Baza kizo ba?
Samha tayi shiru, hydar yace idan fa na tashi abun bayayin kyau kizo kawai dan rungumeni zakiyi sai kice inyi hakuri,
Samha tayi shiru, hydar yace ni kuwa da nine? Da yanxun har nayi miki yanda kike so,
Kallonshi samha tayi ba tare da tayi magana ba, shi kuma murmushi yayi sannan ya daga mata gira ɗaya, yana cewa keko zo mana! Ya karasa maganar yana kashe mata ido daya,
Matsawa tayi kusa dashi, hannunta ya riko yana jawota a hankali harya matso da ita kusa dashi, sannan ya kwantar da ita a jikinshi yana sauke ajiyar zuciya,
Yanda yake fitar da numfashin yasa jikin samha ya mutu ta kasa motsi, murmushi hydar yayi sannan yace kinasan hydar ne? Girgiza kanta tayi alamar A, a, hydar yace baki so na, amma kina rubutawa a jikinki miyasa?
Samha tayi shiru, duk maganar da hydar yake yiwa samha ta kasa magana, ganin bazatayi magana ba yasashi ya dan fara shashshafa ta, yana tambayarta miyasa ta rubuta tana sanshi? Bata bashi amsa ba, ganin bazatayi magana ba yasa hydar yaci gaba da jagwalgwala samha san ransa,
Cikin kuka samha tace don Allah ka barni bana san kana min haka, kallonta hydar yayi sannan yace ai yanxun na fara idan dai bazaki fadamin abinda yasa kika rubuta kina so na ba, dakina ma zan tafi dake tunda kina so na, sai muje in baki hydar gaba dayanshi,
Yarinya kina san hydar ne? Samha tayi shiru, ɗagata yayi daga jikinshi sannan yace sauka, sauka tayi daga jikinsa a hankali sannan ta durkusa kasa, hydar yace tashi tsaye, mikewa samha tayi tana kallon kasa, kallonta hydar yayi sosai a ranshi yace lallai jikin samha bai anshi sakona ko daya ba, to kodai taji karfin hali takeyi dan kada in gane? Kallon samha yayi sosai lallai bataji komai ba tunda har ta iya tsayawa saman kafafuwanta, tsaki yayi sannan ya gyara kwanciyarsa yace kezo nan, yana nuna mata inda zata sake kwanciya a jikinshi,
Cikin kuka samha tace don Allah ka daina wannan abun, dani dakai dukanmu muna cikin fushin ubangiji, kuma ya tsine mana albarka saboda muna aikaita saɓo, da sauri hydar yace kai nikam Allah bai tsinemin ba kuma kema bai tsine miki ba, waye yace miki Allah yana tsinewa miji da mata? Shiru samha tayi dan bata gane inda maganar hydar ta nufa,
Cikin shagwaɓa yace nidai kizo nan nace, yanda yayi abunne yasa samha taji wani yarrrrrr, a jikinta, amma saita goge hawayen idonta ta juya tayi tafiyarta, duk maganar da hydar yakeyi ma samha a banza, dan samha bata saurareshi ba,
Tsoki hydar yayi sannan yace wannan ai daukar alhakine, ni wallahi na gaji da wannan iskanci, kullum saidai kizo ki wani wuce ta gabana kina murza ƙugu, kina tafiya kina tada min hankali ke kuma hankalinki kwance ni kuma ki barni da tashin hankali, duk wasu ma'aurata suna cikin nishadi amma banda ni mtswww,
Tashi yayi ya dauki tarkacen sa yayi sama, a gajiye ya isa dakinshi, zama yayi a gefen gado sannan ya fara dogon nazari, shawara ta farko data fara zuwa ma hydar shine, kodai ya saki samha a matsayin sahib sai yaje a matsayin hydar ya aurota? A hankali ya kwanta saman gado, fuskarsa tana kallon sama, zuciyarsa tace kadai sake mafita,
Dan idan har samha ta fita daga rayuwar sahib ta tafi bata sake dawowa, murmushi hydar yayi, wata zuciyar tace masa karya ne, dan kayi ma samha babban horon da bazata iya rabuwa dakai ba, wayarshi dake ringing ta dawo mishi da tunanin sa, juyawa yayi ya dauki wayar, bayan gaisuwa yace faruk kazo gida yanzun ina san ganinka, faruk yace tom, hydar ya kashe wayarsa,
Samha kuwa tana shiga daki da gudu ta haye saman gado tana kuka, lallai sahib ya cuci rayuwarta daya hadata zama da hydar, dan ita a ganinta duk duniya babu ɗirkeken ɗan iska kamar hydar, dan idan har aka aiketa neman jibgegen dan iska tana ganin hydar zata tsaya dan hydar babban dan iskane na bugawa a jarida gashi baida kunya ko kadan, amma sahib yasan halinsa ya hadata zama dashi wannan ai haukace da rashin sanin darajar addini hade da rashin sanin mahimmanci iyali,
Samha tana kwance saman gado sai kuka takeyi, lallai sahib mahaukacine, amma lallai ya dawo tunda baya santa ya saketa dan da zama da aurensa gara tasan bata dashi saboda zunibin ya mata yawa, lallai tana san ta kasance a jikin hydar dan ita kadai tasan yanda takeji, komai tanaji amma tana jin tsoron azabar Allah tunda akwai auren sahib a kanta, tunanin abubuwan da hydar yayi mata takeyi lallai hydar ya iya taɓa mace komai yanayi cikin natsuwa da nuna kwarewa, murmushi tayi a bayyane tace Allah ka shirya sahib shima ya gyara halinsa, yafi hydar iya komai,
Bayan faruk yazo yayi ma hydar waya yazo, hydar yace ina zuwa ka jirani, faruk yace to, saida hydar yayi wanka sannan ya nufi inda faruk yake jiransa, yau sahib ne ba hydar ba,
Ta baya ya fita, yaje inda faruk yake jiransa, bayan sun gaisa hydar yace faruk saifa ka taimaka min, faruk yace taimakon mi hydar? Gyara tsayuwarsa yayi sannan yace idan ina gaban samha a matsiyin hydar zan rika kiranka in hadaku kuyi magana da ita a matsayin sahib, idanuwa faruk ya zaro sannan yace wallahi bazanyi ba,
Hydar yace miyasa baza kamin ba? Faruk yace kai ba wasa da so yaja maka ba? Nima kana so ka dilmiyar dani? kamar yanda kayi? Hydar yace insha Allah babu abinda zai faru wallahi, faruk yace gaskiya hydar bazan iya ba, dan bazan yadda ka koyamin abinda ba halima ba,
Hydar yace to kayi hakuri ka zauna ma zauni na, zan bata numberka a matsayin hydar, faruk yace wallahi babu wanda zai ɗanɗanamin inyi abinda nasan zan cuci kaina, ajiyar zuciya hydar yayi sannan yace to gaskiya zan hakura da samha tunda bansan mafita ba,
Faruk yace kaji tsoron Allah hydar zaka cuci diyar mutane wallahi, hydar yace ai nima cuceni tayi ta wani lallai ta shige a zuciyata ba tare dana ankara ba, daga wasa sai abun ya zama gaskiya, danni ban yadda ina san samha ba sai ranar danaga ta suma, faruk yace da kasan zaka rabu da ita da baka koya mata zama a jikinka ba,
Hydar yace to ai kowa ya rama kenan, ta rikemin zuciya ni kuma na rama dan nasan ko bata nemi sahib ba dole saita nemi hydar, faruk yace kada ka kawo aikin gaba a yanxu, waye yace maka ana wasa da zuciya? Tunda kaima Allah ya dora maka kaji yanda matan daka zalinta suke ji, kaji tsoron Allah hydar yarinyar nan bata san ko waye kai ba, kace kana santa ta yadda ta soka, kai kuma kaso kayi mata mugunta, amma Allah ya rike maka zuciya ya hanaka zalinci wa samha hydar wannan halinka ne ka sani, da jikinka kake yaudarar zuciyoyin mata, suma matan basu da hankali basu san ba ko wane jikin namiji ake shiga a fita haka nan ba, kaji tsoron Allah hydar idan har kacuci samha wallahi sai Allah yayi mata sakayya,
Zalinci biyu kayi ma samha, kazo mata a matsayin sahib ka hora mata zuciyarta da san sahib, kaje a matsayin hydar ka koya mata shiga jikinka, danni da naga ka ɗagawa mace hannu ta rike ina tausaya ma rayuwarta kaji tsoron Allah hydar,
Hydar yace ai danna yadda da kaina na mata hakan amma ita bata san inayi ba, batajin komai idan tana jikina, yadda da jikin nawa yasa na fara koya mata zama a jikina wannan dalilin yasa nayi mata wannan horon amma na lura samha tana da daskarariyar zuciya, faruk yace to irin abinda kakeyi ne Allah yasa akayi maka, sai kaje ka nemi mafita Allah ya sawake, faruk yana fadin haka ya nufi wurin motarsa yaja yabar gidan,
Murmushin karfin hali hydar yayi sannan ya tashi ya nufi dakinsa, yana shiga a jikin madubi ya matsa ya kalli kanshi sosai sannan yace sahib din banza mtsww, fita yayi daga dakin ya nufi dakin samha,
Samha dake kwance saman gado tana kuka taga sahib da sauri ta tashi zaune tana cewa dan rainin hankali sai yau kaga damar dawowa ne? Daure fuska sahib yayi sosai sannan ya shiga zazzagawa samha ruwan rashin mutunci tare dayi mata fada tasa hydar yayi sharar farlo kamar wani sa'arta, ikon Allah samha ta fada cikin yanayin mamaki, sannan tace lallai sahib amma wallahi baka da adalci matsawa kusa da ita yayi ya daddaga mata hannunshi a saman hancin ta, sannan yace bazanyi adalcin ba, kuma maza maza ki tashi kije ki goge wancan iskanci da kika zana a farlo,
Samha zatayi magana sahib ya daka mata tsawa tare da cewa tashi kada ki daukeni sakarai, ganin babu alamar wasa a tattare da sahib yasa samha tashi da sauri ta shiga toilet ta dauko hypor da klin ta fito,
Sahib yace kuma minti ukku na baki ki gogeshi idan ya wuce haka na dawo zakiji a jikinki, da sauri samha ta fita daga dakin tana gunguni, dariya hydar yayi sannan ya biyo bayanta yana cewa ni kike ma rashin kunya ko?
Samha tace ni bada kai nake ba, sahib yace to da wa kike ne? Samha tace da hydar nake a duk shine munafikinmu yana hadamu fada amma baka ganewa, cikin daga murya sahib yace da Allah rufe min baki, magana samha tayi kasa kasa wanda sahib baisan abinda tace ba, fasa hypor tayi ta zuba a wurin data zana jan bakin ta zuba klin ta duka ta fara goge, haka sahib yayi ta dakawa samha tsawa yana hantararta,
Sai turo baki takeyi tana gunguni, amma hydar bayajin abinda take cewa, saida ta goge wurin tass sannan sahib yace kuma daga yau babu maganar hydar ya sake shara na fada miki, turo baki samha tayi amma batayi magana ba, sahib yace maza kije ki dafa abinci, har wani cewa kikeyi waike kin gaji da dafa abinci wa mutane da yawa, to ki gaji din in gani, Allah yasa inji kin kara wani abu wanda bai min ba kiga yanda zanzo in miki dukan lullusar fitar hayyaci a gidan nan,
Yana fadin haka ya sauko zai wuce sulbin klin yaɗan jashi zuuuuuu, amma baikai kasa ba, samha ta kyalkyale da dariya tace dama ka fadi wallahi sai naga wanda zai tasheka, juyowa sahib yayi yana harararta, gwalo tayi mishi sannan tayi ciki da gudu tana dariya, shima hydar dariya sannan ya fita daga farlo,
Saida samha ta tabbatar sahib ya tafi sannan ta fito, da saurin ta nufi kicin tana zuwa babu bata lokaci ta daura girki, bayan ta dora ne ta fito dan ta dauki towel din data goge wurin ta mayar toilet, tana fitowa taga hydar zaune yana kallo,
Dariya tayi sannan ta matsa kusa da hydar tace bari in baka labari, kallonta hydar yayi amma baiyi magana ba, samha tace ko baka san labarin ne? Murmushi yayi tare da jinjina kanshi alamar yana so, zama samha tayi sannan ta bashi labarin kaf yanda sukayi da sahib, dariya hydar yayi sannan ya ba samha hannu suka kashe,
Hydar ya kara da cewa dama ya fadi da munga yanda zaiyi, samha tace kuma wallahi da bazan tada mugu ba, dariya hydar yayi sosai sannan ya rungumo samha a jikinshi yana cewa miyasa bazaki tada sahib ba? Samha tace yayi girma da yawa, murmushi hydar yayi sannan yace dani dashi waye yafi wani girma samha tace ya za'ayi in sani ne? Dogon kallo hydar yayi mata sannan ya kalli kanshi yana kara rike samha a jikinshi, murmushi samha tayi sannan ta zare jikinta daga jikin hydar a hankali, a ranta tace shidai yana san ya rikeni a jikinshi, da saurin ta tashi tayi sama,
Hydar yabita da kallo yana murmushi, bayan ta fito daga daki zata sauko tace ma hydar kalli ka gani, kallonta yayi ita kuma ta tsaya daidai inda sahib ya tsaya tana cewa hydar kalli kaga yanda yayi, ta dafa karfen benan ta fara kwaikwaiyon maganar sahib da yanda yayi tsayuwar da yanda ya kusa faduwar duk samha ta nuna hydar ya sake shekewa da dariya sosai dan wallahi duk yanda yayi haka samha ta nuna, shi kuma yanda tayi abin ya mishi kyau, murmushi hydar yayi sannan yace ke kuma ya kikayi ne?
Murmushi samha tayi sannan ta fara nunawa hydar yanda tayi da tsugunni datayi tana goge wurin da gungunin da takeyiwa sahib da gwalon da tayi mishi da gudu datayi, murmushi hydar yayi yana kallon samha,
Tahowa tayi a hankali saida tazo tsakiyar farlon sannan ta nuna mishi yanda sahib ya harareta hydar ya sake kyalkyalewa da dariya itama dariya tayi sannan tayi kicin da dan sauri, murmushi hydar yayi sannan ya tashi yabi bayan samha,
Shine ya tayata girkin sunayi suna fira, har suka gama, shine ya fito da abincin ya ajiye a dirning, sannan ya koma suka gyara kicin tare shi yayi shara ita kuma ta goge,
Bayan sun fito daga kicin hydar yace tazo suci abinci samha tace ita batajin yunwa, hydar yace mi kikaci ne? Tabe baki samha tayi sannan tace kawai na koshine, zanje inyi wanka saida safe, hydar yace to Allah ya kaimu, samha tace amin,
Shima ba wani abincin yaci ba, shamsu yayi ma waya suka zo sukaci abinci sun dade suna fira, saida suka gama suka fita sannan hydar ya tashi ya nufi dakinshi shima,
Tou lamarin jiki da jini sai a hankali, yau kam samha an tashi babu lafiya, ta tashi da wani irin matsananci ciwon ciki, tana daki ta ƙudundune sai kuka takeyi, tayi goho saman gado saboda azaba sai juye juye takeyi saida ta kwanta ta tashi dan tana shan wahala sosai,
Shi kuma hydar ya dade a farlo yana jiran fitowar samha, amma bata fito ba, daya gaji da jiran ta bata fito ba tashi yayi ya koma dakinshi yayi wanka yabar gidan,
Samha kuwa ciwon cikin yana lafawa dakel ta matsa kusa da wayarta ta dauka ta fara kiran sahib, saida ta kira har sau ukku bai dauka ba, a na hudun ne ya dauka yace miye? Cikin kuka samha tace banda lafiya miya sameki ne? Ciwon ciki nakeyi, to ki fadawa hydar danni ina da abinda nakeyi banda lokacinki, a hankali samha tace banda number hydar ai, tsaki yayi sanna yace zan turo miki yanxun, yana fadin haka ya kashe wayar,
Samha bin wayar tayi da kallo a ranta kuma tunanin halin sahib takeyi gaba daya ya burkuce mata, sai wani tashen zalinci da yake mata da rashin tausayi, hmmm lallai namiji ƙanin ajaline, niko sai nake gani wadda bata dace ba itace take cewa namiji kanin ajali samha,
Tana cikin tunani sakon ya shigo, number ta gani an rubuta hydar, saida ta sake dafe cikinta sannan ta fara kiran number hydar, babu ɓata lokaci hydar ya dauka bata bari yayi magana ba, cikin kuka samha tace hydar zan mutu, hydar yace subahanallah miye yasa zaki mutu? Kuma wace ce take magana ne?
Wani irin nishi samha tayi sannan tace nice, hydar yace kece wa? Ni samha! Hydar yace wayyo samha sannu ganin zuwa bana gida ne na fita amma ina hanya kiyi hakuri kinji, cikin shashshekar kuka samha tace to ka taho dakai da sahib, gaban hydar ya fadi sosai,
Amma saiya basar yace ki zaɓi daya, ni zanzo ko sahib? Dogon nazari samha tayi sannan tace kasa sahib yazo, hydar yace to babu damuwa zansa yazo kiyi hakuri,
Godiya samha tayi sannan ta kashe wayar, hydar kuwa yana isowa gida, dakinshi ya wuce ya shigo sahib, ya taho dakin samha tun kafin ya shigo dakin ya fara masifa, samha dake kwance ta bishi da kallo, masifa sahib yakeyi yana karawa kamar zai daki samha, wai yana uzirinsa taje ta matsa ya taho shi ina ruwanshi da ciwon cikinta, samha tace kayi hakuri, sahib yace anƙi ayi hakurin ciwon cikinkin banza? Kin wani bi kinsa an tadoni daga wuri mai nisa to ba sannu ba, kuma bazance sannu ba, zan tafi bari ki sake sa a kirani kiga yanda zan miki lullusar futar hayyaci a gidan nan yana fadin haka ya fice daga dakin,
Ajiyar zuciya samha tayi sannan ta sake jawo wayarta ta fara kiran number hydar, cikin kuka samha tace hydar don Allah kayi hakuri kazo, hydar yace au sahib din baizo ba? Samha tayi shiru, hydar yace swry my samha, ina zuwa insha Allah, samha tace to hydar ya kashe wayarshi,
Samha kuwa addu'a take Allah ya bata lafiya duk bala'in sahib saita kakkaɓe aurensa, dama ashe baida mutunci, shida Allah, tarayyarta da sahib ta fara tunowa, a ranta tace kuma fa sahib yamin babban taimako banda sahib da yanxun na fado daga bene na mutu, shigowar hydar ya dawo da ita tunanin da takeyi,
Da sauri ya shigo cikin dakin yana cewa wayyo sannu samha, duk yayi wani kalar tausayi yanda yayi abun kamar a jikinsa ciwon yake, zama yayi a gefen gado da sauri samha taja jikinta ta dora kanta saman jikin hydar tana kuka, shafa gashin kanta yayi tare da cewa sannu,
Cikin kuka samha tace hydar sahib ya daina so na, kamishi magana banajin dadin abinda yakemin don Allah, bayan yasan banda kowa a duniyar nan saishi, miyasa zaimin haka? Hydar yace kiyi hakuri ba gani ba? Duk abinda sahib zai miki zan miki wanda yafi nashi ki kwantar da hankalinki kisa a ranki hydar mai adalci ne, danni a zuciyata kin zauna kuma bazan iya cireki ba samha, samha tayi shiru dan ita bata gane yaren hydar, murmushi hydar yayi sannan yace miyasa kike ciwon ciki ne?
Samha tayi shiru dan bazata iya fadawa hydar ba, hydar yace kinyi shiru, samha bata da yadda zatayi tace aina samu samu sauki, kwanciya hydar yayi ƙafafuwanshi na kasa ya dora kan samha saman cikinsa hannunshi yana saman cikinta, yana mata sannu,
Banda ajiyar zuciya babu abinda samha takeyi, hydar yace ko inkaiki asibiti ne? Ita kunya takeji a gaban hydar a fadamishi abinda yasa take ciwon ciki, itadai period ne amma batasan ya sani da dai sahib ne zata iya fada mishi, hydar yace kinyi shiru, murmushin karfin hali samha tayi sannan tace aina samu sauki ma,
Hydar yace to kiyi bacci, samha tace to, rufe idanuwanta tayi, a ranta tace dama hydar ne mijina ba sahib ba, shi yayi tafiyarshi ya barni saboda wani aikin banzarshi amma hydar ya baro nashi yazo ya kula dani, a fili tace Allah ka shirya min mijina ya daina halin da ba nashi ba, hydar yace amin, nima Allah yasa matata ta so ni,
Ajiyar zuciya samha tayi sannan tace hydar dama kana da mata ne? Gyarawa samha kwanciya yayi ya juyo da ita tana kallonshi hannunsa yasa ya goge mata hawayen idonta sannan yace ina da mata samha, amma bata sona kwata kwata, ta tsaneni kullum sai tace zata iya kasheni kamar dai yanda kike fadamin a da,
Samha tace Allah ya shiryeta, hydar yace amin, amma bana tunani zata so ni har abada samha, murmushi samha tayi sannan tace mi zai hana ta soka mana?, hydar yace bazaki gane ba, samha tace zan gane mana saidai idan baka fada min ba, murmushi hydar yayi sannan yace manta da wannan maganar kinji ko? Samha tace to,
Sauketa yayi daga jikinshi yana cewa bara in kawo miki magani kisha, samha tace to kai malamin asibiti ne? Hydar yace sosai ma, hada allura duk na iya, kuma allurata dadi gareta ko kina so in miki ne? Murmushi samha tayi sannan tace dama allura akwai mai dadi ne? Hydar yace sosai ma sahib bai taba fada miki ba? Samha tace Eh, hydar yace da kina so da nayi miki yarinya dasai kinso kullum kinyi rashin lafiya, don doctor hydar ya dubaki, yana faɗin haka yayi waje,
Dariya samha tayi, tare da rufe idonta, a hankali ta fara tuno tun ranar data fara haduwa da hydar yasa maX ya rufe fuskarshi, da lokacin daya jefeta da wuka, da lokacin data dawo wurin sahib ta tadda hydar da ruwan data watsa mishi a fuska murmushi tayi, sannan ta tuno abinda yake saka mata a ido, ajiyar zuciya tayi sannan tace amma matar hydar mahaukaciya ce, duk wanda ta samu hydar a matsayin miji ai ya more a rayuwarshi, to yaushe yayi auren bayan sahib yace matar ta fasa aure dashi?
Kiran da hydar yake mata ya hanata karasa tunanin da takeyi, a hankali ta sauka daga saman gado tana tafiya a hankali har ta fito, hannunta yaja suka sauka farlo, saman kujera ya zaunar da ita sannan yaje kicin ya hado mata tea ya dawo da kanshi ya bata tasha sannan ya bata magani tasha,
Bayan ta gama yace in maidaki daki ko kuwa? Samha tace kai ina zakaje? Hydar yace ina da meeting yanxun, ɓata fuska samha tayi tana cewa shikenan ni bani da mai so na? Tana maganar tana daga hannunta na haggu tana kwantar da kanta gefe daya kamar zatayi kuka, murmushi hydar yayi sannan yace waye yace miki bana sanki? Samha tace nifa bakai nace baka so na ba, kawai nace banida mai sona ne, hydar yace to aini ina sanki, samha tace to ka zauna kayi jinyata tunda sahib ya tafi,
Ajiyar zuciya hydar yayi sannan ya kalli agogon hannunshi durƙusawa yayi saman guyawunshi ya dafa cinyoyin samha dake kan kujera zaune yana kallon fuskarta yace kiyi hakuri dana gama zan dawo don Allah, insha Allah bazan wuce 30minutes ba 👌🏻,
Samha tace nidai kayi hakuri kaga banda wanda zaiyi aiki so kake sahib yazo yayi min rashin mutunci? Murmushi hydar yayi sannan yace nima inmishi rashin mutunci, kuma idan na dawo zan miki komai har wanka ma kina so ko? Yanda yayi abin yasa samha taji gajiya ta lulluɓeta, ga wayar hydar sai tsuwa takeyi amma sai hakuri yake bawa samha, yace kiyi hakuri kinji yanxun zan dawo insha Allah a daidai lokacin da yake kwantar da ita saman kujera, yana kwantar da ita ya fita farlon da sauri,
Haka dai zaman samha da hydar yaci gaba da tafiya hydar yana bawa samha kulawa sosai sunayin wasa tare hydar yanayin kwallo tare da samha dan ya lura tana san wasan tsalle tsalle dan haka duk wani abu da yasan zai motsa jiki tare sukeyi, samha ta fara fahimtar hydar baida matsala, sahib kuwa kullum tsakaninsu sai masifa da bala'i da jaraba, wani lokaci ta bawa hydar labari wani lokaci kuma ta basar,
Da gudu ta fito daga daki tana cewa bazaka cemin ka fara ba inzo in fara irgawa? hydar ne duƙe a tsakiyar farlo yana press up, da sauri ta sauko tace tsaya tsaya, tsayawa hydar yayi amma har yanxun kanshi yana kasa, power💪🏻 shi ta taba tace lallai wallahi kai kato ne sosai, murmushi hydar yayi sannan ya daga guyawunsa kasa kamar yaro yana rairafe, amma har yanxun kanshi yana kallon kasa,
Samha tace hydar don Allah bari inhau bayanka inga zaka iyayi dani? Murmushi yayi da gefen bakinsa amma baiyi magana ba, kusa da fuskarshi ta matsa ta durkusa a gabanshi ta kamo fuskar shi yana kallonta sannan tace in hau, murmushi hydar yayi ita kuma ta saka ɗan yatsanta cikin beauty point nashi saida tsagar hannunta ta shige daidai inda kunshi yake tsayawa, rike mata hannu yayi yace bana ce bana so ba,
Dariya samha tayi sannan ta tashi da sauri taje ta kwanta saman bayan hydar tace muje mazaje, ruf da ciki tayi ta saƙala hannunta a wuyanshi, hydar yace to ai kin shaken wuya, ki sake hannunki kawai, samha tace ai bana so ka faɗar dani ne, yace bazaki fadi ba, sakin wuyanshi tayi ta maida hannunwan ta a bayanta ta taɓa bayanta dasu ta lafe sosai a bayanshi, sannan tace muje muje mujeeeee mazaje, hydar yaci gaba dayi samha tana irgawa shidai baiyi magana, saida yayi sosai sannan yace nafa gaji, samha tace don Allah ɗan ƙaramin mana, hydar yace ai yanxun kece zaki min,
Da sauri ta sauko daga bayanshi tana cewa wallahi bana iyawa, tana kokarin guduwa hydar ya tashi da sauri ya rikota yace saifa kinmin na fada miki, turo baki samha tayi sannan tace ni wallahi bana iya daukarka kayi babba, hydar yace karyane waye yace baki iya dauka na ne?, Dan gajeran tsaki yayi sannan yace maza duka a gwada ki gani, cikin sakata samha tace nidai bana so ka daina, hydar yace to ba komai Allah ya kaimu anjima naga wanda zai goyaki a mashin dinshin shi,
Murmushi samha tayi sannan tace bari ma inje in mishi wanka, bai sake magana ya wuce abinshi ita kuma da gudu ta nufi kicin dan ta zubo ruwa ta wanke mashin, wani mashin din tseral ne samha ta ganshi a wurin faruk ya goyo budurwarshi sunzo wurin hydar mashin din ya burge samha bayan sunyo ma faruk rakiyane samha tace hydar mashin din nan yamin kyau dan Allah kadan ɗanani akai,
Hydar yace miyasa? Samha tace kawai faruk ya birge nin....bata ƙarasa maganar ba hydar ya bigar mata baki, sannan yace mi kika ce? Samha tayi shiru, hydar yace ke bakijin wani iri kice wani ya birgeki? Ni bana birgeki ne? Samha tayi shiru, ita kuma abinda zatace faruk ya birgeta daya goyo budurwarsa akai dan mashin din idan ka hau saika kwanta saman bayan mai tukawa, ansar makulin hydar yayi ya ɗana samha a cikin gida, shine fa dalilin daya sa ya siyi mashin din kuma dan jaraba duk marecen duniya sai hydar ya goya samha a mashin din,
Da sauri samha ta fito daga kicin da bokitin ruwa a hannunta zata fita daga farlon hydar dake saukowa yace ke ina zakije ne? Da sauri tace zan wanke mashin ne, hydar yace kina hauka zaki fita haka baki ga kayan da yake jikinki ba?, sai yanxun ta kalli kanta, wandone wanda dakel ya wuce gwuwa sai top kanta babu kallabi tsaki hydar yayi sannan yace ni bana san wanke manshin idan ba haka ba zan badashi,
Samha tace yi hakuri, hydar yace na hana wanke mashin daga yau, samha tace tom, yace zo ki wuce kije kiyi wanka, da sauri ta wuce ta gaban hydar tayi daki, tana zuwa babu abinda ta tsaya yi wanka tayi, bayan ta fito ne ta dauki wayarta ta fara kiran sahib, bayan ya dauka suka gaisa sannan tace mishi nifa banda kayan shafa komai ya kare, tsaki yayi sannan yace to ina ruwana? Mutum ba kyau ba sai kilbibin yayi kwaliya mtswww ya kashe wayarshi,
Wannan abu yayi ma samha ciwo cikin kuka ta fito da gudu tayo farlo, tunda ta fito hydar yake dariya a ranshi, tana zuwa ta fada jikin hydar tana kuka da sauri ya tashi yana cewa subahanallah? Miye? Nifa wasa nake bazan bayar da mashin ba, harma nasa an wanke miki yau hada turare zan fesa mishi dan kiji dadi, jeki ki saka kaya ki taho dan yau idan aka fara ɗani sai dare yayi,
Cikin kuka samha tace hydar don Allah wai banda kyau? Ta karasa maganar tana ɓata fuskarta, hydar yace inji waye? Samha tace sahib, ta karasa maganar tana ƙara fashewa da kuka, goge mata hawayen idonta yayi sannan yace ƙarya ne, kina dakyau, gaki fara mai hanci ga gashi ga girare masu kyau idanuwanki irin na hydar ne, kinsan haka matata take cewa wai idanuwana kamar na mage na atini, maganar da samha take fadawa sahib, wannan banzan hydar ɗin da idanuwanshi kamar na mage yana atini,
Samha tace kaima kana fada da matar kane? Hydar yace A, a, kawai dai bata so nane, mi kikayi ma sahib yace baki da kyau?, yayi maganar ne dan ɓatar da maganar matarshi, gyara bakinta tayi amma batayi magana ba, hydar yasan dai samha baza ta faɗa mishi saboda kayan shafa sahib yace haka ba, dan haka murmushi hydar yayi sannan yace kema samha da kinayin kwalliya mai kyau da daukar hankali bazace miki haka ba, da sauri samha tace ai na fada mishi banda kayan shafa ne sai yace wai ni banda kyau kwalliya bazata min kyau ba,, hydar yace to kiyi hakuri ni zan siya miki duk abinda kike so ki daina fadawa sahib tunda ya daina sanki, samha tace to, hydar yace maza kije ki saka kayanki kizo muje muhau mashin dinmu, da gudu ta tashi tayi ciki,
*Jameela musa* ce
💋
[05/04 4:45 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*_FATIMA MUHAMMAND wannan sakon ta aiko zuwa gareku masoyan labarin SO MUGUN WASA kamar yanda nayi alkawarin zaizo gareku gashi na kawo muku shi,_*👇🏻
*_Meelat kin burgeni da wannan bayani kinsan dayawammu karatun kawai sukeyi suji nishadi ba tare da sanin ainihin labarin ba balle ginshikinsa. Idan har samha zata gane hydar a yanzu dole ta gujeshi saboda bb sonsa ko na sisi azuciyarta yanzu kuma hydar yake kokarin dasa kiyayyar sahib a zuciyarta sannan ya kafa tasa gwamnatin ta yadda ko tazo ta ganeshi already takamu da sansa. Meelat don Allah kiyi hakuri da mutun babu mai iyamar sai Allahn sa muna tare da ke kuma alherin Allah ya kyewayeki ta yadda zaki gagari mahassada. Wallahi ina jinki araina_*
*_Ita kuma sabeera sabeer cewa tayi_*👇🏻
*_Aunty meelat tunda sun matsu dajin lbrn samha tagane hydar to sai kibarmu typing din muga yanda zasu hadasu ko ba sunan wnnn littafin love is a bad game ba yakamata mu masu karantawa mu auna mugani haryanzun samha tana son sahib so bana wasa sbd kuduba kuga rashin mutuncin dayakemata amma addu,a takemai allah ya shiryesa kuma idan kunyi hkr ai samha tafara tunani hydar kunga dazarar tagama yadda dashi shi kenan bazai sha wahala dan allah writers din brilliant kuyi hkr daga masu yimuku hassada abin ba dadi amma hakuri za kuyi mai kaunarki ce Aunty meelat sabeeran sabeer_*
*_Ni kuma Meelat Musa cewa nayi don Allah kuyi min hakuri ku bini sannu dan Allah, ku bini sannu, dan kafin in fara rubuta novel din na tsara shi saida na gama kaff sannan na fara typing nasa a online, kuyi hakuri ku kasance tare dani,_*
*SO*
*MUGUN WASA*
*_Dedicated to_*👇🏻
*_Ramlat Abdulrahman real mai dambu_*
*50-52*
Da gudu ta tashi tayi ciki,
Murmushi hydar yayi a bayyane yace ashe kinji haushi nace miki babu wani kyau sai kilbibin kiyi kwalliya, dariya yayi tare da tafa hannuwanshi yace shege ni hydar ni daya na burkuta mata kwalwa, inzo sahib inje hydar, lallai fa akwai babbar cakwakiya idan samha ta ganoni, ganin samha ta fito yasashi yayi tsitt,
Da saurinta ta sauko daga saman benen tana cewa tashi muje, kallonta hydar yayi sannan yace gaskiya bazan daukeki a mashin ina yau ba, samha tace miyasa? A daidai lokacin da take zama kusa da hydar, murmushi yayi sannan yace kullum abinda kike so nake miki amma ni bakyamin? Tsoki samha tayi sannan tace kai komai a rungumeka a sunbace ka?,
Hydar yace wallahi kuwa kamar kin shiga zuciyana, kawai so nake kiɗan lashe min bakina, sai kiɗan rungumeni, sai kice min kina so na, shikenan ni kuma sai in goyaki a mashin kiji dadinki murmushi, sannan ya ƙarasa maganar yana lumshe idanuwanshi,
Samha tace gaskiya bazanyi ba, hydar yace ashe kuwa yau babu hawa mashin a daidai lokacin da yake kwaciyar a kujera, tsaki samha tayi tare da cewa kada Allah yasa ka goya, ta miƙe tayi tafiyarta, hydar yace zo samha, tayi kamar bataji shi ba, da sauri ya tashi ya bita amma kafin yakai harta shige ɗaki ta rufe kofarta da makulli,
Dukan kofar ya farayi yana kiran samha! Samha!! Don Allah bude kofa mana, wallahi wasa nake miki bama sai kinmin ba, samha tayi shiru, cikin sigar lallashi hydar yace samha don Allah kiyi hakuri ki fito kinji, ni wallahi bana san kina fushi,
Tasowa samha tayi tazo ta bude kofar, tana budewa ta koma ciki, da sauri hydar yabi bayanta, yana cewa samha don Allah ki daina fushi, wallahi idan kina zuciya dani Allah ya sani inajin kamar zuciyata zata fito waje, saboda kwata kwata wallahi banajin dadi,
Kallon shi samha tayi sannan tace miyasa zuciyarka zata fito waje akaina? Murmushin karfin hali hydar yayi wanda idanuwanshi sunyi jawur kamar zaiyi kuka, sannan yace saboda ke amana na ne, nima fa amanar ni aka baki ya nuna kanshi da hannu, sannan yaci gaba da cewa ki daina haka wallahi babu kyau wulaƙanci samha, ya karasa maganar kamar zaiyi kuka yana wani kwantar da kansa gefe, duk yayi wani kalar tausayi, hannunta ya riƙo tare da ƙago murmushi mai kartar masa zuciya, yace muje in goyaki a mashin din, samha tace gaskiya bana so yaudai kam bana so, kila saidai ko gobe idan Allah ya kaimu,
Hydar yace to muje in siyo miki kayan shafa da kaina ma zan kaiki saboda inaji dake bana san sahib ya sake ce miki bakya kwalliya, murmushi samha tayi, sannan tace to muje, hijabinta ta dauko, hydar yana so yace kada ta saka hijabi tasa gyale amma yana tsoro kada ta sakeyin fushi,
Saida ta saka hijabin sannan ta biyo bayan hydar murmushi yayi sannan ya tare kofar daki tare da cewa kawo in rike miki hannu, waidan kada ta koma ciki ya tare wurin, murmushi samha tayi sannan ta miƙa mishi hannunta, shima hydar murmushi yayi sannan ya anshi hannun yayi mashi kyakkyawan riko, yana dan murzashi a hankali, ta yadda samha zata rika jin wani baƙon lamari yana shigar duk wasu kofifi na jikinta,
Haka sukayi tafiyar, hydar shine yake tuƙa motar samha kuma tana gefenshi ita kuma ta kwantar da kanta a jikin kofar mota, ba tare da hydar ya kalleta ba, yace samha zoki kwanta anan, yana nuna mata kafadarshi, ajiyar zuciya tayi sannan ta tashi ta kwanta inda hydar ya nuna mata, bayan ta kwanta ne, hydar yace miye? Tunanin mi kikeyi ne? Samha kamar zatayi kuka tace sahib, hydar yace da Allah manta dashi tunda baya sanki ni ina sanki aikema nasan zaki so hydar ko? Dan gajeran tsaki tayi ba tare data bashi amsa ba, murmushin karfin hali hydar yayi sannan yace Allah ya baki hakuri, daga haka bai sake magana ba, amma har yanzun tana kwance a jikinsa,
Kayan shafa turaruka masu tsada na tashin hankali da daddan kamshi, da duk abinda yasan samha tana so yace ta dauka, haka samha tayi ta daukar kaya kamar hauka, saida ta gama tace ma hydar sunyi haka, hydar yace basuyi ba, ki ƙara, samha tace wallahi haka yamin, haka aka kwashi kayan aka jibga musu a mota, hydar ya biya kudi masu yawan gaske, wanda shi baisan sun fita daga cikin asusun kuɗinshi ba, yayin da samha taji hydar ya bata tausayi ya kashe kudinshi masu yawa saboda ita, duk dan ta kyautatawa mijinta, wanda shi tace ya siya mata yace bazai siya ba,
Tun a mota samha take ma hydar godiya, tare da mishi addu'a Allah ya daidai tsakaninshi da matarshi, yace amin, har suka dawo gida samha bata daina godiya wa hydar ba, bayan sunzo ne yasa aka shigar da kayan dakin samha, bayan ankai ne hydar yayi mata saida safe, itama fatan alkairi tayi mishi,
Samha bayan tafiyar hydar ta fara kiran wayan sahib ta fada mishi abinda hydar yayi mata amma ta doka wayar yafi sau adadin yawan ledan pure water amma sahib bai dauka ba, haka ta hakura ta ajiye wayan sannan ta tattara kayan komai ta ajiyeshi a wurin daya dace, sannan ta haye gado tana cewa sahib dai ya canja hali, yana can da "yar matarsa ya manta da lamarin wata samhar banza can, hmm shida Allah, hydar ne yace mata sahib yayi aure da kudin data siyar da gida ta bashi,
Da safe bayan samha ta gama sallah ta fara kiran sahib, saida yaga dama ya dauka, cikin masifa da hayani yace wai miyene? Nikam bana san jaraba, bana san kwanata, bana san mayata, bana san kwakwa, bana san naci, nace na daina sanki, amma da yake zuciya babu sai wani kirana kikeyi fadi inajinki miye?
Cikin natsuwa samha tace dama zance maka hydar ya siyomin kayan shafa, kada ka siyo idan ka samu hali, cike da bala'i yace dama nace miki zan siya ne? Ai bazan siya ba, kuma ina da kudina ko nace miki bani dashine? Sai kuma mi? Samha tace to maganar m card dina da kuma ahalina yaushe zaka sadani dasu? Mtswwwww yayi sannan yace can keta matsewa mawa, ahalinkin banza ni ina wani ruwana da ahalinki? Ko ahalinki ahalin sahib ne? M card kuma nayar da banza a toilet nayi filoshin, sai mi? Samha tayi shiru, tsaki yayi tare da cewa noncess sannan ya kashe wayanshi,
Dakel samha ta haɗiye miyau saboda tsananin ɓacin rai tare da maimata kalmar noncess? Tou pha, Allah ya sawake, dogon nazari tayi tare da goge ɗan kwallan daya ɗigo mata daga cikin idonta,
Jiki a sanyaye samha ta miƙe, ta nufi ɗakin hydar, tana isa a bakin kofa ta tsaya bata shiga ba, dan hydar yace wallahi idan kare ya sake biyota tazo mishi daki zaiyi mata kaca kaca a saman gadonshi, wannan dalilin yasa samha ta tsaya a bakin kofa tana kuka, tare da kiran sunan hydar,
Hydar dake kwance yace samha miye? Cikin kuka tace kazo ina san ganinka, hydar yace gani ki shigo mana, gyara bakinta tayi batace komai ba, hydar yace samha zo, cikin shashshekar kuka tace ai kace in daina zuwa maka ɗaki zakaman abinda bana zato, hydar yace Ey amma ai cewa nayi sai idan kare ya biyoki, yanxun kuma nine nace kazo dakaina, don haka shigo,
A hankali samha ta shiga ciki tana ci gaba da kuka, shi kuma har yanzun yana kwance yana kallonta har ta iso kusa da gadon tahau saman gadon a hankali harta matsa daf da hydar sannan ta kwanta, ba tare da hydar ya sake kallanta ba yace ya akayi? Samha tace zowa nayi, zowa kikayi mi? Tayi shiru, hydar yace wani abu kike so ne? Samha tace A,a, kawai zanyi bacci anan ne, hydar yace niko da fita zanyi yanzun nan ina da abinyi,
Amma tunda kina san kiyi bacci, bari in jiraki ki gama sai in tafi, gyara kwanciyarsa yayi ya juyo yana kallon samha, jawota yayi kusa dashi yaɗan riƙeta a ƙirjinsa, fuskarshi a saman goshinta yana cewa to kiyi baccin,
Cikin muryar kuka samha tace hydar kayima sahib magana, ya daina abinda yakeyi, cikin yanayi na damuwa tattare da sigar lallashi hydar yace mi sahib ya miki kuma?,, cikin shashshekar kuka samha tace daga nace mishi ka siyomin kayan shafa idan ya samu kudi kada ya siyamin, sai yace min yana kuɗi nine bazai ma abinda nake so ba,
Murmushi hydar yayi wanda bai kawo fuskarshi ba sannan yace ba nace ki daina kiranshi ba? Tunda ya daina sanki kiyi hakuri samha ya kamata ki fuskanci rayuwa ki bude idanuwanki da kyau ki gane mai sanki, tunda sahib ya aureki kullum abubu ƙara burkucewa sukeyi bai damu dake ba ta matarsa yakeyi ko jiya na gansu suna tafi a mota bakiga yanda ya wani bi duk ya rungumeta ba, yana kissing nata bari kiga yanda yayi mata,
A hankali ya daga kanshi daga saman goshin samha ya ɗago mata fuska cikin natsuwa da kwarewa ya haɗa bakinshi da nata, yana mata wani irin salon iskanci a bakinta, wai duk a cikin nunawa yanda sahib yake ma matarshi, haka hydar ya samu yayi ta shashshafe jikin samha yana sauke wani irin lumfashi wanda samha bazata iya gane karatun ba, haka hydar yayi ta iskanci yana jagula samha san ran ranshi, saida ya tabbatar sakonshi yaje inda yake buƙata a jikinshi samha sannan ya saketa, amma badan yaso ba, dan kada samha tace mishi wani abu,
Cikin kuka samha tace saina kasheta, da gudu ta sauka daga saman gado ta fice daga dakin, shidai hydar yana kwance katon banza ya kasa tashi, da gudu samha ta isa dakinta tana kuka, tana zuwa toilet ta shiga tayi wanka, a gaggauce ta fito ta shirya cikin wata haɗaɗɗiyar baƙar riga, ta yana gyale a saman kanta,
Tayi matukar kyau sosai, jaka da takalmi goldcoulour ne, dan shine kwalliyar jikin bakin rigar, saida ta gama shirinta tsaff sannan tayi kicin da gudu, wata shareriyar wuka ta ɗauka tana cewa yau saina ci uwarki da kika kwacemin mijina, niko nace waye yace da wuka ake kishi?
Da gudu ta fita daga farlon da shamsu ta fara cin karo, yace hajiya ina zakije ne? Samha tace kasan gidan da sahib ya ajiye matarsa ne? Abin dariya yaso ya bawa shamsu amma saiya basar yace a,a ranki ya dade, kallon Alale tayi sannan tace yawwa kai abokin sahib ne don Allah a ina yake zama da matarshi? Dariya Alale yayi sosai sannan yace nikam ban sani ba, amma mai gida ya san gidan dan ko shekaran jiya yaje,
Samha tace to ai kaima ka sani tunda kaine kake kaishi duk inda zaije, Alale yace gaskiya kam haka ne, amma ranar baije dani ba, dashi da matarshi sukaje gidan, samha tace ina karnukan suke ne? Alale yace suna baya an dauresu ai dama da daddare ake sakinsu, samha tace yawwa ngd, tana faɗin haka tayi gaba,
Tafiya mai nisa sosai tsakanin get na farko bare taje wanda zai sadata da get din da zai fitar da ita gidan gaba daya, tana fara tafiya shamsu ya kira hydar ya faɗamishi, da sauri ya tashi ya matsa jikin window ya fara kiran sunanta, amma samha tayi kamar bataji yana magana ba,
Hydar yace samha bakiji ina miki magana ko? Ba nace kizo ina kiranki ba? Nanma ƙara basarwa tayi, hydar yace to shikenan kije ɗin kuma duk abinda yayi miki kada ki kara faɗamin tunda banda amfani ashe kinsan zaki iya daukan hukunci da hannunki amma kika faɗamin ba komai yayi miki kyau duk abinda kikayi daidai dakene wallahi,
Daga inda take tsaye cikin kuka zatayi magana hydar yace bana san kiyi magana anan zoki fadamin inji miye yake damunki? Tahowa samha tayi tazo ta wuce ta gabansu shamsu tayi ciki, kafin ta shiga har hydar ya fito daga dakinshi ya sauko farlo,
A sukwane hydar ya isa kusa da samha yaja hannuta suka zauna saman kujera, bayan sun zauna ne hydar yace ya akayi ne? Cikin yanayi na ɓacin rai samha tace zuwa zanyi kawai in kashe matar sahib, idanuwa hydar ya zaro sosai sannan yace kinyi hauka ne?
Cikin kuka samha tace ko daya banyi hauka ba, hasalima nafi da hankali, dan ban hada soyayyar sahib da kowa ba a zuciyata, zan iyayin komai akan sahib, hydar yace nasan irin yanda kikeji a zuciyarki samha, taɓe bakinsa yayi sannan yaci gaba da cewa nima irin abinda kikeji haka nakeji harma nawa yafi naki, amma abinda nakeso dake shine kiyi ma sahib uziri harya gama amarcinsa da matarsa, zai nemeki ne kinji?
Samha tace to, ansar wukar hannunta yayi yana cewa ki daina faɗa da wuƙa wannan halin mutane banza ne kinji? Samha tace tom, hydar yayi ta mata nasiha, tare da nuna mata girma irin na hakuri samha tace to zan kwatanta amma gaskiya na rike so sosai, murmushi hydar yayi tare da cewa kuma kina da kalar hakuri don Allah mantar da maganar sahib,
Samha tace haba hydar kada ka manta shi sirrin zuciya yarda ce, harshe ya furta kalamar so kauna ce bana tunanin sahib zai gujeni amma tunda kace in mishi uziri na mishi, sahib ya riga ya zauna sosai a zuciyana, kaga ya kamata ya rike na rike ko? Duk sai muyiwa junanmu adalci, hydar yace gaskiya, samha tace amma yana neman saɓa alkawari bayan yasan ruhi, raina, jikina duk sun laminta dashi, zani faɗa sanshi ya harbi zuciyata ya hana zuciyana ta huta, tunda ya yadda a da naji dadi, amma yanxun ya daina so na,
Shiru hydar yayi dan baisan amsar da zai bawa samha ba, haka tayi ta kwatantawa hydar girma da darajar sahib a cikin babban birnin zuciyarta, shidai shiru yayi bai sake magana ba, ita ta gaji da surutun ta tashi tabar farlon, da kallo hydar ya bita harta haye sama yana kallonta saida ya daina hangota sannan yayi ajiyar zuciya tare da lumshe idanuwanshi,
Da marece hydar yayi ma samha waya tayi wanka yana zuwa, shima wanka yayi yasa kayan wasan kerket a jikinsa, ya dauki na samha, irin dayane da nashi, ya nufi dakin samha, a daidai lokacin data fito daga wanka, sallama hydar tare da shiga ciki, da sauri samha ta nufi inda hijabinta take zata dauka hydar ya matsa da sauri ya riƙe hijabin,
Samha tace bani mana, hydar yace bazan baki ba, miya sa baza ka bani ba? Jin dadi ina san kawai basai kin wani saka hijabi ba, maza maza ki shirya kinga kayankin iri daya da nawa ne, sandar wasan kerket a hannunsa, ya ajiye kayan a gefen gado sannan shima ya zauna yana ma samha wani irin kallo mai wahalar fassarawa,
Turo baki samha tayi sannan ta fara shafa mai, duk abinda takeyi hydar yayi mata ƙuri da idanuwa yana kallonta, harta gama, hydar yace shafa kwalli, samha tace ni bana san kwalli yace ni kuma ina so saboda haka sai an shafashi wallahi, murmushi samha tayi sannan tace nidai zafi yake min a ido, hydar yace kawo kwallin in miki addu,a idan na shafa miki zakiji babu wani zafi,
Babu gardama ta dauka takai mishi, zaro tsinken kwallin yayi yana motsa baki, sannan ya saka abin kwallin a bakinshi yana cewa matso ki gani, tsigunnawa tayi kasa a gabanshi ta dora hannunta saman jikinshi ta ɗaga fuskarta tana kallon hydar shi kuma ya dora hannunshi saman kanta ya shafa mata kwallin, murmushi yayi bayan ya gama sannan yace kinga yanda kikayi kyau? Ya karasa maganar yana kashe mata idanuwanshi, yana lumshesu yana wani bude su,
Tashi hydar yayi ya kama hannun samha yana cewa taso ki gani, tashi samha tayi hydar ya matsa da ita a jikin mirrow yace hajiyata ya kika ganki ne? Murmushi samha tayi sannan tace kuma wallahi yamin kyau kuma babu wani zafi ta karasa maganar tana kallon kwayar idon hydar,
Hydar yace yarinya an gaya miki niɗin na wasa ne? Samha tace gaskiya kai babbane, hydar yace sosai ma, saka kayan muje, samha tace to juya, murmushi hydar yayi sannan ya juya, yanda yayi juyin yasa samha tayi dariya sosai, sannan tace waika auta ne a gidanku? Ba tare daya juyo ba yace mi kika gani ne? Samha tace kai sakataccene na lura, hydar yace bakisan ma na iya sakata ba dan bama kwana wuri daya da kinga yanda ake sakata, yanda yayi maganar yasa samha tsikar jikinta tayi wani yam,
Shiru tayi, hydar kuma dariya yayi sannan yace kinyi shiru, bata ƙara magana ba, murmushi hydar yayi sannan yace kin gama ne in juyo? Samha tace Ey, juyowa yayi yana kallon samha sannan yace yarinya ki bari mu kwana a daki ɗaya kiga yanda nakeyi bacci da matata,
Samha tace A, a, bana bukata, murmushi yayi sannan ya dauki fesincap ya saka mata a kanta yana mata wani irin kallo, murmushi samha tayi data ga kanta a madubi tace kai gaskiya ina da kyau sosai gaskiya na haɗu da yawa, kallon hydar tayi sannan tace nayi kyau? Hydar yace sosai ma, aike din haɗaɗɗiya ne, sandar wasan kerket ya mika mata ansa tayi ta rike sannan yace muje,
Shine a gaba samha tana baya sai rawa takeyi tana tsalle, saida ta kara kallonta a madubi sannan ta fita da gudu, a waje babu kowa, da sauri take bin bayan hydar cikin nishaɗi da jin ta kamar wata sabuwa, wasa hydar yakeyi da kwallon kerket a hannunsa,
A filin wasan hydar ya nunawa samha wurinta yace anan zaki tsaya nine zan rika tullo miki kwallon, kinga anan ramin zaki jefa ta, samha sai murmushi takeyi, tace tom,
Gyara riƙon sandar tayi sosai tana ɗan duƙawa kamar yanda hydar ya nuna mata, sannan tace muje na shirya, hydar yace Aha, sai yaja baya yake tillo kwallon samha saita halbata da sandar hannunta tana dariya sai tsalle takeyi tana yar rawa, haka suke wasansu cikin nishaɗi da jin daɗi, saida samha tace ta gaji dan kanta, sannan hydar yace to, zama tayi a wurin tana maida nunfashi,
Hydar yace bara a dauko mashin shima muɗan ɗana ko? Ya ƙarasa maganar yana ɗaga ma samha gira, murmushi samha tayi hydar ya wuce daga wurin dan dauko mashin, tunda samha ta hangoshi ya taho da mashin ɗin ta tashi tsaye, a ranta tace wallahi hydar yana da kyau sosai, gashi dan gayu kuma mashin ɗin ya masa kyau sosai, murmushi samha tayi sannan ta lumshe idanuwanta ta fara ayyano sahib a saman mashin ɗin, idonta ya kawo hawaye tace ni dama da sahib ne a wannan sansayan marencen nasan nishaɗin daya fi haka,
Har hydar ya iso wurin samha bata san yazo ba, haka yayi ta zagayata da mashin din amma ina samha ta lula duniyar bege, tsayuwa hydar yayi da mashin ɗin sannan ya murzashi da ƙarfi buuuuuuu, bunbunbunn, shine yasa samha ta dawo daga tunani, murmushi hydar yayi sannan yace taho mana, yana miƙa hannunshi,
Jiki babu kwari tayi wurin hydar yana dan tafiya da mashin ɗin a hankali samha tayi wurin ta taka zata haye baya, hydar ya jawota da hannu ɗaya ya zagayo da ita gaba, taba kan mashin ɗin baya bayanta kuma yana kan gaban mashin ɗin baya, kwaciya saman jikinta hydar yayi yana cewa kukanmi kikeyi ne? Zatayi magana hydar yakai bakinshi wurin nata ya sun bace ta, tare da cewa ki daina yawan kuka kinji? Samha tace tom,
Tafiya da mashin din hydar ya farayi samha tace ni zan koma baya, hydar yace A, a, yau a haka zamuyi, samha tace nidai nafisan baya, hydar yace to sauka kije bayan, sauka samha tayi ta koma baya tahau, miƙewa tsaye tayi saman mashin ɗin ta dafa kafaɗar hydar, haka yayi ta zagayawa, shima saida tace to yayi haka muje gida, hydar yace to
A bakin kofar farlo yaci burki da mashin din sannan samha ta dire, kallon hydar tayi tana cewa to faɗamin me zamuci ne? Hydar yace nikam banajin yunwa a daidai lokacin da yake saukowa daga saman mashin din, yaci gaba da cewa ke kuma mi zakici ne? Samha tace umm nima dai kam bana jin yunwa, hydar yace to babu damuwa muje,
Suna shiga samha tace saida safe, hydar yace Allah ya kaimu, tana zuwa daki samha ta kulle kofarta kamar yanda ta saba, wanka ta farayi tare ɗauro alwallah, tana fitowa kayanta ta saka ta fara sallah magirib, tana zaune a wurin har aka kira isha'i tayi tare da addu'oi sannan ta tashi a wurin,
Bakin gado taje ta zauna tare da jawo filo ta ɗora saman cinyarta, ta dora hannuwanta saman pillow ɗin ta zabga tagumi, tunanin halin sahib takeyi,
_Fadawa hydar danni ina da abinda nakeyi banda lokacinki,_
_Banda number hydar ai_
_Mtsww zan turo miki yanzun_
Ajiyar zuciya samha tayi tare da kwantawa saman gadon a hankali,
_Hydar zan mutu_
_Subahanallah miye yasa zaki mutu? Kuma wace ce take magana ne?_
_Nice, kece wa? Ni samha! Wayyo samha sannu ganinan zuwa bana gida ne na fita amma ina hanya kiyi hakuri kinji?_
Gyara kwanciya samha tayi tare da sauke ajiyar zuciya,
_Ka taho da sahib, ki zaɓi ɗaya ni zanzo ko sahib? Sahib yazo,_
_ina uzirina kinje kin wani matsa na taho ni ina wani ruwana da ciwon cikin ki? Anƙi ayi hakurin, ciwon cikinkin banza! kin wani bi kinsa an tadoni daga wuri mai nisa to ba sannu ba, kuma zan tafi bari ki sake sa a kirani kiga yanda zan miki lullusar fitar hayyaci,_
Lallai sahib ka zama ɗan iska wallahi, tayi kwafa,
_Wayyo sannu samha, Hydar sahib ya daina so na, kamishi magana banajin dadin abinda yakemin don Allah_
Lallai sahib ƙiriƙiri ya canja hali to Allah ya shirye ka,
_Ahalinkin banza, ahalinki ahalina ne? M card na yarda banza a toilet nayi puloshin_
Haka dai tayi ta tunane tunane, har bacci ya dauketa,
Hydar kuwa tafiyar samha fita yayi ya nufi masallaci, saida sukayi isha'i sannan ya dawo, shima bai zauna farlon ba yayi ɗakinsa dan hutama rayuwarsa,
Da safe saida samha tayi break sannan ta koma ɗaki tayi wanka, ta shirya cikin riga da sikat na atamfa, tayi kyau sosai, wayarta ta ɗauka tare da cewa yau alo tsiya alo danja a gidan nan, koni ko sahib dan yau duk abinda zai faru saidai ya faru dan yau ɗin nan sai an sadani da kawu, idan kuwa ba haka ba babu zaman lafiya a gidan nan dashi da munafukar matarsa, niko nace ina ruwan matarsa? 🤔
Kiran wayar ta farayi, hydar daya fito wanka jin wayar sahib yana ringing yasashi cewa tou pha Allah dai ya sawake wannan fitina, saidai ta kira kusan sau takwas sannan ya dauka ya fara magana cikin yanayin bacci, ya fara da cewa mayasatu ya akayi ne?
Samha tace nine mayasatu sahib? Tou akwai wata bayan ke? Banda shirme da sakarci kin tasar min madam daga bacci bakisan idan muna bacci ba'a kiran waya ba? Swry my wife mayasatu ce "yar anace kinsan bata da zuciya ne, yayi kamar yana magana da mace a kusa dashi,
Hydar yaci gaba da cewa swry don Allah kada ki wani damu bakiga nafi ji dake ba shi yasa kullum nake kwana a wurinki? Kai haba kada ki wani damu barni zanyi maganinta, don Allah kiyi hakuri muah 💋 samha tace na ci uwar matar dan ubanta ta karasa maganar tana kuka, sahib yace ke ahir ɗinki akan matata ta ina iya somar dake mtsww ya kashe wayan shi,
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un samha tace, tare da faɗar an yanka ta tashi, lallai yau a gidan akwai kutumar babban biredi da botar, nice mayasatu? Nice "yar anace? Wani irin ihu samha tayi tare da cewa idan na yadda Allah ya babbakani, nice ba'aso itace ake so ake kwana a gidanta to bazan yadda ba,
Don Allah kuyi hakuri da wannan wallahi banda chargy ne,
*Jameela Musa* _Meelat Musa ce_
[05/04 4:46 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*_Kowa kukan gidansu yakeji, dan haka nima na gidanmu nake ji, jinjina gareku fatan alkairi addu'ar samun nasara ci gaba, hazaka lafiya da basira, alkairin Allah an daddanku BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, mutane masu mutunci masu kara masu bartaba junansu da sanin darajar wanda suke tare dashi, hakika nikam naji daɗi kuma nayi dace daku Allah ubangiji ya barmu tare Allah ya kara haɗa kanmu ubangiji ya kara kwararo ruwan basira acikin ƙoƙon kawunamu baki ɗaya_*
*SO*
*MUGUN WASA*
_Dedicated to_👇🏻
_Ramlat Abdurahman real mai dambu_
*53-55*
Miye banda shi miye namiji yake bukata a jikin mace wanda banda shi? Jikin mirow ta matsa tare da gogen hawayen idonta, sannan ta ƙarayiwa kanta kyakkyawan kallo,
Kwafa tayi sannan tace lallai wai kamarni sahib zai wulaƙanta? A gabana yake wa wata jaka kiss ko tsoron Allah bayayi, karshe ma jakar matar bata kaini kyau ba,
Da sauri ta fita daga ɗakin tayi kasa, a farlo taje tayi zaune sai kuka takeyi tana jiran fitowar hydar,
Hydar da sauri ya fito dan yabar gida tun kafin samha ta fito,
Yana ƙoƙarin saukowa yaga samha zaune, da sauri yaja da baya ya koma ta baya da gudu ya fice,
Saida ya kusa fita ya tsaya ya sauke ajiyar zuciya ya saita kanshi tare da tattaro ajinshi sannan ya ida fita,
Kallon Alale yayi tare da cewa kaje ka ɗauki samha kace mata kasan gidan sahib, kuje gidan Al' ameen da ita nayi ma matar sa bayanin komai, kaje maza kace ta shirya ku tafi,
Alale yace to, da sauri Alale yabar wurin ya nufo farlo, da sallama ya shiga, samha ta ansa ba tare data kalli inda Alale yake ba,
Cikin girmamawa Alale yace ranki ya dade mai gida yace inkaiki gidan sahib,
Samha tace ina yake hydar din ne? Alale yace zai fita ne, samha tace kaje kace mishi ina san ganinsa,
Alale yace gaskiya kiyi hakuri mai gida yau zaiyi tafiya ne, idanuwa samha ta zaro sosai sannan tace ina zaije ne?
Alale yace zaije *_Germany_* ne ganin likita, da sauri samha ta tashi tsaye tace da gaske? Alale yace wallahi kuwa, samha tace amma miyasa bai faɗamin ba?
Alale yace nima ban sani ba, bata sake magana ba, ta fita daga farlon da gudu, lokacin data isa wurin saidai mota ta baya ta gani domin duka motocin sun gama fita daga get din farko,
Ƙara rugawa tayi da gudu, tana kiran sunan hydar amma hydar bayajin samha, tsayuwa tayi a wurin tana kara fashewa da kuka,
Tambayar kanta takeyi mi tayi ma hydar zaiyi tafiya bazai mata bankwana ba? Ko shima yanzun ya daina tausayinta ne? Ƙara fashewa tayi da kuka sosai,
Alale dai yana tsaye daga nesa da ita yana kallonta, cikin kuka samha ta taho, ba tare da tayi ma Alale magana ba ta wuce ta shige ciki,
Da gudu mai dawo da mutum baya samha ta haye sama, tana zuwa dakinta da gudu ta isa inda wayarta take ta dauka ta fara kiran wayan hydar, amma a kashe wayar,
Samha tace hydar miyasa zaka min haka ne? Bayan kasan kai kaɗai nake gani inji daɗi kaine kake kwantar min da hankali saika tafi ka barni kuma babu sallama mi nayi maka wanda yayi zafi haka?
Cikin kuka samha ta tashi tayi ɗakin hydar, tana zuwa ɗakin tunda ta shiga taga wata zungureriyar farar takarda saman gadon,
Da sauri ta isa wurin gadon, takai hannunta ta ɗauki zungureriyar takardar ta fara dubawa,
_Samha barka da safiya, da fatan kin tashi lafiya? Ya hakuri da hydar & sahib? Sannu kinafa kokari sosai, lallai sai yanzun na yadda ke babbar jarumace 👍🏻, da banda kike jaruma da yanzun sahib yasa miki ciwon zuciya kema, nikam kinga tawa zuciyar rauni ne da ita, kuma ta dalilin san danake ma matata na kamu da ciwon zuciya, lallai kina da zuciya mai kafiya samha, zuciyar hydar kuma rauni gareta, zuciyar sahib kuma tana da san kai, to idan aka haɗa, kafiya, rauni + sankai kai, ƙarshe zai haifar da mi? Ki fiddo min wannan ansar kafin in dawo,_
_Ga Alale nan na bar miki duk inda zakije zai kaiki, idan kina san kuɗi ki rika dauka a inda kika ga ina ɗaukan kuɗi kinji? Naje ganin likita bazan dawo ba sai bayan wata ukku, fatan zaki zama lafiya,_
A hankali samha ta kwanta saman gado, tare cewa, mi hydar yake nufi? Ƙanƙance idanuwanta tayi tare da cije leɓonta na ƙasa,
_Zuciyar samha tana da kafiya_
_Zuciyar hydar kuma tana da rauni_
_Sahib kuma zuciyarsa tana san kai_
Ajiyar zuciya samha tayi tare da cewa lallai akwai alamar tambaya a maganar hydar,
_Kafiya, rauni + san kai, ki fiddo ansa kafin in dawo_
Lallai,
_Kafiya_
_Rauni_ = _{ Nadama, ko rashin adalci }_
_Sankai_
Tashi tayi zauna tare da cewa lallai ƙarshen kafiya, nadama ne, karshen san kai shima nadama ne, karshen rauni ma zai iya zama kayi nadama idan har kayi rauni akan abinda kasan bazai yuwu ba,
To lallai dai, wannan amsa itace, nadama,
_Kafiya_
_Rauni_ = _{ Nadama }_
_San kai_
To waye zaiyi nadama tsakanin sahib samha & hydar?
Dogon nazari samha tayi tare da cewa lallai a cikinmu ina ganin wanda zaiyi nadama,
Nine dani da sahib, saboda ina da kafiya shi kuma sahib yana da san kai, to miye zai faru wanda zamuyi nadama? Me hydar yake nufi ne?
Lallai ya zamar min dole in gano dalilin dazaisa inyi nadama, tashi tayi ta shiga toilet ɗin hydar tayi wanka, harta fito nazarin abinda zaisa ta tayi nadama takeyi,
Saida ta shirya sannan ta ɗauko kaya a inda hydar yake ɗauko mata ta saka, tare da cewa Allah ya kaimu gobe lafiya, maganar Alale ta fara tunowa,
_Ranki ya dade mai gida yace inkaiki gidan sahib_
To a gidan sahib zanyi nadama ne? Kai bazai yuwuba nikam bana nadama saidai hydar da sahib zaiyi nadama, dan idan wani abu ya sameni a gidan sahib hukuma zata hukunta su,
Lallai koma miye a gidan sahib zanji, Allah ya kaimu gobe, murmushi samha tayi tare da cewa ƙalubale gareki matar sahib,
Amma gaskiya sankai rashin adalci ne, hmm mu hadu dai in gani da idona,
Yinin ranar nan samha wasi wasi tayi, tayi a zuciyarta, da kuma marecen jiya yanda ta kasance tsakaninta da hydar yayi ta mata yawo a rai, yaukam samha ta kasa tabuka komai ko abincin data girka kasa ci tayi dan ta saba ita da hydar yana bata a baki, tayi zaune a dirning area ta dora kanta saman dirning sai kuka takeyi,
Shi kuwa hydar bayan tafiyan Alale babu abinda suka tsaya yi sai shiga moto, suka fara fita daga gidan, shine fa samha tana fitowa ƙallin motar ɗaya ta gani, su hydar kuma suka ibi hanya sai birnin tarayya Abuja,
Yaukam samha bacci babu wani daɗi tayi shi har gari ya waye, tana tashi bayan tayi sallah ta kara koma ta kwanta,
Saida ta gaji dan kanta ta farka, tana farkawa toilet ta shiga ta wanke fuskarta da bakinta sannan ta fito, ta nufi BQ a kofar dakin Alale ta tsaya tana cewa zan shirya yanzun, saika shirya kafin in fito,
Alale yace ranki ya dade da kanki? Samha tace Ey, kuma kayi sauri, yace an gama matar Oga, da sauri ya kama bakinshi tare da cewa Oga sahib ikon Allah,
Ba tare da samha tayi magana ba ta wuce, Alale yanajin fitarta ya fara kiran wayar Al' Ameen ya fada mishi cewa gasunan zuwa yanzun insha Allah,
Al' Ameen yace Allah yasa kuzo lafiya, Alale ya amsa da Amin tare da kashe wayanshi,
Samha kuwa saida tayi break sannan taje tayi wanka, ta shirya cikin wani lafiyayyan material mai kyau da tsada, gyale da jaka da takalmi wasu kyau wanda suka dace da material ɗin data saka, tayi matukar kyau sosai,
Tana gamawa ta sauko, kicin ta nufa ta ɗauki lafiyayar wuƙarta, harta ɗaga rigarta zata soka ta, ta tuno,
_Ki daina faɗa da wuƙa wannan haline na mutanen banza_
Maganar hydar, sai kuma sakonsa na cikin wasiƙar daya bar mata,
_Zuciyar samha tana da kafiya_
Ajiyan zuciya samha tayi tare da ajiye wuƙan, da sauri ta fita daga kching in ta fice waje,
Tana fitowa da sauri Alale ya buɗe mata mota, umm su samha aka wani kashe a gidan baya, Alale ya rufe mata sannan ya zagaya mazaunin driver ya shiga yaja suka ɓace daga wurin kamar walƙiya,
Tafiya sukeyi babu mai magana, dama ina ruwanka da driver, saida sukayi tafiya mai nisa sosai sannan samha tace am Alale don Allah ka biya dani ta gidan kawu,
Alale yace gaskiya kiyi hakuri mai gida baice min inje wani wuri ba, gidan sahib kaɗai yace, samha tace ina ruwana da mai gida baice ba,
Kayi yanda nace mana, Alale yace kiyi hakuri wallahi hakan bazai yuwu ba,
Dan hydar yajawa Alale kunne sosai akan daga ba gidan Al' Ameen ba kada yaje da ita ko ina idan kuwa ba haka akwai babban matsala,
Samha tace zamuje ko kuwa? Alale yace don Allah kiyi hakuri wallahi idan ba haka ba zaki yanke min abincina, samha tace to aini duk abinda nake so shine hydar yakemin kai miyasa bazakamin yanda ya saba ba?
Alale yace saboda ni ba hydar bane, ni yaronsa ne a ƙasansa nake kuma kinsan saɓawa ubangidanka rashin amana ne tunda baya nan kiyi hakuri,
Kwafa samha tayi daga haka bata sake magana ba, har suka isa gidan Al' Ameen,
A bakin get Alale ya tsaya tare dayin horn, da sauri mai gadi ya buɗe musu ganin motar hydar ne, dan shine ubangidan Al' Ameen, ya fara kai gaisuwa, Alale yace malam sani ya aiki?
Malam sani yace Alhamdulillah yau ina mai gidan namu ne? Alale yace yaje ganin likita ne, malam sani yace Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana Alale yace Amin, malam sani yace wannan itace Amaryar mai gida ne?
Murmushi Alale yayi tare da jan motar yana cewa um, dan kada Malam sani ya ɓallo aiki, banda jinjina kai babu abinda samha takeyi tare da karewa gidan sahib kallo lallai namiji munafiki ne,
Wannan ƙatoton gidan ya gina? Ga wasu jibga jibgan motoci mai lumfashi na tashin hankali a daidai lokacin da Alale ya fito ya buɗewa samha mota,
Kallon Alale samha tayi tare da cewa wannan ƙattin gwangwanayen na waye? Wai motocin sune gwangwani, Alale yace to na sahib ne gidanma nashi ne,
Haka samha ta ƙara riƙe jakarta sosai tana karewa gidan kallo ya haɗu ta ko ina, wato da sahib yace mata saiya gama gina gidansa zasu dawo shine yana gamawa yayi aure abunshi, wani baƙin ciki taji ta tokare mata zuciya kamar magunar ruwa ta toshe, Murmushi samha tayi tare da tunanin,
_Zuciyar sahib tana da sankai_
Murmushin takaici samha tayi tare cewa lallai sahib akwai san kai, Alale yace muje ciki, murmushin karfin hali samha tayi sannan tabi bayan Alale suka shiga ciki,
A farlo Alale yayi ma samha mazauni saman kujera ta wani kashe tare da ɗaukan ƙafa ɗaya saman ɗaya ta ɗora tana ƙara bin ƙaton farlon da kallo, hotunan sahib ne yana cikin yanayin farin ciki, ga kuma wasu daga kusurwar farlon wanda duk ɗaya yakai tsawon samha, sahib ne da wanda take tunanin itace matarsa,
Wani irin gurnani samha tayi tare da tashi tayi ta ɓarar da hotunan, yanda takeyin abun ya bawa Alale dariya dan haka ya fita daga farlon da sauri, ya fara kiran wayar hydar,
Haka tayi ta hauka tana zubar da hotunan na sama dana ƙasa, matar Al' Ameen ta fito da sauri tare da cewa haba mayasatu? Sai kawai kizo gidana kiyi ta hauka babu ji babu gani?
Samha tace kece wace jaka ke kuma? Haba hajiya samha dani dake ai kinsan waye jaki, nan fa gidana ne, gidan aurena ne, mijina yake sona, shi yasa ya kashe makuɗan kuɗaɗe ya ƙayata mana farlonmu da kujeru na alfarma, haka ya ware zunzurutun kuɗaɗe yayi mana manyan hotuna ya ajiye a farlo dan mu riƙa ganin juna munajin nishaɗi,
Shine dan ɗanyen iskanci kika zo kika fasa ko? Samha tace na fasa dan uwarki kuma yanda na fasa hotunan nan haka zan fasa miki kwakwalwar kanki baki san ni ɗaya nake da mijina ba? Wane ɗan iska yasa kika auranmin miji?
Zama matar tayi saman kujera tare da cewa, abinda yasa na aureshi saboda ina sansa yana so na, shi yasa ya gina gidanshi ya kawoni ya adanani a ciki, ke kuma ya ɗaukeki yakaiki gidan hydar domin kiyi mishi shara da wanke wanke,
Kuma hydar yayi miki babban halakci amma kinƙi ki gode masa, kowa gudunki yakeyi amma hydar ya raɓaki cikin rayuwarsa, sahib ya gujeki a daidai lokacin da kike gaɓar mararin namiji a kusa da ke,
Ya gaya miki maganganu masu muni da ɗaci amma da yake baki da zuciya kanki yana hayaƙin yarinta kin kasa fahimtar waye yake sanki,
Banda Allah ya baki aron dama samha ke harkinkai matsayin zama da hydar a inuwa ɗaya? Samha tace da Allah rufemin baki kada inci kutumar kan babbar biredi da bota, matar Al' Ameen tace bazanyi ba,
Tashi samha tayi taje wurinta tare da gagara mata lafiyayyin marirrika, murmushi tayi tare da dafe wurin a ranta tace kinci albarkacin hydar, a bayyane kuma cewa tayi,
Naji ba komai, nidai mijina yana so na, ke kuma baya sanki, ta kece da dariya mai cin rai tayi ma samha, tare da cewa a fitar min daga gida kuma daga yau na sake ganinki gidan nan zakiga yanda zan zazzaga miki fetir in cinna miki ashana,
Da samha da Surayya matar Al'Ameen haka suka caku kowa yana faɗawa kowa magana mai zafi, Alale ne ya shigo farlon yana cewa ranki ya dade kiyi hakuri, kizo muje ki bari sai mai gida ya dawo zaiyi miki maganinsu,
Haka dai Alale ya lallaɓa samha suka tafi, fitarsu matar Al'Ameen ta zauna tare da sauke ajiyan zuciya tace kai lallai hydar ya jajibo ma kanshi jaraba, wannan yarinya da masifa take, danaga tana da saukin hali dana warware mata komai,
Koda suka koma gida samha banda mita babu abinda take, sai tuno maganganun matar sahib takeyi, wai itace mayasatu, dan tsabagen wulaƙanci har matarsa ya faɗa mawa itane mayasatu,
Haka dai ta gaji da jarabarta tayi shiru, tunda bata da mai bata hakuri, sai yau tasan hydar yana da amfani, lallai da hydar yana nan dayaci mata uwar sahib dashi da wannan guntuwar matar banzan sa,
Tsoki samha tayi tare da cewa kuma matar itama "yar gayu ce, kana ganinta kasan hutu ya zauna mata,
Toko dan hydar yaga matar sahib yasa yace in riƙa gayu, ko nima sahib zaiso ni?
Lallai hydar yana so na, wato baya san in zauna a matsala shi yasa yake cemin in gyara,
Haka dai rayuwar samha taci gaba da tafiya a gidan hydar, addu'arta Allah ya dawo da hydar lafiya yaci mata uwar sahib,
Samha duk ta takura gaba ɗaya batajin daɗin zaman gidan, kuma har yanzu hydar yaki ya ƙirata, bare ta faɗa mishi abinda matar sahib tayi mata,
Rayuwarta bata ɗakin hydar bata ɗakinta, haka zataje tayi kwanciyarta a ɗakinshi tayi ta tunane tuna ne, lallai sabon lamari ku tsaya kuji tunanin samha,
Kwance take a saman gado idonta yana kallon sama,
_Hydar yayi miki babban halakci amma kinƙi ki gode masa, kowa gudunki yakeyi amma hydar ya raɓaki a cikin rayuwarsa, sahib ya gujeki a daidai lokacin da kike gaɓar mararin namiji a kusa dake!_
Mi hakan yake nufi ne? Kota na nufin ni "yar iska ne? Mtswww,
_Naji ba komai nidai mijina yana so na, ke kuma baya sanki,_
_Banda Allah ya baki aron dama ke harkinkai matsayin zama da hydar a inuwa ɗaya?_
Ajiyan zuciya samha tayi tare da cewa lallai hydar ba sa'ar yara bane, tunda duk abinda mace take nema wurin namiji hydar yana dashi 100% saidai abinda baza a rasa ba, dan mutum 9 ne bai cika goma ba, suffanto hydar samha ta farayi, ta dade tana tunaninta daga baya tace lallai fa hydar ɗan gayene,
Yana da kyau mai ɗaukar hankali, kuma idanuwanshi ma suma suna da kyau, suna birgewa idan yayi kallo dasu, murmushi hydar ta tuno yanda yakeyi sai beaty point nasa ya fito,
Haka dai samha tayi ta nazari tare da tunanin hydar a ranta, dan yanzun yanda take tunanin hydar bata tunanin sahib haka, ga lokacin da hydar ya iba zaiyi a germany harya wuce shi sosai,
Ita inda zata samu number hydar tayi waya dashi take nema amma bata samu ba, kuma tayi ma Alale magana yace baida shi, kuma tace yakaita zataje wani wuri yace mota ta lalace,
Gaba ɗaya zaman gida ya isheta kullum bata ɗakin hydar bata ɗakinta bata filin wasansu, sai taje inda aka ajiye mashin tahau ta zauna,tayi ta tunanin marencen su daren tafiyan hydar,
Yauma tsaye take a gaban Alale wai yakaita gidan matar hydar, idanuwa Alale ya zaro tare da cewa ranki ya daɗe me zakiyi a can ne?
Murmushi samha tayi sannan tace kawai zanje ne, Alale yace to wallahi ki rufa ma kanki asiri dan bata san mai gida idan ta ganki zata miki rashin mutunci, haka dai Alale yayi ta ƙaƙuba ƙarya yana ɗirkakawa samha, akan matar hydar,
Wanda cikin natsuwa samha ta gano irin halinta ɗaya da matar hydar amma banbancinsu ita tana san sahib, amma ita matar hydar yana santa ita kuma bata san hydar, murmushi samha tayi tare da darkakawa maganar Alale ❓
Murmushi samha tayi sosai dan ta lura Alale yana da zafin surutu, kallonshi tayi sannan tace to ya sunan matar hydar? Daburcewa yayi dan baisan amsar da zai bawa samha ba,
Samha tace kayi shiru Alale yace kai gaskiya na manta sunan ta, samha tace bakaje ɗaurin aure ba? Alale yace naje mana, samha tace tuno ranar mana,
Dukan da aka kaiwa samha yasa ta saurin miƙewa tsaye, Asma'u ce ta cakume wuyan samha tare dakai mata duka summun bukumun, Alale yace ke Asma'u kinsan abinda kike kuwa?
Samha ganin zata daku da yawa yasa ta fara maida martali, haka sukaci gaba da cakuwa a gaban Alale yana kokarin rabasu amma samha tayi ma Asma'u kyakkyawan riko, dukanta kawai samha takeyi duk ina na jikinta, harsai data cirewa Asma'u haƙori ɗaya,
Asma'u ganin haƙorinta a ƙasa yasa ta yin kukan kura tare da cewa kutumar duma du, ni kika cirewa hakori ɗaya? Zakici kutumar ubanki dake da hydar ɗin zanje in faɗawa dadyna sai zakici uwarki ɓarauniyar banza,
Samha tace dadynkin banza shima idan yazo zanci uwarsa in cire haƙorin banza kamar yanda na cire naki, dadyn zaki daka dan uwarki? Samha tace yo bazan daki banza ba sakara "yar gidan mai dattin hula,
Dadyna ne mai dattin hula? Zaki raina kanki banza "yar wasan caca, samha tace naji ke kuma kwartuwa, nice kwartuwar? Tsoki samha tayi sannan tabar wurin,
Nan Asma'u ta tsaya tayi ta zungurawa uwar samha zangi, saida ta gaji dan kanta sannan tayi tafiyarta,
Tana tafiya Alale ya kira hydar tare da yi masa ya hanya? Hydar yace sun kusa ƙarasowa amma idan ya shigo yana da meeting,
Alale yace to ranka ya dade ko in taho in tara ne? Sai mu taho gida baki ɗaya? Hydar yace A, a, fatan alkairi Alale yayi masa sannan ya kashe wayanshi,
Ita kuwa samha tana zuwa ɗaki saida tasha kukanta sosai tare da tambayar kanta ita kuma wannan wace ce ita? Kuma mi nayi mata tayi min duka? Mi dadynta zaimin dani da hydar?
Mtsww shirmen banza, tashi tayi taje tayi wankanta ta haye gado tayi kwanciyarta,
Hydar kuwa suna isowa saida yayi abinda zaiyi ya gama, sannan sukayo gida, zuciyar hydar tana harbawa, yana shauƙi zaiga nuril ƙalbinsa, tare da addu'ar Allah yasa kada samha ta yaba mishi,
Samha dake kwance tana tunanin duniya, jin shigowar motaci yasa ta tashi da sauri ta matsa jikin window lallai hydar ne, dariya tayi sosai tare da ɗora hannunta saman bakinta, ganin hydar ya fito daga mota yasa ta tabbatar lallai shine,
Wani irin juyi samha tayi tare da zungurawa da gudu irin na "yan gayu, tunda ta fito daga farlo take kiran sunan hydar, shi kuma yana tsaye a wurin mota yana magana dasu shamsu, jin muryar samha yasa hydar juyowa yana murmushi, sannan ya matso daga cikin mutane, da gudu samha ta iso ta rungume hydar, shima riƙeta yayi sosai a jikinshi, yanajin farin ciki yana ratsa shi,
Tou pha, tunfa anan samha ta shiga rattafawa hydar dukan da Asma'u tayi mata, murmushi hydar yayi tare da jan hannunta suka bar wurin,
Saida suka shiga farlo hydar ya saki hannunta yayi gaba da sauri take bin bayanshi tana ci gaba da faɗa mishi, saida sukaje ɗakin hydar samha bata daina surutu ba, kamar an ɗaura mata na'urar labarai,
Aje wayoyinsa hydar yayi a saman bedsite, sannan ya juyo wurin samha ya jawota jikinshi, cikin gajiyayyir murya yace samha wai ke mi yake damun kanki?
Cikin tsiwa samha tace ka dawo fa an fara, wani kaina yana da wani abu, ni babu wani abinda yake damun kaina,
Kallon ta hydar yayi sannan yace hmm ke samha baki iyayiwa mutane sannu da zuwa ba? Na dawo daga tafiya babu ya hanya ba komai sai kawo ƙara an miki an miki ke kullum an miki,
Samha tace ai nasan ka dawo lafiya tunda na ganka, gaka kayi kyau ma ai, sai kamshi kakeyi amma ka ɗan rame ne miya sameka?
Ajiyar zuciya hydar yayi sannan ya kara riƙe samha a jikinshi ya ɗaga kanshi sama, ita kuma tana kwance saman kirjinshi, hydar sai fitar da wani irin wahalallen lunfashi yake saukewa, yau dahar samha tana cikin sanshi har ya hango yanda wannan daren zai kasance a wurinsa,
Samha tace hydar kasan abinda na gani a gidan sahib? Har yanzun samha tana kwance a jikinsa, hydar yace Uumm, samha tace hadayin hoto da jakar matarsa, hydar yace kema sai inyi dake muma musa a farlo,
Samha tace waye yace maka a farlo yasa? Sauko kanshi yayi sannan yace dan naje gidan ai na gani, ke kuma ya kikaga matar sahib? A daidai lokacin da yake sakin samha daga jikinshi yana cire kayan jikinsa danyin wanka,
Samha tace katuwace, hydar yace kinga ko idan ta zauneki bazaki iya motsin kirki ba, dariya samha tayi sannan ta matsa ta zauna saman gado taci gaba da bawa hydar labarin dukan da Asma'u tayi mata,
Kallonta hydar yayi tare da cewa wace Asma'u ce? Nandai samha ta kwashe komai ta faɗa mishi, hydar yace waya kaiki? Ɗiyar kanin dady ne, kinsan halinsa kuwa? Wallahi makircinsa yawa gareshi, dashi aka haɗa kai aka kashe min iyayena amma sai aka laƙaba abun da haɗarin jirgin sama,
Ita Asma'u ɗiyarsa ce, nine yake so na aureta ina lallaɓasu ne badan banda abinda zanyi ba ko sunfi ƙarfina ba, na barsu ne kawai ina kallonsu amma zanyi maganinsu,
Yana faɗin haka ya shige toilet, ita kuma ɗaukar wayarsa tayi tare da kwanciya saman gado tayi ta latse latse, har hydar ya fito wanka, bayan ya fito ne yace samha jeki ki dafa min lipton, tace to tashi tayi tare da ajiye wayar ta fice,
Samha tana fita hydar ya ɗauki wayanshi ya fara kiran wayar Asma'u, bayan ta ɗauka hydar ya fara magana cikin tsakanin ɓacin rai yace miya haɗaki da matata har kika zo har gidana kika daketa? Asma'u tace yaya ciremin haƙori tayi fa,
Hydar yace haƙorin kin banza, an faɗa miki na haɗa samha da wata a faɗin duniyar nan ne? To na rantse da Allah daga yau sai yau idan har kika sake zomin gida wallahi saina ƙarya ki, yana faɗin haka ya kashe wayarshi,
Hydar na kashe waya Asma'u ta fashe da kuka dan tasan zuciyar hydar idan yace zaiyi zaiyi bare har yayi rantsuwa, haka taje ta faɗawa dady lalai da gaske hydar yayi aure,
Dady yace to barni da ita zanci ubanta Allah ya kaimu gobe lafiya, Asma'u ta ansa da amin,
Ita kuma tana gama dafa tea ɗin ta zuba a kofi ta taho dan kawo ma hydar, daidai kofar ɗakinta suka haɗu, hydar ya shige ɗakinta itama ta bishi,
A gefen gado ya zauna ta bashi tea ɗin, yace kinci abinci ne? Samha tace banajin yunwa, hydar yace wai miya sameki ne nifa naga duk kin wani burkuce, itama zama tayi kusa dashi tare da ɗora kanta a jikin hydar, itadai Allah ya sani hydar yana burgeta sosai,
Haka dai tayi ta tunane tunanenta har bacci ya dauketa, shi kua yana gama shan tea ɗinshi ya sauke samha daga jikinshi ya gyara mata kwanciyarta, ya ɗauki kifin ya fita,
Tun cikin bacci samha takejin ala luƙaƙa zagi a farlo, da sauri ta tashi zaune tare da duba a gogo taga 7:09am da sauri ta fita daga ɗakin tayi waje,
Asma'u ce da dadynta, dadyn yake zagin, Asma'u tana ganin samha tayi inda take da gudu, ganin ta kusa zuwa wurinta yasa samha ta ruga tayi ɗakin hydar,
A bakin kofa tayi tsaye dan hydar yace idan tana shigowa ɗakinshi da gudu zataji a jikinta, samha tace hydar taho, hydar dake zaune saman abin sallah yana karatun qur'ani ya juyo, samha tace taso ka gani, juyawa yayi yaci gaba da karatunsa,
Ƙarar marin da hydar yaji yasashi ƙara juyowa, da sauri ya rufe kur'anin ya tashi yana cewa wane hannune ya marar min fuskar matata? Daga samha har dady da Asma'u kallon hydar sukeyi,
Asma'u tace nice nan, da sauri hydar ya kama hannun Asma'u ya ƙaryashi sannan yace mina faɗamiki? Saboda tsabar iskanci har kizo a gabana kina marin samha? Har yanzun samha maimata kallamar,
_Wane hannune ya marar min fuskar matata?_
Wannan tunanin samha takeyi a ranta, tare da maimata kalmar a zuciyarta, bata gama tunanin ba, taji dady yana cewa wallahi wannan ɗiyar saika saketa, da sauri samha takai dubanta wurin hydar,
*_JAMEELA MUSA - Meelat Musa_*
💋
[05/04 4:46 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*_Mai dambu_*
*_Mai dambu_* { _Zuciyar meelat musa }_
*_Mai dambu_*
*_Asmeenat Xeeyan ina miki fatan alkairi, kuma ina ƙara bawa zuciyarki hakuri kinji aminiyata, kiyi hakuri ki manta da wannan lamarin kibar komai a hannun meelat musa ni zanji da komai, Allah ya tona asirin munafiki Allah ya hana mugunta tayi tasiri,_*
*_Gaisuwa gareku marubuntan zamani, fatan alkairi Allah ya kara basira da zahaka ubangiji yasa ku zarce haka a faɗin duniyar marubuta, jameela musa ke cewa ku sarara abunku kuyi ƙarko tare da yin shekaru irin na DABINO_*👇🏻
*_Asmeenat Xeeyan_*
*_Ramlat Abdulrahman mai dambu_*
*_Bilkisu Khalisat_*
*_Ummu Affan_*
*_Halima Tweety_*
*_Hasina Oganniya_*
*_Halima Leema_*
*_Maryam Muhammad_*
*_Raheema_*
*_Surayya_* 💔
*_Ummu Sayyed_*
*_Ummu Farhana_*
*_Saleehat_*
*_&_*
*_Auta Ummu Harny_*
*SO*
*MUGUN WASA*
_Dedicated to_👇🏻
_Ramlat Abdulrahman real mai dambu_
*56-58*
Har yanzun hannun Asma'u yana riƙe a hannun hydar sai wani ƙara murɗeshi yakeyi tare da cewa matata abokiyar wasanki ce?
Asma'u kuwa da tuni ta suma saboda azaba, shi kuwa dady cewa yake saboda wannan ɓarauniyar ka kashe min ɗiya?
To wallahi duk ubanda ya tsaya maka yau saika saketa,
Ubanka harya bar duniya yanajin magana na, kai kuwa baka isa kazo min da raini ba,
Cikin tsananin ɓacin rai hydar yace ubana daban ni daban, can zumuncinku ya haɗaku kuma shine yaji zai iya biyayya akan duk abinda kace yayi,
Dady yace kai ban isa dakai ba? Hydar yace sosai ma, ni baka isa dani ba, danni a faɗin duniyar nan maganar mutum ɗaya nakeji, kuma gatanan tsaye a gabanka, a daidai lokacin da hydar ya harba Asma'u da ƙafarshi ta faɗi ƙasa,
Hydar yaci gaba da cewa samha _ZUCIYATACE_ ya dafa daidai saitin zuciyarsa, sannan yace ita samha _RUHI NA CE_ dan duk wanda ya taɓa samha haƙiƙa yana man wasa da rayuwata ne, duk wanda yayi min wasa da rayuwa haƙiƙa nasan baya ƙauna na, har yanzun hannunsa yana daidai zuciyarsa,
Cikin ɗaga murya mai tada hankali hydar yaci gaba dace to kuwa kaga wasa da rayuwa ganganci ne, dan inajin samha itace _LUMFASHI NA_ kaga kuwa duk wanda naga zai gigin zare min raina, to nine zan kasheshi tun kafin ya kasheni, ya ƙarasa maganar yana dafa kirjin sa,
Dady ya ɗaga hannunsa ya darkakawa samha mari, da sauri hydar ya rumtse idanuwanshi kamar an caka mishi wuƙa, murmushin ƙarfin hali hydar yayi ya kalli dady tare da cewa kada ka ƙara, dan nayi alkawari da zuciyata duk hannun daya hau saman jikin samha bayan nawa saina gundileshi,
Kai kuwa daka tashi dukanta ma kayi? Jinjina kansa yayi tare da cewa yau da bakai bane saina tsiyaya maka idanuwa,
Dady ya saki baki cikin yanayin mamaki yake kallon hydar,
Tsoki hydar yayi sannan ya kalli samha yace wuce kije kiyi baccinki,
Dady yace idan kika shiga saina sassaraki, hydar yace shiga ya sassarakin in gani,
Ta gaban hydar samha ta raɓa ta shige ɗakinsa, shi kuma dady, ya ciro wayarsa ya fara waya,
Shima hydar wayar yakeyi tare da zagin su shamsu duk suna aikin mi suka bar dady ya shigo mishi gida?
Faɗa hydar yayi sosai tare da cewa dukansu suzo yanzun nan yana neman su,
Ita kuwa samha tsayuwa tayi a tsakiya ɗakin tana tambayar kanta, ya akayi kuma hydar yake cewa ita matar sa ce?
Shigowar hydar yasa ta juyo da sauri tana kallonshi, shima ita yake kallo tare da cewa ba nace kiyi bacci ba?
Cike da tsiwa samha tace banaji bacci, amma miyasa kace min ni matar ka ce? Hydar yace saboda ke matar tawa ne,
Samha tace ta ina na zama matarka? Cikin fushi hydar yace ke kada ki kawo min raini, kalmar mata nawa kika sani a yaren hausa?
Samha tace irin wanda ka sani nima shine na sani, hydar yace to yanda kika fahimta haka nake nufi,
Samha tace to aiko lallai idan harni matarka ce bana sanka, kuma Allah ya sani bazan iya zaman aure dakai ba,
Idanuwa hydar ya zaro tare da cewa wallahi ƙarya kike, nine mijinki, kuma maganar bazaki zauna dani ba ai kema kinsan ƙaryar banza ce,
Cikin mamaki samha tace to yaushe ma aka ɗaura min aure dakai har na zama matar ka?
Hydar yace tunani ya zama naki, ni nayi nawa tunda na faɗa miki,
Don haka a cikin abinda na rubuta miki lokacin da zan tafi *_Germany_* anan zakije kiyi dogon nazari tunda kina da wayau nan zaki gano waye hydar a wurinki,
Yana faɗin haka ya fita daga ɗakin dan su shamsu sun iso,
Shima dady bataliyar daya tara suna farlo gaba ɗaya dai gidan ya cakuɗe, hydar hankalinsa a tashe dan kaff ahalin dadynsa babu wanda yasan yayi aure,
Amma yau Asma'u ta tona masa asiri kafin ya gama abinda yakeyi, lallai yasan yau samha saita bar gidan kuma shima yasan yaune lumfashinsa na ƙarshe a duniya,
Kakar hydar wanda ta haifi mamanshi itama dady ya gayyato ta a wurin wannan babbar badaƙala,
Samha kuwa banda kuka babu abinda takeyi tare da faɗin sahib ya cuci rayuwarta, ya saka ta cikin harƙala mi sahib yake nufi da ita?
Bayan gida ya gama haɗuwa "yan uwa da abokan arziki, an cika paff a farlo, babu abinda kakeji sai "yan ƙananan maganganu kowa da abinda yake faɗa,
Kiran hydar akeyi amma shi yana can yana riƙon samha kamar ansashi kama maciji, ita kuma sai wani zuƙewa takeyi tana kuka tare da cewa ita bata auren hydar sahib takeso,
Hydar kuka yakeyi yana cewa samha nine sahib, ina samha bata gane karatun, neman hanyar tsira da rayuwarta takeyi dan tana jin "ya"yan dady sunce zasu kasheta tunda har hydar ya ƙarya yayarsu saboda ita,
Wasu kuwa cewa suke bazai yuwu ba, yama za'ayi yaya hydar ya auri wannan jakar yarinya,
wasu kuma tunani sukeyi yaushe hydar yayi aure basu sani ba?
Kakar hydar ce tace wai Aliyu bazai zo ba? Tana magana da yarenta wanda bai fita,
Dady ne yake ta zazzare idanuwa tare da cewa har kashedi yamin saboda tsinaniyar yarinyar nan waida ba nine na daketa ba saiya tsiyaye min idanuwa babu tausayi,
Samha kuwa girgije hydar tayi daga riƙon dayayi mata, shi kuma ya ƙara ɗamƙota tare da ɗago mata fuska yana cewa samha ki zama mai adalci a rayuwarki, kada san zuciya yasa kiyi abinda daga baya zakiyi dana sani,
Samha tace kai Rrrr da Allah, tunda kaga har banyi dana sani a baya ba, har abadan duniya bazanyi danasani ba, wato saboda ma ka ɗaukeni daƙiƙiya kenen ma kaine sahib? Lallai bansan fushin zuciya yana sa mutum ya zama mahaukaci ba sai yau,
Hydar yace ki gyara kalamanki akaina, danni nasan abinda nakeyi banda taimakon dana ba rayuwarki da yanzun nan baki a faɗin duniyar nan, samha tace bazan gyara ba, kuma ina so ka soke duk wani taimako tsakanin ka dani kaga zan fasa rayuwa ne?
Murmushi hydar yayi tare da cewa ke "yar wasan kwaikwayo, wasan ya isa haka, ai nasan zuciyarki tana san hydar,
Tuff samha tayi sannan tace Allah ya sawaƙe ma rayuwata, zuciya na da gangar jikina su rayu da abokin gaba,
Kakar hydar ce ta shigo ɗakin tana magana da hydar cikin wani irin yare, kamar fulatanci kamar kuma yaren shuwa, yaren dai kamar labaracci ne, hydar shima cikin irin yaren yayi magana sannan suka fita daga ɗakin yana cewa ki jirani ina zuwa, yace ma samha,
Su shamsu da dady da Alale da faruk kowa yabi bayan hydar suka sauka farlon ƙasa dan acanne kowa yake jiransu,
Fitar su hydar samha ta matsa jikin bedsite ta buɗe loker ta ciro biro da joter, ta ɗora a akai ta fara rubutawa kamar haka,
_Zuwa ga hydar,_
_A rayuwa amana tayi ƙaranci, ban taɓa sanin zamba da zalinci halinka bane sai yanzu, kayi nasara wurin jinyatar da zukata guda biyu tunda har kayi ƙoƙarin raba samha da sahib_
_Kayi nasarar rabani da sahib, nikam babu abinda zance maka sai ince sannu da ƙoƙari babban ibilishi, dan duk wanda ya raba aure haƙiƙa yakai babban sheɗani,_
_Na barka da Allah, bazan taɓa yafe maka ba harƙarshen rayuwata ba, kuma saboda baka so na, yasa kasa sahib ya yadar min da m card saboda kana so rayuwata taci gaba da lalacewa a titi, babu dangin uwa ba na uba, haka na taso ban san mai kyau ba bansan mara kyau ba, tunda bani da wanda zasu koya min kyakkyawa ko mummuna, na barka lafiya, nima naje in gano ahalina, kuma daga kai har sahib kada kusha wahalar nema na, dan na riga nayi muku nisa_
_Kunso inyi ta zama a ƙarƙashin ku kamar wata karya, to Allah yaga zukantaku shi yasa ya tseratar da rayuwata daga hannun azzalimai guda biyu, Allah ya taimakeni baku tarwatsamin rayuwa ba, da mutane sun ɗauka ni karuwa ce, tunda har kukayi kokarin yin aure dani a cikin sirri, har kake min fatar kamin ciki, wato in cikin shege ko? To Allah ya fika_
_Daga samha,_
_Zuwa gareka_
_Babban maƙiyi na hydar_
Samha tana gamawa ta ajiye, ta ɗauki hijabi ta saka, sadaf sadaf ta fito babu kowa a sama amma kana jiyo hayani a ƙasa kamar za'a babbakawa gidan wuta saboda bala'i,
Da gudu samha tabi ta baya ta fice, da gudu ta isa bakin get na farko, ta ƙara daddagewa ta ƙara shararawa da gudu,
Kai hydar abinda kayi ka kyauta kenan? Aminin dadyn hydar yake mishi magana, hydar yayi shiru,
Dady yace ai ɗan banzan lalataccen yaro ne nan daka ganshi, bai ajiye komai ba sai rashin kunya da girman kai wato shi kuɗi yana gaya mishi ƙarya, yanajin sa daidai da kowa, shege munafuki,
Wani irin kallo hydar yayi ma dady wanda yasashi saurin sauke kanshi ƙasa, hydar yace daga yau kada ka sake cemin lalatacce tunda kasan ni bashi bane,
Alhaji Lawal aminin dady yace hydar bakasan ba'a aure a ɓoye ba? Wannan rayuwa haka ta yuwu kuwa? Hydar yace Dady ba auren ɓoye bane na bayyane ne,
Dan nine naje wurin danginta na nemi auren samha kamar yanda addi'ni yace, kuma suka yadda suka bani auren ta,
Dady yace toni dai duk ba wannan ba, dole saika auri Asma'u dan bazai yuwu ba, munaji muna gani yaya ya kwanta ya mutu dukan abinda ya bari aka tattara aka danka maka, hada jirgin sama, saika ɗauki dukiyar gidan ɗan uwana kaje kayi ta bishasha dasu,
Ai gida bai ƙoshi ba, baza'a kawai dawa ba, ka auri Asma'u sai su zauna su biyu shikenan sai fitina ta ƙare,
Murmushi hydar yayi da gefen bakinsa sannan yace dady gaskiya kayi haƙuri wallahi kaina baya ɗaukar hayaniyar mata biyu, dady yace to aisai ka saki ita yarinyar ka auri "yar uwarka,
Hydar yace dady ka taɓa ganin gangar jikin data kasance a duniya bayan babu lumfashi ajikinta? To ita samha itace lumfashina da zaran ta ɓace a duniya nima rayuwata ta ƙare,
Dady yace sannu ba'india an gaishe ka baban soyayya, ashe da gaske har yanzun akwai soyayyar idan bana tare dake bana iya cin abinci idan bana ganin zan makance, idan bake ba sai rijiya mai kwalabe, hydar yace ko babu su nidai akwai saurana, danni da mutum ya rabani da samha gaskiya gara kawai a kaca min wuƙa in mutu,
Dady yace to wallahi duk babbar bala'i saika auri Asma'u, hydar yace to a auramin ita in gani, a fusace dady ya miƙe tare da jan hannun Asma'u da aka fesa ma ruwa ta dawo daga duniyar suma,
Tawagar shi suka bi bayanshi suka fice daga farlon, bayan fitar su Alh Lawal yace ma hydar kada ka kuskura ka auri ɗiyarsa dan wallahi idan harka auri yarinyar can sai sulaimanu yaga bayanka,
Nan dai Alh Lawal ya ƙarayi ma hydar nasiha, tare da musu addu'ar zaman lafiya, daga baya shima ya tafi,
Farlo ya rage daga kakar hydar sai faruk sai yaran hydar "yan amana wanda sun riƙe alƙawari da amana sunajin hydar har cikin ransu,
Itama kaka haka tayi ma hydar fatan alkairi tare da musu addu'a Allah ya basu zaman lafiya, tace kuma akai mata jikarta samha har gida, duk a cikin yarensu take magana, hydar yace tom, gaba ɗaya suka raka ta har inda driver yake, saida ta tafi sannan suka dawo farlo aka fara maida yanda akayi,
Ita kuwa samha da gudu ta fice daga gidan hydar tana kuka, gata babu ko asi bare asiya a hannunta, bata da kuɗin da zata hau napep haka tayi tsaye a bakin titi tayi ta raba idanuwa kamar munafika,
Ganin tsayuwan baya fishsheta yasa ta samu napep tahau ta nufi gidan kawu,
Napep na tsayawa a ƙofar gidan kawu taga illo, dan haka da sauri ta sauka taje wurinsa tace malami dan Allah ka biya kuɗin abin hawa mana,
Cikin magana irin ta "yan tasha illo yace haba matar Oga muna ganinki munga kuɗi, duk zafafan motocin gidan hydar kika ɓige da hawan "yar ƙurƙura? Hajiyata keda zamu ga an faka an ajiyeki a cikin mota mai lumfashi sauran dakaran motocin suna take miki baya amma sai kawai ki wani zo a haka harda wani cewa in biya miki kuɗin abin hawa?
Dan gajeran tsaki illo yayi tare da ci gaba da cewa gaskiya mata kin diro babbar faɗowa kikayi, waye yace miki yanzu duniya ana zama? Tsaki samha tayi tare da cewa idan kana biyamin biya min idan ko bazaka biyamin ba kada ka kawo min hauka a cikin al'amurrana, dan yau zafi gareni kaina hayaƙin rashin mutunci yakeyi,
Wata kafirar dariya illo yayi tare da cewa shiga ciki abinki ganinan zuwa, samha ta wuce simi simi ta shiga gida, illo yaje ya biya mai napep sannan shima ya nufi gidan,
Da sallama samha ta shiga, mutane sosai a gidan, amma babu wanda ya ansa mata sallamar, a gefe kuma ga kawu kwance babu lafiya yana cikin hali mai tada hankali,
Samha ta sake cewa Assalamu Alaikum, wannan ƙaro wani mutumne ya ansa mata, tare da cewa bisimillah,
A hankali samha ta isa wurin ta durƙusa ta gaishesu cikin ladabi, gaba ɗaya suka ansa, kawu kuma ya juyo da idonshi ya kalli samha yana san yayi magana amma baya yuwuwa,
Wani ne ya shigo gidan yana cewa yawwa ku fito ga mota nan tazo, mutane suka fara tashi yayin da ake ƙoƙarin kama kawu,
Samha tayi ƙarfin halin cewa ina za'a kai kawu ne? Yace zamu kaishi katsina ne, wurin danginsa domin su nema masa lafiya, samha tace miya sameshi ne?
Yace bisa bincike da likitoci sukayi yawan shaye shaye ya lalata ma kawu "yan hanji, sannan yana ɗauke da ciwon hunhun, yawan tunani da damuwa kuma ya ɗirkaka mishi ciwon zuciya,
An kashe kuɗaɗe sosai amma har yanzun babu wani abinda ya canja, tun muna da abin maganin har yanzun ya ƙare, samha tace nidai kafin ku tafi dashi katsinar kusa shi ya faɗa min ina ahalina suke?
Mutumin yace kiyi hakuri tunda yana cikin halin rashin iya magana, idan mukaje can tunda maganin hausa za,a mishi idan ya samu sauƙi saiya miki bayanin komai, dan gaskiya yana ta maganarki wallahi,
Haka dai aka runguɗa, samha da kawu da saura mabiya bayansa, aka ɗurasu a mota, haka aka cika j5 bayan kowa ya shiga, driver yaja motar sai katsina ta dikko ɗakin ƙara kunya garesu badai tsoro ba,
Dady kuwa tafiyarsu banda zage zage babu abinda yakeyi tare da rantsuwa sai hydar ya auri Asma'u, tare da hararo irin tarin dukiyar da ɗan uwansa ya mutu ya bari, ga motoci na tashin hankali wanda duk ƙarshen shekara sai anyi sabbin zubi zafafan motoci "yan yayi masu kyau da daukar hankali ga tsada, kuma ko mutuwar yayan nasa yayi tunanin hydar zai lalace ne, shi kuma ya ɗauki dukiyar yayi ruf da ciki da ita amma hydar yaƙi ya lalace,
Kullum dady cikin ƙoƙarin tura kwaratan mata yake dan su yaudari hydar su lalata mishi rayuwa toshi harkar mata ma da bayayi, wannan dalilin ne ma yasa daya tashi neman samha dan ya jijjiga mata zuciya yasa yaje a sahib,
Tunda shi ba ɓoyayye bane bayyananne ne shi, kuma yaso ya latsa samha sosai bisa rainashi datayi, amma Allah saiya yiwa zuciyar hydar dabaibayi, Allah ya ɗora mishi san samha matsananinci so, wanda shi hydar yake ganin hakan da Allah yayi mishi babban taimako ne yayi masa, domin da babu maganar wani aure a ransa dan gani yake duk macen daya aura za'a haɗa kai da ita a kashe shi,
Bayan sun gama firarsu kowa ya tafi, hydar ya miƙe cikin farin ciki, a ransa kuwa yana kuɗirin nunawa samha lallaifa shine mijinta dan yayi alƙawari da zuciyarsa dama bazai bari wani abu ya shiga tsakaninsa da samha ba harsai tasan shine mijinta, to yau kuma tunda taji komai dan haka lallai itama yau za'a bata babban tikiti na shiga sahun mata masu aure,
Yau zata san hydar shine rayuwarta, murmushi yayi tare da tuno maganar samha, { _Sahib hydar fa dirjeje ɗan iska ne,_ } murmushi hydar a bayyane yace yau zakisan hydar babban ɗan iska ne, kamar yanda kike faɗawa sahib, a daidai lokacin daya shiga ɗakinsa,
Da sallama ya shiga yana kiran samha, amma babu samha babu labarinta, da sauri ya nufi toilet nan fa yaren irin na tsakar ɗaki ne, da sauri ya juya da nufin fita kuma saiya juyo kamar yaga wani abu a gado,
A hanzarce ya koma bakin gado ya miƙa hannunsa ya ɗauki takardar, ganin an rubuta zuwa ga hydar yasa hydar yayi murmushi mai ciwo, zufa da hawaye hydar ya goge a daidai lokacin daya gama karanta saƙon samha,
Ajiyar zuciya hydar yayi tare da furta kalmar innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, dafa gefen zuciyarsa yayi tare da zama a gefen gado a hankali don wata hajiyaya dayaji tana neman kwaɗashi da ƙasa,
Hannunsa yakai a gefensa ya buɗe lokar bedsite da sauri ya ɗauko maganinsa yasha, bayan yasha a hankali hydar ya sauko daga saman gadon ya kwanta a ƙasa danji yake kamar zai faɗi,
Tunanin samha ya farayi tun daga ranar daya fara haɗuwa da ita a rayuwarshi, tunanin rayuwarshi da ita a matsayin sahib, rayuwarshi da ita a matsayin hydar har zuwa yau da samha bata tare dashi,
Murmushin ƙarfin hali hydar yayi tare da furta ni banma san ta ina zan fara ba, ina kika shige ne? Ina zan ganki? Da hanayi sosai hydar yace ina kike keeeeeeeeeeeee, ya ƙarasa maganar cikin ƙaraji,
Su samha an iso katsina ta dikko lafiya, tunda samha suka shigo katsina takejin farin ciki yana ratsa mata babban birnin zuciyarta, tana cikin farin ciki da nishaɗi, tace ashe haka katsina take shi yasa real mai dambu ta nace saida tazo ganin jamila musa,
Kai lallai katsina tayi kuma katsina akwai kara da mutunta baƙo, lallai duk wanda ya samu ya lafe a cikin babban birnin katsina baya marmarin zuwa ko ina,
Samha bata gama tsinkewa da lamarin mutunci irin na katsinawa ba, saida taga yusra da kausar sunji daɗin ganin samha sosai haka sukayi ta rungume samha irin da yanda abokai sukeyi idan an daɗe ba'a haɗu ba,
Shi kuwa kawu ɗakin ɗaya aka ware mishi a cikin ƙaton gidan kakarsu su yusra wanda yake a cikin unguwar goruba road duk a nan cikin babbar birnin katsina, a ɗakin aka kaishi ya huta, dan yusra tace india za'a kai kawu dan can india sune sukafi manyan likitoci wurin ɓangaren ciki, dan duk abinda ya shafi ciki sun ƙure a wurin,
Yusra da kausar sukaja samha zuwa nasu ɗakin, saida samha tayi wanka taci abinci sannan suka ɗanyi fira, daga baya kuma samha ta kwanta bacci domin hutama rayuwarta,
Suma baccin suka kwanta, amma ƙiriƙiri bacci yace baisan idon samha ba, tashin hankali hydar yazo yayi mata tsaye a ranta, kaji jaraba tunanin hydar ya riƙa zuwa mata a yanayin da take a jikinsa,
Kuka samha ta farayi dan gaba ɗaya bata burin daya wuce tajita a jikin hydar, goge hawayen idonta tayi tare da cewa mi hakan yake nufi?
Har gari ya waye samha bata runtsa ba, yanda taga rana haka taga dare, daka ga samha kasan tana cikin damuwa, ko wurin kalaci samha ruwan tea kawai tasha, bayan sun gama ta koma ɗaki tayi wanka ta saka kayan yusra, ta hau gaɗo ta kwanta,
Hydar kuwa bayan ya samu jikinsa ya daidaita tashi yayi yaje ya watsa ruwa tare da ɗauro alwalla, yana fito jallabaiya ya zura ya nufi masallaci,
Bayan sun gama sallah ne hydar ya kira faruk ya faɗa mishi samha ta gudu fa, faruk yace to ya jikin naka? Hydar yace Alhamdulillah, faruk yace bari inzo muje gidan kawunta mu gani ko za'a ganta a can, hydar yace kyaleta ni nayi imani yau duk inda samha take bata iya bacci ka barta dani kawai ai nine dai ko? Faruk yace kayi hakuri hydar kada kace haka muje, hydar yace wallahi bazanje ba, zata dawo da kanta badai ta shigi hydar ba?
Faruk yace to zanzo in kwana dakai saboda dare, hydar yace kada ka samu damuwa, faruk yace wallahi saina zo, hydar yace Allah ya kawoka lafiya, bayan sun gama wayarne hydar ya tashi ya koma ciki,
Faruk shine yazo ya kwana da hydar saboda kada wani abu ya sameshi babu mai taimaka mishi,
Cikin dare ciwo yayi tsanani, gaba ɗaya hydar ya shiga tashin hankali, dan haka ya fara tashi faruk bayan faruk ya farka hydar yace tunda ni nayi rantsu bazanje ba kaje idan samha tana nan ka bata waya zanyi magana da ita,
Faruk ya kalli agogo yaga 1:55am baida yanda zaiyi ya tashi ya nufi gidan kawu, yana zuwa yaga gidan an danƙara mishi ƙaton kwaɗo,
Dare ne baida wanda zai tambaya dan haka dole ya haƙura ya dawo gida, ya faɗawa hydar, daren dai hydar a asibiti ya kwana,
Yusra ce ta shigo ɗakin tana cewa samha kizo muci abinci mana, samha dake kwance tace banajin yunwa, amma don Allah ki bani aron wayanki, yusra tace mi kikaci ne kike cewa bakyajin yunwa? A daidai lokacin data miƙa mata waya,
Ansa samha tayi ba tare data ba yusra ansar tambayar datayi mata ba, tace yusra bani biro da paper don Allah, yusra tace to, zuwa tayi ta kawo mata sannan ta fita daga ɗakin,
Tashi zaune samha tayi tare da cewa bari in gano matsayina a cikin zukatan mutum biyu, wato hydar da sahib, ta fara rubutawa kamar haka,
_Nadama_
_Hydar rauni_
_Sahib san kai_ = { _Nadama_ }
_Samha kafiya_
_Sahib yana da san kai_
Nazari, tunda sahib yana da sankai, shi kuma hydar yana da rauni, sahib talaka ne, hydar mai kuɗi ne,
Shi sahib shine hydar ya turo shi wurina tunda yaronsa ne, yazo yayi min wayau ya fara soyayya dani, bayan na kamu da sansa, saiya ɗaukeni yakaini gidan hydar tunda shi abokin gaba na ne, a gidan hydar kuma hydar yana ƙoƙarin ya koyama zuciyar samha sanshi tunda ita zuciyar samha tana da kafiya, dan idan yazo kai tsaye bazan so shi ba,
Ajiyar zuciya samha tayi, sannan ta mike tsaye, taci gaba da nazari,
Bayan sahib ya kawoni gidan hydar, sai yace zaki zauna anan saboda banda da inda zan ajiyeki, ki zauna anan kafin zuwa lokacin da zan gama gina gida,
A lokacin sai sahib yaci gaba da bani kulawa sosai a gidan hydar har ya yaudari zuciyata na amince da aurensa, saboda yaga na kamu da sansa, ni kuma na biye masa mukayi aure ba tare da sanin iyayensa ba, sai yayi min ƙarya mamanshi bata lafiya, ni kuma na amince da buƙatarsa a bisa sharaɗin zai samanin ahalina,
Zama samha tayi a gefen gado, sannan taci gaba da zurfafa tunaninta,
Bayan ɗaura aure na da sahib, sai sahib ya fara canjawa ya koma halin da ba nasa ba, sai yace idan ina san abu inyi ma hydar magana, anan sai yayi ƙoƙarin cusa alaƙa mai ƙarfi tsakanina da hydar,
Toda har sahib yana sona tsakaninsa da Allah dole zaiyi kishina, amma saiya ware lafiyayyen ƙato ya haɗani zama dashi, daga nan sai hydar ya biya sahib kuɗi masu yawa, sai sahib ya tafi zama ya dawo tsakanin samha da hydar,
Idan samha ta kira sahib sai yayi mata wulaƙanci sosai, zaman da samha takeyi da hydar yasa take faɗa mishi damuwarta, sai hydar ya lallashi samha, shi kuma hydar tunda mace bata taɓa mishi jiki, shine dalilin daya sa ya koyawa samha zama cikin jikinshi tunda yana da wani kuɗiri akaina daban,
Ajiyar zuciya samha ta sauke lallai mutane biyun nan sun mata yawo da hankali, miye dalilin daya sa mace bata taɓawa hydar jiki?
Samha tace lallai yana da shirin duniya ne, lallai ya zamarmin dole in gano yanzun ni matar wace ce tsakanin hydar da sahib, taci gaba da rubuta,
_Sanka_
_Kafiya_
_Rauni_
_Sankai Kafiya + Rauni_
= _Nadama_
_Sankai Kafiya Ranuni, -Sankai_ = _Nadama_
Ai sankai an fitar dashine saboda an sallami sahib hydar ya bashi kuɗi, saboda haka yanzun babu sahib a cikin wannan lissafi, yanzun lissafi ya rage tsakanin ziciyar hydar da zuciyar samha,
Hydar wurin san ganin ya wahalar da rayuwar samha yasashi ya antaya kogin ƙaunar samha, saboda yana da raunananniyar zuciya,
Bayan hydar ya tabbatar zuciyarsa tana san samha, sai kuma ya gane lallai samha bata sansa saboda zuciyarta tana da kafiya,
Wannan dalilin yasa ya ɗauko sahib yasa ya fara soyayya dani, kam lalai sahib ka kai babban ɗan iska,
Abinda ban gane ba yaushe na zama matar hydar? Wayar ta ɗauka ta rubuta number sahib ta fara kiran wayar,
Bai ɗauka ba, dan haka ta rubuta number hydar ta fara kira, saida ta kira har ta gaji domin hydar baya ɗaukan baƙuwan number, haka ta haƙura ta fara rubuta saƙo kamar haka,
_Suna na samha_
_Hydar na gano amsar tambayar daka min, wannan ansa itace nadama, amma abinda nake so na sani dani dakai waye zaiyi nadama?_
Bayan faruk yaga saƙo ya faɗawa hydar, murmushi hydar yayi sannan yace kirawota,
Bayan an kira samha ta ɗauka, faruk yace hydar zaiyi magana dake, bayan an bawa hydar wayarne, hydar yace kina ta ina ne? Samha tace ina katsina, hydar yace duk abinda kike ki dawo kaduna yau, m card ɗinki da labarin ahalinki duk yana wurina, kuma ahalinki suna nan cikin garin kaduna, samha tace sai nayi nazari idan naji ina buƙatar ahalin nawa zan dawo idan bana buƙata zakajini shiru, ina maka fatan alkairi ka huta kaji hydar,
Tana faɗin haka ta kashe wayar baki ɗaya, murmushi hydar yayi sannan ya kalli faruk yace samha tana iskanci da rayuwa, kaji wai in huta abuna, bayan tasan hutun yana wurinta, kuma ahalin nata ma bata sansu,
Lallai na yadda duk abinda baka so baka sansa, amma babu wanda yayi baban kuskure saini, wai miya kaini ma? Kana ganin yarinya tana min yawo da rayuwa a hannunta ko?
Faruk yace ai kayi wasa kaji daɗi, bakasan shi *SO MUGUN WASA* bane? Waye yace ana wasa da so? Kayi addu'a ma kada ka mutu dan wannan yarinya taci ta gyare, murmushin ƙarfin hali hydar yayi tare da cewa Allah ya jiƙanka hydar, kallon shi faruk yayi sannan ya kecewa da dariya, yace wato harka mutu ko?
Hydar yace Eh mana, ni kawai ma ka tara mutane kace na mutu ya ƙarasa maganar yana matse hawayen dole, dariya faruk yayi sannan yabar ɗakin,
Ita kuwa samha tana kashe wayarta, ta fara nazari,
Idan na koma kaduna, sai inje gidan hydar tunda yace yasan labarin ahalina, idan na koma gidanshi, saiya kwance karnuka su hanani fita daga gidanshi, daga nan sai ya ɗirkakamin ciki kamar yanda ya faɗa a baya,
Bayan nayi ciki saiya fara min wulaƙanci, ni kuma ina hakuri tunda ina san sanin labarin ahalina, daga nan zai riƙamin yawo da hankali akan m card, zan kasance a ƙarƙashin ikonsa daya gama biyan buƙatarsa a kaina saiya sakeni, tunda sun ɓoye sunyi aure dani dagashi har sahib, idan suka sakoni sai in dawo gari ana min Eho nayi cikin shigeya, burin maƙiyi ya cika akaina kenan,
Murmushi samha tayi tare da cewa ƙarya kake, Allah bazai baka nasara akaina ba, ya ubangiji kada ka bari zalinci yayi tasiri,
Haka rayuwar samha taci gaba da tafiya a katsina, kullum bata da wani tunani wanda ya wuce hydar kuma tana san kasancewa a jikinshi dan zama jikin hydar yana sata nishaɗi kuma yana kauda mata duk wata damuwa, wannan dalilin yasa take maraicin sa sosai, takan tuno abubu da dama da suke kasancewa tsakaninta dashi, saida tayi murmushi, wani kuma tayi tsoki,
Yanzu bata da burin daya wuce taga sahib tayi mishi rashin mutunci, ɗan iska daya sa rayuwata ta shiga garari, wai kamar ita ya yaudara? Hmm kuma hydar hada wani cewa shine sahib, kwafa tayi sannan tace duk zakuci uwarku ku biyu ɗin,
Shima hydar an sallame shi daga asibiti, kuma yana ɗan jin sauƙi, abinda yake kwantar masa da hankali shine daya tuna akwai auren shi a kan samha saiya ji sauƙi dan yasan dai duk haukarta bazata kula kowa ba tunda tasan ita matar aure ce,
Haka dai yake "yan huɗɗoɗinsa amma badai kamar da ba, kana ganin sa kasan yana cikin damuwa,
Kawu kuwa jiki ya ƙara lugudewa gaba ɗaya jiki ya jagwalgwale babu sauƙi sai wurin Allah, samha kuwa yanda taga yanayin kawu yasa tafi kowa tashin hankali,
Haka aka ɗauki kawu aka nufi asibiti dashi, banda kuka babu abinda samha takeyi tare da faɗin kawu kaji tsoro Allah kafin ka mutu ka bani address na ahalina, kafa san ka ɗauka alhakina da yawa ka cuci rayuwata ka gurɓata min rayuwata kasa na zamo mara "yanci kowa ya rayu a cikin uwa da uba, idan babu iyaye akwai "yan uwa, amma ni miyasa kamin haka? Haka ake riƙon amana? Wai waye ma ya baka amanata?