.
.
"Hafsat wai wannan tagumin da kikayi na menene? Yau naga gaba daya yanayin naki sai ahankali tamkar wata marar lafiya..." Daya daga cikin yanmatan tafada bayan ta dafa kawar tata,
.
Dukkan jama'ar dake wurin suka amsa cikin farin ciki domin wannan bawan Allah ba karamin taimako yake yiba saboda kusan agarin ma shine lamba daya wurin taimakawa rayuwar marayu.
.
K'ofar da zata sadashi da falon mahaifiyarshi ya bude ya shiga fuskar nan kamar zaice wayyo Allah dan tsananin fushi,
***
Mami ce tayi karfin yin magana cikeda damuwa,
.
"Nasani khadija, kuma nasan kinada hakuri amma daurewa zakiyi kisake yin wani hakurin ki koma dakinki..."
.
Har kofar gida hajiya fa'iza ta rakata suna cigaba da bawa juna hakuri musamman ma mami da take ganin laifin na yusleem ne domin shine yake nema yaja mata lalacewar zumuncinsu da matar da suka dade atare,
.
Cikin lokutan da babu yawa ta kwarance wurin sak'a sannan tafara iya dinkin keke,haka kawarta Amina itama tana yi daidai gwargwado,
.
"To wallahi kaji tsoron Allah yusleem, ina fada maka kaji tsoron Allah domin wallahi bazai barka ba indai kaci gaba da wannan mummunar dabi'ar taka ta auri saki"
.
"Yusleem nakasa gane damuwarka, tun kana karami kai mutumne mai zurfin ciki, amma ai bakada wanda zaka iya fadawa damuwarka sama dani da na haifeka, idan wani abune yake damunka kasanar dani.."
.
Kamar bazaiyi magana ba,daga ido yayi ya kalli surayya sannan ya mayar da dubanshi ga mami,
.
Shi dai a iya saninsa yasan lafiyarshi kalau bashida wata lalura wacce keda alaka da tabin hankali,
.
Yana tafe yana kokarin cire necktie din dake wuyanshi daf da zai shiga falo su surayya suka fito itada kawarta wacce ta Kawo mata ziyara,
.
Kada kai billy tayi tana dan murmusawa,
.
Banza yayi mata yaci gaba da cin abincinsa, bedroom din Mami ta shiga ta fara tsegunta mata maganar kawarta billy, ahaka yusleem yasamesu,
,
"Kai kuwa keda hadi da rukiyya yusleem domin dukkan alamu sun nuna cewar kana tareda aljana..."
.
Shiru yayi baice komai ba dama kuma tasan ba komai din zaice ba,
.
Saurin rufe bakinta tayi tai shiru, mami ce ta shigo tana rikeda dambun nama akan flate, yusleem ta ajiyewa agabanshi ta samu wuri ta zauna tana kallonshi,
,
Dan sunkuyar da kai yayi yasoma shafa sumar kanshi saboda nauyin da maganar ta mami tayi mishi,
.
Nan dinma dai shirun yayi baice komai ba, nan mami taci gaba da mita tana tayi shidai yayi shiru har tayi tagama ta tashi takoma bedroom dinta bai sake cewa koda uffan ba,
.
Ita kuwa mami shirye shirye nema masa aure taci gaba dayi, tuni har tabada sautin ahado masa lefe tun daga kasar dubai, amma har yau yusleem bai san koda kalar yarinyar da Mami keson aura mishi ba,
.
"Yusleem meya hanaka zuwa wurin matar da zan aura maka? Tunfa rannan nace maka kaje ku gaisa amma shine bakaje ba?
.
"To agaskiya Mami ni tayi min kankanta da yawa, ina laifin ma yar 23 zuwa 25,amma kawai ni akawo min wata karamar yarinya tazo tana yimin yarinta.."
.
"Kai kasani dai,nidai kaji abinda nafada maka yau dinnan kaje wurinta ku gaisa"
.
Sunkuyar da kanshi yayi yana murmushi, shi baya son yaji mami tana irin wannan maganar,
.
"Yusleem ai dole inyi wannan maganar domin tazama dole, idan ba marar lafiya ba wanne namiji ne za arinka aura masa kyawawan yanmata yazauna yana kallonsu sai ankwana biyu ka sakesu? Nidai har yau ina nan akan bakana nacewar kana tareda aljana dan haka ya zama wajibi inci gaba da nemar maka mafita"
.
Kananan kaya yasaka dark blue din t shirt mai gajeren hannu da bakin jeans, fuskar nan ahade babu alamun fara'a,kamshin turaren albahrainil madina ne ke ta faman tashi daga jikinsa,
.
Muryar nusaiba ce ta katse masa tunaninsa,
.
Wayarshi ya dauka yafara latsawa zuwa can ya dan kalleta kamar wanda akayiwa dole,
.
Acikin bedroom dinta ya sameta tana yin waya da su khalifa,
.
"Mami shiyasa nace maganar auren nan kibarshi kawai, yanzu ahakura da maganar auren wannan yarinyar, ki bani lokaci zanyi miki magana da kaina kuma da kaina zan gabatar miki da yarinyar da zan aura.."
.
"Mami kidai bani damar ki gani nidai burina yanzu ki hakura da maganar auren nan wallahi yarinyar nan tayi min karama kofa surayya batayi ba ashekaru.."
.
Mikewa yayi yafita Mami ta rakashi da ido ita yanzu tausayi ma yake bata saboda takamaimai ba asan abinda ke damunsa ba,
.
"Hajiya siyama nidai aganina ki rabuda yaron nan karki sake yimasa wani auren har nan da wani lokaci,
.
"Hakane hajiya fa'iza, hakika gaskiya kika fadi shikenan insha Allah zanyi yanda kikace"
.
.
"Ai hajiya kubra yau zuciyar tata babu sauki ranka ya dade domin kuwa tunda amal tabar gidan nan ta tafi kasar India karatu jiya shikenan hajiya ta rasa sukuni acikin ranta.."
.
"Hakane Alhaji sa'id, abin dai sai hakuri kasan lamarin mata, yawwa kafin in manta, dama abinda yasa kaga nazo yanzu shine so nake kayi min rakiya zuwa wani wuri, amma ba jimawa zamuyi ba, yanzun nan zamu dawo.."
.
"Hakane Alhaji sa'id, agaskiya ka Kawo shawara mai kyau kuma mai amfani shiyasa akoda yaushe nake farin cikin kasancewata dakai domin baka bani gurguwar shawara, yanzu abinda za ayi to bari mufara kaiwa gidan yarin ziyara inyaso idan mun fito sai mu karasa sauran wuraren.."
.
.
Dai dai lokacin da Hafsat takarasa dan karbar kudin idon Alhaji sa'id yasauka akanta jin gabansa yayi yafadi nan take zuciyarsa tashiga harbawa da karfi,
.
Wuri yasamu ya zauna yana kallonsu daya bayan daya, dukkaninsu samarine masu kamarshi sai ko dan banbancin da baza arasaba,
***Gidan Alhaji sa'id tawagar mai girma mataimakin gwamna suka wuce direct, hafsat tana zaune abayan mota sai zazzare ido take yi domin bata ma san inda suka nufa ba kasancewar ba fitowa sukeyi ba,
.
.
Atsorace hafsa take binsa da kallo saboda rashin sabo gashi kuma uwa uba bata taba ganinshi ba,
.
Amsawar da yaji hajiya kubran tayine ya dakatar dashi daga kwalla kiran da yake yi mata, falon tafito tana magana muryarta adashe saboda kukan da ta dade tanayi,
.
"Alhaji a ina kasamo amal? Dawo da ita kasa akayi?"
.
Sai a lokacin hajiya kubra tafara bin Hafsat da kallo tun daga kafarta zuwa kayan dake sanye ajikinta, ko shakka babu wannan ba amal bace amma kuma bata da banbanci da amal din sai ko gayu da wayewa wadda amal din zata fita dashi amma hatta kalar fatarsu da komai iri dayane kawai hutu da jin dadi fatar amal zata nunawa ta Hafsat,
.
"Yawwa tunda bukatata tabiya shikenan dama burina ki cire damuwar dake ranki akan amal ki karbi wannan amadadinta"
.
"Kisha kuruminki hajjaju wannan yarinyar babu abinda zai rabaki da ita domin tazama'yarki halak malak.."
.
"Hafsat, kamarku daya da tilon 'yata kwaya daya amal shiyasa lokacin da naganki naji ina sonki har cikin zuciya..., nan dakinta ne ina so ki daukeshi a matsayin naki, kiyi amfani da duk wani abu wanda kika ganshi acikin dakin nan ko kuma cikin gidan nan.."
.
Gabanta ne yafara faduwa zuciyarta tana bugawa da karfi da karfi Wanda har saida ta kaita da zama asaman gadon dake gefenta,
Kasa koda zama hajiya kubra tayi illah kaiwa da kawowa da take ta faman yi dan tsananin farin ciki, tabbas wannan wani al'amari ne daga Allah Wanda shi kadai yabarwa kansa sani,
.
Zama tayi akan kujerar dake makotaka da tashi,
.
"Hakan yayi daidai hajiya kubra,nidai abinda nakeso dake shine dan Allah ki rike yarinyar nan bisa amana duk danasan zaiyi wuya ki gallaza mata tunda bata da maraba da amal to amma wani lokacin ku mata ana ganin kamar kunfi kowa tausayi da rauni sai dai akan gallazawa yaran da ba nakuba kunfi kowa nuna rashin tausayi da rashin rauni, dan Allah ki riketa amana tunda kinga daga gidan marayu na daukota wannan yana nuna cewar ita maraya ce..."
.
"Haba alhaji ai basai kayi min wannan nasihar ba domin ko wanine yakawo min wannan yarinyar wanda bakai ba wallahi zan kula da ita..."
.
"Ya bakiyi wanka kin canja kayan jikinki ba? Tashi ki shiga bathroom kiyi wanka indan kin fito ga drewar din kayan amal nan ki duba duk wanda yayi miki kisaka.." Ta karasa zancen tana nuna mata drewar din da dan yatsanta,
.
"Hafsa kin idar ne?" Tajiyo muryar hajiya kubra na tambayarta,
.
"Ehh amma har yanzu dai banga alamar zata sake ta saki jiki damu ba saboda ganinmu take baki agareta" hajiya kubra tafada fuskarta da yar damuwa,
.
Mikewa Hafsat tayi suka fita zuwa cikin kitchen wanda kallo kawai Hafsat ta bude ido tanayi saboda ita ba taba ganin irin shi tayiba,
.
Suna falon alhaji sa'id azaune har misalin karfe 9 nadare lokacinne hajiya kubra ta mike ta kalli Hafsat,
'