*******************
Hajara tana kwance tana chatting da kawayenta a group taji shigowar messages. Tana dubawa hotuna ne kamar bazata bude ba don bata da data sosai sai ta bude daya. Zumbur ta mike ta bude sauran. Babu shakka ita ce a duka hotunan biyar. Wadda ta turo cewa tayi ga wani style din pre-wedding pictures. Nan da masu cewa sunyi kyau da masu zaginsu. Wani gumi ne taji yana karyo mata lallai baa shaidar mutum, yarinyar da kullum take shigar mutumci ita ce a haka. Tsam ta tashi ta dauki mayafi ta sauka kasan gidanta wurin makociyarta. A'a Hajara shigo mana ina kitchen...a sanyaye ta karasa dama wani abu zan nuna miki a waya. Maimakon kiyi min forwarding, menene mu gani. Ruwan ruden tuwon da take ne ya fallatso mata a hannu da gefen fuska saboda tsabar rudewa. Na shiga uku ni Hadiza me zan gani haka. Hajara tace a group na gani shiyasa na nuna miki don nasan wace Hafsi. Muciyar ta karba ganin yadda hannun Hadiza ke rawa ta karasa mata tuwon. Daren ranar bata yi baccin kirki ba. Mijinta zai tafi office ya ajiyeta a gida duk da bata fada masa abinda ke faruwa ba yasan babu lafiya.
A falo ta hadu da Baffa zai fita ta gaishe shi. Lafiya dai Hadiza irin wannan sammako ko duk saurin ki taya ni cin kosai ne. Murmushin karfin hali tayi. Baffa akwai wasa sai dai baya sake wa yara suyi yadda suke so. Ganin bata biye mishi ba ya mike muje ciki. Mama na shafa mai suka shigo dakin. Hadiza lafiya kuwa...
nan taji tsoron nuna musu hoton sai dai tasan yadda irin hotunan nan ye kawo a social media. Wasu mutanen basu da aiki sai ture turen abinda bai shafesu ba karshe su kunna wuta mai wuyar kashewa. Wayar ta mika wa Mama shima Baffa ya zauna kusa da ita yana gani. Hankalinta bai tashi ba sai da taga 'yarta babu ko dankwali ta shige jikin namiji sai kace kanin uwarta ko na ubanta. Nan take numfashin Mama ya fara sama sama dama ita haka take idan ranta ya baci. Haka ta fita daga ita sai daurin kirji ta shiga dakin 'yan matan. Wayar chaja ta fizgo daga jikin bango ta fara tsula mata. Hafsi ji tayi kamar a mafarki ana dukanta tayi saurin tashi. Yaya Hadiza ta gani sai kannenta. Cikin rashin fahimtar laifinta ta fara rokon gafara. Sai a lokacin Baffa ya shigo ya dakatar da dukan. Kyaleta haka ku zauna. Wayar Hadiza ya bata hoto daya ta kalla ta kama kafar Mama tana kuka...don Allah ku yafe min wallahi bazan kara ba. Ki ma kara mana don ubanki...wai ni dame muka kuskure miki ne Hafsa. Lokaci guda kin fara taka rawar gangar shaidan. Wai ma yaushe akayi wannan hoton? Shiru tayi ba amsa. Nace yaushe akayi hoton nan...lokacin...lokacin. Hadiza ce ta katse ta lokacin me?
Uhm lokacin da muka ce miki zamu daukar hoto da ummati. Nasan za'a rina cewar Baffa. Dama nasan da taimakon wani a lalacewar da kika soma yi. Amma wallahi ba a gida na ba. Gidansu Saifullahin zani in nunawa mahaifinsa, ki kwana cikin shiri aurar dake zanyi cikin kankanin lokaci mutuniyar banza. Nan dai ya hada duka yaran nasa sun sha fada da nasiha. A dakinsa kowa yace da Mama ta tabbatar ta tuntubi Hafsi ko babu wani abu da ya shiga tsakaninsu domin shi yanzu ya tsorata da halin yaran zamani.
Batul Mam
TUN KAFIN AURE💐 9
Wani irin kuka ne mai tsuma zuciya take yi tunda Mama tayi mata wannan tambayar. Wai ko wani abu ya shiga tsakaninsu??? Lallai ta jawo wa kanta tunda an fara zargin ko lalacewar tata ta kai nan. Gabadaya filon ta gama jika shi da hawaye dadin bakin cikinta ma rashin duriyar Saif. A wannan yanayin Ummati ta shigo itama kukan take yi don a falo Mama da Maman Ummati suka hada su ana ta fada gadon itama ta hau suka jeru kamar masu gasar kuka. Iyayensu sunyi fushi sosai. Tayi nisa da tunani kamar daga sama taji wayarta na ringing. A firgice ta tashi don tasan ko waye me kiran. Ringtone dinsa daban ne....ummati ce ta doke mata hannu da sauri tana kokarin dauka. Ta galla mata harara to banza mara zuciya..duk abinda ya samemu a dalilinsa sai yau zai wani nemeki. Cikin muryar data dashe saboda kuka tace bafa ki san me ya same shi ba. Don Allah ki bani wayar Ummati. Ni wallahi haushi kike bani mtww karbi ni ta dangwara mata wayar ta koma gefe. Ba zancen fita don iyayensu mata suna falo ana ta maida zance.
(Matar ina kika shige ina ta waya.)
Kaji rainin hankali yau fa kwanansu shadaya bata samunsa a waya(kai zan yiwa wannan tambayar. Sai da kaga matsala ka guje ni Saif) kuka ne yaci karfinta.
Shima a hankali yake magana( kiyi hakuri ni kunyar sake haduwa dake da kuma Baffa nayi. Matar ina tsoron zama sirikinsu har abada Baffa bazai dena ganina da wannan tabon ba)
Wani irin faduwar gaba taji (me kake nufi? Baffa fa sun taho gidanku tare da baban ummati)
(Nasani na kuma nayi musu bayani. Tun ranar da ya ganmu na sanar da umma don bana son rufafa a maganar aure. Kunya tasa na guje ki don naci amanar Baffa. Kiyi hakuri muyi rabuwar arziki amma bazan iya aurenki ba.)
Yana kashe wayar wani kuka ya kwace mata har su Mama suka shigo. Ummati suka fara tambaya tace bata san me ya faru ba. Kasa fada musu tayi tana ta kuka. Gajiya suka yi da tambayar aka kyaleta. Sai da Baffa ya dawo ya sanar da Mama yadda sukayi mahaifin Saif yace aure ba fashi tare da basu hakuri shi kuma dan yace bazai iya sake kallonsa ba. Zai fadi haka mana tunda yaso gurbata mana rayuwar yarinya. Suna ta maganganu Hafsi na jinsu daga daki tana kara tsanar kanta da abinda tayi.
******************
Junaid mutum ne mai son jindadi, bashi da magana sosai sai ta zama dole. Ko kadan baya daukar raini wannan kuma hali ne ya tarar da dukiyar da ya taso cikinta. matashi ne dan shekara 30 ga tsaho ga kyau ga fatarsa mai kyau saboda tana shan hutu. Gashin kansa da saje kuwa a kwance yake don kudin da ake ajiyewa don gyara shi daban ne. Yana son kula da gashin kansa ko kadan baya son abinda zai bata shi.
Yana kwance kan kujera kansa a cinyar Tilly tana fara shafa masa kai. Doke mata hannu yayi yana magana kasa kasa ki dena taba min kai I hate it. Dan tabe baki tayi to yi hakuri naga ko wanka baka yi ba meye abin bacin rai don na taba? Tashi yayi ya bude fridge ya dauko lemon gwangwani ya fara sha. Ki shirya muje party amma bana son wannan faratan naki kamar mayya ya juya mata baya ji yadda kika kusa kwashe min baya. Yi hakuri Juni ta fada tana murmushi bari na cire su nayi wanka.
Lallai ma yarinyar nan wallahi kinyi kadan abinda ya fada kenan lokacin da ya fito daga wanka ya kama Tilly tana satar masa kudi. A fusace ya karaso gabanta tasha mari hagu da dama. An fada miki bani da hankali ne? Kumatu ta rike tana kuka ni ka mar Juni? Ke 'yar waye da bazan mareki ba? Barauniya kawai get out of my room. Kafa yasa yana kai mata duka tana ta ihu. Da kyar ta rarrafa ta fita ya jefo mata jakarta waje ta ce zaka san ni kayiwa haka Juni sai na bata maka rayuwa. Ta mike da kyar tana dingisawa mugu ko kudina bai bani ba duk kwanakin nan dana yi.
*******************
Dai dai yake kallon mutane kowa da budurwarsa ana ta sha'ani. Shegiya Tilly da nasan haka take ai da tun wuri na nemi me rako ni nan. Kai da wa kake magana Juni? Shafa kansa yayi zancen zuci ne ya fito fili birthday boy...Imi dan wani gwamna ne abokin Junaid ne tun suna secondary duk watsewarsu tare sukeyi. Ina babe din da na ganku tare ne jiya? Tilly barauniya? Ai na bata takardar sallama dazu....sata fa tayi min don rainin hankali. Imi da buduwarsa suka fashe da dariya ai abokina ka fiye kwashe kwashe ne. Ya rungumo yarinyarsa ya Simy akwai wata a kasa ne kada yayi kwanan kadaici yau. Kai kyale ni kawai. Maybe na tafi portharcout gobe. Dont worry I will pay bana son ganinka so quite. Wayarta ta dauko ta mika masa ga hotunan wasu nan duk kawayena ne idan ka zaba kayi min magana. Bakin ruwan suka koma ana ta wasa da raye raye shi kuma yana kallon 'yan mata kala kala a wayar. Tsaki yayi zai kira Simy ta karbi wayarta sai kawai yaci karo da hoton da ya daga masa hankali. Zuciyarsa ce take bugu da sauri da sauri...he wants this girl at all cost abinda kawai yake fada a ransa kenan.
Batul Mamman
TUN KAFIN AURE💐 10
Jikinsa har tsuma yake bai taba ganin macen da ta sace masa zuciya ba kamar wannan. Fatansa daya wannan saurayin daya rungumeta ba mijinta bane. Tura hotunan yariyar yayi daya gani a wayar ya tashi da sauri ya je wurin da Imi da Simy suke ta rawa yana mata liki da dubu daya. Janyo hannunta yayi suka fito daga wurin rawar Imi ya jawo wata suka cigaba. A irin wannan rayuwar ana tafka kazanta da tsabar rashin kishi. Muna mantawa akwai ranar da zamuyi accounting for every second da muka rayu a duniya.
Rawar ta cigaba da yi a gabansa ganin hakan ya sake janta suka kara nisa da mutane. Yarinyar nan nake son duk wani information a kanta. Ta dan nutsu ta kara kallon hoton wai wannan kake nufi? Eh mana are you blind? No...sai tayi dariya sorry. Gaskiya Juni bansan....katse mata magana yayi kada kice baki santa ba. Kudi ya dumbuzo daga aljihunsa ya damka mata a hannu. Ki nemo min duk abinda ya dace ...ya sake kallon hoton...my God she is so pretty. Kallonsa tayi Juni wannan fa pre-wedding pictures ne. Maybe ma anyi auren don na kusa wata da ganinsu. A wani group aka saka na ma manta wadda tayi sending. Ai sai ki sake sending ki tambaya. Look Simy bani account number dinki. Washe baki tayi yanzu kayi magana. Zan nemo ta ko tana gidan miji ne sai tazo ta kashe maka kishi...kanne masa ido tayi ta tafi. Simy 'yar shekaru goma sha tara karamar yarinya ce da iyayenta suka kyaleta take irin rayuwar da take so saboda yanayin aikinsu. Tana abinda taga dama babu me tsawatar mata a cewar su kuruciya ce ke damunta. Wai kuma yar musulmi kenan babu ko tsoron mutuwa.
******************
Kallon 'yan uwanta take ana ta hayaniya. Kanta har wani sarawa yake don ciwo. Wai nan lefenta aka kawo shine har yanzu mutane basu gama tafiya ba. Dakinsu ta nufa kai tsaye wata kakarta tace ai tunda kika dawo bamu watse ba ki tsaya ki kalli abin arziki. Ai ni kam wannan miji yayi ina ma ina da sauran kuruciya. Dariya duk aka sa Hafsi ko sai hawaye. Auren da zaayi ba dadin rai. Abinda komai Baban Saif ne yayi don yace shi ba karamin mutum bane aure ya zama dole. Shi kuma Saif kamar bai taba cewa yana sonta ba alaqar tasu yanzu ba yabo ba fallasa. Da gaske yayi nadamar abinda ya aikata sai dai kunyar iyalin Baffa yasa har ransa baya son ayi auren. Allah Yaso shaidan baici galaba a kansu ba da da wane ido zai tsaya a gaban mahaliccinsa? Ko matasa nawa ne ke tuna irin wannan a lokacin da suke matse 'ya'yan mutane suna aikata haramun?
Ita kanta Hafsi tana tsoron rayuwar da zasuyi. Da wane ido zasu rinka kallon juna. Ba don zuwan Baffa ba da kila shikenan. Rayuwa kenan wasu na nadama wasu kuwa zuciya ta gama bushewa a aikin sabo. Tir da wannan rayuwa ta shaye shaye da zinace zinace. Ya Allah Ka kara shiryamu Ka bamu wadatar zuci.
Batul Mamman💖
TUN KAFIN AURE💐 11
Da gaske Simy ta shiga neman yarinyar hoto don Juni dubu dari da hamsin ya saka mata a account yace cikon sai bukata ya biya. Hoton ta fara turawa groups uku da take tsammanin daga nan aka turo don ta manta inda ya fito. Sai bayan kwana hudu ya kebbi tayi magana tace ai saurayin yayan kawarta ne a kano suke. Jin haka Simy tayi saurin cewa ai yarinyar da makotansu ne sun dade basu hadu ba tana neman address dinta ne. Nan dai ba wani dogon bincike yar kebbi ta turo da number din Zainab. Mata mu rage tallata sirrinmu a social media don Allah.
Kamar akan kaya yake a lagos din sai dai kuma dole ya tsaya don Imi yana nan Simy ba tafiya zata yi ba. Yana cikin restaurant din hotel din da yayi masauki tayi masa waya ta shigo. Nan yayi mata kwatance suka hadu. Sai da ta cika cikinta da abinci wanda ya kasa ci don dokin jin abinda zata fada masa. ta sanar dashi yadda suka yi da yar kebbi cikin tsananin farinciki ya kankameta sannan ta bashi number din Zainab. Tana ta dariya Juni lallai yarinyar nan ta tafi da imaninka idan akwai saura. Ke me kike nufi? Ya daure fuska...ni duk iskanci na bana hadawa da izgilanci ga addini fa. Ga wayarki ya mika mata..zan ciko miki kudinki anjima. It was nice doing business with you Juni. The pleasure was all mine ya bata amsa.
Dakinsa ya koma ya hada kayansa. Bayan ya gama ya kira number din Zainab. Kamar gaske sallama ya fara yi mata ta amsa duk da taji bakuwar murya.
Dan gyaran murya yayi( Zainab ce ko)
(Eh, wa ke magana)
Shiru yayi yana tunanin karyar da zaiyi ( ina yayanki ango to be?)
( ya Saif ya fita)ta bashi amsa.
( suna ta shirye shiryen biki ko)
Mamaki ta fara yi dai amma tayi shiru (eh amma fa still bangane ka ba)
( ina printing din cards na biki ne a nan kusa da unguwarku shine nake son nuna masa sample don kiran kasuwa).
Sai a lokacin ta dan saki rai tayi masa kwatancen gisansu kamar yadda ya bukata ba tare da ta kawo komai a ranta ba. Yarinyar kamar mara wayo ya fada shi kadai, ba wani bincike ta turo da address.
Scrolling waya yayi ya nemi sunan Oldman ya kira. Senator Rufai yayi mamakin ganin sunan Junaid yaron da number dinsa da suke da ita gaba daya basa samu sama da sati biyu. Hakuri Junaid ya bashi tare da sanar dashi zai tafi kano wurin Hajiyan Dangi itama ya bata hakuri. Senator Rufai murna yayi sosai. Yana matukar son dansa lalacewar yaron kawai ke damunsa.
******************
Kano ta dabo tumbin giwa yau tayi babban bako. Junaid Rufai Bukar ne yake tafiya cikin nutsuwa don yau manyan kaya ya saka tare da aski wanda gashin na zuba zuciyarsa na kuna. Hatta faratansa yaje wani salon a lagos 'yan mata sun gyare shi. Shadda yasa light blue anyi mata dinki mai kyau kansa harda hula. Idan ka ganshi sai kasa shi cikin mazan kwarai sai dai abin ba a fuska yake ba.
Yana tafiya maaikatan airport na binsa a baya ganin sunansa yan maula sun rude. Motar da babansa ya turo ce ta karaso gabansa aka saka masa kayansa a cikin booth. Kudin ya basu masu yawa tunda bai san zafin nema ba. Kowa sai murna...Tilly dake bayansa wadda baisan ma jirgi daya suka biyo ba tayi murmushi tasan ba a banza yayi wannan shigar yazo kano ba. Sai ta rama wulakancin da yayi mata a lagos. Wayar Rosie ta nema ta sanar da ita ta shigo gari.
Gyadi gyadi yace da driver din ya kaishi . Dreba ya shafa kai yallabai ai Alhaji ya gina ma Hajiyar gida a hotoro ai kusan shekararta biyu a can. Shima Juni kai ya shafa don yaji kunya. Rabonsa da zuwa sada zumunci 'yan uwansu na kano ya kwana biyu.
Batul Mamman💖
TUN KAFIN AURE💐 12
Tun kafin ya iso Hajiyan Dangi tasa su Sayyada yi masa abinci. Kusan tafi iyayensa murnar zuwansa ma tunda mommy tayi mata waya ta sanar da ita yana hanya. Alkawari ta daukarwa kanta da yardar Allah yaron nan sai ya shiryu. Ita da kaninta kawai iyayensu suka haifa,tunda bata da nata 'ya'yan nasa sune natan. Idan ta bar dan uwanta ya cigaba da sangarta danshi lallai taci amanar mahaifiyarsu.
A falo ya risketa tana karatun Al-Qurani cikin murya maidadi take karanta suratul Sajda. Wata irin nutsuwa da kwanciyar hankali yaji yana ratsa masa zuciya ya kasa karasawa cikin falon. Sai da ta kai karshen aya ta ajiye tare da yi masa nuni da ya karaso ya zauna. Bayan tayi addua tace Junaidu dan gudun hijra ka dawo? Murmushi yayi tare da sosa keya. Yi hakuri Hajiyana bazan kara ba. Kallonsa kawai take yi hatta tafiyarsa irin ta babansu ce. Kamar su ta baci. Inama ace yayi koyi da halayen Malam na kwarai.
Haka ta kira 'yan matan gidan nata suna gaisawa dashi. Wai Hajiyan Dangi ta iya kiwo ya fada a ransa. Ba don yunwar yarinyar hoton nan bace kawai a ransa ai da yasan yadda yayi a sami 'yar rage dare ko da daya ce. Wani shegen murmushi yayi, Hajiyan Dangi dake gafe tana kallonsa tayi tana murmushin...sai na gyara maka zama yaro.
*******************
Ko kafar gida Hafsi bata zuwa yanzu Saif dinma Baffa ya hanashi zuwa a cewarsa sa hadu idan an daura aure. Duk abin duniya ya isheta gashi dai zata auri wanda take so amma babu wannan farincikin ko kadan a ranta. Duk surutunta yanzu ta zama wata abar tausayi. Yan uwanta kuwa sai shirye shirye suke yi hankali kwance.
*******************
Ya kusa awa biyu a gefen gidan sannan yaga fitowar wanda yake jira. Tabar hannunsa yayi saurin kashewa ya tada mota ya bishi a baya. Yinin ranar duk inda Saif yayi Junaid na binsa a baya ba tare da ya sani ba. Takaici ne ya isheshi don kuwa baiga alamun anzo gidan da yake nema ba. Karamin tsaki yayi ganin sun kusa karasawa gidansu Saif din. Horn ya rinka matsa masa kamar hauka dole Saif ya tsaya yayi parking. Wannan takun kasaitar ya dinga ya har ya isa kusa da motar Saif. Ganin bai sanshi ba sai ya mika masa hannu su gaisa. Kin karbar hannun Juni yayi daya tuna yadda suka kankame abar sonsa.....abar sona??? Ya tambayi zuciyarsa. Sannu dai, Saif ko? Eh ya amsa masa fuska a sake...Saif akwai fara'a. Shiru yayi don bashi da abin fada abin har ya fara isar Saif. Ban fa gane ka ba wa kake nema ne? Hoton cikin wayar ya nuna masa idanun Saif har wani kankancewa suka yi don tsabar bacin rai. Yayi imani ko mutum daya bai turawa hotunan ba kuma Hafsi ko wayar kirki bata da ita shiyasa ma bai tura mata ba. Juni ya katse masa tunani I want her kuma zan iya biyanka ko nawa ne ka kaini wurinta. Ikon Allah....kai kuma daga ina? Kana ma da hankali kuwa? ba ko kunya balle tsoro kake fada min hakan. To bari kaji na fada maka this coming saturday zata zama mallakina. Kasa karasa magana Saif yayi saboda tsabar takaici ya tsaya yana magana da kwancen hauka. Shafa kai Juni yayi plan dinsa is working. Sai kuma ya yamutsa fuska tunda baka jin lallami kasani cewa nan da ....sai ya dubi agogonsa kamar 20 minutes yarana zasu dauko min ita su kai min ita hotel. Wani mari yaji a kuncinsa kamar wuta kafin ya dawo hayyacinsa kuwa Saif ya shiga mota ya tayar. Shege ya fada yana shafa kunci amma fa marin da zafi...kodayake its worth it.
Bayan Saif yabi har kofar gidansu Hafsi. Yana tsaye a can gefe ya hango wani dattijo mai cike da kamala ya fito sunyi magana da Saif. Yasan bai wuce barazanar karyar da yayi ba Saif din yake fada shi kuwa bukata ta biya dama plan dinsa yaga gidan kuma ya gani. Sauransa jin sunanta duk da a zuciyarsa ya rada mata suna pretty.
Batul Mamman💖
TUN KAFIN AURE💐13
Wallahi Baffa kamar mahaukaci fa yake magana kuma nayi tunanin da gaske yake. Gyara tsayuwa yayi to Saifullahi ai kadan ma kuka gani. Illar irin wannan abin dama ba na lokaci daya bane. Me zaku fadawa yaranku idan suka ci karo da hoton nan gaba? Shin kuna da bakin tsawatar musu bayan sun san borin kunya kawai kuke yi. Allah Ya kyauta ka tafi gida kawai in Allah Ya yarda babu abinda zai faru. Saif kallon Baffa kawai yake yi don yaga kamar bai yarda da abinda ya fada ba. Shi kadai yasan abinda ya gani a idon yaron nan. Jiki a sabule ya juya ya tafi.
********************
Wannan tafiyar kasaitar yake yi har ya shigo gida yana dan fito don yau zuciyarsa fes take. Tunda yazo kano bai sha giya ba sai taba da shisha suma duk a waje saboda sa ido irin na Hajiyan Dangi. Tsohuwar nan akwai hana ruwa gudu. Turus yayi da ya ganta zaune a kan gadonsa. Fuskar nan babu fara'a koma waje kayi sallama ka shigo kamar dan arna kana min fito kamar mai kiwon kare. Haba Hajiya ai dakina ne kuma nasan babu kowa a ciki meye na sallama kuma. Ashe baka san cewa akwai aljanu da malaikun Allah a ko ina ba. Don baka ganinsu hakan ba yana nufin babu su ba. A duk lokacin da zaka shiga wurin da babu kowa sai ka ce Assalamu alaina wa ala ibadullahis salihin. Ai na iya Hajiya bafa complete jahili bane ni. Naji koma dai kayi. Fita yayi yayi mata kyakkyawar sallama ta amsa sannan ya shigo. Cire kaya ya fara yi yana wurgi dasu tace maza ka gama ka tsince min su ga tsintsiya nan ka share dakin. Me??? Ni din Hajiya? Kai mana Junaidu ko kana jin saurayi kamar ka zan bari a share masa daki. Ni wallahi bacci nake ji duba fa ki gani na dawo da wuri shadaya bata yi ba. Ta mike Allah sai ka gyara dakin nan idan ba haka ba zaka ga yadda zanyi da kai. Tana fita ya fada gado sai dai bai gama gyara kwanciya ba ta dawo. Yauwa kayi sallah kuwa?... .au kwanciya kayi ko to tashi ta fada tana dukansa da slipas din kafarta. Dole ya mike Hajiya bana so fa. Sallah kuma nayi don nasan ina da ayyuka a gabana shiyasa ma tun da Baba yazo muka je muka yi sallar asuba ina dawowa nayi duka sallolina ya kare maganar da murmushi. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun shi kawai take fada. Junaidu lalacewar taka har ta kai haka? Shiyasa ka gagara shiryuwa mana. Ta share wasu zazzafan hawaye dake sauko mata. Ashe baka san cewa wutar masu barin sallah daban take ba? No Hajiya nifa nayi ko bakiji abinda na fada bane. Bakin gado ta zauna Junaidu babu wata sallah da zaka yi ba a lokacinta ba da gangan Allah Ya karba. Harma gara lokacin ya wuce maka bisa kuskure sai ka rama. Ita fa sallah kariya ce daga aikin sabo da alfasha. Rayuwa da mutuwa gaskiya ne Junaidu, azaba ko rahmar kabari gaskiya ne, wuta da aljanna ma gaskiya ne. Maganar Hajiyan Dangi da hawayenta sun taba masa zuciya har bai san lokacin daya dora kansa a cinyarta ba yana bata hakuri. Junaidu ka kiyayi Allah sai Allah Ya kiyaye ka. A yau alkawari daya nake nema a wurinka shine na tsayar da sallah. Nayi miki bazan kara bari naji kiran sallah na kasa tashi ba. Ta shafa kansa Allah Yayi maka albarka. Amin
******************
Ummati ana ta rawar kai biki ya gama matsowa da kyar aka barsu zuwa salon don ko gyaran jiki Hafsi bata yi ba. Wannan kuma duk yana cikin punishment din da aka tanadar musu a gida saboda laifin da sukayi don a cewar Maman Ummati itama haka zaayi mata tunda bakinsu daya.
Sai da Saif yayi jan ido sosai sannan kanwarsa Zainab ta fada masa gaskiya ita ce garin binciken waya taga wadannan hotunan a wayarsa ta tura wayarta, daga nan kuma ta tura wa kawayenta. Da belt ya zane ta tana ihu tana bashi hakuri. Ko da mamansu taji dalilin dukan Allah Ya kara tace musu duk su biyun. Ke banda gulma me ya kaiki bincika masa waya....bayan zainab ta koma daki da kuka Maman tace gobe ma ka sake daukan yar mutane kuje yin hoton rashin kunya....istigfar ya rinka yi a zuci. Allah Yasa daga wannan bazasu fuskanci azabar Allah ba. Don kam shi da Hafsi sunyi nadama sosai.
Batul Mamm
TUN KAFIN AURE💐 14
Duk abinda yayi niyyar yiwa Pretty kamar yadda ya saka mata suna maganganun da Hajiyan Dangi tayi masa yasa duk jikinsa yayi sanyi. Washegari bai bari ya makara sallar asuba ba domin kafin lokaci ma yayi setting alarm. Suna dawowa ya shiga dakin Hajiyan Dangi. Har ka manta yadda ake sallama ne? Ba shiri ya fita yayi sallamar ya jira tayi masa izini ya shigo. A kasa ya zauna cike da ladabi tace yau dannan nawa akwai magana a bakinka. Fadi inji Allah Yasa alkhairi ne. Shafa kai yayi alkhairi ne Hajiya. To ina jinka. Wai yau shine da jin kunya abin ya bashi mamaki... dama yarinya na gani ina son aura kuma idan da hali da wuri nake son auren. Allah mai girma da daukaka ta daga hannu sama ta yabi Allah SWT sannan ta kalle shi. A ina take kuma ya sunanta? Nan fa daya yace a ransa, sai kuma dabara ta fado masa. Nasan gidansu dai amma banyi mata magana ba domin mafi son ki fara nema min izini. A'a wai kuwa Junaidun da ta sani ne wannan? Yau komai a hankalce yake yi. Allah Yasa bata yi masa zancen Sayyada ba itama yarinyar bata sani ba da yazo ya bata kunya. Kwantar da hankalinka bari na fadawa Baba sai musan abinyi zuwa karshen sati. Sanin cewa nan da kwana uku zaa daura mata aure Junaid ya fittike mata shi lallai yau yake son taje. To naji bari dai na fada masa tunda da kanka ka zo da maganar. Tana fita yayi ajiyar zuciya yarinyar da har yanzu baiga zahirinta ba yake tunanin aura....sai dai kuma irin yadda yake jinta a ransa yasan da gaske yake burin rayuwa da ita, baya jin zai taba iya yarda wani ya shiga tsakaninsu.
Sai bayan laasar Hajiyan Dangi ta shirya tare da wata yar uwarsu Gwaggo Mairo suka nufi unguwar sabontiti inda Junaid yayi musu kwatance a matsayin gidansu Pretty. Karba ta mutumci da karramawa Mama tayi musu bayan sun gama gaisawa ne Hajiyan Dangi ta gabatar da kanta tare da fadin dalilin zuwansu. Mama tace kuma nan gidan yaron ya fada muku? Nan ne domin ya kwatanta min gidan ta waje sosai Hajiya ta bada amsa. To Hajiya ni dai banda yaran nan biyu da suka gaisheku bani da wata 'yar sai Hafsa wadda asabar dinnan zaa daura mata aure. Babbar kuwa shekararta uku ma da yin aure. Shiru Hajiyan Dangi tayi sai Gwaggo mairo ce take ta basu hakuri tace nasan yaronnan kam ba kananan yake nufi ba zamu sanar dashi yayi hakuri. Hajiyan Dangi ta fiddo kudi a jakarta tace gashi a bawa amarya. Allah Ya sanya alkhairi. Mama taki karba itama hakurin ta basu. Hajiya sai ta ajiye kudin a kan tebur. Suna kofar fita Hafsi ta dawo daga salon duk a gajiye. Har kasa ta durkusa ta gaishesu. Ko baa fada ba Hajiya tasan wannan ce Hafsar da danta ya gano. Lallai ya rude don yarinyar tana da kyau. A sabule suka fito don ba haka aka so ba. A tunaninta indai yayi aure wasu daga cikin ayyukan barnar da yake aikatawa zasu ragu ko ma ya bari gaba daya.
Tun a mota ta kira shi domin taga missed calls dinsa da yawa sai dai bai dauka ba. Suna isa gida Sayyada ta sanar da ita ai ya tafi masallaci ne. Dadi ne ya cika mata zuciya sannan ta shige daki. Cike da doki ya shiga dakin yana ta washe baki. Har zuciyarta take tausayinsa... junaidu yarinyar nan ashe ranar asabar za'a daura mata aure. Kayi hakuri ka nemi wata. Mikewa yayi hakuri fa kika ce Hajiya. To ma baki basu kudi bane? Ai wallahi da sunga kudi magana zata chanja. Murmushi tayi zauna Junaidu. Ina so ka sani ba fada ta bace Annabi SAW yace babu kyau wani ya shiga cikin cinikin wani ma balle harkar neman aure. Ai ba'a hada nema akan nema. Abu daya zaisa ka iya nemanta sai dai indan wancan yace ya fasa. Wani irin bacin rai yaji a ransa idanunsa sun kada sunyi ja. Fita yayi fuuu ya buga mata kofar daki har sai da ya tsorata ta. Allah Ka shirya mana ta fada a fili.
Jan mota yake a guje kamar zai tashi sama. Baya ganin gabansa ma da kyau. Club ya shiga ya tayar da kura kafin ya tsayar da motar. Idanu duk a kansa ya shiga. Waiter na shirin zuba masa giya ya sunkuce kwalbar yana kafa kai. Sai da ya bugu sosai ya jawo hannun wata yarinya suka fita tare yana tangadi. A waje ya dauko wayarsa ya bata yana lumshe idanu kira min oldman. Waye kuma oldman? Ki dduba za zaki gani a wayar. Ringing biyu ya dauka sai yayi mamakin jin muryar mace ta sanar dashi wurin da dan nasa yake ya daga masa hankali. Yana ajiye wayar ya kira Hajiyan Dangi ya fada mata. Nan tayi masa bayanin abinda ya faru sannan ta sanar da maigidanta inda Junaid yake. A can abuja kuwa Mommy Senator Rufai ya tasa yace mata gobe zamu kano.
Batul Mamman
TUN KAFIN AURE💐 15
Hajiya da maigidanta sun rasa yadda zaayi a dauko Junaid saboda Baba baya iya tuka mota idan dare yayi. Suna ta shawarwari ne suka ji karar motar sa. Da sauri suka fito motar duk ya buge ta a hanya har fitila daya ta lotse. Haka suka kama shi yana ta tangadi sosai suka shiga dashi dakinsa. Hajiyan dangi sai kuka take jin yana ta sumbatu yana cewa ko a aura masa pretty ko ya saceta ta karfi. Haka Hajiyan Dangi ya zauna dashi har yayi bacci shi kuma Baba ya kira senator Rufai ya sanar dashi halin da ake ciki.
Jirgin karfe 7 na safe suka biyo shiyasa kafin karfe 9 sun iso kano. Motoci uku ne suka je tarbar maigirma senate president da matarsa Hajiya Salama.
Gyadigyadi suka nufa gidan Hajiyan dangi. Mommy tana ganin Hajiya ta soma kuka. Bana son irin haka Salama baki san hawayen iyaye cuta ne ga 'ya'yansu ba? Share idon tayi tace kinga irin yadda nake fama da yaronnan ko. Ni fa har cewa nayi baban nasu ya dena saka masa kudi a account amma yaki. Hajiya tace abar maganar nan yanzu bari mu gani ko ya tashi. Su hudu iyayen suka dunguma zuwa dakin da Junaid yake mahaifinsa ya bude kofar ya tarar dashi a kwance yana ta busa taba. Kwarai yayi mamakin ganinsu ya tashi da sauri...mommy na sannu da zuwa. Hannun daya kawo zai tabata ta doke tare da jan tsaki. Yasan fushi take yayi murmushi kawai ya kalli babansa. Oldman ya hanya? Wannan karon Hajiya ce ta doke masa baki. Uban naka kake kira oldman kuma junaidu? Dole kayi ta ganin ba daidai ba a rayuwarka tunda iyayenka ma basu da kima a idanunka. Da ace ka maida hankali kan addini da kasan cewa iyaye sun fi karfin wasa. Duk zama suka yi Senator Rufai ya cire hularsa yasa hannuwansa ya dafe kansa. Ya rasa yadda zaiyi da Junaid fitinarsa kullum karuwa take. Hajiyan Dangi ce ta labarta musu dukkan abinda ya faru game da yarinyar da Junaid yace yana so mai suna Hafsa. Ya maimaita sunanta a ransa yafi a kirga. Baya jin komai game da maganganun da suke yi. Hankalinsa ya tafi can tunanin yadda zai mallaki yarinyar nan mai suna Hafsa.
A wace unguwa suke? Ita ce kalmar da yaji daga bakin mahaifinsa. Da sauri yace sabontiti. Shi kuma wanda zata aura fa? Nan ma Junaid ya bada amsa. Alhaji zaka nema min aurenta? Wallahi nayi maka alkawarin zan shiryu indai na aureta. Hajiyan dangi tace Rufai me kake shirin yi ne? Shima Baba cewa yayi hala ka manta haramcin neman aure akan na wani? Mommy dai binsu ta rinka yi da ido don itama bata san me mijin nata yake nufi ba.
Batul Mamman
0 comments:
Post a Comment