*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*MMN FAREESAH*
1⃣&2⃣
Amsa Kiran mashkur yayi,,kafin yayi Magana Nasir yace,,abokina muke jira kaga lokaci Baya jira,, murmushi mashkur yayi Yana Kallan mummy..
Shikenan Nasir karka damu gani a hanya,kabani 5 minutes Zan qaraso,, shikenan Ina jiranka cewan Nasir Yana kashe wayan..
Murmushi abbakar yayi Yana cewa Ai nasan mummy bazata Bari ya fito da wuri ba,,Dan Dama da kyar ta Bari zeje wannan kauyen"Ni wallahi ta birgeni data nuna bataso Duk be yadda da Hakan ba mansur ya fada Rai bace.
Inama inama,,Kai nifa naso Nike da wannan gatan irin na mashkur da ko zaman Nigeria baniyi, dariya suka sa daidai lokacin da mashkur yazo.
Drive ne ya Bude masa qofa nan ya fito cikin takunsa na qasaita,, Ido suka zuba masa suna kallo,,shiko murmushi yayi ya qarasa kusa da Nasir tare da miqa masa hannu,,Daya bayan Daya suka riqa gaisawa da abokan nasa.
Gaskiya abokina Baka dace da zaman kauye ba,,kauyen ma wai Fulani,,Tabe Baki mashkur yayi tare kallan nasir,,Nasir Ka kirani gashi nazo banga alamun tafiya ba.
Karka damu yanzu zamu wuce drive ya kusa zuwa,, mashkur be qara magana ba,suka cigaba da hira batare daya sa musu Baki ba.
Bala,zaka iya tafiya,, dasauri Bala drive yace, ah ah ranka ya Dade hajiya tabani umarni Karna sake na tafi har sainaga tafiyanka,, girgiza Kai yayi Yana me Jin dadin yadda mummy ke Kula dashi fiye da yadda ta damu da kanta,,
Karka damu kawai kaje Ka gayamata mun wuci,,kayi hakuri ranka ya dade bazan iya tsallake umarnin hajiya ba..
Seka ta Zama Dan wahala cewan Nasir Yana hararan Bala,,
Ba'afi 2 minutes ba sai ga lafiyayyan mota ya faka a gabansu, Basu bata lokaci ba gurin Shiga,nan drive yaja suka Fara tafiya sai kankan Fulani..
Garin kankan..
Karfe uku dai suka safka cikin kauyen dabe wuci a qirga gidajen ba,,suna zuwa aka kaisu gidan me gari,,hannu biyu me gari ya amshesu tare da yi musu sauka ta musamman,,
Fura da nono aka Basu sai kankana da aka jere kusa dasu,daga gefe dabino aka kawo cike da kwarya sai warar Fulani,Wanda akeyinta kama awara saidai ita da nono akeyi ake soyata kama awara.
Nan da nan guri ya cika da kamshi ,,mashkur ne ya saurin dago Ido Jin kamshin dabe taba Jin irinsaba adukkan abincin dasuke ci,,saliva ne ya cika masa Baki,nan da nan ya hadiye Yana Yana tandar Baki..
Guri aka Basu Don su ci abinda suke so,,nan fa yara kauye suka zagaye motansu suna shafawa tare da yimusu zane,,
Da gudu wata yar karamar yarinya tazo tana zana photon saniya a cewarta saniyar yakumbo ce,,nan yara suka riqa tsalle suna murna, mashkur da abokansa Basu San aika aikan da yara ke musu ba,wara kawai sukeci suna santi, dasauri Nasir ya dago Yana kallan inda yaji ihun yara sunata fillanci,,beji abinda suke fadaba sedai yaji ana futanci,,a hankali ya tashi ya leqa ta window,
Lafiyayyan zaki yayi Yana fita a dakin da gudu yayi Kan yaran,,wasu irin Zane ya gani Wanda akayi da karfe wani da qusa,,tini ya hada Kan yaran Wanda suwa yanzu sunfara gudu suna yeee saniyar nijlah tafi ta kowa kyau.
Idon Nasir ne ya safka Kan wata katuwar saniya da nijlah ta zana,photon yayi kyau kama ba jikin mota aka zana shiba,,Kai Nasir ya fada cikin tsawa,wacece nijlah a cikinku???
Cikin murmushi nijlah tace nice,,kece ko aiko saniya tayi kyau,,zoki zanamin wata ingani Dan ni banyadda ke kice kika zana ba"
Da gudu yaran suka dawo jikin Motan,,wasu na cewa suma zasu zana,,suna zuwa Nasir yafara kama hannun nijlah,kafin yakaima sauran Duka,,tini suka fece wasu na kuka,,itako nijlah harta Fara dariya tana cewa.
Kowa ya kirasu, Naga dai ni dayace nijlah ni Dan birni ya Kira ko,,bata rufe baki ba Nasir ya kaimata Duka,,wani gigitancen ihu nijlah tasa tana Kiran yakumbo.
Wayyo Allah yakumbo kizo Dan birni ze kasheni,,kuka sosai nijlah take tana Kiran yakumbo kasan cewar ba'a taba dukan nijlah ba,,sedai taga ana dukan yara,Dan ita bame fitina bace sedai rigima kawai data cika Mata ciki,,
Shiru mashkur yayi Yana sauraran kukan yarinyar,,kai Mansur kama Nasir Ke Dukan yara,,haba Dai Daga zuwanshi kauye zefara da Dukan yara,,
Tashi mashkur yayi Aiko yaci Karo da kyankyawar fuskar nijlah idanta yayi jajur tana kuka kai kace Wani duka me yawa aka ma,, dasauri mashkur ya fita tare da janye nijlah Daga hannun Nasir yace.
Kai Nasir Baka da hankali bakaga yarinya ce itaba,,wacce irin yarinya kai bakaga barnar data aikata jikin Mota ba,,kodan batasan darajar Mota ba..
Tabbas nijlah batasan darajar Mota ba,,Kamar yadda bakusan darajar Dan Adam ba,,fizge hannunta nijlah tayi ana mashkur ta fada jikin yakumbo tana kuka,,Bayan ta yakumbo ta riqa shafawa tana Bata hakuri.
Kiyi hakuri nijlah,baki da Mai Rama Miki sabida maraici,,inama wata me gata kuka taba dakun bar kauyen nan da qafafunku.
Jikin Nasir ne yayi sanyi harya Bude baki zeba yakumbo hakuri yaga ta dauka nijlah tana tafiya tana hawaye,, kwanciya nijlah tayi jikin yakumbo tana fillanci,,Dan Hausa Bata gama Shiga bakinta ba.
Ka gani Ko,kagani nasir Daga zuwanmu kaja mana Magana,menene aciki dantayi Zane jikin Mota,,Ni gaskiya banji dadin abinda ka aikata ba,ya Zama dole muje har gida abasu hakuri.
Shikenan abokina,,Nima bada mugunta na buge taba,,wallahi kaji na rantse sau Daya na daketa a hannu sai hannunta kawai Dana riqe Amma ta riqa wannan kukan har tana birgima,,Allah ya kyauta mashkur yace tare da komawa cikin dakin..
A ranar suka Gama cike komai sedai kowa yace baze iya Zama a wannan kauyen ba Dan haka suka Hana drive tafiya a nufin gobe zasu bar wannan kauye.
Babu abinda zesa na tafi daga wannan kauye indai bana Gama abinda nazo yiba,,sedai Ku Ku tafi Amma ni naga gurin Zama, mashkur yafada Yana gyara Zama..
Kai ina wallahi ,,bazan taba iya rayuwa anan ba, bakaga yaran garin ki mota Basu sani ba,,yo ina zasu sani daga akoru koru babu abinda suka sani,,
Uhmn nidai gaskiya Bazan Iya tafiya ba,senaje Na nemi yafiyar wannan tsohuwa da yarinyarta Naji tace marainiyace, Nasir ya fada cike da nadama" ok kaima Zaka zauna Kenan cewan Mansur Yana dariya,, gaskiya banaji Zan iya,,hhhhh kawai gobe mu Koma birni inyaso kudi suyi aiki a chanza mana gari Amma Ina wannan gari ni banga gurin aiki ba.
Shidai mashkur be qara Magana ba Se Dai murmushi dayake saki Akai Akai.
Karfe 8 na dare Suna zaune sun rafka uban tagumi sabida ba network me kyau balle Ko waya ta debe musu kewa sukaji ana bubbuga kofan Dakin,,kai wayene haka yake mana bugu kama Na..,,hararan Nasir mashkur yayi ya hanashi fadar abinda yayi niyya,,
Ka shigo akace,, dasauri Bello ya shigo Yana washe Baki yace,,sannunku dai Baki,,me garine yace a gayamuku zaaje dandali,ko kuma kunasan zuwa kuyi kallo,,eh gamunan zuwa mashkur ya bada amsa..
Tafiya Bello yayi Yana cewa yau Yan birni zaku sha kallo a dandali Allah yasa danladi me kidan kagane zeso wannan dandali...
Haba mashkur me zamuje kallo a wannan kauyen nibanga abin kallo ba,,ni na gani yafada Yana fita waje,,kaga mashkur Nima zanje,tsaya ganinan,,Nasir ne yafada Yana kallansu mansur..
To yaya zamuyi cewan umar suka suka mara musu Baya..
Tin daga nesa suka hango hanken fulatan kyau da aci balbal gefe guda masu suyan kifine da tsire sai Yan Mata wadanann wasu wuci shekara 12 zuwa 13 ba,,Suma da nasu kayan tallan,raga Dada da kosai da Mai burodi lolxx.
Mashkur har sauri yake Dan tin daga nesa gurin yayi bala'in burgeshi.
Yakumbo na zuwa gida ta kwantar da nijlah tana kallan yadda ta Zama abin tausai,,kiyi hakuri kinji yarinyar kaka,,Allah ze saka Miki..
Nidai ban yadda,ara ta kanni saina Rama,ai dai na ganeshi,uhmn uhmn fa nijlah banisan tsokala.
Yakumbo kema kinsan Bani bari kowanne mara kunya,,inda harfa da riqemin hannu yanzu da iro ya ganci yaya za'ayi,kaka kinsan fa iro da kishi"
Ke qaniyanki nace,wai ba na hanaki Kula wannan iron ba,, nijlah yanzu fa shekara 9 kike se Yan watan ni,, ki Bura kidan qara girma Dan bana tinanin zamuyi muki aure a shakara Goma sha uku,,gwara kisama kanki salama har Malam ya Samu kudin sai Miki katifa da korai.
To kaka, yau Zan gayamasa danaje dandali,,to kaka ki Bani biyar saina tafi,kinga dare sai qara yi shike..
Kiyi hakuri nijlah yauma Bani da ko biyar,,tsalle nijlah tayi ta Fadi qasa tana kuka,,ni wallahi sai kin Bani biyar Naga ba'a zuwa dandali ba biyar,wasu har Goma ake Basu Amma ke kullum hakuri kike Bani.
Wai sai yaushe Zan gayamiki kidena hada kanki da yaran garinann nijlah meyasa kikesan batamin Rai akan Baki kudin dandali ko kinaso Nima na Fadi na mutu..
Nijlah najin an Kira mutu take Shiga hankali ta,Dan haka ta tashi tana turo Baki,,kaka na tafi.
*Yawan comments yawan typing,, comments Kai ke nuna labari yana dadi ko babu,,akullum ina qara gayamuku daku riqa turawa wasu group's bayan kun karanta, nagode*
*Momn sultan ce*✍✍✍
đđ *'YAR SADAKA..*đđ
*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*MMN FAREESAH*
5⃣&6⃣
Kaka na tafi,,adawo lafiya,,Banda tsokala ki Kuma dawo da wuri,,kaka Kenan kinfasan Bana dadewa Amma kullum sekin gayamin saikace yarinya..
Baki yakumbo ta riqe tana kallan yadda nijlah ta tafi tana Taku daidai,kai kace wata babban budurwace!
Yakumbo Bata qara Magana ba nijlah ta fita tana Mita,,haka haka ta batamin lokaci gashi 'yar biyar din ma Bata Bani ba,, murmushi ta saki tare da fari da manyan idanunta tace,,nasan iro Yana dandali Yana jirana, tafiya nijlah take tana tinani harta qarasa dandali,,tin Daga nesa tafara Jin qaran sautin gangan danladi me gidan kagane Na tashi..
Tin Daga nesa su indo da Abu suke kallanta Har ta qarasa suka fara gaisawa,, nijlah Zaki Sai tuwan ruwa?turo baki nijlah tayi tace,,kinga niba ciye ciye ya kawoni ba,,kallo kawai zanyi Na Koma gida,kaka tace kada Na zauna,,Bata Ida rufe baki ba Taji an Kira sunanta" dasauri ta dago Ido tana duban Wanda ya Kira sunanta,,bazata taba manta wannan fuskan ba,,Dan shine mutum Na farko daya taba dukanta..
Murguda masa baki tayi tana cewa,,lafiya Zaka Kira sunana?
kiyi hakuri nijlah Bada niyya nayi Hakan ba,,kinji yarinya, Nasir ya fada Suna Hada Ido da mashkur dayayi kama besan abinda suke ba..
Yarinya Kuma,,nice ma yarinya,,to sannu babba,,dariya Nasir yayi Yana Kallan nijlah,,nidai Duk ba wannan ba,kin yafemin?
Karka damu Allah yanasan me yafiya nayafema,,Nima ka yafemin batama Mota danayi"
Nagode sosai Nasir ya fada Yana murmushi,,sedai Bani Zaki nema tafiyan Bata motor ba,kinga Wanda Zaki nema danba motana bane nashine,Nasir yafada Yana nuna Mata mashkur.
Har qasa nijlah ta sunkuya tana kallan fuskanshi tace,,Dan birni kayi hakuri Kaji, murmushi mashkur yayi,ya Bude baki a hankali yace,Tashi kinji kanwata,,maqale kafada nijlah nan yayi murmushi danya gane nufinta yace, shikenan Na hakura Amma Karki qara zana Mota kinji,,to nijlah tace ta Tashi da gudu zatabi kawayenta mashkur yace kinga nijlah zo..
Juyowa tayi da niyyan zuwa idanta ya safka Kan Na iro daya zuba Mata su alamun tambaya" lah iro yanzu nake dubanka anan,Hade Rai iro yayi Yana hararanta,,kai iro Daga tambaya Sai harara, nikaga tafiyana..
Ke nijlah Ina kikasan wadannan ya fada Yana nuna mashkur" cike da tsoro nijlah tace yayanane Daga birni suka zo" kin tabbata eh mana nijlah ta fada tana kallan mashkur" sosai mashkur ya cika da mamakin wayo irin Na yarinya sedai abinda yake tambayan kansa shin wanene wannan yaran da nijlah tayi Karya.
Nijlah Na ganin tafiyan iro ta qaraso kusa da mashkur tace gani" naira hamsin mashkur ya miqa nijlah Yana murmushi,amsa wannan Duk da Naji kince ba ciye ciye ya kawokiba,,
Nagode sedai kaka ta hanani amsar kudin samari indai ba iro ba,,wanene iro mashkur ya tsinci kansa da tambaya"
Iro yarone dabe wuci shekara 21 ba,,shine yake neman auren nijlah,, mashkur yaji Bello Na bashi amsa"
Kai Bello kana nufin kace wannan yarinya saurayi ne da ita??
Kwarai dagaske Bello ya bashi amsa,rufe fuska nijlah tayi tana dariya" mamaki sosai ya cika mashkur Nasir ne ya qara kallan nijlah yace yanzu Ke yarinya kinsan menene soyayya,,kasa Magana nijlah tayi ganin haka yasa Bello cewa..
Kinga nijlah amsa kije ki Sai abinda kikeso nizan Gaya yakumbo,,kasa amsa nijlah tayi Duk da tanasan siyan Abu a dandali,,qara miqa Mata kudin mashkur yayi,,Kanta a qasa tace Ni biyar Zaka Bani wannan yayi yawa ta fada Kanta a qasa..
Ki amsa wannan Bani da chanji,,wannan shine qaramin kudi a jikina,,Nasir Ko kanada Goma,,ta amsa wannan Nasir ya fada alamun Babu..
Kasa amsar kudin nijlah tayi,,kanwata ki amsa mana,kefa Naji yanzu kina Gaya Wani Ni yayankine kodama Karya kike,,Kunya ce ta kama nijlah nan ta miqa hannu ta amsa kudin,,
Nagode sosai Allah yasaka da alkairi,,Nima gobe Zan Baka fura da nono,,
Bata jira amsar Saba ta Shiga dandali tana murna,,
Bata Dade a gurin ba ta tafi,,tin Daga bakin kofa nijlah Ke Kiran kaka,,kaka!
Kai wannan yarinya Ni harna fara bacci Zaki tadani,,kaka kinga wannan Dan birnin ya Bani kudi harna Sai abin biyar kinga sauran,ta fada tana miqa kaka Chanjin..
Lalala nijlah waya baki wannan kudin kaddai kicemin Wanda ya dakeki dazu,,kaka bashi bane Wanda ya riqe Yana mishi fada,,Kuma Shima yabani hakuri,,to Duk Naji Amma Daga Yau Karki qara amsar kudi ahannun Wani koba na hanaki ba,,kaka Nima ban amsaba,Ina wannan bellon na gidan Liman,eh nagane cewan kaka,to shine yace Na amsa Ze gayamiki,,to Allah ya akaimu goben zansa Malam ya tambaya.
Washe gari karfe 10 na safe Malam yaje gidan liman anan sukayi magana da Bello ya tabbatarwa da Malam yaran bashida matsala,sannan hankali Malam ya kwanta.
Tin asuba mashkur yake Kiran mummy sedai network ya Hana wayan Shiga,,dafe Kai yayi Yana salati,,lafiya mashkur badai wani matsala bane?
Matsalane babba Nasir tin jiya nake Kiran mummy wayan yaqi Shiga gashi kasan halin mummy na tabbata yau bata rintsa ba.
Ni abinda ke damuna Kenan tinda muka zo ban samu kowa a waya ba,,ance semun fita wani Dan kauye anan kusa zamufi samun network,,kaga Nasir Kai kasan da haka Ka Bari nake ta kira,tashi da sauri muje na Kira mummy"
Dariya Nasir yayi yace Kai mashkur tinda muka zo banji Ka Kira Yasmeen ba sai mummy.
Murmushi mashkur yayi kafin yace, Nasir bana hada mummy da kowa na tabbata yanzu Yasmeen tana daki ko bacci taba tashi ba,,mummy ko bazata iya bacci ba Dan bataji lafiya naba.
Nasir be qara magana ba sabida yadda da maganan mashkur ya tashi suka fita,,
Bello suka gani yazo kawo musu kayan kari,,abokaina ina zuwa,,waya mukesanyi cewan mashkur Yana miqa masa hannu,,bayan sun gaisa Bello ya ajiye kayan abincin suka nufi kauyen..
Da Malam suka hadu a hanya nan Malam yake masa godiyan kudin Daya ba nijlah,,bayan Malam ya tafi mashkur ya juya Yana kallan bello..
Bello Naga wannan mutumin sai godiya yake akan naba nijlah naira hamsin,,nawa Raina 50 take daze Namin godiya har haka???
Hmmm Kai agurinka naira 50 bata da yawa Amma Banda gurin Malam da jikarsa nijlah" au dama ba shine mahaifinta ba"
Mahaifinta da maihaifiyarta sun rasu suke Kula da komai nata sedai Basu da karfi,, Dan ma suna San yarinyar kullum addu'a suke Allah ya kawo Mata mijin aure su auran da ita su huta"
Aure kuma nijlah har nawa take daga ganin yarinyar bata Ida shekara 11,, murmushi Bello yace yace ai nata Kai hakabama saura wata 4 ta cika shekara Goma.
Tashin hankali Amma akesan auran da ita cewan Nasir cike da mamaki,,to Nasir ya zasuyi Basu dashi kuma mu a wannan kauyen muna auradda yara shakara 13 zuwa 14..
Hira sosai suka riqa tafiya Bello Yana Basu akan labarin iyayen nijlah da rayuwarta,,tin daga nan mashkur yafara Jin tausan yarinyar jiyake dayana da yadda zeyi Daya taimaketa, akan auren da akesan yimata,,ahaka har suka Kai inda network ya hau Kan wayansu..
Hamdala mashkur yayi ya Kira layin Mummy,,bugu Daya biyu ta dauka muryanta a sanyaye" Assalamu alaikum mummy na kin tashi lafiya??
Kaima kasani ko lafiya ko akasin haka,,yanzu abinda kayi Ka kyautamin Kenan kodan kaga na damu dakai ko auta.
Kiyi hakuri Mummy wallahi ba laifina bane garin me ba network yanzuma seda mukayi tattaki zuwa wani guri me nisa aka samu network.
What mashkur kana nufin bazan riqa samunka a waya ba,,to wallahi kayi gaggawan baro wannan kauyen kafin naci mutumcinka,,Kako San a zaune na kwana.
Pls mummy kiyi hakuri iya yaune Insha Allahu za'a gyara,,yafada haka danya kwantar Mata da hankali"
Nidai nagayama kadawo kafin na Gaya daddynka tinda ni Ka rainani,,inyaso Shi yafada kaji" kiyi hakuri bata amashi ba ta katse Kiran ranta a mugun bace" yasan koya Kira ba dauka zatayi ba Dan haka ya tura Mata text massage.
Layin Yasmeen ya Kira dake zaune kusa abbansu tana Shan ice cream" murmushi tayi tace lah abba kaga mashkur ya kira.
Murmushi abba yayi yace dama na gayamiki ze Kira saiki dauka kafin ya katse,, dasauri ta dauka ta tashi ta koma dakinta,,hello hubby nah!
Na'am baby kin tashi lafiya,,lafiya qlau sai kewanka,,baby daga tafiya harkin Fara kewa da wuri haka,,karki manta shekara guda zanyi,,
Narke masa tayi tana kukan shagwaba tace,,Dan Allah Kada kayimana haka kaface 1 month zakayi Ka dawo" ah ah baby garin da nisa bazan iya wannan sintirin ba,,keya kamata kizo mu gaisa.
Bata fuska Yasmeen tayi tana turo Baki,,kaima kasan bazan iya rayuwa a irin wannan gurin ba,,Kai dai dakaga zaka iya saika zauna"
To ai shikenan kinga Kenan bakisan gani,,Allah hubby inaso Kaine Ka zabamana wannan rayuwa ta nisanta juna,,
Hira Sosai sukayi har Saida Nasir ya kasheshi kafin suyi sallama su koma kauyen,,bayan kwana biyu kowa aka kaishi gurin aikinsa inda mashkur ze riqa koya yara karatu a makarantar primary ta gari.
Sosai yayi mamaki da ganin ko ajujuwan babu gaba daya sun lalace birbiri ya Gama lalata sauran,,a haka yake koya musu duk da ba zuwa sukeba,,watarana sedai yaje Shi Daya yagama abinda zeyi ya dawo...
Nasir yayi sa'a kauyen da aka Kashi a kusa yake sedai Shi ana samun lalbai Dan Har headmaster garesu..
Wasa wasa Shakuwa me karfi Na qara Shiga tsakanin nijlah da mashkur,kullum saita kawo masa warar Fulani shiko yanasan taimaka musu Amma Malam ya Hana yace indai ba auren nijlah yakeso ba Baze amsa kudinsaba,,ba yadda mashkur ya Iya haka ya hakura sedai kullum Yana ba nijlah naira Goma Ko biyar tana zuwa dandali.
Yau tin safe Malam ya tashi bashi da Ko naira biyar balle su Sami abinda zasu sa a bakinsu.
Tinda nijlah ta Tashi take kuka ita yinwa takeji gashi Har karfe 12 Na safe Basu Sami abinda zasu sa a bakinsu ba.
Dan Allah Malam kabar yarinyarnan ta Shiga Ko gidansu Indo ne tasa Wani Abu a cikinta kaga yaro besan Babu ba" Ni kaina abinda nake tinanin kenan sedai Bazan bar yarinya tana zuwa kwadayi gidan mutane ba,,tinda su Basu tausaya sun bamu ba..
Malam me zakayi Kar ka cemin Baka fasa Bada sadakan nijlah ba,,Dan Allah kabari kaqarasa Ko shakara Goma sha biyu ne" kinga yakumbo ki rufemin baki,,Ina yanzu nijlah ta cika shekara Goma.
Dan Allah ba shawaranki nake nemaba..
Amma Malam...!Amma me kinfisu yinwa ya kashe yarinya muna kallo,,Idan Ko Na auradda ita Na tabbata bazata Rasa abinda zata Ciba...
To Malam wazata aura kasan Dai iro bashi da kudin aure Kuma Koda ka bashi sadaka Baze Iya ciyar da nijlah ba sabida Shima dakyar take samu yaci..
Bashi zanba auren taba sedai inaso kisani a kwana kusa Zan auran da ita,,kai malam kafa Duba lamarin nan,
Nijlah Najin batin aure ta tashi tana me Jin Dadi tace,,Malam ka gyale maganan kaka kayimin aure Nima Na riqa tuqa tuwo da kaina mijina Na siyomin tsire inaci...
Yauwa Yar albarka,Allah yasa asamu Wanda Ze Iya riqemana Ke ya Kula da maraicinki,,hawaye kaka ta goge da zanin jikinta tace..
To a gaskiya koka auran da nijlah sedai mijin ya biyota gidannan Dan gaskiya banga Wanda Ze Iya juran rigiman nijlah ba" Idan kinga ana haka Sai kiyi,kinga Nina fita karbomana bashi Ko gari musamu Musa a cikinmu..
Adawo lafiya yakumbo tayiwa Malam kafin ta janyo nijlah ta rungume tana rera kuka" Kaji kaka da baqin ciki,,bakiso Nima mijina ya riqa saimin kayan dadi ..
Yawan comments yawan typing,Dan Allah ku rage godiya ki riqa sharshi Ta hakane zan gane sakon danake San isarwa Yana zuwa muku
Comments & Shaređ
*Momn sultan ce*✍✍✍
đđ *'YAR SADAKA..*đđ
*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*HUSSAIN 80k*
7⃣&8⃣
Kujimin kaka da baqin ciki,baki Nima mijina ya riqa saimin kayan dadi iron na abu, nijlah ta fada cike da yarinta!.
Cikin kuka yakumbo tace!uhmn nijlah Kenan angayamiki kayan Dadi shine aure,,me Kika Sani game da Zaman takewar aure"
Allah kaka Na Sani,,badai ruwa Ake zubawa a buta na alwala ba,Sai kuma ka zauna Idan anyi tuwo a cikin gida ka dauka Langa a zuba masa tuwo..
Nijlah Kenan babu abinda Kika sani"Allah kaka Na Sani Niki Dena kirana yarinya Kuma Naga Abu tayi zamanta a gidan Musa Ai Dai Nima Zan zauna" Allah ya kyauta cewan kaka tana Jin quna cikin zuciyanta..
Tana nan zaune Har Malam ya dawo dauke da Leda a hannunsa,,
Wai haryanzu kina zaune kina tunani Akan abinda bashida mafita Sai wacce na fada" uhmn uhmn fa Malam wallahi nijlah bazata Iya Zaman aure ba,,ka Duba qanqantar shekarunta?
Yakumbo Kenan tin yaushe muke neman mafita bamu samu ba,,se yanzu Dana samu Zaki kawo matsala,,kiyi tinani Dan Allah.
Shiru yakumbo tayi tana nazari kafin tayi iya Bude baki tace" yanzu Malam Idan muka auran da ita akazo haihuwa ta kamu da jajjan fitsari ya zamuyi,, murmushi Malam yayi Dan ya gano abinda yakumbo Ke tsoro..
Indai wannan ne ki kwantar da Hankalinki,na tabbata nijlah bazata samu wannan matsalan ba,,to Malam kasan Wanda Ze aureta??
Kinga yakumbo Idan bakisan ayi aurennan kawai ki fada ni Kuma Zan zuba Miki Ido Naga yadda Zaki Iya Kula da ci da Shan nijlah,, yakumbo kinfi kowa sanin halin nijlah,,yinwa kawai Idan Taji ta riqa surfafa Miki kuka Ke Akan kudin dandali Sai nijlah ta kusan kwana tana ihu,,Ina Sai yanzu da Allah ya kawo mashkur wannan kauye nijlah ta Dan samu gata,,Idan ba haka bane Sai gayamin..
Matsowa nijlah tayi jikin Malam tana murna tace,,Malam kawai kayimin aure ka kyale kaka tayi ta abunta,,Nima Na riqa Cin tsire da kosai irin Na birni Ko,,dungurinta Malam yayi Yana cewa eh Zan Miki aure Amma sekin Dena yiwa mutane kukan dare"
Dasauri nijlah tace Allah nadena,,kaka aidai Na Dade banayi Ko?
Shiru kaka tayi tana sauraran shirme nijlah kafin tayi qoqarin cewa,,Hakane Malam Nima Na yadda Na Kuma amince da auren nijlah sedai inaso ka zaba Mata mijin daze Iya Kula da ita!
Haba yakumbo muda zamu Bada sadakanta mune zamu zaba Wanda zamu aura Mata" to ai abin ne' kinga kedai kawai kiyiwa yarinya addu'a.
Kinga dauki wannan kanzon ki jiqamana Musa a cikinmu" Ni Allah gari kwaki nakeso ba kanzo ba nijlah ta fada cike da shagwaba,,rarrashinta Malam yayi yayinda yakumbo ta tafara jiqa qanzon,,bako Mai haka ta zuba kuli suka ci.
Suna gamawa Malam ya tafi gidan kakannin nijlah Na wurin uwa,,anan ya samesu da magana nan,Basu Bada matsala ba Dan kowa ya amince,nan ya dawo gida cike da farin ciki Na samun nasara Dan a ganinsa auran da nijlah shine Abu mafi sauqi daze Bata farin cikin dasuka kasa Sama Mata Shi a matsayinta Na marainiya Kuma jika a gurin su..
*******
Zaune take ta hannu biyu Akan kumatu da alama tayi zurfi cikin tinanin,,a hankali ta cire hannu ta dauko wayanta dake Kan center table ta qara Danna Kiran layinsa.
Abu daya Ake gayamata Dan haka tayi cilli da wayan tana Tashi tsaye,,Saida Nace karkayi tafiyan nan Amma ka dage Saida kayi gashinan wayama ya gagaremu sedai kayi kasamu lokaci ka Kira,,Anya kuwa mashkur be samu matsala ba..
Girgiza kai daddy yayi Yana qarasowa kusa da mummy, nan ya zauna kusa da ita Yana kallanta cike da kulawa yace,,
Haba Khadija Se yaushe Zan gayamiki kidena sa damuwa a ranki,girma fa ya kamaki,,Karki sa ciwo yamiki illah Akan abinda bashida Wani illah..
Haba Alhaji Taya kake tinanin hankalina Ze kwanta Akan tafiyan mashkur,kako je kauyen kaga inda yake zaune,, toyaya kikeso ayimasa, mashkur Dai ba yarone qarami ba,da inyaji wahala Baze dawo gida ba,Kuma kina kallo nasama masa admission a UK Amma fur yaran nan yace bayaso ga idda yake muradi Toba seki barshi yaje yayi ba..
Cikin kuka mummy tace haba Alhaji kana nufin haka zamu zuba ido mashkur ya zauna cikin matsiyatan mutane dako Nama Sai su shekara Basu Ciba,,to wallahi Bazan taba yadda ba gwara tin farko kasan yadda zakayi da danka..
Girgiza kai daddy yayi Yana Kallan mummy yace" yanzu Ke Khadija Harkin isa ki aibata Fulani kokin manta Nima bafulatani ne,, dasauri mummy tace Amma Dai ba irinsu ba.
Cikin fishi daddy yace,Koma Dai menene jinin fulani kike aure Dan haka ki kyale yaro ya qarasa karatunsa Koma menene saikiyi Daga Baya,,
Turo baki mummy tayi ta Tashi dasauri ta Koma daki tana Kiran babban danta..
Hello mummyna barka da yamma,,yauwa Ibrahim,,mummy lafiya Naji muryanki haka,, mummy Ko baki da lafiya ne,,kuka mummy tasa tana cewa..
Ibrahim ka Kira wannan yaran ka gayamasa ya dawo gida, mashkur Yana neman doramin hawan jini.
Eyyah Mummy meya Samu mashkur din,, mummy Ko jiya munyi waya dashi yace Yana zaune lafiya a garin dayake" toka gayamasa ya dawo gida banasan zamansa cikin wadannan mutanan indai yanasan zamana dashi lafiya.
Shikenan mummy kiyi hakuri zanyi Magana dashi,,eh ka gayamasa yayi saurin neman transfer yadawo cikin gari,,to mummy kiyi hakuri insha Allahu Ze dawo,,kashe wayan mummy tayi tare da sakin tsaki..
*******
Tinda Malam ya Tashi yasa a ransa Yau Ze Bada auren nijlah gako wanne irin mutum ne indai yanada kamala Kuma Ze Iya riqe nijlah..
Yakumbo ya Samu da maganan yayi sa'a Bata bashi matsala ba ta Kuma amince tare da Tarin adduointa ga auren jikar Tata.
Comments &share
*Momn sultan ce*✍✍✍
đđ *'YAR SADAKA..*đđ
*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*MMN MUHAMMAD*
9⃣&1⃣0⃣
Tinda Malam ya fita be qara yiwa yakumbo maganar auren nijlah ba,gashi Yau Har anyi wata guda, Dan haka yakumbo ta garzaya zuwa gidan jummai dillaliya Akan tanaso Akai nijlah birni itama tayi aikatau kosa Samu su rage zafi.
Dakyar jummai ta yadda Dan acewarta nijlah 'yar shagwabace su Kuma alhazan birni Basu San shagwababbun yara indai ba nasu bane,,Seda yakumbo ta Hada da ban hakuri tare da cewa zata jama nijlah kunne..
Nijlah Najin batin aiki tayi murna tare da cewa bazata yimusu rigima ba,,nan yakumbo ta Maida hankali gurin tafiyan nijlah birni aikatau..
Yau nijlah da farin ciki ta Tashi sabida ana bikin yayar kawarta,tinda safe ta tafi Suna party, yayinda Ake al'adu irin Na Fulani.
Ke kikace kinaso amarya,,da bakyaso da ba'a Baki shiba,,haka 'yammata suka riqa wucewa suna rera waqa,,gefe guda manyan matane dauke da wata yarinya 'yar qarama bisa doki,,kawunan kowacce su dauke da kwalla da fanteka sai 'yan komatsan Kaya!!!
Ta ko ina suke shigewa,, wasu gada cikinsu suna rangada guda ...
Tsaki mashkur yaja Yana kallan abokan nasa da sukabi tawagar Yan Kai amarya da kallo,,, washe Baki Bello yayi Yana cewa kagani fa,, aure ya tabbata,, Allah yasanya alkairi,,duka sauran Suka amsa,da ameen Banda mashkur Daya hade giran Sama data qasa...
Kai dallah Malam ware,idan zaka zabo yarinya a karkaran nan ka zaba,bamusan wannan miskilancin naka,, daba kaiwa zuci yayi ba..
Allah ya sawaqe,,ni duk garin nan babu yarinya data isa aura agurina,,Dan wallahi Basu Kai Mata ba,,Zan so kuje birni Kuga inda Mata suke,, hhhhh Bello ya fada Yana kallan mashkur..
Kai kujimin Dan rainin hankalin nan to idan ba Mata bane suwaye""' yauwa tambaya mana Shi cewan Nasir dake zuwa gurin...
Kwailayene,, ko nayi karya,, gaba daya suka amsa da cewa kwarai ma kuwa..
Tabe Baki mashkur yayi Yana cewa,,Ku duba yarinyar nan indo, dududu shekaranta nawa Amma har Malam ya'u ya auran da ita?
eh mana kuma Ka zuba ido nan da wata Tara zata iya haihuwa,, ai mu matanmu na karkara da iya zaman aure suke ba irin naku na birni ba..
Dariya mashkur yayi Yana Sosa Dan yafisu Sanin abinda yake Gaya,,sedai su bazasu gane hakan ba,,sabida nasu al'adan suka sani...
Shirune ya ratsa gurin kafin Nasir yace,, to wai Kai mashkur dama ba soyayya kake da nizlah bah'' qayataccen murmushi mashkur yayi Yana Sosa Kai yace,,
Ai nizlah kanwace agareni,,ina kuma yimata so Wanda bansan irinsaba,, dan da ace ta isa aure nizan aureta na kaita can birni itama ta waye,,
Dariya suka sa suna kallan mashkur Wanda tinda aka ambaci sunan nizlah bakinsa yaqi rufuwa,,,
Koma dai menene munsan kana San nizlah,, Dan shaguwarku da ita abin dubawa ne, Nasir ya fada Yana kallan Bello..
Dariya Bello yayi shiko mashkur ya zuba musu Ido Yana kallansu,, be iya magana ba sabida Jin Kiran sallah da yayi..
Ni kunga tafiyana,, kafin kumin wani fassara na daban,, atare suka tashi suna qara jandada masa abinda ke zuciyarsa...
Sedai Shi Babu wannan a ransa soyayyar Yasmeen kawai yakeji,sedai Yana yiwa nijlah so irin Na tausayawa Amma Bada aure ba.
*******************
Uhmn uhmn,, Allah ni saikin Bani biyar naje dandali,, yaushe raban daki Bani biyar dinki,, kodan kinga Dan birni Yana Bani,,kayya nijlah,, Nima Bani dashine,da inadashi Babu abinda Ze Hana ni baki..
Turo baki nijlah tayi tana kuka tare da birgima a qasa,, kayya mezan gani haka sukaji Malam ya fada,,yakumbo kodai Wani Abu kikayiwa yarinyar nan..
Kai madai Malam Sai kace bakasan halin nijlah ba,, wannan kukan daka ga tanayi Bana komai bane illah Na naira biyar,, ita adole Saina Bata biyar ta kashe,Nace Bani dashi ta kwanta tana birgima,,kaga Idan kayan jikinta yayi datti Sai Muga inda Zan samu kudin sabulun wanki..
Girgiza kai malam yayi Bayan yagama Jin bayanin yakumbo,,nijlah Ko Bata daina birgima ba Dan Har tirken dabobi ta kai tanayi...
Ahankali Malam ya taka ya isa Har inda take ya kamo hannunta"ba musu ta tashi tana turo baki,,kiyi hakuri kinji nijlah ta,,gobe Idan Allah ya kaimu naira Goma Zan baki kije dandali kisai Duk abinda kikeso..
Kawu dagaske kake,,nijlah ta fada tana kallan bakinshi,, kai nijlah meyasa wayenki yayi yawa,,kin tabaji Malam yayi Karya??sukaji yakumbo na tambaya..
Shiru nizlah tayi tana girgiza kai,,Sai kuma tace,,Naga yataba cewa Nima za'a kaini birni nayi aiki irin na jummai,Amma haryanzu be kaini ba,,Kuma Naga hajiyar tana zuwa...
Bata rai Malam yayi yace,kinga nijlah banasan shirme,,kima ajiye wannan maganar Babu ita,,haba Malam ya zakayi haka,,zuwa aikin nizlah shine cigabanmu,,kana Dai kallo abinda zamu kai bakinmu,,wahala yake mana..
Yakumbo,,Malam ya Kira sunanata Har sau uku,,amsawa tayi tana kallansa,,kisani Daga Yau nafasa kai nijlah aiki,,auran da ita zanyi..
Zaro Ido yakumbo tayi tana kallan nijlah,da tinda aka Kira aure tafara rawa tana juyi,,bakin yakumbo na rawa tace Malam aure fa kace,nawa shekarun nijlah,,yake,saifa gambon wata take shekara Goma..
Ni wallahi nayi tinanin ka janye wannan maganar danaji kwana biyu Baka qara yiba.
Eh, nasani,Naga Dai ba haramun bane,,damu zauna da ita,cikin wahala Ai gwara taje can gidan mijinta Kota samu ladan aure,, wannan wanne irin ladane,,nijlah fa Ko wanke wanke Bata Iya sosaiba,,balle azo maganan gyaran gida,,nidai kayi hakuri a kaita gidan aiki hakan zefimin kwanciyarsa hankali...
Hmm Ni kinga tafiyana,, Naji an tada Sallah,,fita Malam yayi yabar nijlah Na rawa tana cewa yakumbo Nima Zaki saimin wannan abun da Ake dafa tuwo..
Ke dallah rufemin baki,ki Kuma Dena wannan rawan kan,,Ko an gayamiki auren Cin tuwo ne,, fari nijlah tayima yakumbo tana cewa,,eh mana nidai gwara akaini gidana,,nasan Ko Goma Zan riqa samu Ina zuwa dandali,,
Acan masallaci Bayan an idar da Sallah Malam ya matsa kusa da Liman ya gayamasa Magana a hankali,, murmushi Liman yayi Yana cewa,,kayi daidai Malam hukuncin daka yanke yayimin Dadi..
Har mutane sun fara bita akace su dawo za'ayi wata Magana,, lah mashkur zo muje naga mutane na koma cikin masallaci,, jeka kawai nizan jiraka ana,,sabida sanin hali yasa Nasir da Bello suka barshi anan su suka dawo cikin masallacin..
Liman ne yafara magana,,to jama'a Allah ya kashe Yaba Wani,,game dukiyar aure Kuma yake sha'awar qarawa mace yazo gata,, Ko saurayin daya shirya,, charaf,,Wani tsoho yayi saurin Daga hannu..
Malam ne ya katse Liman ta hanyar cewa,, *'YAR SADAKA CE* to kunji abinda Malam yace,,yarinya sadaka ce..
Yauwa ga Wani Chan ansamu Liman ya fada Yana nuna tsohon mutumin dake rankwafe Yana murmushi,,yauwa Ala gafatta Malam matso kusa Liman yace da wannan tsoho,,matsowa tsoho yayi kafin Liman ya tambayeshi.
Menene sunanka,,sunana laman ya'u,,to Malam ya'u,,ita wannan yarinya da kace kanaso sunanta nizlah..
Nijlah,, Nasir ya maimaita Sunan tare da fita aguje Yana Kiran mashkur,,
Mashkur mashkur,Dan Allah mashkur kazo ka cece yarinyarnan indai soyayya na gaskiya kake yimata,,kai lafiya wacce yarinya kake Magana,,bakin Nasir Na rawa yace nijlah ce,,gata can za'a Bada sadakanta..
What kana nufin aurenta za'a Bada,,eh wallahi kayi sauri muje Kar a daura auren,,da gudu suka nufi masallacin mashkur Na tinani a cikin zuciyarsa...
Yanzu Idan na Karbi auren nijlah ya zanyi da Mummy,,Waze yadda temakonta,nayi,tayaya Zan fahimtar da iyayena,, Daga zuwa bautar qasa na biqe da aure,,auren ma Na qaramar yarinya Wanda Bata wuci shekara Goma ba!!!
Da wannan tinani suka Shiga cikin masallaci,sunyi sa'a baa daura auren ba,,sedai ana gab da daura wa,,ku dakata Nasir ya fada Yana nuna mashkur,, wannan shiyafi dacewa da auren nijlah indai sabida Allah za'a Bada sadakanta..
Wannan gaskiya ne, mutane suka amsa Suna goyan Bayan mashkur"" Malam ya'u Najin haka yace Sam be yadda ba..
Akan me nasamu Mata zakumin bakin ciki,, hakuri Liman ya Shiga ba Malam ya'u Amma Duk da haka ya dage Shi saiya auri nijlah..
Nasir ne yace kaga tsoho karka damu,,wannan Ze Baka naira dubu Goma kabar masa ita..
Kai yaro kalla idona Malam ya'u ya fada Yana zaro Ido waje..
Atare Nasir da mashkur suka zuba Alhaji ya'u Ido Suna sauraransa.
Nan alhaji ya'u yacigaba da Magana,,wallahi Ko naira dubu hamsin zaku Bani Bazan hakura da auren nijlah ba,,Har Sai kun auramin budurwa me suffa irin ta nijlah,,
What? What me kace tsoho,,to wallahi Ko ka amsa dubu Goma Ko kayi asara gaba daya,,nan Nasir ya juya inda liman Ke zaune yace..
Liman kaga wannan abokina ne dashi mukeso adaura wannan aure indai Malam ya amince.
To Malam Kaji abinda yaro yace,,Liman yafada Yana Kallan Malam,,
Sassanyan ajiyar zuciya Malam ya safke kafin yace,,Liman Bani da zabi kawai kayi Mata zabin daya dace,,to shikenan Liman ya fada tare da gyaran murya.
A matsayina na limamanin wannan kauye Zan auran auren nijlah da wannan yaro,kai yaro Mene sunanka"" kasa Magana mashkur yayi nasir yayi saurin cewa mashkur Hussain.
To Masha Allah, mashkur ka amince Zaka auri nijlah,, mashkur besan lokacin daya Daga kai alaman eh ba.
Ba'a Wani bata lokaci ba aka daura auren nijlah abbakar tare da zankadeden angonta..
Nan Alhaji ya'u ya riqa zagege zagege Yana cewa an nuna bare yafisu,, ya qara da cewa Allah yasa Dan birni ya siyar da nijlah kowa ya huta,,maganganu marasa kai da gindi ya riqayi Har Saida manyan 'ya'yansa suka fiddashi a masallacin.
Mashkur Na fito yaji Wani irin tashin hankali ya ziyarci zuciyarshi nan ya barsu Nasir Suna tattaunawa da Malam Dan koya tsaya Baze Iya cewa komai ba sabida tsantsar tashin hankali..
Jiyayi Idan beyi waya da mummy ba Baze samu kwanciyar hankali ba, Dan haka ya nufi inda suke waya,, Da zuwashi ya fara Kiran layin mummy sedai wayar Na Shiga mummy taqi amsawa tana me Jin haushinsa.
Karin ya qara Kira wayar yaya ta shigo,,nan yayi saurin kai hannu ya dauka Yana Kiran hello yayan mashkur,,ba Wani yayan mashkur da Zaka kirani,,kasa mana uwa a tashin hankali sabida bakasan me kake ba Ko mashkur???
Kayi hakuri yaya wallahi ban tafi da fishin mummy ba Har Saida ta amince Na tafi"
Karya kake mutumin banza da wufi,ahaka kakeso karatun yayima albarka?
Kayi hakuri yaya mashkur yafada zuciyansa Na halbawa day sauri da sauri.
Inaso ka Bude kunnanka da kyau ka saurarani" bakin mashkur Na rawa ya amsa da to yaya.
Kaje yanzu ka Hada kayanka ka dawo gida Idan Har bakasan bacin ranmu" Wani irin Abu mashkur yaji ya buqi zuciyarsa Har Sai da ya dafe da hannunsa yace ,yaya Yau fa kace?
Eh Yau Nace Ko bazaka iyaba Ni a gobe Na dawo qasar nazo Har inda kake,,ah ah yaya kayi hakuri Zan dawo yafada yanajin kuka Na zuwa masa,,yadau Fi kyau yaya ya fada Yana katse Kiran.
Hannu mashkur ya Dora akai Yana cewa Na Shiga uku Ni mashkur meya kaini auren nijlah gashi Ina neman sa kaina a 100,yanzu yaya zanyi?
Be Iya samun amsa ba yaji Wani Kiran Na shigowa cikin wayarsa" Yana dubawa Yana aunty ladefa,zaro Ido yayi waje Yana tinanin fadan da aunty ladeefah zata masa,sedai Baze Iya Qin daukaba sabida yasan abinda Ze biyo baya,hannunsa Na rawa ya dauka Yana Kara wayar a kunne aunty ladeefah tafara da...................
Dan Allah Dan annabi Idan kinsan bazaki Iya comments ba Karki soma karantawa.
Comments &shaređ
*Momn sultan takuce*
đđ *'YAR SADAKA..*đđ
*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*HAJJA FATI...*
1⃣1⃣&1⃣2⃣
Ashe Baka da kirki mashkur,mahaifiyar tamu kakesan kashewa" Anya ko kanasan albarka a karatun naka"
Aunty me kuma nayi,uwarka kayi Dan bantan ubanka,, mashkur ni kake tambaya abinda kayi Dan qaniyanka???
Sanin halin aunty ladeefah da fada yasashi cewa ah ah,,Amma aunty" Amma me Ka rufemin Baki, ko kanaso kagayamin karatunka da zuwa wannan mugun kauyen yafi mummy daraja,,dasauri ya Shiga girgiza Kai kama tana kallanshi...
Au rainin hankalin naka harya Kai ina magana kayimin shiru"
Haba aunty bafa Nina Kai kaina wannan rigar ba,kaini akayi kuma wallahi bantafi ba Saida Mummy ta amince yafada cikin sanyin murya.
To yanzu tace bataso Dan haka Ka tattara kayanka Ka dawo kafin nazo har garin naci maka"
Amma aunty kinsan ko rabi banyi a aikin nan ba,, sai dagamin hankali kuke"inye mashkur nikake gayama haka,,ba laifinka bane laifin mummy ne datake daure maka gindi"
Kiyi hakuri aunty amma"Amma me to wallahi Ka sani a yau nakeso Ka dawo gida kafin gobe, Nima a gobe Zan zo qasar nida yaya saika gayamana dalilin dayasa kakesan dorawa uwarmu hawan jini??
Aunty yanzu yamma yayi bazan iya tafiyan dare ba,,kaika sani nidai magayama karka Bari mu riga zuwa qasar Dan jirgin asuba zamu hau..! Shiru yayi Yana sauraranta batare daya iya magana ba..
Cigaba da magana aunty ladeefah tayi tana cewa, Banda shashanci irin naka mashkur kafi kowa Sanin halin mummy tinda Kai kake zaune da ita Amma Ka take Sanin Ka tafi gurin da tafi tsana a zuciyanta" kana kallo tin muna yara mummy batasan zuwa kauye balle harta rabi Fulani,,kodan lokacin bakada wayo...
Zuciyarsa na quna tare da tilin Dana Sanin zuwanshi wannan kauye yace aunty kiyi Insha Allahu goben Zan zo kafin kuzo,,ni inaga dakun hakura da zuwa nizan ba Mummy hakuri..
Bazamu fasa zuwa ba,,ok kanaso kaje ta lallabeta taqi nuna damuwanta akai bayan Ka dagamata hankali muma Ka dagamana''cikin sanyin jiki da tinanin irin tashin hankalin daze tarar a gida yace shikenan aunty..kit ta katse Kiran tanajan dogon tsaki tare da cewa yaro besan komai ba sai bin talakawa kaskantantu wulaqantantu wadanda Basu San komai ba sai yawo a jeji da shanaye..
Tinda mashkur ya Gama waya ya zauna a gindin bishiyar dafe da kansa Yana ji kama ze fado qasa sabida sarawan dayake masa" dakyar ya iya daga qafafunsa yafara tafiya Yana hada hanya harya Kai dakinsu"
Kan katifanshi ya kwanta hannunsa dafe da kansa yanajin zuciyarsa na azalzalasa akan abubuwa da dama,,rintse idonsa yayi yanasan bacci ya daukeshi sedai abin ya gagara Dan a yadda yakeji bacci baze taba daukansa duk kuwa da irin sunan dayayi gurin satar mutane,,runtse Ido yayi Yana hango kyankyawar fuskar nijlah,, qirjinta yake hanqe yaga Babu komai a jikinta danko qirgan danqi Bata fara ba,,sedai nijlah akwai iyaye dasan ado da kwalliya Duk da Bata da kayan kirki Amma kullum saita chanza Koda Bata samu sabulun wanki ba,,sosai ya zurfafa cikin tinanin yarinyar tare da yaban halayenta,,abu daya yakeji tare da ita shine rigima,,yasani Idan tafara rigima bataji Bata gani saita kwana tana kuka" oh Allah ya fada a Fili,,yanzu Idan nijlah tafara wannan kukan yaya zeyi da ita,,wanne irin mataki mummy zata dauka akansu gaba daya,,Rasa amsa dayayine yasashi saurin Tashi ya fita.
Alwala ya daura nan ya dawo Daki ya shinfida Sallaya..
Sallah yayi Har raka'a biyu nan ya dungura kanshi a qasa Yana neman dauki a gurin Allah..
Bayan an fidda Alhaji ya'u,,Liman yafara Magana kama haka" Malam inaga yakamata mu qarasa gida Domin ayiwa yakumbo bayanin abinda Ke faruwa tare da gayamata wannan aurin aure..
Hakane Liman sedai Ina tsoran yadda yakumbo zata riski wannan labari,,bansan yadda zata dauki rabuwa da nijlah ba,,Malam yaqare maganar da cikin kuka Wanda baza'a kirashi Na bakin ciki ba,,Sai Dai Ko farin ciki..
Haba Malam yaya da kuka,kaida zakayi farin ciki gashi yarinya tayi dacen Miji bame San hayaniya ba..
Kwarai dagaske cewan Nasir,, Ai Liman Idan kaga mashkur yayi Magana to ba qaramin Abu akeyi ba,,bashida San hayaniya,wallahi tinda muka taso da mashkur bantaba ganin abokin fadan Saba kowa yabansa yake,,shiyasa nazabawa nijlah Shi Duk da nasan wasu zasuyi tambaya Shin Ni meya hanani aurenta nasa abokina yayi?
Nan mutane sukafara surutu Suna fito da tambayan dankuwa sunga lokacin da Nasir Ke gayawa mashkur yazo ya taimaki nijlah" wasu nacewa shimeya hanashi taimakonta indai Dan Allah take..
Kuyi hakuri yanzu Zan Baku amsar tambayoyinku" wallahi Ni Nasir Zan Iya auren nijlah Duk da Babu shaguwa tsakanina da ita Kamar yadda ta Shaqu Na mashkur,,sedai banqi amsar aurenta sabida komai ba sedai, Ni inada zafi Bani da rigima sannan abu kadan Ke batamin Rai nayita jibgar yara,,Idan Ko sa'anane Daga lokacin Ina Iya Dena abota dashi..
Nan ya numfasa yace mashkur kadai Ke Iya Zama Dani sabida miskilanci irin nashi da hakuri Wanda Koda nayi Abu sedai yace Allah ya shiryeka koya girgiza kai,,Idan Ko fada Na tsokalo shike Bada hakuri Har adawo daidai.
Natabbata wannan dalili nawa ya isa kugane nijlah ba sa'ar aurena bace Duba da yanayin rigimarta ta Babu gaira Babu dalili..
Sosai Yan gurin sukasa dariya,Bello yace ainaga alama shiyasa Daga zuwanka garinnan kafara Dukan yaran gari" Aina nasan haka halinka yake da rufdugu zamuma" nan ma dariya akayi kafin Liman yace.
Babu shakka Nasir munji dadin kalamanta akan abokinka Kuma muna fada abinda ka fada ya Zama gaskiya" insha Allahu Nasir yafada kanshi a qasa.
To Malam yakamata mu tafi Ko,,nan suka Tashi suka tafi gidan Malam.
Yakumbo dake zaune nijlah nakan cinyanta tana rigima Taji sallamar Malam,,amsawa yakumbo tayi tana kallan nijlah tace.
Toga malam yazo Naga Yana murmushi ga dukkan alamu yayi samuwa inaga Yau zakici shinkafa da miyar dakiketa mafarki"turo baki nijlah tayi tana kallan Malam kafin ta kurma uban ihu tana cewa.
Wallahi yakumbo Babu abinda yakawo bakiga hannunsa Babu komai ba,,nidai Allah saikin siyamin burodi...
Qarasawa Malam yayi ya cewa kinga Yar albarka Tashi kizo kiji Abu Wani Na tabbata Zakiyi farin ciki kinji Yar gidan kaka..
Maqe kafada tayi tana birgima a qasa,,nan Malam ya Kalli yakumbo yace,,kinga yakumbo dauko tabarma ki shinfida a rumfa ya fada Yana nuna yaloluwar rumfar Kara dake maqale jikin Dakin daba lallai ya wuci damuna ba,,
Shinfida tabarma yakumbo tayi tana cewa Ikon Allah suwa muka Samu,,Malam kodai Yau zakka ta biyo ta gidanmu.
Kedai ki shinfida kafin nayimiki albishir,,nan Malam ya juya Yana cewa ku shigo Daga ciki..
Liman ne a gaba Sai Nasir da Bello tare da sauran mutane dake tayasu murna,,wasu Ko yan uwan mahaifiyar nijlah ne...
Tinda suka shigo yakumbo tabisu da kallo tana mamakin abinda ya kawosu adaidai wannan lokaci Kuma gaba dayansu,,kowanne ta Kalla fuskanshi dauke da annuri,,nan ta zauna Kan buhun dawa tana binsu da kallo..
Kinga yakumbo ruwa Zaki Basu ba wannan kallanba,,gaba daya suka Hada baki gurin cewa ah ah alhamdulillah ta zauna kawai muyi abinda ya kawomu..
Gaisu yakumbo tafara nan Taji suna yimata Allah ya Sanya alkairi" Seda suka gama ta juyo tana kallan Liman tace,,Liman me Kuma ya faru Naji ana yimin addu'a..
Eh yakumbo Yau Dai Allah yayi an daura auren yarinyarki" wacce yarinya Liman??, yakumbo ta tambaya mejin faduwar gaba,, nijlah dake kwance a qasa tana sharar hawaye tayi Shiru tana sauraransu tasan Dai ita dayace yarinyar yakumbo Dan haka ta Maida hankalinta gaba daya Kan Liman tanajin amsar dayake bawa yakumbo..
Yakumbo yarki nijlah,yanzun nan,Bayan idar da salla malam yabada aurenta ga.....Ai nijlah Bata jira Jin wane angon ba ta Tashi da gudu sabida Jin Kunya ya kamata,,Daki ta Shiga ta dauko dakalmin Danko Wanda yasha dinki da zare da allura tasa ta fita da gudu ta Bayan gidan,,kasan cewar gidan bashi da danga Babu Wanda ya Ganta.
Mashkur" zabura yakumbo tayi ta miqe tsaye cikin rashin hankali da dimuwa tace,,badai wannan yaran mashkur ba,da naira hamsin bashi masa wahalan badawa???
Eh shifa Malam ya fada Yana Kallan yadda yakumbo ta haukace ta tubure masa..
To Wallahi Baze taba yiwuwa ba ,Akan me Zaka auran da nijlah ga Bako Wanda bamusan asalinsa ba,hasalina karatun arnane ya kawoshi ruga...
Haba yakumbo be kamata kina fadar hakaba,,kinga Nasir yabamu labarin mashkur bashida Wani matsala ki kwantar da Hankalinki.
Cikin kuka yakumbo tace haba Liman yanzu shikenan nijlah zata tafi ta barni" Bazan iyaba,kugayamasa wallahi ki warware wannan aure aba Dan gari yadda koya na juya zanga marainiya,,Anya Ko Malam ka riqe amanar da danmu yabari,,kaico mutuwa kinyiwa yarinyar shigar sauri,wayyo niya Allah Na,,nan fa yakumbo ta juya tana fillanci Niko nayi zugun tare sauraranta sedai banji abinda take gayaba,,ta jima tana kuka kafin Daga bisani sukayi nasaran shawo hankalinta..
Haba yakumbo meyasa Zaki haka,,kinsan bakisan auren Kika yadda naje naba,,kaga Malam niba aureni Bani so Wanda Kaba auren nijlah Baze taba Zama kusa damu ba nijlah zatayi nesa damu bamusan rayuwar dazatayi ba.
Insha Allahu nijlah zatayi rayuwa me kyau ku kwantar da Hankalinku cewar nasir cike da tausayin yakumbo..
To Amma Dai ba yanzu Ze tafi da itaba ko??eh saimun gama service nan da wata 9 insha Allah" gaskiya yayi wuri yadai Yi hakuri Sai nijlah ta qara wayo nan shekara biyu saiya dauketa,,cewan yakumbo tana hawaye.
Shiru Nasir yayi ganin yadda tsohuwan ta Shiga Wani Hali yace to shikenan,,nan sukayi Mata sallama kowa ya tafi gida..
Nasir da Malam Sai Liman suka tsaya Suna tattaunawa..
Tinda nijlah ta fita da gudu ta Shiga gidan kawayenta tana Kiran su daya Bayan dayan,,bayan sun gama hallara ta fara rawa tana cewa Yau ranar auren nijlah Dan haka kowa ya shirya za'ayi wasa Na kece Raini Yau Yar gidan kaka da Malam zata Hada wasa a dandali..
Yeeeeeeee Yau akwai wasa,,ihu suka sa irin na murna suka sukafara zagaye Dan garin Suna waqa..
*'yan wasa ku fito wasa,Idan baku zoba samarinku suzo Bani Na fadaba angon nijlah ne,,angon nijlah ne me jan baki....*
Haka suka riqa waqa Suna wasa Suna Tara jama'a,,cikin lokaci kalilan nijlah da kawayenta suka cika dandali da jama'a" sosai gurin ya cika yakuma kawatar nan fa dandali me kidan kagane yasaki kalanginsa tare da masu kidan kwarya,,masu Kayan saidawa Suma baa barsu Baya ba sun zo..
Kamar yadda akeyi a kowanne biki haka nijlah da kawayenta sukayi Dan sun cika dandali da jama'a anata wasa irin na Fulani,tare da al"Ada irin ta da..
Liman dake tsaye Suna Magana yace,malam kama kida nakeji a dandali" eh Liman Nima haka nakeji Kuma Dai yanzu ba lokacin zuwa dandali bane"
Suna cikin haka saiga wasu yammata Suna tafiya,,Malam ne yace ku yara Ina zuwa,, Malam muna wasan bikin nijlah ne,,tafada tana cigaba da tafiya.
Cike da mamaki yace Ina ita nijlah,,tana dandali tabasu amsa ,, murmushi Malam yayi Dan yasan nijlah zata aikata Duba da yadda takesan auren,,a Fili yace yaro yaro ne kajifa Liman bikin aure sukeyi a dandali.
Eh Ai ta birgeni kaga baza'ayi aure irin Na yaseer da fatima ba,,dariya suka sa,,Liman yace Aiko Yau dandali Ze dauki jama'a Nima baza'a barni Abaya ba..
Tinda suka fita aka zo aka Gaya yakumbo nijlah Na dandali,, murmushi yakumbo tayi ta Rasa inda zatasa Kanta,shin me zatayi farin ciki Ko me..
Ta tabbata Idan tayi baqin ciki ta yiwa Allah butulci Dan haka ta karkata zuwa farin ciki nan itama ta tafi dandali Dan Taya diyar Tata farin ciki..
Bayan tafiyarsu Liman Nasir be bisu dandali ba Dan yace saiyaje ya taho da ango.
Sosai ya riqa sauri harya kai Daki,,nan ya Shiga Yana Kiran mashkur,, mashkur dake zaune Yana Hada Kaya zuciyarsa na quna ya dago jajayen idanunsa ya zuba Nasir.
Dasauri Nasir ya qarasa kusa dashi ,hannunsa ya riqe yace,, mashkur lafiya naganka haka kama Wanda yayi jinya Na wata guda.
Kabari kawai nasir Ina cikin tashin hankali,,ban taba Shiga cikin matsala irin na yanzu ba,,Dana dauki abun da sauqi yanzu Ko magane shayi ruwane,,
Nasir adaidai lokacin da aka dauramin aure Sai gashi a lokacin iyayena da 'yan uwana sukesan rabani da wannan gari Nasir yaya zanyi..
Haba mashkur Kamar yaya, meyasa Zaka kayawa mummy wannan aure Bayan kasan halin mummy" cikin faduwar gaba mashkur yace.
Ban gayamata ba Nasir kafi kowa sanin yadda mummy take Sona take kaunata,,Na tabbata inda mutuwa zata zo daukana mummy zata Iya fansar Raina da nata" Amma kaga mummy tadau zafi Dani harta Kira manyan yayyena ta gayamusu..
Nasir Bani da yadda zanyi,,yazama Dole a Yau Dinan nabar garin nan indai inasan zaman lafiya.
What! Mashkur me kake nufi,,yaya zakayi da nijlah??
Nasir Zan dauki matata,da ita Zan tafi,,Iya wuya Ina tare da ita..
Niko Nace Kamar yadda muke Kenan lolxx....
Kudaure kuna sharing labarinan, Domin wasu su amfana.
Comments & share.
*Momn sultan ce*✍✍✍
đđ *'YAR SADAKA..*đđ
*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*N@DI@*
1⃣5⃣&1⃣6⃣
Wayyo Allah,,yau Naga ta kaina yanzu mezan Gaya iyayen yarinyarnan,,zagaye titi Bello ya riqayi Yana kallan Motan har Saida suka bacewa ganinsa kafin ya daga qafa yaname danasanin amincewa da rakiyan nijlah..
Yanzu mezan Gaya Kaka,,wanne dalili nake dashi Wanda ze tabbatar musu da maganata gaskiya ce,,sosai ya zurfafa cikin tunani Yana tafiya Yana hada hanya a haka harya Kai kauyen kankan,Yana zuwa dakin Nasir ya Shiga nan ya Samu Nasir ya zuba tagumi Yana tinanin rayuwar kadaicin dazeyi a wannan kauye Shi Daya ba abokinsa..
Ko sallama Bello beba yafara da masifa,,Kai Ashe wannan abokin naka bashida kunya,,miskilancin banza yakewa mutane"" dagowa Nasir yayi Yana kallan Bello da jajayen idanunsa yace" lafiya Bello,,Naganka anan?
To a ina zaka ganni Saida muka Shiga mota abokinka ya hankadoni waje,,yace wai ba inda Zan bishi daga Shi sai matarsa zasu tafi,,yanzu me kake tsammanin yakumbo ya dauka,,ni wallahi harna Fara tinanin mashkur Dan yankan Kaine..
Tinda Bello yafara magana Nasir yake dariya harya Kai Aya Nasir be dena dariya ba yanayi Yana kallan Bello,,haushine yakama Bello nan ya Fara hararan Nasir Yana cewa,,Ara ta kanni indai Yanke Kan nijlah zakuyi kaima bamu barinka Ka fita lafiya a wannan kauye..
Nasir be kulaba Saida yagama dariya kafin ya kama hannun Bello Yana cewa,, cool down abokina,,kaga niban iya yaran arna ba,,idan zaka gayamin da Hausa ko fulatanci Ka gayamin..
To shikenan zauna muyi magana,,wacce magana zamuyi alhalin an tafi da nijlah bamusan inda suke ba,,yanzu idan kaima kabi dare Ka gudu ina muka kama..
Haba Bello Ka kwantar da hankalinka nagayama babu wata matsala,,kuma ninasan abinda yasa mashkur yayi haka,,yanzu idan Kaine Ka tafi kiwan shanu sai Ka dawo gida da Mata,,wanne dalili zaka Gaya iyayenka" shiru Bello yayi Yana nazari kafin yace,,Zan gayamusu tsintota nayi a hanya,,to kagani kaima karya zaka Gaya iyayenka,,to tayaya kake tinanin mashkur ze tafi dakai ga kuma nijlah Wanda ya aure batare da Sanin iyayensa ko danginsaba..
Shiyasa akace yabarta anan yafara zuwa ya sanar da iyayensa kafin yakai musu ita,,yanzu ya zeyi Kenan,,Nima bansani ba cewan Nasir Yana qara cigaba da magana..
Inaga wani tinani yayi shiyasa yace Ka dawo shize tafi da nijlah,,Dan haka nakeso kace Kaine kafasa zuwa birni kace su tafi kawai sabida gani kuna ganina,,duk ranar dazan tafi saimu rankaya daku kuje can birni Kuga inda nijlah take,,koya kake gani za'ayi??
Amma Nasir tayaya kake tinanin yakumbo da Malam zasu yadda da wannan karyan,,zasu yadda sai kaqara da cewa dare ne yayi Baku samu mota ba,,dakyar aka samu guda shima gurin mutum dayane,,shine mashkur ya zauna ya Dora nijlah akan cinyensa suka tafi..
Eh to gwara wannan shawaran Amma bazan fita a dakin nan ba sai dare,,hakan yayi,,nan dai suka cigaba da tattaunawa Nasir Yana qara kwamtarwa sa Bello hankali.......
*************
Karfe 1 na Rana a garin Kano yama aunty lateefah,tinda ta Shiga gidan tafara Kiran mummy,,duk ta inda tabi ma'aikatane ke gaisheta sedai ba Wanda ta amsa tana tafiya tana Kiran mummy harta isa dakinta..
Kwance ta Sami mummy ta zuba tagumi tana Kiran layin mashkur,,mummy na ganin lateefah tayi cilli da wayan tana cewa,, shikenan mashkur,, shikenan tinda bayana kakesan gani,,da gudu lateefah ta qarasa kusa da mummy tana tambayanta?
Mummy meya faru da mashkur menene kuma,,ko haryanzu be dawo gida ba?
Ina ze dawo lateefah yafiso saina mutu ze dawo gidannan,, wannan wanne irin karatu yarannan take da Har yazabi bacin raina..
Hannu ladeefah tasa tana gogewa mummy hawaye,,kiyi hakuri Mummy kina kallo nabar aikina Na dawo Nigeria sabida abinda yarannan ya aikata,,duk Da yace Ke Kika amince Amma banji dadin yadda Kika Tashi Hankalinki ba,mummy mashkur ba yaro bane Duk inda yake Ze Iya Kula da kansa,,Kuma shikenan seya tafi cikin matsiyata masu yawo a Jeje wadanda Basu da Wani abinci Sai nono,, wallahi Bazan lamuntaba koya dawo Ko hankalin kowa ya Tashi a gidannan..
Kiyi hakuri Mummy nasan Duk inda mashkur yake Yana hanya"Koda yazo Baze shigomin gida ba Sai an kaishi hospital an Duba lafiyarsa,,nasan zuwa yanzu yaci abubuwa marasa kyau da zasu Iya taba lafiyarsa,,Kuma inaso kufara kaishi toilet Na Baya yayi wankan kafin ya shigomin Daki...
Shikenan mummy za'ayi yadda kikace,,Abu daya nakeso ki kwantar da Hankalinki,,haba lateefa tayaya hankali Ze kwanta Ina zaune cikin Jin Dadi auta Yana cikin wahala kinga lateefa Idan Baze zoba kuje ku daukomin Shi Dan wallahi Na tsani Zama da wadannan mutanan,,shiyasa kikaga Ko nono Bana sha..
Ajiyar zuciya lateefah ta safke tana kallan mummy tana girgiza kai tace,,Dan Allah mummy ki rage wannan damuwan kinsani Idan daddy yaji Baze tabajin Dadi ba,,cike da fada mummy tace.
To yaji man Idan yaji saime dukana zeyi,,Koshi yayi irin wannan rayuwar ne,,Amma mummy Amma me Dan ubanki,,karfa ki batamin Rai.
Kiyi hakuri Mummy Naga Dai daddy Shima bafulatani ne,,kidena nuna kyamarsu a Fili Hakan Ze riqa sosamasa Rai..
Badai kema kina Bayan wadannan mutanan ba mutanan da saisu shekara Goma basuci Nama ba,,mummy kinsan nafiki tsanar Zama a irin wannan guri kawai Dai banaso kina fada agaban daddy..
Sallama Yaya yayi suka amsa nan ya Samu guri kusa da mummy ya zauna Yana gaisheta,,dauke kai mummy tayi taqi amsawa dan a ganinta basuyiwa mashkur Magana ba shiyasa be dawo ba..
Lateefah ce tayiwa Yaya sannu da zuwa nan ya amsa Yana cewa Ina mashkur yake?
Yaya be dawo ba Nima tinda nazo nake zuba idansa gashi Har 4 Na yamma be qaraso ba,,Anya Ko ya taho?
Eh Yana hanya dazu munyi Magana dashi yace nan da 2 hours ze Iya qarasowa..
lateefah meya Samu mummy Ko Bata da lafiya?
Bansani ba,,kaida Nace kagayamasa ya dawo da wuri shine harka samu damar zuwa shibe qarasoba,,kiyi hakuri Mummy kinsan yanayin haryarsu Sai ya hau Mota biyu kafin su zo,,Nace driver zeyi daukansa yace harya kama hanya" karyane wallahi kunsan Allah Idan be dawo Yau ba Saina Saba muku a cikin gidannan..
Tinda daddy ya shigo yafara Jin hayaniya harya shigo falo ya Samesu zaune sun sa mummy tsakiya Suna Bata hakuri..
Daya Bayan daya ya riqa kallansu Yana mamakin zuwansu,,sannu da zuwa sukayi masa ya amsa tare da neman guri ya zauna Yana Kallan mummy yace..
Yanzu abinda kikeyi ya dace Kenan agaban yaranki kina zauna kina koya musu dabi'a mara kyau ta rashin sanin darajar Dan Adam,,to Wallahi kisani kowa da Kika gani da baiwar da Allah yayi masa dan haka kibi Duniya a sannu" turo baki mummy tayi ta budeshi a hankali tace,,to Ni menayi kawai Dan Nace yarona ya dawo gareni Sai ka kama fada kana fishi Dani"
Ki rufemin baki,,kosu Fulanin ba Allah ya haliccesu ba,kinsan bakisan Fulani Kika auri jininsu,,Maryam a gidana Kika Zama abinda Kika Zama shine yanzu Har Kika Iya ....." Daddy kayi hakuri Kasan halin mummy tinba yanzu ba,,kasani Ko kauyensu Inna wuro batasan zuwa Har Allah yamata rasuwa,,daddy Mun girma hadda yara bazamu so ganin haka Yana faruwa a tsakaninka da mummy ba,,munsani daddy kaima ka Sani,,baku taba yin fada da mummy Sai a Kan maganar zuwa ruga lokaci gudu kaika Kadena zuwa daganan bamu sake ganin bacin ranku ba Sai yanzu da mashkur Yaja..
Kallan yaya daddy yayi yace meya dawo dakai kasar nan yanzu,,bakinsa Na rawa yace daddy Wani aiki nazo Yi,,Ke Kuma fa daddy yafada Yana nuna lateefah da cikinta ya duru ruwa harta fara karkarwa..
Ba tambayanki nayi ba,,Ina Kika Baro mijinki?
Nina kirata,,Shima Sadiq Nina kirashi tinda kai bazaka Sashi ya dawo gidaba su zasu Sashi yadawo,,to ai shikenan Idan ya dawo saiki jiqashi ki yanshe Ko,,be jira amsar mummy ba ya fita a falon..
Hira suka cigaba dayi ita Dai mummy jinsu kawai take tana Kalle kalle tare da.neman ta hanyar da mashkur Ze shigo,,Har akafara Kiran Sallar magrib Basu qaraso ba haka Dai kowanne su ya daura alwala sukayi sallah,,Suna cigaba da Zaman jiransa...
Tinda nijlah Taji warin Mai zuciyanta yafara Tashi nan ta fara toshe hanci tana kallan mashkur,,a hankali yake Mata Magana Yana Kallan yadda idanunta sukayi zuru zuru,,
Menene Naga kina toshe baki da hanci,,
Banasan warin Mai ka saukeni cikina juyawa yake tafada tana yinqurin Amai,,kafin motan ta tsaya tafara Kwara Amai a jikin mashkur Har Saida ta Bata gaban rigarsa,,be damu da Hakan ba Saima shafa bayanta ya riqayi Yana Mata sannu,,Seda ta gama me motan ya Basu ruwa a jarka suka wanke jikinsu,,nan suka cigaba da tafiya hancinta a toshe ,,karfe 7 Na dare Suka sauka a cikin garin Kano,,me napep ya tare suka Shiga nan yayi masa kwantancen gidansu kasancewar mashkur be taba Hawa nape ba,,dariya me nape yayi Yana cewa Malam haka kai bakone,,mu ba address Ake bamu ba,unguwa kawai Zaka fada Idan mukaje saika nuna gidanka,,ok kawia mashkur yace yacigaba da jera nijlah sannu,,tinda suka Hau napep bacci ya dauketa Har suka kai gidansu mashkur Bata Sani ba.
Bayan ya sallami me napep ya tsaya tinanin ta yadda zefara tashinta Sai kawai ya dauketa ya kwankwasa get..
Waye ne Ze balle mana kofa qara bugawa mashkur yayi Yana cewa nine baba zoka Bude..
DA gudu baba me Gadi ya Bude kofan Yana yiwa mashkur sannu da zuwa..
Ahankali mashkur yace,,baba ga kayana Dan Allah ka temaka ashigomin dasu,,to ranka ya Dade,,nan baba yafara rufe qofan,,qaran qofa yasa nijlah Bude Ido tana Kalle kalle..
Ahankali mashkur ya safketa Yana jera Mata sannu,,Ina kayana nijlah tafada cike da sanyin kuka.
Kingansu can Karki faramin halin naki,,dasauri ta dauko kullin dankwalinta ta Dora akai tana Kalle kallen gidan..
Hannunta ya kama Yana cewa 'yar kauye Sai Wani Kalle kalle kike,,lah kado kaga wannan abun da Ake nunawa,,lah kado Kalli kaza haka nijlah ta riqa fada Har suka isa qofan falon..
Da sallama mashkur ya Shiga zuciyarsa na harbawa tare da matsanancin faduwar gaba..
Mummy dake zaune tasa abinci agaba Taji sallamar mashkur,,dasauri ta dago ido Aiko tayi sa'a idanta be safka Kan Na mashkur ba saiya sauka Akan santaleliyar surukarta..
Zabura tayi ta Tashi tana nuna nijlah da yatsa bakinta yakasa magana...
Aunty lateefah ce tayi qoqarin Bude baki tace mashkur Kaine haka,,ita Kuma wannan Daga ina,,Ina Zaka kaita..
Mashkur be Iya Magana ba illah zuba musu shanyenyun idanunsa dayayi Yana cigaba da tafiya,,,har Saida yakai jikin kujera Ze zauna hannunsa riqe Dana nijlah yaji muryar mummy tana Magana..
Karka fara Zama min Kan kujera ka Kuma ficemin da wannan aljanar yarinyar"waima a gidan ubanwa ka samota Sai kuma tasa kuka tana cewa.
Kunga irin jajibe jajiben nasa,,ya kamomin wannan qazantar Har gida...
Mashkur wacece wannan Daga ina ka daukota??
Kafin mashkur yayi Magana yaji tsincin muryar nijlah..
Sunana nijlah kawu Daga garin kankan ya daukoni Kuma ni matarsace Ko kado?????????????????????
*Kuyi hakuri wayana ya Samu matsala ba lallai ku qara Jina a 'yan kwanakinan ba,,sedai kuyi fatan Allah yasa ta gyaru da wuri,,Nima ba haka naso ba,,zanyi missig zafafan comments dinkuđđđ*
*Comments & share*
*momn sultan ce*✍✍✍
đđ *'YAR SADAKA..*đđ
*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*DALA.....*
1⃣7⃣&1⃣8⃣
Kallan kallo aka riqayi a falon yayin da mummy ta riqajin Dakin Yana juya mata,,sedai Wani bangare na zuciyanta Yana gayamata Karya yarinyar take,,kallan mashkur nijlah tayi tana murmushi tace..
Dan birni kayi Shiru Baka Basu amsa ba,, mashkur be Iya kallan inda nijlah take ba yacigaba da qoqarin Zama Kan kujera..binshi nijlah tayi tana kallan mummy dake binta da Wani irin kallo Wanda batasan kona menene ba.
Marin da aunty ladeefah tayiwa mashkur ne ya dawo dashi Daga duniyar suman tsaye dayayi..
Dan iyayenka ba tambayanka akeba,,Yaya kaduba yadda ya maida mu mahaukata,,
Kinga lateefah abi komai a hankali shida kanshi zeyi bayani cewan yayan Yana mamakin abinda mashkur ya aikata duk da yasan halin mahaifiyar tasu..
Mummy Bata Iya Magana ba Dan a yadda take Bata Jin abinda suke fada kallansu kawai take sabida gaba daya komai nata ya tsaya ya Dena aiki...
Kallan aunty lateefah mashkur yayi kafin ya safke kansa kasa nan take idanunsa ya kada yayi jajur ga Wani tuquqin bakin ciki daya tokare masa zuciya,,kasa hadiye yawu yayi Yana Kallan kafet..
Lah lah lah,,Amma dai kado anyi mugu,,Babu abinda mijina yamiki Zaki mareshi,,aradu Kaci sa'a kai babbane Dana sheqeka da Sanda,,ka zube anan..
Ke Dan ubanki bamasan hauka kai mashkur ka Bude baki kayimana magana,,a Ina ka samo wannan aljanar yarinyar??
Dakyar mashkur ya Iya tsayar da nutsuwarsa ya dago kanshi dake saramasa Yana kallan yaya,,kafin ya Bude bakinsa Wanda zuwa yanzu yayi masa nauyi yace,,
Dan Allah Yaya kubani lokaci saina yi bayani Amma Daga zuwana kun tsareni da tambayoyi..
Au Allah lallai yaran nan ka samu sake yaya kake Gaya haka,,mummy kingani Duk soyayyar da Kika nuna masa ce tajamana haka,,gashi muna magana Yana mayar mana sabida be daukemu da qima ba,,aunty lateefah ta qare maganan tana huci,,mummy ko Ido ta zuba musu,,zuwa yanzu tana fatan maganan nijlah ya Zama karya Kai inda halima ace nijlah ba cikakkiyar me hankali bace..
Aunty kiyi hakuri niba haka nake nufi ba,,da hakane bazan tabajin magananku a daidai lokacin da kuka buqaci na dawo gida ba,,
Karyar banza cewar aunty lateefah tana nuna nijlah,,wacece wannan?
Hade fuska mashkur yayi,,Zan gayamusu yanzu nagaji da yawa saina huta,,mummy kinajin abinda yake fada kinyi shiru??
Mummy bata iya motsawaba Saida lateefah tayi saurin girgiza ta kafin ta safke nannauyan ajiyar zuciya tana kallan mashkur Daya kafeta da Ido Yana mamakin halinda mummy ta shiga..
Dasauri yayi gurinta Yana cewa,,lafiya sweet mom,,waya tabamana ke"" dasauri ta daga masa hannu alamun karya qaraso inda take,,chak ya tsaya tare da hadiye yawun Daya taru a bakinta,,tinda yake mummy bata taba yimasa irin wannan karbar ba to kodai shima ya shafo abinda take kyama tattare da Fulani,,yayiwa kanshi wannan tambayan..
Bakin mummy na rawa tace,,auta wacece wannan?
Shiru mashkur yayi Yana tinanin amsar dazeba mummy sai ya maida kallansa ga nijlah yanasan yimata magana da ido,,aiko nijlah ta washe Baki tana tinanin amsa mashkur yakesan tabada..
Tace ehhh,,a kankan ya dauko ni kuma Malam ya daura mana" tsawa mashkur ya Daka Mata Yana hararanta tini nijlah ta rufe Baki tana karkarwa tare da komawa bayan aunty lateefah tana boyewa,, da mugun gudu lateefah ta dawo bayan yaya tare da Dora hannu aka..
Dan ubanka kabani amsa kafin yanzu na Saba ma,,yaushe kazama haka mashkur ni nake ma tambaya kana kallona,,,to kodai na chanza ma,, dasauri yace ah ah mummy dama dama.
Dama me,, gaskiya zaka gayamin ko angayama idan zakayi taimako saika kawomin irin jaraba har gidana,,Bama ta tsaya iya get ba shine saida Ka kawomin ita har cikin falona..
Zuciyarsa na dokawa yace mummy kiyi hakuri tare zamu zata zauna da ita"
A ina?mummy ta tambaya..
Batare da fargaba ba mashkur yace anan gidan,,sedai Ka zauna da ita Amma badai mummy ba" shima baze zauna da wannan annobar ba mummy taba lateefah amsa..
Kai Dan birni me suke fada,,Allah dai yasa badani suke ba,,cewan nijlah tana kallan mummy sai kuma ta sunkuya tace sannu ina yini..
Ke tashi anan kafin kimin barbaren kudin cizo Naga alama a wannan jikin naki babu abinda bazaa samu,,Kai mashkur Ka fitamin da ita a falo Ka kuma dawo kayimin bayanin inda Ka daukota..
Mummy marainice shiyasa na kawota ta riqa tayaki aiki,,mummy yarinyar bata da matsala Dan Allah karkice ah ah yafada Yana hada hannu alamun roqo.
A tare mummy da lateefah har ma da yaya suka sa salati suna tafa hannu" lateefah ce tace cewa akayi mummy na buwatar 'yan aiki,,to koma ina buqata saina rasa Wanda Zan dauka sai wannan..
Duk da yarinta da shirme irin na nijlah saida tagane kyamarta suke gashi taji Dan birni Yana maganar aiki zata tayasu,,to wai me suke nufi?
Wanne irin kallo suke min nijlah ta tambayeni kanta,bata dawo daga tinanin ba taji mashkur Yana cewa..
Mummy Dan Allah kiyi hakuri ki tayani riqe amanar da Allah ya doramin,,yarinyarnan marainiyace bata da gata shiyasa na kawomiki ita,,
Karya kake mashkur Idan Zaka fadi gaskiya ka fada ayita ta qare..
Haba Aunty lateefah,,ki tausayamata..
Ya mashkur kodai Suma Suna bakin cikin aurena,,Naga alama Suma irin kakane" Kuma ita wannan qatuwar wacece,,sukaji nijlah Na tambaya???
Ke kimin Shiru Nace dame kikeso Naji,,to wallahi naqara Jin maganarki Saina zaneki anan" turo baki nijlah tayi tana dire diren qafa,,a hankali mashkur yace menene Kuma,,Nina gaji Zama zanyi,,Kuma Dai ka Tina Allah Yana kallanka,,Kuma a wuta yakesa me Karya haka malaminmu ya Gaya a islamiyya,,gwara kawai kace matarkace Ni Kamar yadda ka Gaya Bello..
Gaba daya jikin mashkur yayi sanyi Dan haka ya zauna Kan kafet Yana Kallan mummy...
Mummy kiyi hakuri Nima ba haka naso ba,, mummy ki dauka kaddarace tasa nayi, Sai ya kasa qarasawa..
Qaddara tasa kayi me auta,,ka gayamin Ko hankalina Ze kwanta..
Mummy auren nijlah nayi a,,kafin ya qarasa magana mummy tasa kuka tana cewa..
Shinkenan ka cuci rayuwata ka nuna Kaine da kanka,me kakeso mu Gaya iyayen Yasmeen,,yanzu wannan abun Abar aure ce,,kadubeta kama an daurawa muciya zani..
Kallan jikin nijlah ya riqayi Shima Yana hawaye,,Dan Allah mummy kidena wannan kuka wallahi kukanki masifa ne a gareni da rayuwata mummy na tuba yafada Yana kama qafanta..
Saida mummy tayi kuka me isarta kafin tace ina Baka umarni Daka mayar da yarinyarnan inda Ka daukota kafin..
Mummy kiyi hakuri nijlah amanace agareni nayi alqawarin Zan riqeta duk rintsi,,bazan taba rabuwa da itaba..
Zaro Ido mummy tayi tana kallansu kafin tace a ina zaka zauna da ita?
Mummy Dan Allah ko dakin Baki Kona 'yan aiki ki kaita nasan zata zauna" Kai wallahi ko a dakin Karen gidannan bazan ajiye wannan irin jarabar ba,,gwara tin muna arziqi Ka fita da ita..
Kafin yayi magana aunty lateefah tafara Jan nijlah da niyyar kaita waje,,cikin ihu mummy tace ke lateefah Baki da hankali zaki tana jikin wannan nida Zan iya da tinanin na kaita lahira hannunane bazan iya Sawa a jikinta ba,,Amma zanyi maganinta idan har be fita da ita a gidan nan ba..
Cikin kuka nijlah ta Koma Bayan mashkur tana riqe rigarsa tace,,Dan Allah ka fita Dani zasu kasheni,,Bata sona..
Kiyi hakuri nijlah komai zeyi daidai kinji,,mummy.
Karka qara Kiran sunana saika fara fita da wannan annobar,, mummy Bazan iyaba haqqinta Yana kaina.kiji tausayinmu.
Kaima kasan Bazan taba Zama da ita a gida daya ba Dan haka ka zabamata inda ya dace Kuma a yanzu nakeso ka saketa saki uku.
Mummy kiyi hakuri tinda bazaki Bata gurin Zama ba nizan zauna da ita a dakina,,batin saki Kuma kiyi hakuri Baz...
Lafiyayyun Mari Har guda uku Yaya ya safkewa mashkur Yana nunashi da yatsa,,kayi kadan ka wulaqanta mana uwa,,wallahi sedai kabar gidannan..
Beyi Magana ba ya kama hannun nijlah dake kuka tana Kiran Sunan kaka ya Shiga dakinsa da ita,,a qasa nijlah ta zube tana birgima tana ihu,,shiko bakin gado ya zauna ya dafe kansa Yana Jin Wani irin faduwar gaba..
Cikin kuka lateefah tace,yanzu haka zamu zuba ido mashkur yayi yadda yakeso,, ba Wanda yabata amsa..
Nan mummy ta dauka waya ta Kira daddy tana kuka,tace Alhaji ka dawo gida yanzu,,tana gama fada ta katse Kiran Bata jira amsar Shiba..
Wani layin ta Kira ta miqa lateefah wayar..
Yasmeen dake kwance Kan cinyar mama tana game a waya taga Kiran mummy,,kallan mama tayi jikin Jin Kunya tace,,mama mummyn mashkur ce.
Ki Daga mana cewan mama tana kasa kunne,,Yasmeen Na dauka lateefah tace ..
Sunana lateefah yayar mashkur,,mummy nasan ganinki yanzu....
Wash,, typing da wahala,,mu hadu a page na gaba..
Karku manta da share.
*Momn sultan ce*✍✍✍
đđ *'YAR SADAKA..*đđ
*STORY & WRITING BY...*
*BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO.....*
*MMN AMATULLAH*
*SPECIAL GIFT TO...*
*MOMN ANSAR*
1⃣9⃣&2⃣0⃣
Mummy kuma,,ke Yasmeen dama kina waya da mahaifiyar yaran nan" gizgiza Kai Yasmeen tayi tana kallan mama data kafeta da ido,,amsa zaki Bani,kinfi kowa Sanin bagane wannan yaran naki nake ba..
Cikin yauqi da yanga Yasmeen tace,,Allah mama bamu waya da ita"
Ok!saiki gayamin ta ina mahaifiyar sa ta dauka number ki??
Mama sau dayane mashkur ya kirani da layinta shine nayi saving,,cike da rashin gamsuwa mama tace,,idan bakwa waya da ita yaya za'ayi ta kiraki???
Mama ba ita bane yayanshine,,sunanta aunty lateefah sedai da wayan mummyn ta Kira kuma tace wai mummy nasan ganina..
Mezaki Mata???
Eyyah mama Nima bansani ba,, Yasmeen ta fada tana turo Baki..
To babu inda zakije"wannan ai shirmene ki dauki qafa kije har gidansu saurayi kina magana da mahaifiyar sa,,mama Allah bantaba zuwa ba sedai jikina Yana Bani kamar akwai matsala..
Wanne irin matsala kinga Yasmeen kidena kawo tinani marasa kyau a cikin zuciyanki...
Mama ba haka bane,,wallahi tin jiya gabana yake faduwa ki abinci ban iya Ciba,,gashi sai Kiran mashkur nake wayanshi kashe,,kuma Shi be Kira ba,,gashi yanzu aunty lateefah ta Kira mummy na nemana,,kinga ko da wani abu.
Babu komai Insha Allahu,,karyar da murya Yasmeen tayi tana hawaye tace,,mama Dan Allah kibani dama naje wallahi bazan zauna ba..
Hmmm Yasmeen ina jiyemiki Abu Amma ke Baki gani,,akullum ina gayamiki ki rage wannan soyayyar da kikewa mashkur,,namiji fa mijin mace hudu ne..
Bata fuska Yasmeen tayi tana kallan gefe tace,,,mama kullum gadanki Baya wuci Kan mashkur,,ba aibu bane Danna nuna kulawa da tsananin soyayya gareshi,,mama mashkur Yana Sona har inaga kama Sanda yakemin ya zarta nawa"" duk da haka ki rage nidai ina gayamiki..
To mama Dan Allah naje???
Ajiyar zuciya mama ta safke tana kallan yadda Yasmeen ta narke Mata kama ance wani Abu ya Samu mashkur tace,, shikenan kije Amma sainayi waya dashi mashkur din naji daga bakinsa yakuma hadani da maman nashi..
Mama kenan,,haba mama na saikace Baki yadda da tarbiyyana ba,,mama kinsani mashkur Baya gari kuma wallahi number mamansane barima nakira saikiji da bakinki..
Number mummy Yasmeen ta Kira sedai wayan akashe Dan haka mama tace babu inda zata fita,,kuka Yasmeen tasa tana Jin wani irin yanayi a dukkan jikinta,,jitake kama qirjinta ze fashe zuciyarta ta fito gaba daya Kota huta da abinda takeji,,koya ta motsa Kota Tina sunan mashkur sai taji kama andora Mata dutse aka,,duk yadda taso hakura takasa haka tasa mama agaba tana kuka..
Yasmeen meyasa kikesan dagamin hankali,,ba Duka ba zagi amma kinsani gaba kina kuka saikace qaramar yarinya..
Mama kibari naje ko hankalina ze kwanta,,wallahi mama akwai matsala,,bantabajin irin wannan yanayin ba sai jiya zuwa yanzu,,Insha Allahu bazan wuci 1 hour ba Zan dawo..
Shikenan Yasmeen tinda haka kikeso saikije daki sani gaba kina wannan kukan ko kunya baji..
Share hawaye Yasmeen tayi tana murmushi tace,, nagode mama..
Mama bata iya bata amsa ba Sai binta da kallo tayi tana mamakin yadda Yasmeen ke nuna damuwanta agaban kowa..
Dago jajayen idanunsa yayi ya zubamata ido Yana kallan yadda take kuka tana Kiran kaka,,wani irin juyawa kanshi yake sabida halin dayake ciki ga kuka dake taba masa zuciya,,ahankali ya riqa Kiran sunanta..
Nijlah. nijlah. Nijlah..
Bata amsaba Saima qarawa kukanta sauti tayi,, ya rasa yadda zeyi da ita,,nan ya miqa hannu Yana Magana da shaqanqiyar murya,,zomana amaryar mashkur,,maqale kafata nijlah tayi ta kuma juya masa baya tana turo baki,,duk da haka ranshi be baci ba ya cigaba da kiranta Yana rarrashinta,,amma duk da haka bata iya shiru da bakinta..
Shiru yayi yana kallanta tare da tinanin ta inda zefara rarrashinta.
Ahankali ya tashi Yana tafiya isa inda take kwance,,kafin ya qarasa nijlah tafara birgima tana juyi a qasa..
Haushine ya kamashi Dan haka ya daka Mata tsawa Wanda tasa hantar cikin nijlah kadawa nan take jikinta yafara karkarwa ta fada jikinsa tana safke ajiyar zuciya..
Rungumeta yayi a karo Na farko Yana shafa bayanta"kukan ya isa haka,,ko kinajin yinwa,,daga masa kai tayi tana qara shigewa jikinsa..
Labensa na qasa ya cije Yana tinanin yadda ze bullowa labarin,,sedai yayi alqawarin baze taba rabuwa da nijlah ba,sabida nijlah amanar Allah ce agurinshi...
Ahankali ya Tashi da ita a jikinshi ya zauna gafen bed Yana qaremata kallo,,qara shigemasa tayi sabida karkarwa da jikinta ya dauka..
Kinaso nazaneki,,saurin girgiza masa kai tayi,,bakinta na rawa tace Dan Allah kayi hakuri..
Zan hakura amma saikin dena wannan birgiman da kike,,koni bakiga halin da nake ciki ba???
Shiru tayi,shiko ya cigaba da Magana,, nijlah indai baso kike zuciyana ta buga ba,toki dena irin wannan kukan Kina birgima a qasa saikace yarinya,,dagowa tayi tana kallansa shiko ya dage Mata gira,,wai ko bakisan kin girmaba??.
Nan ma shiru tayi saida taji ya janye jikinsa anata yana qoqarin Tashi tace..
Kado yinwa nakeji"
Kobata fada ba yasan dole zataji yinwa duba da rabanta da abinci nan yayi murmushi yace jeki falo ki gaya mummy..
Bakinta na karkarwa tace,,Nina qoshi"
Yana niyyan Magana yaji ana buga kofan dakin,,beyi Magana ba yayi shiru Yana sauraran bugun..
Mashkur wai bakajina ina tsaye tin dazu baka bude ba" menene ya fada a hankali" mashkur ni kake tambaya menene??
Cike da qosawa yace,,haba aunty lateefah,,wai me kike nema dani,,Nabar Miki falo nan ma saikin biyoni..
Toka fito mummy na kiranka..
Ina zuwa yabata amsa a ciki,, juyawa aunty lateefah tayi tana tafiya tana tinanin abinda ya chanza mashkur yaran da ko Magana bata dameshiba..
Mummy yace Yana zuwa..
Tinda Yasmeen ta hau titi take gudu kama zata Tashi sama,,ba ita ta rahe gudun motan ba har saida ta shigo layin gidansu mashkur,,Yana zuwa tayi horn get man ya bude mata,,bata iya daidaita parking ba ta fito tana sauri zuciyanta da halbawa da sauri da sauri harta isa kofan falon,,a bude yake Dan haka tayi sallama tana jiran a amsa Mata"
Yaya ne ya iya amsawa Yana kallan kofan,,a hankali Yasmeen ta shiga falon kanta a qasa tana mejin kunya..
Qasan kafet ta zauna tace ina yini,,lafiya qalau suka amsa kafin mummy tace..
Ke lateefah jekice yazo yanzu kafin ranshi ya baci,,kafin lateefah ta Tashi mashkur ya qaraso falon,,nan idansa ya safka kan Na Yasmeen Wanda tayi mamakin ganinsa adaidai wannan lokacin..
Murmushi yamata tare da kashe Mata ido,,duk da yadda zuciyarta ke halbawa saida ta mayar masa na martani,,bakinta a bude a hankali tace lvu..
Kusa da mummy ya zauna Yana niyyan kwantar da kansa jikinta tayi saurin tureshi tana hararanshi,,karka soma wallahi,,shiru yayi yace,,ke kuma daga ina mashkur ya tambaya Yana kallan Yasmeen..
Kafin Yasmeen tayi Magana mummy tace,,Nina sa akiramin ita,,inaga zata fini sanin gaskiyar Magana akan wancan aljanar yarinyar..
Dasauri Yasmeen ta daga kai tana satar kallan mummy,,gabanta Na cigaba da faduwa tace,,
Mashkur wacce yarinya ake Magana,,Dan Allah kada ka hada soyayyana da wata ta qare maganar hawaye cike a idanta..
Daddy dake shigowa ya bisu da kallo Yana mamakin abinda yasa gidan nasa ya zama haka kama anyi mutuwa,,kusa sa mummy ya zauna Yana kallan mashkur,,kai kuma saukar yaushe,,kafin mashkur yayi Magana daddy ya qara wata tambayan?
Hajiya bakuwa kukayi,,eh kawai mummy tace tana hararan mashkur, ka tambayi danka shize gayamaka ko wacece..
Qara yin qasa dakai Yasmeen tayi tana goge hawaye Dan ko Magana bazata iya ba..
Mashkur wacece wannan ya fada Yana nuna yasmeen..
Bakinsa Na rawa yace Yasmeen ce,,budurwata,,budurwarka,,wani abune ya faru Naga tana kuka,,shiru sukayi aka rasa Wanda ze yiwa daddy bayani..
Ganin haka yasa daddy kallan Yasmeen ya Kira sunanta.
Bata iya amsawaba daddy yace Tashi kije gida nizan zo muyi magana da abbanku..
Da gudu Yasmeen ta fita tana kuka..
Tana fita daddy yahau mummy da fada,,haba hajiya akan me Kina kallo yaro ze kawo yarinya har gida bazaki tsawatarba,,Nina rasa meyasa kike daurewa yarannan gindi yake abinda yaga dama..
Daddy kayi hakuri Nima bansan da zuwan Yasmeen ba anan na ganta"kai mashkur har kanada bakin Magana,,daddy aure fa yarannan yayi ga matar can ya sata adaki cewan lateefah tana huci...
Sake da baki daddy yace aure kuma,,aure wanne iri" saika tambayi danka cewar mummy..
Kai mashkur dagaskene abinda suke fada??
Bakin mashkur Na rawa yace" kayi hakuri daddy haka Allah ya qaddaramin badaga ni....
Kayimin shiru mutumin banza saida kasani tambayama aure sannan zakayimin shegan taka,,bada niyya nayi wannan auren ba,,kuma banyi Danna tozar taku ba,,daddy ka fahimceni..
Amma ko kayi wauta mashkur,mena rageka dashi,,koka taba kawomin abu kanaso na hanaka,,cike da nadama mashkur ya girgiza kai..
To meyasa kayimin haka,,da wanne ido Zan kalli iyayen wannan yarinyar?
Shiru mashkur yayi Yana matsar ido nan ran daddy ya baci yayi kanshi da duka,,dasauri mummy ta tare tana girgiza masa kai,,kayi hakuri Alhaji,,ba laifinsa bane,,laifin mugayen mutanan ne dasuka daura masa auren ba saninmu..
Ran daddy a mugun bace yace,,idan su Basu sa hankali shibashi Shi,,ko zaman kansa yake,,daddy kayi hakuri wallahi ban na bata ranku nayi wannan auren ba,kada kuyi fishi dani..
Zama daddy yayi Yana kallan mashkur,,nan mashkur ya safke kashi qasa Yana sauraran daddy..
Mashkur ya akayi tayi wannan auren??
Ahankali mashkur ya bude baki Yana Magana,,daddy bantaba tinanin zanyi wani abu batare da saninkuba,,sedai Hakan yafaru bisa kaddara kuma wallahi bani na nema auren yarinyar ba,,sadaka aka bani..
What what Alhaji kanaji fa wai *yar sadaka* anyako Basu zautarmin da yaro ba?
Wallahi mummy karki yadda saiya saketa ta koma Inda ta fito,,tsawa daddy ya daka lateefah Hakan yasa tayi shiru tana muzurai,,Yaya ko kasa Magana yayi Yana nazari...
Mashkur ka tabbata maganar daka fada gaskiya ne,,eh daddy..
Idan har ka sake Na tambaya naji ba haka ba saina sabama,, dasauri mashkur yace eh Na yadda..
Shikenan yanzu ina yarinyar take,,daddy tana daki,,jeka kawomin ita..
Kambu,,ai wallahi bazata taba sabuwa ba,,wai Alhaji me kake nufi shikenan auren ya dauru"
Kiyi hakuri haka Allah ya qaddara maganar lateefah kuma ba abin damuwa bane,,nizan yiwa iyayenta Magana Sai suma suyi hakuri adaura auren kinga yanzu 2 month ya rage ayi biki..
To ai shikenan amma ku sani daga kai har Dan naka,,wallahi sedai yazabi daya ko nijlah ko Yasmeen..
Mashkur dake zuwa falon nijlah Na biye dashi yaji abinda mummy ke fada nan yaji wani irin tashin hankali,,be iya jiran nijlah ba ya qarasa da sauri ya zube gaban mummy..
Mummy Dan Allah karkice zaki rabani da Yasmeen mummy badan bana santa nayi auren nan ba,,daddy kayi Magana"turesa mummy tayi tana daga murya tace..
Nasan bakinku daya to wallahi bazan taba karbar wannan auren ba,,ka rasa Wanda zaka auro Sai yar matsiyata kuma yar fulani..
Ran daddy bace Shima yace,,amma ko kinji kunya,,kuma ina nan ina jiran yadda zakiyi damu nida Dan nawa,, mashkur ka dauki matarka kuje,,ni Zan baka gida azauna..
Tsiru nijlah tayi tana binsu da ido taji daddy yace,,nace ka kawomin matar taka naji shiru..
Kafin mashkur yayi Magana nijlah ta washe baki tace baba gani' kallan Nijlah daddy yayi kafin ya maida kallansa ga mashkur.......
0 comments:
Post a Comment