Doctor '' Al'ameen Abubakar Khabeer Cindo ''and his wife ''Prof. Nafeesa (Baby) Isma'il Audu, '' as you know in the story of *NAFEESAT* They live in Kaduna, and they still live in the city, owned by their five children.
*1_ DOCTOR NOOR (LAWAL AL'AMEEN ~YARON UMMEE NAFEESA~)* Wanda a yanzu ake kiran sa Big Dady, matar sa ɗaya *Hajiya Asiya (Hajiya) ƴa ga Muhsina,* yaran su uku, Doctor Usman, sai Doctor Zainab ~yanzu haka tayi aure,~ sai kuma Yusra.
*2_ HAJIYA RABI'ATU AL'AMEEN (IKRAM) ~WANDA A YANZU TANA AURE A GARIN KATSINA~* tana zaune da iyalan ta acan.
*3_ DOCTOR ABUBAKAR AL'AMEEN ~WANDA YANZU AKE KIRAN SA DA ABBA~* matar sa ɗaya Doctor Fatima (Hajja Fatu) ~ƴa ga Abokin Doc. Al'ameen wato Haidar da ƙanwar sa Ihsan,~ yaran su Biyu, Doctor Al'ameen (Baffa), sai ƙanwar sa Shakira.
*4_ DOCTOR AL'AMEEN AL'AMEEN (ABBU)* Matan sa biyu, ~Bilkisu (Umma) ƴa ga Baseera,~ yaran ta uku Doctor Zulaiha ~tayi aure,~ sai Fadila da autan su Fadil. Sai matar sa ta biyu *A'ISHA (AUNTY AMARYA)* yarinyan ta ɗaya '''NAFEESAT''' suna kiran ta da Ɗahira.
*5_ HAJIYA LAILA AL'AMEEN* yanzu haka tana aure a Kano, ta auri babban Yaron *WALID.* Suna zaune da iyalan su can.
Waɗannan familyn yanzu haka suna zaune ne a gida ɗaya kowa da part ɗin shi, sai dai akwai Babban parlour'n da ya haɗa su, yanzu haka Doc. Al'ameen Wanda a yanzu suke kiran sa da *KAKA* ya kai shekaru 89years. Tuni ya ajiye aikin sa sakamakon yana fama da ciwon ƙafa wanda a halin yanzu yana zaune ne a wheel chair, matar sa Prof. Nafeesa (Baby) Shekaru uku kenan da Allah ya amshi abin sa.
Za kuyi mamaki idan nace muku duk ka familyn Doc. Al'ameen gaba ɗayan su *DOCTORS* ne, wannan shine burin sa kuma Allah ya cika masa.
Babban asibitin da ya gina ya ƙara haɓɓaka shi wanda a halin yanzu Five Block ne, kuma sosai asibitin me suna *(AL'AMEEN FAMILY HOSPITAL)* tayi fice a ƙasar Nigeria, gaba ɗaya familyn suna aiki ne a Hospital ɗin.
Yanzu haka a halin yanzu an shirya yin babban Walima don taya Doc. Ɗahira(Nafeesa) Al'ameen Al'ameen, Doc. Shakira Abubakar Al'ameen, Doc. Yusra Noor Al'ameen, da Doc. Fadila Al'ameen Al'ameen. Murnan kammala karatun su na likitanci, wanda za su soma aiki ne a ranan da a kayi musu waliman tare da sabbin ma'aikata da za'a ɗiba a ranan.
*KU BIYO NI DON JIN LABARIN WAƊANNAN FAMILYN*
Zaune suke su Huɗu a Babban katafaren parlour'n gidan da ya'amsa sunan sa a haɗuwa da ƙayatarwa, da shigowan ka parlour'n Babban Hoton Prof. Nafeesa (Baby) zaka soma cin karo dashi, wanda tayi sa ne lokacin da ta zama Professor, tana sanye da baƙar abaya me tsananin kyawu da burgewa, wanda duk da kasancewar ta baƙa ba ƙaramin kyau yayi mata ba, sai tayane kanta da Milk Colour ɗin Veil, kyakykyawar fuskarta yalwace take da murmushin da ya ƙara fito da tsantsan kyawun ta tare da Dimpul ɗin ta, a tsaye take ta riƙe ƙugu da hannu biyu tare da ɗan ɗage kanta, da alamun sanda akayi hoton bata san ma za'a yi sa ba. kusa da hoton kuma wani tanƙamemen hoton ne da a cikin sa Al'ameen ne tare da ita Babyn, suna zaune manne da juna sun saka ankon shadda me ruwan powder, gefe da gefen su kuma Noor ne tare da Ikram jingine da jikin su, duk kan su dariya suke yi time ɗin da aka ɗauki hoton, sai gefe kuma sauran hotunan ƴan gidan ne kowa da iyalan sa, sannan sai aka ɗau guda ɗaya wanda su kayi gaba ɗaya familyn, shi wannan ba'a daɗe da yin sa ba, don gab da rasuwan Prof. Baby akayi sa, gaba ɗaya idan ka kalle su sosai suke kamanceceniya da juna, sai dai banbancin launi da ya raba su.
Doc. Al'ameen wato KAKA tare da yaran sa maza su uku zaune cikin parlour'n suna tattauna yanda za su gudanar da Waliman yaran su kamar yanda suka saba a duk sanda yaran gidan suka gama karatun su na likitanci.
"Kai takwara yaushe matarka zasu dawo ne? Kasan jibi ne walima, ya kamata su dawo don itama Matata (yana nufin Ɗahira kenan) ta sami damar shiryawa yanda Ya kamata". Kaka dake zaune saman wheel chair yake wannan maganan
ABBU yace, "insha Allahu Dady zasu dawo zan sake tuntuɓan su inji, sabida mahaifin A'isha (matar sa Aunty Amarya) jikin ta yayi tsanani ne shiyasaka suka jin kirta".
Kaka yace, "to shikenan Allah ya dawo da su lafiya".
Gaba ɗaya suka amsa da "ameeen".
Sannan ya kalli Big Dady yace, "Kai kuma da yaushe ne Usman yace "zai dawo?"
Big Dady yace, "Allah ya taimaki Dadyna! na yi masa magana amma yace "in ba ka haƙuri ba zai samu daman zuwa ba sabida aiki sun yi masa yawa".
Cikin nuna alamun fushi Kaka yace, "wai yaushe Usman yabzama me taurin kai ne? Ko don yana tunanin na ba shi dama ya zauna acan yayi aiki shine yake son ɓata min rai? To, ka gaggauta kiran sa ka faɗa masa umarni nake ba sa; dole ne ya zo wannan taron Waliman da za'a yi, ko me yake yi ya'ajiye sa ya halarci taron nan".
Gaba ɗayan su su kace "Allah ya huci zuciyar ka Baba".
"Insha Allahu zan sanar masa Dady kuma zai zo". Cewar Big Dady kenan
Gyaɗa kansa Kaka yayi kana yace, "za ku iya tafiya na sallame ku, Allah yayi muku Albarka".
Gaba ɗayan su suka amsa da "ameen" kana suka tashi suka fice.
Shi kuma Kaka janyo Remote yayi ya sauya tasha zuwa African t.v yana sauraron wa'azi
Da sallama Fadil ya shigo parlour'n, wanda ya kasance shine ƙaramin gidan don shekarun sa baza su wuce 14yrs ba. zama yayi kan kujeran da ke kusa da na Kaka ya saka hannu ya ja gemun Kakan da ya kasance fari fat, yana dariya yace, "Kakus kana hutawa ne?"
Kaka bige hannun sa yayi yana faɗin, "Ƙaniyar ka Fadil, kai ma ka koyi jan min gemun ne yanda Matata take min?"
Dariya ya tuntsire da shi yace, "to ai hakan ya fi dace wa da kai Kakus, don me baza ka aske gemun ba ka bar abu sai faman lilo yake yi, wlh watarana kana barci zan silalo in cire maka kowa ya huta".
Dariya shima Kakan yayi yace, "lallai ka raina ni da yawa amma ina da me maganin ka, ka jira ya dawo zan faɗa masa duk abinda kake min".
Zumbur Fadil ya miƙe yana waro ido waje yace, "afwan Kakus kaima ka san ba mu haka da kai, wlh yau ne kawai nace bari in ɗana Amma baran sake ba, Kar kasanar masa don Allah kaji Kaka na". Yaƙarike maganar nasa yana me marairaice fuska kamar zai yi kuka
"Shaƙiyin yaro ashe kana da tsoro har haka?"
Waro idanu Fadil ɗin ya sake yi yace, "iyyee Kaka taya bazan ji tsoro ba bayan kana son ka haɗa ni da Zakin gidan mu? Ni dai ka ga tafiya na don tunda ka'ambato shi bazan iya zama anan ba". Yana ƙarisa maganar ya ruga aguje yabi hanyar part ɗin su
Da dariya Kaka yabraka shi, kana ya girgiza kan sa aran sa yana cewa, "lallai Usman ka koya ma yaran gidan nan tsoron ka, ba ka a cikin gidan ma shekara da shekaru amma har yanzu tsoron ka be bar cikin ran su ba".
Ci gaba da kallon sa yayi, sai can kuma ya ɗago kansa yana kallon hoton matar sa Baby, Wanda take ita kaɗai ɗin, murmushi da hawaye ne a haɗe suka taho mishi tunawa da rayuwan su, kullum ranan duniya sai ya zub da hawaye a kan ta, coz Ko wacce rana sai ya kalli hoton ta sama da ashirin, kuma aduk sanda zai kalla ko yayi kuka ko yayi dariya sabida abinda zai tuna na game da rayuwan su a wannan lokacin, gaba ɗaya ɗakin sa idan ka shiga hotunan ta ne birjik, da sanda take tashen ta da sanda ta tsufa, har ta bakin gadon sa inda yake saka kansa akwai hoton ta da ya'ajiye a wajen, mutuwan ta ya bala'in girgiza sa wanda yayi kamar bazai rayu ba, sai daƙyar ya dawo hayyacin sa bayan dogon jinyan da yayi, har yanzu har gobe soyayyar ta tana nan daram a zuciyar sa, domin kamar ƙaddara ne da Allah ya saka masa na tsananin ƙaunarta, kullum fatan sa ace ga ranan da zai bi ta, shima ya koma ga mahaliccin sa kamar yanda ta tafi ta bar sa..
Dafa kafaɗun sa da akayi shi ya dawo dashi hayyacin sa, Yusra ce tsaye kansa tana kallon sa, idan da sabo yaci ace sun saba da ganin Kakan nasu cikin wannan halin, kuma sun san da cewa ba komi yake saka sa a halin nan ba illa tuna Kakar su.
"Kaka har yanzu dai ka ƙi ka dena tuna wannan tsohuwar matar taka, har yaushe ne zaka cire ta arai ne kayi rayuwan ka cikin kwanciyar hankali? Mu nan mun ishe ka rayuwa ba sai ka tuna ta ba, me ake yi da tsohon Zuma bayan ga sabbin zuma? Don Allah ka dena ɓata time ɗin ka a kan ta".
Hannu ya saka ya share hawayen yana murmushi yace, "Yusra kenan baza ki taɓa gane wa ba, amma kowa ya san da cewa tsohon zuma shi ne wanda ke magani, sannan ba'a iya manta shi ko wani hali mutum ya shiga, Ni Matata ta fiye min ku duk kan ku, idan da za'a bani zaɓi daku da ita in zaɓa, ita zan zaɓa in bar ku".
Taɓe baki Yusra tayi tace, "to don baka zaɓe mu ba sai me Kaka? Our parents will vote for us because they love us."
Kaka yace, "to naji ban ce kiyi min rashin kunya ba, said me to my room".
"Da can Ni na ɗauko ka?"
Hararan ta yayi yace, "I have noticed that Yusra is jealous of my wife, but you will die. I will never love you. She is the only one who betrays me. kuma wlh idan baki gungura Ni kin mayar dani ɗaki na ba da Yayan ki zan haɗa ki, ke ce farko wacce zan kai ƙara wajen sa".
Turo baki tayi ciki-ciki tace, "ka daɗe baka kai ɗin ba, in yaso sai ya kashe Ni kar ya bar Ni da rai".
"What are you saying?" Kaka said looking at her
"Me kuwa kaji na ce?" Tafaɗa tana huro hanci kafin ta soma tura sa
Murmushi Kaka yayi yace, "na san maganin ku dani kuke zan cen".
Tana gungura sa cikin ɗakin sa ta fito tayi nasu part ɗin cike da haushin Kakan.
[5/21, 9:53 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
_Godiya ta tabbata ga Allah me kowa me komi, tsira da aminci su tabbata ga shugaban mu Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam, Allah Nagode maka da kabani daman rubuta wannan littafin, 🙏🏼ya Allah kabani ikon rubuta abinda zai amfani al.umma ameen._
*EPISODE Two*
Da shigan Yusra parlourn su ta sami Hajiya zaune tana kallo, ƙarisawa tayi ta zauna kusa da ita tana ci gaba da cunno baki gaba
Da ido Hajiya taraka ta dashi kana tace, "Ke dawa? zaki shigo min parlour Babu sallama?"
Yusra kallon Hajiya tayi har a lokacin fuska a turɓune tace, "it's Kaka and I, wai cewa yayi zai haɗa ni da Ya Usman idan ya dawo".
Tsaki Hajiya taja tana hararan ta tace, "ai maganin ku kenan tunda baku da kunya, idan ya haɗa ku dashi sai ku dawo hankalin ku".
Yusra kamar za tayi kuka tace, "to Hajiya ba kakan mu bane menene in mun yi wasa dashi?"
"It's up to you. Get up and go to Zainab's house. I've been waiting for you for a long time. tun ɗazu ta kira Ni a waya kuma na neme ki sama da ƙasa ban ganki ba, sai ki kwana acan in yaso gobe kun taho tare".
Miƙe wa Yusra tayi ta nufi hanyan ɗakin ta, har ta kusa shiga Hajiyan ta kira ta, dakata wa tayi ta juyo tana kallon ta bayan da ta'amsa
"Ki shiga ɗaki na ki ɗauko Flower kwata biyar ki tafi dashi, nima sai kuyi min nawa don bani da lokaci aiyukan za suyi min yawa, cincin ɗin na kwata biyu kaɗai za kuyi min".
"To". Yusra tace hakan tana wuce wa ɗakin Hajiyan.
_*****_
"Calm down, what can I tell you? Shakira, kin san Buri na shi ne In ga ranan da za'a ce mun fi kowa a wannan familyn, I want to see the future of the *AL'AMEEN FAMILY HOSPITAL* back under us. wannan dalilin ne yasaka na saka wa Baffa sunan Kakan ku, kuma dalilin ne yasaka na matsa wa Abban ku yabar Ni na koma makaranta na zama Likita, I know that one day my dream will come true. "
Shakira looked at her mother and said, "Hajja, how do you think this hospital will be ours alone? Kar ki manta fa Familyn mu babba ne kuma kowa yana da gado idan har Kaka akace ya mutu, sannan taya kike tunanin sunan Ya Baffa zai taimaka mana don samun Asibitin nan?"
Hajja Fatu smiled and said, "Hmm, I know what I am thinking. Please keep your eyes peeled. Insha'Allah sai mahaifin ku ya gaji asibitin nan, sai mun fi kowa fice a cikin asibitin nan, sannan sunan Baffa da na saka don ina so ne nan gaba koda bayan ran Kaka ya zamana shi ke juya Hospital ɗin, ma'ana kowa yayi tunanin sunan ɗana ne sannan a manta da kakan ku, Ni a ganina hakan zai yi sauƙin zama namu".
Shiru Shakira tayi tana kallon ta sai kuma ta kwashe da dariya
Hajja Fatu dake faman kallon ta baki hangame tace, "Ke ban son iskanci! Why are you laughing like that?"
Wlh Hajja you laughed at me, wai taya ma kike tunanin Jika zai mallaki Hospital ɗin Kaka idan har don kin saka sunan sa? Bayan kin san da cewa ABBU ma sunan Kakan yaci, to ki faɗa min da ɗa da jika wanne mutane za su yi tunanin Hospital nashi ne?"
"Hmm ai fata nake yi sannan cewa nayi ina so kowa ya ɗauka cewa Al'ameen ɗina ne aka saka, kin ga Ni da Abban ku da ke da Baffa duk muna aiki a cikin asibitin, don haka nake so nan gaba asibitin ya zamto na mu, ke dai kawai ki mayar da hankalin ki da zaran akace kun soma aiki, duk abinda baki fahimta ba kizo waje na ki sanar dani kinji?"
Gyaɗa kanta Shakira tayi tana kallon uwar nata
"Now call me Baffa and we will talk to him."
"Ok".
Tashi Shakira tayi ta nufi corridor'n da zai sada ta da ɗakin Yayan nata.
*****
The next morning gidan Doctor Al'ameen sosai ya cika da mutane ƴan uwa, Hajiya Ikram da Hajiya LAILA har sun iso da iyalan su, haka ma su Aunty Zainab da Aunty Zulaiha, nan da nan gidan ya rincaɓe da hayaniya sai shirye-shiryen abubuwan da za'a yi suke yi.
........ ....... ....... ....... ....
Baƙar Mota ce ta sanyo kai cikin ƙaton gidan da ya tsaru iya tsaruwa, kai da gani kasan mamallakin gidan ba ƙaramin hamshaƙin me kuɗi bane, sosai gidan yake da girma da yalwa Two upstairs ne, idan ka shiga haraban gidan yana da yalwa sosai wanda aƙalla zai cinye motoci kusan ashirin, sai kuma Part ɗin masu aiki da akayi daban, da akwai Garden a ta bayan gidan tare da abubuwan more rayuwa, the home of Doctor Al'ameen and his family.
Motar na packing wata mata da a ƙalla baza ta wuce 45years ba ta fito, sai kuma wata matashiyar budurwa da shekarun ta ba zai fi 25years ba itama ta fito, tana sanye ne da wani Abaya green colour Wanda a gefe da gefen rigan an sanya ratsin blue, sai kwalliyan Flower da akayi da stone masu matuƙar ƙyalƙyali daga sama har ƙasa, tayi Rolling kanta da ɗankwalin Abayan da ya kasance Blue, sai ta saka wani ɗan siririn farin glass Wanda ya ƙara fito da zallan kyawun ta da kwarjinin ta; tare da fito da manyan idanuwan ta da ƙwayan idanun suka kasance sky Green, kallo ɗaya idan kayi mata zaka san da cewa ba ƙaramar mugun haɗuwa tayi ba, fara ce sosai tana da kyawun fuska tare da ƙira me kyau, sai dai ta kasance siririya ce sosai kuma matsakaiciya, kana kallon ta kasan cewa za tayi yanga ne da yawa, don ko maganar ta da tafiyan ta idan tayi zaka san cewa Nature ɗinta ne hakan
Matar kallon drever'n da ya fito cikin motan tayi tace, "Ali where are you doing now?"
"I will go to the hospital because Alhaji said, 'If I drop you off, he will sent me.'"Ali said respectfully.
Gyaɗa kanta tayi kana tace, "ok go, idan ka dawo I'll sent you later".
"To Hajiya".
Daga haka juyawa tayi ta nufi cikin gidan, Matashiyar yarinyan itama tabi bayan ta. koda suka shiga ciki Direct Part ɗin su suka nufa, lokacin da suka shiga cikin ɗan madaidaicin parlour'n su da sallama a bakin su
Fadila ce zaune tana kallo ta'amsa musu
"Welcome Aunty" Fadilan saying
"Yauwa Fadila, ke kaɗai ce zaune?" Aunty Amarya tace hakan cike da fara'a tana kallon ta
Fadila ta bata amsa da "Eh su Umma na General parlour".
"Ok mu ma ai bamu shiga cikin gidan ba nan muka taho, bari in shiga ɗaki in yaso sai in shiga can mu gaisa".
"Toh aunty".
Wuce wa ɗakin ta Aunty Amarya tayi
ita dama tuni Ɗahira ta wuce tasu ɗakin wanda ya kasance tasu tare da Fadila, tana shiga ta'ajiye Jakan dake hannun ta ta zauna gefen gadon ta, zare ɗankwalin da tayi Rolling a kanta tayi ta'ajiye tana bin gadon ta kwanta, kanta na kallon sama yayin da ta ƙure Cilling ɗin ɗakin da kallo, ta ɗan jima ahaka kafin ta sauke ajiyan zuciya tana lumshe kyawawan idanuwan ta, sai kuma ta buɗe ta tashi zaune tana zare Glass ɗin idanun ta ta miƙe ta nufi gaban Looking glass ta buɗe Locker ta'adana, darect Sif ɗin kayan ta tanufa ta ciro wasu riga da wando na Pakistan Milk and Red colour ta zube su saman gado, kayan jikin ta ta soma cire wa kafin ta ɗaura towel ajikin ta tashige toilet, wanka tayi ta ɗauro alwala ta fito, sai da ta shafa Lotions ajikin ta kafin ta saka kayan ta ɗaura Hijab tayi sallan asar da ta wuce su tun a hanya, bayan ta gama ne ta nufi wajen Looking glass ta zauna tana kallon kanta a madubi, tagumi ta zuba still tana ci gaba da kallon kanta
Fadila ce ta shigo ɗakin idanunta ya sauka akanta, sai ta taɓe baki tana ƙarisawa wajen ta tace, "Are you all right?"
Sai a lokacin Ɗahira ta ɗago kanta tana kallon ta, sai kuma takau da kan tare da faɗin "me kika gani?"
Fadila bata ce komi ba ta juya ta tafi, dama wayan ta tazo ɗauka, tana ɗauka ta fice a ɗakin, wannan shi ne halin su su duk ka biyun basu cika kula juna ba duk da duk kan su suna da ƙyaliya, But kasancewar Iyayen su suna kishi shiyasaka su ma suke taya su a junan su, ga dai shi ɗaki ɗaya suke kwana amma sai su wuni su hantse ba wacce zata kula ƴar uwanta, ba me shiga harkar ɗaya sai sun ga dama, ita dama Ɗahira ƴar ba ruwanta ne, bata cika shiga shirgin da ba nata ba, bata da son hayaniya amma tana da fara'a da kirki, komi tana yin abinta ne cikin class, sai dai alokaci ɗaya baza ka taɓa fahimtar halin ta ba sai ka zauna da ita, Fadila ma haka sai dai wani lokacin tana da yawan wulaƙanci a ɗabi'a, domin miskilancin ta yayi yawa don in bata ga dama ba ko kai uban waye baza ta kula ka ba sai taga dama.
Ɗahira cire tagumin tayi ta soma shafe Baby face ɗin ta da kayan makeup, ita gwanar son gayu ne duk sanda zaka ganta bata rabo da kwalliya, Light makeup tayi wanda ya ɗau fuskarta sosai ya ƙara fito da zallan kyawunta, ba maganar wasa ba Ɗahira tana ɗaya daga cikin kyawawan gidan, duk a cikin ƴan matan gidan zan iya cewa tafi su kyau duk da suna matuƙar kama, sai dai ita yanayinta da komi nata ya banbanta da nasu
Buɗe Lockern tayi ta ciro Glass ɗin ta tasanya Wanda ya zame mata ɗabi'a ko yaushe idan zaka ganta tana tare dashi, sai ta miƙe ta nufi gaban gadon ta taɗau wayan ta ƙirar IPhone 11+, takalmin ta kawai ta sanya ta fito batare da ta yafa komi ajikin ta ba baya ga ɗankwali da ta sanya ta rufe tulin gashinta, tana fitowa parlor ta hangi Fadila zaune har yanzu, sai dai wannan lokacin wayan ta take dubawa, ɗakin Mahaifiyar ta tawuce, tana shiga babu kowa hakan yasa ta fito ta doshi cikin gidan, sai da ta wuce wani dogon corridor kafin ta buɗe wani ƙofa ta shige, ahankali ta soma taka Step tana sauko wa sai gata cikin wani kyakkyawan parlour ƙarami, sai tabi ta wani ƙofan ta fito babban parlor'n gidan da ya kasance cike da mutane kowa sai harkan gaban sa yake yi, tana isa ta gaishe dasu sannan ta wuce wajen ƴan matan dake can gefe zaune, zama tayi gefen Shakira da Salma (ƴa ga Hajiya LAILA)
Shakira CE ta soma cewa, "Now I ask Aunty Amarya where are you? She told me kina Sashin ku ai".
Ɗahira She smiled and said, "na tsaya wanka ne".
Fiddausi da ta kasance ƙanwar Salma tace, "to ya Naga hannayen ki rabbana suna dukan cinya, ina tsaraban tamu?".
Kallon ta Ɗahira tayi tace, "What are you eating na baka na zuba? Let me rest for a while, sai ki zo ki taya ni kwance jakan".
Gaba ɗaya wajen su kayi dariya ban da Yusra dake faman latsa wayan ta ko ɗago kai bata yi ba
Shakira tace, "kin ji ƙyale wannan yarinyan bata da hankali, ke da akaje Duba marar lafiya kike zancen tsaraba?"
Ɗage gira Fiddausi tayi tace, "to kuma akace idan anje baza'a yi tsaraba ba? Nasan da cewa waɗannan tsofaffin baza su barta haka ba sai sun haɗo ta da abin lasawa".
Shamsiyya (ƴa ga Hajiya Ikram) tace, "ƙwarai kuwa Fido sai dai idan mu baza'a bamu ba, don naga tunda ta shigo Shakira take ƙifƙifta mata idanu".
Salati Shakira ta saki tana rufe bakin ta tare da zaro idanu, sai suka saki dariya suna shewa, wasu suce "eh su ma sun gani" wasu kuma suce "kai Shamsiyya banda ƙarya".
Dogon tsaki Yusra taja ta miƙe ta wuce abin ta, yayinda duk kan su suka bi ta da idanu kana Salma tace, "Oh, that juju girl, what's wrong with her?"
Dawo da idanun ta Ɗahira tayi gare su tana murmusawa tace, "Ni kun ga tafiya na bari inje in miƙa gaisuwata ga Kaka tunda naga ban ganshi anan ba".
Tafa hannu Fiddausi tayi tace, "ai Kaka yau sai dai yayi haƙuri mun hana sa fitowa, cewa yayi bazai iya da surutun mu ba ya shige ciki ya kwanta".
Tashi Ɗahira tayi tana faɗin "ai gwara haka kar ku ƙara masa damuwa".
Daga haka ta wuce batare da ta kula su da sukayi mata caaa ba.
[5/21, 9:54 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏻
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
*NATSUWA A SALLAH*
_Sallah babbar matsala ce. Ganawa ce tsakanin Bawa da mahaliccin sa, Ubangiji maɗaukakin sarki. Saboda haka ana buƙatar cikakkiyar natsuwa, a tattara hankali wuri ɗaya domin wannan ganawa ta musamman._
_A cikin ayoyi biyun farko na suratul Mu'uminun ana faɗa mana cewa:_
_"Lalle ne, muminai sun sami babban rabo, wanɗanda suke a cikin sallar su masu tawali'u ne."_
_Watau, Muminai wanɗanda idan sun tsaya yin Sallah sai gaɓoɓin su da zukatan su su natsu, babu wani abu mai shagaltar da su daga ambaton zatin Allah maɗaukakin sarki, to, irin su suke rabban ta. Natsuwa cikin sallah da ƙasƙan da kai ga Allah su ne alamun imani na gaskiya da Tauhidi tsantsa, don kuwa ko yaushe bawa yayi kusa da Ubangijin sa sai ya haɗa jin tsoron sa, musamman ma dai a sallah inda yake ganawa da shi, yake tunawa da girman sa._
*EPISODE Three*
A hankali ta sanya hannun ta ta soma jan gemun sa
Hakan yasaka ya buɗe idanuwan sa ya sauke a kan ta, murmushi yayi yana kallon ta yace, "Ni dama nasan babu wanda zai min haka sai ke, When did you come back?"
Murmusawa tayi tana janye hannun ta tace, "yanzu babu daɗewa".
Tashi zaune yayi yana faɗin "To ya me jikin da fatan ya samu sauƙi?"
Sai da ta dawo kusa dashi kana tace, "Alhmadulillah Kakus suna gaishe ku kowa da kowa".
"Mun gode muna amsawa".
"My Kakus miss you so much".
Murmushi Kaka yayi yana ɗaura hannun sa a kan ta yace, "nima haka Matata, You have left me alone I miss you, kin bar ni da waɗannan yaran mara su kunya masu ido a tsakar ka ko hiran basu taya ni".
Dariyan ta me kyau ta saki tana jingina kanta jikin Kakan tace, "Kakana kenan! don't worry, I'll be back. hira har sai ka gaji daji, akwai labarin ma da na samo maka".
"Well I hear you tell me".
Ƙofar da aka turo ne ya sanya Ɗahira rufe bakin ta without saying a word. Big Dady ne tare da Abbu suka shigo da sallama, amsa musu su kayi yayinda Ɗahira ta tashi da sauri ta nufi Mahaifin nata ta rungume shi tana faɗin
"Abbu na".
Murmushi yayi yana shafo kanta yace, "to ya kin dawo ko zaki fara?"
Dariya tayi tace, "I'm really missing you, Abbu."
Sai kuma ta sake shi, Then she hugging Big Daddy and said, "Daddy, I'm the only one."
Shafo kanta yayi shima yana smiled and said, "my daughter when did you come back?"
"Now Dady".
"To ya me jikin yaji sauƙi dai ko?"
Gyaɗa masa kai tayi tana faɗin "Alhmadulillah".
Big Dady yace, "madalla haka ake so".
Sannan ya juya yana kallon Kaka yace, "Dad, we're here to talk about new products da za'a shigo dasu."
Kaka yace, "to shikenan".
Abbu da ya samu wuri ya zauna yace, "Mamana bamu wuri za muyi magana".
Big Dady yace, "a'a barta kawai ta zauna".
Murmushi Ɗahira tayi tana kallon Big Dad tace, "bari dai inje in dawo Dady, because I have some things to do".
"Well shikenan Daughter".
Daga nan fita tayi ta rufo musu ƙofa, She did not go back to the General Parlor. Sai tabi ta wani Corridor da zai sada ta da Part ɗin su, tana cikin tafiya ta hangi Baffa ya taho shima ɗin, yayi shigan nan nasa na ɗamewa irin shigan wizaye, kansa babu hula sai kwantaccen gashin kansa da ya sha askin zamani, sosai yayi masa kyau ya sake fito da kyawun sa ainun, hannun sa Sigari ne yake sha, shima yana hango ta ya matse Sigarin a hannun sa ya kashe kana ya tura shi cikin aljihu
Murmushi ya saki lokacin da ya'iso wajen ta yana faɗin "Oyoyo My Lovely sister". Ya nufe ta da ninyan Hugging ɗin ta
Tayi saurin ja da baya tana murmusawa tace, "Oyoyo My Lovely Brother".
Sai ya ɓata fuska and looked at her and said, "Why don't you let me hug you?"
Still tana murmusawa tace, "ka san ba na so fa".
Ɗage kafaɗa yayi yana cewa, "ok to ya Hanya? kin dawo ko ki neme Ni, kinsan nayi missing ɗin ki sosai".
Ɗan huro hanci tayi tana kallon sa, sai kuma ta ɓata fuska tace, "Ya Baffa kamar warin Sigari nake ji?"
Waro idanu yayi yace, "Really?"
Sai ta harare sa tana cewa, "Where is our promise?"
He smiled and touched his forehead and said, "Sorry Sis ban saɓa miki ba ai".
"I don't agree, ga shi kana bani haƙuri".
"Da gaske my Sister na Dena sha, sai dai idan hancin ki ya juyo miki wani warin daban".
Kallon sa kawai take yi, sai kuma tace, "ok I Believe You".
He smiled and said, "so where are you now?"
"I'll go back to our Part".
"Mu je ki taya ni hira mana".
Girgiza kanta tayi tace, "No grave until tomorrow, now I have something to do."
Baffa haɗe hannayen sa yayi yana kallon ta yace, "Please Mana my sis".
Ɗahira ɗan kawar da kanta tayi
ya sake cewa, "Please kinji?"
"Ok Muje".
Murmushi ya sakar mata yace, "yauwa ko ke fa".
Itama murmushin tayi tabi bayan sa suka jera suka nufi cikin gidan.
Suna shiga cikin ɗakin sa tabi ɗakin da kallo tana yamutsa fuska, sai kuma ta kalle sa tace, "Wai Ya Baffa kwana nawa ɗakin nan be ga shara ba?"
Shafo kansa yayi yana kallon ta shima yace, "wlh kin san ban da lokaci kuma ga shi ke kinje anguwa, and na saka Shakira ita kuma kin san halin ta ba wani iyawa tayi ba"
Gyaɗa kanta tayi kana tace, "ok bari in gyara maka yanzu ko".
"Ok my sis let me help you".
Zuwa tayi ta soma kakkaɓe gadon yana tayata suna hira, bayan sun gama suka share ɗakin tare da wanke Toilet ɗin ɗakin, ita tayi Moping shi kuma ya koma kan sofa ya zauna yana latsa wayan sa
Bayan ta gama ta dawo kan hannun kujeran ta zauna tana kallon sa tace, "Yaya na gama maka bari in wuce sashin mu kar Mama taji ni shiru".
Ok my sister, Thank you so much, that's why I love you so much coz you are so kind".
She smiled and said, "Yayana kenan! I love you more than anyone else in this house. Kaima kana da kirki."
Tashi tayi tana nufan saman drower ta ɗau wayan ta tadawo tana kallon sa da shima ya kafe ta da nashi idanun, murmushi tayi masa tace, "Na tafi Yaya".
Miƙewa yayi ya rako ta har bakin ƙofa kana ya koma ciki yana zama saman kujera tare da aza kansa ya kwantar kan hannun yana lumshe idanun sa, murmushi kawai yake saki yana tuna ɗan kyakykyawar fuskarta, sosai yake matuƙar son ƙanwar tasa, kuma so na aure, burin sa kawai a rayuwa yaga ranan da zai mallaki Ɗahira a matsayin matar sa domin tayi masa tako ina, sai dai har yanzu ya kasa samun ƙwarin gwiwar tunkaran ta yace mata yana son ta
Ɗahira tana da wani irin kwarjini da zai yi wuya namiji ya tunkare ta da zancen so, shiyasaka tun tasowan ta bata taɓa yin saurayi ba duk da tana da farin jini sosai na mutane, a lokacin da suka je ABU Zaria karatun su na Degree yawancin Friends ɗin ta maza ne, kuma duk acikin su babu wanda ba so yake kawo sa wajenta ba but basu iya gaya mata.
Shima haka Baffa ya daɗe yana ƙaunar ta yana dakon son ta Amma har yanzu be iya sanar da ita ba, kuma duk abinda tace "yayi ko ya bari" yana bari, shi ɗin ma'abocin shan Sigari ne don wani lokacin har Alcohol yake korawa, amma babu wanda ya sani a gidan sai ita kaɗai kasancewar tana yawan zuwa ɗakin sa koda ba ya nan, wani lokacin sai tazo ta kwanta tayi barcin ta, yawan kusancin su dashi ne ya saka tasan wannan sirrin nasa, kuma tun sanda tace ya dena sha ya dena, sai dai har yanzu Sigari ne be dena gaba ɗaya ba, amma idan har zata gani zai yi ƙoƙarin ɓoyewa.
*WASHE GARI*
Ranan ne ya kasance ranan Walima, kowa idan ka gani agidan cikin farin ciki yake, sosai gidan ya sake cika sai hada-hada ake yi, har mutanen Maiduguri tushen su kenan duk sun hallaro, duk girman gidan nan sai da aka cika sa da mutane
Ƙarfe 02:00pm. Aka soma tafiya *AL'AMEEN FAMILY HOSPITAL* kasancewar acan ne za'ayi taron, haka motoci manya-manya suke ta jidan mutane suna kai su.
_Kar ku manta da_
*Share*
*Comments*
*Vote*
*Like.*
[5/21, 9:54 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
*NATSUWA A SALLAH*
_Manzon Allah mai tsira da aminci, ya ce, "sallah ba kome ba ce illa miƙa wuya da tawali'u..." Kuma ya ƙara da cewa, "Bawa bai samun ladan sallar sa sai gwargwadon abinda ya hankalta daga sallar." Watau, gwargwadon natsuwar mutum cikin sallah gwargwadon darajar da yake samu gun Allah. Don haka ne ma ma'aikin Allah ya ce, "Allah ba ya juya wa Bawa baya yana cikin sallah matuƙar bai waiwaya ba; idan ya waiwaya kuwa, sai Allah ya bijire masa."_
_Babu abin da yake kawo waiwayo cikin sallah kuwa sai gafalar Bawa da muƙamin Ubangijin sa, watau ya zama tamkar wanda ya tsaya yana ganawa da Ubangijin sa alhali zuciyar sa tana shagale da wani abin dabam. A kan wannan matsala ne Allah yake ce wa Manzon sa, da al'ummar sa ma, a cikin suratul A'ARAF aya ta 205:_
_"Kada ka kasance daga gafalallu."_
_In muka lura sai mu ga cewa ta ya ya kuwa gafalalle zai iya tunawa da muƙamin Ubangijin sa yana cikin wannan hali na rashin kula har wani abin tsoro ya auku? Bugu da ƙari, daman can ga shi Allah ya yi umarni a cikin suratul Ɗ.H., aya ta 14 da cewa:_
_"Kuma ka tsayar da Sallah domin tuna Ni"._
_In mutum ya Yi haka, ana fata ya rabban ta._
_Allah yasa mu dace._
*EPISODE four*
Babban haraban asibitin cike yake da mutane bila adadin, mutane ne kamar tsaki kama daga yara manya masu kuɗi da manyan likitoci duk an gayyace su, har ta da gwamna Malam Nasiru El Rufa'i sai da aka gayyace shi wajen, komi ana yinsa ne akan tsari gunun sha'awa
Ɗahira, Shakira, Yusra da Fadila can na hango su wajen zaman su daban, sosai su kayi kyau cikin shigan su na material fari ƙal da akayi masa ɗige-ɗigen Coffee colour, ɗinkin doguwan riga akayi musu fitted, sai suka yane kan su da Goldeen Veil tare da sanya Hill shoes shima Golden, sosai su kayi matuƙar kyau kamar ka sace su ka gudu sai faman haskawa suke yi kamar taurari
Nan akayi ta gabatar da komi cikin girma da arziƙi, daga ƙarshe aka gabatar dasu a matsiyin waɗanda ake taya murna tare da sauran sabbin ma'aikata da za'a ɗiba.
Wata kyakykyawar Farar mota ce ta shigo haraban asibitin, a hankali motar take tafiya har zuwa inda sauran motocin suke fake, tsawon mintuna 5 kafin aka buɗe motan ya zuro kyawawan ƙafafun sa kana ya fito a hankali yana rufe motan, kyakykyawar saurayi ne da aƙalla bazai wuce 32yrs ba, fari ne tarrr kamar kalatsa shi jini ya fito don har wani ɗaukan idanu yake yi, yana sanye da Milk ɗin riga me gajeren hannu da ya matse sa sosai, sai Blue Jeans tare da sanya Combat a ƙafafun sa shima blue, yana da yalwan gashin kai kwantacce baƙi siɗik tare da ɗan siririn sajen sa, Kallo ɗaya idan kayi wa Guy ɗin zaka tabbatar da ya haɗu ne tako ina, *USMAN NOOR AL'AMEEN* kenan, *(The Younger Doctor)* yaro kyakykyawa me Izza da Son nuna shi wani ne, ma'aboci Son gayu da son hutu
A hankali ya taka ya soma tafiya cike da taƙama ya nufi inda su Big Dady suke.
Har aka gama taron sannan kowa ya soma tafiya gida, sai yamma duk yawancin ƴan uwa suka soma watsewa sai gidan ya rage daga ƴaƴan Kaka sai jikokin shi suka rage waɗanda basu tafi ba, su ma ɗin a gobe duk za su watse su tafi
Washe gari ƙarfe 05:00pm. Na Yamma gaba ɗaya a halin gidan sun hallara a babban parlour bisa umarnin Kaka
Ɗahira ce tafito daga Part ɗin su don ita bata riga ta tafi ba, tana sanye da doguwar rigan atamfa kalan ja da ratsin Milk da ruwan ƙwai, rigan iyakan ta ƙwaurin ƙafafuwan ta kuma sosai tayi mata kyau ta sake fito da tsantsan kyawunta da kwarjinin ta, sai tayi Rolling da ɗan ƙaramin Veil da iyakan sa kafaɗun ta, Slippers ne a ƙafanta tana tafiya tana latsa waya, hira take yi da freinds ɗinta na Facebook sai faman doka murmushi take yi, gab da ta iso ƙofan da zata sada ta da General parlour taji tayi karo da mutum wanda hakan yasaka wayan ta ya zame ya faɗi ƙasa, a hankali ta ɗago kanta tana kallon sa
haka zalika shima ɗin dai-dai da sanda ya sauke nashi idanun cikin ƙwayan idanuwanta da yafi tsana cikin rayuwan sa
kallon sa kawai take yi babu ko ƙyafta idon
While shi kuma ya ɗaure fuska tamau yaja jikin sa ya wuce, gab da zai buɗe ƙofa ya tsinkayi zazzaƙan muryan ta tana cewa
"Ba ka ganin kayar min da waya ne?"
Cak ya tsaya yana juyowa ya kalle ta da tsananin mamaki da ya nuna a face ɗin sa, ita kuwa a lokacin kallon wayan nata da ya fashe take yi cike da tsananin baƙin ciki sannan ta ɗago kyawawan idanun ta tana kallon sa itama fuskarta a ɗaure
A hankali ya tako ya'iso gaban ta still yana ci gaba da kallon ta, duk da ya daɗe be ganta ba kuma tayi masa girma ainun but be yi tunanin cewa ta kai matsayin da har za tayi masa irin wannan maganar ba, shiru yayi yana ƙare mata kallo yayinda itama ɗin shi take kallo batare da ko alaman tsoro ya nuna a fuskarta ba, abinda ya ƙara ba shi matuƙar mamaki kenan, domin yasan ada babu wanda tafi tsoro sama dashi, idan har zata gan shi ko za taji sunan sa tsoro ne da fargaba suke kawo mata cafka, ko kaɗan bata haɗa hanya dashi bare magana ya haɗa su, duk inda akwai shi to ta haramta wa kanta wurin har sanda zai bar wajen
Kuma hakan ya samo asali ne tun sanda ta tashi da wayon ta take matuƙar tsoron sa, ba don komi ba sai tsananin azaban da yake gana mata da tsanar da yake nuna mata afili ko a ɓoye, shi kuwa tun sanda aka haife ta ya haɗa idanu da ita shikenan yaji ya matuƙar tsanar ta, ba don komi ba sai don ƙwayar idanun ta da ya kalla, sabida idan har zai kalle ta sai yaji faɗuwar gaba me tsanani tare da tsoro wanda hakan ne ya saka mishi muguwan tsanar ta cikin ran sa, sosai cikin ƙwayar idanun ta da suka kasance sky green suke bashi tsoro da fargaba, hakan yasa tun tana ƙarama ko ɗaukan ta ba ya yi, da zaran ya ganta duka ne abinda ke haɗa shi da ita, har zuwa kuwa girman ta da ta gane shi ɗin mugu ne, koda laifi sukayi ƴan gidan gaba ɗaya, to ita yake kamawa ya fanshe kaf dukan da zai yi musu akan ta, ko agaban waye babu wanda zai iya hana sa, kuma koda an hana sa sai ya san yanda yayi ya haɗu da ita ya gana mata azaba, Ɗahira ta tashi cikin tsoron sa matuƙa wanda ya haddasa mata tsanar sa fiye da wanda yake mata, kwata-kwata bata ƙaunar sa bata ƙaunar ganin sa koda jin sunan sa ne, ta saka wa kanta shi ɗin maƙiyin ta ne wanda babu wadda tafi tsana a duniya sama dashi
Wajen shekara 9-10years kenan babu shi a ƙasan, yana can ƙasar Turkey yana aiki acan, tun sanda ya tafi karatu ya zauna can sai dai yazo gaishe su, Ɗahira ta dena jin tsoron sa ne don kawai daɗewan da tayi ba ta ganin shi, and sai kuma girma da yazo mata, yanzu baza ta taɓa juran abinda yayi mata a baya ba, domin ita tana ganin ta wuce matsayin da zata zauna wani banza wanda ba iyayen ta ba ya duke ta bare har taji tsoron sa.
Sauke kansa yayi kan wayan yana kallo, sai kuma ya mayar da idanun sa kanta yana sake ɗaure fuska ya ɗaga ƙafan sa ɗaya ya ɗaura saman wayan ya soma murje ta da ƙaton takalmin sa da ya kasance tamkar irin na sojoji, babu abinda ake ji sai sautin ƙaran fashewan wayan
Ita kuwa Ɗahira sauke idanun ta kan ƙafan sa tayi tana kallon wayan yayinda taji hawaye sun ciko mata idanu sabida tsananin baƙin ciki da yazo mata iya wuya, still ɗago kanta tayi tana kallon sa cike da zallan tsana da ya nuna a cikin ƙwayan idanun nata
shi kuma hawayen da ya gani a idanun nata shi ya saka shi jin wani farin ciki tare da sanyi a ransa, magana ce a bakin sa yake son faɗa mata amma girman kai da Izza sun hana sa buɗe bakin, illa juyawa da yayi ya nufi ƙofa ya buɗe ya shige..
Ƙaran rufe ƙofan ne ya saka ta ƙyafta idanun ta wanda hakan ne yasa hawayen ta daman zubowa suka sauka kan kuncin ta, ahankali ta sake mayar da idanun ta kan wayanta da ya gama murƙushe ta duk screan ɗin ya farfashe babu kyan gani, wasu zafafan hawayen ne suka soma sintiri a face ɗin ta, tayi saurin saka hannu ta soma sharewa domin baza ta bama kanta daman nuna raunin ta kan shi ba, dole ne ta nuna masa yanzu ba irin da bane, dole ta nuna masa ba ta tsoron sa, kuma duk abinda yayi mata BASHI ne ya ɗauka dole sai ya biya, don haka ɗaukan wayan tayi ta nufi ciki itama da sauri.
_To fa nan ake yinta, bari muga me zai faru?_
_kar ku manta ku suburbuɗo min Comments ta hakan ne zai bani daman ƙara muku yawan Page._
Plz
*Share and Vote.*
[5/21, 9:54 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏻
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
. *EPISODE Five*
Da shigan ta darect wajen Kaka ta nufa, ta sami waje kan hannun kujeran dake kusa da Wheel chair ɗin sa ta zauna tana sauke kai ƙasa
"Matata lafiya wa ya taɓa min ke?"
Abinda ya saka yayi mata tambayar ya santa idan har tazo wuri dole sai ta tsokane shi, ƙa'ida ne sai taja masa gemu kafin ta nemi wurin zama
Ɗago kanta tayi tana kallon sa sai kuma ta soma wurwurga idanun ta tana kallon mutanen wurin da duk suka nutsu suna kallon ta, a kan Usman dake zaune kusa da Abbun ta ta sauke idanu, yayin da shi kuwa wayan sa yake latsawa ko sanin Allah yayi ruwanta be yi ba
"Tell me my wife. I can't calm down idan ban san abin da ke damun ki ba?"
Dawo da idanun ta kan Kaka tayi cike da marairaice fuska tace, "Kaka Ya Usman ne ya fasa min waya, kuma ya saka ƙafa ya tattaka shi da gangar".
Kaka salati yayi yana kallon wayan dake hannun ta kana ya mayar da idanun sa kan Usman da har yanzu yaƙi ya ɗago kansa duk da yana jin abinda ake yi, shi har a lakocin mamakin yarinyan yake yi ainun, "yaushe har ta samu ƙwarin gwiwar da har zata kawo ƙarar sa? Lallai yarinyan nan dole ya koya mata hankali".
"Fodio, why did you break my wife's phone?"
Shiru yayi batare da ya ɗago kan sa ba, kuma be dena latsa wayan ba
"Kai ba magana ake maka ba? Are you crazy? Uban meyasa ka fasa mata waya? Ka dawo kenan zaka soma takura mata ko?" Big Dady yayi maganar a zafafe yana kallon sa
Sai a lokacin ne Usman ya ɗago kai fuskar nan a ɗaure yana kallon su, sai dai be iya cewa komi ba
Abba yace, "miƙo wayan mu gani uwata".
Miƙa masa wayan tayi, ya'amsa yana juyawa sai ya ɗago yana kallon ta yace, "Agarin ya yafasa miki wayan?"
"Mun yi karo ne shine ya faɗi, da nayi masa magana shi ne ya dawo ya tattaka min da takalmin sa".
"It's your fault, why did you talk to him then? Stop following her shit please". Abbu yayi maganar yana amsan wayan daga hannun Abba and put it aside
Big Dady said, "why doesn't she talk and break her phone?"
Sai kuma ya mayar da kallon sa ga Usman ɗin yace, "Make sure you buy her her phone and pay for it, idan ba haka ba zan mummunan saɓa maka kana jina ko?"
Gyaɗa kan sa kawai Usman yayi yana kallon Ɗahira da kanta ke ƙasa, kawai tunani yake yi a ransa abinda zai yi mata idan har ta shigo hannun sa
Kaka ne yace, "ya isa haka Lawal (Noor), karka ɗau abinda zafi haka mana, yanzu mu mayar da hankali kan abinda ya tara mu. Alhmadulillah and Allah show us this time to see my grandchildren finish their studies and become doctors now, don haka na tara ku in sanar muku da Albishir da na tanadar muku".
Murmushi yayi yana kallon su ɗaya bayan ɗaya kana yaci gaba da cewa, "Zuwa nan da Sunday motocin ku da na siya muku za su iso sai kowa ya zaɓi wanda yake so, wannan shi ne kyauta na a gare ku, sannan ina jan hankalin ku ku mayar da hankali wajen aikin ku, abinda ya kai ku shi za kuyi ba na son wasa,
May God help you all. May God bless you."
Duk ka parlour'n suka amsa da ameen ban da Usman da har yanzu latsa wayan sa yake yi, nan ɗaya bayan ɗaya suka yi ta mishi godiya kana ya kalli Usman yace
"Kai kuma Fodio, the opportunity I have given you is enough. dole ne ka dawo Nigeria kaci gaba da aiki a asibitin mu, domin baza mu zira idanu ace kana can kana ma Nasara aiki suna ƙaruwa mu nan ka bar mu haka ba".
Usman da ya ɗago kansa yana kallon Kaka, a karo na farko yace, "wai Kaka meyasaka kake son takura min ne? I don't want to work here. I want to.."
Be dire maganar ba Big Dady ya daka masa tsawa, hakan yasaka shi yin shiru yana kawar da kai still fuskan sa ba walwala
"Umarni ake baka ba shawara ba ka ajiye aiki ka dawo nan kaci gaba, karka sake mu ƙara ja'inja da kai". Big Dady ya faɗi maganar da kakkausar murya
Murmushi Kaka yayi yace, "ka bar shi nace Lawal; ba na son kana nuna masa zafi, ai ba cewa yayi bazai dawo ba, abi shi a sannu, kowa zai iya tafiya. idan kuma da me magana ko ƙorafi akan wani abu sai yayi magana".
Kafin Kaka ya rufe baki Usman yayi saurin tashi ya fice, haka sauran ma su kayi ta tatashi suna ficewa ya rage daga Kaka sai su Big Dady
*****
Hajja Fatu ce ta shigo parlour'n Hajiya da sallama
Hajiya wacce ke zaune a parlour ta'amsa mata sallaman sannan tayi mata maraba
Zama Hajja Fatu tayi tana kallon Hajiya da murmushi a face ɗin ta tace, "Oh ashe haka abu ya faru? Na zo miki jajen abinda Ɗahira tayi wa Usman ne, gaskiya bata kyauta ba".
Hajiya tace, "Haka ne. amma shima da laifin sa ai, da be taka mata wayan ba baza ta kawo ƙarar sa ba".
Ɗan taɓe baki Hajja Fatu tayi tace, "eh Haka ne kamar yanda ki kace, amma abinda tayi ai be kamata ba, wannan ai kamar tana so ta haɗa Ɗa da uba ne, ko ba kya ganin yanda Mahaifin sa ya nuna fushi dashi? Kuma da ba haka yake nuna masa ba, don Ni kai na shaida ce wajen ƙaunar da yake masa, amma a kan ta ya rufe idanu ya suburbuɗa masa faɗa a gaban ƙannin sa, wannan abun ba yi bane, idan ma uwarta take zugo ta ai zamu gani".
Shiru Hajiya tayi tana sauraron maganganun Hajja Fatu, kuma da alamun sosai zancen yake shigan ta duba da yanda fuskarta ta sauya, domin abinda aka yi wa ɗan nata dama be mata daɗi ba, amma kuma maganganun Hajja ya sake saka ta taji haushi matuƙa
Ita kuwa Hajja Fatu ganin haka ya saka ta sakin wani shu'umin murmushi tana cewa, "Ai sai haƙuri amma dai na san yarinyan nan yanzu hure mata kunne ake yi, ada ai ba ta yin haka duk kuwa da cewa yana dukan ta, amma yanzu tunda ana son haɗa sa da ubansa ai an koya mata yanda zata riƙa kawo ƙarar sa, kin ga hakan zai sa Mahaifin sa ya riƙa fushi dashi".
Hajiya kallon Hajja Fatu tayi don da alamun kalaman nata sun gama ratsa ta sosai tace, "nima naga alamun haka Hajja, sai dai ko ma wa ya koya mata da duk abinda suke nufi da ɗana sai dai ya koma kan su, babu wanda ya'isa ya shiga tsakanin ɗana da mahaifin sa, dole ne ma in ja masa kunne babu ruwan sa da ita tun wuri ya fita harkan ta, ba na son abinda zai saka mu sami saɓani, domin akan ɗana babu abinda bazan iyaba, kowa ya san da cewa ina matuƙar ƙaunar sa; don zan iya yin komi akan sa".
Ajiyan zuciya Hajja Fatu ta saki tana kallon Hajiyan da alamun nuna damuwa a fuskarta tace, "gaskiya ne Hajiya, gwara dai ayi wa tufkan hanci tun kafin magana tasha banban, Allah ya kyauta gaba to, Ni bari in tashi na tafi".
"To shikenan Nagode sai nima na leƙo". Cewar Hajiya da murmushi a fuskarta
Tashi Hajja tayi ta nufi ƙofa ta fice tare da barin Hajiya cikin tunani. Tana fita ta saki wani shu'umin murmushi fuskarta cike da farin ciki, dama abinda take so kenan kuma tana ganin da alamu tarkon ta ya fara kamawa, taku ɗaya zuwa biyu tayi ta tsaya tana juyowa ta kalli ƙofar parlour'n Hajiya, a fili ta furta
"Now the game has started. If I am Hajja Fatu, I will open the heart of everyone in the house. I will make everyone hate you, A'ishah. tare da ƴarkin da kika ƙwallafa rai a kan ta, zan maye gurbin zuciyar kowa da ƙauna ta a ran shi, zaki san kin shigo cikin Familyn da ba na ki ba, mu zuba dani dake.."
"Hajja ke da wace ce zaku zuba? Me tayi miki?"
Da sauri Hajja ta juyo tana kallon ta, wani irin bugawa zuciyar ta tayi, nan da nan tsoro da fargaba ya ɗarsu a cikin zuciyarta har bata san sanda ta fiddo idanu waje ba suna kallon kallo..
_Hhhh to Fans shin wa kuke tunanin wacce Hajja ta gani haka har ta sorata ainun?_
_karku manta da Comments, domin comments ɗin ku shi ke saka na ƙara yawan post._
[5/21, 10:02 PM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT* 🧝🏻
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
*TUNATARWA*
```Manzon Allah mai tsira da aminci, ya yi mana bayani a kan sallah da abin da Bawa yake iya samu. Cewa ya yi, "Yana yiwuwa mutum ya kawo sallah ga baki ɗayan ta amma a ba shi lada wadda ba ta wuce sudusin ta ko ushurin ta ba." Abin da yasa haka kuwa shi ne rashin nutsuwa cikin sallah.
Allah yasa mu dace.```
*EPISODE Six*
Murmushi Hajja Fatu ta ƙirƙiro cikin tsananin ruɗewa da son ɓoye halin da take ciki tace, "am..uhmm babu, auhm Ni da wata ƙawata ce da taci amana ta". Taƙarishe maganar tana sake sakin murmushi
Ɗahira kuwa kallon ta kawai take yi, domin kuwa duk abinda ta faɗa ta riga taji, sai dai tayi tsananin mamaki da al'ajabin abinda Hajja Fatu take faɗa akan Mahaifiyar ta da ita kanta. ita ma ɗin nuna mata tayi kamar bata ji maganar nata ba illa sakin murmushi da tayi tace, "But Hajja, why don't you forgive her? I don't see the point in keeping a person in mind."
Wani irin ajiyan zuciya Hajja Fatu ta saki jin cewa ta yarda da abinda ta faɗa mata, hakan na nufin bata ji maganar da tayi ba kenan, murmushi ta sake ƙirƙirowa tace, "ƴata baza ki gane zafin cin amana ba, amma tunda kin ce in yafe ai Ni me iya yafe mata ne, nima sai yanzu na gane hakan be da wani amfani muyi ta sa'insa akan abinda be kai ya kawo ba".
Sai kuma ta sauya akalan maganar da tambayarta "ina zaki je kika yo nan?"
Ɗahira said, "I will reply to Mamana's message,"
Gyaɗa kanta Hajja Fatu tayi tace, "ok".
Sannan ta juya ta tafi batare da ta sake furta komi ba
Ɗahira kuwa bin bayan ta tayi da kallo har sanda ta ƙule wa ganin ta, maganganun Hajjan ne suka dawo mata
"What does that mean?" Tafaɗa aranta tana sake zurfafa a tunani
Tabbas ta san akwai abinda Hajja ke shiryawa akan Mahaifiyar ta, sai dai kuma duk yanda za'a yi baza ta taɓa bari taci nasara ba, tun farko dama tasan Hajja Fatu ba ta ƙaunar Mahaifiyar ta, Kasancewar ita A'isha wato Aunty Amarya Asalin ta ƴar Soba ce a ƙaramar hukuman Zaria, karatu ya kawo ta Kaduna tana zaune wajen auntyn ta, to anan ne Mijinta Al'ameen ya ganta har ya'aure ta, tun sanda aka kawo ta gidan Hajja Fatu ta nuna ba ta ƙaunarta kuma take son nuna ita ɗin bare ce acikin su, sabida alokacin ƙanwarta dama ta daɗe tana ƙaunar Al'ameen wato Abbu, to hakan ya saka ta ɗau alwashin sai ta fid da Aunty Amarya a cikin gidan ko ta halin ƙaƙa, don a cewarta tunda ƙanwarta bata same shi ba duk a dalilinta, to, itama sai ta rasa shi
Numfashi Ɗahira ta sauke tana ɗauke kanta daga kallon Hanyan da Hajja Fatu tabi, ko kaɗan baza ta so ta faɗa wa Mahaifiyarta wannan maganar ba, domin ta san hankalin ta zai tashi matuƙa, sai dai zata dage da taya ta da addu'a duk wani wanda ke binta da sharri ya koma masa
takawa tayi ta shige Parlour'n Hajiya da sallama
Hajiya da har yanzu take zaune tana tunanin maganar Hajja Fatu, ta ɗago kanta tana bin Ɗahira da kallo, fuska babu walwala ta'amsa mata sallaman
Ita kuwa Ɗahira ƙarisowa tayi ta zauna a kujera tana kallon Hajiya tace, "Hajiya sannu da hutawa".
"Yauwa". Hajiya ta'amsa ataƙaice tana sake tamke fuska
Sosai Ɗahira tayi mamakin halin da Hajiya ta nuna mata, domin ta san ta mace ce me fara'a, kuma suna ɗasawa da ita ainun, tayi mamaki da ganin sauyawar fuskarta amma kuma sai ta dangana hakan da ko wani abun ne ke damunta, don ko kaɗan bata yi tunanin abinda ya faru ɗazu ba
"Hajiya dama Mama ce tace inzo in amsar mata saƙo".
Miƙe wa Hajiya tayi batare da ta tanka mata ba ta shige ɗaki, sai gata ta fito da leda ta miƙa mata
Amsa Ɗahira tayi cike da girmamawa ta tashi ta fice
Ita kuwa Hajiya rakata tayi da harara tana jan tsaki
Ɗahira da har ta fice sai da tajiyo sautin tsakin, hakan yasaka taja ta tsaya tana kallon ƙofar, nan take kuwa abinda ya faru ɗazu ya dawo mata kwanya "kenan Hajiya tana fushi da ita ne saboda abinda ya faru ɗazu?" Ta tambayi zuciyarta cike da mamaki, taɓe bakin ta kawai tayi tajuya tayi tafiyar ta, Part ɗin Hajja Fatu ta shige, babu kowa a parlour sai ta nufi ɗakin Shakira kanta tsaye, tana isa ta tura ƙofar ta shiga da sallama a bakin ta
Shakira dake zaune gaban mirror tana gyara kayan kwalliyan ta ta ɗago da kanta tana kallon ta, sai kuma ta saki murmushi tana cewa, "ƴan mata adon gari me aka kawo min ne?"
Ƙarisawa kusa da ita Ɗahira tayi tana jingina da bango tace, "a'a Ni babu abinda na kawo miki, amsa dai nazo yi, kin san yanzu wayata ta samu matsala shiyasa zaki haɗo min kan Littafaina in tafi dasu".
Dariya Shakira tayi tace, "kai wlh Ƴanmata yau kin bala'in burge Ni, ashe zaki iya kai ƙaran Ya Usman? Shin wai ina tsoron da kike mishi ya tafi?"
Taɓe baki Ɗahira tayi kana tace, "ai dama ɗan hakin da ka raina wataran shi ke tsole maka ido, kema da kanki kin faɗa da ba yanzu ba, Ɗahiran Da; da na yanzu sun sha banban".
Miƙe wa Shakira tayi tana sakin murmushi tace, "gaskiya ne ƴan mata, don yanzu ba lokacin Da damuke yara bane, yanzu mu ɗin DOCTORS ne manyan yara, kinga kuwa baza mu iya ɗaukan raini ba, wlh kin burge Ni amma Ni kam ba na tunanin zan iya fa".
"Dama ai ke matsoraciya ce, Ni dai ɗauko min in tafi Mama jira na take yi".
Drower Shakira ta buɗe ta soma kwaso mata Books ɗin tana cewa, "hmm baza ki gane bane, Ya Usman ya wuce gaban kwatance, wlh ko wacce mace idan har zata haɗu dashi sai dai ta kalle shi da idon soyayya amma ba faɗa ba, kwarjinin sa da kyawun sa tare da isa da izzar sa su kansu sun ishe ka, ina matuƙar shakkan Ya Usman kuma ba na son abinda zai haɗa ni dashi da har zai saka mu saka ƙafan wando ɗaya dashi, but ke kam nasan kashin ki ya bushe wlh don ba ƙyale ki zai yi ba, ya lafiyan Kura ma bare ace tayi hauka, uhmm ke dai kawai ki guji ranan haɗuwan ku".
Ɗahira takowa tayi tazo gaban ta ta soma kwashe Littafan tana zubawa a leda, batare da tabi ta maganarta ba tace, "Ni kin ga tafiya na ba ni da lokacin ku daga ke har shi ɗin".
Tajuya tayi ƙofa zata fice, dai-dai lokacin da Yusra ta turo ƙofan ta shigo suka kalli juna suka ɗauke kai sannan ko wacce ta wuce
ƙarisowa Yusra tayi kusa da Shakira dake zaune bakin gado; itama ta zauna gefen ta tana cewa, "wai ya maganar mu na zuwa shopping yaushe za mu je?"
Shakira tace, "ki bari a kawo mana Mota mana, kin ga sai muje aciki ko ya kika ce? Don Ni wlh bazan fita a tsohuwar mota ba, gwara muje muna tsole idanun Gayu"
Dariya Yusra tayi tana cewa, "shegiya inda ba'a ce za'a ba mu ba fa? ya za kiyi dole ki fita a ciki".
"Uhm baza ki gane bane amma dai gwara mu bari sai ranan Sunday ɗin muje, kin san har gidan su Marcy za muje ranan wlh".
Hannu Yusra ta bata suka kashe tana cewa, "gaskiya ne Tawan ai wlh yanzu ma kika tuna min da ita, ahh ai dole ne ma muje, kai wlh har kin sani na ƙosa ranan tazo, uhmm Allah ya kai mu har na hango irin wulaƙancin da zanyi".
Sai suka kwashe da dariya suna sake tafawa
Shakira tace, "kin san yanzu muka gama hiran ki da mutumiyar taki?"
"Wace kenan?" Yusra ta tambaye ta cike da rashin fahimta
"Wace kika sani ban da Ɗahira, Ni na rasa meyasaka ba ta ƙaunar ki duk sanda zamu zauna sai tayi maganar ki, abun mamakin ma yanda tayi ta zagin Ya Usman anan wajen, uhmm duk wai akan waya".
Ɗaure fuska Yusra tayi tace, "wlh yarinyan nan akwai ranan da zan cire mutunci mu goge raini, ni fa na gaji da kawo miñ ƙarar ta da kike yi a kaina tana zagi na, wlh zan je inji dalilin da ya saka take zagi na". Tana ƙarike maganar ta miƙe da ninyar tafiya
Shakira tayi saurin riƙe ta tana cewa, "ke kuma meye haka? Yau ta soma zagin ki da zaki damu? Wlh idan baki iya kama ɓarawo ba sai ya kama ki, yanzu idan kika je sai kice mata mene? ki bari duk ranan da kika kama ta tana maganar naki sai ki ɗau mataki amma ba yanzu ba, kuma menene na damuwa tunda gani ina faɗa miki komi?".
Yusra dake tsaye har yanzu kallon Shakira take yi har ta dire aya kana ta ɗaura da nata, "But wlh today I have to tell Hajiya everything, dama ina ɓoye mata ne ban son hankalin ta ya tashi". Daga haka ta juya ta fice fuuu kamar ana tura ta
Tana fita Shakira ta saki murmushi tana cewa, "Dama haka nake so gwara kije ki faɗa ma Hajiyar ki don ta ƙara ƙullatan ta, shegiya Ni wlh ba ƙaunar Ɗahiran nan nake yi ba, da wani idanu sai kace na fataken dare, kai ko a turawan ma bana tunanin akwai masu irin wannan idanun.."
Ƙaran buɗe ƙofarta shi ya katse mata maganar ta, tayi saurin juyawa tana kallon me shigowa, ganin Mahaifiyar ta ne ya saka ta sauke ajiyan zuciya har da dafe ƙirji
ƙarisowa wajen ta Hajja Fatu tayi tana kallon ta tace, "What happened to Yusra leaving here in a rage?"
Dariya Shakira ta kwashe dashi tana cewa, "me kuwa zai faru in ba zugo ta da nayi ita da Ɗahira ba, ai yau sosai na fusata ta don har maganar Ya Usman nayi mata, yanzun ma Mahaifiyar ta za taje ta sanar ma wa".
Sai kuma ta kuma kwashe wa da dariya tana cewa, "wlh da ma maganar ya koma kunnen Ya Usman inga yanda zai yi ƙulun kubura da ita".
Hajja Fatu itama dariyan tayi tace, "yauwa ɗiyar albarka ai gwara da kika zugo ta ɗin, idan ta sanar wa mahaifiyar ta na san yanzu gaba ta soma ita da A'isha, hmmm mu zuba yanzu ma aka soma".
Wannan shine halayyan Shakira da Mahaifiyar ta, ko ince ƙudurun su akan Ɗahira da Maman ta
Yusra da Ɗahira basu shiri tun farko; sakamakon zigin da Shakira take yi a tsakanin su batare da sun sani ba, ita Yusra akwai zafin kai da saurin fushi, tun farko dama ba wani shiri suke yi da Ɗahira ba, hakan yasaka Shakira ta samu dama take ƙara wa abun wuta, duk idan suka zauna tare da Yusra sai ta ce mata, "Ɗahira ta zage ta, ko tayi gulmanta", hakan yasaka Yusra ko magana ta dena ma Ɗahira kullum kallon ta da abun take yi, ita kuma Ɗahira dama ba me son shiga harkan da babu ruwan ta bane bare kuma idan ana mata wulaƙanci, don haka itama ɗin sai ta fita harkan ta a cewar ta "duk ranan da ta sauko ta dena ɗaga mata kai sai su ci gaba da mutunci" kuma dama Ɗahira tana ganin itace Babba babu yanda za'a yi ta zauna tana bin ƙanwar ta don kawai tana son su shirya tunda ta san bata yi mata komi ba, duk da su huɗun ba wani tazara ne a tsakanin su ba duk sa'annin juna ne, sai dai Ɗahira aka fara haifa yanzu haka shekarun ta 25years and Two Month, sai Shakira me shekaru 25years cif-cif, sai kuma Yusra me 24years and 8month, maraban su da Fadila kwana goma ne
Gaba ɗaya ahalin gidan halayyan su ɗaya ne na jijji da kai da nuna taƙama, sai dai na wasu ya fi na wasu ne musamman ma Usman da ya fi kowa a gidan, kuma hakan a jinin su yake.
_Hmm now the game has started because there is a lot cakwakiya in this family, just go ahead and follow me and suburbuɗo me a comment to get more Post.
[5/22, 10:47 AM] Oummu Ɗahirah: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*FAMILY DOCTORS*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_
*SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT*🧝🏻
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*🌞
```( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_
*EPISODE Seven*
Sallama tayi ta turo ƙofar ta shigo, Aunty Amarya dake zaune gefen gado ta'amsa mata tana kallon ta
ƙarisowa tayi ta zauna kusa da ita tare da miƙa mata ledan tana cewa, "Ga shi Mama".
Bata amsa ba tace da ita, "Where have you been waiting for me?"
Ɗahira tace, "na je wajen Shakira amsan Littafaina ne".
Gyaɗa kai kawai tayi tana ɗaukan ɗan kitt ɗin dake gaban ta ta miƙa mata tace, "ga shi Abbun ki ya ce in baki kyautar sa ne".
Saurin miƙa hannu Ɗahira tayi ta'amsa tana buɗe wa, murmushi ta saki ganin danƙareriyar sarƙan gwal kana ta kalli Maman nata tace, "ina Abbu ɗin?"
"Ya fita, Ni kuma ki riƙe wannan ledan da kika amso sai ki ɗinka".
Dariyan farin ciki Ɗahira ta saki kana tayi mata godiya tare da nuna murnan ta a fili, buɗe ledan tayi ta soma duba wa, atamfofi ne guda biyu masu kyan gaske sai kuma Material guda ɗaya
"Mama Nagode sosai Allah ya saka da alheri".
Murmushi Aunty Amarya tayi tana kallon tilon ƴartan cike da so da ƙauna tace, "ki dena godiya tunda ya zama dole ne mu yi miki".
Daga nan miƙe wa Ɗahira tayi zata fita, Aunty Amarya ta kira ta ta dawo, sake zama tayi inda ta tashi tana kallon Mamar nata
Ita kuwa cikin sauya fuska tace, "Meyasaka kika kai ƙarar Usman don ya fasa miki waya?"
Shiru Ɗahira tayi tana sunkuyar da kai ƙasa
"I don't want to hear it again, do I?"
Gyaɗa kanta tayi
"Tashi ki je Allah miki albarka".
Sai da ta'amsa da "ameen". Before leaving
Tana fita ɗakin su ta shiga
Fadila na kan gadon ta tana latsa waya sai faman doka murmushi take yi, idan za'a rantse ma bata san da shigowan ta ba
ita kuwa Direct wajen gadon ta ta nufa ta'ajiye kayan hannun ta, fiddo kayan tayi tana gani, har ta gama dubawan ta'adana sannan ta dawo ta zauna ta ciro Books ɗin ta zube su saman gadon
dai-dai lokacin ne Fadila ta ɗago kai ta kalle ta, nan idanunta suka faɗa kan NOVELS ɗin dake zube kan gado, da sauri ta'ajiye wayan ta tataso ta nufo wajen ta tana zama kan gadon;, ta saka hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin litattafan, cikin farin ciki ta ɗago tana kallon Ɗahira tace, "Hey Sis Where did you get this book?"
Ɗahira da take riƙe da ɗaya daga cikin litattafan me suna *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* tana dubawa ta bata amsa, "It's mine".
"Wayyo Allah wlh na daɗe ina neman Littafin *RAUDHAN* nan amma ban samu ba, Please ki ara min in karan ta, sosai nake son Littafan *JIKAR LAWAL GOMA* amma na rasa inda zan samu, ko da naje kasuwa nayi yawo but Allah be sa na samu ba".
Ajiye Littafin hannun ta tayi tana kallon ta tace, "Ni kam samun littafan ta ba ya min wuya, idan kina so sai ki bari adawo min da wayata in saka ki group ɗinta".
Murmushi Fadila tayi tace, "Thanks Sis, kai wlh har naji daɗi! na ƙosa naga ƙarshen abinda zai faru tsakanin *RAUDHA* da Captain Rayyan".
Miƙe wa Ɗahira tayi ta shige Toilet ta bar Fadila nan zaune har ta soma karanta NOVELS ɗin.
_If you need my Book so contact me on this Number 07065334256._
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫
Tun sanda ya fito General parlour ya nufi part ɗin su, cikin ɗakin sa ya shiga ya rufo ƙofan, Direct gaban Royal Bed ɗin sa ya nufa ya zauna a bakin gadon, har a lokacin be saki fuskar sa ba sai dai baza ka iya gane a halin da yake ciki ba, ya jima ahaka yayi shiru yana tunani sannan daga baya ya miƙe ya soma haɗa kayan sa cikin trolly, bayan ya gama Toilet ya shiga be jima ba ya fito ya bar ɗakin, yana fito wa parlour ya tarda Hajiya zaune tana kallo, a hankali ya taka ya'iso wajen ta ya sami waje kan sofa ya zauna
Hajiya kallon sa tayi tace, "Dama kana ciki?"
Gyaɗa mata kai kawai yayi yana mayar da idanun sa kan t.v
kallon sa Hajiya take yi tana karantan yanayin sa, duk da ta san halin ɗan nata ba kasafai kake gane alƙibilan sa ba, kiran sunan sa tayi
hakan ya saka ya juyo yana kallon ta sai dai be amsa mata ba
"Ina son ka fita harkan yarinyan nan ba na son ko kaɗan wani abu ya sake haɗa ku, yanzu ba kamar Da bane".
Usman kallon ta yake yi a rashin fahimta, don be fahimci abinda take magana akai ba, sai dai kuma bazai iya buɗe baki ya tambaye ta ba
itama Hajiya ganin yayi shiru be ce komi ba; sai taci gaba da kallon ta don ta san ba amsa mata zai yi ba
sai da yaja lokaci a zaune a wajen be yi abinda ya kawo sa ba kafin daga bisani daƙyar ya buɗe baki yace,"I'm leaving".
Kallon sa tayi batare da ta gane me yake nufi ba
hakan ya saka ya kawar da kai yana ɗan motsa bakin sa
"Ina zaka je?" Ta tambaye sa don ita bata gane inda za shi ba
In a calm and proud voice he said, "Turkey".
Hajiya tace, "kamar ya zaka koma kai da kace sai kayi kwana biyu?"
Shiru yayi
"Are you talking quietly?"
"I have a job there."
Shiru tayi tana kallon sa, shi kuwa ya kau da kai don be san ma su haɗa idanu
"Shikenan amma ka bari sai gobe sai ka tafi, yau dai ka haƙura".
Be ce komi ba ya miƙe ya nufi ɗakin sa, yayinda ita kuma taraka sa da kallo tana mamakin irin halin sa
Shi kuwa yana shiga keey ɗin mota ya ɗauka ya fito ya zo ya wuce Hajiya still tana bin sa da kallo
parcking space ya nufa ya ɗau motar sa ya bar gidan.
⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫
*WASHE GARI*
Wajen ƙarfe 05:30pm. Na yamma Ɗahira na zaune saman gadon ta tana karatun Novel *(JARUMAI na Jikar Lawal Goma).*
Fadil ne ya shigo ɗakin kamar an hankaɗo shi ko sallama, wajen ta ya nufa yana dariya yace, "Aunty, are you still here?"
Kallon sa kawai take yi batare da ta furta komi ba
sai ya sake sakin dariya yana cewa, "Yaya Usman ne ya bani saƙo in baki shi ne naje ɗakin Kaka neman ki ashe kina nan kina faman karatun Novel, Wai me kuke karantawa aciki ne?" Yaƙarike maganar yana kai hannun sa kan littafin
Buge hannun sa tayi tana hararan sa tace, "kai ba na son iskanci; Yi abun da ya kawo ka ka ware".
Miƙa mata Leda yayi tare da wayan ta da aka farfasa yace, "ga kwaraɓaɓɓiyan wayan ki inji Kaka".
Bata ce komi ba ta'amsa tana ajiye wa taci gaba da karatun ta
shi kuma Fadil tsayawa yayi yaƙi tafiya yana kallon ta
Ɗago kyawawan idanuwan ta tayi ta maida kansa, "What's stopping me?"
"Aunty Ɗahira ki bani wannan wayan mana tunda kin ga kin samu wata".
"What are you talking about now?" Ɗahira ta tambaye sa still tana kallon sa
Ɗan turo baki yayi yace, "ai gaskiya na faɗa ba kwaraɓaɓɓiyan ba ce?"
Hannu tasa da ninyan riƙo sa yayi saurin matsawa ya nufi ƙofa yana mata dariya
"Idan na kama ka Fadil.." Sai tayi shiru tana ƙwafa sannan taci gaba da karatun ta
Fadil yace, "to inzo in amsa Aunty?"
Bata kula sa ba Amma kuma sosai ya'ishe ta; don ita ba ta son hayaniya da yawan surutu, shi kuma Fadil ya san ba ta so shiyasaka yaƙi tafiya sai magana yake mata yana son ya ƙule ta, ko kuma taji haushi ta ba shi wayan ya tafi, sai da ya gaji don kan shi sannan ya fice batare da ta sake kula sa ba
Yana fita ta'ajiye Littafin don tunda ya fara surutun sa ta dena fahimtar Book ɗin, ledan ta buɗe ta ciro wayan dake cikin kwali, sai da ta gama jujjuya ta ahaka kafin ta taɓe baki tana buɗe wayan, the same irin wayan ta ne, Simcard ɗin ta ta cire ta saka a ciki sannan ta kunna tare da gyara zaman ta tana murmushi ta soma latsa wayan.
0 comments:
Post a Comment