*1*
~~~ *C* ikin dimuwa,damuwa da tashin hankali mai tsanani yasake damke hannayenta dake cikin nashi wani irin gumi na keto masa tamkar anyi masa b'arin ruwa aka, idanuwanshi jajur suke sannan kuma sun kankance mutuka,
Anata bangaren itama hakan take domin inbanda hawaye babu abinda take fitarwa, kwalla ce ke ta faman tsiyaya daga cikin kwayar idanuwanta,
"Wai wannan wanne irin shashanci ne haka....? Kai balarabe bazaka kyaleta ayi maza aje ayi mata aikin nan da za ayi mata ba?" Muryar wata yar dattijuwa ya karade wurin da suke, tamkar ansake fama masa wani Miki dake tare dashi haka yayi domin rikon da yayi mata yanzu har yaso yafi na dazu, cikin jarumta da dauriya gamida juriya irinta maza yayi mata wani basaraken murmushi mai tafiya da hankalin duk wata ya mace, cikin karfin hali da kokarinsa na hadiye kukan dake gab da balle masa ya saka kwayar idanuwanshi cikin nata sannan cikin sanyin muryarshi wadda ta hadu da yanayi na tashin hankali da yake cikin yace,
"Is ok my heart.....daina wannan kukan haka,insha Allah zaki shiga lafiya sannan zaki fito lafiya domin kullum addu'ar da nake yimiki kenan.... Allah yayi miki albarka yar aljannah insha Allah tare zaku fito da kyawawan twins dinmu masu kama dake....."
Kawar da kanta tayi daga kallonshi tana zubar da hawaye,
"Kayya.....kayyah Rabin raina,bana jin zan sake rayuwa dakai acikin duniyar nan....nidai kawai ka yafe min,ka yafe min duk laifin da nayi maka a iya zaman mu sannan koda na mutu to ka sanyawa yaranmu sunan da kayi min alkawarin zaka sanya musu....ina tsananin sonka mijina...."
Bai kai ga buda baki ba yaga ta sake burkicewa ciwon haihuwa yadawo mata sabo fil fiyeda dazu babu bata lokaci ma'aikatan lafiya dake tare dasu sukayi azamar tura gadon da take kwance akai zuwa dakin da za ayi mata aiki wanda har lokacin yana rike da hannunta dukkaninsu suna hawaye amma sai dai shi nasa hawayen azuci yake yi ahaka aka shigar da ita cikin dakin shikuma dan dole yaja burki daga bakin kofa bawai dan yasoba.
Daga wajen da yake tsaye yagagara zama sai faman sintirin kaiwa da komowa yake yi yanata faman hade hannayensa wuri daya yana runtsewa gamida da runruntse idanuwa acikin zuciyarsa kuwa baida addu'ar da ta wuce,
"Ya Allah ka sauki Ramlat lafiya,ya Allah kafito min da abinda ke cikin cikinta lafiya......" Haka yaketa faman fada har tsawon mintuna talatin, Yakumbo mariya tayi tayi dashi akan ya nemi wuri ya zauna amma yakasa tamkar wani sabon soja haka ya dake yanata kaiwa da kawowa,zuwa can yajuya ya kalli wurin da yakumbo mariya ke zaune bayan ya duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunshi wanda ya nuna kimanin karfe 11:30 nadare,cikin sassarfa kamar kazar da kwai ya fashewa aciki yanufi wurin yakumbo mariya,cikin russunawa yace,
"Yakumbo bari naje nayi salla ina dawowa...."
"Ko kaifa,yawwa dan albarka, maza kaje kayi mata addu'a domin ita tafi bukata a wannan lokacin..."
Batare da yasake furta komai ba yajuya yatafi domin zuwa inda zaiyi sallar. Binsa da ido yakumbo mariya tayi tana girgiza kai domin tasan halinsa yawan magana ratataa baya cikin dabi'arshi da tsarinsa bare kuma yau da zuciyarshi ke cikin alhini da tashin hankali, wannan yaro dai ba asan adadin son da yake yiwa Ramlat ba sai shi sai ubangijinsa tunda shine yasan zuciyar kowa.
Tunda yayi alwala yashiga masallaci yake salla wadda yake jimawa cikin kowacce sujjada saida yayi salla raka'a hudu sannan yadaga hannu yayi addu'a bayan ya shafa ya mike a kasalance yana gyara kafar wandon jeans din dake jikinsa,haka kawai yaji ya nemi nutsuwa atare dashi yarasa gashi zuciyarshi tayi wani irin nauyi sai bugawa takeyi da karfi fat fat tamkar zata faso kirjinsa tafito,cikin mawuyacin hali da yanayi yafito daga masallacin yana dafe goshinsa wanda yadauki zafi haka siddan,jan kafarsa yarinka yi wacce tayi masa tsananin nauyi kamar jini irin ya taru dinnan sosai ahaka yanufi wurin da yabaro yakumbo mariya,
Hangota yayi atsaye da alama shi take jira dama cikin sauri ya karasa wurinta,
"Mu'azzam Ramlat ta haihu,anciro yara biyu mace da namiji amma macen bata zo da rai ba sai namijin kadai...."
"Suna ina yanzu yakumbo? Ina ita Ramlat din?"
"Muje ka gansu,Ramlat kuma ba afito da ita ba tukunna har sai nan da wani lokaci..."
Shuru yayi baice komai ba yabi bayanta zuwa inda tashiga,yara kam tubarkalla jajur dasu kamar shi sannan tun daga yanzu zaka gane tsananin kyawun da Allah yayi musu amma ita macen babu rai sai iya namijin kadai keta yan callare callaren kukanshi,
"Allah yasa haka shi yafi alkhairi, Allah ya raya mana namijin....." Yakumbo ta fada tana karbar macen daga hannunshi,
"Amin Yakumbo...."
"Na kira su Zaid insha Allah nan bada jimawa ba zasu karaso...."
Jijjiga kai kawai yayi yafita bayan ya dauki namijin yaganshi. Tun bayan da aka gama yiwa Ramlat aiki har asubah bata farfado ba, karshen tashin hankali kowa dake wurin yashiga musamman ma shi uban gayyar dan dakyar ya iya zuwa yayi sallar asubah yana sallamewa ya fito yadawo wurinsu amma tun daga nesa ya fahimci kamar akwai matsala domin yanda ya hango mutane na rusar kuka sannan wasu sunyi cincirindo sun rufe gadon da Ramlat ke kai,jin kansa kawai yayi yana faman juya masa kamar fanka nan yazube ya fadi awurin,kinkimarsa akayi zuwa emergency domin bashi agajin gaggawa.
Tunda aka kwantar dashi ake faman yimasa karin ruwa wanda ake gaurayawa da wasu allurai aciki,bai tashi bude idonshi ba sai misalin karfe 5 na yamma, Cikin zafin ciwon da yake ciki ya yunkura yatashi duk da jikinsa babu wani sauran karfi,
Zaid ne yanufoshi cikin sauri yana fadin,
"Sannu yaya Khalil....tsaya jikinka babu karfi"
Kallonsa yayi da raunannun idanuwanshi sannan cikin sanyin murya yace,
"Zaid muje gida....kaini inga Ramlat..."
Zaid zaiyi magana suka hada idanuwa yasan babu abinda yayan nasa ya tsana irin gardama, lallabawa sukayi suka nufi gida wato family house dinsu tare da sauran yan uwa wadanda ke tare dasu,
Iske gidan sukayi cike dam da mutane babu masakar tsinke anata karbar gaisuwa,shi dai yasan tafiya kawai yake yi amma bazaice ga inda yake zuwa ba kai daga karshe ma gani yayi ganinshi ya dauke gaba daya saboda yagama tabbatar da cewa Ramlat ta rasu,dakin Zaid aka kaishi can aka cigaba dayi masa kare karen ruwa kowa shi yake tausayawa ganin halin da yashiga domin har yafi iyayen Ramlat din shiga rudu da dimuwa,duk wanda yazo gaisuwa idan najikine sai yashiga ya dubashi shi baima san inda yakeba.
Bayan kwana uku da rasuwar Ramlat ya farfado yasamu kansa hankalinsa yadawo gareshi tun da yabude ido kuma yake kuka kamar wani karamin yaro,kowa shi yake bawa hakuri amma angagara gane kansa, hajiya Raihan mahaifiyar Ramlat tare da Alhaji Tamim maihaifin Ramlat shiga wurinsa sukayi suna bashi baki tare da yimasa nasiha amma duk abanza,daga karshe yayan mahaifiyarsa wanda suke kira da Abban London shine yashiga wurinshi ya zauna gefensa cikin nasiha yace,
"Ibrahim kayi hakuri ka rungumi k'addara domin kowa da kagani na haka ne,kayiwa Ramlat addu'ar samun rahamar ubangiji sannan kayi hakuri domin duk abinda Allah yayi akan bayinsa to shine daidai....ba aja da hukuncin ubangiji,idan kaci gaba da irin haka to Allah zai iya yin fushi dakai domin baka karbi k'addara ba ko kamanta Allah yakan jarrabemu da rayuka? Yau ina mahaifinka? Ni ina nawa mahaifan? Mahaifinka ma ya mutu kuma kayi hakuri to meyasa yanzu zaka gaza? Dan Allah kadaina duk wadannan abubuwan ka daure kayita addu'a insha Allah zaka samu madadinta koma wacce tafita....."
Tunda Abban London yasoma maganar bai kalleshi ba sai lokacin jin yace wai zai samu madadin Ramlat koma wacce tafita,tab ina ai shikam yasan bazai taba samun ko kwatankwacin rabinta ba shiyasa ma shida aure yanzu haihata haihata sai dai yaga anayi amma yagama aure aduniya idan yamutu yaje lahira sa hadu da Ramlat dinsa su cigaba da rayuwar aurensu a aljannah,
Har Abban London yagama nasiharsa yafita baima saniba kasancewar yafada kogin tunanin da yasaba. Ganin al'amarin nasa bamai sauki bane yasa hajiya Zaitun mahaifiyarshi sanya limamin dake jansu salla agidan yimasa taimako koda na addu'o'i ne dama kuma babu laifi nasihar Abban London ta dan shigeshi domin har ansamu ya fito daga dakin Zaid yaje wurin jaririnshi dan kimanin kwanaki biyar daukar jaririn yayi yai masa huduba yana fitar da kwalla,
"Menene sunanshi...?" Babbar yayarshi wato anty saudat ta bukata,
"Sulaiman Aryan..."
Daga haka yamika mata shi yatashi yafita,makabarta yasaka Zaid ya rakashi ya nuna masa kabarin Ramlat tun daga wannan lokaci kuma yasamu wurin zuwa sai yaje yasaka kabarin agaba yayita kuka har akayi sadakar bakwai gashi ba ci ba sha sai idan an takura masa hajiya tazo da kanta sannan zai yarda yasha ruwan tea amma rabon da yasakawa cikinsa abinci har yamanta.
Yauma saida yajima agaban kabarin yana rusar kuka kamar daga sama yaji andafashi ta baya cikin hawaye yajuya,wani mutum yagani tsaye dan dattijo dashi cikin taushin murya dattijon yace,
"Kayi hakuri bawan Allah....ka dauki k'addara wannan kukan da kake zuwa kullum kanayi ba mafita bace mafita guda daya ce itace addu'a...."
Gyada kanshi yayi ya goge hawayensa yana furta "nagode....nagode"
Juyawar da zaiyi yaga wayam babu dattijon nan babu alamarsa, addu'a yayiwa Ramlat sannan yamike yana fadin,
"Insha Allah zaki zama abar tunawa acikin zuciyata akoda yaushe Ramlat....bazan manta dakeba da yardar Allah, Allah yasa kina aljannah kina hutawa kin manta da wahalar rayuwar duniya...."
Motarshi yanufa yabude yashiga yanufi gida,duk mutane sun tattafi sai wadanda ba arasa ba wato na jiki jiki,yana yin parking masu tsaronsa dake zaune acan gefe suka mike suka nufoshi domin a yan kwanakin nan yahanasu binsa shi kadai yake zuwa kabarin Ramlat,
Falon hajiya Zaitun ya nufa amma sai karar jiniyar motocin gwamnati suka cika gidan da ma unguwar gaba daya hakan ya tabbatar masa da cewa mai girma gwamna ne yazo yimasa ta'aziya,
Fita yayi yaje ya taryeshi yashigar dashi zuwa dakin saukar baki nan yayi masa ta'aziya sannan ya bukaci ganin jaririn da marigayiyar tabari, Zaid ne ya dsukoshi yakawoshi wurin mai girma gwamna nan ya karbeshi yayi masa addu'a sannan yabada shi yayi musu sallama yatafi bayan ya ajiye kudi daruruwa. Cikin gida yashiga bayan tafiyar mai girma gwamna,zazzaune yasamu kowa afalo ana yin sallama da iyayen Ramlat wadanda zasu bar gombe ayau zasu nufi gida wato jos,da alama kuma dama shi kadai ake jira,
Zama yayi a kasa kusa ba Abban London wanda ke sanye cikin kayan gida amma na sarauta sai dai yau babu jibga jibgan rigunan nan da yasaba sawa shiyasa yafito a siririnsa,
"Ibrahim Allah yakara mana hakurin jure rashin Ramlat yakuma raya abinda tabari,mu zamuje mu tafi amma zamu tafi da jaririn sai mu kula dashi awurinmu....." Alhaji Tamim maihaifin Ramlat yafada yana kallonshi,
"A'a Abba ina neman alfarmar ku kubar min yarona zan rikeshi awurina insha Allah kuma zan rinka kawo muku shi kuna ganinsa...."
"To shikenan hakanma babu aibu fatanmu dai Allah ya rayashi"
Kowa dake wurin da Amin ya amsa,
"To yanzu waye zai shayar dashi? Sai kabawa Humaida ko Lubnah tunda sune suke shayarwa...." Inji anty saudat,
Ai shi sai lokacin ma yatuna da batun shayarwa shi baida ra'ayin kowa ya shayar masa da yaronshi madara zai rinka bashi,
"A'a madara zai rinka sha..." Yafada atakaice sannan cikin sauri yasake kallon anty saudat,
"Da wata cikinsu ta shayar dashi?"
"Babu wadda ta shayar dashi madara ake bashi dama ana sone asanar dakai first sai wata cikinsu ta daukeshi"
"Basai andaukeshi ba abar min shi ni zan kula dashi"
"Kai ina ka taba jin namiji yakula da jariri? Kanada nonon da zaka bashi ne? Wadannan da akace kabawa wata cikinsu ba yan uwanka bane uwa daya uba daya ba?" Yakumbo mariya tafada cikin fada,shiru yayi baice komai ba amma shikam harga Allah bazai iya bawa wani rainon yaronshi ba shine zai kula da kayansa,
"Tunda kai ba mace bane tofa ya zama dole kabawa wata cikin yan uwanka ko yan uwan matarka akula da shi...." Yakumbo mariya tasake fada tana kallonsa,
Idonshi rau rau cikin rawar murya yace,
"Yakumbo kuyi hakuri karku rabani da Aryan bazan iya jurewa ba na rokeku da girman Allah kubar min shi..."
Yakumbo mariya ta bude baki kenan zata sake magana Abban London yayi gyaran murya yace,
"Ya isa haka tunda hakan yake so to muyi masa yadda yake so din ina ganin zaifi,Allah yaraya mana shi mudai shine fatanmu....."
Gaba daya akan hakan aka tafi,aranar yaje babban store ya lodo duk wani abu wanda jariri ke bukata,madara kuwa yasiyota tafi gaban abinda tafi,umma barira k'anwar abbansu yadauka ta dawo family house dinsu gaba daya da zama tana tayashi kula da Aryan dayake ita din ahalin yanzu bata da aure kuma duk yaranta sun manyanta dama guda uku ne,shine da kansa ke yiwa Aryan wanka ya shiryashi yabashi abinci duk wani abu na kula da jariri ya iya ahalin yanzu kamar dama can yajima yanayi,indai kaga umma barira tayiwa Aryan wanka ko tsarki ko wani abu mai kamada haka to Khalil baya nan amma indai yana nan shine ke yimasa komai gaba daya rayuwarsa yanzu ta ta'allaka ne akan kula da Aryan ko aikinsa yar sama sama yake yimasa cikin haka har Aryan din yacika shekara daya nan kuma su yakumbo mariya suka sakashi agaba da maganar lallai lallai lokacin da zaiyi aure kuma yayi domin bazai yuyu yayita zama babu mace ba,duk lokacin da suka yi masa irin wannan maganar tayar masa da hankali sukeyi yayita kuka har takaishi da kwanciya a asibiti,daga karshe suka yanke shawarar hadashi aure da kanwar matarshi margiyaya mai suna zulaiha amma fafur yaki aminta wai shi bazai iya auren kanwar Ramlat ba yana jin kunyarta koda bata raye daga karshe dai sai hakura sukayi suka zubawa sarautar Allah Ido suka cigaba da rakashi da addu'a domin duk wadda aka samo masa akan za ahadasu aure baya yarda idan kuma ance yasamo da kansa sai yace shi baida wannan lokacin haka dai suka kyaleshi suna tayashi da addu'a.
***
BAYAN SHEKARA SHIDA.............鉁嶏笍
*_Ummi Shatu_*馃憣馃徎
: 漏锔? *HASKE WRITERS ASSOCIATION.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*D'AND'ANO....*
*MIJIN MATACCIYA....*馃挒
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
WATTPAD:-ummishatu
亘爻賲 丕賱賱賴 丕賱乇丨賲賳 丕賱乇丨賷賲.
*3*
Washe gari
**
~~~Tunda yafara tafiya akan titi kowannensu yayi shiru babu wanda yayi magana har saida sukayi tafiya mai nisa sannan ya dan kalleta inda take zaune agefen kujerarshi hannunta rike da wayarta tana dubawa,
"Hanan.... Bakice komai ba fa kinyi shiru kin barni da nazari....."
"Ai nayi magana mujahid kawai dai baka ji dadinta bane,nafada maka kayi hakuri ka jira nagama service dina sai ka turo iyayenka,to inma banda abinka kai da kayi hakurin shekara da shekaru ai bana tunanin hakurin shekara daya zai zame maka damuwa, wallahi insha Allah kamar yaune zamu yi aure......"
Dan sassauta gudun da yake yi yayi sannan ya kalleta cikin sanyin jiki,
"Wallahi ni gani nakeyi kamar baza muyi auren nan ba hanan shiyasa kika ga duk hankali na yatashi....."
"Hmm kajika da wata magana kuma.... Dan Allah kadaina wannan maganar"
"Shikenan nadaina"
Da wannan maganar yana ta faman nanata ta suka isa unguwar kurna gidan anty salaha wato babbar yayar su Hanan,saida Hanan ta shigar da mujahid suka gaisa sannan yayi musu sallama yatafi amma da yamma zai sake dawowa ya dauki Hanan. Agidan anty salaha dinma dai maganar guda daya ce shine ta tafiya service wuni sukayi suna wannan hirar har lokacin tafiyar Hanan yayi nan ta kira mujahid yazo ya dauke ta anty salaha nata fadan wai karfi da yaji ta maida mujahid driver dariya Hanan tayi tace wai ai dama namiji bawan matane idan bai kyautata mata ba tunda yana sonta har sai yaushe?,haka dai suka karasa gida cikin farin ciki da kaunar juna bayan mujahid ya dan yimata siyayya ahanya. Acikin yan kwanakin Hanan tagama hada komai nata da take bukata kullum cikin lissafi take su shamsu na tayata ai kuwa aranar da akayi posting ta duba dash board dinta nan taga ankaita Abuja tsalle ta daka sannan ta dire tana fadin "yes" murna kamar zata taka rawa nan ta soma kiran yan ajinsu wadanda suke mutunci tana tambayar inda aka kaisu sai dai fin rabi duk sunansu bai samu fitowa ba yanzu sai zuwa batch na gaba wadanda sunan nasu kuma yafito duk wasu garuruwan aka turasu ita kadai aka tura Abuja sai ko wasu yan department din wadanda bama lallai ta sansu ba. Aranar da za ashiga camp din aranar ta shirya ta tafi,da tare da shamsu zasu tafi zai rakata amma ganin Abuja ne yasa aka barta ta tafi ita daya shamsu sai tsokanarta yake yi yana cemata gaskiya ba karamar sa'a tayiba domin Abuja special posting ake turawa can ba kowa ake kaiwa ba amma fi tura yaran manya wurin,ita dai yau baki har kunne zata tafi camp,wata dirkekiyar trolley ta tafi da ita wadda ta hade gaba daya kayanta aciki amma sauran abubuwan bukata kamarsu bokitin wanka da makamantansu tace sai taje can zata sissiya,har tasha shamsu ya rakata yasata a motar Abuja direct sannan yatafi, mujahid kuwa daga can inda yake wato jahar yobe yakirata awaya yafi sau 30 acewarsa shi da yasan cewa ita daya zata tafi da baiyi tafiyar nanba da yajira yarakata, murmushi tayi tace masa babu matsala insha Allah zata kular masa da kanta.
***
Tunda yadawo daga makaranta ya hakimce akan kujera yana ta faman buga tv game dinshi umma barira tayi kiransa har ta gaji yaki tashi suje tayi masa wanka tabashi abinci yaci,
D'an turo baki yayi lokacin da umma bariran ta shigo takai hannu ta kashe game din da yake yi,
"Ka tashi muje kaci abinci nace ko,ga David can tun d'azu yagama hada abinci amma inata kiranka kayi kunnen uwar shegu....."
Shure shure yafara yi zaiyi kuka ganin ta kashe masa game dinsa,zama tayi akusa dashi sannan cikin fara'a tace,
"Yawwa yaron babanshi,maza tashi muje kaci abincin kafin abbanka yadawo yakaika unguwar ko?"
Daga kai yayi yana dariya,
"Umma Daddy ai zai siya min doki ko?"
"Ehh zai siya maka duk wanda kake so"
Makalkaleta yayi ta daukeshi suka fita zuwa dining area wanda ke hade da kitchen dinsu,kan kujera ya haye umma barira ta zuba masa abinci tabashi abaki sannan ta daukeshi zuwa dakinshi tayi masa wanka bayan ta shiryashi ne Khalil yakira waya nan suka lalace wurin hira shida Aryan tamkar sun shekara basu ga juna ba sai surutu Aryan din keyi masa shi kuma yana biyeshi dakyar umma barira ta sa Khalil ya katse wayar shi kuma dan rigimar tata nan ya kwanta yafara bacci.
***
Tunda tagama registration tasaka white take faman daukar hotuna wadanda tayisu sunfi guda 50 wani ita daya wani kuma itada sabbin kawayen da tayi wato Khadija da hajara,tun lokacin da tafara hotunan take ta turawa shamsu da mujahid, kayan kam ba karamin karbarta suka yi ba dan duk inda ta gifta sai kaji ana cewa "yarinya mai kyau", dan hijabin dake jikinta iya kafadarta ne baida girma sosai sai farar t shirt ta kamfanin Polo da farin wando wanda ya tsaya iya kwaurinta tasaka farar safa da farin combos sannan ga yar karamar jaka daure a kugunta. Ba kadan ba tayi mutukar kyau wanda har ita da kanta ta shaida hakan.
Tun shigarta camp bata taba karbar abincin da ake rabawa aciki ba maami market take shiga ita da su khadija suje suci abinda suke so su biya kudi,gashi ta samu wani guy ya makale mata wai shi Ashraf wanda ko ba afada mata ba tasan dan masu ido da kwalli ne kai kusan ma yaran dake camp din duk yayan masu fada aji ne dan sai yanzu take gasgata maganar da yaya shamsu yafada mata cewar special posting ake turawa camp din Abuja,
Tana son ta shiga parade domin yana burgeta amma Ashraf ya hana ta sai hakura tayi,haka zai jata zuwa maami market yayita kashe mata kudi itada friends dinta,gaskiya taji dadin zaman camp dinnan da tayi domin tayi shi ne cikin walwala da jin dadi babu abinda take yi sai dai taci abinci ko wankin kayanta biya take yi awanke mata baya ga cin abinci babu abinda take yi koda yaushe tana clinic ita da Ashraf suna hirar duniya, ranar da akayi canival day kuwa aranar tasan Ashraf ya danganci sarauta domin shigar yayan sarauta yayi,ita kam kayanta na hausawa ta saka ita da kawayenta atamfa dinkin riga da skirt harda mayafi ranar ma sunsha hotona kamar babu gobe. Saida suka yi sabo da mutane sosai acikin satin ukun da sukayi a camp,ranar talata suka fita inda aka tutturasu duk guraben da yakamata,abin haushi duk cikinsu kowa inda aka turashi daban amma duk da haka sun yanke hukuncin cewa zasu zauna awuri daya ita da su Khadija wato a corpers lodge din da aka tanada musamman dan yan kano,
Haushi kamar ya kasheta lokacin da taga wai makaranta aka turata su kuma su hajara duk ministries aka kaisu, Ashraf kuwa mutuminta yana babbar fada domin shi dama sai da ya zabi inda yake so sannan ya gayawa babanshi kuma can din aka kaishi,
Su hajara nata tsokanarta suna kiranta da malama ta shirya ta nufi makarantar domin yin report,tun acikin taxi take faman mita acikin ranta domin gaskiya Abuja akwai tsadar rayuwa yanzu daga inda mai taxi ya daukota zuwa makarantar da zai kaita yace sai tabashi dari bakwai wai da dan nisa ita dai duk abinnan yafara damunta gaskiya ba zata iya wannan tsadar rayuwar ba idan taga babu haza itama redeploy zata yi. Lokacin da taje makarantar yar kauye ta zama domin bata taba ganin hadaddiyar makaranta makamanciyar wannan ba a tarihin rayuwarta, makarantar ta hadu ta tsaru fiye da hasashen mai karatu,gata tana da girman gaske gashi ta kawatu ta ko ina kamar a k'asar turai gaskiya wannan makarantar ko shakka babu zata yi tsada domin taci kudinta,
Tana tafe tana sake yaba kyawu da tsarin makarantar acikin zuciyarta,a k'asa take tafiya saboda mai taxi din da ya kawota tun daga gate suka rabu,taji dadin ganin wasu mutum biyu sanye da kayan hidimar k'asa irin nata domin itanma sanye take da uniform dinta riga mai tambarin NYSC da wandonta sai farin hijabi marar girma yayinda ta daura rigar jacket din a kugunta sannan tasha farar safa da farin takalmi wato dai ta zama fully kitted gwadas da ita gwanin ban sha'awa dan kayan sun sake fito da ita sosai. Su ukune kacal yan hidimar k'asar da makarantar ta nema da kanta aturo mata su saboda tana da bukatarsu kamar yadda aka saba,suna zaune itada sauran corpers din su uku suna dan tattauna rayuwar camp wanda ke da alhakin karbarsu yafito daga office din principal yana basu hakuri akan bata musu lokacin da ya danyi,
Kamar daga sama tana tsaka da bincika handbag dinta domin ciro biro da kuma posting letter dinta taji an rungumeta ta baya juyawar da zatayi taga wani kyakkyawan yaro mai mutukar kyau da daukar hankali,
"Momy.... momy uncle yace min kin mutu.... Momy dama baki mutu ba? Kizo muje wurin daddy...."
Daure mata kai maganganun yaron sukayi wanda har saida ta sake kura masa ido ta kalleshi,farine sol yaron sanye cikin uniform dinshi tsaftacacce yasha stocking ga suma akanshi antaje masa ita tayi kyau gwanin burgewa,tana kokarin yi masa magana chioma taja hannunta sakamakon kiran da senior master yayi musu nan ta wuce office din senior master batare da ta kara bi ta kan yaronba,yana kokarin binta shi kuma principal yafito nan ya rakashi class da kanshi............鉁嶏笍
*_Ummi Shatu_*馃憣馃徎
漏锔? *HASKE WRITERS ASSOCIATION.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*D'AND'ANO.....*
*MIJIN MATACCIYA...!*馃挒馃挒
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Wattpad:-ummishatu*
亘爻賲 丕賱賱賴 丕賱乇丨賲賳 丕賱乇丨賷賲.
_*Har yanzu yan shidan haske masu dauke da fararen alqaluma na cigaba da kawo muku hazikan littattafai guda shida reras masu dumi da sanyi wadanda suka hadar da Gidan rina,hayatuddin,izzata,Da ciwo a zuciyata,tana k'asa tana dabo da kuma Burin zuciya ta,bugu da kari zaku samu wadannan dadadan labaran akan farashi mai sauki daidai da aljihunku naira 500 kacal,burin haske akoda yaushe shine ta saku dariya,maza garzaya ki nemi naki domin da abaka labari ai gara ka bayar,haske maganin duhu.*_
*4*
~~~Koda tafito daga office din senior master bayan yagama accepting dinsu bata ga wannan yaron ba na dazu amma kuma maganganun yaron nata kai kawo acikin kwakwalwarta musamman ma maganar da yayi da yanda yazo ya riketa kamar dama can yasanta,
Da tunanin yaron da bata san ko waye ba tabar makarantar ta nufi zonal office domin taje tayi documentation zuwa gobe kuma sai ta nufi gida kanon dabo domin anbasu hutun sati biyu kowa yaje gida ya kintso sai yadawo da shirin zama,duk da bata son koyarwa kuma bata sha'awarta amma wannan kam tana jin zataji dadin aiki dasu domin makarantar ta azo agani ce kuma class biyu kacal aka bata wato JSS 2 da JSS 3 inda zata rinka koyar dasu darasin turanci dama abinda ta karanta kenan wato BSC English.
Aranar ta gama harhada kayanta domin da safe sammako take son yi zuwa gida bata son takai rana ahanya,mujahid kuwa kamar sun shekara basu ga juna ba yadda yabi ya rikice mata ya dameta da waya ba dare ba rana yana tambayar yaushe zata tafi idan babu dama shifa sai yazo da kanshi dan yaganta. Sassafe ta fita ta samu taxi yakaita tasha inda zata shiga motar kano kuma cikin nasara tana zuwa motar ta cika dama mutum daya ake jira babu bata lokaci suka dauki hanyar kanon dabo tumbin giwa.
***
A guje yashiga cikin babban falon gidan yana kiran "Daddy.... Uncle..... Papa..."
"Kai Aryan menene haka kake gudu sai ka yanke jiki ka fadi ko?..."
"Umma Ina Daddy na?"
Dariya umma barira tayi ta mika hannu ta jawoshi jikinta,
"Banda abinka dan jikalle na ina zaka samu ganin babanka yanzu? Tun fa kafin ka tashi daga bacci yafita yace zaije waccan kasar arnan ni banma rike sunan garin ba,ai ko zai shigo gidan nan to ba yanzu ba...., Maza muje acire kaya ayi wanka azo aci abinci ayi shirin islamiyya malam yana nan zuwa"
Bata fuska yayi kamar zai saka kuka jin abinda umma barira tace,shi Daddyn sa yake son gani,shi yake son fadawa abinda yagani yau,da gudu ya shige dakinsa ya dauki kantamemiyar wayarshi ya zauna akan gado yana neman layin baban nashi amma bai samu ba ahaka umma barira tazo ta iskeshi nan ta karbe wayar ta ajiye asama sannan tajashi zuwa toilet tayi masa wanka ta shiryashi sai rakwarkwabe fuska yake yi irin baya so dinnan.
Misalin karfe 1 na dare ya shigo gidan tare da mukarrabansa, direct sashensa yashiga yayi wanka yasaka kayan baccinshi masu silbi riga da wando maroon colour,ga abinci nan akan table kala daban daban wanda duk aciki baya jin akwai wanda zai iya ci, da kanshi yashiga kitchen ya hada coffee sannan yafita ya nufi dakin Aryan,
A gefen gadon Aryan din ya zauna yana dan kurbar coffee din dake hannunshi yana yi yana nazarin d'akin,ga littattafai nan acan k'asa kan center carpet da alama home work yayi yagama kuma shine ba adebe littattafan ba yabarsu awurin,
Da kanshi ya tattarasu yasaka masa cikin school bag dinshi sannan yasake komawa gefenshi ya zauna tare da kunna yar karamar fitilar dake girke gefen gadon Aryan wato bedside lamp.
Cikin magagin bacci yaron yafarka ganin Khalil zaune kusa dashi yasashi kokarin tashi zaune,mayar dashi Khalil yayi ya kwantar tare da dan rungumoshi jikinsa cikin sanyin murya yana fadin,
"Koma kayi baccinka Aryan...., Nazo ne inganka dama,yi bacci kaji yaron kirki"
"Daddy naganta yau..... Kace min ta mutu ashe bata mutu ba Allah naganta"
Duk a tunanin Khalil magagin bacci ne yasa Aryan wadannan surutan na shirme shiyasa yayi gaggawar dakatar dashi ta hanyar fadin,
"Shhhhhh,Nace kayi bacci ko? Kar nasake jin bakinka awurin"
Maida idanuwanshi yayi ya rufe yana motsa baki alamun yana son yin magana amma babu damar yi,shafar kanshi Khalil yafara yi tun daga sumarshi har zuwa fuskarshi alamar so da kulawa mintuna kadan yasake komawa bacci,sai da yaga yayi nisa acikin baccin sannan yayi masa addu'a ya shafe masa jikinsa dashi sannan yakashe masa bed side lamp din da ya kunna yatashi ya fita bayan ya lullube shi ya rufe masa kofar dakin,
Bedroom ya wuce direct ya nemi wuri ya zauna saman kujerar dake can girke gefe daya da center table a gabanta,lumshe idanuwanshi yayi take tunanin da yasaba bijiro masa ya fara bijirowa kwakwalwarshi kamar koda yaushe wato tunanin matarshi Ramlat margayiya,
"Allah sarki Ramlat kin tafi kin barmu da kewarki da tunanin ki da kaunarki da kuma begenki da kishirwar ganinki..... Sai dai kash nasan bazan sake ganinki ba sai a darus salam,Allah ya jikanki,yaron mu ma da bai sanki ba kullum cikin mafarkinki da begenki yake...."
Daurewa yayi ya hadiye hawayen dake barazanar zubo masa,ahankali ya jingina da jikin kujerar ya kwanta sannan ya lumshe idanuwanshi yana tunani aranshi. Tsawon mintuna masu yawa ya dauka yana tunanin daga karshe dai ya tashi yashiga bathroom duk zufa ta jikeshi tamkar yana gaban wuta,ruwan sanyi ya sakarwa kansa bayan ya kunna na'urar dake bada ruwa. Ruwa yayita kwararawa kansa sai da yaji dan dama dama sannan yafito bayan ya daura alawala,
Wani kayan yasake sakawa sannan ya tsaya gaban mahaliccinsa kamar yanda yasaba akoda yaushe,sallah yayita yi har karfe 3 na dare tayi sai lokacin ya kwanta bacci amma kuma baccin ya gagreshi sai tunani dake ta addabar ruhinsa daga karshe dai yayi nasara baccin ya daukeshi bashi ya farka ba sai asubah. Bacci yasake komawa bayan yayi sallar asubah,yana cikin bacci yaji Aryan yana tashinsa,
"Daddy kace min mommy na ta mutu kuma jiya naganta a school..... Papa naga mommy jiya katashi kaji..."
Cike da bacci a idonshi ya bude idanuwansa yatashi zaune yana kallon Aryan wanda ke sanye cikin uniform din makaranta sai kamshin turaren silver boy yake yi idanuwanshi sunsha kwalli baki, murmushi Khalil yayi sannan yajawoshi jikinsa ya rungume,
"Good morning lovely son...."
"Daddy naga mommy jiya a...."
"Mu fara gaisawa first sai ka fada min,ko baza ka gaida ni ba yau?"
"No Daddy zan gaida ka, Good morning"
"Morning my love,how was your night? Wa kace kagani jiya?"
"Uncle mommy na mana wadda kake nuna min a hoto har kace min ta mutu lokacin da za a haifeni..."
Dan jimm Khalil yayi yana nazarin maganar da Aryan yafada,lumshe idanuwanshi yayi ya shafi sumar Aryan,
"To naji Aryan...ai idan aka mutu ba a dawowa ita kuma mommy dinka ta mutu"
Bude baki Aryan yayi zai sake magana Khalil ya dakatar dashi sakamakon kaiwar da idonshi yayi kan agogon dake ajiye kan bed side drawer,karfe 7:40 agogon ya nuna,
"Aryan ya isa maza jeka ka tafi school kaga ka kusa makara"
Kiss yayi ma yaron a kumatu sannan ya saukar dashi daga kan gadon yana tambayar shi yaci abinci? Daga masa kai yayi alamar ehh,
"Me kaci?" Yasake tambayarshi yana son kawar da damuwar dake saman fuskar yaron,
"Potatoes smiley & egg muffin"
"Good boy,umma ta hada maka da chocolate ko?"
Kai ya daga masa,kumatunshi yaja sannan ya rakashi ya koma ya kwanta bayan ya rufe kofar d'akin nashi,wani baccin yake son yi amma yasan ba mai yuyuwa bane domin yau yanada commitments da yawa gashi yana son ya je gombe ayau yadawo duk da dama yasaba hakan, hakura da baccin yayi yatashi yayi wanka ya shirya cikin fararen kaya yafita dama already table ashirye yake amma iya ruwan tea kadai ya iya sha yafita yaje ya gaida umma barira daga nan yafita office,a office dinma babu abinda yaci duk da ankawo abinci conference room din nasu,bashi yabar office ba sai 6 na yamma wato dab da magriba,daga can wani uzurin yasake wucewa bai fito ba sai misalin karfe 8 da kusan rabi kai tsaye kuma gobe suka nufa.
Lokacin da yashiga family house dinsu a gombe tuni wasu ma har sunyi bacci agidan amma dai hajiya Zaitun wato mahaifiyar su bata kai ga yin baccin ba hakama sauran yanmatan gidan duk suna tare a falonta suna hira,
Zama yayi agefen yanmatan gidan wato mufida da zarah da Sarah wadanda duk yan riko ne hajiya ke rikesu amma ita Zaid ne dan autanta,
"Mufida ku kawo min abinci inci wallahi rabona da abinci har na manta....."
Tashi suka yi dukansu suka fita ita kuma hajiya tasamu wuri ta zauna tana kallon d'an nata wanda aganinta yanzu duk ya lalace yaki yin kiba amma da ba haka yakeba,
"To ba dole kayita zama da yunwa ba mu'azzam tunda ka ki yin aure ka zabi yin rayuwa kai kadai babu mace... Yanzu da kana da aure yaushe matarka zata barka da yunwa wuni guda..."
Bai kai ga yin magana ba su mufida suka shigo kowaccensu rike da food flask,tuwon shinkafa suka kawo masa miyar taushe sai gasasshen nama da kunun aya mai sanyi wanda yaji kwakwa da madara da dabino sosai,saida yaran suka fita sannan ya kalli hajiya bayan yafara kwasar girkin dake gabansa,
"Wallahi hajiya ba rashin aure ne ke hanani cin abinci ba, lokacin cin abincin ne ma babu kwata kwata, rabona da gida fa tun karfe 8 nasafe ahakanma dan dai ina daurewa ne bana son yin nesa da Aryan amma da wallahi sai inyi kwana biyu banje gidanba...., Ni yanzu ma banida lokacin aurenne gaba daya"
"To koma dai yaya ne ai gara ace kana da matar akan ace babu Khalil,kai kaine babba kuma kana nema ka zama babban kwabo...... Ko tafiye tafiyen k'asashen wajen nan da kake yi acan kake aikata son ranka?"
Cak ya tsaya daga cin abincin da yake yi sannan cikin sanyin murya yace,
"Wallahi tallahi hajiya ni harkokin aikina ke fitar dani waje bawai wani abuba,haba hajiya ai ko dan Ramlat bazan iya aikata mummunan laifi kwatankwacin wannan ba..."
"Nima bance kana aikatawa ba amma dai yadace kayiwa kanka fada,mutum ya radi kansa tun kafin duniya ta radeshi, mutane suna ganin kana da kudi da komai na rayuwa amma baka da mata to gani zasuyi kamar wani abu kake aikatawa agefe..."
"Hajiya wallahi duk lokacin da kika yimin maganar auren nan jinina ne yake hawa saboda bana sonta..."
"Ai shikenan,to Lubnah ta haihu yau da safe ta samu yarta mace,sai ka samu lokaci kaje kayi mata barka"
"To insha Allah, Allah yaraya,zan dawo inyi mata barka idan nasamu lokaci, Ina zaid kuma"
"Ai yatafi Abuja tunda rana,baku hadu bane?"
"Bamu haduba ai rabona da gidan tun 8 nasafe"
Hira ya zauna suka sha da hajiya sosai kai idan ba sani kayi ba sai kace agarin zai kwana,karfe 1 da yan mintuna suka kama hanyar Abuja,
Lokacin da yashiga part dinsa a mutukar wahale yake ga gajiya ga kuma damuwar dake addabar mararsa,cire rigar jikinshi yayi yarage daga shi sai iya singilet da dogon wando,wayarshi ya dauka ya kira number nura PA,mintuna kadan sai ga nuran yashigo,
Cikin mawuyacin hali ya kalli nura, "Nura ina zaka samo min kanwa ko lemon tsami?"
"Ranka yadade kanwa kuma? A wannan daren? Ai yanzu babu inda za asamu kanwa acikin garin Abuja,dama dama lemon tsamin ma"
"Je kasamo min lemon tsamin"
Sake gyara kwanciyar shi yayi bayan nura yafita yana dafe da mararsa wacce ke murda masa wannan yana daya daga cikin dalilin da yasa baya son yaci abinci ya koshi domin duk ranar da ya koshi to sai ahankali.......鉁嶏笍
*_Ummi Shatu_*馃憣馃徎
8/14/20, 10:06 AM - Ummi Tandama: 漏锔? *HASKE WRITERS ASSOCIATION.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*D'AND'ANO....*
*MIJIN MATACCIYA....*馃挒馃挒
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Wattpad:-ummishatu*
亘爻賲 丕賱賱賴 丕賱乇丨賲賳 丕賱乇丨賷賲
*Alqaluma shida daga k'ungiyar haske na nan na cigaba da baje kolin basirarsu cikin farashi mai sauki daidai da aljihunku, akan naira dari biyar kacal zaku samu labarai guda shida cis wadanda suka hadar da Gidan rina, Hayatuddin, Izzata,Burin zuciya,Tana k'asa tana dabo,sai kuma Da ciwo a zuciyata,karku bari abaku labari,burin haske gamsar daku cikin nishadi da farin ciki.*
*5*
~~~*T* amkar zaiyi kuka haka ya zama kwakkwaran motsi yana neman ya gagareshi,yana baje saman Rug din dake shimfide tsakiyar falonshi yana shan sanyayyiyar iskar _air condition_ din da ta wadata falon da sanyi marar karfi wanda bazai cutar da jiki ba,
Juyi yake tayi shi kadai bayan ya tasa kansa da daya daga cikin pillows din dake kan kujerun falon sannan ga wani pillow din guda daya shima ya saka kasan kafafunshi,
Tsaki yaja yakuma karawa, yayi tsaki awurin yafi sau 30 saboda bacin rai,
"Mtswww shima nura yaje ya wani nemi wuri ya zauna kamar an aiki bawa garinsu.....mtsawww duk abinda mutum bazaiyi da kansa ba ai dama wahala gareshi dan sai abinda yagani kawai"
Juyi yayi yakoma kan damtsen hannunshi na dama dayan hannun kuma na kan mararsa,
Ahaka ya kwashe fiyeda mintuna 20 sai lokacin nura yabude kofa yashigo yana fadin,
"Tuba nake yallabai....wallahi ba asamo anan kusa bane amma dai gashi andace"
Tashi zaune yayi dakyar idonshi a lumshe ya karba kawai batare da yace ko uffan ba,
Har nura yajuya zai fita ya dakatar dashi ta hanyar fadin,
"Bani wuka a kitchen...."
"To yallabai" fita nura yayi yashiga kitchen yaje kan kitchen wire ya ciro daya daga cikin wukaken dake jere akai yakoma ya kai masa lokacin kuma yana jingine da jikin kujera sai faman ajiyar numfashi yake yi,
Karbar wukar yayi shi kuma nura yajuya yafita. Lemon tsamin ya yanyanka wurin guda uku take ya matse su abakinsa ya shanye yana mai yamutsa fuska saboda tsami,tamkar abin shiri cikin mintuna kadan yajishi garau ya dawo cikin nutsuwarsa, bedroom dinshi yawuce yaje yayi wanka yasa kayan bacci sannan ya fita zuwa dakin Aryan,shi kadai yasamu yana kwance yana bacci bayan ya gama game domin ga ga game dinnan na tayi ko kashewa baiyi ba, sannan ga text books dinshi nan suma bisa saman gadon,
Sai da ya kintsa masa komai sannan yayi masa kiss a kumatu yafita. Bedroom dinshi ya shiga ya kwanta bayan yayi shafa'i da wutri domin yau kam bacci yakeji da gaske bada wasa ba saboda jiya bai samu bacci ba yanda ya kamata kuma yau da safe ma haka,duk da gobe babu aiki ana yin public holiday amma shi yana da tarin ayyuka wanda dole sai ya fita yaje ya gabatar dasu, pic din Ramlat ya kalla sannan ya kwata ya lumshe idanuwansa bayan yayi addu'ar bacci.
Washe gari da safe asubanci yayi yafita daga gidan tun kafin mutanen gidan su tashi, shiyasa lokacin da Aryan ya tashi kuka yafara yi bayan yaje bedroom din Khalil bai ganshi ba shi ina Daddynshi? Sai da Zaid yafito yayi masa wayo sannan ya hakura daga karshe Zaid din ya daukeshi suka fita tunda yau babu makaranta.
Duk da Khalil ya fadawa Aryan cewa ya daina maganar yaga mommynshi a makaranta ba ita bace ita ta rasu bai hakura ba kullum cikin maganar yake kuma idan yaje makaranta yakan duba gaban staff room wai ko zai ganta, kullum sai yaduba wurin amma bai sake ganinta ba, Khalil kuwa har yagaji da maganar nan gashi da zarar Aryan yayi masa maganar sai yaji damuwar sa da raunin dake cikin zuciyarsa sun dawo sabo fill. Yau ma da suke zaune a falonshi shida Aryan da Zaid Aryan yana game a wayarshi sai yasaka pause yajuya ya kalli Khalil wanda ke magana da zaid yana cewa,
"Ai Zaid mutane ne kadai ke ganin kamar muna jin dadi amma wallahi azahirin gaskiya wahala muke sha,sam fa mutum baida hutu sannan baida lokacin kansa kana gani kai kanka tunda kazo bamu haduba bamu zauna dakai ba sai yau.... Kai ai wannan rayuwa tana da wahala"
"Daddy..... Mommy"
Jin abinda Aryan yafada yasashi juyawa ya kalleshi shi wallahi yasoma gajiya da wannan maganar mommy din domin bata masa rai ma take yi,
"Daddy zamuje da mommy new york?"
"Ban saniba,ba nafada maka idan kagama exams dinka zan kai ka can ba? Kamin shiru da bakinka"
Shiru yayi ya kama bakinshi kamar yadda Khalil yasaba sashi idan ya hanashi surutu sai yasashi ya kama bakinshi.
***
A bangaren Hanan kuwa cike da farin ciki da murna ta isa gida tana ta dokin ganin mutanen gida kamar irin ta shekara dinnan bata gansu ba domin dama ita bata saba yin tafiya taje wani wurin tayi kwanaki ba shiyasa wannan dan sati uku zuwa hudun da tayi take ganin kamar watanni ne tayi batare da taga yan gida ba.
Tun aranar mujahid yazo domin shima cike yake da dokin ganinta,
Kamar yadda ta kawowa kowa dake gidan tsarabar turare shima mujahid haka ta kawo masa turaren secret man,
Tallafe kumatunsa yayi yana kallonsa saboda azahirin gaskiya tayi bala'in kyau domin da alama weather din garin Abuja ta karbi fatar jikinta tayi wani luwai luwai sai sheki take yi tana kyalli,
"Wai yallabai menene ka tisani agaba kana kallona kamar yau kafara ganina?"
Murmushi mujahid yayi sannan ya janye idanuwanshi daga kanta ya mayar kan sitiyarin motarshi,
"Wallahi kinyi kyau ba karya,gaskiya Abuja ta karbeki,ko can zamu zauna ne?"
Yar dariya tayi sannan ta shafi fuskarta,
"Wai haka ma su yaya shamsu suka ce,wai nayi kyau kamar bani ba yar dukununun fatata duk ta haska tayi kyau ashe da gaske ne...."
"Allah dagaske ne kinyi kyau amarya ta kamar irin kin fara cin amarci dinnan..."
"Uhmmm zaka fara ko,kai a kullum baka da magana sai ta aure"
"To bashi ne araina ba? Ai dole intayi miki maganarsa ko zaki ji tausayina ki bani dama"
"To nidai yanzu gobe kazo ka kaini gidan anty salaha inje mu gaisa inbata labarin Abuja"
"Duk yanda kikace haka za ayi da girman kujerarki...."
Cikin sati biyun da tayi a kano ta harhada kayanta jimilla gaba daya wadanda zata tafi dasu sannan ta sissiya wadanda take da bukata,ranar da zata tafi yaya shamsu ne da mujahid suka kaita basu suka baro garin abuja ba sai magriba yayinda ita kuma ta zauna zaman shirya kayanta a daya daga cikin dakunan dake cikin quarters din makarantar domin yanzu tabar Lodge hukumar makarantar bright future tabasu masauki a quarters din malamai wanda ke dauke da komai na more rayuwa,
Wallahi sosai abun ya burgeta kuma yayi mata dadi haba zatayi service a dadi komai yana zuwar mata cikin sauki duk ma dai da term din yakare domin exams za afara to amma yazama dole su kasance suna kusa.
Washe gari ashraf ne ya tadata daga bacci wai zaizo yaganta kafin yabar Abuja,tana fitowa daga wanka yakaraso kaya kadai tasa tafita ta sameshi waje yana jiranta,suna tsaye dashi suna hira motar Khalil tashiga cikin makarantar inda zasu ajiye Aryan sannan yawuce kaduna shida nura PA,duk da ba akusa suke ba ahakan Aryan ya hangota,kama hannun Khalil yayi yace,
"Papa kalli mommy can...."
Khalil bai kulashi ba ya saka hannu cikin aljihunsa ya ciro wayarshi ya soma latse latse har suka ajiye Aryan bai kulashi ba sai babbata rai Aryan din ketayi,
Tun daga ranar walwalar Aryan ta ragu ahaka har suka fara exams ita kuwa Hanan bama sosai take shiga cikin makarantar ba saboda jarabawa akeyi aikin da ake basu kadanne ba wani aiki sukeyi sosai ba amma dai suna yin nasu daidai gwargado,ana yin hutu ta tattara nata inata ta nufi gida kanon dabo.
***
Tunda aka gama exams Aryan ke faman yiwa Khalil rigima akan maganar mommynshi, Aryan irin yaran nanne da basa mantuwa kai sai ma ka manta da abu shi bai manta ba,
Rarrashinsa Khalil yafara yi yana cemasa,
"Kamanta da maganar mommy dinnan kaji yaron kirki,ana yimuku hutu zan kaika Jos kaga yan uwan mommynka sannan zan kaika gombe wurin hajiya ai zakaje ko? Daga nan zan daukeka mu tafi new york inda zaka kare hutunka gaba daya acan,kullum zamu rinka zuwa central park kana shan ice cream...."
Makale kafada Aryan yayi yana turo baki,
"Ni wurin mommy nake so..."
"Kai..... Shut up.....ba na hanaka wannan maganar ba? Get out of here ko in bugeka,marar jin magana"
Tsawar da Khalil yayi masa ce ta razanashi yafita da gudu yaje ya zauna a falo yana kuka abunka da yaran hutu wadanda basu saba ba take temperature din jikinsa ta sauya kansa yafara ciwo shikenan sai numfashi sama sama,
Shi kuma uban na can dakinshi yagama shiryawa zai fita zai tafi kano ta'aziyar baban wani classmate dinshi,duk atunaninshi Aryan na wurin umma barira,har zai fita ta kofar side dinshi sai yafasa domin bai yiwa umma barira sallama ba,
Ta babban falo yabi acan ya hango Aryan sheme saman carpet yana wani irin abu kamar mai iska,kansa yaje ya dagashi duk hankalinsa atashe,baima tsaya ya saurari fitowar umma barira ba yanufi waje dashi,
Asibiti suka kaishi nan aka fara bashi taimakon gaggawa,shidai a iya saninshi Aryan lafiyayyen yarone bashi da wata lalura sai dai ko boyayyiya wacce bata bayyana ba,
Abinda likita yafada masa ne yayi mutukar girgizashi wai zuciyar Aryan yar mitsitsiya ce sannan dole aguji bacin ran shi adaina hanashi abinda yake so,to ai dama Khalil a iya saninshi abinda Aryan yakeso yake masa dan shi ko fada bai yarda wani yayiwa yaronsa ba,
Aranar da daddare aka sallamesu,tunda suka koma gida yaketa nan nan da Aryan ranar ma tare suka kwana,da zarar yayi masa maganar mommy kuwa sai yace ehh zai nemo masa ita duk inda take,abun har mamaki yabashi saboda irin yanda yaga yaron yanata murna yana farin ciki,shima farin cikin yaji ya samu kansa aciki domin farin cikin Aryan shine nasa, Aryan ya cancanci dukkan soyayyar da ta dace daga gareshi domin yarasa mahaifiyar shi a lokacin da yake tsananin buk'atarta baiji dumin jikinta ba haka kuma bai sha ruwan madarar dake fita daga jikinta ba shiyasa yanzu dole ya zame masa uwa kuma uba dole yasamar masa da dukkan farin cikin da yake buk'ata koda kuwa hakan zaisa shi yarasa nasa farin cikin......鉁嶏笍
*_Ummi Shatu_*馃憣馃徎
8/14/20, 10:06 AM - Ummi Tandama: 漏锔? *HASKE WRITERS ASSOCIATION.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*D'AND'ANO.....*
*MIJIN MATACCIYA....*馃挒馃挒
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Wattpad:-ummishatu*
亘爻賲 丕賱賱賴 丕賱乇丨賲賳 丕賱乇丨賷賲
*6*
~~~*R* anar hutu Khalil da kansa yakai Aryan makaranta saboda tunda suka tashi daga bacci yaga alamar da rigima Aryan din yatashi dan sai wani tutturo baki yake yi breakfast ma saida lallami yasamu yaci amma da umma barira tayi tayi dashi ya zauna yaci yaki ci daga k'arshe ta kira Khalil awaya,yana kwance yana bacci yaji karar wayar landline ta cika masa kunne wacce ke ajiye saman drawer din gadonshi,dole tasa yatashi ya daga wayar domin yasan daga cikin gidan ake kiransa ko securities ko wani daga cikin jama'ar dake cikin gidan addu'ar shi dai bata wuce Allah yasa ba baki yayi ba da sanyin safiyar nan domin ko wanka baiyi ba,
Muryar umma barira yaji tana cewa,
"Mu'azzam zo kaji da wannan kinibabben yaron naka dan ni bazan iya ba nayi lallashi har nagaji yaki jin lallashina tunda kai kaine ubansa kila zaiji naka....."
Jin abinda umma barira tace yasashi yin murmushi mai dauke da sauti yasauka daga saman gadon yana kokarin zira silifas dinshi dake ajiye gaban gadon domin tana gama fadar abinda ta fada ta katse layin,
Gaban closet dinshi yaje ya tsaya yacire farar riga armless din dake jikinsa yasaka jallabiya kalar ruwan kasa sannan yafita,
A babban falo yasamesu suna drama umma barira nata tura masa soyayyen dankalin turawa wanda ya wadatu da kwai ga plantain shima agefe da wainar kwai sharba sharba amma yaki ci sannan ga tea dinshi nan a dan karamin cup dinshi,
Umma barira na ganin yashigo ta mike ta nufi cikin falon tabar dining room din tana fadin,
"Khalil wannan yaron naka dan jakar ubane ayita shan kansa amma yana sake botsarewa.....to nidai nayi nawa jeka kaima ka gwada taka sa'ar"
Murmushi Khalil yayi yana kallon Aryan wanda ke zaune saman dining yana ta turo baki,
"Ai ni dama tunda naga har yanzu bai shigo dakina ba nasan da walakin.... Bari naje na bashi abincin....."
Daga haka yawuce wurin Aryan ya zauna akusa dashi sannan ya dagashi ya dora kan cinyarsa,
"Baba na yau kuma abinci ake yiwa yaji? Uhmmm? Yau fa za abaku hutu amma banga kana murna ba.... Kana da kiwar zuwa school Aryan,nifa when i was young kamarka banyi gardamar zuwa makaranta ba..."
"Papa ni bazan ci wannan ba..."
"To me zaka ci? Fada min maza adafa maka kaci ka tafi school ka karbo report card dinka"
"Noodles...."
"To ai mai saukine bari adafa maka within 5 minutes...."
Tashi yayi yafita ya kira kuku nan da nan kafin wani lokaci ya dafa noodles din mai kunshe da vegetables aciki da kifin gwangwani sannan ga soyayyen kwai akai,
Zama yayi yabashi abaki yaci ya koshi sannan yaje ya kaishi da kansa daga nan ya juyo gida domin kamar koda yaushe yauma yana da inda zaije.
Tunda yafita bai samu dawowa ba sai misalin karfe 10 saura na dare yayi mamaki sosai da yaga wai idon Aryan biyu a wannan lokacin baiyi bacci ba,yana ganinshi ya ruga da gudu ya rungumeshi yana rike da report card dinshi a hannu,daukarshi Khalil yayi yana karbar report card din,fuskarshi ce ta fadada da murmushi da fara'a har yakai bakinshi kan goshin Aryan yayi masa kiss,
"Yaron kirki this time around baka yarda suhail ya kwace maka first position din ba?? Kayi kokari,zan yi maka duk abinda kake so kaji...me kake so?"
Kwantar da kanshi yayi jikin kafadar uban sannan ahankali yace,
"Mommy..."
"To Aryan din Daddy..."
Tare dashi sabe a kafadarshi yawuce bedroom dinshi ya ajiye shi saman gado shi kuma ya fara kokarin rage kayan jikinsa.
Bayan yayi wanka yayi shirin bacci yana zaune saman Rug da Aryan kan cinyarsa yana bacci umma barira ta kira waya tana tambayar ko suna tare da Aryan domin ta shiga dakinsa bata ganshi ba kuma baya wurinta,niyyar tsokanarta yayi yace,
"Umma baya wurina ni nan ni kadai ne"
"To sai ku bazama nemansa domin nima baya tare dani"
"Umma kenan kin ganshi nan yana bacci,hira ma muke yi yayi bacci ya barni..."
"Aima yayi kokari da har kadawo ka sameshi ido biyu shida kafin 8 wani lokacin yayi bacci amma yau ya dan taba baccin rana wuni yayi yana bacci inajin shiyasa baiyi na daren da wuri ba"
"Ai nima nayi mamakin ganin idonshi biyu lokacin da na shigo"
"Ina ruwan mai gida"
Katse wayar yayi yana dariya shi bama dan yayiwa Aryan alkawari ba da ya turasu umarah shida umma barira,babu abinda zaice da ita sai godiya domin tana tsananin kaunar gudan jininsa ko ita ta haifeshi sai haka abinda hajiya mahaifiyar shi zatayi masa shi umma barira take yimasa duk tsawon lokacin nan da ta dauka tare dasu shekara da shekaru bazai iya cewa ga laifinta ba kullum cikin tattalinsu shida yaronsa take. Cikin dakinshi yakai Aryan suka kwana tare,bayan kwana biyu da yiwa su Aryan hutun makaranta Khalil yasa umma barira ta shirya kayanta da na Aryan shima ya shirya nasa suka nufi gombe domin shima ya dauki hutu a office,tun da suka je gomben ma bai zauna ba kullum cikin karbar baki yake da yawon gaishe da yan uwa da abokan arziki,duk wasu dangin hajiyarsu da dangin abbansu sai da yaje ya gaidasu tare da yimusu rabon masu gidan rana,kwanansu uku a gombe ya dauki Aryan suka tafi jos wurin iyayen Ramlat,shi a hotel ya sauka bayan yakai Aryan gidansu Ramlat sai dai kullum yana zuwa gidan domin ya duba Aryan,harga Allah yana jin dadin irin yanda ummi kanwar Ramlat ke kula da Aryan sannan duk itace ke wahala da tiriniyar kaishi gidajen yan uwa,har gobe iyayen Ramlat basu daina kwadayin sake hadashi aure da itaba amma shi bazai taba iya auren ta ba da ace zai iya to da ya aureta ko dan kulawar da take yi da dansa. Kwanansu biyu a garin jos daga can suka wuce Calabar babban birnin jahar cross river domin ya fahimci Aryan yana son yaje yaga yan uwanshi wato yaran Khalid cousin dinshi,kwanansu daya da yini daya adaren ranar suka tashi suka nufi babban birnin new york.
Kamar yadda yasaba duk lokacin da suka tafi hutu shida Aryan yakan samu lokaci sosai ya zauna tare da yaron suyi ta hira yana bashi labaru na ban dariya da nishadi da tatsoniyoyi kala daban daban hakan ba karamin sake kara musu shakuwa da sakin jiki da kusanci yake yi da yaron ba, sannan yakan ware musu lokaci a kullum su fita su zaga gari su je wuraren shakatawa da wurin wasannin yara domin debewa Aryan kewa banda shagunan sayar da kayayyaki da yake kaishi ya siyo masa duk abinda yake so. Wannan karon ma hakance ta faru a k'asar new york,duk inda yadace yakai Aryan yakaishi sannan sun samu lokaci sosai wurin kasancewa da juna,sunsha hotuna har sun gaji dama Khalil yakan tafi da yar karamar camera saboda daukar hotunan tarihi,
Satinsu uku sannan suka fara haramar dawowa,saida suka je babban kantin sayar da kaya dake cikin birnin Khalil ya jibgo masa kayan sawa da takalma dan hatta school bag dinshi da combos da sauran kayan sawarshi duk acan yasiyo masa,
Baiyi wata tsaraba mai yawa ba sai yan abubuwan da ba arasa ba ya sissiya daga nan suka nufo gida Nigeria,a Abuja suka sauka dama tun da Khalil yace gobe zasu dawo umma barira ta shirya ta tafi Abuja dan haka can suka tarar da ita,
Daga Aryan tayi ta rungume suna dariya gaba dayansu yana sanye da dark blue din jeans da jar t shirt ta kamfanin polo sai jan takalmi shima na kamfanin polo,yanda yayi wannan shigar shima uban ita yayi sak jeans da t shirt duk irin na Aryan.
Bayan sun dawo sai da sukaje gombe suka gaida hajiya sannan suka juya aranar,ranar Monday Aryan suka koma school shi kuma Khalil yakoma office shikenan yazama busy kullum bashida hutu.
A bangaren Hanan itama ta shirya ta koma Abuja bayan hutu yakare nan kuma akaje aka fara koyar da dalibai babu kama hannun yaro duk sai ta zama busy itama saboda marking din script din dalibai kadai ya isheta shiyasa yanzu bata da lokaci sosai.
Shi kam Khalil Aryan ne ya bi duk ya dameshi da maganar mommy gashi baya samun lokaci sosai amma kullum yaron cikin maganarta yake daga karshe da yagaji sai yatura PA dinsa yace yaje ya binciko masa koma wacece wannan yarinyar da Aryan keta faman magana akanta kullum.
Cikin kwanaki biyu kacal nura yazowa da Khalil amsa lokacin Khalil din yadawo daga bauchi yana dan hutawa acikin falonsa,dan russunawa nura yayi sannan yace,
"Ranka yadade sunanta Sa'adatu mustapha mai jama'a taura,mahaifinta haifaffen garin taura ne,amma yanzu haka suna zaune acikin garin kano a unguwar sabon titi mandawari...."
Dan murmishi Khalil yayi yashafi sumar kanshi sannan yace,
"Ashema 'yarmu ce,to ai ta kwana gidan sauki,nura kana iya tafiya, nagode"
"Nabarka lafiya yallabai" daga haka yajuya yafita, murmushi Khalil yasake yi akaro na biyu yana jin dadi har can cikin kasan ransa zaiyi surprising Aryan,zai kawo masa Mommy har gida ya ajiye masa ita yayita kallonta hakan ita kadaice mafita. Acikin satin yaje har gombe yasamu hajiya da Abban London da maganar ai kuwa zo kaga murna wurin iyayen nasa musamman ma hajiya da dama tafi kowa matsuwa da damuwar rashin auren nan nasa,washe gari Abba da kansa ba sako ba yashirya ya tafi kanon dabo neman aure,
Da dafarko shi mahaifin Hanan ma yayi zaton ko batan kai akayi amma da Abba yayi masa bayani sai ya fahimta yagane ba batan kai aka yiba,nan yace yabada auren hanan ai ko da ace akwai wani to zai iya hanashi yabawa Khalil bare ma babu,shi ai Khalil nasa ne atakaice dai Abba bai baro kano ba sai da ranar auren Khalil sannan abbanta yace Khalil din yasamu lokaci yaje su gana.
Yan hidimar k'asa kuwa ana can Abuja ana hidimtawa k'asa yanda ya kamata,kullum suna mak'ale da mujahid awaya dawowarta kuwa zuwansa biyu kullum cikin maganar tabari yatura gidansu yake amma ta murje idonta tace sam ita ba yanzu ba. Wata ranar alhamis sukayi waya da abbanta nan yake cemata,
"Uwar masu gida ki daure ki samu kizo acikin weekend dinnan domin inada muhimmiyar magana dake sannan kuma zamu samu bakuncin manyan mutane"
"To Abba insha Allah gobe dama nake son tahowa"
Tunani tai tayi aranta bayan sun gama waya da abba,to ko suwaye manyan bakin da zasuyi kuma oho,ko menene dalilin da yasa Abba yace taje gida oho,ko wacce muhimmiyar magana zasuyi da yace mata zasuyi duk Allah masani amma gaba daya hankalinta yatafi gida kawai so take ta ganta acikin garin kano,aranar taje tayi yar siyayyar kayan marmari domin yin tsaraba dama anyi musu alawee tun ranar Monday,washe gari tun 7 tafita taje tayi signing sannan ta tafi tasha ta hau mota cikin lokaci k'ank'ani mota ta cika fam suka kama hanya.......鉁嶏笍
_Game bukatar biyan kudin wannan book din zai turo naira 200 ta Account number dina 3112877210 Aisha Ibrahim first bank,sai atura shaidar biya ta wannan number din 07044644433 ko kuma atura MTN recharge card zuwa wannan number din 07044644433 sai atura shaidar biya ta the same number da aka tura katin nagode._
*_Ummi Shatu_*馃憣馃徎
8/14/20, 10:06 AM - Ummi Tandama: 漏锔? *HASKE WRITERS ASSOCIATION.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*D'AND'ANO.....*
*MIJIN MATACCIYA.....*馃挒馃挒
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*Wattpad-ummishatu*
*Alqaluma shida daga k'ungiyar haske na nan suna cigaba da baje kolin tasu basirar,nemi naka kaima adama dakai cikin farashi mai rahusa.*
*7*
***Har motarsu ta isa kano tunani daban daban bai daina kai kawo acikin ranta ba,duk ta kasa samun nutsuwa sai tufkawa da warwarewa take ta faman yi tana son gano dalilin wannan kiran gaggawar da Abba keyi mata wanda abisa dukkan alamu akwai abinda ke faruwa ko kuma yake shirin faruwa.
Ita dai har motarsu tashiga kano ta sauka ta tare mai napep ta shiga zuwa gida zuciyarta bata daina yimata wasi wasi ba,alla alla takeyi taganta agida dan taga abinda ke faruwa shiyasa jiki a sanyaye ta shiga gidan bayan ta sallami mai napep din da ya sauketa,
Mamaye ce kadai tana kwaba fulawar da zatayi dan wanke a kofar kitchen abisa dukkan alamu shima yaya shamsu baya nan,ganin fuskar mamaye awashe sannan kuma asake alamun babu matsalar komai yasata ta danji sanyi acikin ranta,
Kayanta ta shigar cikin daki sannan ta dawo wurin mamaye suka fara gaisawa,
"Mutanen Abuja kinsha hanya kuma kun fito da wuri..."
"Ehh wallahi mamaye tun wurin 7 fa muka fito dan ni ko karyawa ma banyi ba"
"To ai akwai ruwan zafi a flask sai kije kihada shayi kisha"
"To bari insha abisa lalura amma shan shayi da rana ai sai ahankali"
Daga haka ta tashi tawuce falo ta hado tea ta dauko bread ta sake dawowa wurin mamaye. Sai la'asar sannan abbba yadawo lokacin suna zaune da mamaye da yaya shamsu suna hira,
Wurin Abba taje suka gaisa sannan suka dan taba hira kadan har zata tashi abba ya dakatar da ita,
"Uwar masu gida sai kuma kikaji kira ko?"
"Ehh Abba dama nima ina son inzo gidan inganku ai"
"To wani abokina ne kuma aminina ya nemi wata alfarma awurina wadda nikuma bazan iya kin yimasa itaba,ya bukaci inbashi aurenki nikuma bazan iya hanashi ba...."
Jin abinda Abba yace yasata zaro ido tare da jin firgici gamida gagarumar faduwar gaba,bata san lokacin da tace,
"Abba abokin ka?"
"Ehh uwar masu gida... abokina amma nasan insha Allah zaki sameshi kamar yadda kike so,zaki ji dadin kasancewar shi mijinki, matarsa ce ta mutu a lokacin haihuwa,dansu daya kacal wanda ta mutu ta bari...."
Kamar wacce aka zarewa laka ajikinta haka taji bata san lokacin da hawaye ya ziraro ta idanuwanta ba,
"Abba kuma shine da kansa yaganni yace yana sona?"
"Shine Hanan,shi yaganki anan Abuja,acan yake da zama minister ne,shine ministern yada labarai,matasa,raya al'adu da wasanni,yanemi da inbashi aurenki kuma na bashi nan da sati uku za adaura muku aure,sai kije kifara shirye shiryen da duk ya kamata.... Allah yayi miki albarka"
Bata iya cewa komai ba ta tashi tafita idanuwanta cike da hawaye tausayin kanta da kuma mujahid take yi,yanzu me zata cewa mujahid? Da wacce kalma zata dosheshi har tayi masa bayani? Da wacce kalma yadace tayi amfani wurin sanar dashi wannan bakin labari?
Daga mamaye har yaya shamsu babu wanda tayiwa magana tawuce daki taje ta kwanta tasoma shakar kuka,duk tsawon shekarun da suka dauka tare da mujahid bata taba jin sonshi ba sai yau da taji zata rasashi,wata zazzafar soyayyar shi take jin tana shigarta babu k'akk'autawa,
Tajima tana kuka kafin mamaye tashigo ta zauna gefenta tasoma bata baki,
"Hanan kiyi shiru wannan kukan baida wani amfani,kiyi shiru ki mika al'amuranki ga Allah ki nemi alkhairinsa da kuma albarka acikin aurenki...."
Kamar jira take tasake fashewa da wani hargitsattsen kuka mai tsayawa arai,
"Mamaye abokin Abba ne fa wai,wai abokin Abba,mamaye yanzu ni anyi min adalci kenan idan aka aura min wannan mutumin? Mutumin da ya haifi yani? Mutumin da yafara ban kwana da duniya yana kusantar kabari,inama laifin abani zabi idan ina sonshi a aura min idan bana so abarni amma sai kawai ayi min dole ayanke hukunci batare da anji ra'ayina ba...."
"Ki daina fadin haka Hanan,iyaye sunada damar zabawa yaransu mazaje hakan bai saba ka'idar musulunci ba,kiyiwa mahaifinki biyayya sannan kiyi addu'a insha Allah bazaki tabe ba"
"Mamaye nidai har ga Allah bana sonshi, tayaya zan auri sa'an babana? Abokin Abba fa,sa'an abba ne fa mamaye, yanzu Abba yarasa wanda zai aura min sai abokin sa?"
"To ni me kikeso inyi akai Hanan? Yariga da ya yanke hukunci,aikin gama yagama, k'addara tariga fata sai dai kawai kidau hakuri kiyita addu'a, Allah ya zaba miki abinda yafi alkhairi a rayuwarki"
Daga haka mamaye ta tashi tafita tabarta tana ta faman gursheken kuka kamar ranta zai fita,
Wannan wacce irin k'addara ce? Ita mema yakaita Abuja yin service gashi nan mutum yaganta yazama silar rushewar farin cikinta, duk yanmatan Abuja yarasa wacce yagani yake so sai ita? Dan dai kawai yana da kudi sai yarinka amfani da damarsa yana taka duk wanda yaso? Insha Allah sai Allah yasaka mata,ita dai tasan Abba bawai kudi yabi ba wurin aurar da ita ga wannan bawan Allah,koda yake yace abokinsa ne watakila wannan shine dalilin da yasa ya bayar da ita batare da yajira yaji ra'ayinta ba.
Wayarta ta dauka tana share hawayen dake zuba daga idanuwanta tana face hancinta da tissue,text massage ta turawa mujahid kamar haka,
_Ban taba sanin cewa bakaine abokin rayuwa ta ba sai yanzu da k'addara ta gifta,ashe ba Kaine mijina ba shiyasa kayita bina akan zaka turo gidanmu amma naki gashi yanzu Abba ya bayar dani ga abokinsa,ya zanyi mujahid? Wallahi ina tsananin sonka musamman ma yanzu da ake neman rabamu._
Ai tunda mujahid yaga massage dinta hankalinsa shima yabar jikinsa,jiki yana rawa yakirata,shiru yayi yana sauraren sautin kukanta da yacika kunnuwanshi,
Daga shi har ita sun kasa cewa komai ita sai kuka takeyi murya adashe,
Cikin sanyin murya mai kunshe da damuwa yace,
"Hanan kiyi shiru....kiyi hakuri ki daina kuka kinji,ni nafi cancanta da inyi kuka bake ba domin wallahi ko tantama banayi soyayyar da nake yimiki ta ninka wacce kike yimin.... Ina sonki fiyeda tunaninki,kullum da sonki nake kwana nake tashi...."
"Mujahid tsohone fa,wai minister ne a Abuja, Abba baiyi min adalci ba,abokinsa fa zai aura min"
"Hanan ina son ganinki,yaushe zan ganki?"
"Mujahid sai dai mu hadu agidan anty salaha kaga bazai yuyu kazo nanba Abba yaganka,idan nafita zan kiraka"
"Shikenan babu matsala amma ki daina kuka kinji"
Shiru tayi ta katse wayar amma maganar ta daina kuka kam tasan abune wanda bama zai taba yuyuwa ba, ai dole tayi kuka rabuwa da masoyi sai dole bawai dan ana so ba, mujahid ako ina zata kirashi masoyinta domin yana tsananin kaunarta kamar ita kadaice macen da tayi saura a duniya,
Kuka kam tayi shi ta kara har tagaji, zuciyarta koda yaushe cikin kunci take da radadi Allah ya isa kuwa tayiwa abokin Abba tafi sau dubu domin shine mutum na farko da yafara yunkurin rabata da farin cikinta,
Washe gari ta tashi da niyyar zuwa gidan anty salaha amma Abba yace babu inda zataje tajira saboda zatayi bako domin yau angon yace zaizo su gana,tamkar zata fashe haka tazama saboda tsabar cikar da tayi.
***
Tunda ya fadawa Aryan cewa nanda 3 weeks zai kawo masa Mommyn shi yaron ke cikin farin ciki marar misaltuwa,
Dadi ne ya lullube zuciyar Khalil sosai saboda ganin Aryan cikin farin ciki,aranar ya shirya yatafi gombe yaje yaga Abba suka tattauna akan yanda abubuwan zasu kasance anan Abba kece masa sai yasamu lokaci yashirya yaje su gana da yarinyar,yadai ansawa Abba da toh amma harga Allah ba zuwa zaiyi ba shi ina yaga wani lokacin zuwa zance wurin budurwa yanzu? Acikin ayyukan sa wanne zai tsallake yatafi hira? Duk ma ba wannan ba shifa auren nan kawai zaiyi shine saboda Aryan bawai saboda kansa ba shi idan dan ta shine shida aure sai dai yaga anayi amma ayanzu kam babu macen da ta isa,
Maimakon yaje sai kawai yatura PA dinsa yaje yaga Hanan sannan yakai mata sako,
Lokacin da nura PA yaje Hanan a murtuke taje ta sameshi a dakin saukar baki dake kofar gida,motar ma da yazo da ita kawai abar kallo ce saboda kyanta da tsaruwarta,duk azotanta akwai ubban gayyar sai taga sai iya mutum daya,
Dan russunawa nura yayi sannan yace,
"Ranki yadade barka da fitowa,ayi mana afuwa yallabai bai samu damar zuwa ba da tare zamu zo dashi to sai kuma meeting na gaggawa ya sameshi,amma duk da haka ga sako yabayar inkawo miki...."
Envelope ya ajiye mata da wata babbar leda,
"Babu komai.." shine kadai abinda tace bayan yagama rattabo mata bayanin. Daga haka yamike da niyyar tafiya domin tuni dama tun kafin fitowarta yaci snacks da drinks din da aka tanadar masa,
"Amm yawwa sannan yace idan kina bukatar ganin hotonshi sai in......"
Tun kafin ya karasa ta dakatar dashi,
"Bana bukata...."
Mamaki ne ya addabi ruhin nura PA ita kuwa wannan yarinyar ya take kokarin yin sakarkaba? Ya take kokarin yiwa kanta asara? Ita da Allah yayi mata gam da katar da kabakin arziki ya zabota cikin dubban mata amma shine take nema ta butulce?
Saka takalmansa yayi sannan yasake dan russunawa,
"Na barki lafiya ranki yadade"
"Nagode,ka gaida gida"
Fita nura yayi babu jimawa itama ta tashi tafita batare da ta dauki kayan da nura ya ajiye mata ba sai yaya shamsu ne lokacin da yashiga ya fito mata dasu yabita cikin gida ya kai mata,
Tana daga kwance cikin daki tajiyo muryar abba yana cewa,
"Uwar masu gida kina ina? Inbanda shirmenki uwata kuma akawo miki kaya ki taho ki baraso acan? Ai sai ki dauka ki duba haka akeyi"
Fita tayi ta saka hannu biyu ta karbi kayan awurin Abba sannan tajuya takoma daki zuciyarta nayi mata wani irin tukuki........................鉁嶏笍
_Ga wadda keda bukatar biyan kudin littafin mijin matacciya sai ta aiko da naira 200 ta account 3112877210 Aisha Ibrahim first bank sai atura shaidar biya ta wannan number din 07044644433,ko kuma katin waya na MTN zuwa ga 07044644433 sai atura shaidar biya ta wannan number din da aka tura katin,domin neman Karin bayani za a iya tuntubar marubuciyar kai tsaye ta wannan number 07044644433._
*_Ummi Shatu_*馃憣馃徎
8/14/20, 10:07 AM - Ummi Tandama: 漏锔? *HASKE WRITERS ASSOCIATION.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*D'AND'ANO.....*
*MIJIN MATACCIYA......*馃挒馃挒
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*8*
***Kamar tayi fatali da kayan da ya aiko mata haka taji nan ta watsar dasu saman gado takoma gefe ta kwanta,tsabar yawan kukan da takeyi yanzu har takai takawo ma bata iya kukan sai dai tayi girim tana tunani wanda hakan ba karamin daga hankalin mamaye yakeyi ba ita tsoronta ma kar hawan jini ko ciwon zuciya ko kuma wata lalurar mai kama da haka ta kama mata yarinya hakanne ma yasa mamaye tasamu Abba da maganar tace masa kodai zaiyi hakuri ya janye maganar auren nan yabawa minister hakuri saboda yarinya bata so ita kuma tana gudun fadawarta mawuyacin hali,
Budar bakin Abba sai cewa yayi ai muddin idan suka ga ba ayi auren nanba tofa kwanan dayane acikinsu ya kare amma shi ko bayan ransa bai yarda Hanan ta auri wani miji bayan abokinsa ba,shine kadai mijin da ya zaba mata kuma ya yarda ta zauna dashi,
Haka mamaye tafito jiki babu kwari domin Abba fada yayi ta yimata yana cewa ya zata biyewa shirmen Hanan duk da ta girma ai har yanzu bata san abinda zai amfaneta agaba ko sabanin haka ba tunda abinda babba ya hango daga zaune yaro ko yahau rimi ba lallai ya hangoba,shi yasan mijin da yadace da hanan sannan yasan waye ya kamata yazama tare da ita shiyasa yayi mata wannan zabin.
Kasancewar yanzu bata iya kuka yasata yin shiru tana sauraren fadan da mamaye ke yimata cikin lallami da nasiha tana cewa ta daure ta cije tayiwa mahaifin ta biyayya insha Allah zataji dadi agaba sannan zatayi farin ciki ko dan biyayyar da tayiwa mahaifin ta sannan mamaye ta kara da fadin,
"Insha Allah Hanan sai kin yi alfahari da mahaifin ki,sai kinyi dariya agaba ko dan bin umarnin mahaifinki da kikayi kika masa biyayya,iyaye ba zasu taba cutar da yayansu ba sai dai abisa kuskure,duk abinda kikaga mahaifinki yayi to yayi miki ne dan soyayyar da yake yimiki,ke kanki shaida ce mahaifin ki yana tsananin sonki saboda ma soyayyar da yake yimiki da ace bani na haifeki ba to da bazan iya zama daku ba domin yafi fifitaki akaina... Ko kin manta yanda kuke hade min kai keda shi...?"
Murmushi mamaye tayi,itama Hanan din murmushi tayi tana tuno shekarun baya nan abubuwan da suka faffaru abaya suka soma dawo mata kamar yanzu ne suke faruwa,
Kamar yanda mamaye taso haka ta dan saki ranta tana hira har da su dariya idan mamaye ta fada mata wani abu,sai da aka kira sallar magriba sannan suka tashi,ita da yake bama sallar zata yi ba kitchen tawuce ta zubo abinci dan kadan domin yanzu bata iya ci dayawa,sai da tagama cin abincin sannan takoma cikin daki nan ta bude sakon da minister ya aiko mata,
Ledar tafara budewa nan taga tamfatsetsiyar sabuwar waya kirar kamfanin Samsung mai mutukar kyau da daukar hankali harda sim card aciki,
Tabe baki tayi cike da jin haushi tace,
"Tsabar ya rainawa mutane hankali da wayo shine shi baizo ba saboda yafi karfin yazo sai aikowa yayi,kuma ko waye yace masa bani da arzikin waya da har zai siyo ya bayar akawo min.... Saboda ga yar talakawa ko" kwafa tayi da karfin gaske sannan ta bude envelope din tana tsaki,
Kudi tagani bugun Abuja sababbi fil yan dubu dubu wanda bazata iya kiyasta adadinsu ba sannan kuma ga dan karamin card nan ajiki anrubuta,
_Ibrahim Sulaiman I._
Sai phone number dinshi a k'asa, maganar PA ce ta fado mata inda yake cemata,
"Akwai number dinshi ajiki yace idan kina da bukatar magana dashi ko wani abu mai kama da haka sai ki kirashi...."
Ita bazata kirashi ba amma dole ce zata sa tayi hakan ko dan tunatar dashi kuskuren da yake neman tafkawa dan kawai yana da kudi,saboda kawai yana da dama shine zaiyi amfani da karfin mulkinsa wurin musgunawa wasu,
Number wayar tashi ta kwafa tasoma kira domin so take ta fada masa maganar da zata bakanta masa rai watakila ma idan yaji haushi yace yafasa tunda bata da kunya,
Saida ta kira wayar sau hudu amma bata shiga sai dai ta danyi wata yar kara sai ta yanke,tsaki taja ta harhada kan kayan ta mayar dasu cikin leda tana kokarin tashi tajiyo karar shigowar text massage,
Kamar bazata duba ba sai kuma ta dauka tana dubawa,
_Am Little busy now,text me please._
Shine abinda taga anturo da wata special number mai dauke da 33333, tunani tafara yi to waye kuma wannan? Zuwa can tagane minister ne,kai duk yanda akayi shine tunda ita dai yau bata kira kowa ba sai shi,kai shi dinne ma,
Saida ta duba number tasake dubawa sannan ta mayar masa da reply,
_Ya kamata dai idan angirma asan angirma,duk zawarawan duniyar nan da rikakkun yanmata ka rasa wacce zakace kana so sai ni,nidai ka cuceni kuma kasani kawai zanyi zaman biyayya ne bawai dan ina soba saboda ni inada wanda nake so,idan kuma dan kana da kudine to ni kudinka baya gaba na._
Shine abinda ta rubuta ta tura masa amma shiru babu amsa har tagaji ta daina ma tsammanin zai turo mata da reply, "kaji irin wulakancin nasu ai" tafada aranta kafin ta tashi taje tashiga wanka,har tagama komai nata ta shirya ta kwanta mutumin nan baibi ko ta kanta ba,har tagama yanke tsammanin zai kulata domin 11 tawuce.
***
Lokacin da Hanan ta kirashi yana cikin meeting da yan uwansa ministoci,shi a ka'idar wayarshi idan ka kira asalin layinshi bazai shigaba sai dai idan text massage kayi masa to wannan zai shiga har yagani amma idan kira kayi to bazai shigaba amma dai zai ga kiran a dayan layinshi da akayi forwarding kiran zuwa can,to idan yasanka zai kiraka ta special line dinshi idan kuma bai sanka ba shikenan sai yakyale,itama Hanan dalilin da yasa ya san itace shine abbanta yatura masa number din tunda jimawa tun bayan lokacin da yabashi aurenta da yakirashi domin yimasa godiya yatura masa number dinta wai ko zai kirata shi kuma baice a'a ba amma aganinshi me zai kirata yace mata? Shi baida bukatar number dinta saboda baida case da ita,
To yau yana tsaka da meeting yaga kiranta shine yayi mata text, lokacin da ta dawo masa da reply ma shi ko budawa baiyi ba saboda lokacin har yasake shiga wani meeting din da masu bada shawara ta musamman akan harkokin wasanni da matasa gashi yan jarida suna waje sunyi cincirindo suna son ganawa dashi dangane da wani rade radi dake ta faman kaiwa da kawowa acikin gari na cewa wai gwamnatin tarayya zata sauke wasu masu ruwa da tsaki a harkar gwamnati har su dari daya,
Gaba daya bai samu kansa ba sai wurin misalin karfe 11 sai a lokacin yabar office bayan yagama ganawa da yan jarida yanufi gida,
Agajiye yake mutuka sannan ga ciwon baya dake dan damunsa da kuma ciwon kirji shiyasa tun kafin yakarasa gida yasa nura yakira masa likitansa wato Dr Al'amin,
Duk jikinsa jinsa yake babu karfi ga rashin cin abinci,yana komawa gida yayi wanka yasa jallabiya da gajeren wando aciki,a dan karamin falon shakatawarshi ya zauna ya hada coffee mai zafi yasha yana gama sha yaji amai na kokarin fito masa, bathroom din dake cikin falon yashiga yayi aman sannan yadawo falon ya zauna daidai lokacin da PA yashigo yana sanar dashi zuwan Dr cemasa yayi yashigo sannan ya dan kishingida jikin kujerar da yake kai,
Sai da Dr yagama dubashi sannan ya daure masa hannunshi da wata yar roba yana duba jijiya saboda anan ne zai dan yimasa allura sannan zai kara masa wani dan karamin ruwa leda daya,
Sai lokacin ya dauki wayarshi yasoma duba sakon da aka tutturo masa nafi yawa friends ne da masu neman taimako ahaka har yazo kan na Hanan,ganin abinda tace abin yaso ya bata masa rai,wai yara kanana sai su zagi mutum dan kawai maganar aure ta hadasu, yanzu ita wannan yarinyar ko ahanya ta ganshi ta isa ta fada masa wannan maganar ba dan maganar aure ta shiga tsakani ba?
_Ok_ shine abinda yatura mata kawai,yaci gaba da karbar ruwan dake shiga jikinsa wanda Dr ke kara masa,ajiye wayar yayi agefe ransa adan bace,
"Ranka yadade wallahi stress ne kawai ba wani abuba, sannan kuma yallabai maganar nan tawa dai kamar koda yaushe,dole fa sai ansamu abokiyar debe kewa..... Saboda agaskiya kana bukatar mace ko dan lafiyarka"
Shiru Khalil yayi yana dan sake jingina sosai cikin kujera, so yake idan yagama da Dr yaje yaga Aryan saboda yau throughout bai ganshi ba,yadai ganshi da safe kafin yafita lokacin ko ma tashi daga bacci baiyi ba kasancewar yau asubanci yayi.
Wurin karfe 12 saura sakon minister yashigo wayar Hanan dama har lokacin bata yi bacci ba,tana dubawa taga ok,ranta yayi mutukar baci,inbanda rashin mutunta dan adam Menene zai ce mata wani ok,
Tsaki tayi tasake tura masa da wani text din,
Bai kulata ba sai da Dr yatafi shima PA yatafi, bedroom din Aryan yaje ya dubashi sannan yakoma part dinshi yawuce bedroom ya kwanta domin Dr yace yadan samu bacci akalla na awanni shida. Massage din da yaji yashigo tun dazu ya duba,
"Again?" Yafada ganin Hanan ce ta sake turo masa da reply,
Budewa yayi ya tsurawa sakon nata ido cikin nutsuwa,
" _Ni dai ancuceni anrabani da wanda nake so saboda kawai budurwar zuciya,angirma ma ba za a hakura ba,yadai dace idan angirma asan angirma._"
Afili ya karanta sakon kamar yana karantawa wani,wai shine mai budurwar zuciya, murmushi yayi saboda shi abinma dariya yaso bashi,sai dai gaskiya turancinta ya burgeshi saboda duk sakonnin tana turosu ne da harshen turanci da alama dai ta kware a fannin,
Bai cemata komai ba ya ajiye wayar tashi saman bedside drawer sannan yakashe bedside lamp din dake gefen gadonshi ya lumshe idanuwanshi saboda son bin umarnin Dr,yana son ya dan samu bacci kamar yadda Dr yace......鉁嶏笍
_Ga mai bukatar siyan littafin mijin matacciya zai tura naira 200 ta account dina 3112877210 Aisha Ibrahim first bank sai atura shaidar biya ta 07044644433,ko kuma recharge card na MTN ta wannan number din 07044644433 sannan sai atura shaidar biya ta number da aka turawa._
*_Ummi Shatu_*馃憣馃徎
8/14/20, 10:07 AM - Ummi Tandama: 漏锔? *HASKE WRITERS ASSOCIATION.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*D'AND'ANO.....*
0 comments:
Post a Comment