*Ina masoyan ANFA? wato marubuciyar DAN FASHI, ku garzaya jikin soket domin ku dirkakawa wayoyinku chargy tsaraba mai dadi ANFA tazo muku da ita, masoyan ANFA karku sake ku bari a baroki ku baya karku kuskusara ku bari meelat musa ta baku labari, shin Hajiyata ko kinsan MAHIMMANCIN BUDURCHI? Kinsan darajar budurchin ki? Kinsan ƙima da daukaka da buducinki yake nema miki a gidan aurenki? Wannan daliline yasa ANFA tayi dogon nazari tare yin kundunbala ta kutsatsa tasa kwalwarta dogon nazari don bamu babban labarin akan MUHIMMANCHIN BUDURCI ku kasance da ANFA ku nemi wayoyinku a kusa daku kowa ta zurawa wayarta ido domin ganin wannan kayataccen labari mai taken MUHINMANCHI BUDURCHI ni meelat musa nake cewa asha karatu lafiya, ANFA daukacin BRILIANT WRITER'S ASSOCIATION a madadin kowa da kowa na kungiyar brilliant ni meelat musa nake cewa Allah yasa a fara a sa'a,*
*SO*
*MUGUN WASA*
*Dedicated to*👇🏻
_Ramlat Abdulrahman real mai dambu_
*35-37*
Shekenan saika wani kama kayi tafiyarka abinka ka barni anan? To anan nayi zamana ta nuna wurin da hannunta, sannan taci gaba da cewa kada ka sake min irin haka daga yau kaji na fada maka!
Murmushin karfin hali hydar yayi sannan yace to insha Allah bazan sake ba Allah ya baki hakuri, yana fadin haka yayi gaba dan ya kagara ya shiga ciki ya huta danji yake kamar zuciyarsa zata fado kasa,
Samha tace to ina kuma zakaje? Kazo ka mayar dani gida mana, ba tare daya juyo ba yace wane gidan? Samha tace gidanmu mana, bai sake magana ba ya shige cikin farlon samha tabi bayansa tana kara cewa idan bazakaje ba ka fada man mana, sai ka kawoni ka wani kama ka ajiyeni?
Murmushi yayi sannan yace mai gida yace anan zaki kwana! Zaro idanuwa samha tayi sannan tace in kwana? In kwana anan gidan? Kawai sai in wani kama in kwana gidan katti sai kace wata "yar iska, tunda nazo a gidan nan banga mace ba maza kawai suke shawagi kamar kifi a cikin ruwa,
Sahib yace daga yau kada in sake ji kince ke kamar wata "yar iska, idan har kika sake fadar haka zansa hydar yayi miki dukan rabani da yaro, murmushi samha tayi kadan sannan tace komai hydar komai hydar to ai sai kaje ka fada ko an gaya maka ina tsoron sa, ni wallahi ina iya fasa masa baki mtsww dama baisan dazu ya bani haushi ba, wallahi ai shima hydar din dan iska ne,
Sahib yace samha kina da hankali kuwa? Ubangidan nawa ne dan iska? Samha tace ai ba babanka nace ba, zaka wani bi ka tada hankali sai kace an tsine maka albarka, ni wallahi bana san kana zama da wannan hydar din banzan dan wallahi na lura ka fara koyan dabi'un sa, idan har kana dabi'un hydar tsakani da Allah gaskiya nidai saidai ince Allah ya kara mana hakuri baki dayanmu,
Gaban hydar ya fadi das das, da sauri yace tsaya kiji wane dabi'u nakeyi irin na hydar samha? Samha tace Oho kaima ka sani danni wallahi idan har bana san kasuwa ko sautu bana bayarwa, murmushi karfin hali yayi wanda bai kawo a bakinsa ba sannan yace duk dan na tafi na barki kike so muyi fada ko? To Allah ya baki hakuri nikam bazanyi fada dake,
Tsaki samha tayi sannan tace mu tafi ka mayar dani gida, sahib ya matsa kusa da ita sosai, sannan yace kiyi hakuri don Allah mu kwana anan da safe sai muje training kuma zan kaiki kiyi yawo sosai daga nan sai mu dawo muyi zamanmu anan zan miki labari mai dadi ya karasa maganar yana murmushi, dan bayasan samha ta tafi dan lallai idan har taga farida zata iya fadawa samha komai shi kuma bayasan a wargaza masa shiri,
Samha tayi shiru sahib yace ko kin daina so na ne? Kallonsa samha tayi sannan tace A, a, ina sanka mana murmushi hydar yayi sannan yace zo muje sama to, idanuwa samha ta zaro sannan tace sama fa kace? Hydar yace Ey mana hydar bayanan yayi tafiya ne tun lokacin daya fito ina shara kuka gaisa? Ai yana komawa yayi fitarsa,
Samha tace ta ina ya fita ne? Hydar yace muje in nuna miki wurin ki gani, yana fadin haka yayi gaba samha tana bin bayansa cikin tsoro, tana cewa ai dazu daka tafi wallahi duk tsoro ya kamani shi yasa na zauna a waje, sahib yace tsoronmi? Samha tace kada hydar yazo, sahib yace tsoron hydar kikeji ne? Samha tace A, a, tsoron irin barin jinin da zanyi a gidan nan dan naso yazo yamin zance banza in sauke kansa kasa, kalli nan kaga ikon Allah ta daga gefen rigarta, wukace daure a kugunta cikin kubenta,
Sahib yace waike bana hanaki yawo da wuka ba bazaki daina ba ko? Murmushi samha tayi sannan ta kalleshi tace haba sahib, ina da abokin gaba zanyi sakaci? Kasan abokin gaba kullum cikin shiri yake so kake a mameni? Ai yana marina ko zagina kafin ya rufe bakin ko ya sauke hannu daya mareni saidai yaji wuka ta shige cikin bakin tabi ta makoshin sa, ko kuma in sauke hannun daya mareni dashi, tana maganar tana nunawa, da hannunta yanda zatayiwa hydar,
Murmushi yayi sannan yace bani wukar, samha tace gaskiya bazan bayar ba tana boye wukar a bayanta, sahib yace ba nace ki bani wukar nan ba? Yayi maganar cikin kakkausar murya, samha tayi shiru hydar yace idan kika bari na sake magana wallahi saina mareki, yanda yayi maganar ne yasa ta mika mishi wukar tare dayin gunguni tana murguda bakinta tana hararar sahib, tsareta yayi da idanuwanshi duk sai taji tsoro ya kamata dan haka ta dukar da kanta kasa, sahib yace wato zaki kashe hydar ko? Wai dan Allah miyasa kika rainani ne?
Samha tace nifa bakai na raina ba, sahib yace to wa kika raina idan ba ni ba? Samha tace nifa ba dakai nake fada ba, sahib yace dani kikeyi fada mana tunda kina fada da ubangida na, da baki rainani ba idan nace ki daina abu saiki daina amma da yake kin dauke wani lusari sai maganar tabi ta bayan kunnenki ta wuce ko? Turo baki samha tayi amma batayi magana, tsoki hydar yayi sannan yace wuce muje, samha tace nima daga yau bana san ana min tsoki, murmushi sahib yayi amma baiyi magana ba, yayi gaba samha tana bin bayansa,
Ya salam abinda samha ta fada kenan, tana kara waiwaye waiwaye tana kallon dakin gaskiya dakin ya hadu, haka tayi ta kyauyanci tana kalle kalle, shi kuma hydar yana gaban wedrof yana kashe wayarsa dan kada ayi ta kiransa gaban samha, juyawa samha tayi ta nufi wurin, da sauri ya rufe yayo wurinta kafin ta iso, murmushi samha tayi sannan tace sahib insha Allah saina gina mana irin wannan dakin,
Sahib yace kiyi addu'a ni inyi mana wanda yafi wannan insha Allah, samha tace a haka zaka gina mana gida mai kyau kullum kazo kayi tsugunne kasan hydar? Taci gaba da cewa kawu yace babana ya bashi kudi masu yawa ya bani amma wai kudin sun bata kaga idan aka gano kudin ya bani sai inyi mana ginin gida mai kyau sauran kudin kuma sai kayi kasuwanci kaga daga nan sai mu dauko mama mu dawo da ita wurinmu ni zanci gaba da kula da ita insha Allah, wai lokacin da hydar zaiyi tafi zuwa *switzerland* ai cewa yayi ma samha zaije kauye ganin mamansa bata da lafiya ita kuma ta siyar da gidan kawu ta bashi kudin, towai idan sunyi aure maman za'a dauko a dawo da ita wurinta ita tana kula da ita,
Murmushi hydar yayi cikin kwantar da murya yace kai amma nagode sosai samha, kuma nasan mama zatayi farin cikin kasancewa dake insha Allah, samha tace in Allah ya yadda,
Hydar yace jeki kiyi wanka, samha tace tom, nuna mata toilet yayi ita kuma tana cewa ta ina hydar ya fitane? Sahib yace gama wanka zan nuna miki, samha tace to wane kaya zan saka? Hydar yace zan baki cikin lefen da hydar ya hadawa matarsa, dariya samha tayi sannan tace fasa auren tayi ko? Ai babu mai iya zama dashi ga zuciya ga nuna shi wani ne, sakarai ai wallahi saina rama abinda yake min yana shafamin wani abu a ido sahib kasan inda yake ajiyewa? Sahib yace A, a, ya za'ayi in sani tunda ba dakina bane? Samha tace wallahi abun nan zafi gareshi don Allah kayi mishi wayau ka gano min abun in lallaba in saka mishi a ido yaji yanda nakeji,
Hydar yace to zan gano miki amma idan ya gane nashi ne ya zance mishi? Murmushi samha tayi sannan tace barni dashi nine zan sane a jikinsa, murmushi sahib yayi sannan yace ni kuma idan har kikayi sata a jikin hydar ba tare daya sani ba, wallahi zan baki naira miliyan daya, idanuwa samha ta zaro tare da cewa a ina zaka samu? Sai yanxun hydar ya dawo hayyacinsa ya gane shi ba hydar bane, yace swry i mean zan baki 1k,
Tsaki samha tayi tare da cewa kaima an fara koya maka wannan karyar, adaidai lokacin data shige toilet, tana shiga hydar yayi dariya tare da zama gefen gado, lallai bari yaga idan har samha zata iya daukar wani abu a jikinsa, idan kuwa har tayi sane a jikinshi lallai samha ta shahara kuma ta kware wurin iya sata,
Samha bayan ta gama wanka towel ta dauro sai ta saka hijabinta sannan ta fito, hydar ya nuna mata kusa dashi ta zauna, inda ya ajiye kayan da zata saka ya nuna cewa gasu nan, naje masallaci sai nayi isha'i zan dawo, samha tace a dawo lafiya, yace yawwa sannan ya fita,
Hydar na fita samha ta tashi ta matsa jikin mirrow a bayyane tace sakarai ji don Allah saikace wata mace mtswww, mai ta shafa da powder tana cewa saina fesa turarenka munafiki turare ta dauka tayi ta fesawa saida taji ya kare sannan ta ajiye ta dauki wani ta daga shi sama tana fesawa tana fadin nasan zakaji bakin ciki idan kazo kaga kadan daga cikin aikin samha saida ya kare sannan ta ajiye ta dauki na ukku, ta fara feshewa sahib ya fado mata a rai tace kada kuma fa yazo ya wulakantashi, da sauri ta maida ta ajiye, inda hydar ya ajiye kayan taje ta dauka ta saka sannan ta fara sallah,
Hydar kuwa a masallacin cikin gidanshi yaje yayi sallah saida akayi isha'i bayan sun gama sallah yace su shamsu suje su kawo mishi kawu yanxun,
Ranka ya dade mutumin nan fa aure za'a daura mishi da samha, idanuwa hydar ya zaro tare da dafe daidai zuciyarsa ya maimata aure? Eh ranka ya dade, hydar yace waye zaiyi musu auren? A wurin dangin babansu shamsu ya fada,
Innalillahi wa'inna ilaihir raj'un hydar ya fada yana kokarin mikewa amma ya kasa tashi, a hankali ya koma ya zauna sannan yace a ina ahalin samhar suke ne? Kuma kai waye ma ya fada maka zaiyi aure da samha ne? Cikin ladabi shamsu ya fiddo i.v din bikin kawu da samha ya mikawa hydar tare da cewa Allah ya huci zuciyarka mai gida, dan idan hydar yana cikin zuciya abun babu kyau,
Ansar i.v din hydar yayi ya duba, lallai da gaske aurene zasuyi nan da sati daya, wasu aljannun hawayene suka zubo daga idon hydar, ya kalli Alale yace kalli, lallai wuri fa ya kuremin, Alale yace wuri bai kure maka ba mai gida,
Gyara zama hydar yayi sannan yace Alale kada ka manta samha bata san hydar bata kaunar hydar ka fadamin taya zata amince da bukata kafin kwana bakwai? Abinda na lura samha tana da zuciya idan ta tsani abu ta tsaneshi kuma idan tace abu ta tsaya akanshi tana da tsatstsaun ra'ayi, kuma ka taba ganin inda aka hada kiyayya da soyayya? Cin tausayi Alale ya duka kusa da hydar sannan yace mai gida kayi hakuri ka fadawa samha cewa hydar yana santa kaji abinda zata ce maka,
Murmushin karfin hali hydar yayi sannan yace wallahi bazata so hydar ba tana ganin sahib, shamsu yace mai gida kawai kaje a daura maka aure da ita daga nan saiyi bala'in da za'ayi, kallonshi hydar yayi sannan yace so kake tabi dare ta kasheni?
Haka dai yaransa sukayi ta fada mishi mafita domin gaskiya suna tausawa hydar halin da yake ciki, kamar akan samha ya fara soyayya gaba daya duk ya wani bi ya haukace,
A hankali hydar ya dafa bango ya tashi Alale yana cewa ranka ya dade a dauko kawun ne? Hydar yace bana bukatar ganin sa kawai ya fadamin inda zanga dangin samha, kuma wane ma jakine zai daura musu aure idan banda suke mahaukata? Ya gudu musu da diyar dan uwa kuma sai yaje a daura musu aure su kuma su biye masa suyi musu aure ba tare da sunga samha ba?
Wannan jakancin ne da rashin sanin darajar dan dan'uwa, ace diyar dan uwanka an gudu da ita tarin shekaru masu dama, amma kuma aje maka da bukatar aurenta sai kuma kawai su anshi bukatar kawu?
Tsoki hydar yayi ba tare daya sake cewa komai ba ya nufi ciki, da tafiya mai sauri ya shiga cikin farlon ya fara hawa tsep din benen farlon da gudu harya isa dakin daya bar samha,
Yanda ya shiga dakin yasa samha mikewa da sauri tare da cewa lafiya? Ajiyar zuciya hydar yayi sannan yace samha zo kiji wata magana, da sauri samha ta matso bakin kofar dan hydar bai shiga cikin dakin dukansa ba hannunsa daya yana rike da handile din kofar, cikin tsoro ta matso kusa dashi sannan tace miye?
Rike hannunta hydar yayi sannan yadan matse shi kadan ya daga hannu sama daidai kirjinsa ya dora hannunta da nashi daya rike hannunta, sannan yace samha,
Cikin zakuwa samha tace wai miye don Allah? Hydar yace kinsan abinda nake so dake? Samha tace A,a, jan hannunta yayi suka shiga cikin dakin a gefen gado suka zauna har yanxun yana rike da hannun samha a nashi,
Samha tace wai miye kasa gabana sai faduwa yake yi, ko m card din kuma ya bata? Da dayan hannunsa ya dago habarta tana kallon fuskarsa sosai sannan yace samha wata alfarma zan roka Allah yasa zan samu,
Murmushi samha tayi sannan tace haba sahib ai duk abinda kake so daga gareni kada ka wani tsaya jin shakku ko fargaba kawai ka fada kanka tsaye ni kuma zan maka koma miye matsawar bai sabawa Allah ba, ajiyar zuciya hydar yayi sannan yace kinyi al kawari ko? Jinjina kai samha tayi sannan tace nayi maka alkawari ta karasa maganar tare da sassauta kallon ta ma'ana ta rage girman idanuwanta tayi kallon have corent ta zuge idanuwan, yanda tayi abun yayi mata kyau sosai,
Murmushi hydar yayi sannan yace samha kin yadda sahib yana sanki sosai ko? Murmushi tayi sannan tace shakka babu, hydar yace idan nace miki hydar yanamiki fiye da san da nake miki zaki yadda? Murmushi samha tayi sannan tace inajinka, hydar yaci gaba da cewa inajin fa hydar yana sanki ne samha, murmushin karfin hali samha tayi sannan tace,
Sannan tace nawa hydar ya baka harka manta dani a cikin zuciyarka? Wato kudi ya rudeka har zaka manta da soyayyarmu ko? Dan tsabagen hauka shine zaka tunkareni kana min maganar hydar? Shi yasa tun wuri nace maka mubar gidan sa, duk duniya babu abinda na tsana irin hydar bana san hydar bana kaunar hydar Allah ya tsinewa hydar albark... bata karasa ba sahib yayi mata wani irin azababben mari da sauri samha ta mike tana rike da wurin da hydar ya mareta hawaye na zubowa da idonta kallon sahib tayi sosai sanan tayi murmushin takaici tace sahib nika mara saboda hydar? Sahib yace naje na mareki bana ce kidai na zagin hydar ba?
Samha tace yanxun hydar yafini matsayi a wurinka? Hydar yayi shiru, samha tace dakai nake magana kayi wani kamar bakajina, hydar yayi shiru yana kallon samha cikin wani irin yanayi, goge hawayen idonta tayi da bayan hannunta sannan ta juya ta dauki kayanta data cire ta nufi toilet, ajiyar zuciya hydar yayi sannan ya shafa kansa, ya saka dan yatsansa a bakin sa yadan ciza shi kadan, a zuciyarsa yake magana, shifa ya kawo samha gidan nanne dan ya koya wa zuciyarta san hydar ya kuma zatayi mashi haka ne? Dama ya sani tun farko baizo a matsayin sahib ba, yanxun da komai ya zama labari Yana tunanin ne samha ta fito daga toilet,
Ta mayar da kayanta data cire wanda ta saka suna a hannunta ta linkesu, tana goge hawayen idonta, hydar yace ke miye haka ne? Waike samha baki san wasa ba? Batayi magana ba, ta ajiye kayan data cire a gefen gado sannan ta dauki nikaf dinta tayo hanyar fita, a gigice hydar ya riketa yace samha miye haka? Ina zakije ne? Nifa wasa nake miki kiyi hakuri don Allah,
Kara goge hawayen idonta tayi sannan tace dan nazo gidan nan zakai min wulakanci ne? Saboda ina sanka shi yasa kake min yawo da hankali ko? Hydar ya jawo samha jikinsa sosai sannan yace kiyi hakuri insha Allah bazan sake ba, gyara baki samha tayi amma batayi magana ba, hydar yayi ta bata hakuri tare da tayata zagin hydar tunda yaga hakan yana mata dadi, murmushi samha tayi sannan tace nayi,
Jan hannunta yayi har bakin gado sannan yace ta kwanta, kwanciya tayi yaja bargo ya lulubeta sannan ya durkusa saman guyawunsa a bakin gadon daidai fuskar samha yace samha, ina sanki sosai, murmushi samha tayi sosai sannan tace nima ina sanka sosai sahib,
Daidai zuciyarta ta taba sannan tace, nagode miki zuciyata kinmin adalci da kika sani na yadda naso mai inganci kuma so guda daya wanda babu hadi kuma so mai "yanci na tabbata gamona dakai alkairine sahib, ka rabani a gidanka anan kadai nakejin zan samu natsuwa, sahib dan Allah kada ka barni wallahi ina sanka kuma duk abinda hydar zai baka kada ka yadda ya rabamu nayi maka alkawari ni zan sama maka babban farin ciki a rayuwarka, murmushi hydar yayi cikin karfin hali sannan yace,
Haduwarmu nida dake silarta soyayya ce, na dade ina neman na samu burinki duk wanda yaso aka soshi yai babbar nasara tunda kin soni da gaske nima bani barinki, samha bazan iya kwatanta miki yanda nakejinki a raina ba,
Dan kin zamo min wani sashe na rayuwata idan har ina cikin farin cikin inajin nishadi sosai idan inayin fushi akamin maganarki inajin natsuwa samha, dan kin zamar min sinadirin rayuwata, tunda nake samha ban taba soyayya ba sai akanki, amma bance miki banda "yan mata ba, ina dasu sosai amma kwata kwata babu maganar aure yanxun a rayuwata, amma idan kin yadda kina so na, insa a daura mana aure dake nan da sati daya?
Murmushi samha tayi sannan tace na yadda zan aureka, amma kamin alkawari zaka samanin ahalina, murmushi hydar yayi sannan yace kada ki damu insha Allah zan hadaki da farin ciki sosai samha, murmushi samha tayi sannan tace na gode, mikewa hydar yayi sannan yace saida safe, samha tace saida safe, da sauri hydar ya fita daga dakin yana fita ya rufe kofar,
A farlo ya zauna saman kujera sannan ya kirawo faruk a waya bayan ya dauka suka gaisa yace faruk kaji yanda mukayi da samha kuma? Faruk yace A, a, hydar yace kaga nazo da ita gidan nan ne kawai dan in samu in koya ma zuciyarta so na, amma sai naji wani bakon labari wai zatayi aure da kawu,
Na sameta kai tsaye nace mata inajin hydar yana santa, kaji yanda take tsinemin albarka? Dariya faruk yayi sosai sannan yace lallai abun mai girma ne, shima hydar dariya yayi sannan yace amma kasan yanda nace mata? Faruk yace A, a, hydar yace nace mata ta yanda inyi aure da ita nanda sati daya?
Faruk yace toya tace ne? Hydar yace cewa tayi ta yadda, amma in sama mata ahalinta, faruk yace lallai akwai daru sosai ya za'ayi ayi zaman auren nan hydar? Dariya hydar yayi sosai sannan yace yanda na koyawa zuciyarta san sahib haka zan koya mata san hydar, faruk yace kada ka manta zaman aure daban lokacin ba'ayi aure ba daban, hydar yace kada ka samu damuwa, sai Allah ya kaimu gobe zamu hadu, faruk yace Allah ya bamu aron rayuwar,
Yau duka zuciyoyi biyu na masoyan sunyi bacci ne cikin jin dadi, samha tana jin dadi zatayi aure ta samu mai kula da rayuwarta ta huta da sace sace da gogayya da maza, hydar kuma yanajin dadi zai daura aure da samha bata isa ta gudu mishi ba, tunda aurenta akanshi babu idan zataje idan kuma akayi auren to lallai yasan dolenta zata hakura,
Da safe bayan hydar yayo sallah ya dawo a farlo ya zauna yayi karatun Qur'ani sai 7:04am ya ta tashi yaje ya ajiye Al'Qur'anin inda yake ajiyewa, sannan ya nufi dakin da samha take, tana kwance tana bacci, kusa da gadon ya matsa sannan ya tasheta yace tayi wanka zasu fita,
Da sauri ta sauko daga saman gado tana cewa kai? Na kwana a gidan mutane, halan da hydar yazo ya yace ne? Tabe baki hydar yayi sannan yace dadi yaji ya ganki kina bacci a gadonsa, murmushi samha tayi sannan tace nasan yaji bakin ciki a ransa, hydar bai sake magana ba,
Yace ni yanxun dai hydar ya aikeni ne, dan haka faruk zaizo ya tafi dake kije wurin trainging idan na dawo zanzo in taho dake, samha tace to saika dawo hydar yace yawwa, yana fadin haka ya fice, hydar yasa a tafi da samha ne tunda ta saba fita kullum kullum dan tayi nishadi hydar yace taje tare da faruk,
Daga saman benen yabi wata hanya ya sauka kasa, sannan a sake hawan wani ya nufi wani dakin bacci, shima dai dakin an kayatashi sosai yafi wanda samha ta kwana a ciki kyau da kuma tsaruwa, yana shiga jallabiyar jikinsa ya cire ya nufi toilet, wanka yayo ya fito da rigar wanka a jikinsa karamin towel a hannusa yana goge jikinsa, da sauri ya isa wurin wayarsa dake ringing, faruk ne, dauka yayi tare da sallama, faruk yace gamu fa munzo, hydar yace nima yanxun nan na fito wanka bani samha,
Faruk ya mikawa samha wayar ta ansa, yace albishirinki? Samha tace goro kuma fari ƙaƙal sahib yace naga hydar ya fita da abinda yake miki zalinci dashi dariya samha tayi sannan tace zan sane shi, dariya hydar yayi sannan yace to saina dawo, samha tace yawwa, kashe wayar yayi sannan yace dani dake yau zanga kwarararre,
A bangaren samha kuma hangowa takeyi ga hydar nan da zugarsa yana gaba suna binsa, tunani ta farayi ta ina zata fara? Wata zuciyar tace mata ta bayansa zaki zagaya hannuwanki biyu duk ki saka a aljihunsa, wata zuciyar tace idan kuma ba a aljihun wando ya saka ba fa? Kallon faruk tayi tare da cewa kiramin sahib don Allah,
Bayan ya kira hydar ya fada mishi cewa samha zatayi magana dakai, hydar yace bata, tashi tayi daga kusa da faruk sannan tace sahib wane irin kaya hydar ya saka ne? Murmushi yayi sannan yace bazaki gane shi ba? Samha tace ina ganeshi mana kawai dai inji idan masu aljihu da yawa ne ya saka, jinjina kai yayi sannan yace kayan training ne a jikinsa, samha tace suna da aljihu ne? Yace Eh aljihu biyu ne daya a gefen haggu daya a gefen dama, samha tace to kayi sauri kazo kada kuma ya ganeni yayi min duka, yace to, kashe wayar samha tayi sannan ta mayar wa da faruk ta zauna tana jiran zuwan hydar,
Bata dade da zama ba sosai motocin hydar suka fara shigowa ji tayi gabanta yana faduwa cikin tsoro ta kalli faruk sannan tace sahib ya taho ne? Murmushi faruk yayi sannan ya dauke kanshi tare da cewa nima ban sani ba, tashi yayi ya nufi inda hydar yake fitowa daga mota,
Hydar na fitowa ya fara gaisawa da mutane, da wutsiyar idonsa yake hango samha, fuskarsa dauke da murmushi yayi inda take zaune, tana ganin hydar ya taho ta mike da sauri lokacin daya iso wurin tare da cewa ina kwana, hydar yace lafiya qalau gani nazo kince zaki sace abinda nake saka miki a ido kina iyawa ko? Gaban samha ya fadi a ranta tace shi wallahi sahib baida rufin asiri komai saiya kwashe ya fadawa hydar? Hydar ya tsinke tunaninta ta hanyar cewa kinyi shiru ko har kin karaya ne?
Cikin dakiya samha tace Eh nace zan sace idan baka daina sakamin a ido ba, fiddo abun yayi sannan yace kin ganshi ko? Kalli a inda zan mayar dashi anan na ajiye kin gani ko? To zoki dauka? Murmushi samha tayi sannan tace idan na tashi dauka ai ba shawara zanyi dakai ba amma tunda naga inda ka ajiye zaka iya tafiya abinka,
Ba tare da hydar yayi magana ba ya juya yayi tafiyarsa abinsa, yana tafi samha tayi dariya tare da kallon abun a hannunta, tace jaki harna dauka bai sani ba, lokacin daya matso kusa da ita yace ya saka a aljihu, a lokacin da take bashi amsa a lokacin ta saka hannunta a aljihunsa tana magana tana kallonshi harta dauka hydar bai sani ba,
Bayan hydar sun gama abinda suke sun fito, ko inda samha take bai kalla ba ya shige mota suka tafi, saida faruk ya tabbatar sunkai gida sannan ya dauki samha suka tafi,
Lokacin da faruk sukaje hydar har yayi wanka ya canja kaya ya fito sahib yazo farlo ya kashe saman kujera 2seater yayi kwanciyarsa, a bakin farlo faruk ya tsaya samha ta fice daga motar shi kuma faruk ya wuce da motar danyi parking,
Da sallama samha ta shiga cikin parlourn sahib ya amsa tare da cewa na rigaki dawowa, dariya samha tayi sannan ta isa inda yake kwance, tashi yayi zaune yadan jirge saman kujerar kafarsa daya saman hannun kujera yana kalon samha cewa wallahi na gaji sosai, zama samha tayi kusa dashi sannan yace ni kuma yau nayi sane a aljihun ubangidan ka, fiddowa tayi ta nunawa sahib ya kalleta tare da bude idanuwansa yace ya akayi kika daukeshi?
Samha tace bana fada maka ba saina dauka, murmushi yayi sannan yace na tabbata a lokacin da kika dauka hydar ya jiki kyaleki yayi, samha tace wane shi? Idan ina sane a jikin mutum baya taba sani saida idan ya tafi yayi ta wasiwasi, hydar yace A,a yajiki dan naji yana fadawa faruk wai a lokacin da kika matsa kusa dashi a lokacin kika saka hannunki a aljihunsa shi kuma dayafi kwarewa sai yayi miki vidio kalli ki gani adaidai lokacin da yake nunawa samha,
Idanuwa samha ta zaro sosai sannan tace kai wannan mutumin shegen wayau ne dashi sahib yace ai kema kinajin kina da wayau ko? Samha tace waye ya turo maka kai kuma? Jingina bayansa yayi da kujera sannan yace yanxun ya turo min a whatsapp yace wai in kalli matar da zan aura har yanxun baki daina sane ba,
Samha tace don Allah kayi hakuri tunda ai na fada maka, kawai dan ka bashi kunya sai kace mishi naje nayi, sahib yace babu ruwana, kema kin fadamishi da kanki, samha tace aiko ban fada kaima saika fada ni kana bani mamaki duk maganar da nayi dakai sai ka wani zagaye kaje kana fadawa hydar haka zamuyi aure kullum kana tona mana asiri?
Murmushi yayi sannan yace aida hydar din za'ayi zaman aure, samha tace ban gane ba? Hydar yace umm zaki gane bari ayi auren, samha bata kawo ma kanta komai ba, dan haka tayi diff bata sake cewa komai ba, wayar hydar tana hannunta tana lallatsawa, shi kuma hydar ya gyara kwanciyarsa ya fara bacci,
Bikin samha da hydar ya rage saura kwana biyu kuma hydar yaje ya kutsa yaci uwar kawu ya tusa keyarsa gaba yaje yakai hydar wurin ahalin samha, hydar yayi ma ahalin samha well peryar na kudi yayi barin kudi hydar baisan darajar money ba, su kuma banzaye anga kudi an rikece babu mai maganar a kawo samha, saboda rashin adalci dan anga mahifinta baya raye basa binciken hydar suga ya kamata su aurar da samha a gareshi ko bai dace a bashi samha ba, babu wanda yace hydar daga ina yake, sudai kawai kudi hydar ya lura da hakan dan haka ya balle bakin banki yayi tayi musu dukan rashin mutunci da kudi ya firgitasu ya gigitasu ya haukata su su kuma sukayi ta ihu sai hydar, haka suka yankawa hydar sadaki wai naira miliyan daya a haka hydar ya bada sadakin samha, tun a gaban hydar aka raba kudin sadakin aka bawa kowa kasansa, da hydar ya tafi saida yayi kuka tare da tirr da hali irin na ahalin samha,
Samha kuwa bata san abinda ake kullawa ba, itadai tasan kawai zatayi aure da sahib, kuma ya fada mata baida halin wani farty ko lefe, samha tace ita babu komai, dan burin samha kawai ta wayi gari ta ganta a gidan sahib a matsayin matar aure,
Kawu ya bawa hydar wasikar da haifin samha ya bashi amma ya rantse cewa babu kudin nan da babanta ya bayar kuma duk sace sacen da yasa su samha da yusra da kausar babu ko sisi,
Hydar yace tou idan dai samha ta yafe mishi shikenan idan kuma bata yafe mishi ba tou wallahi ya shirya biyan ta hakkinta, yanxun dai hydar kokari daya shine wanda suka kashe maman samha kadai yake nema, kuma yasa anyi azabawa su wawu amma magana dayace basu san inda suke ba, amma suna waya dasu kuma sune suke kiransu kullum da sabon layi idan har suka kira hydar zasuyi magana dasu,
Kam cakwakiya kenan lallai samha zatayi wa hydar rashin mutunci, yau ake daura aurenta da hydar wannan wane irin rainin hankaline? Shin wai yama za'ayi zaman auren? Bayan samha bata san hydar tou pha, bari inji in zungurawa wayana chargy kafin a shafa fatiha mu gani,
Kam lallai yanxun aka fara muguntar so dan hydar yayi alkawari yanda zuciyarsa ta horu da san samha shima saiya koya ma zuciyarta, niko nace anya zaka iya hydar? 🤔 muje zuwa,
*Meelat Musa ce*
[05/04 4:45 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*Allah sarki fadeela lamiɗo na gode sosai da kulawarki a gareni Allah ya kara basira da hazaka ubangiji yasa a kammala DAUKAN FANSA lafiya, nagode sosai na gode, na gode, na gode, sai munyi waya insha Allah, masoyan littafin DAUKAN FANSA ina muku fatan alkairi ni meelat musa nake cewa asha karatun lafiya,* 🤝🏻
*Gaisuwa gareku*👇🏻
*Saffa One*
*Asma'u Abubakar lolo*
*Ayush Munka'ill Akash*
*SO*
*MUGUN WASA*
*Dedicated to* 👇🏻
_Ramlat Abdulrahman real mai dambu_
*38-40*
Samha yaune daurin aurenmu har yanxun kina so na ko kin canja ra'ayinki akaina ne? Sahib ne tsaye a gaban samha yake mata magana,
Murmushi samha tayi sannan tace ina sanka har yanxun kuma ban tunanin akwai ranar da zan canja zuciyata daga sanka da takeyi, ina sanka sosai kuma na godewa zuciyata sosai ta karasa maganar tana murmushi,
Murmushi sahib yayi sannan ya zauna kusa da samha, yana cewa amma fa ni ban fadawa "yan uwana ko daya ba, babu wanda yasan zanyi aure tunda kinga mamana bata da lafiya idan har mutane sukaji zanyi aure zasuyi ta surutu sosai akaina,
Kuma nasan duk wanda yaji zanyi aure babu wanda zasufi jin haushi irin dangin mamana, murmushi samha tayi sannan tace miyasa zasuji haushi ne? Hydar yace zaki gane sai nan gaba ya karasa maganar yana murmushi,
Samha tace miyasa bazan sani yanxun ba? Tabe bakinsa yayi sannan yace yanxun wurin yayi sauri ne, amma kiyi hakuri insha Allah zaki fahimcenki, kamar yanda kika fada cewa kinaji a jikinki gamonki dani alkairi, samha alkairi ne,
Ki saka natsuwa a jikinki, ki fahimceni duk runtsi duk wahala kiyi min alkawarin bazaki taba guduna ba, zuciyarki ta zamo mai adalci kuma ki zama mai tuna alkairi komai kankantar sa ki nisanta sharrin da wani yayi miki a zuciyarki kinji ko?
Murmushi samha tayi tare da jinjina kanta alamar gamsu, sannan tace sahib rainon dakamin ka koyawa zuciyata sanka karka canja halinka tunda ka sani zuciyata da ruhina na baka, bani da burin daya zarce inga harokaranka ma'ana farin ciki da annuri a fuskarka,
Murmushi hydar yayi mai ƙayatar da zuciyar samha, amma baiyi magana ba, yana kallonta, yadan dade idanuwansa na kan kyakkyawar fuskar samha, sannan yace samha sai magana na gaba, amma bansan yanda zaki dauki abun ba,
Samha tace miye? Murmushi hydar yayi da gefen bakinsa sannan yace kinga ban gama gyaran gidana ba, kuma banda kudi amma nayi wa hydar magana ya taimaka mana da wurin zama sai yace tunda bai cika zama gidan nan ba zamu iya zama kafin Allah ya bani iko inyi, dan Allah kiyi hakuri mu zauna anan kinji samha? Samha tace to sahib babu damuwa ubangiji ya baka iko hydar yace Amin,
Tashi yayi cikin farin ciki wata "yar rawa yayi tare yin wani dan tsalle yayi kasa a hankali tare da kwaso shoki, yanda yayi abun yayi mishi kyau sosai da yake yana da tsawo dan shoki tafi ma mai tsawo kyau, dariya samha tayi sosai, shi kuma da sauri yayi sama tare da cewa munje daurin aure sai mun dawo daga can zan wuce bazan dawo ta nan ba, samha tace to Allah ya tsare daga can hydar yace amin a daidai lokacin da yake sauka daga saman benen farlon da samha take yana hawa saman wanda zai sadashi da dakin dadyn sa,
Samha kuwa a hankali ta silale ta kwanta saman kujera tare da kara tuno rawar sahib dan abun ya burgeta sosai dariya tayi mai sauti sosai sannan tace wallahi sahib baijin magana murmushi tayi, sannan tace ikon Allah yau gani zanyi aure babu wani tsalle ko amarya ma babu mai kawo ni har na riga nazo gidan mijin dakai na, Allah sarki duniya, ko ina kawu bawan Allah shima fa yana sona kamar yanda sahib yake so na, hada rubuta suna na a kirjinsa, wayyo Allah kawu tun ina karama kake cemin 3 3 2, ni lokacin bana gane yaren,
Allah sarki kawu amma nasan idan kaji labarin aurena zakaji bakin ciki, dan gajeran tsaki samha tayi sannan tace canma kai ka sani munafikin Allah, ai ka cucuni kawu amma na yafe maka tunda ni na samu mijina zanyi aurena in huta abuna,
Hydar kuwa cikin farin ciki ya shiga daki jikin mirrow ya matsa da sauri ya cire fuskar ya dora a saman mirrow tare da cewa sahib zauna anan muje daurin aure mu dawo, cikin zumudi ya shige toilet babu dadewa yayo wanka ya fito, yana fitowa ya kira faruk tare da cewa kun tafi ne? Faruk yace Eh mana hydar yace to nima gani ina zuwa insha Allah, faruk yace kazo lafiya, da sauri hydar ya kashe wayarsa tare da ajiyewa a gefen gado,
Dariya kawai hydar yakeyi wani bangare na zuciyarsa kuma yana gargadinsa da lallai ya gama murnar da zumudin zaici uwarsa wurin samha, da sauri ya matsa jikin madubi ya kalli kansa murmushi yayi tare dayin magana a bayane yace haba da Allah babu wani damuwa insha Allah,
Saida ya gama shirinsa tsaf cikin manyan kaya ya hadu sosai yayi kyau na bada mamakiyos, masu karatu kuma basai na fada muku irin gayun hydar ba kawai ku tayani hango sa,
Bayan ya gama yayi murmushi a hankali tare da fara rerero wakar Aashiqui2 mashup, jikin madubi ya matsa tare da murza hularsa sosai, niko nace zakaci gidanku duk ka gama wake waken,
Yana gamawa ta baya ya fice abinsa inda motoci suke jiransa, yana fita yaransa suka fara kirarasa tare da kara bashi kwarin gwuiwa, budewa hydar mota akayi ya tattara babbar rigarsa ya shige aka rufe,
Suma saura shiga motoci sukayi gaba daya motocin suka fice daga gidan sai wurin taron daurin aure, tun zuwa motocin hydar kallo ya koma sama wai shaho ya dauki giwa, nan fa wanda suka san hydar suka fara kokarin matsawa kusa dashi tare da mika hannu dan su gaisa, kowa kokarinsa ya taba hydar yace ya gana dashi, masu fiddo waya suna daukar hotuna da hydar suna yi dan suje suce sun ganshi ido da ido suna yi, yaukam yaran hydar basuyi kokarin hana kowa ya rabi hydar ba saboda rana ce ta farin ciki a wurin sa,
Haka aka fara gabatar da taron daurin aure, tare da shedawa al'umma hydar ya biya sadakin auren sa da samha lakadan ba ajalan ba, bayan an gama gabatar da taron daurin auren hydar naseer hamza, da amaryarsa hafsat yusuf usman, an gama daura aure lafiya wuri ya cakume da hayani yayin da addu'ar zaman lafiya tare da masu addu'ar samun zuri'a dayyaba ya fara tashi a bakin al'umma,
Yayin da wasu mutane kuma suke ganin hydar yayi musu fadawa toti ruwa daya auri samha, wasu kuma suna ganin samha tayi babban nasara, kowa dai da abinda yake fada a bakinsa, bayan an kammala komai hydar da zugarsa suka nufo gida amma zuciyar hydar tana cikin fargaba dan baisan yanda zaman nasu zai kasance da samha ba,
Bayan su hydar sun dawo gida anan sukayi shagalinsu sosai shidai hydar baya ciki, yana can ya shige daki yana nemawa kansa mafita, yana kwance saman gado tunani barkatai a zuciyarsa wayarsa ta fara ringing,
Dubawa yayi ganin kanin dadynsa ne yake kiransa yasa shi tashi da sauri, daukar wayar yayi cikin girmamawa, tare da sallama suka gaisawa bayan gaisuwa yacewa hydar lallai ka nuna mana kai mai tarin dukiyane tunda ubanka ya mutu ya bar maka kaburin kudi yasa kayi aure ba tare da saninmu ba tunda kana ganin baka bukatar komai a wurinmu shi yasa kayi aure ba tare da saninmu ba,
Ajiyar zuciya hydar yayi sannan ya goge zufar data keto mishi a goshi sannan yace dady waye yace maka nayi aurene? Yace duniya ta fada ko kana tunanin yanda aka sanka zakayi abu a boyene? Murmushi hydar yayi sannan yace naje daurin aurene yau daya daga cikin yarana ne yayi aure shine ake ganin kamar nine, dady bayan nasan ka bani Asma'u ta za'ayi inyi aure?
Haka dai hydar yayi ta tsara dady shima dadyn da yake dabbal arab ne sai ya yadda tare da cewa haba ai nayi mamaki wallahi hydar dama nace gaskiya badai kaine ba, hydar yace gaskiya ne, haka dai sukaci gaba da fira daga baya sukayi sallama,
Bayan hydar ya gama waya da kanin dadynsa ya tashi tare da fara rage kayan jikinsa, babbar riga ya cire sannan ya cire takalmin kafarsa ya saka silipers ya nufi dakin samha,
Da sallama ya shiga dakin samha ta ansa tare da maido dubanta inda ake sallamar ganin hydar tayi dan haka ta jawo hijabi da sauri ta saka, fuskarsa a daure ya fara shiga cikin dakin a hankali harya isa bakin gadonta,
Zama yayi a gefen gado da sauri samha ta sauka kasa tare da gaishe shi cikin girmamawa ya ansa babu yabo ba fallasa, kallon samha yayi sannan yace zuwa nayi in miki Allah yasa alkairi, kan samha a kasa tace to mun gode sosai, hydar yace Allah ya baku zaman lafiya tace amin,
Mikewa hydar yayi jiki a sabule zuciyarsa sai suya takeyi mishi cikin wani irin yanayi, dan yaso ace dagashi har samha yau duk suna cikin farin ciki baki dayansu, amma baida yanda zaiyi dole yayi a hankali,
Yana fita daga dakin tabi bayansa da kallo tana cewa shege munafiki, ta fara yatsina fuska tare da fara kwaikwayon maganar hydar tana tabe baki, _zowa nayi inyi miki Allah yasa alkairi, Allah ya baku zaman lafiya_ tsaki tayi sannan tace Ai Allah zai zaunar damu lafiya insha Allah,
Kuma bari sahib yazo in fada masa kada ka sake shigo mana dakinmu, ko kuma ka ware mana inda zamu rika zama mtswww,
Hydar yana komawa daki duk jinsa yayi wani haggunce, murmushi yayi sannan yace wai tana gani na ta saka hijabi, komi take boyewa? Ya karasa maganar yana dariya, kayan jikinsa ya cire bayan ya gama ya haye gado yayi kwanciyarsa,
Ita kuwa samha bayan ta gama iskancinta na kwaikwayon maganar hydar tashi tayi taje tayi wanka bayan ta gama ta shirya cikin kayan da sahib ya bata ta saka,
Bayan ta gama shirinta tsaff ta kalli kanta cikin madubi tace Allah sarki samha ke kuma taki rayuwar haka tazo? Kowace "yar gata idan tayi aure kawota akeyi gidan miji cikin farin ciki "yan uwa da abokan arziki suna murna tare da masu addu'ar zaman lafiya, amarya tana kuka ana bata hakuri ana lallashinta cikin so da kauna, hawaye ya gangaro daga idon samha, sannan tace niko ban samu hakan ba,
Matsawa tayi kusa da wayarta ta dauka sannan ta fara kiran sahib, cikin bacci hydar yaji ringing din wayarsa dan haka a gajiye ya mika hannunsa ya dauka cikin muryar bacci yayi magana cewa, samha? Cikin kuka samha tace sahib kana ina ne? Da sauri hydar ya tashi zaune tare da cewa miye kike kuka? Goge hawaye samha tayi sannan tace nidai na fasa auren nan don Allah, hydar yace miyasa kika fasa ne? Samha tayi shiru tare da kashe wayarta,
Jin samha ta kashe wayarta yasa hydar saukowa daga saman gado da sauri, yana cewa ke yarinya wallahi karya kike yi nine zaki yi ma wasa da zuciya? Tsaki yayi sannan ya shiga toilet yayo wanka yana fitowa ya shirya, yasa kananan kaya, bayan ya gama ya dauki fuska ya saka tare da cewa aiki fa ya sameni,
Dan gajeran tsaki yayi sannan ya fita ya nufi dakin samha, ita kuma tana zaune a gefen gado sai kuka tayi, da sauri sahib ya shiga cikin dakin tare da cewa waye yace miki amarya tana kuka ne? Samha tayi shiru murmushi yayi a daidai lokacin da yake zama kusa da ita, jawota cikin jikinsa yayi sosai, sannan yace wai miye kike kuka ne?
Samha tace nidai gaskiya na fasa auren nan, dariya yayi sannan yace har kin karaya ne? Yaci gaba da cewa haba keko? Ina ke ina rabuwa da sahib? Ai kinzo kenan babu koma matacce ya tafi lahira, ko anyi miki wani abu ne? Girgiza kai samha tayi alamar A, a, hydar yace to kiyi hakuri don Allah ki daina kuka kinji samha?
Cikin kuka samha tace to gaskiya mu tashi daga gidan nan, hydar yace miyasa zamu tashi? A daidai lokacin da yake daga samha daga jikinsa, hydar yaci gaba da cewa kinga ki rufamin asiri muyi zamanmu anan samha da kudin da zan kama mana haya kinga sai in kara in siyawa mamana magani tunda Allah ya taimakemu an bamu aron gida,
Cikin tausayawa hydar samha tace to, amma tana san ta fadawa sahib yace ma hydar ya daina zuwa mata daki kai tsaye gaskiya amma kuma bata san yanda sahib zai fassara abin ba,
Haka dai yayi ta rarrashin samha yana kwantar mata da hankalinta, saida yaga ta samu natsuwa sannan yace ta tashi suje farlo, amma samha tace a, a, yayi juyin duniya amma samha tace A, a, ita kuma saboda hydar taki fita,
Ganin bazata fita ba yasa shi kwanciya a hankali ya dora bayansa saman gado kafafawunsa yana kasa ya jawo samha kusa dashi ya riketa yana sauke ajiyar zuciya, wanda shi kadai yasan abinda yakeji a zuciyarsa,
Samha tace har yanxun baka ga ahalina ba? Yace Umm samha tace to ina kawu? Hydar yayi banza bai bata amsa ba, samha taci gaba da cewa bawan Allah nasan yana can yana nemana yanxu, hydar baiyi magana ba, samha taci gaba da cewa sahib a kirjinsa ya rubuta suna na, da sauri hydar ya rufe idonsa, samha tace kaji sahib, hydar yace da Allah shiru mtsww, tabe baki samha tayi, hydar yace,
Waike baki san akwai babanci da lokacin da baki da aure da yanxun da kike da aure? Samha tayi shiru hydar yace to bakinki ya rufe akan maganar ko wane namiji na fada miki, batayi magana ba amma tana kallonsa, yace ke yanxun idan nazo ina miki maganar yan mata na zakiji dadi ne? Ko kuma idan nace su rike zuwa gidan nan fa, samha tace Allah ya baka hakuri,
Dan gajeran tsaki yayi sannan ya mike, yana cewa ni jibi tafiya zanyi zanje kauye ganin mama, kuma idan na tafi zan dade ban dawo ba, da sauri samha ta mike tare da cewa ai sai muje tare ko? Hydar yace kinmanta babu wanda yasan na aureki ne? A haka kike so inje dake ince musu ke wace ce ta?
Gyara baki samha tayi amma bata ce komai ba, hydar yaci gaba da cewa to kinga hydar yayi mana babbar halacci a rayuwarmu samha kada ki kuskura kiyi masa rashin kunya kada ki batawa hydar rai dan wallahi ban hada hydar da kowa ba, idan har kika kuskusra na dawo yace min kin masa wani abu lallai zakiga fushi na, kinsan bacin raina? Ya tambayi samha,
Samha tace bansan bacin ranka ba kuma bana so in sani har karsen rayuwata, hydar yace yawwa sannan kuma kije ki rika share masa dakinsa duk abinda yace yana so kiyi masa kuma kada ki kuskura ki sabawa duk bukatarsa akanki, kinji ni ko?
Cikin hayani samha tace wannan ai haukane, inace yanxun nan ka gama fadamin cewa akwai banbanci tsakanin da, da kuma yanxun da nake da aure, in banda hauka taya za'ayi kace inje dakin katon banza dan iska inyi masa shara? Sai kace wata karuwa? Hydar yace bazaki gyara kalamanki akan hydar ba ko? Samha tace wallahi bazan gyara ba, kullum saina bata dan iska katon banza harnan dakina ya shigo saboda jahiline harda zamarmin a bakin gado,
Cikin daga murya sahib yace yaje ya zauna ai gadonsa ne ba naki bane? Ko kece kika siya masa ne? Itama cikin tsananin bacin rai tace gadonsan banza idan yana san gadon yazo ya cire banzan abinsa ko ance mishi idan ban kwana a gado ba zan mutune? To ko a gidan kawu a saman katifa nake kwana da sauri ta cire hijabinta tare da cewa kalli jikina nunamin a ina jikina ya lalace ko akwai banbanci kyau din jiki tsakanin mai kwana saman gado da wanda yake kwanciya a katifa Mtswww,
Sahib yace wannan can matsalarki ne ba tawa ba, nidai na fada miki kuma wallahi idan har a dakin nan zai kwana zanga idan kin isa ki hanashi ya kwana shida gidansa, cikin kuka samha tace to wallahi ajali zai kawoshi dan zaka kaga yanda zanci ubans......bata karasa ba sahib ya kasheta da mari ya kara marinta saida yayi mata ukku sannan ya barta, cike da zafin zuciya itama ta daga hannunta ta watsa mishi mari cikin bacin rai hydar ya rike hannunta sannan ya sake faffaska mata mari yana cewa ke baki da kunya kamarni zaki daga hannu ki mara? Cikin kuka samha tace kamar kaidi mi? Ni ina ruwana da girmanka, hydar yace ke ni zakimin rashin kunya?
Cikin kuka samha tace kai bakasan ko ni wace ce ba? Ko jin kunyar marina bakayi ba? Ina matsayin matarka? Sahib yace ni ba mijinki bane amma dan rashin kunya kika daga hannu kika mareni? Yau kina cikin fushin Allah yarinya kin mari mijinki, goge hawayen idonta tayi sannan tace to idan nace bazan zauna dakai ba ai sai a goge zununbin hydar yace yanxun ma kin kara wani zunubin,
Tsaki yayi sannan ya fice daga dakin, yana fita samha taci gaba da masifa cewa in banda iskanci ansan gaskiya amma ana boye saboda san zuciya da tsabagen san abun duniya, komai hydar komai hydar sai kace wani babanka mtsww,
Cikin fushi hydar ya isa dakin shi, lallai samha ta raina shi, amma zaiyi maganin rashin kunyarta, Allah ya kaimu jibin lafiya,
Tunda daga ranar da samha tayi fada da sahib bai sake zuwa ba, kuma idan ta buga mishi waya baya dauka, ta tura sako babu reply, kuma ta nemi shi a gidan bata ganshi ba, tayi "yan koke kokenta ta gaji, Ranar da sahib zaiyi tafiya kamar yanda ya fada mata, text kawai ya tura mata cewa,
_Samha kiyi hakuri da rashin daukar wayarki da nakeyi, kuma bana reply sakonki, kinsan ina da matsar ciwon zuciya maimakon ki kwantar min hankali shine kike so ki kasheni ko? To idan baki sona ina da masu kauna na, wannan dalilin yasa nayi nesa dake dan ni ina san farin cikinki tunda ke baza ki iyamin biyayya akan abinda nake so, kuma ga hydar nan amana idan kika mishi ko kallon banza na dawo ya fadamin wallahi zakiyi mamaki yanda zanmiki, na tafi saina dawo idan kinga dama kimin addu'a idan kuma kinga haggu kada kiyi,_
Lokacin da samha taga sakon da sauri ta fara kiran sahib amma sai taji "yar inyamura ta cikin waya tace ayi hakuri wannan waya a kashe take, tashi tayi ta fito da gudu cikin 360 ta sauko daga saman benen ta saukowa parlo taga hydar zaune a farlon saman kujera, wani irin kallo yayi mata sannan yace "yan mata ina zakije ne? Ko inda yake zaune bata kalla ba tayi harya fita, tana taba kofar tajita a rufe ta jijjigata amma taji bata budewa, a hankali ta dawo zata wuce hydar yace ke zonan, samha tayi kamar bataji shi ba, tana kokarin hawa sama ya tashi ya nufi wurin da sauri,
Tsayuwa samha tayi tare da daure fuska sosai sannan tace bazan yafe maka ba, dan iska kaine kasa mijina yayi fushi dani ta karasa maganar hawaye yana digowa daga idonta, murmushi hydar yayi sannan yakai hannunsa saman lips din samha yace kai bakin nan naki ya iya tsiwa,
Bige hannunsa samha tayi tare da cewa kadai ji kunya kuma kayi asara wallahi tana kokarin juyawa hydar ya fizgota ya riketa a jikinsa sannan yayi mata wani irin kallo, yace niba sahib bane danni bana daukar iskanci ninan dakika ganni dokewa nakeyi inyi wa yarinya duka da bulala harsai tayi fitsarin wahala,
Samha tayi shiru hydar yace "yar rainin hankalu dan baki da kunya inajinki kina durawa uwata zagi dan babu manya a gidanku, daga yau idan na sake jin kin zageni saina lashe bakinki marar kunya kawai da Allah ni wuce muje ki mammatsa min jikina, ya karasa maganar cikin wata irin murya mai sa tsikar jiki ta tashi,
Yanda yakeyi mata wani irin kallo yasa ta sauke kanta kasa tana gunguni, hydar yace wuce muje, samha tace ni gaskiya ba "yar iska bace sai kace wata jaka inje in taba jikinki? Hydar yace ni babu wani ruwana ko kina iskanci ko bakyayi nidai jikina nake so kwai a shashsha famin, samha ta fizge hannunta daga hannu hydar da sauri ya rikota tare da cewa ke ki kiyayeni wallahi,
Shi dan iskan dazai tafi bai fada miki ba? Samha tace kaine dan iska ba mijina ba, dariya hydar yayi sosai sannan yace naji ni dan iskane ai kema sahib dan iska ne, samha tace gaka jibgegin dan iska, daure fuska hydar yayi sannan yace koni dan iska ne ko ba dan iska bane bai dameni ba muje, yaja hannunta yana sauka da ita daga saman benen,
Samha tana kwacewa amma ta kasa, ta fara tirjewa tana kuka daukarta hydar yayi sama har saman kujera sannan ya sauketa, gefen fuskarta yadan shafa sannan yace kina da kyau gaskiya lallai mijinki ya more, ga kyakkywar fata ya karasa maganar yana kashe mata ido,
Zama yayi sannan yace bari kiga inda zaki dan matsamin yana kokarin cire riga, da sauri samha ta mike tayi hanyar bene har tana faduwa dogon kallo hydar yayi mata wanda tana gudu amma yana zooming nata a idonsa harta shige daki ta rufe kofa da karfi, a hankali hydar ya kwanta saman kujera yana dariya,
Samha kuwa tana shiga daki ta fara kuka da gudu ta isa wurin wayarta ta dauka ta fara kiran wayar sahib dan ta fada mishi abinda hydar yayi mata wakar dai dayace ake rera mata cewa kiyi hakuri wayar a kashe take,
Saida samha tasha kukanta ta gaji, sannan ta ajiye wayar ta kwanta, bata dade da kwanciya ba bacci ya dauketa,
Saida samha tasha baccinta ta gaji sannan ta tashi tayi wanka, har yanxun bata daina kuka ba, harta shirya tasa kayanta kuka takeyi, saida tayi sallah isha'i sannan ta fita dan taci abinci tasan hydar yana masallaci,
Taje ta zauna saman dirning table ta fara cin abinci tana ci tana kuka, hydar ya shigo a haka ya sameta da wutsiyar idonshi ya kalleta ya wuce abinshi,
Itama batayi magana ba taci gaba da cin abincinta, saida ta gama sannan ta tashi ta nufi dakinta, tana zuwa ta rufe,
Hydar kuwa yana zuwa ruwa ya watsa sannan yasa jallabiyarsa yayi kwanciyarsa abinsa,
To kullum dai haka kowa yake rayuwarsa samha ta fito ta shige kicin ta dafa abinci taci ta koma daki shidai yana kallonta, babu gaisuwa tsakaninsu idan ta fito dai yana kallonta da wutsiyar idonshi,
Yauma kamar kullum hydar yana kwance farlo saman kujera 3seater samha ta sauko, tazo zata wuce taji yana waya cewa kai sahib ka kiyayeni idan ba haka ba zan wulakanta ka, kaidin banza waye kai? Ni ka daina wani bani hakuri dan banaji kuma bazanyi ba, nasan dai nayi maka halacci amma ka zama butulu, kamarni kazo ka ajiye min yarinya karama a gidan dan ta raina min hankali bazata iya gaisheni ba? Ta sameni a wurin bazatamin sallama ba? Yau kwananka nawa da tafiya dakina yayi datti dakaina kake so na share ne?
Hydar ya lunfasa zuwa wani lokaci yace to ni babu wani abinda ya dameni ka kirata ka fada mata da kanka idan kuma ba haka saidai kasan inda zaka koma kuma na koreka daga aiki daga yau na fada maka, yana fadin haka ya kashe wayarsa sannan ya tashi yayi dakinsa,
Samha dake zaune tana cin abinci dakel ta hadiye lomar bakinta da sauri ta ajiye cokalin hannunta, ta tashi ta nufi daki da gudu, tana shiga taji wayarta na ringing, cikin tashin hankali ta nufi wurinta da sauri gabanta yana faduwa, tana daukar wayar ta fara cewa sahib don girman Allah kayi hakuri kada kawani bata ranka munji ma dadi daya koremu sai muyi tafiyarmu mu samu gidan zama, gidan banza gareshi gidan wofi don Allah ka rufa min asiri kada ka bari ya rabamu da makircin sa,
Sahib yace da Allah rufe min baki wannan ai daukar alhakine, samha tace wane irin daukar alhaki kuma? Sahib yace saiki bar mutum ya zauna dakinsa da datti duk abinda kikeyi kije ki share masa na fada miki, sannan kuma yana so kiyi masa tausa to kiyi masa duk yana cikin aikin da nake masa idan ba haka ba zaki hadu da fushin zuciyata, cikin sanyi samha tace kayi hakuri ai bansan dakin ba, maganar masach kuma sahib bai kamata ba,
Sahib yace nine nake aurenki ko kuwa? Samha tace kayi hakuri, tsaki yayi sannan yace tashi tsaye, tashi samha tayi babu musu, sahib yace jeki jikin kofa, tafiya tayi har takai bakin kofa, sahib yace bude, budewa samha tayi sannan yace taho idan kin tafi sai ki shigo ta haggu, shiga samha tayi sahib yace yi dama samha ta shiga ya sake cewa kara shiga dama, shiga tayi sannan yace sauko daga saman bene,
Sauka samha tayi sannan yace kinga wata kofa mai golding ko? Tace Eh yace bude zaki ga bene tana budewa sahib yace hawo, hawa samha tayi sannan yace kiyi ta tafi zaki ga wata glass kofa har dakin hydar, idan kinje ki bashi hakuri sannan kuma ki gyara mashi dakinsa kinji ko? Samha tace to sannan sahib ya akashe wayarsa,
Tunda samha ta tunkari wurin takejin kamshin "yan gayu harta shiga, da sallama ta shiga, hydar yana kwance saman gado daga shi sai gejeran wando, da sauri samha ta juya a zuciyarta tace lallai hydar kwallon dan iska ne,
Daga saman gado yace ya akayi ne? Ba tare data juyaba tace mijina yace inzo inyi maka shara kuma naga dakin baiyi datti ba, hydar yace ai basai yayi datti ake sharewa ba, samha tace to kuma yace in baka hakuri, hydar yace ai idan mijinki yamin laifi ba haka yake bani hakuri ba, zo nan, samha tace ai naga babu kaya a jikinka ne, hydar yace ina ruwanki da kayana ko rashin kayana? Kedai ba hakuri aka ce ki bani ba? Gidana ne nan dole in zauna yanda nake so, kema ban hanaki ki fito da daurin gaba ba,
Samha tace aini ba "yar iska bace, hydar yace niko kinga dan iska ne ni shi yasa ma nake zama da gajeran wando abuna, samha tace to Allah ya shiryeka, hydar yace kai ba amin ba a barni da iskancina nafi jin dadi, nidai bani hakuri kafin zuciyata ta fara tsimama,
*Meelat Musa ce*
[05/04 4:45 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*Jinjina gareki ummu farhana marubuciyar littafin "YAR HIJIRA gaskiya aikinki na kyau, masoya brilliant kada ku bari a baku labarin littafin yar hijara nemeshi da kanki domin kisha karatunki abunki kada ku kuskura REAL MAI DAMBU ta baku labari*
*SO*
*MUGUN WASA*
*Dedicated to* 👇🏻
_Ramlat Abdulrahman real mai dambu_
*41-43*
Daga inda samha take tsaye tace shiru da Allah can, bayan ta lumfasa taci gaba da cewa dan uban zuciyar ta dade bata kumbura ba karewar tsimama, kaini harka fada min tsimamar zuciya da kangara?
To lallai ya kamata kasan labari akan mai girma samha, danni bana daukar shashanci kuma bana daukar iskanci, ka tashi kasa kayanka wallahi idan ba haka ba zan dauke ka hoto a haka in tona maka asiri na fada maka,
Dariya hydar yayi sosai sannan ya sauko daga saman gadon yayo tattaki zuwa gaban samha, da sauri ta rufe idanuwanta, hydar yace waike mai girma samha? A ina wani girma, bayan kuna kasana dake da mijinki duk a karkashin iko na kuke, baku da wani "yanci bare gata, baki ga saboda girmana da isa irin tawa ba yasa mijinki ya barmin ke dan in rike morewa abuna? Duk dama bakimin ba gaskiya naga idanuwanki irin na "yan chaina ne, basu da saurin daukar hankalin namiji ko kuwa kece baki iya sarrafasu ba?
Dakel samha ta hadiye miyan bakinta saboda bacin rai amma har yanxun idonta a rufe yake, hydar yaci gaba da cewa waike har kike wani cewa zaki daukeni hoto a haka dan ki tonamin asiri to daukarni mtsww, kawai dai nasan ba asirina kike so ki tona ba zakije ki ajiye a wayarki kina kallona kinajin dadi dan nayi imani sahib baida irin wannan kyakkyawan surar,
Cikin kuka samha tace tirr, tirr da hali irin naka kaiko baka dace da rayuwa ba, kaci baya kuma kayi asara, hydar yace waye yace miki naci baya? Kuma waye yace miki ni nayi asara? Ai duk abinda babbar giwa take dashi karama ma tana dashi duk kayan da babban jaki ya dauka karami ma zai dauka saboda dama dukansu dan wahala akayosu, kinga kamarke mijinki yarona ne tunda yana kasana dake dashi duk kuna a karkashi ikona, kimin shara ki dafamin abinci kuma ki bani a baki idan naga dama har wanka sai ince kimin kuma idan dare yayi a shinfida daya zan rika kwana dake ni kuma idan wata yayi inba sahib albashi mai yawa kinga daga nan idan ya gaji da samun kudin kuma ya gaji da ina hutawa dake sai ya gina gida ya tashi ya bani wuri,
Maza maza a cire hijabi a fara gyaramin gado, cikin kuka samha tayi bakin gado ba tare data cire hijabinta ba kuma batayi magana ba ta fara aiki, hydar yace ke wallahi baza kimin aiki da hijabi ba sai kin cire, tsaki samha tayi cikin daga murya tace bazan cire ba dan isk,........hydar yace wallahi duk ranar da gigi yasa kika zageni saina cire miki kaya nafada miki, idanuwa samha ta zaro sosai amma batace komai ba,
Matsawa hydar yayi kusa da samha sannan ya fara kokarin cire mata hijabi, jin hydar yace zai zindireta yasa batayi magana ba ta cire hijabinta da kanta, ta ajiye a gefe, taci gaba da aiki tana gyara gado tana tsinewa sahib albarka a ranta, shi dama hydar haka yake so yaga ya cusa kiyayyar sahib a ran samha, ita kuwa samha gani takeyi kwata kwata baiyi mata adalci ba taya za'ayi tana matsayin matarsa amma ya barta a gidan hydar saboda san abun duniya, sai kuka samha takeyi tana aiki shi kuma hydar ya jingina da mirrow sai dariya yakeyi a ransa,
Saida samha ta gyara dakin fes ta goge shi, sannan hydar yace saura farlo har yanxun gajeran wando ne a jikinsa, shine a gaba yana wata tafiyar iskanci, kan samha a kasa har suka isa farlo hydar yace duk kujerun nan sai an daga su an share an goge, batayi magana ba ta fara, shi kuma yana daga dirning area yana hangenta yana dariya a ransa,
Haka samha tayi ta jijjibar kujeru tana daga su kamar wata katafila saita dage ta share ta goge sannan ta mayar, haka tayi ta yi harta gama gyarawa, wurin hydar taje cikin girmamawa ta durkusa har kasa sannan tace na gama,
Yace maza a dafo abinci ba tare daya kalli inda take ba, a hankali samha ta mike ta nufi kicin saida ta gyara kicin din sannan ta dora girki, tana kicin tana aiki hydar yace a dafo min tea, samha tace to,
Ruwan zafin dake cikin flarks ta dauka ta juye a tukunya ta dafa shi, sannan ta juye a kofi takai ma hydar, kallonta yayi fuska a daure yace wannan tea din? Samha tace Eh, hydar yace har ya tafasa kenan ko? Samha tace ai na dazu ne na dimama, cikin daga murya hydar yace waye yace miki a dumama tea? Idan har aka dumama tea ya zama guba wato kasheni zakiyi ko?
Yi yayi kamar zai watsa mata ruwan zafin da sauri ta rufe idonta tare da kauda kanta gefe ta dora hannunta saman fuskarta, murmushi yayi sannan yace daukarshi ki shanye, cikin kuka samha tace ai yanxun nan kace idan an dunduma tea ya zama guba so kakeyi insha in mutu?
Hydar yace baki san mutu ne? Cikin kuka samha tace kayi hakuri don girman Allah, hydar yace kina so inyi hakuri ko? Samha tace Eh hydar yace to sai kinmin kiss saiki zaba ko kiss ko shanye tea sauri sauri saurii,
Tsaki samha tayi sannan ta mike ta dauki tea din ta kafa kanta duk zafinsa saida ta shanyeshi sannan ta daga kofin ta saddashi kasa alamar babu komai a ciki, dan zaro idanuwa hydar yayi a ransa yace wato yarinyar nan bazata canja ba, tabe bakinsa yayi a ransa yace wato gara ta mutu da ta taba wanda ba maharraminta ba, murmushi yayi a bayyane ita kuma samha tuni ta koma kicin taci gaba da aikinta,
Saida ta gama dafa abincin ta sake dafa tea din sannan ta juyo komai tazo ta ajiye a gaban hydar ta koma ta gyara inda ta bata a kicin, sannan tazo zata wuce hydar yace ina kuma zakije? Tace zanje in huta ne, hydar yace inake ina hutawa yarinya? Saura aikinki ukku bani abinci wanke min motoci sai kuma kiyimin wanka,
Da sauri samha ta duka saman gwuyawunta tace don girman Allah ka soke maganar wanka ka rufamin asiri don Allah, hydar yace wallahi bazan rufa ba, ni in rufa miki asiri sai kace wani banza? Nifa ba laifina bane laifin sahib ne shine ya hadani dake, cikin kuka samha ta matsa kusa da hydar ta rike kafafuwansa tana kuka mai tada hankali tana bawa hydar hakuri,
Amma da yake hydar tantirin dan iskane ko kallonta baiyi ba, ita kuma sai kare yage baki takeyi kamar anyi wa kura wurgi da nama, da wutsiyar idon sa ya kalleta sannan yace tashi, jikinta na rawa ta tashi yace jeki ki wanko hannunki, da sauri ta matsa ta wanke hannunta ta dawo, kallonta yayi sannan yace zauna, zama tayi babu musu hydar yace kince bazakimin wanka ba ko? Samha tace Eh, hydar yace to bani abincin inci da sauri ta dauki cokali girgiza kansa yayi alamar A,a, sannan yace da hannu zaki bani,
Hannunta tasa ta fara ibar abinci tana bashi a baki cikin iskanci yake hada hannun da lips dinshi yana dan rike hannun cikin kware ma iskanci yanda yakeyin abun yasa samha taji jikinta yana rawa, shi kuma sai kara daddagewa yakeyi yana yi cikin salon iskanci,
Haka dai samha taci gaba da bashi abincin yana ci, harya gama, sannan yace to jeki, jiki a sanyaye samha ta mike hydar ya gyara zaman sannan yace kullum haka zaki rika min kinjinko? Samha tace to, tana fadin haka ta wuce da gudu ta nufi daki, hydar kuwa dariya yayi mai isarsa sannan shima ya tashi ya nufi nasa dakin,
Samha kuwa tana zuwa daki wayrta ta dauka ta fara kiran sahib, dariya hydar yayi sannan ya dauka, cikin kuka samha tace wallahi sahib ka bani mamaki, banji dadin abinda kamin ba, cikin lallashi hydar yace samha kiyi hakuri kiyi biyayya wa mijinki ba'a sabawa idan ba haka ba zakici da wuta balbal,
Cike da masifa samha tace da Allah rufemin baki kaima sai Allah ya babbaka da wutar mai zafi koda ban zuwa isilimiya naji mai wa,azi yana cewa babu biyayya wa miji a cikin sabon Allah sai ka dauki dirjejen kato ka hadani zama,
Sahib yace kiyi hakuri samha ki kwantar da hankalinki kudi kawai zamu tara muyi hafiyarmu, samha tace innalillahi wa'inna ilaihir raji,un amma sahib baka tsoron Allah duk yanda hydar ya yadda dakai zakayi mishi butulci, kuma shine dani zaka nemi kudin? Sahib yace to miye a ciki? Kawai ki rika wanka kina saka matsatstsun kaya kina fitowa kije dakin hydar ki gaisheshi ki mishi duk abinda yake so shima zaiji dadi kinga daga haka sai ya kara mana kudi masu yawa, in taimakawa mahaifiyata in taimaki rayuwarmu samha kuma tunda kin iya sata hydar yana da kudade na tashin hankali kuma yanayin wawiyar ajiye ki rika sace mana kina tara mana,
Samha tace Allah ya sawake aini da nasan zanci gaba da sata da bazan aureka ba, amma tunda abin yazo da haka kaima baka san baka iya rikeni ba saida ka aureni abinda nake so dakai ni bazan iya zunubi biyu ba kayi hakuri ka sawwake min aurenka akaina,
Sahib yace to sai mi? Ni dama an fada miki sanki nakeyi ne? Dan naga kina nemin mutuwa akaina na taimaki zuciyarki amma zakimin butulci banza sakara wanda bata san arziki ba, samha ta ciko bakinta ta dirkakawa uwar sahib zagi amma sai taji ya kashe wayarsa,
Samha tace lallai namiji dan iskane, amma sahib dan iskane amma zanyi maganinsa, insha Allah, hydar kuwa kashe wayar yayi baki daya sannan yaje yayi wanka yayi alwallah yana fitowa kaya ya saka ya nufi masallaci,
Bayan hydar ya dawo masallaci dakinsa ya wuce abunsa dan duk yaransa babu ko daya yace suje sai ya gama da samha zai nemesu dan bazai yuwu ba kamar shi aji mace tana mishi rashin mutunci duk da sunsan komai su kuma a tunaninsu mai gida zai more amarcinsa ne,
Da safe samha kasa tashi tayi saboda wahalar da hydar ya bata ta share share, duk gabobin jikinta ciwo suke mata tana kwance cikin wahala idanuwanta sai digar hawaye sukeyi tun ba'aje ko ina ba, sahib ya fara mata wulakanci hada yi mata gori, sai yanxun ta tuna da maganarsa cewa samha nifa da wasa nake sanki, kara goge hawayen idonta tayi sannan ta sauka a hankali daga saman gado ta nufi toilet, sai yanxun tayi nadamar sanin sahib,
Saida ta gama wanka ta fito ta saka bakar riga mai kyau ta yafa gyalen tayi kyau sosai, dan hydar yace ta daina zuwa mishi da hijabi idan ba haka ba zata ga yanda zaiyi mata, dan yace duk ranar daya sake ganinta da hijabi sai yasa ta tayi mishi wanka kuma ya rantse idan ba wanka ba kwanciya a gado daya, samha dai tana cikin damuwa,
Dakin hydar ta nufa, a bakin kofa ta tsaya sannan tayi sallama hydar ya amsa tare da cewa shigo, a hankali samha ta shiga saida takai bakin gadonsa sannan ta zube saman gwuyawunta ta gaishe shi, ansawa hydar yayi sannan yace mi akayi miki jiya kike zage zage? Murmushin karfin hali samha tayi kanta a kasa sannan tace ba komai, hydar yace sahib ya bata miki raine? Samha tace kai haba a,a, babu wani abinda yamin, kallonta hydar yayi sosai duk ta bashi tausayi kana ganin samha kasan tana tare da damuwa, cikin sigar lallashi hydar yace ko inkai wurin training ne? Samha tace A, a, hydar yace to kina san wani abu ne? Hawayen da take boyewa ya zubo mata daga idonta cikin kuka tace nidai sahib zaka taimakamin kace ya dawo don Allah,
Cikin tausayawa hydar yace mi zaiyi miki ne? Samha tace kawai ina san ganin sa ne, hydar yace ke kice mishi ya dawo da kanki mana, samha tace A, a nidai ka taimakamin don Allah, hydar yace to zan taimaka miki amma bisa sharadi daya samha tace tom,
Hydar yace to matso, a hankali samha ta matsa gyara kwanciya hydar yayi sannan yasa hannunsa biyu ya tallabo fuskar samha daidai bakin ya matsa da nashi yana kokarin hada bakinta da nashi da sauri samha tace A'uzubillahi, dariya hydar yayi sannan yace nine kike cewa A'uzubillahi? Kamar kinga shaidani, to naji shikenan tunda kince muje ki bani abinci,
Saukowa yayi daga saman gadon itama samha mikewa tayi itace a gaba hydar yana bayanta suna tafiya, hydar yace haba samha ke ko "yar yangar nan ta mata bazakiyi ba? Shiru samha tayi dan tasan tana iyayin magana hydar ya taba mata jiki,
Hydar yace bakiji ina magana ne? Cikin girmamawa ta juyo tace kayi hakuri ni ban iya ba, hydar yace shi yasa sahib yake miki wulakanci baki san yanda ake kula da miji ba kina tafiya kina tada kura, samha tace ai ko ruwa ka watsa sai makiyi yace ka tasar masa da kura, hydar yace nine makiyin ki samha? Tace Eh mana in banda kiyayyar anan ina wani kura yake zakace ina tafiya ina baza kura?,
Hydar yace to badai zaki gyara kalaminki ba a kaina ko? Hakuri samha ta bashi baiyi magana ba ya wuce ya sauka kasa, itama bin bayanshi tayi ta sauka, shi ya zauna ita kuma ta wuce kicin danyin girki,
Hydar kwanciya yayi yana jiran samha ta gama abinci yaci, wayarsa ya dauka ya kira faruk suka gaisa, faruk yace ina amarya? Dariya hydar yayi sannan yace wace amarya tana nan ta ɓaddamin lissafi ni nama fara gajiya wallahi,
Faruk yace kada ka gaji kayi hakuri, dan gajeran tsaki hydar yayi sannan yace ni bana san wani abu ya shiga tsakanina da samha harsai ta yadda tana sona, kuma ko naje a matsayin sahib babu abinda zan mata saina tsaida mata hankali wuri daya sannan dan idan na birkice mata kwalwa nima burkutamin zuciya zatayi wallahi dan tana iya gudu kuma kasan bazan iya gano ta ba wallahi,
Faruk yace to Allah dai ya taimaka hydar yace amin , ganin samha tana tahowa yasa hydar cewa sahib ka dawo hakanan matar ka tana sanin ganinka, dariya faruk yayi sannan ya kashe wayarsa dan ya gane inda zance hydar ya nufa,
Samha ta matso gaban hydar ta tsugunna ta dafa kujerar da yake kwance kallonta yayi sannan yace miye? Kallonshi samha tayi amma itama taki tayi magana,
Tsawa hydar ya daka mata tare da cewa miye zaki wani zo kiyi ta kallona kamar wani sa'arki? Bata fuska samha tayi kamar zatayi kuka, hydar yace miye wai? Samha tace nidai gaskiya bana san girki, harararta hydar yayi sannan yace nine zan rika dafa miki abinci dan gayu?
Da Allah tashi ni inajin yunwa zaki zo ki wani ce wai bazaki dafa abinci ba, tsaki samha tayi sannan ta tashi ta nufi kicin cikin sauri tana gunguni, hydar yace ki zageni dakyau zan kamaki wallahi, tana zuwa kicin din indomie ta dafa sai mita takeyi,
Bayan ta gama ta zuba a filet ta taho saida tazo gaban hydar ta dangwarar da abinci tana cewa ni wallahi na gaji da dafa ma kato abinci, hydar yace ni kuma ban gaji ba, wanko hannu kizo ki bani da sauri,
Da fushi tayi kicin taje ta wanke hannunta ta dawo zama tayi kusa da hydar sannan ta dauki filet din ta ajiye a tsakiyarsu ta fara bashi kamar dai yanda ya saba haka yauma yakeyi mata, saida ta gama bashi hydar ya rike hannun yana lasarshi cikin kwarewa yanda yakeyin abun yasa samha taji tsikar jikinta yana tashi ga wani irin kallo da yakeyi mata, murmushi hydar yayi gani samha tana cikin wani hali a hankali ya matsa kusa da ita ya kara jawota kusa dashi hannun daya lasa ya saka a bakin samha yace mata kema kiyi a bakinki kiji hannunki akwai dadi yanda yayi maganar ne yasa jikin samha mutu murus kamar an watsa ma wuta ruwan sanyi,
Ba musu samha ta farayi kamar yanda hydar yayi mata shi kuma ya kara riketa sosai a jikinsa yana yin wani irin nunfashi mai tada hankali, jikin samha ya fara karma murmushi hydar yayi sannan yace miye? Daidai kunnenta yayi maganar cikin yanayin gajiya yayi da wata irin murya a hankali samha ta sauke ajiyar zuciya, hydar yace mi yasa kike san sahib ya dawo? Ba gani ba, zan miki duk abinda kike so ki daina tunanin sahib a ranki bazai dawo ba har abada,
Samha tana san tayi magana amma ta kasa, kwanciya hydar yayi sannan ya dagota ya dorata saman kirjinsa yayi mata kyakyawan riko yaci gaba da jagwalgwalata amma samha ta kasa magana kuma ta kasa hana hydar, murmushi yayi sannan yace bude idonki, a hankali samha ta bude idonta tana kallon hydar wasa ya farayi da idonsa cikin wani irin yanayi wanda ba samha ba ni kaina bansan shi ba, tunda yasan idonshi yana daukar hankalin samha, yana mata kallon yana murmushi da gefen bakinsa, a hankali ta sake rufe idonta hydar yace bude ki kalleni bude idonta tayi tana kallon hydar bude bakinsa yayi da niyar hada bakinsa da nata innalillihi wa"ina ilaihir raji'un samha tace da sauri ta sauka daga saman jikin hydar da sauri,
Dariya hydar yayi sannan ya tashi dakel ya zauna saman kujera, samha tana kokarin guduwa ya riko hannunta, wayarshi ya mike mata sannan yace kallarki da Allah, idanuwa samha ta zaro lallai hydar dan iskane wato duk abin nan daukarsu yayi, cikin kuka samha tace din girman Allah ka goge, hydar ya anshi wayar sannan ya mike yace ba kince zaki daukeni da gajeran wando ba? Ni kuma zan watsashi a whatsapp facebuk da Instagram duk in balbada ki kowa dakowa ya gani kuma ince matar aurece ke kike neman ubangidan mijinki, ya karasa maganar yana bude idanuwansa, cikin kuka samha tace don girman Allah kayi hakuri ka goge,
Hydar yace wallahi bazan goge ba bake kinajin mai wayau bace? Samha tace dan girman Allah ka rufamin asiri, hydar yace kina so in rufa miki asiri? Cikin kuka samha tace Eh, daga hannunwansa sama yayi sannan yace to zoki rungumeni, cikin kuka samha ta matsa kusa da hydar ta rungumeshi hydar yace sosai zaki rikeni ba kadan ba, ta kara rikeshi sosai hydar yace to kice kina so na, cikin kuka samha tace ina sanka, hydar yace kice har abada zaki daina san sahib samha tayi shiru hydar yace uhum ke nake jira idan baki fada ba zan fara posting fa, cikin kuka samha tace gaskiya nidai ina san sahib sosai kuma ina kewarsa,
Hydar yace to sakarmin jiki bari ki gani a gaban idonki zan fara turawa cikin kuka mai yawa samha tace don Allah ka rufamin asiri hydar yace to muje dakina ki bani hakuri, sakin hydar tayi yayi gaba tabi bayanshi tana kuka shi kuma sai dariya yakeyi a ransa,
A dakin hydar wanka yasa samha tayi bayan tayi wanka ya bata kaya ta saka, shima wanka yayi bayan ya fito ya saka bakar jallabiya kuma tayi mishi kyau sosai kallon samha yayi sannan yace kiyi sallah zanje masallaci yanxun nan zan dawo, samha tace to fita hydar yayi daga dakin da sauri ya sauka bene yana farin ciki sai iskanci yakeyi, ita kuwa samha tana sallah tana kuka tana tsinewa sahib albarka duk shine yaja mata wannan bala'i,
Bayan hydar ya dawo saida ya kwanta saman gado sannan yace ma samha tazo su kwanta, cikin shashekar kuka tace nidai zanje dakina ne, hydar yace okey muje tare to, samha tace nidai bazan kwana wuri daya dakai ba, hydar yace miyasa? Nifa ba dan iska bane gajeran wando kadai nake sakawa babu wani abunda zan miki wallahi kawai rike zanyi inji dadi, ya karasa maganar yana rungume hannuwansa yana dariya tare da daga kafafuwansa sama yana ma samha gwalo,
Tashi samha tayi zata fita daga dakin hydar yace wallahi idan kika fita zan miki Allah ya isa, a bayyane samha ta maimata Allah ya isa? Ba tare data waiwayo ba, Hydar yace sosai kuma wallahi bazan yafe miki ba zakiyi bacci da tsinuwar mala'iku akan zonan samha, tsaki tayi sannan tayi haryar fita da sauri hydar ya sauko daga saman gado yaje ya rikota,
Samha zatayi magana hydar ya dora dan yatsansa saman bakinshi yace shittttt yana dan bude idonshi hawaye kwance a idonsa, samha ta kara kallon hydar sosai amma batayi magana ba, hydar yace nifa na bawa sahib kudi masu yawa dan haka ya yadda dani yace ya barmin ke inyi yanda nake so dake amma tunda ni bana neman mata kawai zandan rikeki muyi bacci don Allah,
Taho taho taho yana maganar yana dan girgiza jikinsa, tsaki samha tayi sannan tace sai kayi ta abu kamar karamin yaro, hydar yace idan ina gabanki ni jaririne nidai zo mu kwanta, agogo ya kalla sannan yace lokacin baccina yana wucewa nidai taho,
Cire hijabin jikin samha yayi ya yadar a tsakar dakin yajata har saman gado, saida ta fara hawa sannan hydar ya hau jikinsa sai kyarma yakeyi, kuji iskanci bargo yaja ya lullubesu sannan ya rungumeta sosai ya dora kafarsa saman jikinta yana cewa yawwa muyi baccinmu za'ayi ta rubuta miki lada har safiya ta waye, cikin kuka samha tace ina dai ja ana dirkakamin zunubi hydar yace danma baki bari na taba nan ba, yakai hannunsa daidai kirjinta yace dasai kinfi samun zumubin da yawa, janye hannunsa samha tayi murmushi yayi sannan yace a hakanma na gode Allah yayi miki albarka,
Samha sai kuka takeyi shi kuwa hydar baccinsa yakeyi cikin kwanciyar hankali da natsuwa baima san samha tana kuka ba, bude bargon samha tayi tana kallon kyakyawar fuskar hydar gaskiya hydar yana da kyau gashi dan gayu kuma sai yayi tayin abu mai kyau da shiga rai, murmushi tayi sannan ta rufe idonta, a ranta tace duk macen data auri hydar ta more dan hydar komai nasa yana daukar hankalin mace, murmushi tayi zuciyarta na hasko mata idan hydar yana shagwaba yanamai kyau, goge hawayen idonta tayi a bayyane tace sahib bakayi wa zuciyata adalci ba, murmushi hydar yayi dan duk abinda samha take yanaji kuma yana kallonta dan tunda ta yaye bargo idonsa biyu budewar datayi ne yasa ya farka amma bai bude idonsa ba,
Dayaji samha tace sahib bakayi wa zuciyata adalci ba, bayan hydar yayi murmushi yace waye yace baiyi miki adalci ba amma har yanxun idansa a rufe, cikin kuka samha tace don Allah kace ya dawo hakanan hydar yace zai dawo sai kinyi ciki amma, cikin tashi hankali samha ta zaro idanuwa har yanxun idon hydar a rufe yake, amma sai yace ki gama zazzaro idon cikin zan rirkaka miki nasan idan sahib ya dawo zaice nayi kokari ya kara maganar yana murmushi,
Samha tace aika dan iska ne, hydar yace Ey wallahi kuma nima shi yasa nake sanki, samha tace to an fada maka nima "yar iskane kamar ka? Hydar yace ko daya wallahi keba "yar iska bane amma ni zan koya miki, daga haka hydar bai sake magana ba, haka samha ta gaji da tunani barkatai har bacci ya dauketa,
Karfe 1:02am hydar ya farka saida ya gyarawa samha kwanciyarta ya dire daga saman gado toilet ya nufa alwalla yayo sannan yazo ya fara sallah kamar yanda ya saba, saida aka kira sallah asuba ya tashi samha tayi sallah shi kuma ya wuce masallaci,
Bayan samha ta gama sallah tana zaune saman abin sallah hannunta a sama 🙏🏻 tana addu'a Allah ya dawo mata da sahib lafiya Allah ya fidda shedan daga zuciyarta a daidai lokacin da hydar ya shigo yana cewa ba amin ba,
Juyowa samha tayi ta kalli hydar sannan tace ina ruwanka da addu'a ta ne? Hydar yace niko nake da ruwa da addu'ar ai idan har naga hannunki a sama kina addu'a ne Allah ya tsinewa hydar Albarka kuma idan har na tsine na lalace saikinfi kowa bakin ciki da tashin hankali wallahi tunda hydar bai da mama baida baba banda yaya banda kani banda budurwar banda ɗa banda jiki, ke kuwa hydar shine ginshikin rayuwarki wallahi idan na lalace saikinfi kowa shiga matsala, samha tace toni ina ruwana da kirkinki? Ka hydar yace to kici gaba dayi a daidai lokacin daya ke kwanciya saman gado,
Saida samha ta gama addu'u'oin ta sannan ta tashi ta nufi toilet da sauri hydar ya tashi shima ya bita, tana shiga toilet taga hydar ya shigo, samha tace yi hakuri bara in fita, hydar yace A, a ni wanka zanyi ma kema kawai kiyi abinda zakiyi kowa yayi hidimarsa babu ruwan kowa da kowa, samha tace to aini na fasa abinda zanyi hydar yace bazai yuwu ba, tunda kin shigo sai kinyi,
Samha tace nikam na gaji gaskiya hydar yace niko ban gaji a daidai lokacin daya kara matsawa kusa da ita ya matseta jikin bango yace sahib fa ya raina miki hankali yana can yayi aure kuma karya yake miki baida wata mama, ashe har kudi kika bashi yayi ma maman sa magani? Da kudin yaje yayi aure ya barki anan a matsayin baiwa jira kiji abinda yace, jiya mukayi waya dashi nayi miki recording, samha tace sahib din? Hydar yace da kansa mana bakiga ya raina miki hankali ba kullum idan yayi tafiya yana ce miki wai baya da network a garin karya fa yakeyi kashe wayarsa yakeyi saboda kada ki kirashi a gaban matarsa, baki ga kullum sai nayi waya dashi ba?
Shiru samha tayi tana nazari lallai fa haka ne, amma sahib yakai dan iska shine yayi aure bai gaya mata ba? Ita zai dauka mahaukaciya? Shi yasa daya tashi aurensu yace bazai fadawa kowa ba? Hawaye ya zubo daga idon samha, hydar yace ki daina kuka samha nidai nasan baki so na, shi yasa zakiga duk abinda nake fada karya ne ga reacord in kiji ko kuma ki kirawo sahib da kanki, cikin fushi samha ta wuce daga kusa da hydar tayi dakinta da gudu tana kuka,
Dariya hydar yayi sannan yaje ya dauki wayar ya kunna ta da sauri, yana budewa kiran samha yana shigowa, samha tace sahib miyasa yanxun ka daina so na? Ko nayi maka wani abune? Kwanciya hydar yayi sannan yace gaskiya samha kiyi hakuri saida na aureki naga nayi hauka sosai amma kiyi hakuri, samha ta sassauta muryarta sannan tace to sahib mi nayi maka don Allah hydar yace to naga kina so kimin wasa da zuciya shine dalilin daya sa na hakura dake, zaki iya kama gabanki ni gaskiya bana sanki,
Samha tace haba sahib wannan kalmar baza ka daina fadinta a bakin ba? Da Allah kayi hakuri idan na tafi yanxun ina zanje? Bayan kamin alkawari zaka nemo min ahalina kace kaine zaka sama min farin ciki, kuma kasan mutane suna jirana a waje su kasheni saboda m card a gaban idonka mutuwa tayi wasan kura da raina aka jefoni daga saman bene sahib ka taimakeni don Allah don annabi kayi hakuri ka zauna dani,
Murmushi hydar yayi sannan yace gaskiya kiyi hakuri banda kudin dazan iya rikeki ba, amma idan zakiyi kokari ki sato mana a wurin hydar to, samha tace gaskiya bazan iya ma hydar sata ba, amma zan tambayeshi idan ya yadda ina mishi wanki da guga da wanki motoci sai in tara kudin, hydar yace miyasa bazakiyi ma hydar sata ba?
Samha tace ya bani tausayi yace min baida kowa a duniya shi daya ne, sahib yace kenan kin fara san hydar ko? To koshi zaki aura ne? Samha tace ai gara in fada daga saman bene in mutu da in auri hydar, hydar yace ai tausayi yana cikin so kinga kin fara kamuwa da san hydar samha tace hydar din banza, murmushi yayi sannan yace to kodai ma bana banza bane idan ya daukeki aikin to idan bai daukeki ba kina iya kama gabanki sai anjima yana fadin haka ya kashe wayar gaba daya sannan yaje ya ajiye a inda yake boyewa,
Samha kuwa tana tsaye har yanxun tana jin tashin hankali a zuciyarta sai wani barazar fitowa takeyi daga mazauninta, kuka takeyi sosai tare da cewa lallai na yadda sahib ba da gaske yake so na ba, wani irin ihu samha tayi tare da faduwa kasa somammiya, hydar jin ihun samha yasa shi tashi da gudu ya nufi dakinta,
Cikin kuka hydar ya shige cikin dakin gaba daya, inda samha take kwance a kasa ya dagota fuskarta ga hawaye dake fita daga gefen idonta, daga ta yayi ya dorata saman gado a gigice ya dauko ruwa a frig ya fara yayyafa mata, ajiyar zuciya samha tayi tare da bude idonta, cikin kuka samha ta kalli hydar sannan tace hydar mutuwa zanyi, hydar yana kuka yace ki rufa min asiri samha kada ki mutu kafin ki mutu nine zan fara mutu,
Samha tace kai baka da budurwa kaga ka huta da bacin rai ni a yanxun na zabi mutuwa akan rayuwa, cikin kuka hydar yace samha bazaki mutu ba, fadamin duk abinda kike so a duniya zan miki wallahi, murmushir karfin hali samha tayi sannan tace sahib nake so, hydar yace idan sahib yazo zaki yi farin ciki? samha tace Eh, hydar yace to sahib zai dawo insha Allah yaushe kike san ganin sa? samha tace gobe goben nan, hydar yace gobe batayi miki nisa ba? Samha tace idan ma zaizo yanxun yanxun ina so, murmushi hydar yayi sannan ya kwantar da kansa a kirjin samha yana kuka mai tada hankali lallai idan ya sake zama a matsayin sahib babu ranar da samha zata so shi, kodai ya fada mata shine sahib? amma yanda samha take haka idan tasan shine sahib zuciyarta zata tarwatse,
Hydar kuka samha kuka babu mai ba wani hakuri, ita tana kukan sahib shi kuma yana kukan haukan dayayi tun farko yazo a matsayin sahib, saida hydar yayi kuka har kansa yayi ciwo sannan ya sauke kansa daga jikin samha yace taje tayi wanka zaiyi wanka shima,
Dukansu wanka sukayi hydar ya zuge cikin kananan kaya masu kyau sai kamshi yakeyi, kayan da samha zata sa ya taho dasu ya kawo mata yace ta saka ta sameshi waje, fita yayi ya fita waje,
Yana fita ta saka kayan ta fita da sauri, a waje ta sami hydar tsaye a jikin mota sai murmushi yakeyi wayarsa ya ciro yana cewa bara in miki hoto kinga yanda kika hadu? Yanda yayi abunne yasa samha tayi murmushi tare da gyara gyalen jikinta tace kayi mai kyau don Allah ka turawa sahib, murmushi hydar yayi sannan ya fara daukarta sai canja style takeyi, hydar yace to cire gyalen ki gani nasan zaifi ji dadi idan ya ganki babu gyale, cire gyale tayi ta bawa hydar ya rike, wallahi hydar dan iska ne, sai sawa yake samha tana ta wani murgudewa yana mata hoto,
Bayan ya gama daukarta ya matsa kusa da ita ya dan rungumeta yana cewa muyi tare kinga idan ya gani zaiji dadi yace muna zaman lafiya ko? Samha tace to, kallonta hydar yayi sannan yace matso nan ki gani a jikinsa ya nuna mata yace ta dan kwanto, haka yayi ta sawa tana hayewa jikinsa da sunan hoto, saida ya gama ya nuna mata hotunan sunyi kyau sosai sannan hydar tace to rungumeni sannan in turawa sahib,
Daga hannayensa yayi sama, samha ta rungumeshi tana sauke ajiyar zuciya hydar yace rikeni sosai, kara rikeshi samha tayi hydar yace saifa kinyi da gaske kara rikeni da kyau, samha tace na gaji, sauko hannuwansa yayi sannan yace toni bari in miki kiji, a hankali ya jawota jikinsa ya riketa sosai yana sauke ajiyar zuciya hawaye na diga daga idonshi lallai idan har samha ta fita daga rayuwarsa mutuwa zaiyi wallahi dan baiga abinda zai zauna yayi a duniya ba, wayarsa dake ringing yasa ya saki samha daga rikon da yayi mata amma tana kwance saman kirjinsa,
Tsaki yayi sannan yace gani nan zuwa, bayan ya gama wayarne yace muje samha, shigewa sukayi gaba dayansu a mota hydar yaja suka bar gidan,
*Jameela Musa ce*
[05/04 4:45 pm] Washa: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
*SO*
*MUGUN WASA*
*{ Love is a bad game }*
*JAMEELA MUSA* { meelat musa }
*Story, Writing & Editing*
*by*
*Meelat Musa*
*SO*
*MUGUN WASA*
*Dedicated to* 👇🏻
_Ramlat Abdulrahman real mai dambu_
*44-46*
Suna fita hydar yace samha in kunna miki waka ne? Turo baki samha tayi sannan tace bana, so murmushi hydar yayi sannan yace,
Naga "yan mata suna san waƙa a mota wai sunce tafiyar tafi dadi ana tafiya ana nishadi,
Samha tace niko bana san nishaɗi, hydar yace nikam ina so inyi nishaɗi kuma ina so inji dadi a rayuwata, kamar ke yanzun idan kika kwantar da jikinki a jikina dadi nake ji,
Samha tayi shiru hydar yace don Allah idan kika rungumeni bakyajin dadi? Ki fadamin gaskiya bana san ki boyemin komai,
Samha tace ni babu wani abinda nakeji, murmushi yayi sannan yace niko nasan jikina yana da dadi shi yasa nake so ki shigo cikinsa dan kiji dadi sosai nake dage miki hannuwana sama, amma tunda bakya so na daina,
Samha tayi shiru, hydar yace to ni in riƙa rungumeki? Samha bata bawa hydar amsa ba,
Murmushi hydar yayi sannan yace yi hakuri dan Allah ki dan kwanta a jikina, ni inasan inji mace tana shashshafa min jikina daɗi nakeji,
Kallon hydar samha tayi murmushi yayi tare da ɗaga mata gira yana kashe mata ido ɗaya, da sauri samha ta rufe idonta a ranta tace gaskiya hydar dan iska ne, kamar yaji abinda tace yayi dariya, sannan yace keko idan nayi miki saiki karɓa amma saiki wani rufe ido? Taya zan rika birgeki mana?
Tsoki samha tayi sannan ta juya kanta gefe bata sake magana ba, har suka isa inda zasuje hydar shima bai sake magana ba,
Parking hydar yayi sannan yace ki zauna anan kada ki fita kinji zanyi meeting idan na gama zamuje wurin training daga nan kuma sai mu wuce gida,
Gobe kuma kamar yanxun sahib yana nan kusa dake, murmushi samha tayi sannan tace na gode maka hydar,
Murmushi yayi sannan ya mika mata hannu suka hade hannuwansu🤝🏻 hydar yana kallon samha yana murmushi,
Ya dade rike da hannunta sannan ya sake mata hannunta tare daɗan shafa gefen fuskarta yana cewa saina dawo,
Murmushi samha tayi ba tare da tayi magana ba, shi kuma hydar ya fice abinsa, tana zaune a motar har hydar ya gama meeting ya dawo,
Da zugar yaran sa hydar ya dawo dukansu suka fara gaishe da samha cikin girmamawa, suna mata fatan alkairi tare da addu'ar Allah ya basu zaman lafiya,
Cikin rashin fahimta ta kallesu sannan kuma ta kalli hydar murmushi yayi tare da daga mata dira ɗaya yana dan kwantar da kansa gefe daya,
Itama yaƙe tayi mishi wanda yafi kuka ciwo, yanda tayi abun ne ya bawa hydar dariya sosai, amma baiyi ba sai ya basar,
Alale yace ranka ya dade tafiya zamuyi ne? Hydar yace Eh amma ni zandan kai samha wani wuri kuma kuna iya tafiya kawai,
Fatan alkairi sukayi wa hydar sannan ya shiga mota yaja yabar wurin,
Nan su shamsu suka tsaya suna ta sheganta wai mai gida yana soyayya haka sukayi ta iskancinsu daga baya suma kowa ya kama gabanshi,
Samha sai so takeyi ta tambayi hydar game da Allah yasa alkairin mi akeyi musu amma yanda hydar ya hade ransa kamar zaiyi mata duka yasa batayi magana ba,
Saida yaje wurin training amma ba wani abu yayi ba kawai fita yayi yaɗan gaisa da mutane dan ya dade baizo ba tun bayan aurensu da samha,
Bayan ya gama gaisawa da mutane ne, ya dawo yaja motarshi sukayi tafiya gida, haka dai yadanyi yawo da ita tare da mata fira wai dan hankalinta ya kwanta dan yana so ta canje maganar sahib ne a ranta,
Sai dare suka dawo gida, ta baya suka shiga suka sauka dakin hydar a gajiye samha ta haye gado dan hutawa tunda sundan shana a gari, bata dade da kwanciya ba bacci ya dauketa, shi kuma hydar alwallah yayi yaci gaba da sallah,
Da safe kuwa samha koda ta tashi bata ga hydar ba, dan haka dakinta ta tafi tayi wanka ta taci gayunta,
Bayan ta gama ta sauko parlour nanma bata ga hydar ba, kicin ta nufa dan samawa cikinta mafita, tana shiga ta window in kicin ta hango hydar baya yana kwallo shi kadai,
Murmushi tayi sannan ta matsa jikin window tace ashe kaima ka iya boll? Ba tare daya kalli inda samha take ba yace kema kin iya ne?
Cikin zumudi samha tace na iya wallahi har yanxun wasan sa yake da boll din kuma bai kalli samha ba, yace to zo mu gani idan kin iya, dariya tayi sannan ta fita kicin din da sauri,
Da gudu ta isa wurin hydar sannan tace to muyi, rike kwallon yayi a hannunsa sannan yace kije dakina, a cikin wedrof idan kika bude daga kasa zaki ga kaya ki dauka ki saka,
Cikin sakata samha tace muyi da wannan mana, kusa da ita hydar ya matso sannan yace ai wannan baza suyi miki dadi ba, wancan riga da wando ne kiyi sauri kije ki saka,
Dariya samha tayi sannan ta ruga da gudu murmushi hydar yayi sannan yaci gaba da wasansa, babu dadewa samha ta dawo,
Amma da hijabi a jikinta ba tare da hydar ya kalli inda take ba yayi murmushi har yanxun wasan sa yake da kwallo bai daina ba,
Samha tace na saka kayan, hydar yace ai naga baki shirya ba, samha tace na shirya mana, hydar yace to idan kin shirya ki cire hijabin mana,
Dariya tayi sannan ta saka kanta cikin hijabi tana kallon kayan jikinta, duk halittun jikinta sun nuna fa, murmushi hydar yayi dan ya gane abinda take nufi,
Fiddo kanta tayi sannan ta kalli hydar da sauri ya dauke kanshi daga kallon da yakeyiwa samha, amma yana kallonta da wutsiyar idonsa,
Samha tace kayannan sunmin kadan fa, hydar yace ai zasuyi miki daidai, ni nama gaji tunda bazaki yi ba, da sauri samha tace A, a yi hakuri don Allah muyi tare,
Taka kwallon yayi da ƙafarsa sannan yace to cire hijabin, cirewa tayi ta mikawa hydar kanta babu kallabi gashin kanta ya sauka a gadon bayanta duk data daureshi sai lilo yakeyi a jikinta, tana mika mishi hijabin ya riketa yadan shafata kadan sannan ya saketa, yana mata wani mayataccen kallon a ransa yace samha akwai diri, ci gaba da kallon ta yayi wanda har samha taji babu dadi,
Murmushi hydar yayi sannan yace to taho, da sauri samha tayi wurin inda yake kafarsa tana kan boll din, tana matsowa suka fara wasa, haka hydar yayi ta gyarata yana dariya, saidai ta bishi da gudu data zo zata kama boll din saiya juyata ya turata wani wuri,
Abin yayi ma samha dadi dan haka ta saki jikinta tanajin farin ciki a ranta sosai, saida suka gama kwallon ne, ne hydar yace to zo ki simbaceni, {kiss} samha tace kai wai miye haka? So kake sahib ya shigo ya ganmu a haka ne?
Daga kai sama hydar yayi tare da bude hannuwansa yana cewa taho taho taho,,,,,,,, murmushi samha tayi sannan ta matsa wurin hydar cikin sauri, rungumeta hydar yayi sosai yanajin dadi naratsa masa tun daga cikin kwakwalwar sa har ƙarƙashin tafin ƙafarsa,
A hankali ya sauko kanshi, a gajiye ya lalubo bakin samha ya shigar da nasa a ciki ya fara aikawa samha da sabon sakon da bata taba jin irin taken ba tunda Allah ya kawota duniya,
Samha ji tayi kafafuwanta basa daukatar jikinta sai kyarma yake dan ita kadai tasan abinda takeji, dan tunda take duniya babu namijin daya taba mata irin wannan abun, sai hydar, dan haka batayi yunkurin hanasa ba, saida ya gaji dan kanshi sannan ya saki samha,
Hannunta yaja dayan hannunsa kuma yana rike da boll din da suka gama wasa, haka yajata sukayi farlo, bayan sun shiga ya zaunar da ita saman kujera sannan ya wuce kicin yana halba kwallon a hannunsa yana buga ta kasa tana dawowa sama yana rike ta a hannunsa,
A daidai bakin kicin ya yada kwallon sannan ya shiga ciki, samha kuwa tana zaune kamar wata gunkiya niko nace ina ruwan ba sabanba,? An wani jingina da kujera sai wani tunanin abinda hydar yayi mata takeyi,
Abin ya tsaya mata a rai, murmushi tayi sannan ta dora kanta saman hannun kujera ta rufe idonta, tun farkon haduwarta da hydar ya fara dawo mata tsaff a cikin ƙoƙon kanta,
Saidai tayi murmushi tare da gyara kwanciyarta, haka tayi ta juyi tana murmushi tare da mammatse ido sai kace hydar ya kamata a gado,
Hydar dake tsaye gabanta binta da kallo yayi tare da tambayar kansa ko miyasa takeyin haka? Murmushi yayi lallaima ya gano abinda take tunani, a bayyane yace sahib, da sauri ta bude idonta tana kallon hydar, murmushi yayi sannan yace sahib ko?
Itama murmushi tayi sannan ta tashi zaune, zama hydar yayi kusa da ita sannan ya jawo samha a jikinsa, yace kada ki wani damu babu dadewa sahib zaizo insha Allah,
Samha tace kai amma wallahi na gode maka sosai hydar, murmushi hydar yayi a ransa yace zaki gode min dai, amma bari inzo miki as sahib din zaki ci gidanku wallahi,
Mikewa hydar yayi sannan yace yau inaji dake hau bayana inyi miki goyo, dariya samha tayi sannan tace haba wannan ai abin kunya ne, hydar yace kai haba babu wani abin kunya don Allah ki hau bayana muje,
Murmushi samha tayi sannan tace nifa gaskiya na wuce goyo, hydar yace inji waye ya fada miki ne? Samha tace ni na gani dakaina baka ga na zama katuwar mata ba? Hydar yace kai ni inaganinki kamar wata jaririya, hawo hawo hawo my samha, ya karasa maganar cikin sakata dariya samha tayi sosai, dan yanda hydar yayi abun taji tana san ta hau bayan nashi, kallonshi tayi sosai a ranta tace wallahi hydar hadadɗene sosai komai yana mishi kyau,
Saman kujerar ta mike tsaye hydar ya matsa da bayansa samha ta haye, tana jin kunya sai boye fuskarta takeyi a bayan hydar kamar yana ganinta, murmushi yayi sannan ya fara tafiya, kwantar da kanta tayi sosai a bayanshi tanajin dadi sosai,
Saida yakaita daki a saman gado ya kwantar da ita, shima gadon ya hau, ya kwanta saman jikin samha, cikin jin kunya ta rufe idonta da hannunta, murmushi hydar yayi sannan yace ina da nauhi ne? Murmushi samha tayi amma bata bude idonta ba kuma bata bawa hydar amsa ba,
Haɗa hannuwanta yayi ya rike duka biyun sannan yace don Allah idan kina tare dani ki daina rufe idonki, idan kina kallona inajin dadi, ina sanki sosai idanuwanki suna min kyau idan kina jin tsoro samha, zaro idanuwan tayi cikin yanayin tsoro kamar yanda hydar yake so, murmushi hydar yayi sannan yace na gode sosai, dora goshinsa yayi saman fuskarta,
Ya dade a haka sannan ya daga samha, yace to samha zan tafi bazaki sake gani na ba, samha tace miyasa? Murmushi hydar yayi sannan yace zan barki da sahib nasan yana zumudi yazo wannan lafiyayyar fatar nasan yau sahib zai more abinsa ya karasa maganar cikin sigar a tausaya masa,
Da sauri samha ta tashi ta sauko daga saman gado tayi wurin da hydar yake tsaye sannan tace miyasa kakeyin kuka ne? Murmushin karfin halin hydar yayi sannan yace ba dole inyi kuka ba, tunda ina sanki amma bakya so na? Kina ta murna sahib zai dawo,
Murmushi samha tayi sannan tace kayi hakuri ka daina kuka kuma ma ai sahib bazaice maka komai ba, tunda shine da kanshi yace ya yadda dakai to miye zakayi damuwa ne?
Cikin kuka hydar yace sahib ya yadda dani amma kefa kin yadda dani ne? Murmushi tayi sosai sannan tace na yadda dakai mana, hydar yace to idan kin yadda dani ina so ki cire kayan jikinki duka, idanuwa samha ta zaro sosai sannan tace kai dan iska ne? Hydar yace Eh kuma ina so inyi iskanci dake ke bazakiyi dani ba?
Da sauri samha taja baya hydar ya bita, wayyo Allah tace, sannan tace hydar miye haka? Daure fuska hydar yayi yana tunkarar samha cikin tashin hankali samha tace don girman Allah kayi hakuri,
Wani irin kallo hydar yayi mata sannan yace zan baki miliyan goma, samha tace Eye? Hydar yace Eyy, girgiza kai samha tayi cikin kuka tace bana so, hydar yace miliyan ishirin samha tace bana so, yace talatin tace A, a, haka yayi ta fadar miliyans of naira samha tace bata so,
Hydar yace to wallahi idan baki cire kayanki kikamin abinda nake so ba zan kashe ki, da sauri samha takai hannunta ta fasa glass din madubi ta ciroshi sannan tace dakaina zan kashe kaina kafin ka kasheni tana kokarin cakawa cikinta hannunta sai jini yake zuba saboda kwalaben daya shiga a cikin hannunta, da gudu hydar ya matsa ya rike hannunta,
Samha tace sakemin hannu, hydar yace waye yasa kika fasan mirrow? Kinsan ko nawa na siya? Kudi da yawa amma kikamin asara? Lallai yanda kika fasa min haka nima zan farfasa miki fata, tsoki yayi sannan yace bara sahib din yazo zaki bashi labari yana fadin haka yayi waje,
Yana fita samha ta zauna kasa tana kuka, shi kuma hydar da farin cikin sa ya isa dakinsa, samha baza tayi mishi sata ba, sannan baza tayi iskanci dashi ba, dadi yaji sosai tun kafin ya isa dakinsa ya cire rigar jikinsa, amma yanxun yasan wannan abun dayayi ma samha ta kara tsanarsa a ranta , to duk dai da haka ya wuce da wannan wurin samha babu sata babu fasiƙanci, saura ya koyawa zuciyarta sanshi,
Wanka yayi yaci uban gayenshi sannan ya dauki fuskar sahib ya saka, wayar da yake kiran samha ya dauka ya kunna sannan ya kashe tashi ya boye, fita yayi ta baya, ya zagayo ta inda suke shiga, yana shigowa ya wuce kicin ya da sauri ya shiga, yana shiga ya bude lokar,
Inda ya boye goruba da taura da magarya irin dai kayan kauye, dauka yayi ya fita daga kicin din yana fita daga kicin din ya fara kwarara sallama, samha dake zaune tana kuka taji muryar sahib tashi tayi ta fito da gudu,
Tana fitowa ta hangoshi tsaye a tsakiyar parlour rike da ledoji, murmushi tayi sannan ta goge hawayen idonta da bayan hannunta ta babbako da gudu kutumar babban burodi da boter ta rungumeshi tana dariya, ajiyar zuciya hydar yayi sannan yadan matse hawayen idonshi,
Cikin kuka mai sautin dariya tace kai amma ka iya bazata wallahi, ansar ledar hannunsa tayi sannan tayi gaba hydar yabi bayanta yanajin bakin ciki a ransa, samha tace sahib naji ledar nan da nauhi da alama kayomin tsaraba ko? Murmushin karfin hali ya ƙago sannan yace Ey,
Surutu tayi ta mishi har suka isa daki, a gefen gado hydar ya zauna, sannan ya kalli samha yace mi akayi miki kike kuka? Murmushi tayi tare da boye hannunta a baya tace ba komai mi ka gani ne? Faduwar gaba taji dan lallai bata san taya zata fadawa sahib ba abun ba,
Murmushi yayi dan yana so ya fara matsa mata a matsyin sahib dan ta fitar dan ta fara tsanar sahib a zuciyarta, saboda yace dan ubanki bakiji ina magana ne? Cikin tashin hankali samha tace ubana kuma? Yace Ey dama ubana zan zaga? Dariya samha tayi sannan tace nidai bazan zagi ubanka ba,
A fusace ya mike tsaye yana cewa nine kike cewa ubana? Da sauri samha ta mike cikin sigar lallashi tace kayi hakuri daga dawowa kuma sai fada don Allah? Kwantar da hankalinka nayi maka girki kayi wanka ka huta sai a fara fadan ko? Sahib yace au fadan za'ayi ma ko? Tace Eh tunda kana so ayi aisai in kama maka,
To dan ubanki kiyi fadan yanxun mana, samha tace kai bafa tsoranka nake ji ba, ko an fada maka ni banzace zan zauna kayi ta zungurawa iyayena zagi ne?
Sahib yace an zaga, naje na zagesu, banza jaka dake, cikin fushi samha tace akwai babban banza jaki ma irinka? Dan iska da baka san darajar matar aure ba, kazo ka ajiyeni a gida dani da wani dirjejen kato shima dayan dan iskan kamar kai,
Sahib yace kai kai kai? Cikin mamaki ya kalli samha sannan yace dan uwarki hydar ne dirjejen ƙato? Ya akayi kikasan dirjeje kato ne shi? Cikin duk abinda zai faru ya faru samha tace ai kasa shi ya dirdirjeni, to daya cire kayansa naga ashe kato ne,
Wani irin mari hydar yakai wa samha harsai data fadi kasa, da sauri ta tashi itama ta kashe shi da mari, sannan tace dan ina aurenka zaka mayar dani kamar fulawa kayi ta dukana? sakarni yau duk wanda ya tsaya maka a gidan nan saika bani takardar sakina, bansanka na tsaneka wallahi yau ina iya kashe ka ta karasa maganar tana ƙara fashewa da kuka,
Sahib yace to? Yayi maganar ne cikin mamaki, sannan yace nine zaki kashe? To anki a sakeki kuma tunda har kikayi zagi wa hydar gidan nan kin bani dani wallahi sai kin zama abin tausayi dama an fada miki sanki nakeyi? Banza barauniya,
Samha tace naji ni sata nakeyi kaifa? Wanda baka kishin iyalinka, dan iskan hydar din nan har lallashemin baki yayi dan ubanshi hada kwanciya dani a gado daya munafiki sai yayi ta rungumeni katon banza wanda baya tsoron Allah,
Sahib yace ke tsoron Allah yasa kika biye mishi kikayi? Samha tace duk ba kaine kaja ba? Kaine kace inyi masa komai a matsayin mijina kamar yanda zanyi maka, Allah ya sawake ma daya ciny....... Nushin da sahib yakai mata shi ya hanata karasa maganar, a hankali ta zauna gefen gado tana kuka,
Sahib yace wallahi zanyi shedar hydar bazayi iskanci dake ba, kice yau duk kin zage uwarsa? Cike da bacin rai samha tace baƙin cikina daya ma bai bari na zagi uwarsa ba ya fita, ta karasa maganar tana kuka, tsoki sahib yayi sannan yace nikam bazan iya kwana dake ba, yau din nan zanyi tafiyata, ga tsaraba nan, idan kin gama haukan na dawo,
Cikin rarrashi samha tace yi hakuri kaine wallahi duk ka ɓatamin rai daga magana sai zagi sai kace kana jirana ne? Tashi tayi tare da cewa bara in haɗo kayana mu tafi, yace to kiyi sauri, cike da zumuɗi ta matsa ta fara tattara kayanta, hydar yana ganin hankalinta ya koma wurin haɗa kaya yasa shi sulalawe yabar dakin samha,
Da gudu ya isa dakinsa, ya canja kaya tare da cire fuskar ya haye gado yayi kwanciyarsa, samha kuwa bayan ta gama hada kayanta ta dauko da niyar tafiya taga babu sahib, da sauri ta fito ta fara dubashi amma babu shi, da gudu ta fita daga farlo, ganin wasu jibga jibgan karnuka tayi masu kama da kuraye a kofar farlon, suna ganin fitowarta da gudu suka fara, wan wan wan wan hab hab hab, da gudu samha tayo ciki suka biyota,
Da gudu ta haye bene amma binta sukeyi, ganin kada ta shiga dakinta su cinyeta babu wanda yaji ya gani yasa tayi dakin hydar da gudu, yana jin ihuta shi kuma minafikin Allah yana cikin bargo sai dariya yakeyi, da gudun tashin hankali ta shiga dakin tabi takan hydar ta wuce bayansa tana kuka,
Banza yayi da ita kamar baisan ta shigo ba, su kuma karnukan a bakin kofa suka tsaya sai wani zalzalo harshe sukeyi suna kallon samha, sai shashshekar kuka takeyi tana tsugunne saman gado bayan hydar, banda dariya babu abinda hydar yakeyi cikin bargo harda hawaye,
Samha ganin bargon na motsi yasa ta yaye bargon hydar ta gani ya daure girar sama data kasa yana harararta, murmushin karfin hali samha tayi sannan tace kaine? Kallonta yayi sannan yace nine ya akayine?
Samha tace dama daki zanje ne, hydar yace ba dakin kika wuce ba kika zo nan? Ajiyar zuciya samha tayi sannan tace don Allah ka rakani, jan bargonshi yayi ya lulluɓe tare da cewa wallahi babu wani inda zanje, haka ta gaji da tsugunni ta zauna, ganin zaman bazai fisheta ba, ta hakura ta kwanta, tare da dafe hannunta dataji ciwo,
Shashshekar kuka tayi, tayi har ta gaji tayi bacci, saida hydar ya tabbatar tayi bacci sannan ya tashi yayi mata dressing a hannuta dataji ciwo ya cire mata hijabin jikinta ya lullubeta da bargo,
Koda asuba da hydar zai tafi masallaci bai tashi samha ba, saida yaje yayo sallah ya dawo sannan ya tasheta, tana tashi yace tashi ki tafi kiba mutane wuri, da sauri samha ta tashi a hankali ta sauko daga saman gadon, ta fara tafiya hydar yace idan kin gama abinda kikeyi zaki dafa abinci dan yau duk wani ma'aikaci da yake gidan nan zai dawo,
Samha tace ai tafiya zanyi saika samu wanda zai dafa musu danni bazan zauna inyi ta wahala ba sai kace wanda bata da Nci, hydar yace to a sauka lafiya, kuma idan har kare ya sake biyoki kika zo min daki wallahi sai nayi miki abinda baki tunani, kinji kuma nayi rantsuwa wallahi a saman gadon nan zan miki kacha kacha na fada miki,
Samha batayi magana ba ta fice daga dakin tana kuka, da sauri ta sauka kasa, saida taje daidai kofa ta leka taga karnukan nan suna nan, tsoki tayi sannan tace "yan iska duk saina kasheku guba zan zuba muku "yan iska duk kuci ku mutu,..juyawa tayi ta koma,
Da sauri ta nufi dakinta tana zuwa toilet ta nufa tayi alwalla sannan tazo tayi sallah, tana gamawa ta koma gado tayi kwanciyarta,
Hydar kuwa fitar samha a hankali ya kwanta, fadansu na jiya as sahib ya fara tunani murmushi yayi sannan yace Allah ya sawake, lallai ina da jibgegen aiki a gabana ya za'ayi samha ta fara san hydar? Tsaki yayi sannan yace Allah ya dorani kanki samha,
Saida tasha bacci ta tashi dan kanta, wanka tayi bayan ta gama ta shirya ta koma gefen gado ta zauna, hannunta ta kalla da aka nannaɗe da bandej sannan tace in banda rashin galihu haka zanyi wani girki babu wani mai sona, kawu yana can yana jira in dawo yaci gaba da sakani sace sace, shi kuma hydar sai wani daure fuska yakeyi, "yar dariyar ma ya daina min dana bashi hakuri kuma yanxun idan ina san ganin sahib ya zanyi? Gashi gidan ba'a fita yazo ya ajiye karnuka,
Haka dai hydar yaci gaba da horar da samha da wahala, kullum haushinsa takeji, shi kuma sahib ko ankira ma ba'a samu,
Kuma tana san ta tambayi hydar amma babu fuska, kuma idan ya fita daga gida sai tayi bacci yake dawowa, dan haka duk abubuwa sun dami samha, gashi daga farlo bata zuwa ko ina saboda da karnukan daya a bakin farlo,
Haka take dafa abinci mai yawa, tun bata saba ba harta saba, kuma hydar bayacin abincin samha yanda ta zuba haka zata zo ta dauka zamane dai na samha tanajin haushin hydar shi kuma yana jin dadin zaman kuma yana kara santa, amma ita batashi takeyi ba,
Hydar ne zaune a farlo, yana zaune saman kujera 2seater ya jingina bayansa da hannun kujerar kafafuwansa yana saman dayan hannun, yana karatun Al- qur'ani amma hankalinsa yana kan samha, dan tunda safe yakejin kamar zaginsa takeyi, yana so ya tantancene idan zaginsa takeyi,
Ita kuma da mita ta fito daga kicin da katuwar kula a hannunta tana gunguni saida ta ajiye a saman dirning sannan tace nifa gaskiya na gaji da girkin abinci wa katti dan wallahi hakurina ya kare a daidai lokacin da taja kujerar dirning ta zauna, hydar yi yayi kamar baiji abinda take cewa ba,
Samha taci gaba da cewa kuma wallahi bazan sake share farlon nan ba tunda ni ba jaka bace, kullum sai inyita sharewa wani lokaci ma sai ace min baiyi ba saina sake, nanma basarwa yayi bai mata magana ba,
Tsaki tayi sannan tace to wallahi saidai a raba farlon nan biyu, kowa ya rika sharewa shima abincin kowa ya rika dafawa dan wallahi kowa yana san ya huta ni sai a ƙaƙuba min rankatakaf aikin gidan nan gani "yar yarinya aisai wahala tasa bazan girma ba, da wutsiyar idonshi ya kalleta amma baiyi magana ba,
Tashi tayi da gudu ta nufi sama, bata dade ba ta dawo da jan baki guda biyar a hannunta, hydar dai yana kallonta, bude jan bakin tayi ta duka ƙasa sannan ta fara darkakashi a saman farin teryils din, jan janbaki biyar saida ta ƙarar dashi wurin raba farlon, saida ta gama rabawa sannan tace yawwa gashi nan an raba, ga wurinka can ga nawa nan idan kabi min ta wurina wallahi mutum zaiga yanda zan mishi kaca kaca a wurin, wai maganar da hydar yayi mata cewa idan ya sake ganinta dakinshi, shine itama ta rama, murmushi hydar yayi sannan ya mayar da kanshi yaci gaba da karatun alqur'anin sa,
Ita kuma zama tayi daga saman tsef din bene tana ci gaba da gunguninta, wanda hydar baisan abinda take cewa ba, harya gama karatunsa ya rufe qur'anin ya tashi,
Ta gefenta ya raba ya wuce, kuma bai taka inda tace ba wurinsa bane ba, ganin ya wuce yasa ta tashi ta bishi tana ci gaba da mita sai tsiwa take mishi, shidai baiyi mata magana ba, har kofar dakinsa ta tsaya tana jaraba, bata iya shiga cikin dakinshi dan yace duk ranar data shigo dakinshi na lahira sai yafita jin dadi, wannan dalilin yasa bata shiga ba tana tsaye a bakin kofa ta rike kugu tana masifa,
Ganin ya shiga wanka yasa ta hakura ta koma parlour ta zauna tana jiran fitowarsa, shi kuma yana gama abinda yakeyi ta can ya fice, yabar samha da hauka,
Ganin bazai fito ba yasata ta hakura ta koma dakinta, da daddare kuwa hydar saida ya tabbatar samha tayi bacci ya dawo, ta farlon ya shigo, inda samha tace wurinsa ne ya gani wurin kaca kaca duk ta yayyaga takaddu da ledoji ta zubar a wurin, ita kuma wurinta ta share ta goge fes, tsaki yayi saida ya share wurin ya gogoshi sannan ya dauki biro da paper ya rubuta mata,
_Na rantse da Allah na sake samun kin ɓata min wuri nima saina ɓata miki naki,_
Saida ya gama sannan ya aje a saman kujera, bayan ya ajiye ya haura sama, dakin samha ya fara shiga tana kwance tana bacci, shiga cikin dakin yayi a gaban gado ya tsaya yana kallon samha,
Kallon hannunta yayi data runtse dukawa yayi sannan ya kama hannun ya bude, murmushi yayi ganin abinda ta rubuta, wai _i love sahib_ biro ya ciro daga gaban aljihunsa sannan ya bude hannun, ya rubuta _i love hydar_ yana gama rubutawa saida ya sumbaci samha sannan ya fice daga dakin,
Da safe yana zaune a farlo yana break samha ta fito, dan kowa shi yake girka abinda zaici, bata kalleshe ba, kuma bata gaishe shi ba, saida tazo ta wuce ta kusa dashi harta kusa shiga kicin yace ke zo nan,
Da baya baya ta dawo batayi magana ba, tazo gabanshi ta rike ƙugu, daure fuska hydar yayi sannan yace zo nan mana, kusa dashi ta matsa, kallon idonta yayi sannan yace keni abokin wasanki ne? Samha tace mi nayi maka kuma? Cikin daga murya hydar yace kamarni zaki rika rubutawa a hannunki wai kina so na?
Samha tace waye yace na rubuta, hydar yace zan miki karya ne? Yana maganar yana zaro ido, samha tace ni wallahi ban wani rubuta ba, hydar yace idan aka duba kin rubuta mi zan miki? Samha tace komai ma kamin, tunda tasan bata rubuta ba,
Wani irin kallo hydar yayi mata sannan yayi murmushi yace to bude hannuwan mu gani, kusa dashi ta kara matsawa tana bude hannun, kallonta hydar yayi sannan yace kindai ce komai in miki ko? Samha tace Eh, jinjina kansa yayi sannan yace karantomin duk abinda kika rubutu a hannun,
Daga hannuwan tayi tana kallon su, sannan tace _I love sahib_ hydar yace uhum, idanuwa samha ta zaro tare da cewa aaaaa, hydar yace inajinki, shiru samha tayi, murmushi hydar yayi sannan yace karanta fa, samha ta fara wallahi ban rubuta ba, hydar yace miye baki rubuta ba? Samha tayi shiru, murmushi mugunta yayi sannan yace jeki ki zauna a can ki jirani in gama, yana nuna mata wurin da hannunshi,
Samha tace kayi hakuri don Allah, tsawa hydar ya daka mata wanda yasa ta sauka daga wurin da sauri taje ta zauna inda hydar ya nuna mata, shi kuma sai sauri yake ya gama break ɗin dan yasan yau ko banza sai yadan rage zafi,
Yana gamawa ya sauko sannan ya nufi inda samha take zaune, yace tashi, tashi samha tayi tana kallon hydar,
Zama yayi saman kujerar ya kwantar da kanshi saman hannun kujera ya bude kafafauwanshi kana ganin kwanciyar kasan hydar kwallon dan iskane, wani irin kallo yakeyi ma samha wanda yasa taji duk tsikar jikinta ta tashi, yana mata kallon cikin wani irin yanayi yana murmushi da gefen bakin sa,
A hankali samha ta kalli kasa tana wasa da yatsunta, murmushi hydar yayi sannan yace kallarni mana, daga kanta tayi ta kalleshi shi, bude daradaran idanuwansa yayi masu firgita samha sannan yace zoki kwanta a jikina ki bani hakuri, samha tace ai basai na kwanta ba kayi hakuri don Allah, hydar yace wallahi bazanyi ba, maza kizo ki kwanta idan ba haka ba kuma zanje dake dakina, samha tayi shiru tana kallon hydar, shima ita yake kallo yana cewa bazaki zo ba?