Hajiya tace, "Hope you are well?"
"Alhamdulillah." Ta amsa ta tana kallon ta
Zabba'u tace, "Weldon you slept. Today is a holiday."
Murmushi tayi mata
"Go to Breakfast there and lie down." According to Hajiya
Hakan yasa ta tashi ta wuce kan dainning ɗin
Ummee da ke aiki a computer ta ɗago tana kallon Hajiya tace, "Hajiya zamu fita da MEEMA zuwa kasuwa, kiyi mata magana sai mu je tayi shopping abun da take so, and Ina so in je gidan Hajja Salma sai mu je tare su gaisa, dama tayi min complain bata san ta ba."
"To ke meyasa baza ki faɗa mata ba sai Ni? Ki sanar mata idan zata bi ki sai ku je."
Ummee tace, "ok." Sannan ta ci gaba da aikin ta.
Bayan MEEMA ta gama Breakfast ɗin ne ta dawo parlour'n ta zauna
Ummee looked at her and said, "We are going to go shopping. If there is anything you need, we will go and buy it."
"No I don't need anything." Tafaɗa ba tare da ta kalli Ummeen ba
"Why do you say that? I know you need MEEMA, you will follow me to go because I want to go to my friend's house and greeting".
Shiru MEEMAN tayi bata ce komi ba
Hakan yasa Ummee tayi tunanin ko ta amince ne, sai ta ci gaba da aikin gaban ta
Hajiya tana ji bata tanka ba hiran su suke yi ita da Zabba'u
While MEEMA tana latsa wayan ta
Can Ummee bayan ta gama abin da take yi ta tashi tana kallon MEEMAN tace, "Go get ready and we'll go out."
"I will not go anywhere." Tafaɗa a wannan lokacin tana kallon ta
Shiru Ummeen tayi kamar zata yi magana kuma sai ta juya ta haye sama
Hajiya kallon MEEMAN tayi tace, "Why are you like that?"
Da ido ta bi ta ba tare da ta fahimce ta ba
"Don't do that to your mother. She's your mother. You shouldn't argue with her. Get up and follow her."
Girgiza kanta ta soma yi har hawaye sun cika mata ido. "No, I'm not going. I'm not happy if I follow her." Tafaɗa tana miƙe wa ta wuce ɗaki da sauri
Da kallo suka bi ta har ta ƙule
Zabba'u tace, "wai Ni Hajiya mene ne ya haɗa su ne take yiwa Hajiya ƙarama haka? Kawai fitan da zasu yi ne tare shi ne take cewa baza ta je ba hakan be dace ba."
"To ai duk yanda kika gani da laifin Zulaiha. Sannan kinga rayuwar su da na nan ba ɗaya bane. Dole sai kin taimaka min wajen mun fahimtar da ita muhimmancin uwa, yanzu tana kallon mahaifiyar ta ce a maƙiyiyar ta kuma kin san hakan be dace ba tunda uwa uwa ce. Ni kaina ba na so ta ci gaba da nuna wa mahaifiyar ta tsana."
"To Allah ya kyauta Hajiya, ai a sannu zata saba komi zai wuce tunda yanzu suna tare a gida ɗaya". Cewar Zabba'un tana tashi tsaye zata wuce kichen. Sai kuma suka ji Nocking hakan yasa ta wuce bakin ƙofan ta buɗe. Zaro ido tayi tana kallon Matar da ke tsaye riƙe da hannun ƙaramin yaro da bazai gaza shekaru bakwai ba. Washe baki tayi tana kiran sunan ta. Sai kuma ta juya tana cewa, "Hajiya Jalila ce ita da Habeeb."
Jalila murmushi tayi ta shigo tana cewa, "ina Hajiyar tawa? Yau na kawo miki Mijin ki."
Dariya Hajiya tayi da cewa, "maraba lale yau dai muna da babban baƙi kenan?"
"Ai ba mu kaɗai bane har da Abban shi." Inji Jalilan tana zama
Kafin ma suyi magana sai ga shi ya shigo
Hajiya bata san sanda tayi yunƙurin tashi daga kujeran da take zaune ba. Sai dai kasancewar ta kasa dole ta zauna tana bin ɗan nata da kallo
Shi kuma da sauri ya iso yana kiran sunan ta. Ai rungume ta yayi tsaban murna sai ga hawaye
Itama haka hawayen ta fara bakin ta na rawa tace, "Hashimu ashe zan sake ganin ka? Kai ne dai ka dawo?"
Ɗago kansa yayi yana murmushi da hawaye a tare yace, "Hajiya Allah yayi mun dawo. Yau dai gani ga Hajiyata." Sai ya sake rungume ta
Zabba'u kuwa baki har kunne, ai sai ta ruga zuwa sama don sanar wa da Ummee. A tare suka dawo Ummee kamar zata kifa tsaban sauri
Shi kuma yana ganin ta sai ya tashi ya nufe ta yana faɗin, "Aunty."
Hannayen sa ta riƙe cike da tsantsan farin ciki tace, "na kasa yarda da aka ce min kai ne ashe dai kai ɗin ne? Gaba ɗaya ka manta damu?"
"Haba Aunty Kar ki CE haka, kin san aiki. Inda muka je gaba ɗaya babu network muna daji, jiya na sauka muka taho yau." Yafaɗa yana koma wa ya zauna
Itama zama tayi sannan aka sake gaisa wa
Zabba'u tuni ta cika musu gaba da drinks
Hayaniyan su ne ya fito da MEEMA dake ɗaki
Uncle Hashim shi ya fara hango ta, sai ya waro ido yana faɗin, "wa nake gani kamar MEEMA?" Sai kuma ya kira sunan ta
Hakan yasa ta dawo da idon ta kanshi. Sai kuma ta nufe shi itama tana kiran sunan shi
Cike da farin ciki ya tashi ya rungume ta yana cewa, "When did you come back here? Are you already here?"
Hajiya ce ta ba shi amsa tana faɗa mishi dalilin dawowar ta
Hannun ta ya riƙe suka koma suka zauna. Cike da tausayin ta yayi mata ta'aziyyar mahaifin ta
Kasa magana tayi saboda yanda idanuwan ta suka cika da hawaye
Yace, "Be patient my daughter. Pray for him because he is the only one who needs it. May God forgive us for his loss."
Duk suka amsa da, "Amin." Ban da MEEMAN da har yanzu ta kasa magana
Hajiya kallon Habeeb tayi da ya maƙale a jikin mahaifiyar shi tace, "kai kuma baza kazo bane mu gaisa? Ko har ka manta da Ni ne tunda dama ka rabu da zuwa gaishe Ni?"
Tashi yayi ya iso wurin ta
Ta kama shi tana shafa kanshi tace, "Miji na yau dai ga ka a gida, ga kuma Baba ya dawo ko sai murna?"
Murmushi yayi yana gyaɗa mata kai
"Ai yau tunda muka tashi da safe yake murna zai zo wajen Kaka, dayake ya tashi da zazzaɓi a jikin sa amma hakan be hana shi murna ba, zaman mota ne yasa duk yayi yaushi kafin mu zo amma da kuzarin shi muka zo don ya dame Ni har yanzu ba'a kawo ba?" Cewar Jalila tana murmushi
Dariya duk suka yi
Hajiya tace, "ayya ashe mijin nawa babu lafiya ne? Ai ko be kamata a bar shi haka ba. Zabba'u ki samo mishi magani sai a ba shi, amma kafin nan ki dama mishi ko Custard ne sai a ba shi kafin a gama girki."
"To Hajiya." Tafaɗa tana yinƙura wa ta tashi
Su kuma hira suka ɗan fara taɓa wa
While Uncle Hashim kallon MEEMA yayi suka sakar wa juna murmushi. Sai ya saka hannu ya riƙe nata hannun yana cewa, "My baby has grown, how did you grow up so much? I miss you so much."
Dariyan farin ciki ta saki wanda zai tabbatar maka da cewa tabbas tana a cikin farin ciki sosai. Dayake sun saba da shi, a lokacin da tana yarinya kusan ko yaushe yana yawan ziyartan su can Riyadh musamman domin ta, tunda dai aka ƙara mishi matsayi a wurin aiki ne ya dena zuwa amma duk da haka suna waya sosai, sai kuma tafiyan nan da yayi ya jima dole ta dena jin wayan shi, duk da bata yi tunanin ko aiki ne yasa ta dena samun shi a waya ba sai dawowar ta da Hajiya ta sanar mata. Kanta ta ɗaura a saman kafaɗan shi tace, "I miss you so much, Uncle!"
"Now I know you graduated?"
Gyaɗa masa kai tayi
"Now you are getting married. However I thought I would come back and find out you are married and I will see your children walking." Ya ƙare maganar yana kwatanta wa da hannun sa
Duk dariya suka yi har su Hajiya da suke hiran su daban
Yayinda ita kuma ta shagwaɓe fuska da cewa. "Uncle I am still a young girl."
"Really?"
Tura masa baki tayi
Murmushi yayi yana sanya hannu ya ɗan bugi goshin ta
Tace, "oshhh! Uncle it's hot."
"You still don't change my daughter."
"I also see that she is still unchanged." Cewar Jalila tana murmushi
Hajiya tace, "Now that you're back, you're going to get marry her."
"No. I'm not going to get married now. I haven't finished my studies yet. I'm just starting to work and I'll be long before I get married." Tafaɗa tana kallon shi
"Well daughter no matter what you say, what you want is what I want too." Shima yayi maganar idanun shi a kanta yana mata murmushi
Itama murmushin tayi tana sake mayar da kanta a jikin shi
Jalila tashi tayi tana cewa, "Hajiya bari in Kai kayan mu ɗaki." Ta wuce ta ja Trollyn tayi sama
A lokacin ne Zabba'u ta dawo da Custard ɗin ta gama dama mishi. Ta zauna tana cewa, "to zo ga shi na gama dama maka ka sha."
Taso wa Habeeb ɗin yayi daga jikin Hajiya ya taho wurin ta. Ita take ba shi da kanta bayan ta zaunar da shi a cinyan ta.
Da haka dai suka kasance a ranan suna tare suna ta hira. Sallah kaɗai ke tayar da su a wurin. Sai da aka gama abinci suka haɗu gaba ɗaya suka ci a saman dainning sannan suka dawo Parlour suka dasa hira.
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
"Har yanzu Allah be bamu Sa'a a kan wannan yaron ba, na rasa meyasa har yanzu yake tsallake shirin mu. Yanzu wai ya zamu yi ne?"
"Momy ba fa matsalar mu bane, kin san kwana biyun nan ba ya zama dole baza mu samu damar aiwatar da komi ba, kuma kinga yau gidan cike da jama'a duk masu taya shi murnar samun kujeran nan ne, dole mu jira har sanda komi zai yi sauƙi."
Tsaki ta ja tana tashi ta soma zagaye. Can kuma ta juyo tana kallon Abdul tace, "yanzu ina Umar Faruk ɗin?"
"Na bar shi da wasu Mutane a waje, ya ce yanzu zai shigo idan suka gama."
"To ka tashi ka je kar yazo ya tarar da mu a nan."
Tashi yayi ya fice.
Babu jima wa sai ga Umar Faruk ya shigo parlour'n da sallama
Momy saurin sauya fuskar ta tayi tana murmushi tace, "ah ah my son ƙariko mana ka zauna."
Taho wa yayi ya zauna a kujeran da ke facing ɗin nata
"Yanzu Abdul ya fita yake sanar min da daddaɗan labari. Ashe har an sanar da zaɓen ne?"
Murmushi yayi da cewa, "A'a Momy akwai saura, mu namu ba'a tabbatar ba dai. Zuwa anjima muke tunanin komi zai kammala."
"To ai dai tunda kaji haka insha Allahu kai ne da Nasara, na san yaro na bazai wuce shi ne da Nasara ba da yardan Allah. Kai na Mutane ne kamar yanda mahaifin ka shima na Mutane ne, ina da tabbacin kai ne zaka lashe zaɓen nan."
"Amin Momy." Yafaɗa cike da jin daɗi
Gyara zaman ta tayi tace, "ya maganar mu da muka yi da kai a kan neman matar aure? Kar ka manta fa yanzu kowa idon shi na kanka, kana da wannan babban matsayin amma ace baka da mata wannan be dace ba, dole ka nema wa su Hafsah mahaifiya ko su ma zasu ji daɗin uwa a halin yanzu, Nusaiba ta rigada ta tafi inda kowa zai je baza ta taɓa dawowa ba. Ba na so Mutane suna ma yaro na kallon ƙaramin mutum wanda zai gaza musu. A kullum da wannan batun nake kwana nake tashi kullum ina cikin zullumi da tunani." Ta ƙare maganar nata fuskar ta cike da damuwa
Shiru yayi kansa a ƙasa ya gaza cewa komi
"Umar ka duba magana ta komi ina yi ne domin ka, bazan so ace yau duniya tana zagin min ɗa ba, kai ɗana ne wanda nake ji kamar Ni na zuƙuna na haife ka. Mahaifiyar ka ta haife ka ne kawai amma Ni nafi kowa ƙaunar ka. Ina son ka ba na son abinda zai same ka, ba na iya barci a ɗan kwanakin nan tunda ka kama siyasan nan." Ta ƙare maganar da fashe wa da kuka
Da sauri ya ɗago yana kallon ta jin muryan kukan ta. Sai kuma ya tashi izuwa gaban ta jikin sa har rawa yake yi ya riƙo hannayen ta. "haba don Allah Momy mene ne na kuka kuma? Don Allah ki dena. Duk abun nan da kika ga ina yi; wa nake da shi da zan yi dan shi idan ba ku ba? Bani da kowa sai ku, na rasa kowa nawa amma kun zauna da ni, kin zame min mahaifiya sannan ga ɗan uwa na samu ga kuma ƙanwa duk kin maishe su nawa. Kina nuna min duk ƙaunar da uwa zata nuna wa ƴaƴan ta. Don Allah ki dena kuka na yarda zan yi aure ko domin farin cikin ki ne Momy." Sai yayi shiru saboda jin hawaye sun cika mishi ido. Daƙyar ya furta. "Zan yi auren Momy."
Murmushi tayi tana saka hannu ta riƙe nashi hannayen tace, "Allah ya maka albarka my son, Ni dama buri na inga kana farin ciki ne a rayuwa, tunda Matar ka ta mutu ka gaza yin aure wanda hakan be dace ba, kowa yana maka kallon Mutumin kirki ba na son a soma maka akasin haka tunda yanzu ka ga idanun duniya a kanka suke, kana da babban matsayi a duniya, ina son aci gaba da kallon ka a haka. Tashi ka je Allah yayi maka albarka."
Amsa mata yayi yana miƙe wa tsaye cike da sanyin jiki ya fice. Kai tsaye Part ɗin shi ya wuce ya shiga. Ɗakin yaran shi ya wuce ya duba ya ga suna barci sai ya haye sama inda ɗakin shi yake. Ya shiga ya yiwa kansa masauki a gaban gadon shi. Shiru yayi yana me kama kanshi da hannayen shi biyu. Shi Mutum ne me sanyin hali da rashin son hayaniya, shiyasa ko ya ya ne aka yi wani abu ko ya ɗan samu damuwa a ranshi yanzu sai duk ya rasa kuzarin shi, sai nan da nan kanshi ya soma ciwo har ya rasa sukunin shi, yana da matuƙar sanyin hali da tausayi sosai, abu kaɗan ke ɗaga mishi hankali shiyasa a sanda ya rasa Matar shi tashin hankalin da ya shiga ne ya haddasa mishi ciwon zuciya. Wanda har yanzu fama yake yi da kanshi kullum cikin magani. Ba ya son abubuwan da za suna tuno mishi da matar shi a koda yaushe shiyasa ya kasa ƙara aure yau kimanin shekaru shida kenan. Ta haifi Yusra da kwana ɗaya Allah ya ɗauki ranta sakamakon guban da ta ci a cikin abinci wanda su Momy suka sanya mata.
Nusaiba ta kasance ɗaliban likitanci yarinya ɗaya tilo a wurin mahaifan ta da suka kasance Malamai, a nan Kaduna suke zaune kuma ba wasu masu kuɗi bane, sai dai suna da rufin asiri sosai. Tun Umar Faruk yana karatu a ƙasar Amurka lokacin ya dawo hutu suka haɗu da ita sanda ya kai ziyara wajen wani abokin shi a makarantar su. Kamun kanta da tsantsan tarbiyyar ta yasa Umar Faruk ya faɗa soyayyar ta, domin Nusaiba ba wata kyakkyawar yarinya bace amma akwai ta da tarbiyya sosai, tun tana ƴar shekara goma tayi saukar alƙur'ani me girma. Kuma a sanda ta girma tana koyar da ɗaliban mahaifin ta a makarantar da ya buɗe. Binciken farko da Umar Faruk yayi a kanta wajen abokin shi wanda ya santa sosai. Shi ya tabbatar mishi da Malama ce ita sosai da kuma ƙoƙarin ta. Hakan yasa ya faɗa soyayyar ta kafin komawar shi ƙasar waje. Be yi ƙasa a gwiwa ba da taimakon abokin nashi ya bayyana mata soyayyar shi. Inda cikin ƙanƙanin lokaci suka gina soyayyar su me tsafta har zuwa sanda ya gama karatun shi ya dawo ya aure ta. A lokacin ya rasa iyayen shi domin tun yana yaro mahaifiyar shi ta rasu, shi kuma mahaifin shi ya auri Hajiya Salamatu wacce ita ce Momy, ta zo da yaran ta biyu gidan kuma tayi zama da mahaifin shi na shekara ɗaya kafin Allah ya ɗauki ranshi sakamakon ciwo da yayi. A lokacin Umar Faruk ya sake zama Maraya babu uwa babu uba bare ƴan uwa, sai Momy da ƴaƴan ta da suka nuna mishi ƙauna bisa son mallakar dukiyar shi da suke son yi, ya ɗauke su tamkar jinin shi be taɓa tunanin ba da zuciya ɗaya suke ƙaunar shi ba, be da wasu dangi da suka fi mishi su, duk abinda suke so yana musu kuma yana tsananin yiwa Momy biyayya tunda ya ɗauke ta kamar ita ta haife shi, yana ji a ranshi ya rasa uwa ce amma ita ce ta maye mishi gurbin ta. Sai dai shigowar Nusaiba cikin rayuwar shi sai ta fara fahimtar zagon ƙasar da suke yi mishi, wanda ta so ta fahimtar da shi ba ƙaunar shi ta Allah da Annabi Momy take yi ba amma ina bata ci galaba ba. Lokacin ta haifi Hafsah da shekara biyu ta samu cikin Yusra. Tun lokacin suke tagen yanda za ayi su kashe ta domin ba sa son tazo ta haihu ta sama mishi Magaji na miji, domin shi kanshi so suke yi su kawar da shi a doron duniya su mallaki komi da kuma dukiyar shi, basu ci Nasara ba sai da ta haihu a lokacin tana fama da rashin lafiya sakamakon haihuwar ya zo mata da tangarɗa, suka saka mata guba a cikin abinci ta ci ta mutu wanda ya ja cece kuce a tsakanin likitocin asibiti da ƴan sanda sakamakon a asibiti ta mutu, an gane cewa guba taci sai dai maganar be kai ga kunnen Umar Faruk ba suka san yanda suka yi suka siye ɗan sandan aka binne maganar.
Mutuwar Nusaiba ya taɓa Umar Faruk sosai domin Allah ya ɗaura mishi ƙaunar ta a zuciya, yana matuƙar son ta kuma yana jin ta a zuciya matuƙa. Mace ce me shiga zuciya bata da hayaniya ko kaɗan, tana da kirki da halin ƙwarai wanda idan har ka zauna da ita dole ne sai ka so ta. Mutuwar ta ya taɓa shi hakan yasa har yayi jinya sabida damuwar da ya saka a zuciya, wanda yanzu ya haifar mishi da ciwon zuciya.
Har yanzu burin su Momy su ga bayan shi amma sun kasa cin Nasara, yanzu haka suna ta shirin yanda zasu kashe shi ne ba tare da an yi zargin kisa bane domin su mallaki komi, mahaifin Umar Faruk wato Alh. Aliyu Bature ya rasu ya bar mishi ɗumbin dukiya har da gidajen mai guda uku wanda ake ji da su a nan Kaduna. Yanzu haka shi Umar Faruk ɗin ya gina babban Company na sarrafa shinkafa wanda shi ke kula da shi tare da Abdul. Sanadin shigan shi siyasa kuma mutanen mahaifin shi ne suka saka shi, tun ba ya sha'awa sai dai ya basu gudummawa domin ya san manyan mutane sosai, har dai a yanzu sun ci galaba inda kai tsaye suka nema mishi kujeran Senata kuma ga shi Allah ya ba shi.
*****
Ajiyan numfashi ya sauke yana miƙe wa tsaye tare da nufan drowan mirror ya buɗe, maganin shi ya ciro ya buɗe ya ɗauki wanda zai sha sannan ya wuce bakin Fridge, buɗe wa yayi ya ɗauki faro ya sha maganin dashi sannan ya wuce bakin gadon shi ya soma cire kayan jikin shi. Wanka ya shiga ya fito yana tsane jikin shi da towel bayan wanda ya ɗaura a ƙugun shi. Wayan shi da ta fara ƙara ya nufa ya ɗauka yana zama a gefen gadon, peacking yayi yana kara wa a kunne. Congratulations ɗin da ake masa yasa ya saki murmushin shi me kyau yana amsa wa cike da farin ciki. Koda ya gama amsa call ɗin sai wasu kuma suka ci gaba da kiran shi dole ya ɓata lokaci yana amsa calls kafin ya tashi ya shirya a cikin sauri, wani farin tissue ya saka wanda har farin Singlet ɗin da yayi using dashi ana gani. Kayan sun yi masa kyau sabida ƴan dai-dai ne iya jikin sa, sai ya murza hula baƙi ya nufi gaban mirror yayi amfani da turarukan shi wajen feshe ko ina na jikin sa da turare, nan da nan ɗakin ya sake tashi da ƙamshi sosai. Bayan ya gama jerin takalman sa ya nufa ya zari ɗaya wanda ya kasance baƙi ne ya zura ya ɗauki keey ɗin mota da wayan shi ya fito
Fitan shi sai ga motoci sun fara shigowa gidan. Sun yi kusan goma haka suke ta tururuwan shigowa, Mutane ne cike a cikin su suka firfito suka nufe shi ko wanne yana mishi congrats
Hannu yake basu fuskar sa a washe yana amsa musu
Abdul ne ya iso wajen yana son mishi magana
Dole ya ɗau excuse a wajen su ya matsa zuwa wurin shi
Nan Abdul ɗin ya sanar mishi, "Momy ce tace a sanar mishi akwai girkin da ta shirya musu shi da abokan shi zuwa bayan sallan isha'i."
Murmushi yayi cike da farin ciki ya gyaɗa mishi kai kana yace, "ok insha Allahu zamu yi ƙoƙarin zuwa, ka sanar mata zuwa ƙarfe goma zamu zo."
Abdul ɗin amsa mishi yayi ya juya ya tafi
Shi kuma ya koma cikin mutanen suka ci gaba da gaisawa. Kana kuma suka ɗunguma gaba ɗaya suka fice a motocin su, while Umar Faruk Yana a cikin nashi tare da securities ɗin shi da suka bi su a baya.
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏼
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NO_24*
*WASHE GARI*
"I want you to tell me about your country, because I also want to go abroad, especially to the Arabian Peninsula." Cewar Laɗifa tana murmushi
MEEMA wacce take latsa Laptop, ɗago Kai tayi ta kalle ta da murmushi a fuskar ta, a ranta Habibah kawai ta faɗo mata a rai. "Ok, I'll tell you, but not now. We have a lot of work to do now."
Ɓata fuska Laɗifa tayi tana miƙa tare da kwantar da kanta a saman kujeran da take zaune, sai kuma tace, "I'm very tired too, and I'm hungry so we should go and get something to eat."
Hannun ta MEEMA ta ɗago tana duban agogo sai ta mayar da idanuwan ta a a kanta tace, "It's 12:40 pm. Stay tuned."
"No now we're going. I'm tired of work." Ta sake faɗa tana miƙe wa. Sai ta saka hannu ta rufe Laptop ɗin gaban MEEMAN tana cewa, "Get up and let's go please. I'm very hungry."
Shigowar Idris yasa MEEMA tayi shiru bata ce komi ba
Shi kuma kallon su yayi, sai kuma ya kama haɓa yana mayar da idon sa kan Laɗifa yace, "ke kuma fa? Where are you going when you get up?"
"Wlh Brother na gaji yau yunwa nake ji kamar ban ci abinci ba."
Hararan ta yayi yace, "kin gan ki? Na kula ke acici ne wlh. Ok, let's get up and eat now."
Washe baki Laɗifa tayi tace, "yauwa ko kai fa Yayan mu."
MEEMA tashi tayi itama ta bi bayan su suka fice. A motan Idris ɗin suka ƙarisa restaurant da suke shiga cin abinci. Kowa yayi odan abinda zai ci suka zauna suna ci suna hira. Ƙarfin hiran duk Idris ne yana basu labari suna dariya, kasancewar sa me son Wasa da dariya shiyasa ko baka yi ninya ba sai kayi dariya idan har yana baka labari. Da suka gama suka koma wajen aiki. Sai three O'Clock suka tashi kamar ko yaushe, Idris ya ɗauki MEEMA suka wuce gida
Suna zuwa layin gidan su suka ga motoci kusan biyar a jere, sai wasu masu baƙaƙen kaya da alamu securities ne
"It looks like something is being done here." Cewar Idris yana faka motan shi daga bakin Gate ɗin su
MEEMA bata ce komi ba illa kallon wajen da take yi, sai kuma ta juyo da kallon ta gare shi tace, "And who are these people?"
"I don't know MEEMA, but I think someone came here."
"Ok." Tace tana ɗaukar jakar ta. Sai da tayi masa godiya sannan ta buɗe motan ta fice
Shi kuma ya danna horn me gadin su ya buɗe mishi ya shige
MEEMA da ƙafa ta taka zuwa bakin Gate ɗin su ta shige ciki. Tana isa bakin ƙofan parlour zata buɗe sai Uncle Hashim ya buɗe suka fito shi da Umar Faruk. Da kallo ta bi su tana ɗan matsa wa baya
While they are also watching her
"My daughter are you back?" According to Uncle Hashim he was smiling at her
Itama murmushin tayi tana gyaɗa masa kai don she could not speak
Uncle Hashim kallon Umar Faruk wanda idanun sa ke kan MEEMA yayi yace, "this is MEEMA, the Aunty's girl."
"Really?" He asked looking at him
"Yes. She is back here to stay." Sai kuma ya kalli MEEMAN yace, "My daughter this is my friend, my best friend, his name is Umar Faruk."
MEEMA kallon shi tayi ta ɗan yi murmushi kaɗan tare da cewa, "Hello Uncle."
"How far?" Yafaɗa shima yana kallon ta
"I'm fine." Sai kuma ta kalli Uncle Hashim tace, "Uncle I'll go inside."
"Ok daughter. Let me accompany him outside."
Kanta kawai ta jinjina mishi tana wuce wa ta shige ciki
Su kuma suka taka suka nufi waje. Sai da suka fita suka tsaya a bakin Gate ɗin
Umar Faruk yace, "but I know this girl, kwanaki ta zo gida na."
"Haba dai? To wa ta sani a gidan?" Uncle Hashim yafaɗa da mamaki
"Sun zo ne ita da wata, amm.. ina ga From t.v I see they come."
"Ok I understand. Tana aiki ne a gidan t.v ai, but Dude I'm wondering if I'll give it to you? Don kallon da kake mata I think kana ciki ne." Yafaɗa yana dariya
Shi kuma murmushi yayi da cewa, "kai halin ka na nan ko? Baza ka sauya ba, dama aka ce idan ka rabu da ganin mutum kar ka tambayi idan ya canza, domin halin shi na nan."
Murmushi Uncle Hashim yayi yace, "Allah da gaske nake yi, ka san daughter na ce kuma wlh kun dace sosai. Tunda naga ka ƙi sake aure tun tafiya na ga shi har yanzu kana nan a haka, na san yanzu ai Yusra ta girma sosai tunda tana shan nono muka rabu."
"She's grown up, now she's in school too."
"Allah Sarki Yusra da Hafsah, insha Allahu I will come in and see them later, zamu gaisa da Momy ai".
"Allah ya kai mu." Sai ya ba shi hannu suka gaisa suna wuce wa wurin motan. "But will you stay here for two days?"
Uncle Hashim yace, "insha Allahu. Zan yi two weeks ni gaskiya, sai dai Jalila za su koma tunda akwai school ɗin Habeeb."
Daga nan sallama suka yi ya shiga motan da ɗaya daga cikin securities ɗin ya buɗe mishi
Har sai da motocin suka tafi kafin Uncle Hashim ya shige gida. A haraban gidan ya tsaya yana amsa call, yana nan tsaye ne ya hangi wani guy yana shigo wa ciki, ganin ya dumfaro wurin shi sai ya katse kiran yana mayar da hankalin sa a kan shi, kallon sani yake mishi sai dai be ce komi ba har ya iso wurin shi, ya ba shi hannu suka gaisa kafin ya tambaye shi, "wane yake nema?"
Murmushi Sajjad yayi yana ɗan shafa kanshi kamar yanda ya saba yace, "suna na Sajjad Aliyu, ni ɗa ne wajen Kawu Faruk surukin nan gidan."
Tabbas sai a yanzu ya gane fuskar MEEMA yake gani a tare dashi, sai ya washe baki yace, "ah kace daga Yola kake? You Are welcome, let's go inside."
Sajjad bin Bayan shi yayi har cikin gidan
Sai dai babu kowa a Parlour, sai yace mishi, "ya zauna bari ya kira mutanen gidan." Ya wuce ciki. MEEMA ya fara kira sannan ya kira Ummee, ya shiga ɗakin Hajiya ya gunguro ta suka fito
Tunda MEEMA suka yi ido huɗu da Sajjad ai sai ta ja ta tsaya daga inda take ta kasa ƙarisowa
Shima haka yana ganin ta ya miƙe tsaya idanun sa ƙyam a kanta nan da nan farin ciki ya cika shi da ganin ta
Fitowar Uncle Hashim tare da Hajiya ya kalle ta yace, "let's go daughter." Sannan ya wuce
Ummee itama sai a lokacin ta fito suka zauna a kan sofa
"Ka zauna mana." Uncle Hashim yafaɗa yana kallon Sajjad ɗin
Babu musu ya zauna. Sai kuma ya fara gaishe da su
Ummee da ke mishi kallon sani tace, "kamar na so in Gane ka? Sajjad ko?"
Murmushi yayi yace, "Yes Ummee Ni ne."
"Ikon Allah kai ne a nan? Kai da wa kazo?" Tafaɗa da mamaki
"Ni kaɗai."
Murmushi tayi sai kuma ta kalli Hajiya tace, "Hajiya wannan ɗa ne wurin miji na, mahaifin shi Yayan Faruk ne ai."
"To Masha Allah, sannu da zuwa, ki ce ɗan uwan MEEMA ne ai, Ga kamanni wlh." Tafaɗa cike da fara'a
Uncle Hashim yace, "to ai ga daughtern can ta ƙi ƙariso wa." Sai ya ɗaga murya ya kira ta
Dole a yanzu ta iso wurin sai dai fuskar ta a ɗaure tamau tana kallon Sajjad ɗin
"Daughter do you recognize him? This is your cousin". Cewar Uncle Hashim Yana murmushi
"Na'am. I recognize him Uncle, But what did he come to do here? I don't want to see him."
Mamaki duk kan su suka yi da maganar ta
Musamman Ummee da ta san zai yi wuya MEEMA ta gane Sajjad, kasa shiru tayi tace, "How come you know him after you've never seen him?"
Cikin muryan kuka da ya ƙwace mata tace, "When I landed here country I went to their house and stayed. They wanted to marry me without my knowledge. One day before we were to get married I knew. That's why I came here. And I don't want him, I hate him so much."
"Subhanallah.. married again? Don't you know?" Hajiya tafaɗa da tsantsan mamaki
Itama Ummee kalman auren ta sake maimaita wa fuskar ta cike da damuwa
Sajjad da kanshi ke ƙasa ya kasa cewa uffan
Sai Uncle Hashim da ya tashi a zuciye yace, "kai tashi ka kama hanya ka bar mana gida, nan ba wajen zaman ka bane..."
Hajiya ce ta katse shi da cewa, "a'a Hashim ai baka san me ya kawo shi ba, kuma kana da tabbacin da laifin shi ne?"
"Da laifin shi mana Hajiya, ba shi ne wanda za'a ɗaura mishi aure da ita ba ba bare da amincewar ta ba? Don kawai zalunci, dama ai ba ƙaunar ta suke yi ba kuma mun san da haka, tabbas akwai abinda yasa suke son yi mata aure ba tare da amincewar ta ba, wato auren dole suka so suyi mata?" Yafaɗa a fusace
Da gudu MEEMAN ta isa wurin Uncle ɗin ta rungume shi tana kuka
Hakan ya ƙara hassala shi yana kallon Sajjad ɗin da cewa, "kai baka ji me nace maka bane? Ka tashi ka bamu wuri ka koma inda ka fito tunda baku da mutunci."
Cikin hawayen da suka kufce mishi Sajjad ɗin ya zube a kan gwiwowin shi yana roƙon su da Allah, "su bar shi a nan ya zauna, wlh yana tsananin ƙaunar MEEMA bazai iya rabuwa da ita ba..."
Katse shi yayi da cewa, "tashi nace, wlh ka bari na sake maka magana sai dai uwar ka ta haifi wani a gidan nan."
Su Hajiya sun san halin Uncle Hashim akwai zuciya ba ya son raini, dama dalilin da yasa ya shiga aikin soja kenan domin akwai shi da zuciya sosai idan ranshi ya ɓaci. Dole Hajiya ta soma rarrashin sa da cewa, "ka ga Hashimu kayi haƙuri ya fita a hankali kar kayi masa wani abun kaji ko?"
"To Hajiya uwar me yake jira da bazai fita ba?"
Duk hayaniyar Uncle Hashim ɗin ne ya fito da su Jalila da Zabba'u suka zo suka tsaitsaya suna kallon ikon Allah
Sajjad ba don ya so ba ya tashi ya fice yana sharan hawaye
Zabba'u da ita ce bakin ta ke ƙaiƙayi take bin ba'asin me ya faru. Sai da aka sanar mata sannan hankalin ta ya kwanta. Sai kuma ta koma tana faɗan albarkacin bakin ta, sai tsiya take yi tana faɗin, "ai wannan mugunta ne ace zasu yiwa yarinya aure ba da amincewar ta ba, haka ake yi ne?"..
Shi kuwa Uncle Hashim tuni ya ja hannun MEEMA zuwa ɗakin ta, a can ya rarrashe ta domin kuka take ta yi sosai ta kasa yin shiru. Sai da ya kwantar mata da hankali kafin ya fito ya yiwa su Hajiya sallama a kan, "zai je gidan abokin shi." Ya fice
Su kuma sai mayar da zacen suke yi, daga ƙarshe kuma suka koma hira.
The following day. Lokacin Hajiya na zaune a ɗaki tana lazimi Uncle Hashim ya shigo ɗakin duk a rikice. Kallon sa tayi tana tambayar sa, "lafiya Hashimu wani abun ne ya faru?"
Sai da ya zauna a kan sofa ya gaishe ta kafin yace, "wlh Hajiya babu lafiya, ina zaune a ɗaki aka kira Ni ake sanar min Umar Faruk yayi hatsari jiya da dare."
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.. a garin ya ya? Da sauƙi dai ko?" Tafaɗa itama a rikice
"To Hajiya ban sani ba wlh, sai dai idan na je yanzu zan gani."
"Subhanallah.. ai ba kai kaɗai zaka je ba, mu tafi gaba ɗaya, Allah sarki jiyan nan fa ya zo gidan nan, yanzu da ace mutuwa ce sai dai mu ji an ce ya mutu, oh Allah! Allah yasa dai ba magauta bane domin dama duk wanda ya shiga siyasa ai baza a raba shi da su ba."
"Haka ne Hajiya. Nima wlh Ina tunanin haka." Yafaɗa fuskar shi duk a dame
"To ka jira Ni bari in Yi wanka. Ka turo min Zabba'u da Allah."
Yace, "to." Yana miƙe wa ya fice. Sai da ya je ya sanar wa Zabba'u wacce take kichen tana haɗa kumallo kafin ya nufi Steps zai haye
A lokacin ne MEEMA ta fito daga ɗaki a cikin shirin ta na zuwa Office. Ganin shi yasa tayi saurin ɗaga murya da cewa, "Uncle good morning."
Tsaya wa yayi ya juyo. "Ah ah my daughter. You wake up?"
"Na'am Uncle." Tafaɗa tana Isa wurin shi. Ta kama hannun shi tayi masa kiss tana kallon shi
Shi kuma ya shafa kanta yana murmushi da cewa, "Do you go to work?"
Jinjina masa kai tayi tana mayar mishi da martanin murmushin
"Ok. Let's go out together I'll drop you off at work. We're going to greet my friend who came here yesterday. It had an accident last night."
Waro ido waje tayi da cewa, "This one we greeted yesterday?"
"Yes daughter."
Fuskar tausayi tayi tace, "eyya. God forbid. He don't hurt?"
Sai da ya riƙe hannun ta da alamun rarrashi yace, "insha Allah It's easy for him, will you go and greet him?"
Gyaɗa kanta tayi don ta kasa magana, haka kawai taji gaban ta na faɗuwa while idanun ta sun cika da hawaye
Ganin yanda ta koma sai yayi murmushi yana cewa, "You Care about him?"
Still gyaɗa mishi kai tayi don ta kasa yin magana, sosai bakin ta yayi mata nauyi
"Ok let's go to my room, don't worry ok? Insha Allah he will be fine."
Hannun su a saƙale da juna suka wuce sama. Ɗakin Ummee yayi Nocking still Yana riƙe da hannun MEEMA
Tana buɗe wa suka haɗa ido da MEEMA
Ita kuma tayi saurin ɗauke kanta tana sake haɗe kyakykyawar fuskar ta
Ummee yanda ta ga MEEMAN ne yasa ta tambayi Uncle Hashim bayan ta amsa gaisuwar shi. "Me ya sami MEEMA kamar akwai wani abun da ke damun ta?"
Sai da ya ɗan kalli fuskar ta kafin yace, "eh Aunty, na sanar mata da hatsarin da Dude yayi ne shi ne duk ta shiga damuwa. Dama shi na zo faɗa miki Umar yayi hatsari jiya da dare."
"Subhanallah.. innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.. da sauƙi ko?"
"I don't know aunty, Amma Hajiya tace mu shirya gaba ɗaya sai mu je mu duba shi."
"Ok to bari in shirya." Tafaɗa tana koma wa cikin ɗakin
Shi kuma ya ja hannun MEEMAN suka wuce nasu ɗakin
Shigan su ɗakin Jalila ganin su tare yasa ta washe baki tace, "oh yau tare kake da daughtern taka har nan?"
Murmushi yayi yana zama a gefen Habeeb
While MEEMA na tsaye. Sai ta gaishe da Jalilan tana ɗan sakin fuskar ta
Habeeb da sauri ya taso ya rungume ta yana kiran ta da, "Aunty."
Hakan yasa ta saka hannu ta sake rungume shi tana mishi magana
While Uncle Hashim kuma yana sanar da Jalila abun da ke faruwa. Sannan ya sanar mata, "ta shirya su je duba shi".
MEEMA tana tare da su har suka shirya sannan suka sauko ƙasa. Tun suna yin Breakfast gaba ɗaya ta sauya, abincin kawai take ci hankalin ta ba ya jikin ta, haka kawai a zuciyar ta ta ƙosa ta je ta ganshi, duk ta damu fatan ta Allah yasa yana ƙoshin lafiya. Babu abinda ke mata gizau sai kyakykyawar fuskar shi, ita kanta mamakin yanda ya tsaya mata a rai take yi, amma kuma gani take yi tausayin sa ne ya shige ta kasancewar hatsari yayi, Allah-Allah take yi su tafi
Da suka tashi tafiya mota biyu suka cika suka tafi asibitin da aka ce yana can.
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NASIHA*
_Duk wanda ya karya ginshiƙin addinin sa, duk wanda ya bijire wa umurnin mahaliccin sa, duk wanda ya saɓa wa koyarwar Annabin sa wanda aka aiko shi ya kasance jagora ga al'umma, duk wanda ya ji kalmomin Ubangiji da suke gaya masa me ya kamata yayi ya kuma fahimce su amma duk da haka ya dage a kan hanyar tsageranci da hamɓare su, duk wanda yake fankamar shi ya fi ƙarfin ya bauta wa Allah Ubangijin sa, to, duk wani horon da ya same shi bai yi yawa ba. In ya tsaya tsaf ya ƙi yin Sallah lalle ya fita daga daular Islama kuma ba shi da damar ya kuka da hukunci da ya dace da shi Kamar dai yadda Alƙur'ani yayi bayani. Allah yasa mu dace._
*NO_25*
A haraban Hospital ɗin suka tsayar da motocin kafin suka fito. Uncle Hashim ya fito da Hajiya ya zaunar da ita a wheelchair ɗin ta, sannan sai Zabba'u ta tura ta suka yi cikin asibitin. Tun kafin ma su tambayi ɗakin da aka kwantar da shi suka hango securities a gaban wani ɗaki. Hakan ya tabbatar wa da Uncle Hashim nan ne ɗakin da Abokin shi yake. Can ya nufa suka take mishi baya
Securities ɗin tsayar da su suka yi suna tambayar, "ina zasu je?"
Uncle Hashim ne yayi musu bayani
Kasancewar sun gane shi yasa suka bar su suka shiga
A ɗakin daga Momy sai Abdul ne zaune sun tasa Umar Faruk a gaba gunun tausayi, kai kace sun damu da shi ne a yanda suka nuna, musamman ma Momy wacce gaba ɗaya idanun ta sun jiƙe da ruwan hawaye sai kai gyalen ta take yi tana kwashe su
Yayinda shi kuma yana kwance a saman gado idanuwan sa a rufe, da alamu ba wasu rauni ya ji ba sai dai a kansa da aka naɗe mishi da bandage, sai kuma ƙafar shi ɗaya ta dama da itama duk an saka mishi bandage a ciwukan da ya ji, sai kuma ƙaramar yatsar shi itama ta hannun dama wacce aka saka mishi drip
Shigowar su yasa su Momy suka bi su da kallo suna amsa sallaman nasu. Kasancewar Momy ta gane su musamman ma ganin Uncle Hashim da tayi yasa ta washe baki tana tashi tsaye tare da musu lale marhaban
Shima Abdul tashi yayi ya bai wa Ummee kujeran sa
Sannan aka gaisa cike da mutunci. Su Hajiya suka yi musu, "ya me jiki?"
Momy ta amsa da faɗin, "alhmadulillah. Ya samu barci ne mu ma tunda muka zo be farka ba."
"Allah Sarki! Allah ya ba shi lafiya. Wlh hankali na ya tashi da jin labarin hatsarin shiyasa muka taho gaba ɗaya." Cewar Hajiya cike da damuwa
Momy tace, "wlh kuwa. Ai abun ne da tashin hankali. Nima ya zo ya gaishe Ni a jiyan yake ce min zai fita meeting, wlh a Raina sai da naji ban amince da fitar nashi ba, amma kuma tunda ya zama dole babu yanda zan yi, be fi mintuna goma ba aka kira mu aka sanar mana yayi hatsari, kuma motar tashi ce kaɗai ta kwace ma drever'n, Allah yasa akwai mutane tare dashi aka yi saurin taimakon shi tunda hatsarin ba sosai bane, ai mun auna arziƙi." Ta ƙare maganar tana sake share hawayen fuskar ta
Haƙuri duk suke bata. Hajiya na sake tausan ta
Sai kuma ɗakin ya ɗan yi jugum
A lokacin ne Umar Faruk ya buɗe idanun sa
Hakan yasa Uncle Hashim da ke tsaye ya koma gefen gadon ya zauna yana kallon shi
A hankali yake bin mutanen ɗakin da kallo yana yi yana ɗan lumshe idanun sa
Uncle Hashim ya soma mishi sannu kafin sauran su soma gaishe shi da jiki
Kanshi kaɗai yake ɗaga musu yayinda ya sauke idon shi a kan MEEMA wacce ta tsaya a can baya ta zuba mishi ido
But yana kallon ta sai ta ɗauke nata idon daga kallon shi tana ɗan gyara tsayuwar ta kasancewar ta soma gajiya, ɗan ɗago kai ta sake yi ta sauke a kanshi ta ga har yanzu ya kasa ɗauke ido a kanta, sai ta janye nata tana sauke kai ƙasa tare da wasa da yatsun hannayen ta. Ta kula yana da yawan kallo a yanda ta fahimta, kaifin idanun shi yake sa take gane ita yake kallo, hakan ke haifar mata da faɗuwar gaba me tsanani, sosai gaban ta ke bugawa wanda yasa ta kasa tsayuwa wuri ɗaya tana ɗan jujjuya jiki
Momy wacce ta lura da kallon da yake yiwa MEEMA yasa ta mayar da kallon ta gare ta, sai yanzu tayi mata kallon ƙurilla domin tun shigowar ta baza tace akwai ta a cikin ɗakin ba ma, duba da yanda ta ja can baya ta tsaya. Hakan yasa ta ɗan washe baki tana cewa, "ita kuma wannan kyakykyawar yarinyar fa daga ina?"
Zabba'u tayi saurin bata amsa da faɗin, "ai ɗiyar Hajiya ƙarama ce, sunan ta MEEMA."
"Allah Sarki! Masha Allah yarinyar kyakykyawa da ita."
Duk murmushi suka yi
While Abdul da shima sai yanzu ya kula da ita, tunda ya kafa mata ido ya kasa ɗauke wa, sai ƙare wa halittan ta kallo yake yi daga sama har ƙasa tamkar idanun sa za su fito waje har buɗe baki yayi
Uncle Hashim da shima yana kula da kallon da Umar Faruk yake bin MEEMA da shi, sai yayi murmushi yana matso da fuskar sa gefen sa, ya ɗan raɗa masa maganar, "sai na tsole idon idan baka dena kallon ta ba, ko dama ba jinya kake yi ba?"
Hakan yasa ya saki kyakykyawar murmushin sa yana ɗan lumshe idanun kamar zai rufe su sai ya juyo su ga kallon Uncle Hashim ɗin, be ce komi ba illa murmushin da yake saki, sai kuma ya ɗan karkata kai ya kalli Habeeb da ke jikin Jalila ya yafico shi da hannu
Hakan yasa yaron ya iso wurin shi
Yayi mishi murmushi da cewa, "har da kai kaima ka zo duba ni?"
"Eh Uncle. Ya jikin ka?."
"Alhamdulillah my boy. Kai ma ya naka jikin?"
"Ai naji sauƙi." Yafaɗa yana ɗaura hannun sa a kai
Zabba'u tace, "ai ya ji sauƙi sosai in dai Habeeb ne."
"Eyya shima be da lafiya ne ashe? Allah ya sawwaka ɗan yaro na, taho mu gaisa ko." Cewar Momy fuskar ta cike da fara'a
Daga Hajiya har su Ummee amsa mata suka yi da, "Ameen Ameen."
Iso wa yayi wajen ta, ta ɗaura shi a cinyan ta tana tambayar shi
Daga haka ɗakin yayi shiru illa sauraron surutun da Habeeb yake yi tare da Momy.
Ita kuwa MEEMA duk ta gama gajiya, gaba ɗaya fuskar ta ta sauya tamkar zata yi kuka sabida rashin sabo
Ta gefen ido duk Umar Faruk yana kallon ta, a ransa kuwa dariya ta ba shi yana mamakin sangarta irin nata domin ya kula tsayuwar nata ne ya dame ta take shirin kuka. Sai dai ya kasa yanda zai yi yayi mata magana bare yace, "ta zauna." Wanda hakan ne a cikin zuciyar sa
Shima Abdul ya kula da yanayin ta hakan yasa ya buɗe baki da ninyan yin mata magana
Sai Uncle Hashim yace, "Daughter, you are tired? Come here and sit down and let me out."
Murmushin yaƙe ta ɗan saki sai dai bata ce komi ba ganin inda yake nuna mata ta zauna ɗin, ma'ana a saman gadon shiyasa ta kasa motsa wa
Hajiya tace, "ai mu ma ba daɗe wa zamu yi ba, But before we leave, go and sit down since you are tired."
Kanta ta ɗan gyaɗa ta nufi wajen ta ɗofana mazaunan ta a inda Uncle Hashim ya matsa mata, hakan yasa har jikin ta ke gogan juna da cinyan Umar Faruk. A tare suka lumshe idanun su ko wanne yana jin wani abu ya tsirga mishi; wanda ita ta kasa jure wa dole ta sake jan jikin ta ta matsa gefe sosai ta yanda baza su haɗe ba.
A haka dai suka zauna jigum sai su Hajiya da suke ɗan taɓa hira. Sai da wasu mutane da suka zo gaishe da Umar Faruk ɗin suka shigo sannan su Hajiya suka yi musu sallama suka fice a ɗakin. Manyan Mutane ne kusan su goma ƴan siyasa suka zo gaishe da shi.
Uncle Hashim da MEEMA a mota ɗaya suka koma. Dayake zai sauke ta a wajen aiki. Yana zuwa ya sauke ta ya wuce tunda akwai inda zai je
Tunda ta shiga ciki suka gaisa da waɗanda ta ci karo da su ta wuce Office ɗin su. Sai dai tana shiga babu kowa sai ta tsaya ba tare da ta zauna ba. Tana shirin juya wa zuwa Office ɗin Idris sai wata me suna A'isha wacce itama aiki take yi a gidan t.vn, ita ta hange ta ta ƙariso wurin ta tana cewa, "Hi MEEMA".
"Hi." Ta amsa mata tana kallon ta
Murmushi A'isha tayi tace, "Today I thought you would not come, and Laɗifa did not come, and you is ok?"
"Fine. I went somewhere."
Isowar Idris wajen shi yasa A'isha ta yiwa MEEMA sallama ta wuce
Yana isowa suka gaisa yake tambayar ta, "Where are you going? I've just come to pick you up but your gate Man says you're all out."
"We went to the hospital."
"Subhanallah.. Who is sick?"
Shiru tayi, sai kuma tace, "This man we went to his house me and Laɗifa and interviewed, amm... Senate."
"Ok Senator Umar Faruk Aliyu, You went to him?"
Gyaɗa masa kai tayi da faɗin, "na'am."
"Ok I heard, right now I want to go and talk to him about the accident, now go to the office and rest when I finish my work so we can go together and talk to him. From there we go to greet Laɗifa and She is not feeling well."
Fuskar ta ne ya sauya tana ɗan sake buɗe manyan idanuwan ta tace, "really? I don't know, i didn't call her, easily her body?"
Ɗan numfashi ya ja kafin yace, "Calm down, insha'Allah. Her body is fine, but I just called her and she couldn't pick up the phone. Her mother informed me of her condition. Go inside and finish your work and we'll go."
Ɓata fuska tayi hawaye na ciko mata a idanu tace, "I can't work now until I see her condition. I'm scared."
Murmushi yayi a ransa yace, "MEEMA rigima! tana jin ta kamar wata yarinya ce." Sosai ya kula akwai dolanci da sangarta irin na ƴaƴan masu kuɗi a tattare da ita, irin waɗan da aka shagwaɓa ɗin nan sosai. komi nata tana yin sa ne tamkar wata ƙaramar yarinya, ba ta kunyar ta yiwa ko waye taɓara ko kuma tayi masa kuka, bata da wahalan kuka ko a gaban waye ne. "Fine. Let's go to my office and pass from there."
Kanta ta ɗaga mishi tana bin Bayan shi. Daga can bayan ya gama abinda zai yi suka fito suka wuce asibitin da aka kwantar da Senator Umar Faruk.
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
A can kuwa gida lokacin da su Hajiya suka koma. Me gadi na buɗe musu ƙofa Ummee ta tura hancin motan ciki. Tunda suka shiga suka ga wata jan mota wanda sun tabbatar ba na gidan bane
Me gadi na rufe Gate ɗin ya iso wurin su da gudu. A lokacin duk sun fito suna ƙoƙarin fito da Hajiya. Ya gaishe su yana cewa, "Hajiya dama baƙi ne suka zo nan gidan. Ga su can a cikin mota."
"Baƙi kuma?" Da Hajiya da Ummee suka haɗa baki wajen faɗa
"Eh wlh. Nayi yunƙurin tsayar da su daga waje amma sun ƙi tsaya wa, dole suka saka Ni na buɗe musu ƙofa suka shigo. Bari inyi musu magana sai su zo." Ya ƙare maganar yana wuce wa wajen motan da hanzari
Bayan yayi musu magana ne sai suka fito daga motan
Ai Ummee na ganin su ta gane su, Kawu Ali ne da Kawu Zubairu
Hajiya kuma sai da suka iso gab da ita itama ta shaida fuskar su
Su suka fara gaishe da Hajiya kafin itama ta saki fuska ta amsa su tana musu lale marhaban
Ita Ummee ta kasa musu magana sai kallon su da take yi, domin ta san halin su tunda ta gansu a nan ba alheri ne ya kawo su ba, baza ta manta sanda suke zuwa can Riyadh suke cin musu mutunci ba ita da Faruk da ɗiyar su. Sanadi har da rashin ƙaunar da suke nuna mata yasa ta bi ruɗin ƙawaye ta bar mijin ta a halin laluran da yake tsananin buƙatar ta ta taho nan. Daƙyar ta buɗe baki a yanzu ɗin ta gaishe su
Duk amsa wa suka yi fuska a ɗaure suna wani ciccin magani
Ita dai taɓe baki kawai tayi tayi gaba abin ta
Hajiya ce ta ce musu, "su shiga ciki."
Sannan ne suka bi bayan su suka shiga Parlour. Sai da suka zauna aka ƙara gaisa wa
Kafin Kawu Ali ya soma magana da faɗin, "ba wani abu ya kawo mu nan ba sai maganar Zulaiha. To mu mun zo ne mu tafi da ita kawai babu wani kace nace duk da dai wulaƙancin da ɗana ya fuskanta zuwan shi nan, yarinyar nan ta ci mana mutunci ba kaɗan ba amma duk da haka muka biyo baya saboda a matsayin mu na dolen ta, ba don haka ba wlh babu yanda za'a yi mu tako ƙafar mu mu taho nan. Don haka sai ku bamu ita mu tafi da ita abun da ya kawo mu kenan."
Hajiya da ta zuba musu ido tana kallon su jin yayi shiru sai tace, "to Aliyu kake ko wa? Zancen gaskiya baku yiwa yarinyar nan adalci ba, ita a yanda ta faɗa mana so Kuka yi kuyi mata aure ba tare da amincewar ta ba, hasali ma bata san da zancen ba sai da biki ya zo. Hakan ai ba kyautuwa bane..."
Bata ajiye numfashi ba Kawu Zubairu ya tada jijiyan wuya da cewa, "to ke a ganin ki Hajiya har sai an tambaye ta sannan zamu iya mata aure? Muna da ƴancin da zamu iya aurar da ita ga duk wanda muke so, sannan shi wannan yaron ɗan mu ne haka itama ƴar mu ce, ganin babu ran mahaifin ta yasa muke so mu rufa mata asiri mu aurar da ita ga ɗan mu kamar yanda ya ce yana so, amma mu ma ba'a son ran mu bane tunda babu yanda za'a yi muna ji muna gani mu ɗaura wa ɗan mu yarinyar da ta gama gantale wa ta kasa auruwa, yarinyar da kaɗan ya girme mata don mun yanke wannan hukuncin shi ne zai zama abun magana? Ai idan ba'a gode mana ba baza ayi Allah wadai da mu ba."
Sosai maganganun Kawu Zubairu ya ɓata wa Hajiya rai
Ba ita kaɗai ba har Ummee wacce tana ji tana gani ana son aibata mata ɗiya. Shiyasa tayi saurin cewa, "maganar gaskiya Yaya bazai yiwu ace ku zo har cikin gidan mu kuna gaya wa Mahaifiya ta da ɗiya ta magana ba, idan na jure a baya wancan nayi shiru ne domin ɗan uwan ku, amma yanzu babu wanda zai zo har gidan mu ya ci mana fuska, ita MEEMA ai ɗiya ta ce kuma ta dawo hannu na baku da halin amsar ta, ita da kanta ta zaɓi nan don haka babu wanda a cikin ku zai tafi min da yarinya wani wuri."
"Auu iyeeeee! Wuyan ki ya isa yanka Zulai mu kike faɗa wa haka?" Cewar Kawu Ali a zafafe
Hajiya tace, "gaskiya ce ta faɗa, babu inda zaku je mata da ɗiya tunda ba arziki ne da ku ba."
Kawu Ali yace, "to wlh baku isa ba, dole sai mun tafi da ita tunda mu ne ya zama wajibi ta zauna da mu, idan ba haka ba wlh babu inda zamu je ƙafar mu ƙafar ta, har ku kun isa? Matsiyatan banza matsiyatan hofi! ɗan uwan mu ya bar dukiya dole ai ku ɗauke ta, meye bamu da labari a kai, nan ita uwar ta ta tafi ta bar su sai yanzu da kuka san ya mutu shi ne kuke da bakin cewa zaku riƙe ta, to zan gani, wlh tallahi sai dai kotu ta raba mu da ku."
"Yo kuce kuɗi kuka biyo ba yarinya ba? Akwai wasu matsiyata ne bayan ku? Tunda ba mutunci ne daku ba ku fice min a gida tun kafin ku ga abin da zai faru da ku, ƴan iska mara sa mutunci." Inji Hajiya itama a zafafe kamar zata tashi tsaban rigima
Nan fa sai cacan baki ya kaure wanda dole su Jalila ita da Zabba'u suka fito tunda su basu a wurin
Yanda suka taru suke ta cin ma ƴar tsohuwa mutunci ne yasa Ummee itama take tare mata
Jikin Jalila na rawa ta nufi ɗaki ɗauko waya ta kira Uncle Hashim ganin abun nasu ba na ƙare bane. Tana kiran shi ya ɗauka ta sanar mishi da halin da ake ciki
Kankace me ya kashe wayan da faɗin, "ga yi nan zuwa yanzu-yanzu."
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
Idris na Isa hospital ɗin ya faka motan suka fito suka shiga ciki. Sai dai koda suka je shiga ɗakin securities ɗin shi sun hana su shiga duk da Idris ya nuna I.D card ɗin shi
Da ya dame su da naci ne sai ɗaya security ɗin ya shiga ya sanar wa da Umar Faruk ɗin. Babu jima wa ya dawo ya sanar musu, "ba ya buƙatar hira da su."
Fitowar security ɗin ne ya bar ƙofan a buɗe wanda ya bai wa Umar Faruk damar hango kayan MEEMA, baƙin Abayar da ta sanya tabbas shi ne ya hango tunda dashi ta zo ɗazu. Sai leƙa kai yake yi sai dai ya kasa yin magana domin ya san ko ya ɗaga murya baza su ji ba, bare shi ba me son hayaniya bane. Yana kallo har suka tafi sai ya ɗan yarfa kai gefe yana mayar da idanun sa ya lumshe su. Allah yasa sai ga security ɗin ya shigo da sauri ya buɗe ido yana kallon sa ya sanar mishi, "yayi maza ya kira mishi Macen tazo."
Hakan yasa ya fita da sauri ya isa haraban Hospital ɗin
A lokacin har sun shiga mota Idris na ƙoƙarin tayar wa
Sai ya isa wurin da sauri. Ya tsayar da shi yana faɗa mishi saƙon Umar Faruk ɗin. Ganin Idris ɗin zai fito sai yace dashi, "ita kaɗai yake buƙata."
Koma wa yayi ya zauna Idris ɗin yana duban MEEMA wacce take zaune a cikin motan. Bata ma san me suke cewa ba tunda hankalin ta na kan waya tana latsawa. Yace da ita, "MEEMA come out and join Senator Umar Faruk he wants to talk to you."
Duban sa take yi da mamaki but taƙi yin magana sai ɗan ƙara buɗe kyawawan idanuwan ta da tayi
"Yes. He said he should be called you. I think you will talk together." Sai ya miƙa mata recorder ɗin hannun shi yace, "Go with this and discuss."
Ɗan jim.. tayi tana kallon shi, sai kuma ta saka fararen hannayen ta ta amshi recordern ta fice. Bayan security ɗin tabi har zuwa ɗakin da yake ciki. Shi security ɗin ya tsaya a waje ita kuma ta tura ƙofan ta shige a hankali kamar wacce take tsoron shiga.
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏼
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NO_26*
Tunda ta turo ƙofan ta shigo idanun sa na kanta ya kasa ɗauke su
Ita kuma ganin kallon da yake mata yasa ta kawar da kai tana takowa a hankali zuwa cikin ɗakin, tsayawa tayi ta kasa ƙarisawa illa sauraron bugun zuciyarta da ke ƙara hauhawa take yi
Shi ne yace mata, "Come and sit down here." Ya nuna mata kujeran da ke bakin gadon nashi
Hakan yasa ta ɗan kalle shi sai kuma ta taka izuwa kujeran ta zauna a hankali. Kanta a ƙasa ta kasa ɗagowa
Sai ɗakin yayi shiru illa shi da yake faman kallon ta ko kaɗan ya kasa ɗauke ido a kanta, be san meyasa ba tunda ya fara ganinta ta tsaya mishi a rai, ba ya gajiya da kallon kyakykyawar fuskar ta hakan yasa be iya control kansa, wani lokacin be ma san yana kallon ta ɗin ba sai daga baya yayi ta mamakin kansa. Yanzun ma daƙyar ya iya buɗe baki yace, "Do you need anything from my place?"
Kanta ta ɗago ta kalle shi a wannan lokacin sosai sai dai fuskar ta babu walwala. Bata iya ce mishi komi ba illa kallon shi da take yi
Shima sai ya tsira mata ido yana kallon cikin idanun ta yayinda yake jin tamkar wani abubuwa suna jansa izuwa cikin nata idanun
Ta kasa jure wa ta ɗauke idanuwan ta tana mayar da su ƙasa. Sai kuma a hankali ta furta, "how your body?"
Yanda muryan ta ya bugi kunnen sa yasa ya lumshe idanun sa sabida daɗin sanyin muryan ta. Ya ɗau lokaci a haka kafin ya ware idon a kanta yana furta, "alhmadulillah. How did you get home?"
"Fine." Tafaɗa a taƙaice. Sai kuma ta ɗan ɗago ta dube shi da cewa, "We want to talk about your accident. If you don't mind I'd like to talk to you?"
Idanun sa cikin nata yace, "I don't want to talk to journalists. I have nothing to tell you. And I see that you want to restrict me."
Jin maganar nasa yasa ta tashi tsaye still tana kallon shi, sai dai bata ce komi ba ta juya ta fice tana mamakin, "to meyasa ya kira ta idan babu abinda zai ce da su?"
Shi kuma ya kasa tsayar da ita yana kallo ta fice domin be san me zai ce mata ba, shi dai ya bi umarnin zuciyar sa ne wacce ta saka shi ya kira ta ba shi da abun ce mata.
Tana isa wajen motan ta buɗe ta shiga
Idris da ke faman jiran ta kallon ta yayi ya tambaye ta, "Did you interview him?"
Girgiza masa kai tayi kamar baza tayi magana ba sai kuma ta kalle shi tace, "He says he doesn't need to talk to us."
Mamaki ne bayyane a fuskar sa, sai yace, "But why does he need to see you if not the interview would bother us?"
"I don't know." Tafaɗa a hankali tana kawar da kanta gefe
Shima be ce komi ba ya ja motan suka fice. Sai da ya cilla motan a kan titi kafin ya sanar mata, "their house Laɗifa will pass."
Bata ce masa komi ba har suka kai bakin gidan
Ya taka birki suka fito suka shiga cikin gidan su Laɗifa. Da Umman ta suka soma cin karo a tsakar gida don haka Idris ya gaishe ta. Itama MEEMA ta gaishe ta da Hausan jin Idris ya gaishe ta
Cike da fara'a ta amsa musu tana musu lale marhaban. Kana kuma tayi musu jagora zuwa ɗakin nasu
Suna shiga suka ga Laɗifan a kwance a saman kujera
Ganin su yasa ta tashi zaune da murnan ta tana washe baki, duk da kana kallon ta zaka fahimci tana jin jiki amma hakan be sa ta ƙi nuna farin cikin ta da ganin su ba
Idris da ya ƙware wajen tsokana sai ya kama haɓa yana cewa, "Umma anya yarinyar nan ba ciwon aure ne ke damun ta ba? Dama na faɗa miki ki gaggauta aurar da ita kin ƙi, kullum ita ciwo ba ta shafe sati bata yi ciwo ba."
Dariya Umma tayi
While ita kuma Laɗifa hararan shi tayi tace, "masharranci kawai, kai me ya hana ka auren sai Ni zaka ce nayi? Idan ka gaji da gani na ka aurar da Ni mana." Sai kuma ta kalli MEEMA tace, "Sister come here and sit."
Zama MEEMAN tayi a gefen Laɗifan
Idris da shima ya sami wuri ya zauna sai ya taɓe baki yace, "ai Ni bani da kuɗin miki aure, amma zan sanar wa Baba tunda naga alamu aike na kike yi. Wlh ina faɗa miki yarinya gwara kiyi auren ki kar ki biye ta tawa, Ni yaro ne har yanzu ban isa aure ba idan kika ce sai kin jira Ni ai kuwa zaki yi kwantai a gida don Ni ba take nake yi ba, bar gani na haka na san abun da yake zuciyar ki."
Ɓare baki tayi kamar zata yi kuka tace, "Umma kin gansa ko ki ce ya dena ba na so, nima me zan yi da kai ai kayi min ƙanƙanta."
Zaro ido waje yayi, zai yi magana kuma sai suka haɗa ido da Umman, sai ya kwashe da dariya yace, "Allah arziƙin ki ɗaya akwai Umma da sai na faɗa miki magana Al'ƙur'an."
Umma tace, "ai Ni Idris ba kunyata kake ji ba da kayi maganar ka ma. Hmm Allah ya shirye ka baza ka sauya hali ba wlh."
Dariya kawai yake yi
Laɗifa kuma bata kula shi ba illa riƙe hannun MEEMA da tayi tana kallon Umman nata tace, "Umma wannan ita ce MEEMA wacce nake baki labari ƙawata."
Murmushi tayi Umman tace, "Masha Allah ga ta kyakykyawa, Ashe Zulaiha tana da yarinya kamar ta ban taɓa sani ba wlh. Sannu ƴar nan ga shi ko ruwa ban kawo miki ba, na zauna ina jin shirmen Idris."
Dariya yayi yace, "ai Umma bata san me kike cewa ba. Bari Ni in taimaka in ɗauko mata ruwan." Ya tashi izuwa wurin Fridge ɗin
Ita kuma Umma tace, "au ba ta jin Hausa ne?"
Laɗifa tace, "eh Umma, har yanzu ta kasa koya wlh, kuma kwanaki har na fara koya mata amma ko tunawa ba tayi." Ta ƙare maganar tana dariya
"Allah Sarki." Cewar Umman. "Da sannu zata iya tunda tana tare da mu Hausawa."
Ruwan da Idris ya kawo mata MEEMAN ta amsa ta kurɓa kafin ta ajiye. Cike da sanyin murya tace da Laɗifan, "I'm worried about you, but I'm glad to see you. God get well soon."
Murmushi Laɗifa tayi tace, "Ameen thanks MEEMA."
Idris yace, ,"ai ta warke sosai. Get up and let's go since her body is fine."
Murguɗa masa baki Laɗifan tayi da cewa, "baza ta tashi ba, a nan zata zauna, kai ka tafi kai kaɗai."
"Kina ji ko Umma? Yarinyar nan naki ta raina Ni wlh zan fasa mata baki."
Umma tace, "ai kun fi kusa wlh babu ruwana."
Hakan yasa Laɗifa tayi masa gwalo
Yayi ƙwafa shi kuma yana kaɗa mata yatsa alamun, "zai riƙe ta."
Da haka dai suka zauna suna ta shirmen su, duk da Laɗifa ba ta jin daɗin jikin ta sai da ta biye mishi don Idris akwai wasa, ko ba ka so idan ya saka ka a gaba sai ka biye mishi
Daga baya ya tashi yace, "za su tafi." Suka yi musu sallama suka fice. Kai tsaye wajen aiki suka koma.
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
Zuwan Uncle Hashim da ya tarar da yanda suke ta cin ma Hajiya mutunci ai sai ya hau su da faɗa. Dama ga shi akwai fushi nan da nan ya zuciya yace Jalila, "ta ɗauko mishi bindigan shi duk sai ya harbe su."
Yanda suka ga Uncle Hashim ɗin yake yi ne tamkar be da Kai, sun san tsab zai iya harbe su kamar yanda yace, hakan yasa suka ɗibi jiki suka fice daga waje suna ta zage-zage a kan, "sai an basu gadon su." Daƙyar suka bar gidan
Hajiya tace, "ku ne matsiyata, gado ne za'a raba a kawo muku naku har inda kuke, MEEMA kuma babu inda zata koma a nan zata zauna." Nan ta saka Uncle Hashim ɗin da zancen, "idan MEEMA ta dawo yayi magana da ita a kan dukiyar Mahaifin nata".
"Ai Hajiya ki bar zancen waɗannan matsiyatan, gadon ne baza a raba ba inga wanda zai sake tako mana gida yace zai ci mana mutunci, ƴan iska matsiyata."
Hajiya tace, "a'a dole ne a raba ko don mamacin, kana ganin yanda suke tada jijiyan wuya duk wannan fitinan a kan Faruk zai ƙare, gwara a raba ko zai samu salama a cikin ƙabarin shi, inyaso ko can Riyadh ɗin ne sai ku je tare a san abun yi."
Kansa kawai ya gyaɗa ya haura sama da sauri domin har yanzu a cikin fushi yake, bindigan na hannun shi tunda Jalilan ta kawo mishi, Da da farko ta ƙi kawo wa ne tana tsoron abun da zai biyo baya, sai da ya hau ta da faɗa sannan ta kawo a lokacin su kuma su Kawu Ali tuni sun fice a gidan.
Su Hajiya suna falo suna mayar da zancen duk kan su sai cece kuce suke yi suna tsine wa su Kawu Ali musamman yanda Ummee take ta faɗar mugun halin su, abubuwan da suke musu tun Faruk yana da rai, dama ba shi suke ƙauna ba dukiyar shi suke so, ga shi kuma yanzu sun biyo sahu har suna iƙirarin zasu aurawa ɗan su MEEMA ne.
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
*TWO DAYS AGO*
"Ke ɗaga kanki mana, wai lafiyan ki ƙalau? Na kula tunda muka zo school ɗin nan kike cikin damuwa karatun ma be dame ki ba yau". Cewar Abida wacce ke zaune a kan deks tana taunan chewing gum idanun ta a kan Luwaira. Ganin ta ƙi ɗago kai yasa ta bugi bayan ta tana cewa, "wai Ni kike wa wulaƙanci Luwaira? Ina magana kin yi banza da Ni."
Sai a lokacin ta ɗago kan nata ta zuba wa Abidan idanu. Fuskar ta babu walwala tace, "me kike so in CE miki? Abida ba na son takura don Allah ki bar Ni in huta."
Taɓe baki tayi tana wani yatsina da taunan chewing gum ɗin bakin ta, sai da ta dage ta ɗirka ƙwai ta fasa shi tuss a kusa da fuskar Luwairan kafin tace, "kin san hali na, idan har baki kula Ni ba wlh na dinga damun ki kenan, bazai yiwu ace tun ɗazu muna tare dake kin bar Ni ina ta zuba Ni kaɗai ba, sannan kin wani luƙume kai a benci kamar wata kunkuru ki ce bazan tanka ba. Dalla ki faɗa min damuwar ki Ni fa ƙawar ki ce."
Tsaki Luwaira ta ja, ta san halin Abida shiyasa ta buɗi baki tace, "baza ki gane ba koda nayi miki bayani Abida..."
Katse ta tayi da faɗin, "ba dai ki fahimtar da Ni bane ta yanda zan gane, idan kika faɗa min damuwar ki ai zan gane."
"Hmm matsala ce ta soyayya Abida. Ban taɓa sanar da ke ba amma tunda kin matsa zan sanar miki, na san zaki kalle Ni da wani irin kallo sabida abinda zaki ji ya fito a baki na. Soyayyar Umar Faruk ne yake son kashe Ni, duk yanda na so na jure amma abin ya faskara na kasa."
"To ban gane ba. Wani Umar Faruk ɗin? Ko kin yi sabon saurayi ne?" Abidan ta tambaye ta tana tsare ta da ido
Ita kuma sai ta girgiza mata kai, sai da ta ɗan yi shiru na wasu daƙiƙu kafin tace, "Yayana Umar Faruk wanda kika sani, wanda muke gida ɗaya da shi; shi nake nufi."
"Kutmar..." Ta saki wani zagi tana duro wa daga saman deks ɗin da take, sai kuma ta koma ta zauna a kan kujera tana facing ɗin Luwairan tace, "ke kar ki haukata Ni mana da yawa, yayan ki dai Yayan ki wanda na sani? Senator Umar Faruk na gidan ku; shi kike so? To ta ya hakan zai yiwu bayan na san Yayan ki ne?"
Kanta Luwaira ta sauke ƙasa tace, "Ba Yayana bane, Umar Faruk ba Momy ta haife shi ba, hasali ma Momyn mu ita ce take auran mahaifin shi ta zo da mu gidan nan, sannan bayan ya rasu mahaifin shi sai ta riƙe Umar Faruk a wurin ta tamkar ɗan da ta haifa, bamu da wani alaƙa da Umar Faruk bayan wannan da nake faɗa miki."
"Tab ɗijam... Gaskiya ban taɓa tunanin ba Momy bane ta haife shi duba da yanda take tsananin ƙaunar sa da nuna masa kulawa, duk da a yawancin lokuta ina mamakin yanda shi ya fita daban da ku, sai dai kasancewar na ga hoton Mahaifin shi shiyasa naga kamanceceniyar su tare, hakan yasa nayi tunanin shi ɗin ya biyo Mahaifin ku ne, ashe duk wannan abun shi ba ɗan Momy bane?"
Gyaɗa mata kai tayi ta ƙara da cewa, "haka ne. Amma kuma maganar gaskiya sai dai Momy ba ta ƙaunar na aure shi."
"To a kan me? Meyasa hakan bayan duk abinda na miji me ji da kanshi ya kai har ya zarta a so shi? A ko yaushe ina ma kaina kallon ban kai ajin da Umar Faruk zai so ni ba, bayan haka da tuni na afka a ƙaunar shi, sai dai ina ganin tabbas zan sha wahala duba da yanda rayuwar shi take, ba na tunanin zai iya so na domin babu ƙofan bayyana hakan, amma ke kuna gida ɗaya da shi kuma kin fi kowa sanin yanda yake ji da ke amma ki kasa sanar mishi, tun yaushe ma kike fama da dakon son shi?"
Luwaira tace, "tun da muka dawo gidan su da zama, kamar yanda nace miki Momy ba ta ƙaunata da shi saboda wani dalili wanda sirrin mu ne bazan iya faɗa miki ba."
Shiru ne ya biyo bayan zancen nata, yayinda Abidan ta kafe ta da idanu tana tunani a ranta. Sai can kuma ta ja numfashi da cewa, "to yanzu ya zaki yi? Idan har kin amince Ni zan taimaka miki, ya kamata ace ke ce kika mallaki babban ƙadaran nan ba wata ba, dama ce a gare ki, Umar Faruk ya wuce duk yanda kike zato, idan da zaki san yanda ƴan mata suke rushing a kanshi zaki sha mamaki tunda na san ke kanki sheda ce, amma babu inda zancen shi be zagaya ba a duk faɗin garin nan, ba na son kiyi rashin shi ƙawata, duk yanda za'a yi ki mallake shi domin kun dace wlh, idan ba haka ba zaki mutu a ƙaunar shi, ke ya kamata ki fahimtar da shi halin da kike ciki, kar ki wani biye ta Momy duk da ban san dalilan ta ba, amma ina mamakin ta ya ya take son hana auren ku duk da tarin ƙaunar da take nuna mishi."
Shiru Luwaira tayi, a zuciyar ta tana son ta bayyana mata sirrin su na son ganin bayan Umar Faruk domin su mallake komi nashi, amma kuma tana tsoro, shiyasa ta sauke numfashi tace, "zan faɗa miki dalili amma ba yanzu ba."
Gyaɗa kanta kawai tayi kafin tace, "fine. Allah ya Kaimu lokacin, yanzu tashi mu je mu samu wani abu mu ci yunwa nake ji, duk chewing gum ɗin nan ya gama ƙwaƙwule min ɗan hanji."
Tashi Luwaira tayi ta ɗauki jakan ta suka fice. Sai da suka je suka ci abinci sannan suka dawo aji, dayake lecture ɗaya suke dashi ana gamawa suka yi gida. Kowa drever'n gidan su ya zo ya ɗauke ta.
Luwaira na koma wa gida ta shiga Parlour ta tarar da Momy zaune ita da su Hafsah. Da gudu yaran suka isa wajen ta suka rungume ta suna mata Oyoyo
Murmushin ƙarfin hali ta sakar musu tana rungume su duka. Daga nan ta ja su zuwa kan sofa ta zauna ta ɗaura Yusra a jikin ta
Cikin murna Hafsah tace, "Aunty Dadyn mu ya dawo, an dawo da shi daga asibiti yanzu."
"Da gaske?" Tafaɗa cike da farin ciki a zuciyar ta jin abinda Hafsan tace
"Eh Aunty. Amma bamu je mun gan shi ba har yanzu."
"Ok ku tashi mu je yanzu sai in Kai ku wurin shi."
Yanda Luwairan take rawan jiki ne yasa Momy ta bi ta da harara. Sai dai kasancewar bata kalle ta ba bata san ma tana yi ba. Har suka fice sannan tayi ƙwafa tana ɗauke kai daga kallon bakin ƙofan da suka fice.
Kai tsaye Part ɗin Umar Faruk suka wuce. Babu kowa a babban parlour'n don haka suka wuce ƙaramin parlour'n
Ai kuwa yana zaune a saman sofa daga shi sai baƙar Singlet a jikin sa da dogon wando Robber kamar na sanyi itama baƙa, ƙasan wandon da mazugi wanda ya bai wa wandon damar tsuke masa ƙafa. Gaban sa kuma computer ne yana dannawa a hankali idanun sa ƙirr a kai. Jin motsin su yasa ya ɗaga kai ya dube su, ganin su yasa ya saki yalwataccen murmushi wanda ke ƙara fito da zallan kyawun sa da kamalan sa. Nan da nan ya buɗe hannayen sa suka zo suka faɗa jikin sa ko wannen su na kiran sunan, "Dadyyyy."
Ita kuma Luwaira hannayenta ta naɗe a ƙirji tana bin su da kallo tare da sakin murmushin da be kai har zuci ba, domin a zuciyar ta ji take yi kamar ta je ta ture su ita ta shiga faffaɗan ƙirjin sa da koda yaushe yake mata gizau a cikin mafarkin ta, bata da wani buri sama da ace an wayi gari ta mallaki wannan basaraken namijin me tsananin haiba da kwarjini gami da nagarta. Tabbas duk wanda ya sami Umar Faruk ya gama dace da duniya domin duk inda na miji ya kai da ji da kanshi ya kai, kyawu nasaba gami da kuɗi duk ya haɗa, ga uwa uba tsantsan ilmi da tawali'u da son ibada. Shiyasa sosai take baƙin ciki da kishi da yaran shi duk idan ta gansu maƙale dashi, ko kaɗan ba ta iya sukunin zuciya sai dai dauriya da take azawa kanta wajen ta ga ta ɓoye abin da ke cin ranta... Maganar da yayi mata shi ya dawo da ita dogon tunanin da ta afka wanda yasa har guntun murmushin da ke fuskar ta ya gushe bata sani ba, da sauri ta gyara kanta tana sake yalwata fuskar ta da wani ƙirƙirarren murmushin tace, "na'am Yaya."
"Ya naga kin tsaya a nan? Come and sit."
Zuwa tayi ta zauna a kan sofa wanda ke kallon nashi still tana murmushi
Sai ya ɗan ƙura mata ido tare da cewa, "me ke damun ki naga kamar kina da damuwa ko? Please faɗa min abinda ke damun ki domin ba na son ganin ki a cikin damuwa, ko kaɗan ba na jin daɗi."
"Oh Yaya babu komi wlh, babu abinda ke damuwa." Tafaɗa maganar tana sosa kai tare da sake faɗaɗa fuskarta da fara'a
Numfashi ya ja tunda shi dama ba Mutum bane me son takurawa makusantan shi. "Well. But kiyi haƙuri har yanzu ban cika miki alƙawarin ki ba. Ki ƙara haƙuri da Ni kinga yanzu nauyi ya hau kaina Ni kaina yanzu bani da lokacin kai na, amma insha Allahu i promise you wannan week ɗin motan ki zata shigo."
"Allah yaya babu komi na san ai baka manta da Ni ba, Allah ya kai mu rai da lafiya."
Murmushi yayi yace, "Amin." Sai kuma ya mayar da kallon sa kan Yusra wacce ta langaɓe masa a jiki yace, "Ya dai my Baby?"
Tura baki tayi gaba tace, "Dady yunwa."
"Yunwa kuma Baby?" Yafaɗa yana ware ido
Ta gyaɗa mishi kai
"To baku ci abinci bane? Hafsah baku ci komi bane da kuka dawo school ɗin?"
Hafsah tace, "mun ci Dady, Momy ta saka Talatu ta girka mana kus-kus amma ita bata ci ba."
Fuskarsa ne ta nuna alamun damuwa, sai dai yayi shiru be ce komi ba
Hakan da Luwaira ta gani ne sai tayi saurin cewa, "Yaya bari in dafa mata a nan tunda yunwa take ji. Me zaki ci in dafa miki?" Ta ƙare maganar da kallon Yusran tana mata murmushi
"Indomie zan ci."
"Nima zan ci Dady ta dafa har da Ni." Cewar Hafsah cikin sauri
"To kuna so ku mayar da ƙanwata kukun ku ne? Basu takura miki ba ko sister?" Yayi maganar yana kallon fuskar ta
Murmushi ita kuma tayi tace, "haba dai a'a wlh, ai babu damuwa, bari in je in dafa musu."
"Ok thanks my Sister. Nima ban san meyasa Kukun su har yanzu be dawo bane, ina tunanin zan sama musu wani."
Luwaira ita dai tuni ta tashi ta nufi kichen. Hakan yasa Hafsa ta bi ta tana tsalle-tsalle
While Yusra ita kuma ƙara maƙalewa a jikin sa tayi
Shafa kanta yayi kafin ya ci gaba da latsa computern shi, jefi-jefi yana ɗago kai yana mata magana yana hura mata iska a fuska ganin tana wani lumshe idanu
Hakan yasa ta ɗan dawo da kuzarinta ta saki jiki har tana dariya. Ta soma tsalle a jikin sa kamar yanda ta saba
Ɓoyayyen ajiyan zuciya ya sauke ganin ta saki jikin ta sosai. Ya san duk da yunwa ya mayar da ita haka, ko daga kallon ta zaka gane ƙarfin hali kawai take yi saboda Yusra akwai ci ba ta wasa da cikin ta, abu kaɗan ke saka tayi wani yaushi da ita tunda ta kasance me son gazar-gazar. Shiyasa yake matuƙar ƙaunar yarinyan saboda sak mahaifiyar ta ne, har lukutin jikin ta na Nusaiba ne.
*Nayi iya yi na wajen sanar muku ina buƙatar more comments but har yanzu You don't changes, I'm very tired! from today insha Allah I will not posted again. Nima ina bukatar Comments ɗinku domin shi ke saka Ni naji daɗi a raina har na tabbatar da cewa ana karantawa, ko Thanks ka rubuta min zai tabbatar min kana karantawa, amma yanzu na gane babu masu bukata insha Allahu na dakata daga yau sai kuma sanda Allah ya waiwayo Ni. Bissalam 🙏🏻 Ina ma Real masoyana Barka.*
💎💎💎
*MEEMA FAROUK*
💎💎💎
*NA_NAFISA ISMA'IL*
*WATTPAD_UMMUDAHIRAH*
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏼
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar da wannan littafin ga Shugaba adila *SAFNA ALIYU JAWABI,* Allah ya daɗa ɗaukaka ki Amin._
*NO_27*
Bayan Luwaira ta gama dafa musu indomien sai ta zubo ta kawo musu parlour'n. Sannan tayi masa sallama ta fice
Shi kuma yana ta faman aikin shi har suka gama cin abincin suka koma wasa da juna. Daga ƙarshe kuma barci ne ya ɗauki Yusra. Hakan yasa ya tashi ya wuce sama inda ɗakin shi yake ya bar Hafsah tana kallon cartoon. Da shigan shi ɗakin inda yake ajiye towul ɗin shi ya nufa ya zari ɗaya ya wuce cikin Toilet. Wanka yayi ya fito sanye da towul ɗin a jikin sa. Kai tsaye gaban mirror ya nufa ya gyara suman kanshi kana ya wuce wajen sif ɗin kayan shi ya zaro wani farin yadi me tsananin haske da taushi, kayan dai-dai jikin sa suke sun masa kyau ainun tare da ƙara haskaka skin ɗin shi, sai yayi amfani da baƙar hula tare da cover shoes su ma baƙi, sannan ya wuce gaban mirror ya feshe ko ina na jikin shi da turaruka masu tsananin ƙamshi da shiga rai, agogo ya ɗauka ya ɗaura a tsintsiyan hannun sa kafin ya zari wayoyin sa guda biyu ya zuba a aljihun wandon sa ya fice da keey ɗin mota a hannu.
A lokacin da ya fita falo ya tarar da Hafsah itama tana gyangyaɗi, kai tsaye wajen ta ya nufa ya kira sunan ta. "Baby na KE ma barci kike ji?"
Kanta ta gyaɗa mishi ba tare da tayi magana ba
"To Ni kuma ga shi zan fita. Amma tashi mu je wajen Momy sai ku kwanta a can."
Tashi tayi shi kuma sai ya nufi wajen Yusra ya ɗauke ta ya aza ta a kafaɗan shi, tare da riƙe hannun Hafsan suka fice. Part ɗin Momy ya nufa yayi Nocking a bakin ƙofan kafin ya tura da sallama a bakin sa ya shiga. Babu kowa a parlour'n don haka ya sauke Yusra a saman kujera ya shimfiɗa ta
Yana cikin gyara mata kwanciya ne sai ga Talatu me aikin Momy ta fito daga kichen. Wajen shi ta nufa tana gaishe shi tare da mishi, "ya jiki?"
Murmushi yayi mata kamar yanda ya saba ya amsa ta cikin mutuntawa. Kana ya tambaye ta, "ina Momy?"
"Tana ɗaki bari in Kira maka ita."
"A'a ba sai kin kira ta ba, ga su Hafsah nan ki shiga da su ciki suna jin barci ne, idan Momy ta fito ki sanar mata na fita."
"To ranka ya daɗe!" Tafaɗa cikin girmamawa kana ta matso da zummar ɗaukar Yusran
Shi kuma ya shafa kan Hafsah kafin ya juya ya fice. Kai tsaye haraban gidan ya nufa nan da nan securities ɗin sa suka nufo sa suna kai gaisuwa gare shi. Tsayar da su yayi da hannu kana ya wuce gaban wata farar mota ƙirar jib zai buɗe da kanshi, amma sai ɗaya daga cikin security ɗin ya zo da gudu ya buɗe masa. Sai da ya shiga ciki kafin ya kalle shi fuskar sa a sake yace, "ba na son ku biyo baya na."
"Amma ranka ya daɗe!..."
Katse shi yayi da cewa, "ya isa. Haka nake buƙata ba na son ku biyo NI zan iya da kai na ok?"
"Ok Sir. Allah ya tsare." Yafaɗa yana sara mishi. Sannan ya mayar da ƙofan motan ya rufe mishi
Shi kuma ya ja motan a hankali ya fice a gidan.
******
Momy da ke tsaye a bakin windown ɗakin ta tana kallon duk abin da ke faruwa. Bata saki labulen ba har sanda ta ga fitar Umar Faruk sannan ta ja dogon tsaki tana yarfe labulen. Sai ta koma zagaye ɗakin hannayen ta a goye a baya, gaba ɗaya damuwa ta nuna a fuskar ta kasancewar gani take yi wankin hula na son Kai su ga dare, har yanzu sun kasa cin nasara a kan shi, ga shi abinda suka shirya domin ganin bayan shi hakan be kasance ba, ya tsallake hatsarin da suka shirya mishi yanzu basu san kuma abinda zasu yi ba next? Tunanin Momy duk ya tafi ga matakin da zata ɗauka a kanshi. Ya zata yi? Zuciyar ta tana bijiro mata abubuwa da dama a ranta wanda har yanzu ta kasa yanke ƙwaƙwƙwaran makaman abin da zasu yi. Maganar Abdul ne ya faɗo mata a rai sai ta saki dogon numfashi tana komawa bakin gado ta zauna tare da tsirawa waje ɗaya ido. ita yanzu abinda ke damun ta kar yace zai auro wata ya kawo ta cikin gidan nan kamar yanda take buƙata, duk da ba har zuci take mishi maganar ba amma ba ta son ya sake aure, gaskiya akwai matsala dole ta samo mafita, amma kuma ba ta so ɗiyarta ta aure shi domin dole nan gaba zata rasa shi, "amma kuma idan dogon burin ki zai cika fa?" Wata zuciyar ta tambaye ta haka.
✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️✳️
A hankali yake tuƙin motan cikin ƙware wa, duk da tuƙin yake yi but hankalin shi gaba ɗaya ya tafi ga tunanin abun da ke zuciyar sa, shiyasa lokaci-lokaci yake fuszar da iskan bakin shi yana ɗan dukan sitiyarin motan kaɗan-kaɗan a haka har ya kai gidan Hajiya. Ya danna horn me gadi ya fito
Ganin da yayi Umar Faruk ne sai ya koma ya buɗe mishi Gate ɗin ya shiga da motan
Parking space ya nufa ya faka motan
Da gudu me gadin ya taho ya buɗe mishi ƙofan yana washe baki da faɗin, "Barka da zuwa ranka ya daɗe!"
Murmushi yayi mishi yace, "Yauwa. Kana Lafiya?"
"Alhamdulillah ranka ya daɗe!" Yafaɗa cike da fara'a kamar zai duƙa mishi
Shi kuma fitowa yayi a motan kafin yace, "Allah yasa Captain yana nan?"
"Eh yana nan don yanzu ya dawo gidan ma."
"Ok." Yace dashi sannan ya saka hannu a cikin aljihu ya zaro sabbin kuɗi ƴan dubu ɗaya ya ba shi
Nan ya soma mishi godiya kamar zai je ƙasa don duƙa masa
Shi kuma murmushi yayi yace, "kar ka damu ka dena min godiya."
"Ai ranka ya daɗe! Dole ne. Allah ya ƙara buɗi yasa kafi haka, Allah ya tsare ka da duk kan sharrin maƙiya."
"Amin Amin." Ya amsa shi cike da jin daɗi kana ya wuce ya tafi. Kai tsaye ƙofan shiga parlour'n ya nufa yayi Nocking
Babu jima wa sai ga Uncle Hashim ya fito yana waya. Ganin shi yasa ya waro ido waje yana kashe wayan kana ya ba shi hannu tare da cewa. "ah ah patient ɗin mu ne a nan? Ya aka yi haka?"
Murmushi yayi ya miƙa mishi hannun suka cafke kana yace, "Ai naji sauƙi Malam."
Matsa mishi yayi ya shigo sannan ya rufe ƙofan suka shiga Parlour
Zabba'u da Jalila ne zaune a parlour'n. Don haka suka soma gaishe shi Zabba'u na faɗin, "ikon Allah har ka samu sauki da zaka fara yawo Umaru?"
Murmushi yayi yana zama
Shi kuma Uncle Hashim yace, "nima abun da na gani kenan. Yau fa aka sallame ka? Gaskiya zan ɗau mataki a kan masu tsaron ka da har suka bar ka ka fito, i know Momy bata san ka fito ba?"
"Haka ne. "But I'm relieved. I came to greet Hajiya."
"A'a ai baka kyauta ba kuwa. Ina kai ina zuwa gaishe da Hajiya baka da lafiya, itama baza taji daɗi ba, bari in Kira ta." Cewar Zabba'u tana tashi ta wuce
Ita kuma Jalila tuni ta tashi ta kawo mishi drinks ta ajiye mishi
Godiya yayi mata sannan ya tambaye ta, "ina Habeeb?"
"Yana tare da Ummee a ɗakin ta".
Fitowar Hajiya itama sai da tayi mishi faɗan zuwan nashi
Shi kuma yace, "ya zo gaishe ta ne kawai."
Tace, "haba dai Umar. Kana wasa da lafiyan ka dai, amma mene ne na zuwa gaishe Ni bayan yau aka sallamo ka?"
Uncle Hashim yace, "hm Hajiya bar shi kawai."
Tace, "duk da haka dai mun gode, sai dai ka riƙa kula da lafiyan ka. Ya jikin naka Yanzu?"
"Alhamdulillah Hajiya."
"Masha Allah haka ake so ai. Allah ya daɗa tsare ku ya taimaki rayuwar ku."
"Amin Hajiya." Shi da Uncle Hashim suka amsa
A lokacin Ummee itama ta fito suka gaisa take tambayar shi itama jikin nashi?
Yace, "da sauƙi Aunty."
"To Masha Allah mun ji daɗi Allah ya tsare gaba."
Daga nan ɗan hira suka taɓa kafin suka fita da shi da Uncle Hashim zuwa waje. Sai da suka kai baƙin motan shi sannan ya kalle shi yace, "Your daughter is not here?"
"Oh ko dai wurinta ka zo ne? Tell me the truth?"
Murmushi yayi yace, "No Ina tambaya ne saboda ban ganta ba."
Uncle Hashim yace, "bata dawo daga wajen aiki ba, amma na san yanzu zata shigo tunda three ya kusa."
"Ok." Yace yana ɗan kaɗa keeys ɗin hannun sa
"I still don't trust you Dude, tell me the truth you come to her?"
"Yes. I think about your talk, I want to marry her if there is no problem, because.." sai ya ɗan ja numfashi kafin yace, "because she entered my soul. I love her!"
Farin ciki ne ya bayyana a fuskar Uncle Hashim, cike da tsantsan farin ciki yace, "da gaske kake yi Aboki na?"
"Yes." Yafaɗa yana gyaɗa mishi kai
"Oh I can't tell you how happy I feel in my heart, naji daɗin abun da ka faɗa, insha Allahu zan shige maka gaba a kan samun ta, ina bayan ka dude because you fit so well."
Murmushi kaɗai Umar Faruk yake yi be sake cewa komi ba, shi kansa a zuciyar sa farin ciki ne yake ɗawainiya da shi, yana ga hukuncin da ya yanke hakan shi ne dai-dai, zuciyar sa zata fi aminta da ita a kan ta zame mishi Abokiyar rayuwa, ya san hakan zai faranta ran Momy idan yau aka ce ya je mata da zancen ya samu matar aure duk da be da tabbacin ita MEEMAN zata amince, but yana sa ran hakan
Uncle Hashim yace, "Let's go back inside and wait for her to come back sai ku gaisa."
Daga nan gidan suka koma. A nan Uncle Hashim yake sanar wa su Hajiya abun da ke faruwa
Babu wanda be nuna murnan sa ba musamman ma Ummee da ta fi kowa farin ciki, tabbas ta ga dacewar ɗiyarta da Umar Faruk saboda shi Mutum ne me matuƙar kirki, ko ba komi hakan zai kusanta ta da ɗiyarta tunda zata yi aure a nan, kuma tana fatan ta ga auren ta yanzu tunda ta kai girman da ya kamata tayi aure domin rayuwar mu a nan daban da can inda ta tashi, 26/27years ai ya wuce ace har yanzu tana zaune babu aure.
******
Koda MEEMA ta dawo babu wanda yayi mata maganar sai Uncle Hashim, sai yace mata, "she prepares and eat and a visitor comes to her."
Dayake lokacin yana parlour'n sama an kai shi ya zauna zaman jiran ta
"A visitor came over me?" She asked in surprise
"Yes daughter. Get ready and go find him."
Ɓata fuska tayi tace, "then Uncle why did you come of me?"
Dafe goshin sa yayi kafin ya kalle ta yace, "daughter please leave your questions and go to him, he will tell you what he has come to do."
Daƙyar ya shawo kanta da tambayoyin da ta tsare shi da su. Ta ci abinci sannan tayi wanka ta saka doguwar riga kamar yadda ya zame mata jiki, Abaya ce ja da kwalliyan Stones a gaban. Sai tayi Rolling da mayafin
Har zata fita sai Jalila ta shigo ɗakin ta ganta, tace, "Where are you going to go without a make up?"
Ido ta zuba mata fuskar ta da mamaki
Sai ta kamo hannunta ta zaunar da ita a gaban mirror ta soma mata shafe-shafe
Bata ce mata komi ba illa bin ta da take yi da ido. Sai da taga abun ya wuce gona da iri domin ita ta tsani kwalliya sosai a fuskar ta, "no Aunt I don't want. Leave me alone."
Murmushi ita kuma tayi tana kallon ta tace, "You're so beautiful."
Ɗan tura baki tayi tana kawar da kai
Ita kuma dariya tayi mata ta kamo hannun ta suka fice. Sai da suka fito ta saki hannun nata tace, "Go upstairs he waiting for you". Daga haka ta juya ta wuce Parlour inda su Hajiya ke zaune
Ita kuma kamar baza ta tafi ba sai kuma ta taka a hankali ta soma hawa matattaƙalan benen, tana zuwa bakin ƙofan da zata shiga parlour'n ta ja ta tsaya, tunani kawai take yi, "Then who came to her?" Bata da me amsa mata tambayar ta hakan yasa ta tura ƙofan ta shige. Sosai gaban ta ya faɗi kawai arba da shi da tayi zaune a saman kujera. Sai ta sake waro ido tana sake duban shi kamar wata status a wurin
Haka zalika shima kallon ta yake yi yana aiyana tsantsan kyawun da Allah ya bata, musamman yanzu da ya ganta da Powder a fuska ta saka kwalli a fararen manyan idanun ta, hakan ya ƙara fito da zallan kyan ta domin be taɓa ganin fuskar ta da kwalliya ba. Yanda ya ga ta tsaya ta ƙi takowa ne sai ya tashi tsam ya isa gaban ta
Idanun ta ƙirr a kanshi har yanzu tana mamakin ganin shi kuma tana son tabbatar da cewa, "Is he her guest?"
"Why did you stop here?" He spoke slowly looking at her
Hakan yasa ta ɗan ƙyafta idanuwan ta tana kawar da su, sai kuma ta sake ɗagowa ta kalle shi, ganin sun haɗa ido ta sake ɗauke kai
Shi kuma murmushi yayi yace, "Let's go and sit down." Sannan yayi gaba
Hakan yasa ta taka tabi bayan shi kamar an tsamo ta a ruwa coz yanda take tafiyar. Slowly she sat down in the chair looking at him, sai ta haɗa hannayen ta a saman cinyoyin ta ta dunƙule su wuri ɗaya tana sauraron bugun zuciyar ta da sauyin yanayin da ke baƙuntan ta
Shiru ne ya biyo bayan zaman nata. Shi kansa be san ta ina zai fara ba shiyasa kawai ya kafa mata ido yana kallon ta, sai da ya ɗau kamar mintuna biyar yana mulmula baki da tunanin ta inda zai fara kafin ya ɗan ja numfashi yana sake tsayar da idanun sa ƙyam a kanta ya soma kiran sunan ta
Hakan yasa ta ɗago dara-daran idanuwan ta ta sauke a kanshi wanda fuskar ta har ta soma tsatstsafo da zufa sakamakon halin da take a ciki
"I know you will be surprised to come to your place even though I know your Uncle has informed you." Sai ya sake jan numfashi ya ci gaba da faɗin, "MEEMA is nothing come to you but a word of love. I am currently in love with you That's why I let you know. I hope you will be the mother of my children if you don't mind." Still sai ya kira sunan ta
Kiran sunan ta da yayi a ƙarshen maganar nasa yasa ta lumshe idanuwan ta tana sake tamke hannun ta sosai
"I love you MEEMA! please trust me As your beloved please."
Sosai maganar nasa ya shige ta har cikin zuciya, sai dai ta kasa ko motsin kirki domin har zuciyar ta ta dena aiki a halin yanzu, maganganun nasa kaɗai ke kai kawo a cikin kunnuwan ta suna sake mata yawo tamkar yana sake maimaita mata. Bata san sanda ya iso gaban ta ba sai kawai ganin shi tayi durƙushe a gefen ta. Da sauri ta ɗaga kai ta zuba masa idanun ta wanda hakan yasa suka shige cikin nashi. Kasa ɗauke kai tayi domin yanda take jin wani baƙon yanayi na shigan ta sabida haɗa idanun da suka yi
Karantan yanayin ta yake yi na ɗan soconni kafin yace, "I want to hear your answer if there is no concern please."
Tsit tayi ta ƙi yin magana domin bata san me zata ce ba
"Okay I'll give you time to think, but you know I'm a big man I need your answer in a little while because I hope soon we will be husband and wife." Sai ya tashi tsaye yana tusa hannayen shi a aljihun wandon shi. Kamar zai yi magana a yanda ya kafa mata idanun shi, sai kuma ya fuszar da iska ya juya ya ɗan yi taku biyu kafin ya kalle ta yace, "I will go, good bye." Sannan ya juya ya fice.
Ta kasa motsa wa a wurin tun fitan nashi. Idanun ta kawai ke motsi a jikin ta, sosai ta shiga wani yanayi da bayyana mata kalaman soyayya da yayi, ba wai don bata saba ji ba, hasali ma baza ta iya cewa kai tsaye ba ta ƙaunar shi ba sabida abubuwan da take ji a game dashi, amma kuma tana da wanda zuciyar ta take ƙauna har yanzu, "ISHAQ." zuciyarta ta furta mata. Har yanzu shi ne a zuciyar ta, tana son shi matuƙa kuma shi take da burin ta aura, but bata san meyasa ba tana jin wani irin shauƙi tare da marari a zuciyar ta wanda take ji tamkar shi ne ya fi dacewa da ita, bata san meyasa ya tsaya mata a rai ba musamman yanzu da ya gama bayyana mata abun da take ji kamar tana buƙatar jin sa a bakin sa. Yanda zuciyar ta take bugawa a halin yanzu sabida tunanin da suka cinkushe mata yasa ta tashi da sauri ta nufi ƙasa ta shige ɗakin ta. Kan gado ta faɗa tana mayar da idanun ta ruf ta rufe. Ta jima a haka bata sake yin motsi ba kuma bata ba wa zuciyar ta damar yin wani tunani ba, har sanda Uncle Hashim ya shigo ɗakin bayan Nocking ɗin da yayi mata. Tashi tayi zaune tana kallon sa
Shi kuma ya zo ya zauna a gefen ta kana yace, "MEEMA I want to talk about something understands." Sai ya saka hannu ya kamo hannayen ta biyu ya haɗa da nashi. Cikin ido yake kallon ta yace, "I know you heard what my friend brought to you. He loves you very much and wants to marry you. What did you say?"
Shiru tayi tana sauke kai ƙasa
Sai ya saka hannu ya kamo fuskar nata ta yanda zata sake facing ɗin shi yace, "Tell me. Do you like him? I want an answer from your mouth."
Nan ma she kept quiet because she had nothing to say
Sai yace, "MEEMA let me know what's on your mind, no one will restrict you ok? Do you like my Friend?"
"Uncle, I have the one I want.." she said calmly.
"Who is he?" Ya katse mata maganar yana kallon ta
"ISHAQ. I still love Ishaq very much. But I still haven't got his phone, every time I call But his phone did not ring." Sai ga hawaye sun soma zubowa a fuskar ta, nan da nan ta soma shashsheƙan kuka
Mamaki ne ya kama shi, sai ya riƙo kafaɗun ta yace, "Why you crying Daughter? What happened to you? Or because you can't find him on the phone?"
Girgiza kanta tayi, sai kuma ta kwanto da kanta a jikin sa cikin shashsheƙan kukan da a yanzu ya ƙaru tace, "Uncle I love him but I know he broke up with me."
Kasa magana yayi illa shafa mata kafaɗa da yake yi alamun rarrashi. Can sai ya ɗago kanta yana kallon ta yace, "Now you don't like my friend but Ishaq?"
Shiru tayi tana runtse idanun ta
Shi kuma sai ya bi cuty face ɗin ta da kallo a ransa yana nazartan yanayin ta, tabbas idan ba hasashe yake ba he sees his friend's love in her eyes amma kuma tana son dannewa sabida wani. Don haka dole ya san abun yi bazai bari abokin shi ya rasa ta ba, sun fi dace wa da juna koda be san wancan ba. Hannayen ta da ya saki ya sake riƙo wa yanzu tare da kiran sunan ta
Sai ta buɗe idanun ta da suka soma sanja kala ta zuba mishi
"Tell me about your boyfriend. What do you have in common? Did you fight?"
Sai da ta ja majina kafin ta buɗe baki a cikin raunin murya tace, "I started to break up with him, but when I came to this country I told him to follow me and ask to marry me, but since I came I have not got his number again, I informed my friend to go home and check on him.." sai ta tsagaita sabida yanda muryan ta ya harɗe sakamakon shashsheƙan da take yi. Kana taci gaba da faɗin, "but he refused to listen to her. He refused to let them speak."
"MEEMA raise your head and look at me".
Babu musu ta ɗago kanta tana kallon shi
"I will tell you the truth now that he is separated from you, he cannot follow you here and marry you, you also know the truth, forget him. keep my friend as your life partner, he loves you. Umar Farouk is very kind has a good attitude, He was once married but his wife died, and she bore him two children Hafsah and Yusra, he loved them very much, and now he lives with his father's wife and children in their house. I promise you you will be happy, he will take care of you." Sai ya sake kiran sunan ta a hankali, be bari ta amsa ba yaci gaba da cewa, "my daughter. Please accept my friend's love. Please allow him to show you his love for you. If you do not like him you may part with him in the future, but now I beg you give him a chance ok?"
Kanta ta jinjina mishi a hankali hawayen cikin idanun ta suna sake zubo wa
Sai ya saka hannu ya ɗauke mata yana murmushi yace, "Why are you crying Daughter? Because my friend told you he loves you is because you're all in trouble?"
Fuskar ta ta kwaɓe a yanzu ɗin tana shirin yin kuka tace, "laà Uncle."
"To what's wrong?"
Shiru tayi masa tana sauke kai ƙasa
Sai ya ɗaura hannun sa ɗaya a kanta yace, "I give him your Number you will always look for him. Let me go." Sai ya mike ya fice ya barta a wurin ko motsin kirki ta gaza yi.
💎💎💎
0 comments:
Post a Comment