isar da saƙon ta
RAUDHA ci gaba tayi da harkan ta, tamkar bata san jiran ta ake yi ba, sai da ta ɓata time kafin ta miƙe tsaye, wayan ta ta ɗaga tayi Selfie 🤳 tana turo baki gaba, sannan sai ta shiga WhatsApp ta tura wa Rayyan, a ƙasan ta rubuta, "Good morning Ƙalby, I Love you xoxoxo" ta saka emojis na love ta tura masa".
Murmushi tayi kafin ta kama hanyan barin parlour'n, ko kaɗan bata yi tunanin sauya kayan jikin ta ba, tana sanye cikin kayan barci riga da wando masu santsi, kalan ruwan Powder, wandon Three qwater ne amma burgujeje tamkar skert, sai rigan ɗan shimi me hannun vest da kwalliyan bakin leshi a gaban, kanta da baƙin hula me raga-raga, ƙafanta kuma babu takalmi sai Socks
Duk da yanzu ba ta fita da irin shigan nan, amma har yanzu bata dena yin sa ba in dai a gida ne.
Lifter ta hau ya kai ta ƙasa. Tana sauka ta shiga cikin parlour'n
Zulain da Sharif dake zaune, suka hange ta tana nufo su, sai gaba ɗayan su suka ƙura mata idanu, ko wanne a ransa yana yaba tsantsan kyan da Allah yayi mata, gaba ɗayan su ganin dirin jikin ta sai da ya tafi da duk natsuwar su. har ta iso wajen ta zauna kan sofan dake kallon su, ta ɗaura ƙafan ta ɗaya kan ɗaya tana bin su da ido, amma su gaba ɗaya hankalin su ya fita jikin su
Itama sai da ta gama ƙare musu kallo, musamman Zulain ganin sa da tayi Bature, duk da kasancewar sa ba fari ba, domin ko kama ƙafan hasken ta be yi ba, amma kuma gashin kanshi fari ne irin na turawa, da ganin shi dai kasan Bature ne shi. Taɓe baki tayi kafin tace, "ku ne kuke nema na?"
Sai a time ɗin suka dawo hayyacin su, yayinda duka suka yi murmushi, Zulain na shirin magana wayan ta ta soma ƙara
Ɗago wayan tayi tana kallo, sai ta saki murmushi tana peacking Call ɗin ta kara a kunne, sai a time ɗin ne ta kalle su ta ɗaga musu hannu alamun tana zuwa, "Hello Ƙalby". Tafaɗa still tana murmusawa
Daga Zulain har Sharif kallon ta kawai suke yi, babu wanda yake jin abinda take faɗa kasancewar ta juya harshe zuwa larabci ganin suna kallon ta. Zulain in ban da Hello ɗin da tace ba ya jin komi, haka shima Sharif, gwara shima Ƙalby ɗin da ta faɗa ya gane me take nufi, a ransa ya ce, "lallai kam! wannan yarinya anya ba mu kawo kan mu inda za'a wulaƙanta mu ba?" (A raina na ce da sauƙi dai Sharif, da abaya kazo ina tunanin baza a baka wurin zama ba bare a kalle ka na arziƙi, ko ba haka ba Fans?🤣)
Duk abinda take yi sosai take ƙara shigan zuciyan Zulain, be taɓa ganin yarinyan da ta burge shi irin ta ba, duk da kasancewar sa bature amma wayewar ta sosai ya burge sa, ba ta da maraba da su. Be dena tunanin ba har sanda ta gama wayan
Ta kalle su tana faɗin, "afuwan na tsai da ku ko? I'm sorry".
"No problem Cuty, girman ki ne ai". Zulain ya faɗa yana murmushi
Itama murmushin tayi idanun ta akansa tace, "ok me ke tafe da ku?"
"Soyayya". Cewar Zulain still yana murmusawa
Ɗan waro ido tayi, sai dai bata kai ga magana ba yaci gaba da faɗa mata yanda ya kamu da tsananin ƙaunar ta, ko kaɗan babu ɓoye-ɓoye a lamarin shi, tunda dama su turawa ba kunya suka cika ba
Har ya dire maganar shi RAUDHA kallon shi take yi, a rayuwan da tayi a Madina ta samu mutanen da suka sha sanar mata suna ƙaunar ta, sai dai yanda ta ƙi ba su dama ne, yasa dole suka haƙura. tuni Ƙalby ɗin ta ya sace mata zuciya, kuma ba ta tunanin koda da wasa zata iya haɗa soyayyar shi da wani, duk da tana ganin waɗanda suka burge ta matuƙa, musamman ma yanzu Zulain ɗin nan, sosai taji a ranta yayi mata, ya haɗa komi ne wanda ɗiya mace idan ta ganshi dole ta so shi...
Shigowar Daddy da sallaman shi, shi ne ya katse musu gaba ɗaya tunanin su, wanda Zulain da Sharif sun tsaya ne su ji amsar da zata ba su, yayinda ita kuma ta faɗa kogin tunani
Miƙe wa gaba ɗaya suka yi har RAUDHA, su Sharif suna masa sannu da zuwa
Sai a time ɗin ne ma ya gane su, nan da nan ya washe baki yana faɗin, "a'ahh ku ne ashe? Sharif and Zulain ko?"
Murmushi suka yi suna amsa mishi da "Eh".
"To ku zauna mana, Sannun ku da zuwa".
Zama suka yi kamar yanda ya ba su umarni, shima ya zauna akan sofa, inda itama RAUDHA ta koma ta zauna
"My daughter ko wajen ki suka zo ne?" Daddy ya tambaye ta yana murmusa wa
"Na'am Daddy". Ta amsa mishi tana murmushi
"Ok Masha Allah, bari in Baku waje to?" Yayi maganar da fara'a yana shirin tashi
Sai ta langaɓe kai tana cewa, "Daddy da ma kayi zaman ka".
"No daughter, KU dai gama maganar ku, in ya so sai ki kira Ni daga baya mu gaisa sosai".
Gyaɗa masa kai kawai tayi, shi kuma ya wuce ciki.
Kallon su tayi tace, "ku daure ku ci wani abun mana, ga shi baku taɓa komi ba?"
Murmushi Zulain yayi yace, "no ba ma buƙatar komi ɗin ne a yanzu, illa amsar ki, ki daure ki sanar da Ni abinda ke zuciyar ki ko da nima tawa zuciyar zata samu sukuni daga zugin da ta daɗe tana min".
Sharif Ya amshe zancen da faɗin, "Please RAUDHA, ɗan uwana na matuƙar ƙaunar ki fiye da yanda kike zato, tun haɗuwar da kuka yi a airport ya kamu da soyayyar ki. A taƙaice dai ya kasa samun sukuni tun zuwan sa ƙasan nan, sai kuma Allah yasa bazai sha wahala ba, ya haɗu dake cikin sauƙi anan gidan, ina ga Allah ya ƙulla wani alaƙa a tsakanin ku ne shiyasa har ya sake haɗa ku batare da ya sha wahala haka ba, ki duba magana ta RAUDHA, Zulain na ƙaunar ki matuƙa".
Murmusa wa tayi sabida maganar Sharif ɗin, idanun ta a kansu tace, "eyya gaskiya ban san me zan ce muku ba yanzu, amma dai zan iya sanar muku da cewa na rigada na ba wa wani.."
Katse ta Sharif yayi da faɗin, "ba sai kin faɗa ba RAUDHA, don Allah ki dai ba wa Ɗan uwana dama ko sau ɗaya ne, ta hakan ne kaɗai zaki fahimci wanene shi, kuma zaki so shi wlh, domin shi ɗin na daban ne, ba ko wace mace take samun Sa'a wajen mallakar irin su ba".
Wannan karon dariya RAUDHA tayi tace, "uhmmm Sharif kenan! Na ga alamu kana son ɗan uwanka da yawa ko?"
Murmushi duka suka yi
Jinjina kanta tayi tace, "amma Ni ba na so mu ja zancen da tsawo haka, ina da Masoyi na, ina son shi yana so na, so babu amfanin mu ɓata lokaci akan abinda bazai yiwu ba".
Lumshe ido Zulain yayi, sai kuma ya buɗe akanta, cikin ido suke kallon juna ya ce, "I love You RAUDHA, bazan iya haƙura da ke ba har sanda na ga kin zama mallakin wani, ma'ana an ɗaura miki aure. Yanzu ma na soma son ki, idan har baki kore Ni ba, Ni kuma zan ci gaba da gwagwarmayan samun ki har sanda Allah zai yi ikon sa".
Kau da kanta tayi, sai dai bata iya cewa komi ba, sai ta tashi tana faɗin, "bari in Kira muku Daddy".
Ta juya ta tafi abun ta.
Koda ta kira musu Daddy, ɗakin ta ta wuce bata sake bi ta kansu ba, don bata san ma sanda suka tafi ba. Sai da Daddy ya kira ta sannan ta fito, anan yake tambayar ta "me suka zo yi wajen ta?" Ta sanar mishi da komi tunda babu ƴar kunyan haka a tsakanin su
Murmushi Daddy yayi yace, "Baby in baki shawara?"
Gyaɗa masa kai tayi tana cewa, "Yes Dad".
"Ok gaskiya yaron nan yayi matuƙar dacewa da ke, ki daure ki duba son da yake miki kar ki yi watsi da shi akan wani".
Murmushi tayi idanun ta akan sa tace, "Daddy kai ma kasan ina da saurayi na, ban ga abinda zai saka na ɓata lokaci na kan wanda bazan taɓa son shi ba idan har Ƙalby na tare dani. So Daddy Kar ma su biyo ta hannun ka su ba ka cin hanci ka ce shi zan aura".
Waro ido yayi yana dariya yace, "Baby?"
"Yes Daddy." Tafaɗa tana dariya itama
Shafa kanta yayi yace, "ki dena maganar haka kin ji Baby na? Domin wanda kike so shi nima nake so, duk wanda kika kawo a matsayin Mijin ki, shi ne zai kasance Mijin ki, ba zan taɓa baki wanda ba ke ne kika kawo ba".
Dariya tayi tana ɗaura kanta saman kafaɗan sa tace, "Daddy Nima Wasa nake maka fa".
Hancin ta ya ja yace, "i know Baby, but yaushe ne zaki kawo min suruki na in ganshi, yakamata kema ki zo kiyi auren nan ko da nima zan soma ganin Jikoki na ta wajen ki".
Ƙyalƙyale wa tayi da dariya tana cusa kanta a hannun sa tace, "Daddy".
"Umm Babyn Daddy, ai gaskiya na faɗa".
Murmushi kawai tayi bata yi magana ba
Shima sai be sake cewa komi ba ya sauya maganar suka ci gaba da hira.
[3/23, 7:48 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Ismail Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
```®Ɗaya tamkar da Dubu```💪✓
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
2021.
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON FORTY FOUR*
_______📖 Daddy ya saka ana ta shirye-shiryen tarban iyayen Rayyan da za su zo, an gyara musu ɗakunan ƙasa da ba a amfani da su, duk wani abubuwan jin daɗi ya saka an zuba musu
Alh. Hassan da suke kiran sa da Uncle Hassan, shine Abokin Daddy. Asalin Abotan su ya fara ne sanda Daddy yayi zaman Bayelsa yin wani course, to anan suka haɗu da Uncle Hassan Wanda gaba ɗaya ahalin su sunan da suke kiran sa da shi kenan, tun yana ƙarami, kasancewar sunan Kawun sa shima ya ci, to lokacin da aka haife sa a lokacin ne Kawun nasu ya rasu, shiyasa da aka mayar da sunan Kawun shi ne suke kiran sa da Uncle Hassan kamar yanda suke kiran Kawun, har Allah yasa ya girma da sunan ake kiran sa, yanzu haka har iyalan sa duk Uncle suke kiran sa, su Rayyan ba sa kiran sa da Baba sai dai Uncle.
Kasancewar Daddy yana yawan zuwa gidan su Uncle Hassan, anan kusa da gidan su ya haɗu da mahaifiyar su RAUDHA, suna maƙotaka ne da gidan su Uncle Hassan, inda babu ɓata lokaci soyayya me ƙarfi ya shiga tsakanin su, koda ya tashi aure sai Allah yasa ita ɗin rabon sa ne, a time ɗin iyayen sa suna raye, har can suka je nema masa auren Ruƙayyah, inda aka ba shi babu wani ja'inja
Anan Zaria suka soma zama, cikin ƙofan doka, Allah da ikon sa rayuwa taci gaba da gudana, inda a gefe ɗaya suna Abotan su sosai da Uncle Hassan, shima be daɗe ba yayi aure a can Bayelsa
Babu jima wa Matan nasu suka haihu a tare, inda yaran suka ci sunan Rayyan da Suhaib. Haka rayuwa taci gaba da gudana, Ruƙayya dai bata sake haihuwa ba, sai matar Uncle Hassan Hansa'u da ta haifi Umar Faruk, suna kiran sa da Faruk tunda sunan mahaifin ta ne, wani lokacin kuma su kira sa da Abba, daga shi kuma sai Usman da suke kiran sa da Zannurain, sai kuma Abubakar autan su, shi ne sa'an RAUDHA, an haife shi babu daɗe wa aka haifi RAUDHA, shekarun ta biyar a duniya Ruƙayya ta rasu a wajen haihuwar ƙanwar ta, lokacin tana cikin naƙuda, domin har ta kusa haihuwa, da ita da abun da ke cikin ta gaba ɗaya suka koma ga Allah saboda ta sha wahala a lokacin. Wannan dalilin ne Daddy da Suhaib suka ɗauki son duniya suka aza wa RAUDHA, ga tsaban tausayin ta da suke ji.
🌐🌐🌐
Drever yaje ya ɗauko su a airport sanda suka sauka, suna iso wa Uncle da Daddy suka rungume juna, ko wannen su cike da farin cikin ganin Abokin sa, domin sun jima rabon da su haɗu sai yanzu, shiyasa Uncle Hassan ya shirya zuwa gaba ɗaya har iyalan sa
Sai da suka daɗe suna gaisa wa cike da barkwanci kafin suka samu wuri suka zauna, inda su Faruk ɗaya bayan ɗaya suka hau gaishe shi. Ya amsa musu cike da fara'a yana tambayan su school da aikin su. Sannan suka gaisa da Ammee cikin mutunci
Uncle ne ya soma tambayan RAUDHA, kasancewar shi kaɗai ya san ta, ita kanta Ammee tun tana yarinya rabon da ta sake ganin ta
Daddy na murmushi yace, "yanzun nan zata dawo, ta je gidan ƙawar ta ne (Ramcy)".
"To Masha Allah, Allah ya dawo da ita lafiya".
"Ameen ameen". Daddy yafaɗa still yana murmusa wa. sai kuma ya kalli su Faruk ya ce, "Abba sai kuma ga ku a Nigeria ko?"
Dariya suka yi gaba ɗaya, inda Abubakar yayi tsalan ɗin cewa, "wlh kuwa Daddy, wannan shi ne zuwa ta na farko ƙasar ku, ashe dai yana da daɗi".
Daddy dariya yayi yace, "sosai ma Habu, ai zan sa a zaga da ku zaku fi jin daɗin garin sosai".
Duka suka yi dariya
"Ya kamata Ku yi wanka ku huta, bari in saka a nuna muku masaukin ku". Daddy ya faɗa yana kallon su da murmushi
Gyaɗa masa kai suka yi, don su ma sun fi buƙatar hakan
Daddy da kansa ya nuna musu, be ma bari an nuna musu ba, har Ammee itama ɗaki ta wuce, inda Daddy ya dawo suka ci gaba da hira da Uncle suna ta dariya, babu abinda suke yi sai tuna baya, idan sun tuno abinda yayi musu daɗi da ba su dariya har kashe hannu suke yi.
A lokacin ne RAUDHA ta shigo gidan
Daddy na ganin ta yace, "yauwa Baby kin ga har su Uncle ɗin ki sun ƙariso baki dawo ba, sai tambayan ki yake yi".
"My daughter ƙariso mana". Uncle yafaɗa yana nuna mata kusa da shi
Da murmushi a fuskar ta ta ƙariso wajen sa ta zauna, sannan ta gaishe sa cikin mutunci sosai
Hakan sai ya faranta ran sa, ya saka hannu a kanta yana shafa wa ya ce, "Allah ya miki albarka my daughter".
"Ameen Uncle".
Murmushi yayi yace, "kin girma sosai my daughter, rabo na da ke tun kina ƙarama, amma kuma kina nan a yanda kike, domin ko aina na ganki sai na shaida wannan ɗiya ta ce".
Dariya suka yi daga ita har su ɗin
Anan ne itama Ammee ta fito, ta ƙariso ta zauna idanun ta akan RAUDHA da itama take kallon ta
Kafin ma tayi magana RAUDHA tayi ƙoƙarin gaishe ta, sabida ba ƙaramin kamannin Rayyan ta gani a tare da ita ba, kamar an tsaga kara, wannan dalilin ne yasa ta gane mahaifiyar shi ce
Cikin fara'a Ammee ta amsa ta tana cewa, "taho nan kusa dani mana ɗiya ta in ji ɗumin ki".
Taso wa tayi tana murmushi ta dawo kusa da ita, sosai taji farin ciki da wannan ƙauna da iyayen Rayyan suka nuna mata, har sai da ta tuno sa, a ranta tana cewa, "shi kuwa be da kirki kamar su, ko wa ya biyo oho masa".
Anan ne su ma su Faruk duk suka fito, inda Daddy duk ya gabatar mata da sunayen su
Farin ciki duk ya cika RAUDHA, musamman da tagan su har su uku, sai ta washe baki ta soma ba ma Abubakar hannu wai su gaisa
Sai hakan gaba ɗaya ya burge su har su Ammee, duka suka saki murmushi
Abubakar kuwa hannun ya miƙa mata yana dariya yace, "Abubakar Sadiq your friend".
Gyaɗa kanta tayi tana sake washe baki tace, "ana RAUDHA"
Duk dariya suka sake yi
Sai shima Zannurain ya miƙo mata hannu yana dariya yace, "Ni dai ba friend ɗin ki bane, Yayan ki ne, Ki kira Ni Bro Zannu".
Kasancewar yayi maganar ne cikin barkwanci, duk sai suka yi dariya gaba ɗaya
"Bro Zannu". Itama ta faɗa cikin dishewar muryan ta me daɗi tana murmushi, sannan sai kuma ta kalli Faruk dake tsaye ya harɗe hannayen sa yana kallon ta yana murmushi. Sosai gaban ta ya faɗi sabida ganin kamannin su ɗaya da Ray, har ta Yi tunanin ko shi ne, sai taga kuma wannan be kai shi haske ba, sannan be da jiki kamar shi, Faruk siriri ne sosai
Hannu ta miƙa masa tana murmushi
Sai ya saka nashi shima yana murmushin yace, "kina lafiya?".
"Ana bikhair.. ant?" Tayi maganar idanun ta a kansa tana ci gaba da murmushin ta me kyau
"Ana jayyidan".
Dainning suka wuce gaba ɗaya suka ci abinci, ita dai RAUDHA ba ci take yi ba tana zaune gefen Abubakar suna zuba surutu, sai dariya take yi
Cike da nishaɗi haka suka kasance a ranan har yamma, anan ne RAUDHA taja hannun Abubakar suka nufi bayan gidan, inda anan ne aka saka basketball, da kuma abubuwan Game dai kala-kala
Tare suka soma ƙwallon suna ta dariya, fara wa da iya wa har ya ci ta biyu, nan ta saka mishi rigima wai bata yarda ba
Sai kawai ya faɗi ƙasa yana ta mata dariya, shi kawai dariya ta bashi sabida yanda take shagwaɓan ta tamkar yarinya, baza ka taɓa tunanin ƴar shekara 24 bane
Kaɗa kai tayi, ta zuƙuna ta soma kanannaɗe farar wandon ta, sai ta kama gashin ta ta sake ɗaure shi da kyau, ta tashi tana tsalle tace, "to taso mu ci gaba, yanzu sai na sa ka kayi kuka".
Dariya ya sake kwashe wa dashi.
Daga nesa Faruk na tsaye yana kallon ta yana murmushi, gaba ɗaya RAUDHA ta gama tafiya da imanin sa, salon ta da komi nata burge sa yake yi, yana nan yana kallon yanda suke ƙwallon, duk RAUDHA bata iya ba amma ta dage sai ta ci Abubakar, shi kuma sai saka mata ƙwallo yake yi ta kasa cin ko guda ɗaya, duk ta gama gajiya sai nishi take yi, don daƙyar take gudu ma
Kamar ance ta kalli inda yake tsaye, ta hange shi kuwa ya kafa mata idanu, da gudu ta nufe sa ta ƙariso wajen sa tana nishi, idanun ta a kansa tace, "Plz Brother taimaka min in ci shi, wlh wayau yake ta min duk ya gajiyar dani".
Dariya maganar nata ya ba shi, wai wayau yake mata, bayan bata iya bane
"Kaji?". Tayi maganar tana riƙe masa hannu
Murmushi yayi yace, "wa yace miki na iya? Nima irin ki ne ai".
Langaɓe kai tayi kamar zata yi kuka
Zannurain ne ya ƙariso wajen yana tambayan me ke faruwa
"Yauwa Dear Zannu, zo mu je ka taya Ni cin Friend, ka ga sai cinye ni yake yi".
"Ok mu je". Zannurain yafaɗa yana yin gaba tare da kanannaɗe hannun rigan sa
Faruk dai yana tsaye yana kallon su har sanda suka tashi wasan, sannan ya juya ya bar wajen.
🌐🌐🌐
Washe gari wajen ƙarfe 10:30am sai ga Suhaib ya zo shi kaɗai, lokacin RAUDHA da Abubakar da Zannurain sun fita zaga gari, sai Faruk ne da be bi su ba, time ɗin ma barci yake yi
Uncle rungume Suhaib yayi kafin suka gaisa, ya soma tambayan sa iyalan sa
Yace, "suna gida, sun ce in gaishe ku sosai". Sannan ya gaishe da Ammee
Ta'amsa cike da fara'a itama tana tambayan sa iyalan, sannan tace, "meyasaka baka zo da su ba?"
Shafa kansa yayi yace, "babu komi wlh, nima na zo ganin ku ne ai".
"Ka kyauta ai, amma su ma da kazo da su mun ga juna, tunda ba daɗe wa za mu yi ba, kuma idan mun tafi ba kawo mana su zaka yi har Bayelsa ba". Ammee tafaɗa hakan da fara'a
"Haka ne Ammee, ban yi tunanin hakan ba wlh".
Daga nan hira suka ɗan taɓa, inda Suhaib yake tambayan "ina su Faruk?"
Kafin ma su ba shi amsa, Faruk ya fito daga ɗaki
Ammee tace, "ga Faruk ɗin nan ya fito, su kuma sauran sun fita da RAUDHA".
Faruk gaishe shi yayi, inda ya amsa mishi yana tsokanar sa da faɗin, "har da kai ƙaton kawai aka zo da kai?"
Dariya Faruk yayi yana shafa kansa yace, "ai ban wuce zuwa anguwa ba Yaya Suhaib".
"Eh naga alama, amma ai ka isa ajiye mata, har yanzu shiru da kai da Dude".
Uncle yace, "bar su Suhaib, ai na san maganin su, ina gajiya nima auren zan yi musu, ka ga wannan ƙiri-ƙiri ga matar sa a gida, amma har yanzu sai kwana-kwana yake mana, kuma shi ya amsa yana son ta, amma yanzu kuma yana son Wai ya koma karatu ne, abun dai da yaga ɗan uwansa nayi shine shima yake son yayi. Ko sha'awar ka ɗan uwan (yana nufin Rayyan) ba ya ji, ga ka har ka tara iyalan ka gunin sha'awa".
Daddy na murmushi yace, "ai komi nufin Allah ne, wata rana sai labari, idan lokaci yayi za su yi".
Uncle sauya maganar yayi suka ci gaba da hiran su, inda Ammee ta tashi ta koma ciki, dama gaisa wa da Suhaib ya fito da ita. Su kuma Suhaib da Faruk suka fita waje suna zanta wa.
A lokacin ne su RAUDHA suka dawo, duk suka nufi wajen su
RAUDHA rungume sa tayi tana murnan ganin sa, tace, "Yaya ina su Daddy na?"
"Suna gida ban zo da su ba".
Buga ƙafa ta soma yi tana mishi rigima
Abubakar ya dunguri kanta yace, "ke dai kin cika rigima wlh, ki bari mu gama gaisa wa mana, kin wani ƙwaƙwime sa kin hana shi ya san damu a wajen".
Dariya suka yi gaba ɗaya
Inda ita kuma tabi sa zata bige sa, ya gudu. Nan suka soma zagaye wajen suna dariya
Zannurain yace, "mu dai ku dena zagaye mu haka".
Bata ƙyale shi ba kuwa, sai da ta kama shi ta naushe shi a kafaɗa
"Aushh! Wlh Yaya Suhaib wannan yarinyan muguwa ce, ta iya mugun ta".
Sosai Suhaib yake dariya, musamman yanda ya ga ƙanwar tasa ta saki jikin ta, fara'an ta ma daban ne, shi kansa yasan ƙanwar tasa tana cikin nishaɗi sosai. Family wani abu ne me girma da daraja, me saka nishaɗi a zuciya.
Anan suka shantake, sai daga baya suka shige gidan.
Da rana sai ga Rayyan ya zo.
[4/5, 9:31 PM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Ismail Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
2021.
*NASIHA*
'''Muna iya lura cewa ga al'ada in an Kira talaka zuwa fadar sarki yakan gyara fuska, ya yi ado don ya sami kyakykyawar maraba daga Sarki. To, in haka ne, ina ga in ya tashi zuwa tsayuwa gaban Ubangijin sa? Bawan da aka neme shi ya zo gaban Ubangiji, Sarkin sarakuna, mamallakin mamallaka, lalle kam ya fi kamata ya gyara kansa saboda wannan muhimmin muƙami. Ya kamata ya gyara kansa ta tsarkake tufafin sa da jikin sa, ya fito cikin kama mafi kyawu, kamar dai yadda aka umurci musulmi duka a cikin suratul A'ARAF, aya ta 31:
_"ya ɗiyan Adam! Ku riƙi ƙawar ku a wurin ko wane masallaci"_
Allah yasa mu dace.'''
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON FORTY FIVE*
_______📖 Lokacin da Rayyan ya shigo gidan, time ɗin su Daddy gaba ɗaya suna masallaci, sai Ammee dake zaune a Parlour, RAUDHA ta ɗaura kanta a saman cinyoyin ta suna ta hira suna dariya, sosai RAUDHA ta saki jiki da Ammee, sai tana kallon ta tamkar Mahaifiyar ta, bata taɓa kewar Mahaifiyar ta ba tunda take, sabida Daddy da Suhaib sun ɗauke mata komi, duk abinda uwa zata yi mata suna mata, ba su taɓa barin gurbin da zata ji kewar Maman ta ba, shiyasa ta taso ko kaɗan bata taɓa tuna wa da ita ba, ko a hoto ba ta ganin ta, duk da suna da hoton nata, amma ita ba ta ɓata time ɗin ta wajen ganin ta a hoto. shiyasa yanzu da Ammee take nuna mata ƙauna da kulawa, sai taji sosai take kewar Maman ta, sai taji tana matuƙar ƙaunar ta, har tana jin da ma tana raye ta so ta itama kamar yanda Ammee take mata fa. a jiya da take tunanin nan har sai da tayi kuka sosai, shiyasa a ranta yanzu ta ɗauki Ammee tamkar tana tare da maman ta ne, komi da zata iya faɗa mata zata iya sanar wa Ammee
Yanda RAUDHA ta saki jiki sosai, hakan sai ya faranta ran Ammee matuƙa, sosai take jin soyayyar ta a ranta, kasancewar ta me ƙaunar ɗiya mace, tunda Allah be bata ba.
Sallaman Ray, shi ya dakatar da su daga hiran da suke yi suna dariya, a tare suka amsa mishi har RAUDHA da tayi tunanin ko Faruk ne, tunda muryan su ba shi da banbanci, sai dai yanda taji ƙamshin turaren sa ya daki hancin ta, sai tayi saurin lumshe idanu tana sake zuƙo turaren sosai, but duk a tunanin ta ba shi bane.
Allah ya sani turaren sa yana matuƙar mata daɗi, bata san meyasa ba. tana jin sanda suke gaisa wa da Ammee, sai hakan ya bata mamaki tayi saurin ɗago kanta tana sauke idanun ta akan shi, yanda idanun ta suka faɗa cikin nasa sai tayi saurin ɗauke kai tana koma wa ta kwanta
Murmushi shi kuwa yayi, ya kalli Ammee dake shafa kanta a yanzu ɗin yace, "Ammee su Uncle fa?"
"Sun je masallaci".
"Ok Nima bari inje dama ban yi sallan ba". Har ya miƙe kuma sai ya kalli RAUDHA da idanun ta ke rufe yace, "pretty babu gaisuwa?"
Wani irin sara wa gaban ta yayi, dasauri ta buɗe idanun ta tana sakin numfashi me ƙarfi, sake mayar da idanun ta tayi, ahankali ta furta, "naharan sa'idan".
Murmushi yayi ya kalli Ammee da itama take murmushin, don sosai zuciyan ta ta ɗarsa mata wani abu yanzu-yanzu da Rayyan ɗin ya kira RAUDHA da Pretty, sai ta ga sosai suka dace da juna, har tana ji a ranta da ma su kasance mata da miji
Shi kuwa Ray, har ga Allah manta wa yake yi yake kiran ta da suna Pretty a ko ina, sabida bakin sa ya saba. Sallama yayi wa Ammee ya fice
Sai a time ɗin RAUDHA ta buɗe idanun ta, sosai ranta yake kawo mata tunani kala-kala "meyasa yake kiran ta da sunan da Ƙalby ɗin ta ke kiran ta? Shin ba shi da wani sunan da zai iya kiran ta da shi ne sai wannan? Meyasa take jin muryan sa na shige da na Kalby? Ko dai shi ne?" Take ƙirjin ta yayi wani irin buga wa, tayi saurin tashi zaune tana riƙe wajen
"Lafiya Daughter? Me ya faru ne?" Ammee tafaɗa tana riƙe mata ɗaya hannun cikin kulawa
Kallon ta tayi, sai kuma ta saki murmushi tana faɗin, "babu komi Ammee na tuna wani abu ne, bari inje ɗaki ina dawo wa".
"Kin tabbatar?" Ammee ta sake tambayar ta
Gyaɗa mata kai tayi tana miƙe wa tsaye
"Ok ki kula".
Kai tsaye ɗakin ta ta wuce, ta soma neman layin Ƙalby, sai dai akashe ake ce mata, ta gwada ya kai fiye da biyar, but the same answer. Runtse idanu tayi tana buɗe wa da sauri, sai kuma ta tashi ta soma zagaye wajen tana tunani kala-kala
Wani Gwauron numfashi taja tana dukan cikin tafin hannun ta da ɗaya hannun, afili ta furta "Nooo impossible!". Hannun ta ta saka a baki tana cizon yatsan ta, taci gaba da Safa da marwa, sai kuma taja burki da sauri tana riƙe goshin ta
"A'a tunani na ne wannan, amma wlh Ƙalby bazai taɓa zama shi ba! Me zai saka ma yayi min irin wannan wasan? Meye haɗi na dashi? Na tsane shi fa! I hate him so much". Taƙarike maganar kamar zata yi kuka
Zama tayi daɓas akan gadon ta, ta sake ɗaukan wayan ta ta kira Numban nasa, a time ɗin yana shiga sai dai ba'a ɗauka ba, sai da tayi two missed calls kafin a ɗaga. Tana kara wa a kunne abinda ta soma tambayan sa, "ina ka shiga Ƙalby?"
Murmushi Ray ya saki, yana gyara muryan sa yace, "Pretty Ina aiki ne".
"Aiki kuma? Wani aiki kenan bayan yau ba ranan aiki bane?" Ta sake tambayar sa da sauri, ita kanta a ruɗe take, so kawai take yi ya bata ƙwaƙƙwaran amsar da zuciyar ta zata iya yarda dashi
Stiil Murmushi yayi yace, "kin manta nace miki muna zuwa Gona Ni da Abba na?".
Shiru tayi
Ya sake cewa, "lafiya dai Pretty? Me ke damun ki? Ina ji a jiki na akwai abinda ke damun ki?"
"Yeah akwai Ƙalby, Ni na gaji da ɓoye min kanka da kake yi, ina so mu haɗu". Tayi maganar da tsananin sanyin murya
"Kar ki damu Pretty nayi miki alƙawari Very soon zamu ga juna, amma don Allah ki faɗa min meyasa kike son mu haɗu da wuri?".
Shagwaɓe murya tayi tace, "Ni ina son ganin ka ne fa, kuma ka ga su Daddy suna ta tambaya na kai, sannan Ni fa ina so mu yi aure nan kusa ne, kai nake jira".
"Ohhh Pretty Ni kike jira? Ashe kin ƙosa kamar Ni anan?" Yayi maganar cikin dariya
Itama dariyan tayi tana kwanciya kan gadon, ta sake matse wayan a kunnen ta, cikin ƙasa-ƙasa da murya tace, "to dama kai kaɗai ka ƙosa, nima ai har da Ni".
"Me kika ce Pretty?"
Saurin faɗin, "no ba da kai nake yi ba?"
Dariya ya kece dashi, itama tana taya sa, yace, "ok kenan dama akwai wanda kike magana da shi bayan Ni?"
Turo baki tayi kamar tana ganin shi tace, "a'a babu kowa fa".
"To nace da Ni kike yi kika ce ba dani ba?"
"Au da kaina nake yi".
Dariya yayi yace, "kin ganki ko? Zaki sake maimaita abinda kika faɗa duk sanda muka haɗu".
Dariya tayi kawai tana rufe idanun ta
"Baby in tambaye ki mana?"
"Ina ji Ƙalby". Tayi maganar tana tashi zaune
"Wai dama kina da kunya haka?"
Turo baki tayi sabida bata yi tunanin tambayan kenan ba, sai da ta harari wayan kafin tace, "ban sani ba".
"Oh Allah ya baki haƙuri my Pretty, kin san me? Wlh kina saka Ni nishaɗi duk sanda zan kasance ina waya dake".
Murmushi tayi tace, "buri na da fata na kenan, a koda yaushe ka kasance cikin farin ciki, ina matuƙar matuƙar ƙaunar ka Ƙalby".
Lumshe idanun sa yayi cike da jin sanyi a ransa yace, "nima haka My Baby, Ina matuƙar ƙaunar ki, fata na ki kasance mata a gare Ni, kuma uwar ƴaƴa na, Allah ya nuna min ranan da zan mallake ki, ina ga ranan ko uhmmm farin ciki na bazai misaltu ba".
Murmusawa tayi idanun ta akan hannayen ta da take wasa da su, ta amsa masa da "ameen" cikin muryan ta me daɗi.
Da haka suka ci gaba da wayan cike da nishaɗi, ko wanne na bayyana ma ɗan uwansa irin farin cikin da yake ji idan suna tare da juna.
Ƙarfe biyar Ray yabar gidan, Suhaib kuma sai zuwa dare ya bi jirgi ya koma Abuja.
A ɗan kwanakin da su Ammee suka yi kafin su tafi, sosai RAUDHA ta shaƙu da su gaba ɗaya, har Faruk da be da yawan magana, shima yanzu sun saba sosai. sati ɗaya suka yi suka soma haraman tafiya, RAUDHA ta so bin su, amma dayake akwai bikin Ramcy sai ta fasa, amma Daddy sai ya ce mata "ta je tunda bikin saura Two weeks ne, sai tayi sati ɗaya ta dawo".
Murna sosai RAUDHA take yi, nan da nan ta haɗa kayan ta a Trolly tabi su suka tafi.
.
_To Fans mu dai mun tafi Bayelsa, wanda yaga zai iya bin mu ya biyo mu, wanda kuma be da kuɗin Jirgi ya jira mu har mu dawo. Mu dai shhhhhiiii ✈️ mun shilla.🥴_
[4/6, 8:53 AM] نفيسة أم طاهرة: 🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Ismail Lawal Goma._
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattapad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
2021.
.
*NOT EDITED* ___________________________📗
*SEASON FORTY SIX*
_______📖 Sun Isa Bayelsa wajen gabanin magriba, driver ya zo ya kwashe su ya nufi da su tanƙamemen gidan su, gidan flet ne me kyan gaske
Suna shiga parlour'n matasan duk suka wuce ɗakunan su, inda Ammee ta nuna wa RAUDHA ɗakin da zata zauna, tana fita ta shiga Toilet tayi wanka sannan ta ɗauro alwala, doguwar riga blue ta saka kafin ta gabatar da sallah
Bayan ta idar ta fito Parlour, babu kowa sai Ammee da itama zaman ta kenan
Tace, "ƙariko mana ɗiya ta".
Taho wa tayi ta zauna a gefen ta
Ammee na murmushi tace, "kin ji sabon wuri, da fatan dai ya miki?"
Itama murmushin tayi tace, "Yayi min Ammee".
"To Masha Allah haka nake so, bari in saka a kawo miki abinci ko kina jin yunwa".
"A'a Ammee a bari sai anjima zan ci".
Ammee tace, "to shikenan, kinga dai gidan mu ko. Nasan yanzu dare yayi ne shiyasa babu wanda zai zo sai zuwa gobe zaki ga ƴan uwa, Family House ɗin mu na nan baya ne, mutanen gidan duk ƙannin Uncle ne da matan su da ƴaƴan su, zuwa gobe insha Allahu sai mu je ku gaisa".
"To Ammee". RAUDHA tafaɗa tana murmushi.
A lokacin su Faruk suka shigo da sallaman su
Amsa musu suka yi.
Zannurain sarkin tsokana yace, "Hajiya RAUDHA ga ki ga garin mu, to ya kika ji namu garin? Da fatan dai yayi miki zam-zam ko?"
Dariya tayi tace, "Bro Zannu ai komi zam-zam". Har da mishi waigi da hannu 👍
Wannan karon dukan su suka yi dariyan
Abubakar yace, "ai sai kin gaji da yawo, Allah ya kai mu dai gobe, gaba ɗaya babu inda bazan zaga dake a garin namu ba".
Ammee tace, "a'a babu inda ɗiya ta zata je gobe, hutu zata yi, idan ma yawon zaku fita sai dai zuwa jibi, yanzu ku tashi ku je ku ci abinci don ga yi can Asabe ta gama jera wa. Ina Uncle ɗin ku?"
"Yana wajen su Baba Iliya a waje". Abubakar ya bata amsan hakan
Tashi suka yi su ukun zasu nufi kan dainning, har sun yi gaba sai Abubakar ya dawo yana cewa, "Friend ke fa? Baza ki taso mu ci abincin ba?"
Girgiza kanta tayi tace, "ba yanzu ba".
"Cabb.. don Allah ke kuwa ba kya jin yunwa? Duk uwar daɗewan nan da muka sha a hanya?"
Hararan sa Ammee tayi tace, "dayake ance maka kowa ma irin ka ne, wuce ka tafi kai dai kaje kaci abincin ka".
Turo baki yayi yayi gaba
Ita dai RAUDHA sai dariya take mishi
Ammee tace, "ƙyale shi ai halin sa sai shi in dai Abubakar ne".
Daga nan hira suka ci gaba da yi. Inda Faruk shima ya dawo ya zauna kusa da su ana yi da shi
Sai da aka kira sallan isha'i kafin su wuce masallaci, su kuma RAUDHA da Ammee suka nufi ɗaki don gabatar da nasu.
*WASHE GARI*
Ƙarfe 11:30am RAUDHA ta tashi daga barci, wanka tayi ta shirya cikin riga da skert ƴan kanti, rigan me ruwan madara ne me gajeren hannu, sai kwalliya da akayi da jan zare aka saka Stones, sai kuma skert ɗin ja ne, daga ƙasan an zizara kalan ruwan madara, yana da faɗi skert ɗin sai tsagu ta baya, hula ta saka irin na saƙa me tuntu fari, an yi harafin *R* a gaban da jan zare, flet shoes ta zira a ƙafafun ta ta ɗauki wayan ta tafito Parlour.
Ammee na zaune ita da wata matashiyar yarinya me kimanin shekaru 22, yarinyan tana da girman jiki da tsaho shiyasa idan ka ganta zaka yi zaton ta haura 25yrs.
Hango ta da Ammee tayi nan da nan ta washe baki tana nuna mata kusa da ita "ta ƙariso"
Sai da ta gaishe ta kafin ta zauna tana kallon yarinyan da itama take kallon ta
Ammee tace, "ku gaisa mana Suhaima".
Gaishe ta Suhaiman tayi. RAUDHA ta amsa tana murmushi
Ammee ta sake cewa, "ita ce ɗiyar Baba Iliya, Sauran duk sun zo sun tafi kina barci ban tashe ki ba".
Murmushi kawai RAUDHA tayi
Sannan Ammee tace, "ta je tayi Breakfast in ya so Suhaima ta raka ta zuwa gidan ta gaishe su".
Tashi tayi ta nufi wajen dainning, sai da ta gama karya wa kafin ta dawo tana tambayan Ammee su Abubakar
Ammee tace, "Abubakar ya shiga school, Zannurain kuma sun wuce wajen aiki da Uncle ɗin ku, shi ya hana Ni ma in tashe ki, yi maza ɗauko mayafin ki ku je ku dawo".
Amsa mata tayi da, "to" sannan ta wuce ɗakin, bata jima ba ta dawo riƙe da ƙaramin mayafi a hannun ta baƙi, rataya shi a wuyan ta tayi suka fita da ita da Suhaima
A waje suka iske Faruk na waya, da hannu yayi musu alaman su jira sa. Yana gama wa ya kalle su yana murmushi yace, "sai ina kuma? Sarkin yawo an samu ƙawa ko har an soma jan ta?"
Dariya Suhaima tayi tace, "kai yaya Faruk kai kuma. Ammee ce fa tace in raka ta gidan mu".
Ita dai RAUDHA murmushi tayi, sannan ta gaishe shi tana cewa, "kai baka je aikin ba?"
Idanun sa akan ta yana murmusawa yace, "ban je ba, sai zuwa anjima zan leƙa, ku mu je in raka ku".
Tare suka jera suka nufi babban gidan nasu, sashi-sashi suka je da RAUDHA ta gaisa da mutanen gidan, sannan suka yaɗa zango sashin su Suhaima, sun jima suna hira kafin suka fito suka yo gida
RAUDHA anan waje ta bar Suhaima da Faruk suna magana ta shigo gida. Tana shiga ciki Ammee ta tambaye ta Suhaiman? Take sanar mata "tana waje ita da Faruk".
Hira suka soma yi, can sai ga Suhaima ta shigo ta zauna aka ci gaba da yi da ita.
Suhaima ita ce yarinyan da suke soyayya da Faruk, da tuni sun yi aure amma yace ba yanzu ba, wai karatu zai koma.
Sosai RAUDHA take jin daɗin zaman ta a cikin wannan Familyn, kowa na son ta kuma yana nuna mata ƙauna. musamman ma kasancewar ta samu Suhaima, tunda ita mace ce tana jin daɗin zaman su tare, kullum suna yawo a cikin gari, idan basu fita da su Abubakar ba, to Suhaima zata ja ta su fita tare, har gidajen ƙawayen ta suke zuwa tare
Ana gobe zata tafi sai ga Rayyan ya dira gidan, lokacin Ammee ce kaɗai zaune a Parlour ya shigo, tace, "a'a kai kuma daga ina? Saukar yaushe?"
"Yanzu Ammee". Yayi maganar yana zama
"To aikin kuma fa?"
Murmushi yayi yace, "kai Ammee kya bari mu gama gaisa wa ai ko?"
Taɓe baki tayi tace, "to".
Dariya yayi yace, "Ammee kenan, wai to".
Itama dariyan tayi tace, "to in ban ce to ba me kake so in CE?"
Murmushi kaɗai yayi sannan ya gaishe ta. ta amsa tana tambayan sa lafiyan sa da aikin nasa
"Alhmadulillah Ammee, ina mutanen gidan?"
"Ai gaba ɗaya ba sa nan, Ni kaɗai ce, yanzu ma Suhaima da RAUDHA suka fice".
Numfashi yaja kafin ya miƙe yace, "bari in ci abinci Ammee, yunwa nake ji".
Wuce wa yayi kan dainning, yaci abincin sannan ya wuce ɗakin sa, yayi wanka ya ɗauro alwala ya tafi masjid, kasancewar a time ɗin ana kiran sallan Azahar ne. Daga can sai ya wuce family House ɗin su don gaida su.
Babu jima wa su RAUDHA suka dawo gidan, a gajiye suka shigo, sabida yawon da suka sha yau ɗin, Suhaima ma bata zauna ba tayi gidan su
RAUDHA kuma ɗaki ta shige tayi wanka ta saka riga da skert Robber, light green colour, ta fito Parlour ta zauna akan dainning tana zuba abinci.
Ammee ce ta fito daga kichen tace mata, "ɗiya ta bari na shiga ɗaki na kwanta zuwa anjima, idan Uncle ɗin ku ya dawo ki tashe Ni".
"To Ammee". Ta amsa mata tana ƙoƙarin ɗaukar wayan ta dake ring
Abincin da ta saka a baki take tauna wa tana kallon wayan, number ne shiyasa bata yi peacking ba ta ajiye, taci gaba da cin abincin ta, sake kira akayi, sai da akayi mata Three missed calls kafin ta ɗaga tana kara wa a kunne.
Daga can ɓangaren Zulain ne yayi sallama
Ta amsa mishi tana tambayar "waye ne?"
Murmushi yayi yace, "Zulain ne Masoyin ki?"
Ɗan jim tayi don ta manta shi ma
Ya sake cewa, "har kin manta Ni Ko? Uhmmm".
"Sorry i remember.. but aina ka samu Numba na shi ne abinda ya bani mamaki?".
"Kin san duk wanda yake son abu, to samuwar hanyar da zai bi don mallakar shi ba abu bane me wahala, Sharif Ya samo min wajen yayan ki".
"Eyya". Tafaɗa tana kai abincin baki
"Uhmmm me kike ci haka babu tayi?"
Murmushi tayi tace, "ko zaka ci ne? Shinkafa ne. Duk da dai nasan ba iya cin ciman mu zaka yi ba?"
"Wa ya faɗa miki? Ai muna dafa wa acan".
"Really".
"Yes sweetie".
Dariya kawai tayi taci gaba da cin abincin ta tana sauraron sa.
A lokacin ne Ray ya shigo parlour'n, idanun sa a kanta ya faɗa yana ganin yanda take sakin murmushin ta me ƙara mata kyau, take yaja numfashi yana sake ƙare mata kallo. Ahankali ya soma takowa cikin parlour'n hannayen sa cikin aljihun wandon sa
Motsin da taji kaɗan shi yasa ta waigo idanuwan ta suka faɗa kansa, tsayar da idanun ta kawai tayi tana kallon sa a ranta tana mamakin ganin shi ɗin
While shima idanun nasa akanta ne, ya nufo inda take, dai-dai ya ƙariso wajen take faɗin, "ok shikenan zan yi missing naka nima, shikenan ko?"
Daga can Zulain yace, "No ban yarda ba, don nace dai ki faɗa ne kika faɗa, amma Ni kaɗai ne nayi missing ɗin ki".
Ray tuni ya runtse idanun sa saboda wani irin kishi da ya turniƙe shi, tuni zuciyar sa ta raya masa ba da Suhaib ko Daddy take waya ba. Buɗe ido yayi ya sauke a kanta, sai kuma ya ja kujera ya zauna yana ci gaba da tsare ta da ido
Haka kawai taji baza ta iya ci gaba da wayan a gaban sa ba yana kallon ta, don haka tayi wa Zulain sallama ta kashe wayan
Anan Ray ya sake tabbatar da ba su bane tunda ta kira sunan sa
Abincin ta taci gaba da ci batare da ta kula sa ba, sai tsinkayar muryan sa tayi yana cewa
"Meyasaka kika tsane Ni RAUDHA?"
Take ta ɗago manyan idanuwan ta ta sauke a kansa, kallon kallo suke wa juna ko wannen su zuciyar sa na saƙa masa abubuwa a game da ɗan uwan sa. Ganin kallon da yake mata yana saka ta jin wani iri, sai ta ɗauke nata idon tana mayar wa ga Plate ɗin abincin ta, sai dai tambayar da yayi mata yake kai kawo a ranta amma kuma bata da alamar tanka masa
"Why kika tsane Ni nace? Ko gaishe Ni ba kya son Yi a matsayi na na Yayan ki, why?"
Shiru tayi tana caccakan abincin da Spoon ɗin hannun ta, sai kuma ta miƙe tayi hanyar barin wajen
Take ya saka hannun sa ɗaya ya kamo nata, babu zato taji ya janyo ta zuwa jikin sa..
0 comments:
Post a Comment