Tana lek'ensa ta windo har ya bar gidan sannan ta sauke labulen gami da zubewa kan kujera tana dariyar farinciki. "Na sameshi!" Ta fad'a a fili kafin ta dauki ragowar tea din ta saita daidai saitin da ta ga ya sha ta hau korawa a cikinta tana mai lumshe idanu, wani irin soyayyarsa na k'aruwa a ranta. Ta dire kofin bayan ta kammala, sai kuma jikinta yayi sanyi. Baifa furta yana sonta ba? "Sannu bata hana zuwa." Ta ayyana hakan a ranta. Cike da nishad'i ta tattara kayan karin ta mayar kicin domin ji tayi gaba d'aya yunwarta ta kau. Ranar yini tayi da wani nishad'i marar misaltuwa. To shi d'inma hakan ce gareshi, don har Abba saida ya tambayeshi ko anyimishi albishir da aljanna. Dariya kawai yayi. Itama a ranar sunyi waya da Aisha, wacce shirye-shiryen biki ya 6oyeta don alokacin sauran watanni biyu da kwanaki. Nan Aisha ta sanarmata lallai a wannan daren tayi kokarin kyautatawa mijinta. Tayi shiri, irin shirin da tasan zaiyi saurin birkita tunaninsa. Sukayi dariya. "Kinsan fa har yanzu ya k'i furtamin yana sona?" Tsaki Aisha ta ja. "Kedai ki bada kai, wannan kuma sadda zai furta ma bakisani ba, kuma na gayamaki wallahi Yaya yana sonki. Ki bi dai shawarwarina. Na yarda zaki iya fin haka." Suka k'ara darawa kafin suyi sallama. Misalin d'aya na rana, ta dauki waya tayi kiransa kamar yanda Aisha ta gayamata. Saida ta kammala dariyar sunan (Angrybird) da ta sanyamishi. Saidai har ya kammala rurinsa baki d'aga ba. Bata sauke wayar data kunnenta ba sai gashinan ya kira. Ta shige d'akinta tana goye da Hanif wanda yayi bacci a bayanta. "Assalamu alaikum." Yayi sallama cikin tattausan muryarsa. Ta lumshe ido ta bude tana murmushi. "Waalaikumussalam, Barka da rana Yaya." "Bintunaa! Ya dace a chanjawa Yaya suna, a k'ara mishi matsayi please." Tayi shiru batace komai ba, ya d'ora da fad'in. "To gayamin ya kike? Ina bebina?" "Lafiya lau, gashinan yayi bacci." Ya jinjina kai kamar tana ganinsa. "Masha Allah. Kinsan ina nake kuwa?" "A'a " "Gamunan tare da Abba munzo daurin aure Katsina." Ta zaro ido. "Katsina?" Yayi 'yar dariya. "Hey, kin tsorata ko? Ba kwana zanyi ba ai, zanzo ki bani karfin mata goma." Ai tuni ta kashe wayar tana dariya, shima dariyar yayi cikin jin wani irin nishadi marar misaltuwa. Bata motsa daga inda take tsaye ba ta ji shigowar sak'o. Ta bud'o. "Kina k'ara burgeni Bintuna, miss you! Ayi mana addu'ar dawowa lafiya." Ta karanta yafi sau biyar da wani, k'arshe ta zauna gefen gado tana cigaba da karatun. Wani sanyi ne takeji yana ratsa zuciyarta, wai kuwa dagaske Yayanta Ma'aruf d'inne kuwa? Wannan Ma'aruf din da suke yawan samun sa6ani har Mami kan kirasu mage da 6era? Sai kuma ta ji tanason ba shi amsa. "Miss you too, Allah Ya maidoku lafiya YAYANA." Ya saki ajiyar zuciya. Wai meke faruwa haka? Da ace ba gida guda suka task da Bintu ba, kuma baisan soyayya ba, zai iya rantsewa ko wani abin tayi mishi ya soma sonta har haka, irin son da babu wacce ya ta6a yiwa sai Ma'unsa. Ita kuwa Bintu da wuri ta kammala ayyukanta don wajejan hudu na yamma ya shaida mata sun taho. Ta k'ara gyara Hanif ta shiryashi cikin kana kaya marasa nauyi. Itama ta shiga da zummar wanka, ta zaro ido ganin abinda bata zata ba. Tayi shiru, ashe fa tuni aka shiga sabon wata. Hakanan ta hakura ta kimtsa jikinta ta fito. Batayi wani shiga mai birkitarwa ba kawai ta sanya yadinta marar nauyi mai hannu (3quater) dinkin doguwar riga, saidai ya kamata. Haka ya dawo gidan har da ledarsa ta kaza a hannu. Dariya ta ciyota alokacin da ta sanya hannu tana kar6ar ledar. Ya matso da ita. "Ya akayi?" Ta sunkuyar da kanta tana girgiza kai. "Bakomai." Tayi furucin a hankali. Yayi 'yar dariya. "Ashe inada maganin tsiwarki? Lallai nayi sake a baya. Yau dai (the game will be over). Daga haka ya shige dali yana wani takun kasaita har batasan sadda tayi dariyar mugunta ba (Kuyi maneji da wannan ..kuyi hkr wlh ba da son raina yake kadan ba.!!) Bayan sallar Magriba, suna zaune yana wasa da Hanif ita kuwa ta dukufa tana zubamishi abinci kana ganin fuskokinsu kasan suna cike da jin nishad'i. Shi nasa na murnar yau zai samu abinda ya jima cikin tsananin so da bukata, yayinda ita kuma ya had'e mata biyu, ga hirar da sukeyi cike da nishad'i ga kuma na muguntar da Ma'aruf baisan da zamansa ba, har sai kuma ta ji ya bata tausayi. "Wai Bintuna duk me ya sanyaki wannan fara'ar?" Ta dubeshi ta kauda kai tana murmushi. "Bakomai." Murmusawar shima yayi, zuwa yanzu ya gama fahimtar ita dinma tana sonshi, kawai dai jan aji ne irin na mata. Misalin goma da rabi na dare, suna zaune daga shi sai ita a falo, Sarah da Hanif sunyi nisa da bacci. Ta mik'e tsaye, ya rik'o hannunta wanda ta jishi har kwanyarta. Ta dubeshi, idanunsa a lumshe. "Ina zaki?" Ya nemi sani da muryarsa wacce ta chanja sanadin tunaninta da ya fad'a. Ta kuramishi idanu. "Zanyi shirin kwanciya ne." Ya saki hannun bayan ya sauke idanunsa akanta, ta kauda nata da sauri sai kuma ta shige. Bayan ya shirya ya sanya hannu ya dauki wayarsa ya kirata, tana gani ta k'i amsawa saboda wani nauyinsa da takeji. Ta zubawa wayar ido yanata ruri, alokacin ne kuma ta ji shigowarsa dakin. Ta mik'e tsaye da sauri, sai kuma tayi k'as da kanta ganin ko riga babu a jikinsa. Ya dubeta daga sama har k'asa, sannan ya sauke ajiyar zuciya ganin irin shigar da tayi wanda shi kadai Allah Ya yarjewa gani. "Meyasa bakya amsa kirana? Sai ma ido da kika zubawa wayar?" Ta girgiza kai, baki bari tayi magana ba ya soma abinda ya matsu da shi. Har saida ta kaisu da zubewa a k'asa. Alokacin kuma ya d'ago ha6anta har numfashinsu na bugun hancinansu da sauri-sauri. "Tashi muyi sallah." Shaf, ta mance da batun rashin sallarta sai alokacin. Ta lumshe idanunta, murya na rawa ta amsa. "Bani da sallah." Ya saki ha6anta yana murmushi, duk a zatonsa wasa takeyi. "Bari na gani." Ya d'ago ya dubeta kamar yayi kuka, sai kuma ya mik'e ya fita kawai. Tausayinsa ya kamata, da kyar ta iya mikewa ta kashe fitilu ta kwanta. Babu jimawa da kwanciyarta, ta ji shigowarsa hakan yasa ta saurin rufe ido. Kwanciya yayi ya juyota jikinsa ya sumbaci goshinta. "Allah Ya tashemu lafiya." Ta amsa a hankali. Cikin dare ya kasa saita kansa, haka yayita juyata son rai yana yanda yaso, kafin a karshe ya mike ya bar mata dakin. Ta bishi da kallon tausayi yanda yayi mata da kuma kalaminsa gareta har yana furucin bazai iya rayuwa babu ita ba. Ta lumshe ido tana murmushi a haka sabon bacci yayi awon gaba da ita. Shi kuwa tun daga ranar ya rage ra6arta hakanan ya rok'eta da suturta jikinta duk sadda suke tare kada ya sa6a umarnin Mahaliccinsa. Idan kuma ya fita aiki, ta fita makaranta suna tare a waya, bini-bini ya kirata har itama ta saba da kiransa idan ta ji shiru. Baya dawowa gidan sai magriba, haka zasu zauna suyita hira, gaba d'aya yanzu ya sakar mata har ta daina kunyarsa. Hirarsu a yanzun ya bambanta da na baya don hirar soyayya ce da mutunta juna. Kamar dai a yau, tana kwance saman doguwar kujera tana lissafa kwanakin period dinta, a goben ne take da kwana bakwai cif wanda a kwanan zatayi wanka. Ta ji shigowar motarsa da tsayuwarsa. Saidai kafin ta motsa wayarta ta hau k'ara, ta dauka ta duba. Tayi mamakin ganin yayannata ne. Ta d'aga da sallama, ya amsa. "Ki fito, yau zance nazo." Abin ya bata dariya. Ta amsa da toh. Dakinta ta shiga ta k'ara kallon kanta. Riga da siket na brown lace ne a jikinta, tayi kyau ya zauna d'as a jikinta. Ta k'ara feshe jikinta da turare ta murza jan baki. Mayafinta ta dauka marar nauyi ta yafa a kafad'arta, sannan ta zura takalminta mai tsini ta fita. Hanif na tare da Sarah a d'aki, bata bi ta kansu ba ta fita. Yana sanye da shadda sky blue, hularsa kuma dark blue. Dinkin boda, ya zauna sosai jikinsa, yayi kyau har ya gaji. Kafarsa d'aya ya tankwashe saman kujera, kansa kwance a kujerar ya zubawa hanya ido, a sannu kuma yana sauraron kid'an dake tashi a rediyon motarsa. Ido ya zubamata sadda ta fito tana wani irin taku na jan hankali, bata ganinsa sakamakon gilashin ba haske, saidai jikinta ya bata ita din yake kallo. Yasa hannu ya bud'e mata gaban motar tun kafin ta k'araso. Ta shigo ta rufe. Tayi mishi sallama. Ya sauke ajiyar zuciya don baisan Bintu na da kyau haka ba saida ya soma sonta. Ya amsa yana tambayarta mutan gida Abin ya sanyata dariya. "Wai Yayana menene haka?" Hannunta ya rik'o. "K'ara'i, sonki ya sanyani Bintuna." Ta zaro ido tana dubansa, baki ta6a cewa yana sonta ba, zataso a yau ya furta. Ya hura idanun. "Bakya sona ne? Yau fa baki zaki bude malama, hira ta kawoni, zan bayyana miki sirrin dake raina." Tayi farr da ido, ya kauda kai yana wani irin murmushi, ya kar6i wannan sak'on. "A baya, nayi zaton mace d'aya ce ta dace da ni, mace d'aya ta dace na mallakawa komai nawa. Nayi zaton yanda nake, ni d'in MIJIN MACE D'AYA ne, banyi aune ba, mutuwa tayi min YANKAR KAUNA da matar da na so na kuma fi sonta fiye da kowace mace a duniya." Ya d'an tsagaita kafin ya cigaba da magana. "Na zo nayi biyayya bayan da na jajircewa zuciyata na yarda da KADDARA, na aureki." Ya k'ara matse yatsunta yana dubanta duk kuwa da cewar idanunta baya gareshi. "Bintun Mami, Bintun Ma'aruf. Kinsan me yafi had'ani dake?" Sai lokacin ta dubeshi ta girgiza kai gami da turo baki. Yayi 'yar dariya. "Bakya ji, na lura kina da fitina da tsokanar fad'a. Ba kuma sai na fad'amaki wanene Ma'aruf ba. Wannan shine ya kawo rashin jituwarmu. Kafin kuma na zo na had'u da jarabta ta sonki. Ban k'ara sanin ina sonki ba, sai bayan da na nisanta gareki har na kwanaki talatin da d'aya, zuwana Lagos kenan. Bayan na dawo nayi kokarin soma janyoki a jikina domin nuna miki irin so da kaunar da nakeyi miki a aikace batare da na furta ba." Ya d'anyi shiru yana mai cigaba da murza yatsunta, ta sauke ajiyar zuciyar tana kar6ar sak'on a sannu-sannu. "My Queen." Yayi furucin da wata muryar da ta ji kamar ba ta shi ba. "Ina sonki, ina kaunar na kasance tare da ke har abada. Kin shirya kar6ata matsayin miji kuma uba ga 'ya'yanki?" Ta sunkuyar da kanta k'asa. Gaskiya ne, da ba'ason zurfafa k'iyayya a addini, bakasan sadda zaka soma son abinda kake k'i ba. Ya d'ago ha6anta. "A'a my queen, you have to answer me." Ta lumshe idanunta. Murya na rawa ta furta a hankali. "Na amince, ina sonka." Haka yayita aika sak'o kafin ya barta yana murmushi ya soma da bud'e kofofin. "Nagode my queen." Daga haka suka shiga ciki, ran kowannensu k'al. Ranar ma basu raba shimfid'a ba. Washegari kuwa da Magriba, yana shigowa ya risketa tana sallah a d'akinta. Ai baisan sadda ya washe hak'ora ba don farinciko sannan ya juya zuwa d'akinsa. Abincin daren nan dakyar ya ci. Ita kuwa gaba d'aya ta tsorata da yanda ya soma nunamata. Haka dai ta daurewa zuciyarta ganin ya riga ya gama matowa. A daren bayan sunyi sallar nuna godiya ga Mahaliccinsu yayi musu dogon adduoi. DAREN ALKHAIRI KENAN...! * * * Kuka takeyi sosai, yana rarrashinta, dole tayi shiru ganin yanda duk ya bi ya damu kansa da kukannata. Da kansa ya taimaka mata ta tsarkake jikinta kafin ya barta ta k'arasa. Ranar ya tsinci kansa da wani irin farinciki marar misaltuwa. Lallai Allah Ya mishi babbar kyauta, a yau gashinan ga madadin Asma'u. Yau shi ya taimakawa Sauda da d'awainiyar gidan, ita kuwa kunya ce ta hanata fitowa ma. Tana jin shigowarsa d'akin tayi saurin ture kanta k'ark'ashin filo. Ya k'arasa yana dariya ya hau yi mata cakulkuli, babu shiri ta hau dariya gami da ture filon. Ya sumbaci goshinta, ta lura yanason yin hakan kafin ya kwanta ya soma yi mata wasu nauyayyun zantuttuka acikin kunnenta. Zata mik'e cikin zafin nama ya janyota, tayi narai-narai da ido, kwalla suka cikamata idon. "Don Allah kayi hakuri." Ya kwaikwayi muryarta. "Don Allah ki nunamin karfinki na mata goma." Ai sai ta tura kanta jikinsa tana dariya. Yayi mata kyakkyawan runguma. * * * Acikin wannan satin, ba'a cewa komai. Da ka gansu kasan suna cike da more rayuwa babu wata matsala a gabansu. Sai gashi wata muguwar shakuwa ta daban ta shiga tsakanin Bintu da Ma'aruf wanda ta bawa kowa mamaki. Akwai sadda da yamma suna zaune gaba d'aya a falon Mami ana hira har Hashim da Sally wadanda suka kawowa Mamin ziyara, lokacin sauran kwanaki biyar ya rage bikin Aisha. 'Yar kwarewa Ma'aruf yayi, nan da nan Bintu ta rikice ta mance a inda suke ta hau shafa bayansa tana mai mik'a mishi ruwa. Cike sa tausayawa tace. "Sorry my king." Ya amsa, gyaran muryar da Rufa'i yayi ta farkar da su. Mami dai kauda kanta tayi kawai tana murmushi, yayinda Rufa'i da su Hajara suka sanya dariya. Ma'aruf ko a jikinsa sai ma ita Bintun ce ta dan ji nauyi. "Oh, Allah Hakim, yau 'yar Mami ce ke wannan rikicewar akan abin gudunta? Soyayya lallai tana dadi " Mami ta mike don sai alokacin ta ji kunya. Daman ita Bintu ke kunyar, ai kuwa tana bada baya ta dubi Yaya Rufa'i. "To meye? Wasu ma suyi mana." "Lah, ni kike gayawa haka? Eh lallai, kinmanta sadda yake bulale ki nake yare miki? Aisha kinga halin d'an adam." Bintu na dariya ta zauna gefen mijinta wanda ke sauraronsu da murmushi dauke saman fuskarsa. "To ai bulala ce ta soyayya, yanzu ba gashinan tayi rana ba, ai hakane ko my king?" Suka tuntsire da dariya har Ma'aruf din. "Yes my queen, ashe kingane. Ku dai ku rike girmanku ba'a shiga tsakaninmu da queen, ko harshe da hak'ori ma haka suka ganmu suka kyale. Ato." Dariyar aka k'ara. Hashim ya d'ora da fad'in. "To d'an iska, dadin abin dai..." "Ya isa." Ma'aruf ya dakatar da shi ta hanyar mik'ewa yana dariya gudun kada yayi mishi iskanci. "Malam tashi muje ku gaisa da Abba." Haka suka wuni cike da jin wani irin annashuwa. * * * BIKI BUDURI....! ((SAIRAN POST DAYA KO BIYU IN SHA ALLAH..!) A yau ake bikin sanya Aisha a lalle. Wannan yasa gidan nasu yake a cike da 'yan uwa, cikinsu kuwa har da mutanen Rano. Wannan karon har Umma abokiyar zaman Inna itama ba'a barta a baya ba wajen halartar bikin autar Mami. Bintu babu zama, sune wancan babban shagon na kayan kicin, sune acan shagon gyaran gashi. Ya zamana ta dawo gidan da zama, duk yanda Ma'aruf yaso hanawa bai samu hakan ba kasancewar ta samu daurin gindi wajen Mami. A daren da akayi kamun Aisha, suna zaune a can d'akinsu tare da su Atika harma da Hafsa kanwar Ma'u wacce itama takanas ta zo kwana adalilin mijinta yayi tafiya, kasancewar gidansu basu da sa ido ballantana har abin ya zama wani babban al'amarin da zai shafi ZUMUNCI A YAU. Sai hira sukeyi suna kyalkyala dariya. Rabin hirar kuwa Atika ke basu akan matar saurayinta. Yanda yake bala'in shakkar daukar koda wayarta a gaban matar. Wayar Bintu da tayi k'ara ya sanyasu dubanta suna tsokana. "Toh sarakan soyayya." Ta murgud'a baki tana dariya kafin tace suyi shiru ta d'aga da sallamarta. "My king, fatan dai ka bar fushin?" "Idan kinaso na daina, zo ki sameni anan d'akina. Ta zaro ido. "Lah, baka tafi gida ba? Karfe goma fa " Yayi 'yar dariya. "Kina wasa, ai na gayawa Mami saidai nima na kwana a gidannata." Ta hadiye dariyarta, suma tasu suka gimtse don kuwa a hands free wayar take. "Allah Sarki My King, shikenan ai, da safe Dan dolo sai ya mik'o maka kayan karinka. Allah Ya tashemu lafiya." Ta kashe wayar gaba d'ayanta, me zasuyi banda dariya. Aisha ta d'akamata duka a cinyarta. "Wallahi kina daukar alhakin yayana, kinsan dai abinda yake nema." "Ai idan batayi hakan ba, babu mai kiranta da Bintu." Cewar Hafsa cikin dariya. Ta zaro ido. "Lallai ma, kunyi zaton nima ina iskanci ko? Ba abinda na iya." Sukayi dariya. Kasancewar basusan labarin ba yasa Aisha fesa musu. Ai kuwa nan sukayita tuntsire dariya. Ranar kwanan farinciki sukayi, ita kuwa tana sane ta k'ular da Ma'aruf. Har washegari daurin aure da yini, babu abinda ya sake hadasu, koda tayi kiransa a waya sai ya k'i dauka. Hakanan ko sun hadu d'akin Mami bai ko kallonta. Jikinta yayi sanyi, da kanta ta soma neman shiri. Don haka ana ta shirye-shiryen tafiya dinner, itama ta shirya cikin ankon da sukayi kalar pink, ta ci ado har ta gaji da haduwa, jikinta babu dadi, daurewa kawai takeyi don tana bala'in son zuwa fatin. Ta dubi Aisha, "Kuna iya tafiya, kinsan ni tare da King dina zan taho." Sukayi murmushi kafin ta fita zuwa sashensa na gidan. Saidai yayanta Saifu ta iske, shi ke sanarmata yana can gidansa. Haka Mami ta saka aka kaita don ta tafi kafe saidai su tafi tare. Da shigarta ta iskeshi saman doguwar kujera a kishingide yana amsa waya. Sam baiji shigowarta ba, ta karaso da sallamarta, alokacin ya ji ya amsa saidai bai ko dubeta ba. Ta zauna da sauri sanadin jiri-jiri da ke kwasarta, jikinta yayi zafi, ta tuna rabonta da abinci tun wajen k'arfe d'aya na rana da ta ci. Bayan ya kammala wayar ya mik'e zaune. Sai lokacin ya dubeta, tayi mishi kyau kwarai. Ya yi kamar bai ga kwalliyar ba ya kauda kansa. Ta marairaice fuska gami da mik'ewa tsaye. Babu shiri ta soma kokarin zubewa awajen, da azama ya tarbota. "Lafiya?" Ta soma kukan shagwa6a. "Kaine kake fushi da ni, duk ka tayarmin da hankali." Ya dagota. "Abar wannan maganar, jikinki fa da zafi, kin kuwa ci abinci?" Ta girgiza kai. Ya mike yana fad'in "Ina zuwa." Ta kwanta a saman kujerar tayi lamo tana tunanin yanzu watakil ansoma shagalin fatin. Can sai gashinan ya fito cikin kananun kaya. Ya dagata zaune yana jan tsaki. "Wannan kayan ma ai k'arawa kanki wani nauyin ne Queen." Zai ragemata ta nok'e har da hawayenta. "Nifa wajen Dinner na biyo mu tafi." Ya zaro ido. "Kina a wannan halin? A'a muje dai na nema miki abinci sai mu wuce asibiti." Ya nace, itama ta kafe harda kukanta, ya zaayi ma bataje dinar nan ba bayan ta ci buri akansa? Haka ya amince suka tafi, tayi-tayi ya chanja kaya ya k'i. Ta lafiyarta yakeyi. Yaso su soma zuwa asibitin, ganin haka nan da nan ta mike ta daure tace ita fa ta samu sauki daman yunwa ce. Ya girgiza kai kawai. Bintu akwai k'arfin hali. Sun shiga yana rik'e da ita har mazauni. Bayan sun zauna, ya sanya aka kawomata abinci tun kafin ma a soma ciye-ciye. Ta ci tayi nak ta ture, sai lalla6ata yakeyi, sun burge mutane da yawa musamman sarakan soyayya, wato 'yan ROF whatsapp.(lol). Fauza kasa jurewa tayi ta isa wajensu ta daukesu hoto, tana fatan kasancewa da habib dinta haka wataran. Sally ta k'ara kankame hannun Hashim dinta a kunne ta radamishi. "I love you." Shima ya ji sanyi, don soyayyar abokinsa da Bintu na burgesa. Ba'a je ko'ina ba ta soma shek'a amai. Hankulan mutane ya dawo kansu, Ma'aruf ya ja ta sukayi waje, ma'aikatan wurin suka gyare wajen tsaf aka cigaba da shagali kowa hankalinsa yana ga Bintu. Ko meke damunta? Kai tsaye shi kuma yana kaita mota suka nufi asibiti harda Atika wacce yasa ta hau su je. Likita ya aunata ya buk'aci fitsarinta, ai kuwa result ya nuna tana da ciki. Hamdala kawai Ma'aruf yayi ta yi har suka fito hannunsa cikin nata. Suna shiga mota ya sumbaci goshinta. Hawaye suka zubomata na farinciki. Nan dai zance ya cika gidan ta bakin Atika cewar Bintu na dauke da juna biyu. Kowannensu ya hau murna, Bintu bata da masaniyar wainar da ake toyawa don yayannata cewa yayi gidanta zata kwana ta huta. Har aka kai Aisha babu inda ta fita, Mami ma ta goyi bayan Ma'aruf a wannan karon. * * * SANNU BATA HANA ZUWA...! A yau har ga Bintu ta cika watanni tara cif dauke da cikin bebinsu da Ma'aruf. Sai kuma a wannan lokacin ne ta shiga damuwa sosai, ba na komai ba sai na tsoron haihuwa. Sau da yawa Mami ke kwantar mata da hankali don tuni ta komo gidan Mamin duk kuwa da ba da son ran mijinnata ba wanda yaso ta zauna gabansa ta haihu. Takan ce, tana tsoron mutuwa kamar yanda Ma'u ta rasu. Ma'aruf da zarar ta soma zantuka haka har ma ta hau rok'on gafararsa, sai ya ji hankalinsa ya tashi, akwai sadda ya zubda hawaye yana rok'onta akan ta bar sanyamishi damuwa. Haka dai har wata ranar litinin da daddare nak'uda ta taho gadan-gadan. Babu shiri Mami ta kwasheta sai asibiti. Cikin ikon Allah, mintuna baifi arba'in ba da zuwansu, ta haifo d'iyarta mace santaleliya. Ma'aruf wanda ya zo tun wayar da Mami tayi mishi, suna tare da Mamin a tsaye suka ji kukan jaririyar. Sai kuma nos ta fito ta sanar dasu haihuwar. "Ya lafiyar uwar?" Shine farkon abinda Ma'aruf ya nemi sani. Hankalinsa ya kwanta jin tana cikin koshin lafiya. Murna kam ba'a cewa komai, washegari haka yan uwa sukayita zuwa gidan Mami don a washegari aka sallamesu. Abinda ya burge Ma'aruf ga Bintu, bai wuce ganin da kanta ta nemi a sanya sunan Ma'u ba, shi kam ya so sanya sunan Innarta. Haka nan aka yiwa yarinya hud'uba da Asma'u suna kiranta BINGEL(lol). * * * BAYAN WASU SHEKARU...! Barrister Fatima Bintu bakinta ya k'i rufuwa adalilin yau ake bikin yayesu daga makaranta. Tana rik'e da hannun Hanif da Bingel ta rungumosu Yaya Rufa'i ya daukesi a hoto. Ta k'arasa ta sumbaci goshin bebinta Amir mai sunan mahaifinta Muhammad dake rik'e a hannun Abida sabuwar 'yar aikinta. Nan ma ta kar6eshi akayi musu hoto, kafin ta k'arasa ta rungume Maminta tana hawayen farinciki. "Yau ga Bintunki ta fito a yanda kikeso, I am now a Barrister.' Sukayi dariya, itama Mamin ta sharce hawayenta na farinciki. "Allah Shine abin godiya." Sukayi dariya. Ta janyo Aisha wacce ke rik'e da d'anta Mustapha suka had'u suka sanya Mami a tsakiya aka dauki hoton. Daga bisani kuma gaba dayansu har Abba suka dauka. Bintu ta cika tayi fum saboda rashin zuwan Ma'aruf akan lokaci. Har da hawayenta. Koda Abba yayi niyyar kiran wayarsa, hanawa tayi. Har suka bar wajen suka dunguma zuwa gida babu shi da labarinsa. Ganin an nufi gidan Abba bata damu ba ko kad'an, fushin da takeyi da mijinta yasa ta yanke koda kwana ta kama ta kwana anan ba zata k'i ba. Saidai ta cika da mamakin yanda aka faka motoci a kofar gidan, su d'inma anan sukayi fakin suka fito cike da mamaki tattare da su. Fitowar Saifu yayan Bintu dauke da d'ansa a hannu ne ya basu mamaki. Ya gaidasu Abba da fara'arsa, baice komai na daga tambayoyin da suke mishi ba yayita musu iso zuwa ciki. A babban falon na Mami suka tarar da mutane cike, Ma'aruf na tsaye gaban wani k'aton cake yana kunna kendir. Ya dago ya sakarwa matarsa murmushi, tuni dukkan wani 6acin ranta ya gushe. Nan fa bakin kowa ya gaza rufuwa ana ta murnar ganin juna. Bayan Bintu ta yanka cake tayi kamar zata sanyawa Ma'aruf sai tayi azamar turashi bakin Hanif, akayi dariya. Duk da iyayen dake a falon, baisa yayi dabarar yi mata magana ba. "Ina sonki fiye da kullum. Babbar kyautarki shine, na biyamiki umrah." Ta dago dara-daran idanunta ta dubeshi tana dariyar farinciki. Da ace akwai hali da ta rungume mijinta, kawai sai ta soma fidda hawayen farinciki tana dubansa. A haka Rufa'i ya daukesu hoto ana dariya. TAMMAT BI HAMDULILLAH Inda mukayi kuskure a gafarcemu. Nagode sosai yan uwana masoyana, shakka babu kun nunamin kauna, fatana Allah Ya hadamu haka a aljannarSa. Amin. Godiya ta musamman ga Ummu Abdool, Bingel. Kun zamo wasu jigo a rayuwata, Allah Ya bar zumunci, amin
Showing posts with label BINTU 1-END. Show all posts
Showing posts with label BINTU 1-END. Show all posts
Tuesday, August 15, 2017
BINTU Part 007 (THE END)
Tana lek'ensa ta windo har ya bar gidan sannan ta sauke labulen gami da zubewa kan kujera tana dariyar farinciki. "Na sameshi!" Ta fad'a a fili kafin ta dauki ragowar tea din ta saita daidai saitin da ta ga ya sha ta hau korawa a cikinta tana mai lumshe idanu, wani irin soyayyarsa na k'aruwa a ranta. Ta dire kofin bayan ta kammala, sai kuma jikinta yayi sanyi. Baifa furta yana sonta ba? "Sannu bata hana zuwa." Ta ayyana hakan a ranta. Cike da nishad'i ta tattara kayan karin ta mayar kicin domin ji tayi gaba d'aya yunwarta ta kau. Ranar yini tayi da wani nishad'i marar misaltuwa. To shi d'inma hakan ce gareshi, don har Abba saida ya tambayeshi ko anyimishi albishir da aljanna. Dariya kawai yayi. Itama a ranar sunyi waya da Aisha, wacce shirye-shiryen biki ya 6oyeta don alokacin sauran watanni biyu da kwanaki. Nan Aisha ta sanarmata lallai a wannan daren tayi kokarin kyautatawa mijinta. Tayi shiri, irin shirin da tasan zaiyi saurin birkita tunaninsa. Sukayi dariya. "Kinsan fa har yanzu ya k'i furtamin yana sona?" Tsaki Aisha ta ja. "Kedai ki bada kai, wannan kuma sadda zai furta ma bakisani ba, kuma na gayamaki wallahi Yaya yana sonki. Ki bi dai shawarwarina. Na yarda zaki iya fin haka." Suka k'ara darawa kafin suyi sallama. Misalin d'aya na rana, ta dauki waya tayi kiransa kamar yanda Aisha ta gayamata. Saida ta kammala dariyar sunan (Angrybird) da ta sanyamishi. Saidai har ya kammala rurinsa baki d'aga ba. Bata sauke wayar data kunnenta ba sai gashinan ya kira. Ta shige d'akinta tana goye da Hanif wanda yayi bacci a bayanta. "Assalamu alaikum." Yayi sallama cikin tattausan muryarsa. Ta lumshe ido ta bude tana murmushi. "Waalaikumussalam, Barka da rana Yaya." "Bintunaa! Ya dace a chanjawa Yaya suna, a k'ara mishi matsayi please." Tayi shiru batace komai ba, ya d'ora da fad'in. "To gayamin ya kike? Ina bebina?" "Lafiya lau, gashinan yayi bacci." Ya jinjina kai kamar tana ganinsa. "Masha Allah. Kinsan ina nake kuwa?" "A'a " "Gamunan tare da Abba munzo daurin aure Katsina." Ta zaro ido. "Katsina?" Yayi 'yar dariya. "Hey, kin tsorata ko? Ba kwana zanyi ba ai, zanzo ki bani karfin mata goma." Ai tuni ta kashe wayar tana dariya, shima dariyar yayi cikin jin wani irin nishadi marar misaltuwa. Bata motsa daga inda take tsaye ba ta ji shigowar sak'o. Ta bud'o. "Kina k'ara burgeni Bintuna, miss you! Ayi mana addu'ar dawowa lafiya." Ta karanta yafi sau biyar da wani, k'arshe ta zauna gefen gado tana cigaba da karatun. Wani sanyi ne takeji yana ratsa zuciyarta, wai kuwa dagaske Yayanta Ma'aruf d'inne kuwa? Wannan Ma'aruf din da suke yawan samun sa6ani har Mami kan kirasu mage da 6era? Sai kuma ta ji tanason ba shi amsa. "Miss you too, Allah Ya maidoku lafiya YAYANA." Ya saki ajiyar zuciya. Wai meke faruwa haka? Da ace ba gida guda suka task da Bintu ba, kuma baisan soyayya ba, zai iya rantsewa ko wani abin tayi mishi ya soma sonta har haka, irin son da babu wacce ya ta6a yiwa sai Ma'unsa. Ita kuwa Bintu da wuri ta kammala ayyukanta don wajejan hudu na yamma ya shaida mata sun taho. Ta k'ara gyara Hanif ta shiryashi cikin kana kaya marasa nauyi. Itama ta shiga da zummar wanka, ta zaro ido ganin abinda bata zata ba. Tayi shiru, ashe fa tuni aka shiga sabon wata. Hakanan ta hakura ta kimtsa jikinta ta fito. Batayi wani shiga mai birkitarwa ba kawai ta sanya yadinta marar nauyi mai hannu (3quater) dinkin doguwar riga, saidai ya kamata. Haka ya dawo gidan har da ledarsa ta kaza a hannu. Dariya ta ciyota alokacin da ta sanya hannu tana kar6ar ledar. Ya matso da ita. "Ya akayi?" Ta sunkuyar da kanta tana girgiza kai. "Bakomai." Tayi furucin a hankali. Yayi 'yar dariya. "Ashe inada maganin tsiwarki? Lallai nayi sake a baya. Yau dai (the game will be over). Daga haka ya shige dali yana wani takun kasaita har batasan sadda tayi dariyar mugunta ba (Kuyi maneji da wannan ..kuyi hkr wlh ba da son raina yake kadan ba.!!) Bayan sallar Magriba, suna zaune yana wasa da Hanif ita kuwa ta dukufa tana zubamishi abinci kana ganin fuskokinsu kasan suna cike da jin nishad'i. Shi nasa na murnar yau zai samu abinda ya jima cikin tsananin so da bukata, yayinda ita kuma ya had'e mata biyu, ga hirar da sukeyi cike da nishad'i ga kuma na muguntar da Ma'aruf baisan da zamansa ba, har sai kuma ta ji ya bata tausayi. "Wai Bintuna duk me ya sanyaki wannan fara'ar?" Ta dubeshi ta kauda kai tana murmushi. "Bakomai." Murmusawar shima yayi, zuwa yanzu ya gama fahimtar ita dinma tana sonshi, kawai dai jan aji ne irin na mata. Misalin goma da rabi na dare, suna zaune daga shi sai ita a falo, Sarah da Hanif sunyi nisa da bacci. Ta mik'e tsaye, ya rik'o hannunta wanda ta jishi har kwanyarta. Ta dubeshi, idanunsa a lumshe. "Ina zaki?" Ya nemi sani da muryarsa wacce ta chanja sanadin tunaninta da ya fad'a. Ta kuramishi idanu. "Zanyi shirin kwanciya ne." Ya saki hannun bayan ya sauke idanunsa akanta, ta kauda nata da sauri sai kuma ta shige. Bayan ya shirya ya sanya hannu ya dauki wayarsa ya kirata, tana gani ta k'i amsawa saboda wani nauyinsa da takeji. Ta zubawa wayar ido yanata ruri, alokacin ne kuma ta ji shigowarsa dakin. Ta mik'e tsaye da sauri, sai kuma tayi k'as da kanta ganin ko riga babu a jikinsa. Ya dubeta daga sama har k'asa, sannan ya sauke ajiyar zuciya ganin irin shigar da tayi wanda shi kadai Allah Ya yarjewa gani. "Meyasa bakya amsa kirana? Sai ma ido da kika zubawa wayar?" Ta girgiza kai, baki bari tayi magana ba ya soma abinda ya matsu da shi. Har saida ta kaisu da zubewa a k'asa. Alokacin kuma ya d'ago ha6anta har numfashinsu na bugun hancinansu da sauri-sauri. "Tashi muyi sallah." Shaf, ta mance da batun rashin sallarta sai alokacin. Ta lumshe idanunta, murya na rawa ta amsa. "Bani da sallah." Ya saki ha6anta yana murmushi, duk a zatonsa wasa takeyi. "Bari na gani." Ya d'ago ya dubeta kamar yayi kuka, sai kuma ya mik'e ya fita kawai. Tausayinsa ya kamata, da kyar ta iya mikewa ta kashe fitilu ta kwanta. Babu jimawa da kwanciyarta, ta ji shigowarsa hakan yasa ta saurin rufe ido. Kwanciya yayi ya juyota jikinsa ya sumbaci goshinta. "Allah Ya tashemu lafiya." Ta amsa a hankali. Cikin dare ya kasa saita kansa, haka yayita juyata son rai yana yanda yaso, kafin a karshe ya mike ya bar mata dakin. Ta bishi da kallon tausayi yanda yayi mata da kuma kalaminsa gareta har yana furucin bazai iya rayuwa babu ita ba. Ta lumshe ido tana murmushi a haka sabon bacci yayi awon gaba da ita. Shi kuwa tun daga ranar ya rage ra6arta hakanan ya rok'eta da suturta jikinta duk sadda suke tare kada ya sa6a umarnin Mahaliccinsa. Idan kuma ya fita aiki, ta fita makaranta suna tare a waya, bini-bini ya kirata har itama ta saba da kiransa idan ta ji shiru. Baya dawowa gidan sai magriba, haka zasu zauna suyita hira, gaba d'aya yanzu ya sakar mata har ta daina kunyarsa. Hirarsu a yanzun ya bambanta da na baya don hirar soyayya ce da mutunta juna. Kamar dai a yau, tana kwance saman doguwar kujera tana lissafa kwanakin period dinta, a goben ne take da kwana bakwai cif wanda a kwanan zatayi wanka. Ta ji shigowar motarsa da tsayuwarsa. Saidai kafin ta motsa wayarta ta hau k'ara, ta dauka ta duba. Tayi mamakin ganin yayannata ne. Ta d'aga da sallama, ya amsa. "Ki fito, yau zance nazo." Abin ya bata dariya. Ta amsa da toh. Dakinta ta shiga ta k'ara kallon kanta. Riga da siket na brown lace ne a jikinta, tayi kyau ya zauna d'as a jikinta. Ta k'ara feshe jikinta da turare ta murza jan baki. Mayafinta ta dauka marar nauyi ta yafa a kafad'arta, sannan ta zura takalminta mai tsini ta fita. Hanif na tare da Sarah a d'aki, bata bi ta kansu ba ta fita. Yana sanye da shadda sky blue, hularsa kuma dark blue. Dinkin boda, ya zauna sosai jikinsa, yayi kyau har ya gaji. Kafarsa d'aya ya tankwashe saman kujera, kansa kwance a kujerar ya zubawa hanya ido, a sannu kuma yana sauraron kid'an dake tashi a rediyon motarsa. Ido ya zubamata sadda ta fito tana wani irin taku na jan hankali, bata ganinsa sakamakon gilashin ba haske, saidai jikinta ya bata ita din yake kallo. Yasa hannu ya bud'e mata gaban motar tun kafin ta k'araso. Ta shigo ta rufe. Tayi mishi sallama. Ya sauke ajiyar zuciya don baisan Bintu na da kyau haka ba saida ya soma sonta. Ya amsa yana tambayarta mutan gida Abin ya sanyata dariya. "Wai Yayana menene haka?" Hannunta ya rik'o. "K'ara'i, sonki ya sanyani Bintuna." Ta zaro ido tana dubansa, baki ta6a cewa yana sonta ba, zataso a yau ya furta. Ya hura idanun. "Bakya sona ne? Yau fa baki zaki bude malama, hira ta kawoni, zan bayyana miki sirrin dake raina." Tayi farr da ido, ya kauda kai yana wani irin murmushi, ya kar6i wannan sak'on. "A baya, nayi zaton mace d'aya ce ta dace da ni, mace d'aya ta dace na mallakawa komai nawa. Nayi zaton yanda nake, ni d'in MIJIN MACE D'AYA ne, banyi aune ba, mutuwa tayi min YANKAR KAUNA da matar da na so na kuma fi sonta fiye da kowace mace a duniya." Ya d'an tsagaita kafin ya cigaba da magana. "Na zo nayi biyayya bayan da na jajircewa zuciyata na yarda da KADDARA, na aureki." Ya k'ara matse yatsunta yana dubanta duk kuwa da cewar idanunta baya gareshi. "Bintun Mami, Bintun Ma'aruf. Kinsan me yafi had'ani dake?" Sai lokacin ta dubeshi ta girgiza kai gami da turo baki. Yayi 'yar dariya. "Bakya ji, na lura kina da fitina da tsokanar fad'a. Ba kuma sai na fad'amaki wanene Ma'aruf ba. Wannan shine ya kawo rashin jituwarmu. Kafin kuma na zo na had'u da jarabta ta sonki. Ban k'ara sanin ina sonki ba, sai bayan da na nisanta gareki har na kwanaki talatin da d'aya, zuwana Lagos kenan. Bayan na dawo nayi kokarin soma janyoki a jikina domin nuna miki irin so da kaunar da nakeyi miki a aikace batare da na furta ba." Ya d'anyi shiru yana mai cigaba da murza yatsunta, ta sauke ajiyar zuciyar tana kar6ar sak'on a sannu-sannu. "My Queen." Yayi furucin da wata muryar da ta ji kamar ba ta shi ba. "Ina sonki, ina kaunar na kasance tare da ke har abada. Kin shirya kar6ata matsayin miji kuma uba ga 'ya'yanki?" Ta sunkuyar da kanta k'asa. Gaskiya ne, da ba'ason zurfafa k'iyayya a addini, bakasan sadda zaka soma son abinda kake k'i ba. Ya d'ago ha6anta. "A'a my queen, you have to answer me." Ta lumshe idanunta. Murya na rawa ta furta a hankali. "Na amince, ina sonka." Haka yayita aika sak'o kafin ya barta yana murmushi ya soma da bud'e kofofin. "Nagode my queen." Daga haka suka shiga ciki, ran kowannensu k'al. Ranar ma basu raba shimfid'a ba. Washegari kuwa da Magriba, yana shigowa ya risketa tana sallah a d'akinta. Ai baisan sadda ya washe hak'ora ba don farinciko sannan ya juya zuwa d'akinsa. Abincin daren nan dakyar ya ci. Ita kuwa gaba d'aya ta tsorata da yanda ya soma nunamata. Haka dai ta daurewa zuciyarta ganin ya riga ya gama matowa. A daren bayan sunyi sallar nuna godiya ga Mahaliccinsu yayi musu dogon adduoi. DAREN ALKHAIRI KENAN...! * * * Kuka takeyi sosai, yana rarrashinta, dole tayi shiru ganin yanda duk ya bi ya damu kansa da kukannata. Da kansa ya taimaka mata ta tsarkake jikinta kafin ya barta ta k'arasa. Ranar ya tsinci kansa da wani irin farinciki marar misaltuwa. Lallai Allah Ya mishi babbar kyauta, a yau gashinan ga madadin Asma'u. Yau shi ya taimakawa Sauda da d'awainiyar gidan, ita kuwa kunya ce ta hanata fitowa ma. Tana jin shigowarsa d'akin tayi saurin ture kanta k'ark'ashin filo. Ya k'arasa yana dariya ya hau yi mata cakulkuli, babu shiri ta hau dariya gami da ture filon. Ya sumbaci goshinta, ta lura yanason yin hakan kafin ya kwanta ya soma yi mata wasu nauyayyun zantuttuka acikin kunnenta. Zata mik'e cikin zafin nama ya janyota, tayi narai-narai da ido, kwalla suka cikamata idon. "Don Allah kayi hakuri." Ya kwaikwayi muryarta. "Don Allah ki nunamin karfinki na mata goma." Ai sai ta tura kanta jikinsa tana dariya. Yayi mata kyakkyawan runguma. * * * Acikin wannan satin, ba'a cewa komai. Da ka gansu kasan suna cike da more rayuwa babu wata matsala a gabansu. Sai gashi wata muguwar shakuwa ta daban ta shiga tsakanin Bintu da Ma'aruf wanda ta bawa kowa mamaki. Akwai sadda da yamma suna zaune gaba d'aya a falon Mami ana hira har Hashim da Sally wadanda suka kawowa Mamin ziyara, lokacin sauran kwanaki biyar ya rage bikin Aisha. 'Yar kwarewa Ma'aruf yayi, nan da nan Bintu ta rikice ta mance a inda suke ta hau shafa bayansa tana mai mik'a mishi ruwa. Cike sa tausayawa tace. "Sorry my king." Ya amsa, gyaran muryar da Rufa'i yayi ta farkar da su. Mami dai kauda kanta tayi kawai tana murmushi, yayinda Rufa'i da su Hajara suka sanya dariya. Ma'aruf ko a jikinsa sai ma ita Bintun ce ta dan ji nauyi. "Oh, Allah Hakim, yau 'yar Mami ce ke wannan rikicewar akan abin gudunta? Soyayya lallai tana dadi " Mami ta mike don sai alokacin ta ji kunya. Daman ita Bintu ke kunyar, ai kuwa tana bada baya ta dubi Yaya Rufa'i. "To meye? Wasu ma suyi mana." "Lah, ni kike gayawa haka? Eh lallai, kinmanta sadda yake bulale ki nake yare miki? Aisha kinga halin d'an adam." Bintu na dariya ta zauna gefen mijinta wanda ke sauraronsu da murmushi dauke saman fuskarsa. "To ai bulala ce ta soyayya, yanzu ba gashinan tayi rana ba, ai hakane ko my king?" Suka tuntsire da dariya har Ma'aruf din. "Yes my queen, ashe kingane. Ku dai ku rike girmanku ba'a shiga tsakaninmu da queen, ko harshe da hak'ori ma haka suka ganmu suka kyale. Ato." Dariyar aka k'ara. Hashim ya d'ora da fad'in. "To d'an iska, dadin abin dai..." "Ya isa." Ma'aruf ya dakatar da shi ta hanyar mik'ewa yana dariya gudun kada yayi mishi iskanci. "Malam tashi muje ku gaisa da Abba." Haka suka wuni cike da jin wani irin annashuwa. * * * BIKI BUDURI....! ((SAIRAN POST DAYA KO BIYU IN SHA ALLAH..!) A yau ake bikin sanya Aisha a lalle. Wannan yasa gidan nasu yake a cike da 'yan uwa, cikinsu kuwa har da mutanen Rano. Wannan karon har Umma abokiyar zaman Inna itama ba'a barta a baya ba wajen halartar bikin autar Mami. Bintu babu zama, sune wancan babban shagon na kayan kicin, sune acan shagon gyaran gashi. Ya zamana ta dawo gidan da zama, duk yanda Ma'aruf yaso hanawa bai samu hakan ba kasancewar ta samu daurin gindi wajen Mami. A daren da akayi kamun Aisha, suna zaune a can d'akinsu tare da su Atika harma da Hafsa kanwar Ma'u wacce itama takanas ta zo kwana adalilin mijinta yayi tafiya, kasancewar gidansu basu da sa ido ballantana har abin ya zama wani babban al'amarin da zai shafi ZUMUNCI A YAU. Sai hira sukeyi suna kyalkyala dariya. Rabin hirar kuwa Atika ke basu akan matar saurayinta. Yanda yake bala'in shakkar daukar koda wayarta a gaban matar. Wayar Bintu da tayi k'ara ya sanyasu dubanta suna tsokana. "Toh sarakan soyayya." Ta murgud'a baki tana dariya kafin tace suyi shiru ta d'aga da sallamarta. "My king, fatan dai ka bar fushin?" "Idan kinaso na daina, zo ki sameni anan d'akina. Ta zaro ido. "Lah, baka tafi gida ba? Karfe goma fa " Yayi 'yar dariya. "Kina wasa, ai na gayawa Mami saidai nima na kwana a gidannata." Ta hadiye dariyarta, suma tasu suka gimtse don kuwa a hands free wayar take. "Allah Sarki My King, shikenan ai, da safe Dan dolo sai ya mik'o maka kayan karinka. Allah Ya tashemu lafiya." Ta kashe wayar gaba d'ayanta, me zasuyi banda dariya. Aisha ta d'akamata duka a cinyarta. "Wallahi kina daukar alhakin yayana, kinsan dai abinda yake nema." "Ai idan batayi hakan ba, babu mai kiranta da Bintu." Cewar Hafsa cikin dariya. Ta zaro ido. "Lallai ma, kunyi zaton nima ina iskanci ko? Ba abinda na iya." Sukayi dariya. Kasancewar basusan labarin ba yasa Aisha fesa musu. Ai kuwa nan sukayita tuntsire dariya. Ranar kwanan farinciki sukayi, ita kuwa tana sane ta k'ular da Ma'aruf. Har washegari daurin aure da yini, babu abinda ya sake hadasu, koda tayi kiransa a waya sai ya k'i dauka. Hakanan ko sun hadu d'akin Mami bai ko kallonta. Jikinta yayi sanyi, da kanta ta soma neman shiri. Don haka ana ta shirye-shiryen tafiya dinner, itama ta shirya cikin ankon da sukayi kalar pink, ta ci ado har ta gaji da haduwa, jikinta babu dadi, daurewa kawai takeyi don tana bala'in son zuwa fatin. Ta dubi Aisha, "Kuna iya tafiya, kinsan ni tare da King dina zan taho." Sukayi murmushi kafin ta fita zuwa sashensa na gidan. Saidai yayanta Saifu ta iske, shi ke sanarmata yana can gidansa. Haka Mami ta saka aka kaita don ta tafi kafe saidai su tafi tare. Da shigarta ta iskeshi saman doguwar kujera a kishingide yana amsa waya. Sam baiji shigowarta ba, ta karaso da sallamarta, alokacin ya ji ya amsa saidai bai ko dubeta ba. Ta zauna da sauri sanadin jiri-jiri da ke kwasarta, jikinta yayi zafi, ta tuna rabonta da abinci tun wajen k'arfe d'aya na rana da ta ci. Bayan ya kammala wayar ya mik'e zaune. Sai lokacin ya dubeta, tayi mishi kyau kwarai. Ya yi kamar bai ga kwalliyar ba ya kauda kansa. Ta marairaice fuska gami da mik'ewa tsaye. Babu shiri ta soma kokarin zubewa awajen, da azama ya tarbota. "Lafiya?" Ta soma kukan shagwa6a. "Kaine kake fushi da ni, duk ka tayarmin da hankali." Ya dagota. "Abar wannan maganar, jikinki fa da zafi, kin kuwa ci abinci?" Ta girgiza kai. Ya mike yana fad'in "Ina zuwa." Ta kwanta a saman kujerar tayi lamo tana tunanin yanzu watakil ansoma shagalin fatin. Can sai gashinan ya fito cikin kananun kaya. Ya dagata zaune yana jan tsaki. "Wannan kayan ma ai k'arawa kanki wani nauyin ne Queen." Zai ragemata ta nok'e har da hawayenta. "Nifa wajen Dinner na biyo mu tafi." Ya zaro ido. "Kina a wannan halin? A'a muje dai na nema miki abinci sai mu wuce asibiti." Ya nace, itama ta kafe harda kukanta, ya zaayi ma bataje dinar nan ba bayan ta ci buri akansa? Haka ya amince suka tafi, tayi-tayi ya chanja kaya ya k'i. Ta lafiyarta yakeyi. Yaso su soma zuwa asibitin, ganin haka nan da nan ta mike ta daure tace ita fa ta samu sauki daman yunwa ce. Ya girgiza kai kawai. Bintu akwai k'arfin hali. Sun shiga yana rik'e da ita har mazauni. Bayan sun zauna, ya sanya aka kawomata abinci tun kafin ma a soma ciye-ciye. Ta ci tayi nak ta ture, sai lalla6ata yakeyi, sun burge mutane da yawa musamman sarakan soyayya, wato 'yan ROF whatsapp.(lol). Fauza kasa jurewa tayi ta isa wajensu ta daukesu hoto, tana fatan kasancewa da habib dinta haka wataran. Sally ta k'ara kankame hannun Hashim dinta a kunne ta radamishi. "I love you." Shima ya ji sanyi, don soyayyar abokinsa da Bintu na burgesa. Ba'a je ko'ina ba ta soma shek'a amai. Hankulan mutane ya dawo kansu, Ma'aruf ya ja ta sukayi waje, ma'aikatan wurin suka gyare wajen tsaf aka cigaba da shagali kowa hankalinsa yana ga Bintu. Ko meke damunta? Kai tsaye shi kuma yana kaita mota suka nufi asibiti harda Atika wacce yasa ta hau su je. Likita ya aunata ya buk'aci fitsarinta, ai kuwa result ya nuna tana da ciki. Hamdala kawai Ma'aruf yayi ta yi har suka fito hannunsa cikin nata. Suna shiga mota ya sumbaci goshinta. Hawaye suka zubomata na farinciki. Nan dai zance ya cika gidan ta bakin Atika cewar Bintu na dauke da juna biyu. Kowannensu ya hau murna, Bintu bata da masaniyar wainar da ake toyawa don yayannata cewa yayi gidanta zata kwana ta huta. Har aka kai Aisha babu inda ta fita, Mami ma ta goyi bayan Ma'aruf a wannan karon. * * * SANNU BATA HANA ZUWA...! A yau har ga Bintu ta cika watanni tara cif dauke da cikin bebinsu da Ma'aruf. Sai kuma a wannan lokacin ne ta shiga damuwa sosai, ba na komai ba sai na tsoron haihuwa. Sau da yawa Mami ke kwantar mata da hankali don tuni ta komo gidan Mamin duk kuwa da ba da son ran mijinnata ba wanda yaso ta zauna gabansa ta haihu. Takan ce, tana tsoron mutuwa kamar yanda Ma'u ta rasu. Ma'aruf da zarar ta soma zantuka haka har ma ta hau rok'on gafararsa, sai ya ji hankalinsa ya tashi, akwai sadda ya zubda hawaye yana rok'onta akan ta bar sanyamishi damuwa. Haka dai har wata ranar litinin da daddare nak'uda ta taho gadan-gadan. Babu shiri Mami ta kwasheta sai asibiti. Cikin ikon Allah, mintuna baifi arba'in ba da zuwansu, ta haifo d'iyarta mace santaleliya. Ma'aruf wanda ya zo tun wayar da Mami tayi mishi, suna tare da Mamin a tsaye suka ji kukan jaririyar. Sai kuma nos ta fito ta sanar dasu haihuwar. "Ya lafiyar uwar?" Shine farkon abinda Ma'aruf ya nemi sani. Hankalinsa ya kwanta jin tana cikin koshin lafiya. Murna kam ba'a cewa komai, washegari haka yan uwa sukayita zuwa gidan Mami don a washegari aka sallamesu. Abinda ya burge Ma'aruf ga Bintu, bai wuce ganin da kanta ta nemi a sanya sunan Ma'u ba, shi kam ya so sanya sunan Innarta. Haka nan aka yiwa yarinya hud'uba da Asma'u suna kiranta BINGEL(lol). * * * BAYAN WASU SHEKARU...! Barrister Fatima Bintu bakinta ya k'i rufuwa adalilin yau ake bikin yayesu daga makaranta. Tana rik'e da hannun Hanif da Bingel ta rungumosu Yaya Rufa'i ya daukesi a hoto. Ta k'arasa ta sumbaci goshin bebinta Amir mai sunan mahaifinta Muhammad dake rik'e a hannun Abida sabuwar 'yar aikinta. Nan ma ta kar6eshi akayi musu hoto, kafin ta k'arasa ta rungume Maminta tana hawayen farinciki. "Yau ga Bintunki ta fito a yanda kikeso, I am now a Barrister.' Sukayi dariya, itama Mamin ta sharce hawayenta na farinciki. "Allah Shine abin godiya." Sukayi dariya. Ta janyo Aisha wacce ke rik'e da d'anta Mustapha suka had'u suka sanya Mami a tsakiya aka dauki hoton. Daga bisani kuma gaba dayansu har Abba suka dauka. Bintu ta cika tayi fum saboda rashin zuwan Ma'aruf akan lokaci. Har da hawayenta. Koda Abba yayi niyyar kiran wayarsa, hanawa tayi. Har suka bar wajen suka dunguma zuwa gida babu shi da labarinsa. Ganin an nufi gidan Abba bata damu ba ko kad'an, fushin da takeyi da mijinta yasa ta yanke koda kwana ta kama ta kwana anan ba zata k'i ba. Saidai ta cika da mamakin yanda aka faka motoci a kofar gidan, su d'inma anan sukayi fakin suka fito cike da mamaki tattare da su. Fitowar Saifu yayan Bintu dauke da d'ansa a hannu ne ya basu mamaki. Ya gaidasu Abba da fara'arsa, baice komai na daga tambayoyin da suke mishi ba yayita musu iso zuwa ciki. A babban falon na Mami suka tarar da mutane cike, Ma'aruf na tsaye gaban wani k'aton cake yana kunna kendir. Ya dago ya sakarwa matarsa murmushi, tuni dukkan wani 6acin ranta ya gushe. Nan fa bakin kowa ya gaza rufuwa ana ta murnar ganin juna. Bayan Bintu ta yanka cake tayi kamar zata sanyawa Ma'aruf sai tayi azamar turashi bakin Hanif, akayi dariya. Duk da iyayen dake a falon, baisa yayi dabarar yi mata magana ba. "Ina sonki fiye da kullum. Babbar kyautarki shine, na biyamiki umrah." Ta dago dara-daran idanunta ta dubeshi tana dariyar farinciki. Da ace akwai hali da ta rungume mijinta, kawai sai ta soma fidda hawayen farinciki tana dubansa. A haka Rufa'i ya daukesu hoto ana dariya. TAMMAT BI HAMDULILLAH Inda mukayi kuskure a gafarcemu. Nagode sosai yan uwana masoyana, shakka babu kun nunamin kauna, fatana Allah Ya hadamu haka a aljannarSa. Amin. Godiya ta musamman ga Ummu Abdool, Bingel. Kun zamo wasu jigo a rayuwata, Allah Ya bar zumunci, amin
Share this
Monday, August 14, 2017
BINTU Part 006
BINTU Part 006 . Zuwan Aisha gidan ya yi musu dadi. Haka zasu zauna suyita hirar duniya idan ba makaranta. A kokarin Bintu bai wuce koyaushe ta nunawa Aisha lafiya lau suke da mijinta ba. Har takan dauki waya tayi kiransa saidai har wayar ta gama rurinta baya ko kallonta. Saidai a wayance tayita zuba zance don burge Aisha. Satinsa d'aya da tafiya, amma ko text bai ta6a yi mata ba, da zummar gaisuwa. A yanzu kuwa ta daina samun layinsa, saidai ta ji Aisha tace yayi kiranta ko kuma Mami. Jikinta yayi sanyi, haka kawai ta tsinci kanta da shiga damuwa. Kodai furucinta ya bawa Yaya Ma'aruf haushi? Ashe zai damu da ta nuna damuwa akanshi? Ta kai dubanta ga Aisha wacce ke kwance rigingine a saman gado tana amsa wayar masoyinta Ashir, sai wani narke murya takeyi da murmushi. Daga inda take ta zubawa wayarta ido kawai amma kunnuwanta suna ga Aisha tana sauraronta. Kawai sai ta ji abin ya burgeta, inama ita da Yaya Ma'aruf su dawo haka? Sai ta ji nauyi, kada dai ta kamu da son Ma'aruf ne? Ta girgiza kai, kokusa bata fahimtar abinda akeyi a group din nasu ta whatsapp ta tsinci kanta da komawa contact ta lalubo lambar Ma'aruf, har lokacin hotonnan ne akai bai chanja ba. Ta bud'o tana duba, a hankali takejin wani abu na yawo a zuciya da gangar jikinta. Tayi nisa a kallonsa ta ji Aisha ta makomata filo. "To 'yar is me kikeyi kika wani nutsu?" Bintu batajin wasa a yau, ta ajiye wayar ta dawo kusa da Aisha ta zauna. "Tashi ki bani wasu amsoshi don Allah." Aisha ta mik'e zaune ganin Bintu dagaske take ba wasa. "Ina sauraronki." Bintu ta muskuta tana fuskantarta. "Ya mutum zai gane ya fad'a tarkon so?" Me Aisha zatayi banda dariya. Ta d'aga hannu sama. "Allah na godemaka da Ka bani tsawon ran ganin wannan rana. Cabd'i!" Ta girgiza kai kad'an tana had'e rai cikin son kauda 'yar kunyar da ta ji. "Malama banason haka, idan bazaki bani amsa ba ki bar yimin dariya." Ganin Aisha bata da niyyar dainawa ya sanyata daukar wayarta a fusace ta shige d'aki. Kan gado ta fad'a tana murmushi, daman tasan hakan zata faru tunda ta riga ta gama cika baki a baya. Tana jin sadda Aisha ta shigo gami da zama gefenta, ta had'e rai. Aisha ta gimtse dariyarta ta soma magana duk kuwa da cewa Bintun ta juyamata baya. "Idan ka soma son mutum, zaka tsinci kanka cikin yawan tunaninsa, haka kuma da zarar ka ganshi kun had'a ido zaka ji kamar wasu kibiyoyi ke fitowa daga idanunsa suna shiga naka har suna haddasa maka wani kasala, har ka kasa jure kallon ka sauke idanunka. Komai na mutum zai dawo yana burgeka, ko muryar mutum ka ji sai ka ji wani sanyi na dadi. Babban abinda ke tabbatarwa ka kamu da soyayyar mutum shine KISHI. Nan duniya zakaji baka kaunar abokin takara a zuciyarsa. Ba kuma ka kaunar wani ya ra6eshi da sunan so. Ko yaya kaga ya sakarwa wani fuska ya kula da shi fiye da yanda yake kula da kai sai ka ji tashin hankali sosai, da damuwa da bakin ciki a zuciya. Matukar kina jin wadannan abubuwan da na lissafa, shakka babu (You Are In Love)." Bintu ta bud'e lumsassun idanunta tana duban fuskar gadonta, ta ji gabanta yana bugu da sauri-sauri. Ta kamu da son Ma'aruf yanzu? Kenan dukkan abinda takeji a ranta akansa soyayya ce? "Kenan alamomin da nakeji akan Yaya Ma'aruf suna nuni da cewar inasonsa?" Batasan sadda ta watsowa Aisha tambayar ba. Aisha ta rasa inda zata tsoma ranta don dad'i, don ta jima da gane cewar babu abinda ya ta6a shiga tsakaninsu kawai dai ta barta a yanda ta so ne. "Idan har kina jin abubuwan da na lissafa akansa, to lallai kin fad'a cikin matsanancin soyayyarsa." Sai kuma ta ji wata iriyar kunyar Aisha, lura da hakan ne yasa Aisha mik'ewa ta fita da zummar d'ora musu girki. Ta sauke ajiyar zuciya ta mik'e zaune. "Inason Yaya Ma'aruf." Shine abinda ta furta cikin siririyar murya. * * * "Ina sonki Fatima Bintu." Cewar Ma'aruf kenan a yayinda yake kwance cikin kujera idanuwa a lumshe yana tunanin Bintu wanda ya zame mishi jiki tun zuwansa Lagos. Gaba d'aya kewarta ta dameshi, baisan ya damu da yarinyar ba sai bayan da ya nisanta da ita. Yana fushi da ita akan ta nuna halin ko'in kula da tafiyar da zaiyi, wato dai bata damu da shi ba. A rayuwarsa yana so yaga an damu da shi. Sai ya kai zuciyarsa nesa yake k'in daukar kiranta, lallai shi yana son tilasatawa ransa ya fiddata. Yanaso yabar tunanin wani abu nata da ita kanta. Yana so ya yakiceta a ransa. Wannan yasa ya yanke shawarar yin wata d'ayan da ogansu yace yayi acan batare da ko sau d'aya ya dawo hutun karshen sati Kano ba. Sanin da yayi ma idan yazo ba wani abun zai samu awajenta ba. Ya numfasa ya mik'e zaune. Kalmar nan ta "So" baiyi zaton zai k'ara furtata ba ballantana ya ji ta a ransa. Sai ga shi zuwa yanzu ya gama tabbatarwa ransa ya fad'a dumu-dumu cikin kogin son matarsa kuma 'yar uwarsa abokiyar fad'ansa Bintu. Sai kuma yayi murmushi sadda ya tunano rashin jituwarsu tun afarkon zuwanta gidansu har zuwa girmanta. Rufa'i ya dannawa kira, ya sanar dashi cewar wata d'aya zaiyi don haka ya dauki su Aisha ya maidasu gaban Mami. Daman ya kammala waya da Abba ya shaida mishi. Ya yiwa Bintu gajeran sak'o babu wani abin jan hankali ciki ya shaidamata su had'a kayansu Rufa'i zaizo ya tafi da su gidan Mami. Ta yi kasak'e tana duban sak'on alokacin suna tare da Aisha tana k'ara koyar da ita yanda zata shawo kansa. Ta sanarwa Aisha kafin su soma shiri. Ranta duk babu dad'i jin zai cinye wata d'aya a garin da basu da wani addini sosai. Haka suka kammala shiri suka nufi gidan Mami. Saidai tana ganin Mami ta mance da batunsa ta hau murna. Ganin yanda ta d'an rame sai Mami tayi zaton ko ciki ne. Ta shiga nan nan da ita. Murmushi kawai sukayi ita da Aisha. . A wannan wata d'ayan, wanda aka ci sati uku kenan da Bintu tayi a gidan Mami, ta yishi cikin kwanciyar hankali, duk kuwa da cewar babu wata mu'amalar arziki dake shiga tsakaninta da Yaya Ma'aruf face gaisuwa da take mik'a mishi ta whatsapp, shima wani sa'in za'a nunamata ya je kuma ya gani amma babu amsa. Sai sadda ta ci sa'a ne yake amsa mata, daga amsa gaisuwar kuma bai k'ara cewa uffan. . Tun tana yi har ta soma gajiya, wani sa'in ta watsar. Shi kuwa ya d'auki hakan kawai a matsayin rainin hankali, tunda gwana ce wajen hakan. Ganin yana neman cutuwa sosai da bukatunsa, ya sanyashi farlantawa kansa azumin litinin da alhamis. Haka kuma da yawaita dauke hankalinsa da wani abu da ba zai jawo mishi motsuwarsa ba. Saidai iyakar dauriya yinsa kawai yake, akwai sadda Lawisa ta kusa cin galaba akanshi. Sukayi doguwar hira a waya mai ta6a sosai, a k'arshe suka yanke zata kawomishi ziyara har Lagos. Koda zuwanta da soma gudanar da abubuwa, tun kafin lamura su 6aci, ya dawo nutsuwarsa inda wata kyakkyawar zuciyarsa tayi mishi tuni da "Bafa matarka bace." Da sauri ya fisgeta daga jikinta ya mik'e yana kiran innalillahi a fili kafin ya fad'a ya wanke jikinsa. Nan ya taddata tana hawaye, bai bi ta kanta ba ya kama hanyar fita sai kuma ya tsaya batare da ya juyo ba, cikin kakkausar murya yace. "Kiyi hanzarin barin gidannan tun kafin na dawo." Yana shirin ficewa yaji ta rungumoshi ta baya, ya runtse ido, kafin ya juyo ya tureta. "Karki k'ara kusantoni! Ki rabu da ni Lawisa, please daga yau ki fita hanyata." Hannunsa ta rik'e a gigice. "Bazan fita ba, ka taimaki rayuwata Ma'aruf kada ka barni ha.." . "Ki kyaleni! Ki kyaleni nace!! Kafin na dawo ki tattara abinda kikasan mallakinki ne ki bar gidannan!!" Ya fad'a a tsawance kafin ya sa kai ya fice. Ranta ya 6aci sosai da wannan wulakancin da yayi mata, ita kuwa ko shine autan maza ba zata k'ara kallonsa ba. Ta dauki wayarta ta kira d'aya cikin mutanenta na Lagos. Nan tayi kwatancen inda take, a take kuwa Alhajin yasa direbansa zuwa d'aukarta. Ko wanka bata tsaya yi ba ta shirya tsaf ta bar gidan. Ma'aruf bai jima sosai ba ya dawo, ya ji dad'in rashin ganinta a gidan, ya zauna ya rik'e kai. Idanunsa sunyi ja sun kumbura adalilin kukan da ya ci, yau ga shi ya kusa tafka kuskuren da da ace ya faru ba zai iya yafewa kansa ba. A gefe kuma ga soyayyar dake azabtar da shi, ya ji haushin yanda ta bar turomishi sak'on gaisuwa ko don baya kulata sosai ne? Batasan cewa yana jin dadin hakan ba? Ajiyar zuciya ya saki, fatansa ya kammala aikinsa yaje ayi wacce za'ayi don ba zai zauna da cuta ba. Acan kuwa, Bintu bata k'ara bi ta kansa ba, ta danne abinda takeji a ranta dangane da shi. Ta nemi zuwa Rano ganin iyayenta tunda sun samu hutu. Kasancewar shima Rufa'i zai kai Hajara ganin gida, yasa Abba bai hanata ba ya kira ya sanarwa Ma'aruf. Allah Ya tsare hanya, shine kawai abinda yace. Farinciki ya rufe Bintu yau zata ga 'yan uwanta. Suma can sun shirya tarbarta sosai. Tare suka je har Aisha. Yan uwa sunyi murnar ganinsu. Inna ta shiga nan nan da su. Kwanansu uku suka soma shirin tahowa don Rufa'i zaizo daukarsu. Inna ta k'ara yiwa Bintu nasiha sosai akan rik'e hakkokin mijinta da sauransu. Ta yaba kwarai ganin Bintun ta yi hankali, ta zama wata mai sanyi da nutsuwa, batasan cewa soyayya ke nukurkusarta ba har ta ladabtar da ita ladabin dole. Aisha ta samu abubuwa sosai a wajen 'yar Rano kasancewar bikinta baifi sati hud'u da kwanaki ba. Haka suka baro Rano cike da kewa. A safiyar asabar ne ta koma gidanta kamar yanda Mami ta umarceta. Tare suka je da Aisha sai 'yar yarinyar da aka samo mata da bata wuce sha uku ba da zata tayata rainon Hanif, har da Hanif din wanda suna isa Bintu ta goyeshi a bayanta. Suka gyara komai don a ranar akesa ran dawowar Ma'aruf kamar yanda ya shaidawa Mamin. Kicin suka fad'a suka hau girke-girke. Suna yi Aisha na k'ara bata shawara. "Kwalliya fa zaki ci malama, irin wanda na gayamiki. Kada ki nunamishi fushinki Bintu. Kiyi hakuri, kece dole wajen yi mishi biyayya, amma fa ban hanaki jan aji kad'an ba, karkiyi yanda zai tsinke." Sukayi dariya, Bintu ta dafa kirjinta. "Bakiji yanda gabana ke bugu ba, a tsorace nake fa. Kinsan Yayanki akwai disgawa." Aisha ta girgiza kai. "Akanki ba, kuma kema kinsan abinda yasa yake miki hakan, kin nuna mishi baki da kunya." Bintu ta harareta. Aisha ta dara kad'an. "Allah kuwa rashin girmamashi sosai ne yasa yakemiki wasu abubuwan. Ki tuna keda kanki kin sha yabon yanda sukeyi da Anti Asma'u, yana sakarmata fuska, wasa da dariya duka, koda kuwa a gabanmu ne. Yana da mutunci wallahi ba wai kuma don Yayana bane. Ita gaskiya fa a fad'eta." "Ya gasamin maganganu fa." "Wannan kuma kinfini sanin ta sigar da zaki rama, saidai ina k'ara baki shawara, kada ki ja aji ta yanda zai tsinke wallahi." Murmushi kawai tayi, suka cigaba da aiki suna hira, anan ne Bintu ke labarta mata yanda sukayi da Lawisa. Me Aisha zatayi banda dariya, har da rik'e ciki. Ta jima tana dariya da k'arawa. "Kai wallahi kinyi daidai. Toh wallahi ko don saboda su ya dace ki bada kai bori ya hau kada kiyi sakiyar da ba ruwa." Aisha ta k'arashe tana mai kwafa. "Bakisan wacece Lawisa ba. Yar iska ce, idan ma nayi kiranta karuwa banyi k'arya ba wallahi. Ki tashi tsaye karki bari su samu k'ofa." Bintu ta girgiza kai da gamsuwa da wani irin tsoro. Bayan sun kammala, Aisha ta yiwa Hanif wanka, itama Bintun ta fad'a band'aki. . Mintuna ashirin da kammala shirinta da komai, ta fito falon inda Aisha da Sarah mai rainon Hanif suke zaune suna kallo. Ba Aisha ba, daidai da Sarah saida ta saki baki wajen kallonta. Wani shegen siket ne bak'i mai shek'i amma ba shi da kyalkyali, tsaga gareshi tun daga gwuiwa har k'asa, sai wata riga ja mai igiyoyi wanda ya tafi X ko kirjinta bai rufu yanda akaso ba, bata da hannuwa sai na vest. Ta rufe kanta da jar hula mai wani laushi duk da hakan, tufkakkan gashinta bai kammala rufuwa ba. Ta rik'e k'ugu ta karkace kai kad'an yayinda ta d'an tsuke baki. "Ya?" Aisha ta had'e yatsunta biyu. "Wow! Kinyi kyau wallahi." Ta k'araso tana mai yin farr da ido. "Nasani." Aisha ta d'aka mata duka a cinya sukayi dariya. "Yau dai da wuya Yayanmu ya d'auke idanunsa akanki." Sai kuma jikinta yayi sanyi. Fatanta kada ya gwatsaleta. "I hope so." "In sha Allah, kedai kada ki damu." Cewar Aisha. . Angonnata basu shigo Kano ba sai bayan Magrib. Tuni Aisha ta tattara ta wuce. Duk yanda Bintu ta so zamanta har zuwa sadda zai shigo amma fir ta k'i. Tana zaune ta rik'e Hanif tana mishi wasa ta jiyo tsayuwar mota. Ji tayi gabanta ya fad'i, ashe daman don batason Ma'aruf ne yasa batajin nauyin yin komai a gabansa? Tayi saurin duban Sarah. "Shiga d'aki." Sarah ta mik'e da sauri ta fad'a d'akin Hanif. Kwankwasa k'ofar da akayi yasa ta nufar k'ofar, Hanif yana rungume a jikinta bata ajiyeshi ba. A hankali take tafiya har ta isa k'ofar ta bud'e. Ido cikin ido suka dubi juna. Kowannensu yana kokarin isarwa d'an uwansa sak'o. Sai kuma ya juya da sauri, Isa direban Mami ya tara gami da kar6ar akwatinsa. "Nagode Malam Isa." Ganin haka, yana shigowa ta sa hannu ta rik'o trolley din, shi kuma yayi amfani da hagunsa wajen amsar Hanif dake mak'ale a hannunta na dama. Wani shock sukaji gaba d'ayansu, ya narkar da idanunsa wajen kallon abinda ya fi tafiya da imaninsa a wajenta. Ita kuwa ta dauke idanunta. Murya na rawa ta furta. "Yaya sannu da zuwa." Baki amsa ba har ta juya ta nufi d'akinsa tana rausayar da batasan yanda akayi ta soma ba, wannan kam yafi (natural) tafiyarta had'uwa da tada hankali. Baiyi k'asa a gwuiwa ba ya tura k'ofar da k'afarsa ya mara mata baya. A daidai k'ofa suka had'u, caraf ya rik'o hannunta ya ja zuwa ciki. Ta dubi yanda ya rik'e hannunnata gam kamar mai tsoron a rabasu, sannan ta dubeshi a tsorace, gabanta na bugu da k'arfi da kuma sauri-sauri. Ya ajiye Hanif a saman gado ya jawota gaba d'aya zuwa jikinsa gami da yi mata kyakkyawan rumfa ruf. Gaba d'ayansu sun ji a jikinsu kuwa. Daidai kunnenta ya yi magana. "I'm in need of you Fati." Yanda yayi maganar da irin muryar da yayi amfani da ita wajen yin ce ta sanya tsintar kanta cikin rawar jiki. Bata ankara ba ta jishi yana cigaba da abinda bazata iya jura ba. "A'a! Bintu, not so fast!" Da sauri ta daddage ta tureshi, bata bi takan Hanif ba ta fice a guje. Sai ma ta ba shi dariya, hakan ya sanyashi murmusawa. . Hankalinta ya tashi, ta fad'a kan gado tayi shiru. Ya akayi ta kasa danne zuciyarta? Ta ji haushin kanta, Allah Yasa dai bai gano lagonta ba. Bata kammala tunane-tunanenra ba ya shigo da sallamarsa. Ta daure ta amsa a nutse batare da ta dubeshi ba. Shi d'inma bai damu ba ya mik'amata Hanif. "Rik'eshi." Ta kar6eshi baki bar dubanta ba ya yamutse fuska kad'an. Kamar yace wani abu sai kuma ya fasa ya fice. Ta bishi da kallo tana murmushin takaici, wasu siraran hawaye suka sirnano daga idanunta. Iyakar saninta, tana da rik'o wani lokacin, amma ta rasa dalilin da yasa zuciyarta ke neman gazawa wajen rik'on abinda Yaya Ma'aruf yayi mata. Magana kam, ya gaggasa mata, saidai ta tsorata da abinda Aisha tace akan matan dake kawomasa hari zasu iya zamowa barazana a rayuwarsu. "Amma bai furta yana sonki ba. Kodai bukatar ce kawai yake nufi?" Ta ji zuciyarta babi dadi da wannan tunanin da tayi. Ta yi ringingine saman gado tana duban Hanif dake wasa da zobenta. Tunaninta bai wuce anya dagaske Ma'aruf yana sonta ba? Tafi bawa zuciyarta kawai bukatarta yakeyi. Ba don hakan ba ma bazai nemeta ba. Da bakinsa ya kushe halittarta, ya nuna mata nan duniya ya k'arfin kasancewa da ita. Ita kuwa ta yaya ma Aisha zatace kada ta k'i bada kai? Ta numfasa ta rik'o hannun d'an kamar shine uban take maganarta a fili. "Kai, bazan yi yanda yakeso da wuri ba, sai naji gaskiyar abinda ke zuciyar babanka." Hanif dai banda ihu-ihunsa da 6angale dariya babu wani abu da yakeyi. Ta d'an kama kumatunsa. "Ni ce fa Bintun Mami! Zamiyi maganinsa ko?" Ta k'arashe da 'yar dariya. Ba ita ta fito daga dakin ba saida ya kwalamata kira. Ta janyo (After Dress) ta zura tana murmushi ta fita. Yana zaune saman kafet yana amsa wayar Abbansa, saidai hakan bai hanashi binsu da kallo ba har suka zauna. Hanif ta ajiye gefe sannan ta mik'e ta dauko komai na bukata wajen cin abinci. Ta soma zubawa ta ji muryarsa. "Fati." Bata amsa ba, ba kuma ta fasa abinda takeyi ba, saidai kiranta da yakeyi da Fati, yana sanyamata jin wani abu. Ya k'ara kiranta da murya da sigar da bazata iya ji ta kyale ba. Dole saida ta yi dagaske wajen saita tunani da nutsuwarta, ta d'ago fuskarta a daure, ba k'aramin namijin k'ok'ari tayi ba wajen dubansa. "Na'am." Ganin yanda ta tur6une fuska sai ya ji haushin kansa. Ya manta da cewar Bintu ce fa, yanzun d'an abubuwan da ya aikata zasu sanya ya janyowa kansa sabon raini. . Ya sosa hanci. "Kada dai ki dauki abin d'azu a matsayin wani abu, haka aure ya gada. Eh, kuma ba zai yiwu gida bai k'oshi ba a bawa na waje. Abar batun nan, ya wajaba lallai a gareni ni da ke mu zamto masu tsoron Allah mu dunga sauke hakkokin juna. Hakan zai fi mana kyau." Shi kam, bak'a sosai yaso yarfamata. Baisan ya akayi ya kasa ba. Anzo ga6ar da zata maida martani, don haka ta tura mishi farantin abincin gabansa, ta dubeshi ta kauda kai tana murmushin mugunta. "Na farko dai ni bani da bukata, hakki kuma na yafe nawa, kuma Yaya ka manta kace babu abinda zakayi da jikina. Ka kuma ce kallona kan tashi zuciyarka. Ni ce fa wannan yarinyar da kake fad'a. To nidai bani buk'atar komai nagode da niyya." Ya rasa me zaice? Saidai ya maze ya sha mur. Kamar yayi magana sai ya fasa ya hau cin abinci yana ta nanata maganganunta a ransa. Lallai ma yarinyar nan, wato haka take da riko? Ya ji ta ba shi haushi, ya d'an dubeta da niyyar fad'a, saidai bazai iya ba, wai wane irin muguwarl soyayyarta ce tayi mishi kamu har haka? Kallonta ma wani nishad'antar da zuciyarsa yakeyi. Ya daure batare da ya kalleta ba cikon sanyin murya yace. "Please leave me alone." Yanda yayi maganar baisa ta nuna tausayinsa a fuska ba, iyakar magana ai ya gasa mata. Ta dauki Hanif har da wani cillashi sama tana dariya. Daga haka ta shige dakin Hanif. Ji yayi ransa na k'una, wato ko a jikinta? Shi kuwa yaya zaiyi ne ta gane zuwa yanzu yayi nadama? Lallai so na sanya ladabin dole. Yau shi ke bin Bintu! Ya runtse ido. * * * Tun daga ranar ya fita hanyarta, duk da cewar ta damu a 6oye, hakan baisa a fili nuna kamar batasan me yake yiwa fushin ba. Ta daure ta cigaba da walwalarta yanda ta saba babu ko nuna wata alama ta damuwa. Ranar da ta je gida wuni, shima ranar yana ajiyeta ya nufi gidan abokinsa Hashim. "Ya akayi ne wai? Please mafita zakaban banason dariyar banza." . Hashim ya tsagaita dariyarsa. "Sorry, mamaki dai nayi ne. Kamar ka ace ka auri wannan ficikar yarinyar har ma ka soma sonta? Abinda ko a mafarki bazakayi kuskuren gani ba kenan." Ya fahimci Hashim na tunano mishi furucinsa ne. Ya lumshe ido kafin ya bud'esu ya dubeshi ransa a 6ace, ya ja guntun tsaki. "Bazaka gane ba, banason tuna baya." Hashim ya numfasa ya gimtse dariyarsa. Daidai sadda Salimarsa ta shigo ta ajiye musu kayan motsa baki. Ta tambayi lafiyar Amarya. Ya amsa da murmushi. "Lafiya, ai kun kyauta tunda shi bai kawoki ba kekuma bakizo ba." Hashim da Sally sukayi dariya. "Tuba nake, zaku ganni very soon in sha Allah." Ya jinjina kai yana shafa sumarsa fuskar dauke da murmushi. Bayan fitarta daga falon, Hashim ya dubeshi. "Kai zakayi wannan yak'in har ka siye zuciyarta." Ya yatsine fuska yana dubansa. "Ta yaya kenan? A tunaninka zan durkusa na rok'eta ta soni? Never! Furuci d'aya nayi mata wanda a yanzu nake (regretting, I'm in need of her)." Hashim ya ja tsaki. "Kana da matsala, dole kuma ka sauke wannan ji da kai ko ince girman kan da kake nunamata wallahi." . Hashim ya dubi abokin nasa da tausayi yace ma'aruff dole ka daure anjuma kaje kayi raping din bintu ko tana so ko bata so ....hehehe lol zuciyarta? Ta ji haushin kanta, Allah Yasa dai bai gano lagonta ba. Bata kammala tunane-tunanenra ba ya shigo da sallamarsa. Ta daure ta amsa a nutse batare da ta dubeshi ba. Shi d'inma bai damu ba ya mik'amata Hanif. "Rik'eshi." Ta kar6eshi baki bar dubanta ba ya yamutse fuska kad'an. Kamar yace wani abu sai kuma ya fasa ya fice. . Ta bishi da kallo tana murmushin takaici, wasu siraran hawaye suka sirnano daga idanunta. Iyakar saninta, tana da rik'o wani lokacin, amma ta rasa dalilin da yasa zuciyarta ke neman gazawa wajen rik'on abinda Yaya Ma'aruf yayi mata. Magana kam, ya gaggasa mata, saidai ta tsorata da abinda Aisha tace akan matan dake kawomasa hari zasu iya zamowa barazana a rayuwarsu. "Amma bai furta yana sonki ba. Kodai bukatar ce kawai yake nufi?" Ta ji zuciyarta babi dadi da wannan tunanin da tayi. Ta yi ringingine saman gado tana duban Hanif dake wasa da zobenta. Tunaninta bai wuce anya dagaske Ma'aruf yana sonta ba? Tafi bawa zuciyarta kawai bukatarta yakeyi. Ba don hakan ba ma bazai nemeta ba. Da bakinsa ya kushe halittarta, ya nuna mata nan duniya ya k'arfin kasancewa da ita. Ita kuwa ta yaya ma Aisha zatace kada ta k'i bada kai? Ta numfasa ta rik'o hannun d'an kamar shine uban take maganarta a fili. "Kai, bazan yi yanda yakeso da wuri ba, sai naji gaskiyar abinda ke zuciyar babanka." Hanif dai banda ihu-ihunsa da 6angale dariya babu wani abu da yakeyi. Ta d'an kama kumatunsa. "Ni ce fa Bintun Mami! Zamiyi maganinsa ko?" Ta k'arashe da 'yar dariya. Ba ita ta fito daga dakin ba saida ya kwalamata kira. Ta janyo (After Dress) ta zura tana murmushi ta fita. Yana zaune saman kafet yana amsa wayar Abbansa, saidai hakan bai hanashi binsu da kallo ba har suka zauna. Hanif ta ajiye gefe sannan ta mik'e ta dauko komai na bukata wajen cin abinci. Ta soma zubawa ta ji muryarsa. "Fati." Bata amsa ba, ba kuma ta fasa abinda takeyi ba, saidai kiranta da yakeyi da Fati, yana sanyamata jin wani abu. Ya k'ara kiranta da murya da sigar da bazata iya ji ta kyale ba. Dole saida ta yi dagaske wajen saita tunani da nutsuwarta, ta d'ago fuskarta a daure, ba k'aramin namijin k'ok'ari tayi ba wajen dubansa. "Na'am." Ganin yanda ta tur6une fuska sai ya ji haushin kansa. Ya manta da cewar Bintu ce fa, yanzun d'an abubuwan da ya aikata zasu sanya ya janyowa kansa sabon raini. Ya sosa hanci. "Kada dai ki dauki abin d'azu a matsayin wani abu, haka aure ya gada. Eh, kuma ba zai yiwu gida bai k'oshi ba a bawa na waje. Abar batun nan, ya wajaba lallai a gareni ni da ke mu zamto masu tsoron Allah mu dunga sauke hakkokin juna. Hakan zai fi mana kyau." Shi kam, bak'a sosai yaso yarfamata. Baisan ya akayi ya kasa ba. Anzo ga6ar da zata maida martani, don haka ta tura mishi farantin abincin gabansa, ta dubeshi ta kauda kai tana murmushin mugunta. "Na farko dai ni bani da bukata, hakki kuma na yafe nawa, kuma Yaya ka manta kace babu abinda zakayi da jikina. Ka kuma ce kallona kan tashi zuciyarka. Ni ce fa wannan yarinyar da kake fad'a. To nidai bani buk'atar komai nagode da niyya." Ya rasa me zaice? Saidai ya maze ya sha mur. Kamar yayi magana sai ya fasa ya hau cin abinci yana ta nanata maganganunta a ransa. Lallai ma yarinyar nan, wato haka take da riko? Ya ji ta ba shi haushi, ya d'an dubeta da niyyar fad'a, saidai bazai iya ba, wai wane irin muguwarl soyayyarta ce tayi mishi kamu har haka? Kallonta ma wani nishad'antar da zuciyarsa yakeyi. Ya daure batare da ya kalleta ba cikon sanyin murya yace. "Please leave me alone." Yanda yayi maganar baisa ta nuna tausayinsa a fuska ba, iyakar magana ai ya gasa mata. Ta dauki Hanif har da wani cillashi sama tana dariya. Daga haka ta shige dakin Hanif. Ji yayi ransa na k'una, wato ko a jikinta? Shi kuwa yaya zaiyi ne ta gane zuwa yanzu yayi nadama? Lallai so na sanya ladabin dole. Yau shi ke bin Bintu! Ya runtse ido. * * * Tun daga ranar ya fita hanyarta, duk da cewar ta damu a 6oye, hakan baisa a fili nuna kamar batasan me yake yiwa fushin ba. Ta daure ta cigaba da walwalarta yanda ta saba babu ko nuna wata alama ta damuwa. Ranar da ta je gida wuni, shima ranar yana ajiyeta ya nufi gidan abokinsa Hashim. "Ya akayi ne wai? Please mafita zakaban banason dariyar banza." Hashim ya tsagaita dariyarsa. "Sorry, mamaki dai nayi ne. Kamar ka ace ka auri wannan ficikar yarinyar har ma ka soma sonta? Abinda ko a mafarki bazakayi kuskuren gani ba kenan." Ya fahimci Hashim na tunano mishi furucinsa ne. Ya lumshe ido kafin ya bud'esu ya dubeshi ransa a 6ace, ya ja guntun tsaki. "Bazaka gane ba, banason tuna baya." Hashim ya numfasa ya gimtse dariyarsa. Daidai sadda Salimarsa ta shigo ta ajiye musu kayan motsa baki. Ta tambayi lafiyar Amarya. Ya amsa da murmushi. "Lafiya, ai kun kyauta tunda shi bai kawoki ba kekuma bakizo ba." Hashim da Sally sukayi dariya. "Tuba nake, zaku ganni very soon in sha Allah." Ya jinjina kai yana shafa sumarsa fuskar dauke da murmushi. Bayan fitarta daga falon, Hashim ya dubeshi. "Kai zakayi wannan yak'in har ka siye zuciyarta." Ya yatsine fuska yana dubansa. "Ta yaya kenan? A tunaninka zan durkusa na rok'eta ta soni? Never! Furuci d'aya nayi mata wanda a yanzu nake (regretting, I'm in need of her)." Hashim ya ja tsaki. "Kana da matsala, dole kuma ka sauke wannan ji da kai ko ince girman kan da kake nunamata wallahi." [7/26, 12:44 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶ ©Rufaida Omar (July...2016) <<44>> Shi kuwa iyakar dauriyarsa kawai yayi, yana son kusantar tafi haka, saidai bayaso yayi gaggawar da zata fassarashi baibai. Watakil ba zata fahimci yanda yake so da kaunarta ba. Ya ji sadda tayi bacci, shi d'in kuwa ya jima kafin baccin yayi awon gaba da shi hakance ta sanya baiji kiran sallar asuba ba. Ta k'ura mishi ido tana kallon irin baiwar da Allah Ya bata na samun mutum mai kyau da kwarjini irin Ma'aruf, ba wayonta ba ba komai ba. Bacci yakeyi hankalinsa kwance, dakyar ta iya mik'ewa ta fad'a toilet. Saida ta kammala tsarki da alwala ta fito. Har lokacin bai tashi ba. . Ta d'ora zani saman rigar baccinta tayi shirin tayar da sallah tsaf sannan ta tashe shi a hankali ta hanyar bubbuga k'afarsa. Ya waro ido yana 'yar mik'a. Ganinta da hijab, ya sanyashi azamar mik'ewa. Saida ya kammala sannan ya fice zuwa masallacin gidan dake kallonsu. Ita d'inma Sarah ta tayar, ta koma tayi nata. Ta jima da gama addu'o'inta da komai, har rana ta d'an fito, tana son ta d'an runtsa saidai tana tunanin Hanif. Zata fita sukaci karo zai shigo, ta tsorata, ai ta dauka babu abinda zai maidoshi. Ta gaisheshi ya amsa kafin ta ba shi hanya. "Ina zaki?" Ta dubeshi. "Aiki zanyi." Ya ja hannunta ya rufe k'ofar. "Aiki da asubar nan Fati? Bari zuwa anjima naga yau dai ba makaranta zaki ba. Bai bari tayi magana ba ya nufi ciki da ita. Har gado ya ajiyeta ya kashe fitilun ya zagayo ya kwanta gefenta. Ta runtse ido jin abinda yakeyi. Ya kuramata idanu yana murmushi. "Fati." Ya kira sunanta cikin sigar da ba zata jura ba. Bata iya amsawa ba. "Look into my eyes, please." Ta bud'e idanunta a hankali ta sauke cikin nashi, da sauri kuma ta maida ta rufe. Yayi murmushi ya soma magana ba tare da ya bar abinda yakeyi mata ba wanda ke kunce notinan kanta. "Zaman da mukayi dake tare yasa na damu dake yanzun, kin samu wani babban gurbi a zuciyata Fati..." Sai kuma yayi shiru. Ba wannan takeson ta ji bani ta so ba, yanda ya soma bi da ita yasa ta soma fita hayyacinta, saidai da sauri ta mik'e zaune ya dubeta da soyayyun idanunsa. Da saurinta ta mik'e kafin ya ankara ta nufi k'ofa. "Tsaya!" Ya fad'a da 'yar muryarsa. Ta tsaya cak, ta sa hannu tana m'ara suturce jikinta, a yanzun shi kuma ya shiga matsanancin damuwa, Bintu bata son shi, shine kawai abinda yasa wa ransa. Hakan yasa shi mik'ewa gami da gyara rigarsa ya nufi inda take. , "D'akinki ne. Baki kamata na takuraki ba." Daga haka ya fice. Ta bishi da kallo kafin ta lumshe ido tana murmushi. Ta yarda ta kuma gaskata cewar Ma'aruf fa yana sonta yanzun, saidai ta so yayi furucin da bakinsa ba wai yayita kwana-kwana ba. Ta koma ta kwanta gami da tattaro zanin gadon da filon da yayi matashi tana shinshina cike da jin sanyi a ranta. K'amshin turare Yaya Ma'aruf kawai ke tashi. Wasu ruwan hawaye suka kwaranyo mata. Ko a mafarki idan ance mata zata fad'a wannan hali na soyayya ba lallai ta gaskata ba, sai gashinan daga ita har Yayannata Allah Ya jarabcesu da fad'awa kogi na soyayyar juna, so mai wahalar da zuciya da gangar jiki kuwa. Shima a can, kasa bacci yayi, idan har bazai samu kan Bintu ba, to zai iya kamuwa da mugun ciwo kuwa don shi kad'ai yasan yanda yakeji a ransa. Yayi amanna cewar bazai iya son wsta ko kusantarta wata d'iya mace ba sai ita. Ita kad'ai yake so yake kuma buk'ata. Ya lumshe ido yana sakin ajiyar zuciya. Bintu kuwa har ta kammala komai ta bawa Hanif abincinsa tayi mishi wanka Ma'aruf bai fito ba. Ta gaji da zaman jira ta bar Hanif a hannun Sarah itama ta fad'a wankan. Har ta kammala ta shirya cikin doguwar riga d'inkin buba ta fito falon, shiru babu labarinsa. Hankalinta ya tashi, ta kasa daurewa kawai ta nufi d'akinnasa. Da sallamarta ta shiga, abin mamaki baya dakin, jin motsin ruwa ya bata tabbacin yana wanka ne. Hakan yasa ta fita. Saida ta kammala karyawa ta fiddowa Sarah keken Hanif baranda ta shiga turashi, ita kuwa zama tayi jugum har zuwa sadda ya turo k'ofar ya fito. Tasan yau babu aiki, to meyasa ya shirya cikin manyan kaya. Zama yayi a gefenta, duk yanda yaso ya nunamata yayi fushi, bai iya hakan ba, musamman ma ganin yanda ta ci ado, duk sai ya raina ajinsa, to ita d'inma hakanne a wajenta. "Fati." Ta narke fuska. "Nidai gaskiya ka daina kirani Fati." Yana murmushi ya jefamata tambaya. "Why?" Ta turo baki "Sunan fa Mami ne, kacemin Bintu na yanda kwa ya sanni da shi." "Ok, Bintuna, had'amin tea." Ta dubeshi ido waje sai kuma tayi k'as da kanta don batason kallon da yakeyi mata, irin kallon da Aisha ke gayamata a baya ta k'aryatashi, a yanzun kuwa ta gask'ata lallai akwai shi. Batayi aune ba ta ji ya tallafo ha6anta da hannunsa na dama kafin kuma ta ankara tuni ya soma mata sak'o. Abinda ya keyi zai tabbatar ya mance a inda suke, wannan karon ba k'arfinta ne ya kwaceta ba sai wayarsa da ta dauki ruri. Alokacin ta ja gefe. Ya duba Abbansa ne, cike da girmamawa ya dauka. Abba ya hau fadan dadewar da yayi bai zo sun wuce ba. Ya bashi hakuri gami da mikewa, a tsaye ya kora tea din kadan sannan ya koma daki, jimawa kadan ya fito cikin yadi maimakon shaddar da yasa a farko. Ta kauda kanta, yana murmushi yace"Saina dawo, zan fita da Abba. Ki shirya tarbata mai karfin mata goma." Ai a guje ta fad'a dakinta, ya fice yana dariya. , (Nagode wadanda sukamin ya jiki, da ma wadanda basuyiba a rubuce amma sun kirani, da ma wadanda basuyi duka ba amma sun damu da hakan. Allah Yabar zumuncinmu..love oll)
Share this
BINTU Part 006
BINTU Part 006 . Zuwan Aisha gidan ya yi musu dadi. Haka zasu zauna suyita hirar duniya idan ba makaranta. A kokarin Bintu bai wuce koyaushe ta nunawa Aisha lafiya lau suke da mijinta ba. Har takan dauki waya tayi kiransa saidai har wayar ta gama rurinta baya ko kallonta. Saidai a wayance tayita zuba zance don burge Aisha. Satinsa d'aya da tafiya, amma ko text bai ta6a yi mata ba, da zummar gaisuwa. A yanzu kuwa ta daina samun layinsa, saidai ta ji Aisha tace yayi kiranta ko kuma Mami. Jikinta yayi sanyi, haka kawai ta tsinci kanta da shiga damuwa. Kodai furucinta ya bawa Yaya Ma'aruf haushi? Ashe zai damu da ta nuna damuwa akanshi? Ta kai dubanta ga Aisha wacce ke kwance rigingine a saman gado tana amsa wayar masoyinta Ashir, sai wani narke murya takeyi da murmushi. Daga inda take ta zubawa wayarta ido kawai amma kunnuwanta suna ga Aisha tana sauraronta. Kawai sai ta ji abin ya burgeta, inama ita da Yaya Ma'aruf su dawo haka? Sai ta ji nauyi, kada dai ta kamu da son Ma'aruf ne? Ta girgiza kai, kokusa bata fahimtar abinda akeyi a group din nasu ta whatsapp ta tsinci kanta da komawa contact ta lalubo lambar Ma'aruf, har lokacin hotonnan ne akai bai chanja ba. Ta bud'o tana duba, a hankali takejin wani abu na yawo a zuciya da gangar jikinta. Tayi nisa a kallonsa ta ji Aisha ta makomata filo. "To 'yar is me kikeyi kika wani nutsu?" Bintu batajin wasa a yau, ta ajiye wayar ta dawo kusa da Aisha ta zauna. "Tashi ki bani wasu amsoshi don Allah." Aisha ta mik'e zaune ganin Bintu dagaske take ba wasa. "Ina sauraronki." Bintu ta muskuta tana fuskantarta. "Ya mutum zai gane ya fad'a tarkon so?" Me Aisha zatayi banda dariya. Ta d'aga hannu sama. "Allah na godemaka da Ka bani tsawon ran ganin wannan rana. Cabd'i!" Ta girgiza kai kad'an tana had'e rai cikin son kauda 'yar kunyar da ta ji. "Malama banason haka, idan bazaki bani amsa ba ki bar yimin dariya." Ganin Aisha bata da niyyar dainawa ya sanyata daukar wayarta a fusace ta shige d'aki. Kan gado ta fad'a tana murmushi, daman tasan hakan zata faru tunda ta riga ta gama cika baki a baya. Tana jin sadda Aisha ta shigo gami da zama gefenta, ta had'e rai. Aisha ta gimtse dariyarta ta soma magana duk kuwa da cewa Bintun ta juyamata baya. "Idan ka soma son mutum, zaka tsinci kanka cikin yawan tunaninsa, haka kuma da zarar ka ganshi kun had'a ido zaka ji kamar wasu kibiyoyi ke fitowa daga idanunsa suna shiga naka har suna haddasa maka wani kasala, har ka kasa jure kallon ka sauke idanunka. Komai na mutum zai dawo yana burgeka, ko muryar mutum ka ji sai ka ji wani sanyi na dadi. Babban abinda ke tabbatarwa ka kamu da soyayyar mutum shine KISHI. Nan duniya zakaji baka kaunar abokin takara a zuciyarsa. Ba kuma ka kaunar wani ya ra6eshi da sunan so. Ko yaya kaga ya sakarwa wani fuska ya kula da shi fiye da yanda yake kula da kai sai ka ji tashin hankali sosai, da damuwa da bakin ciki a zuciya. Matukar kina jin wadannan abubuwan da na lissafa, shakka babu (You Are In Love)." Bintu ta bud'e lumsassun idanunta tana duban fuskar gadonta, ta ji gabanta yana bugu da sauri-sauri. Ta kamu da son Ma'aruf yanzu? Kenan dukkan abinda takeji a ranta akansa soyayya ce? "Kenan alamomin da nakeji akan Yaya Ma'aruf suna nuni da cewar inasonsa?" Batasan sadda ta watsowa Aisha tambayar ba. Aisha ta rasa inda zata tsoma ranta don dad'i, don ta jima da gane cewar babu abinda ya ta6a shiga tsakaninsu kawai dai ta barta a yanda ta so ne. "Idan har kina jin abubuwan da na lissafa akansa, to lallai kin fad'a cikin matsanancin soyayyarsa." Sai kuma ta ji wata iriyar kunyar Aisha, lura da hakan ne yasa Aisha mik'ewa ta fita da zummar d'ora musu girki. Ta sauke ajiyar zuciya ta mik'e zaune. "Inason Yaya Ma'aruf." Shine abinda ta furta cikin siririyar murya. * * * "Ina sonki Fatima Bintu." Cewar Ma'aruf kenan a yayinda yake kwance cikin kujera idanuwa a lumshe yana tunanin Bintu wanda ya zame mishi jiki tun zuwansa Lagos. Gaba d'aya kewarta ta dameshi, baisan ya damu da yarinyar ba sai bayan da ya nisanta da ita. Yana fushi da ita akan ta nuna halin ko'in kula da tafiyar da zaiyi, wato dai bata damu da shi ba. A rayuwarsa yana so yaga an damu da shi. Sai ya kai zuciyarsa nesa yake k'in daukar kiranta, lallai shi yana son tilasatawa ransa ya fiddata. Yanaso yabar tunanin wani abu nata da ita kanta. Yana so ya yakiceta a ransa. Wannan yasa ya yanke shawarar yin wata d'ayan da ogansu yace yayi acan batare da ko sau d'aya ya dawo hutun karshen sati Kano ba. Sanin da yayi ma idan yazo ba wani abun zai samu awajenta ba. Ya numfasa ya mik'e zaune. Kalmar nan ta "So" baiyi zaton zai k'ara furtata ba ballantana ya ji ta a ransa. Sai ga shi zuwa yanzu ya gama tabbatarwa ransa ya fad'a dumu-dumu cikin kogin son matarsa kuma 'yar uwarsa abokiyar fad'ansa Bintu. Sai kuma yayi murmushi sadda ya tunano rashin jituwarsu tun afarkon zuwanta gidansu har zuwa girmanta. Rufa'i ya dannawa kira, ya sanar dashi cewar wata d'aya zaiyi don haka ya dauki su Aisha ya maidasu gaban Mami. Daman ya kammala waya da Abba ya shaida mishi. Ya yiwa Bintu gajeran sak'o babu wani abin jan hankali ciki ya shaidamata su had'a kayansu Rufa'i zaizo ya tafi da su gidan Mami. Ta yi kasak'e tana duban sak'on alokacin suna tare da Aisha tana k'ara koyar da ita yanda zata shawo kansa. Ta sanarwa Aisha kafin su soma shiri. Ranta duk babu dad'i jin zai cinye wata d'aya a garin da basu da wani addini sosai. Haka suka kammala shiri suka nufi gidan Mami. Saidai tana ganin Mami ta mance da batunsa ta hau murna. Ganin yanda ta d'an rame sai Mami tayi zaton ko ciki ne. Ta shiga nan nan da ita. Murmushi kawai sukayi ita da Aisha. . A wannan wata d'ayan, wanda aka ci sati uku kenan da Bintu tayi a gidan Mami, ta yishi cikin kwanciyar hankali, duk kuwa da cewar babu wata mu'amalar arziki dake shiga tsakaninta da Yaya Ma'aruf face gaisuwa da take mik'a mishi ta whatsapp, shima wani sa'in za'a nunamata ya je kuma ya gani amma babu amsa. Sai sadda ta ci sa'a ne yake amsa mata, daga amsa gaisuwar kuma bai k'ara cewa uffan. . Tun tana yi har ta soma gajiya, wani sa'in ta watsar. Shi kuwa ya d'auki hakan kawai a matsayin rainin hankali, tunda gwana ce wajen hakan. Ganin yana neman cutuwa sosai da bukatunsa, ya sanyashi farlantawa kansa azumin litinin da alhamis. Haka kuma da yawaita dauke hankalinsa da wani abu da ba zai jawo mishi motsuwarsa ba. Saidai iyakar dauriya yinsa kawai yake, akwai sadda Lawisa ta kusa cin galaba akanshi. Sukayi doguwar hira a waya mai ta6a sosai, a k'arshe suka yanke zata kawomishi ziyara har Lagos. Koda zuwanta da soma gudanar da abubuwa, tun kafin lamura su 6aci, ya dawo nutsuwarsa inda wata kyakkyawar zuciyarsa tayi mishi tuni da "Bafa matarka bace." Da sauri ya fisgeta daga jikinta ya mik'e yana kiran innalillahi a fili kafin ya fad'a ya wanke jikinsa. Nan ya taddata tana hawaye, bai bi ta kanta ba ya kama hanyar fita sai kuma ya tsaya batare da ya juyo ba, cikin kakkausar murya yace. "Kiyi hanzarin barin gidannan tun kafin na dawo." Yana shirin ficewa yaji ta rungumoshi ta baya, ya runtse ido, kafin ya juyo ya tureta. "Karki k'ara kusantoni! Ki rabu da ni Lawisa, please daga yau ki fita hanyata." Hannunsa ta rik'e a gigice. "Bazan fita ba, ka taimaki rayuwata Ma'aruf kada ka barni ha.." . "Ki kyaleni! Ki kyaleni nace!! Kafin na dawo ki tattara abinda kikasan mallakinki ne ki bar gidannan!!" Ya fad'a a tsawance kafin ya sa kai ya fice. Ranta ya 6aci sosai da wannan wulakancin da yayi mata, ita kuwa ko shine autan maza ba zata k'ara kallonsa ba. Ta dauki wayarta ta kira d'aya cikin mutanenta na Lagos. Nan tayi kwatancen inda take, a take kuwa Alhajin yasa direbansa zuwa d'aukarta. Ko wanka bata tsaya yi ba ta shirya tsaf ta bar gidan. Ma'aruf bai jima sosai ba ya dawo, ya ji dad'in rashin ganinta a gidan, ya zauna ya rik'e kai. Idanunsa sunyi ja sun kumbura adalilin kukan da ya ci, yau ga shi ya kusa tafka kuskuren da da ace ya faru ba zai iya yafewa kansa ba. A gefe kuma ga soyayyar dake azabtar da shi, ya ji haushin yanda ta bar turomishi sak'on gaisuwa ko don baya kulata sosai ne? Batasan cewa yana jin dadin hakan ba? Ajiyar zuciya ya saki, fatansa ya kammala aikinsa yaje ayi wacce za'ayi don ba zai zauna da cuta ba. Acan kuwa, Bintu bata k'ara bi ta kansa ba, ta danne abinda takeji a ranta dangane da shi. Ta nemi zuwa Rano ganin iyayenta tunda sun samu hutu. Kasancewar shima Rufa'i zai kai Hajara ganin gida, yasa Abba bai hanata ba ya kira ya sanarwa Ma'aruf. Allah Ya tsare hanya, shine kawai abinda yace. Farinciki ya rufe Bintu yau zata ga 'yan uwanta. Suma can sun shirya tarbarta sosai. Tare suka je har Aisha. Yan uwa sunyi murnar ganinsu. Inna ta shiga nan nan da su. Kwanansu uku suka soma shirin tahowa don Rufa'i zaizo daukarsu. Inna ta k'ara yiwa Bintu nasiha sosai akan rik'e hakkokin mijinta da sauransu. Ta yaba kwarai ganin Bintun ta yi hankali, ta zama wata mai sanyi da nutsuwa, batasan cewa soyayya ke nukurkusarta ba har ta ladabtar da ita ladabin dole. Aisha ta samu abubuwa sosai a wajen 'yar Rano kasancewar bikinta baifi sati hud'u da kwanaki ba. Haka suka baro Rano cike da kewa. A safiyar asabar ne ta koma gidanta kamar yanda Mami ta umarceta. Tare suka je da Aisha sai 'yar yarinyar da aka samo mata da bata wuce sha uku ba da zata tayata rainon Hanif, har da Hanif din wanda suna isa Bintu ta goyeshi a bayanta. Suka gyara komai don a ranar akesa ran dawowar Ma'aruf kamar yanda ya shaidawa Mamin. Kicin suka fad'a suka hau girke-girke. Suna yi Aisha na k'ara bata shawara. "Kwalliya fa zaki ci malama, irin wanda na gayamiki. Kada ki nunamishi fushinki Bintu. Kiyi hakuri, kece dole wajen yi mishi biyayya, amma fa ban hanaki jan aji kad'an ba, karkiyi yanda zai tsinke." Sukayi dariya, Bintu ta dafa kirjinta. "Bakiji yanda gabana ke bugu ba, a tsorace nake fa. Kinsan Yayanki akwai disgawa." Aisha ta girgiza kai. "Akanki ba, kuma kema kinsan abinda yasa yake miki hakan, kin nuna mishi baki da kunya." Bintu ta harareta. Aisha ta dara kad'an. "Allah kuwa rashin girmamashi sosai ne yasa yakemiki wasu abubuwan. Ki tuna keda kanki kin sha yabon yanda sukeyi da Anti Asma'u, yana sakarmata fuska, wasa da dariya duka, koda kuwa a gabanmu ne. Yana da mutunci wallahi ba wai kuma don Yayana bane. Ita gaskiya fa a fad'eta." "Ya gasamin maganganu fa." "Wannan kuma kinfini sanin ta sigar da zaki rama, saidai ina k'ara baki shawara, kada ki ja aji ta yanda zai tsinke wallahi." Murmushi kawai tayi, suka cigaba da aiki suna hira, anan ne Bintu ke labarta mata yanda sukayi da Lawisa. Me Aisha zatayi banda dariya, har da rik'e ciki. Ta jima tana dariya da k'arawa. "Kai wallahi kinyi daidai. Toh wallahi ko don saboda su ya dace ki bada kai bori ya hau kada kiyi sakiyar da ba ruwa." Aisha ta k'arashe tana mai kwafa. "Bakisan wacece Lawisa ba. Yar iska ce, idan ma nayi kiranta karuwa banyi k'arya ba wallahi. Ki tashi tsaye karki bari su samu k'ofa." Bintu ta girgiza kai da gamsuwa da wani irin tsoro. Bayan sun kammala, Aisha ta yiwa Hanif wanka, itama Bintun ta fad'a band'aki. . Mintuna ashirin da kammala shirinta da komai, ta fito falon inda Aisha da Sarah mai rainon Hanif suke zaune suna kallo. Ba Aisha ba, daidai da Sarah saida ta saki baki wajen kallonta. Wani shegen siket ne bak'i mai shek'i amma ba shi da kyalkyali, tsaga gareshi tun daga gwuiwa har k'asa, sai wata riga ja mai igiyoyi wanda ya tafi X ko kirjinta bai rufu yanda akaso ba, bata da hannuwa sai na vest. Ta rufe kanta da jar hula mai wani laushi duk da hakan, tufkakkan gashinta bai kammala rufuwa ba. Ta rik'e k'ugu ta karkace kai kad'an yayinda ta d'an tsuke baki. "Ya?" Aisha ta had'e yatsunta biyu. "Wow! Kinyi kyau wallahi." Ta k'araso tana mai yin farr da ido. "Nasani." Aisha ta d'aka mata duka a cinya sukayi dariya. "Yau dai da wuya Yayanmu ya d'auke idanunsa akanki." Sai kuma jikinta yayi sanyi. Fatanta kada ya gwatsaleta. "I hope so." "In sha Allah, kedai kada ki damu." Cewar Aisha. . Angonnata basu shigo Kano ba sai bayan Magrib. Tuni Aisha ta tattara ta wuce. Duk yanda Bintu ta so zamanta har zuwa sadda zai shigo amma fir ta k'i. Tana zaune ta rik'e Hanif tana mishi wasa ta jiyo tsayuwar mota. Ji tayi gabanta ya fad'i, ashe daman don batason Ma'aruf ne yasa batajin nauyin yin komai a gabansa? Tayi saurin duban Sarah. "Shiga d'aki." Sarah ta mik'e da sauri ta fad'a d'akin Hanif. Kwankwasa k'ofar da akayi yasa ta nufar k'ofar, Hanif yana rungume a jikinta bata ajiyeshi ba. A hankali take tafiya har ta isa k'ofar ta bud'e. Ido cikin ido suka dubi juna. Kowannensu yana kokarin isarwa d'an uwansa sak'o. Sai kuma ya juya da sauri, Isa direban Mami ya tara gami da kar6ar akwatinsa. "Nagode Malam Isa." Ganin haka, yana shigowa ta sa hannu ta rik'o trolley din, shi kuma yayi amfani da hagunsa wajen amsar Hanif dake mak'ale a hannunta na dama. Wani shock sukaji gaba d'ayansu, ya narkar da idanunsa wajen kallon abinda ya fi tafiya da imaninsa a wajenta. Ita kuwa ta dauke idanunta. Murya na rawa ta furta. "Yaya sannu da zuwa." Baki amsa ba har ta juya ta nufi d'akinsa tana rausayar da batasan yanda akayi ta soma ba, wannan kam yafi (natural) tafiyarta had'uwa da tada hankali. Baiyi k'asa a gwuiwa ba ya tura k'ofar da k'afarsa ya mara mata baya. A daidai k'ofa suka had'u, caraf ya rik'o hannunta ya ja zuwa ciki. Ta dubi yanda ya rik'e hannunnata gam kamar mai tsoron a rabasu, sannan ta dubeshi a tsorace, gabanta na bugu da k'arfi da kuma sauri-sauri. Ya ajiye Hanif a saman gado ya jawota gaba d'aya zuwa jikinsa gami da yi mata kyakkyawan rumfa ruf. Gaba d'ayansu sun ji a jikinsu kuwa. Daidai kunnenta ya yi magana. "I'm in need of you Fati." Yanda yayi maganar da irin muryar da yayi amfani da ita wajen yin ce ta sanya tsintar kanta cikin rawar jiki. Bata ankara ba ta jishi yana cigaba da abinda bazata iya jura ba. "A'a! Bintu, not so fast!" Da sauri ta daddage ta tureshi, bata bi takan Hanif ba ta fice a guje. Sai ma ta ba shi dariya, hakan ya sanyashi murmusawa. . Hankalinta ya tashi, ta fad'a kan gado tayi shiru. Ya akayi ta kasa danne zuciyarta? Ta ji haushin kanta, Allah Yasa dai bai gano lagonta ba. Bata kammala tunane-tunanenra ba ya shigo da sallamarsa. Ta daure ta amsa a nutse batare da ta dubeshi ba. Shi d'inma bai damu ba ya mik'amata Hanif. "Rik'eshi." Ta kar6eshi baki bar dubanta ba ya yamutse fuska kad'an. Kamar yace wani abu sai kuma ya fasa ya fice. Ta bishi da kallo tana murmushin takaici, wasu siraran hawaye suka sirnano daga idanunta. Iyakar saninta, tana da rik'o wani lokacin, amma ta rasa dalilin da yasa zuciyarta ke neman gazawa wajen rik'on abinda Yaya Ma'aruf yayi mata. Magana kam, ya gaggasa mata, saidai ta tsorata da abinda Aisha tace akan matan dake kawomasa hari zasu iya zamowa barazana a rayuwarsu. "Amma bai furta yana sonki ba. Kodai bukatar ce kawai yake nufi?" Ta ji zuciyarta babi dadi da wannan tunanin da tayi. Ta yi ringingine saman gado tana duban Hanif dake wasa da zobenta. Tunaninta bai wuce anya dagaske Ma'aruf yana sonta ba? Tafi bawa zuciyarta kawai bukatarta yakeyi. Ba don hakan ba ma bazai nemeta ba. Da bakinsa ya kushe halittarta, ya nuna mata nan duniya ya k'arfin kasancewa da ita. Ita kuwa ta yaya ma Aisha zatace kada ta k'i bada kai? Ta numfasa ta rik'o hannun d'an kamar shine uban take maganarta a fili. "Kai, bazan yi yanda yakeso da wuri ba, sai naji gaskiyar abinda ke zuciyar babanka." Hanif dai banda ihu-ihunsa da 6angale dariya babu wani abu da yakeyi. Ta d'an kama kumatunsa. "Ni ce fa Bintun Mami! Zamiyi maganinsa ko?" Ta k'arashe da 'yar dariya. Ba ita ta fito daga dakin ba saida ya kwalamata kira. Ta janyo (After Dress) ta zura tana murmushi ta fita. Yana zaune saman kafet yana amsa wayar Abbansa, saidai hakan bai hanashi binsu da kallo ba har suka zauna. Hanif ta ajiye gefe sannan ta mik'e ta dauko komai na bukata wajen cin abinci. Ta soma zubawa ta ji muryarsa. "Fati." Bata amsa ba, ba kuma ta fasa abinda takeyi ba, saidai kiranta da yakeyi da Fati, yana sanyamata jin wani abu. Ya k'ara kiranta da murya da sigar da bazata iya ji ta kyale ba. Dole saida ta yi dagaske wajen saita tunani da nutsuwarta, ta d'ago fuskarta a daure, ba k'aramin namijin k'ok'ari tayi ba wajen dubansa. "Na'am." Ganin yanda ta tur6une fuska sai ya ji haushin kansa. Ya manta da cewar Bintu ce fa, yanzun d'an abubuwan da ya aikata zasu sanya ya janyowa kansa sabon raini. . Ya sosa hanci. "Kada dai ki dauki abin d'azu a matsayin wani abu, haka aure ya gada. Eh, kuma ba zai yiwu gida bai k'oshi ba a bawa na waje. Abar batun nan, ya wajaba lallai a gareni ni da ke mu zamto masu tsoron Allah mu dunga sauke hakkokin juna. Hakan zai fi mana kyau." Shi kam, bak'a sosai yaso yarfamata. Baisan ya akayi ya kasa ba. Anzo ga6ar da zata maida martani, don haka ta tura mishi farantin abincin gabansa, ta dubeshi ta kauda kai tana murmushin mugunta. "Na farko dai ni bani da bukata, hakki kuma na yafe nawa, kuma Yaya ka manta kace babu abinda zakayi da jikina. Ka kuma ce kallona kan tashi zuciyarka. Ni ce fa wannan yarinyar da kake fad'a. To nidai bani buk'atar komai nagode da niyya." Ya rasa me zaice? Saidai ya maze ya sha mur. Kamar yayi magana sai ya fasa ya hau cin abinci yana ta nanata maganganunta a ransa. Lallai ma yarinyar nan, wato haka take da riko? Ya ji ta ba shi haushi, ya d'an dubeta da niyyar fad'a, saidai bazai iya ba, wai wane irin muguwarl soyayyarta ce tayi mishi kamu har haka? Kallonta ma wani nishad'antar da zuciyarsa yakeyi. Ya daure batare da ya kalleta ba cikon sanyin murya yace. "Please leave me alone." Yanda yayi maganar baisa ta nuna tausayinsa a fuska ba, iyakar magana ai ya gasa mata. Ta dauki Hanif har da wani cillashi sama tana dariya. Daga haka ta shige dakin Hanif. Ji yayi ransa na k'una, wato ko a jikinta? Shi kuwa yaya zaiyi ne ta gane zuwa yanzu yayi nadama? Lallai so na sanya ladabin dole. Yau shi ke bin Bintu! Ya runtse ido. * * * Tun daga ranar ya fita hanyarta, duk da cewar ta damu a 6oye, hakan baisa a fili nuna kamar batasan me yake yiwa fushin ba. Ta daure ta cigaba da walwalarta yanda ta saba babu ko nuna wata alama ta damuwa. Ranar da ta je gida wuni, shima ranar yana ajiyeta ya nufi gidan abokinsa Hashim. "Ya akayi ne wai? Please mafita zakaban banason dariyar banza." . Hashim ya tsagaita dariyarsa. "Sorry, mamaki dai nayi ne. Kamar ka ace ka auri wannan ficikar yarinyar har ma ka soma sonta? Abinda ko a mafarki bazakayi kuskuren gani ba kenan." Ya fahimci Hashim na tunano mishi furucinsa ne. Ya lumshe ido kafin ya bud'esu ya dubeshi ransa a 6ace, ya ja guntun tsaki. "Bazaka gane ba, banason tuna baya." Hashim ya numfasa ya gimtse dariyarsa. Daidai sadda Salimarsa ta shigo ta ajiye musu kayan motsa baki. Ta tambayi lafiyar Amarya. Ya amsa da murmushi. "Lafiya, ai kun kyauta tunda shi bai kawoki ba kekuma bakizo ba." Hashim da Sally sukayi dariya. "Tuba nake, zaku ganni very soon in sha Allah." Ya jinjina kai yana shafa sumarsa fuskar dauke da murmushi. Bayan fitarta daga falon, Hashim ya dubeshi. "Kai zakayi wannan yak'in har ka siye zuciyarta." Ya yatsine fuska yana dubansa. "Ta yaya kenan? A tunaninka zan durkusa na rok'eta ta soni? Never! Furuci d'aya nayi mata wanda a yanzu nake (regretting, I'm in need of her)." Hashim ya ja tsaki. "Kana da matsala, dole kuma ka sauke wannan ji da kai ko ince girman kan da kake nunamata wallahi." . Hashim ya dubi abokin nasa da tausayi yace ma'aruff dole ka daure anjuma kaje kayi raping din bintu ko tana so ko bata so ....hehehe lol zuciyarta? Ta ji haushin kanta, Allah Yasa dai bai gano lagonta ba. Bata kammala tunane-tunanenra ba ya shigo da sallamarsa. Ta daure ta amsa a nutse batare da ta dubeshi ba. Shi d'inma bai damu ba ya mik'amata Hanif. "Rik'eshi." Ta kar6eshi baki bar dubanta ba ya yamutse fuska kad'an. Kamar yace wani abu sai kuma ya fasa ya fice. . Ta bishi da kallo tana murmushin takaici, wasu siraran hawaye suka sirnano daga idanunta. Iyakar saninta, tana da rik'o wani lokacin, amma ta rasa dalilin da yasa zuciyarta ke neman gazawa wajen rik'on abinda Yaya Ma'aruf yayi mata. Magana kam, ya gaggasa mata, saidai ta tsorata da abinda Aisha tace akan matan dake kawomasa hari zasu iya zamowa barazana a rayuwarsu. "Amma bai furta yana sonki ba. Kodai bukatar ce kawai yake nufi?" Ta ji zuciyarta babi dadi da wannan tunanin da tayi. Ta yi ringingine saman gado tana duban Hanif dake wasa da zobenta. Tunaninta bai wuce anya dagaske Ma'aruf yana sonta ba? Tafi bawa zuciyarta kawai bukatarta yakeyi. Ba don hakan ba ma bazai nemeta ba. Da bakinsa ya kushe halittarta, ya nuna mata nan duniya ya k'arfin kasancewa da ita. Ita kuwa ta yaya ma Aisha zatace kada ta k'i bada kai? Ta numfasa ta rik'o hannun d'an kamar shine uban take maganarta a fili. "Kai, bazan yi yanda yakeso da wuri ba, sai naji gaskiyar abinda ke zuciyar babanka." Hanif dai banda ihu-ihunsa da 6angale dariya babu wani abu da yakeyi. Ta d'an kama kumatunsa. "Ni ce fa Bintun Mami! Zamiyi maganinsa ko?" Ta k'arashe da 'yar dariya. Ba ita ta fito daga dakin ba saida ya kwalamata kira. Ta janyo (After Dress) ta zura tana murmushi ta fita. Yana zaune saman kafet yana amsa wayar Abbansa, saidai hakan bai hanashi binsu da kallo ba har suka zauna. Hanif ta ajiye gefe sannan ta mik'e ta dauko komai na bukata wajen cin abinci. Ta soma zubawa ta ji muryarsa. "Fati." Bata amsa ba, ba kuma ta fasa abinda takeyi ba, saidai kiranta da yakeyi da Fati, yana sanyamata jin wani abu. Ya k'ara kiranta da murya da sigar da bazata iya ji ta kyale ba. Dole saida ta yi dagaske wajen saita tunani da nutsuwarta, ta d'ago fuskarta a daure, ba k'aramin namijin k'ok'ari tayi ba wajen dubansa. "Na'am." Ganin yanda ta tur6une fuska sai ya ji haushin kansa. Ya manta da cewar Bintu ce fa, yanzun d'an abubuwan da ya aikata zasu sanya ya janyowa kansa sabon raini. Ya sosa hanci. "Kada dai ki dauki abin d'azu a matsayin wani abu, haka aure ya gada. Eh, kuma ba zai yiwu gida bai k'oshi ba a bawa na waje. Abar batun nan, ya wajaba lallai a gareni ni da ke mu zamto masu tsoron Allah mu dunga sauke hakkokin juna. Hakan zai fi mana kyau." Shi kam, bak'a sosai yaso yarfamata. Baisan ya akayi ya kasa ba. Anzo ga6ar da zata maida martani, don haka ta tura mishi farantin abincin gabansa, ta dubeshi ta kauda kai tana murmushin mugunta. "Na farko dai ni bani da bukata, hakki kuma na yafe nawa, kuma Yaya ka manta kace babu abinda zakayi da jikina. Ka kuma ce kallona kan tashi zuciyarka. Ni ce fa wannan yarinyar da kake fad'a. To nidai bani buk'atar komai nagode da niyya." Ya rasa me zaice? Saidai ya maze ya sha mur. Kamar yayi magana sai ya fasa ya hau cin abinci yana ta nanata maganganunta a ransa. Lallai ma yarinyar nan, wato haka take da riko? Ya ji ta ba shi haushi, ya d'an dubeta da niyyar fad'a, saidai bazai iya ba, wai wane irin muguwarl soyayyarta ce tayi mishi kamu har haka? Kallonta ma wani nishad'antar da zuciyarsa yakeyi. Ya daure batare da ya kalleta ba cikon sanyin murya yace. "Please leave me alone." Yanda yayi maganar baisa ta nuna tausayinsa a fuska ba, iyakar magana ai ya gasa mata. Ta dauki Hanif har da wani cillashi sama tana dariya. Daga haka ta shige dakin Hanif. Ji yayi ransa na k'una, wato ko a jikinta? Shi kuwa yaya zaiyi ne ta gane zuwa yanzu yayi nadama? Lallai so na sanya ladabin dole. Yau shi ke bin Bintu! Ya runtse ido. * * * Tun daga ranar ya fita hanyarta, duk da cewar ta damu a 6oye, hakan baisa a fili nuna kamar batasan me yake yiwa fushin ba. Ta daure ta cigaba da walwalarta yanda ta saba babu ko nuna wata alama ta damuwa. Ranar da ta je gida wuni, shima ranar yana ajiyeta ya nufi gidan abokinsa Hashim. "Ya akayi ne wai? Please mafita zakaban banason dariyar banza." Hashim ya tsagaita dariyarsa. "Sorry, mamaki dai nayi ne. Kamar ka ace ka auri wannan ficikar yarinyar har ma ka soma sonta? Abinda ko a mafarki bazakayi kuskuren gani ba kenan." Ya fahimci Hashim na tunano mishi furucinsa ne. Ya lumshe ido kafin ya bud'esu ya dubeshi ransa a 6ace, ya ja guntun tsaki. "Bazaka gane ba, banason tuna baya." Hashim ya numfasa ya gimtse dariyarsa. Daidai sadda Salimarsa ta shigo ta ajiye musu kayan motsa baki. Ta tambayi lafiyar Amarya. Ya amsa da murmushi. "Lafiya, ai kun kyauta tunda shi bai kawoki ba kekuma bakizo ba." Hashim da Sally sukayi dariya. "Tuba nake, zaku ganni very soon in sha Allah." Ya jinjina kai yana shafa sumarsa fuskar dauke da murmushi. Bayan fitarta daga falon, Hashim ya dubeshi. "Kai zakayi wannan yak'in har ka siye zuciyarta." Ya yatsine fuska yana dubansa. "Ta yaya kenan? A tunaninka zan durkusa na rok'eta ta soni? Never! Furuci d'aya nayi mata wanda a yanzu nake (regretting, I'm in need of her)." Hashim ya ja tsaki. "Kana da matsala, dole kuma ka sauke wannan ji da kai ko ince girman kan da kake nunamata wallahi." [7/26, 12:44 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶ ©Rufaida Omar (July...2016) <<44>> Shi kuwa iyakar dauriyarsa kawai yayi, yana son kusantar tafi haka, saidai bayaso yayi gaggawar da zata fassarashi baibai. Watakil ba zata fahimci yanda yake so da kaunarta ba. Ya ji sadda tayi bacci, shi d'in kuwa ya jima kafin baccin yayi awon gaba da shi hakance ta sanya baiji kiran sallar asuba ba. Ta k'ura mishi ido tana kallon irin baiwar da Allah Ya bata na samun mutum mai kyau da kwarjini irin Ma'aruf, ba wayonta ba ba komai ba. Bacci yakeyi hankalinsa kwance, dakyar ta iya mik'ewa ta fad'a toilet. Saida ta kammala tsarki da alwala ta fito. Har lokacin bai tashi ba. . Ta d'ora zani saman rigar baccinta tayi shirin tayar da sallah tsaf sannan ta tashe shi a hankali ta hanyar bubbuga k'afarsa. Ya waro ido yana 'yar mik'a. Ganinta da hijab, ya sanyashi azamar mik'ewa. Saida ya kammala sannan ya fice zuwa masallacin gidan dake kallonsu. Ita d'inma Sarah ta tayar, ta koma tayi nata. Ta jima da gama addu'o'inta da komai, har rana ta d'an fito, tana son ta d'an runtsa saidai tana tunanin Hanif. Zata fita sukaci karo zai shigo, ta tsorata, ai ta dauka babu abinda zai maidoshi. Ta gaisheshi ya amsa kafin ta ba shi hanya. "Ina zaki?" Ta dubeshi. "Aiki zanyi." Ya ja hannunta ya rufe k'ofar. "Aiki da asubar nan Fati? Bari zuwa anjima naga yau dai ba makaranta zaki ba. Bai bari tayi magana ba ya nufi ciki da ita. Har gado ya ajiyeta ya kashe fitilun ya zagayo ya kwanta gefenta. Ta runtse ido jin abinda yakeyi. Ya kuramata idanu yana murmushi. "Fati." Ya kira sunanta cikin sigar da ba zata jura ba. Bata iya amsawa ba. "Look into my eyes, please." Ta bud'e idanunta a hankali ta sauke cikin nashi, da sauri kuma ta maida ta rufe. Yayi murmushi ya soma magana ba tare da ya bar abinda yakeyi mata ba wanda ke kunce notinan kanta. "Zaman da mukayi dake tare yasa na damu dake yanzun, kin samu wani babban gurbi a zuciyata Fati..." Sai kuma yayi shiru. Ba wannan takeson ta ji bani ta so ba, yanda ya soma bi da ita yasa ta soma fita hayyacinta, saidai da sauri ta mik'e zaune ya dubeta da soyayyun idanunsa. Da saurinta ta mik'e kafin ya ankara ta nufi k'ofa. "Tsaya!" Ya fad'a da 'yar muryarsa. Ta tsaya cak, ta sa hannu tana m'ara suturce jikinta, a yanzun shi kuma ya shiga matsanancin damuwa, Bintu bata son shi, shine kawai abinda yasa wa ransa. Hakan yasa shi mik'ewa gami da gyara rigarsa ya nufi inda take. , "D'akinki ne. Baki kamata na takuraki ba." Daga haka ya fice. Ta bishi da kallo kafin ta lumshe ido tana murmushi. Ta yarda ta kuma gaskata cewar Ma'aruf fa yana sonta yanzun, saidai ta so yayi furucin da bakinsa ba wai yayita kwana-kwana ba. Ta koma ta kwanta gami da tattaro zanin gadon da filon da yayi matashi tana shinshina cike da jin sanyi a ranta. K'amshin turare Yaya Ma'aruf kawai ke tashi. Wasu ruwan hawaye suka kwaranyo mata. Ko a mafarki idan ance mata zata fad'a wannan hali na soyayya ba lallai ta gaskata ba, sai gashinan daga ita har Yayannata Allah Ya jarabcesu da fad'awa kogi na soyayyar juna, so mai wahalar da zuciya da gangar jiki kuwa. Shima a can, kasa bacci yayi, idan har bazai samu kan Bintu ba, to zai iya kamuwa da mugun ciwo kuwa don shi kad'ai yasan yanda yakeji a ransa. Yayi amanna cewar bazai iya son wsta ko kusantarta wata d'iya mace ba sai ita. Ita kad'ai yake so yake kuma buk'ata. Ya lumshe ido yana sakin ajiyar zuciya. Bintu kuwa har ta kammala komai ta bawa Hanif abincinsa tayi mishi wanka Ma'aruf bai fito ba. Ta gaji da zaman jira ta bar Hanif a hannun Sarah itama ta fad'a wankan. Har ta kammala ta shirya cikin doguwar riga d'inkin buba ta fito falon, shiru babu labarinsa. Hankalinta ya tashi, ta kasa daurewa kawai ta nufi d'akinnasa. Da sallamarta ta shiga, abin mamaki baya dakin, jin motsin ruwa ya bata tabbacin yana wanka ne. Hakan yasa ta fita. Saida ta kammala karyawa ta fiddowa Sarah keken Hanif baranda ta shiga turashi, ita kuwa zama tayi jugum har zuwa sadda ya turo k'ofar ya fito. Tasan yau babu aiki, to meyasa ya shirya cikin manyan kaya. Zama yayi a gefenta, duk yanda yaso ya nunamata yayi fushi, bai iya hakan ba, musamman ma ganin yanda ta ci ado, duk sai ya raina ajinsa, to ita d'inma hakanne a wajenta. "Fati." Ta narke fuska. "Nidai gaskiya ka daina kirani Fati." Yana murmushi ya jefamata tambaya. "Why?" Ta turo baki "Sunan fa Mami ne, kacemin Bintu na yanda kwa ya sanni da shi." "Ok, Bintuna, had'amin tea." Ta dubeshi ido waje sai kuma tayi k'as da kanta don batason kallon da yakeyi mata, irin kallon da Aisha ke gayamata a baya ta k'aryatashi, a yanzun kuwa ta gask'ata lallai akwai shi. Batayi aune ba ta ji ya tallafo ha6anta da hannunsa na dama kafin kuma ta ankara tuni ya soma mata sak'o. Abinda ya keyi zai tabbatar ya mance a inda suke, wannan karon ba k'arfinta ne ya kwaceta ba sai wayarsa da ta dauki ruri. Alokacin ta ja gefe. Ya duba Abbansa ne, cike da girmamawa ya dauka. Abba ya hau fadan dadewar da yayi bai zo sun wuce ba. Ya bashi hakuri gami da mikewa, a tsaye ya kora tea din kadan sannan ya koma daki, jimawa kadan ya fito cikin yadi maimakon shaddar da yasa a farko. Ta kauda kanta, yana murmushi yace"Saina dawo, zan fita da Abba. Ki shirya tarbata mai karfin mata goma." Ai a guje ta fad'a dakinta, ya fice yana dariya. , (Nagode wadanda sukamin ya jiki, da ma wadanda basuyiba a rubuce amma sun kirani, da ma wadanda basuyi duka ba amma sun damu da hakan. Allah Yabar zumuncinmu..love oll)