Lokaci k'an k'ani suka isa Asibitin, ko kad'an ya Umar baya buk'atar had'uwa da Dr Jafar, Dan haka yasa sukabi tabaya shida Asma'u.
Saidai kumar abin fad'a suna karya kwana saiga Dr jafar shida wasu Norses.
Ya Umar Harya d'auke kansa saikuma yaga rashin dacewar hakan, gyara tafiyarsa yayi yadawo kan hanya sosai, sa6anin da daya koma gefe.
Shima kansa Dr jafar baiyi niyyar gaisawa da ya Umar ba, amma ganin ya Umar yanufoshi ga wani kwarjini daya masa saiya dake shima.
Sallama ya Umar yamasa, da k'yar Dr jafar ya amsa, ya Umar yayi murmushi yana mik'a masa hannu, haj Jafar talaka baya ganinku?.
Wata dariyar k'eta Dr jafar yayi tareda fad'in mu mun Isa? Aikune manya-manya maganin k'ana-k'ana.
Dariya sosai ya Umar yayi wadda har zuciyarsa yayita, yazame hannunsa daga na Dr jafar yana fad'in to mungode, ya aikin?.
Alhmdllh Dr jafar yafad'a cikin 'yar kunya.
Asma'u kam tana gefe ko kallo baima ishetaba, Dan yana jerin manyan wad'anda tatsana wlhy. Koda yad'ago suka had'a ido, yawashe baki zai gaisheta saita daka masa wata uwar harara.
Ruf yarufe bakinsa yakasa magana.
Abin nasu yaso bama ya Umar dariya, amma saiya gimtse yayima Dr jafar sallama yabi bayan Asma'u dahar takusa shan kwana.
Harara Dr jafar yaraka bayan ya Umar da ita.
Nikam bilynku na ce, "ohodai ihu bayan hari kenan."🤷🏽♀😜
Da k'yar ya Umar yacimma Asma'u suka k'arasa office d'in Dr Al'ameen batareda suma juna maganaba.
Cikeda fara'a Dr Al-ameen yakar6esu Dan dama yasan da zuwansu, cikin barkwanci aka gaisa sannan yafara tambayar waye bashida lafiyane?.
Ya Umar yanuna Asma'u, wlhy doctor my wify ce babu lafiya, kullum sai yawan barci datakeyi, so gashi sai ramewa takeyi babu gaira babu sabar.
Dr Al-ameen ya maida kallonsa kan Asma'u yana fad'in madam abinda oga yafad'a gskyane?.
Fuska tad'an marairaice, Dr nifa nagaya masa k'alau nake amma yak'i yarda, babu inda yakemin ciwo saidai yawan barcin kawai.
Murmushi Dr Al-ameen yayi batareda ya ce, ''komaiba.
Rubutu yayi atakarda kafin yad'ago yana mata 'yan tambayoyi.
Duk tana basa amsa yanda yakamata. Bayan yagama tambayarta ya ce, "ga bayinan tashiga tayo masa fitsari a wata 'yar kwalba daya mik'a mata.
Kar6a yayi jiki a sanyaye Dan itama tafara zargin Kodai batada lafyarne da gsk?.
Mintuna kad'an tadawo, Dr Al-ameen ya kar6a sanan yay kiran Norse Hafsat. Saida ta gaisheahi sanan yamik'a mata kwalbar, sister plz ina buk'atar result dangane da fitsarinan yanzu.
Rissinawa tayi takar6a tana fad'in okey sir.
Sunanan zaune a office d'in, marasa lafiya suka cigaba da shigowa Dr Al'Ameen yana dubasu.
Bayan kamar minti talatin saiga sister Hafsat da takarda ahannunta.
Rissinawa tayi tabama Dr Al-ameen sanan tafice.
Kallon farko da Dr Al-ameen yayma takardar fuskarsa ta Nuna alamar farinci. Yad'ago yana kallon ya Umar da Asma'u.
Alhaji Umar congratulations, madam tana d'aukeda babbar k'yautane.
Doctor kana nufin matata tanada ciki kenan?.
Hakane Alhaji Umar, ALLAH ya inganta.
Ya Umar yad'aga hannu sama yana muk'a godiyarsa ga ubangijin talikai. Asma'u kam mamakine yakamata, dama haka akeyin cikin salin alin? Itafa wlhy ko ciwonkai bataji, babu wani wuri dake mata ciwo, saidai kawai kasala da barcin datakeyi yanzu babuji babu gaini........
Ya Umarne ya rungumeta yana fad'in Alhamdllh, wanan yasaka Asma'u dawowa hayyacinta.
Har k'yautar agogo mai masifar k'yau na azurfa ya Umar yayma Doctor, agogo ahannunsa yake amma yacire yabashi.
Ya Umar ya ce, "amma Doctor kofa laulayinnan namasu ciki batayi, saidai barcin kawai, da rama?."
'Yar dariya Dr Al-ameen yayi, karka damu wanan bawata matsala bane, kowacce mace akwai salon cikinta. Wasu zakaga sun farane da amai, wasu kwad'ayi, wasu ciwon ciki, wasu zazza6i, wasu basason abinci, yanayin kala-kala yake zomisu, wasukuwa kamar na madam d'inkane babu ciwo komai, watama saitaje watan haihuwa ko irin ciki yakai wata biyar d'inan sanan take fara laulayi.
Jin jina kai ya Umar yayi Alamar gamsuwa, magunguna yarubuta musu da Asma'un yakamata tad'an fara amfani dasu Dan inganta lafiyarta da jaririn cikinta.
sukai masa godiya sanan suka tafi. Daka kalli fuskar ya Umar Kasan yanacikin farinciki, yanason yara amma aka rabashi da nasa, ALLAH gafurun rahimun gashinan ya azurtashi da samun wani.
Itadai Asma'u tayi shiru, dukda tana cikin matuk'ar farinciki itama zata zama uwa, amma tana fargabar ranar haihuwa Dan ance akwai wahala....
Ganin sun tsaya k'ofar gidansu tad'ago da sauri tana kallon ya Umar. gira yad'aga mata yana biyan mai adaidaita kud'insa.
Hannunta yakama suka nufi cikin gidan, itama fuskarta d'aukeda farincikin ganin innarta da abbanta.
Kwace hannunta tayi zata shek'a da gudu, da Sauri ya Umar yarik'eta, k" tsaya karkimin ganganci mana, tsayawa tayi saboda rik'e hannunta dayayi, ya harareta kinmanta da abinda ke jikinkine?.
Bakinta tad'an turo gaba amma batace komaiba. Jan hannunta yayi suka k'ara cikin gidan.
Afalo suka tadda fatee da Hasiya suna yankan d'inki, sunajin sallamar Su Asma'u suka tashi suna ihun murna, rungume juna sukayi, ya Umar yazauna yana murmushi.
Ihunsune yafito da inna daga d'akinta, tana fad'i kai lafiyarku kuwa kuke mana ihu haka?.
Asma'u tana ganin inna tasaki su fatee tanufi inna ta rungume.
Wai! Asma'u zaki karyani aii.
A'a innata, INA murnar ganinkine.
Itama saita rungumeta tana fad'in sannunku da zuwa to.
Ya Umar ya ce, "inna barka da fitowa."
Barka kadai Umaru, wannan rigimammar tahanani zama.
Dariya yayi shima, inna ai tana murnar ganinkune, kwana nawa bata gankuba?.
Da sauri Asma'u ta ce, "wata bakwai kenan rabona da gidannan, tundafa nayi aure saud'aya nata6a zuwa saikuma yau." ‘tak'are maganar tamkar zatayi kuka.’
Hasiya da fatee kam dariya suke mata, inna ma saida ta dara, ta ce, "umaru kana fama wlhy."
Murmushi yayi, yana sunkiyar dakai k'asa.
Asma'u da fatee da Asiya kam tuni sun shige d'aki, kira inna ta kwalama fatee tafito, inna gani.
O yau Dan kunga Asma'u shine ko ruwama bazaku kawoma yayankuba.
La'ila wlhy inna na mantane, da sauri tafita saigata da ruwa harma da zo6o da abinci.
Ya Umar yafad'ama inna abin farincikin daya samesu. Yana maganarne kansa ak'asa.
Dariya inna tayi Dan ganin yanda ya Umar yamaida ita surukarsa yau. To Umaru ALLAH ya inganta.
Ameen yafad'a a la66ansa.
Hirarsu suka cigaba dayi shida inna, dukda dai yaud'in akwai 'Yar kunya tsakani.
Itama Asma'u tanacan itada k'annenta.
Sunkai wajen awa hud'u agidan sanan suka tafi, Asma'u nata zum6ura baki ita bayanzu zata tafiba.
Ya Umar bai kulataba suka tafi, daga nan sai gidan mama.
Tarba sosai mama tamusu wadda tayi matuk'ar bama ya Umar mamaki, amma saiya danne mamakinsa yasaki jiki da ita sosai kodan Asma'u.
Itama yafad'a mata Asma'u nada ciki. Rungumeta mama tayi tana saka mata albarka, duk mugun halin mama nason kud'i tana k'yaunar jikokinta, sosai ta nuna farincikinta, suma Rafi'a da Mufida sunyi matuk'ar farincikin ganinta, nanko sukaita shan hirarsu.
Anan Umar yabarta sai bayan isha'i yadawo suka koma gida.
____________________
Bayan wasu satittika.
Abubuwa nata tafiya yanda yakamata, Asma'u tanata rainon cikin dabatajin kamar akwaishi, har yanzu tana nan da barcin tsiyarta. Ya Umar ma yana bata kulawa ta musamman, jiyake da ita aynun, komai takeso shine daidai.
Ana haka matar Muktar ta haihu, sosai akasha hidima, ya Umar yataka rawar gani, hakama su Asma'u sune amarori.
Taro yatashi lafiya, Asma'u tacigaba da rainon cikinta.
Wata ranar laraba da safe Anty Sa'a tazo dakanta takawoma Asma'u alk'awarinta.
Bayani tamata sosai yanda zata fahimta, amma ta ce, "kada tasha sai nan gaba cikinta yayi kwari.
Godiya sosai Asma'u tamata.
Anan takusan yini, sai gabda azuhur tatafi gida.
Angama komai danganeda mall d'in ya Umar, kuma kayan dasukayi oda sun iso, komai anzuba awajen, yakoma tamkar yanda yake ada, dukda dai kayan basu cikaba tamkar da d'in.
Amma kokad'an ya Umar baya zuwa wajen da rana ballema wani yagansa, muktar da Harris da Sadam ne ke kula da wajen, shikuma Yakoma zaman shago kamar da.
Harris ma bai fad'ama kowa ya Umar ya bud'e mall nasaba, yadai Sanar da iyayen nasa yasamu aiki a tsohon gurin ya Umar, wad'anda suka sayi wajenne suka d'aukeshi aiki.
Bikin Mufida nata matsowa, kullum mama tana zuba idanu taga ya Umar yakawo mata kud'i, amma saitaji shiru wai malam yaci shirwa.
Tunda tana kawaicin jira har ranar ta tambayesa maganar kud'in.
Murmushi yayi kamar yanda yasaba, muryarsa a tausashe ya ce, "mama har yanzu basu baniba, amma kitayani da addu'a ALLAH ya kwato min......"
Da sauri tad'aga masa hannu, cikin masifa ta ce, " kai sauraramin! Nizaka madai sakarai Umaru!? Shin wane shegene zai sayi Abu ya hanaka kud'inka?.
Nafa lura yanzu kaima ka canja, harma gara Abubakar d'in dakai.
Kud'i karik'e karka bada, ALLAH bazai hanamu yanda zamuyiba, nitashi kabani guri shashasha kawai.
Anutse ya Umar yatashi yafita batareda yace da ita komaiba.
Yana fita wayarsa tafara wringing............
_kuyi hak'uri da wanan._
*_(((S))).......2017_*
*_Love you all_*
[12/27/2017, 3:16 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_Mutuwa! mutuwa!! Mutuwa!!!. Mutuwa maiban tsoro, batabarin kod'an yaro, ko jinjiri saita d'auka, takaishi koda bayaso mak'abarta. Sarki ALLAH jallah, Jallah nidai natuba ALLAH, rabban kayafemu albarkacin manzo nawa d'an gata._*
_wannan wak'a gsky Ce, kuma tana ta6amin zuciya aduk lokacin Dana tunata wlhy._
😭😭😭
*_page→55-56_*
..........A kasalance yad'aga, dan wringing d'in wayar bak'aramin fad'uwar gaba yasashiba. Komiye dalili oho.
Asslamu alaikum, yayi maganar cikin sanyi.
Daga can yazeed ya amsa masa shima muryarsa a raunane, yad'ora da fad'in abokina kakalli labarai kuwa?.
Yanzuma a sanyaye ya Umar ya amsa masa da a'a abokina, amma miya faru?.
Jimmm yazeed yayi, zuwa can kuma ya sauke ajiyar zuciya, Umar sirikinkane sukayi had'arin jirgi yanzunan babu dad'ewa.
Da Sauri ya Umar ya dafe k'irji, cikin matuk'ar razana ya ce, "kana nufin dady mahaifin lubna!!!?.
Eh Umar, idan kana kusada TV ka kalla gashinan suna nunawa........
Bai bari yazeed yagama fad'aba yajuya cikin gidansu arazane.
Mama tana zaune har yanzu tana mita da zagin ya Umar saitaga yashigo aburkice, baibi takantaba yanufi TV ya kunna, NTA yakamo, ilai kuwa abinda suke nunawa kenan, had'arin yafarune a hanyarsu ta zuwa legos daga nan kano.
Mama ma sai jikinta yayi sanyi tatsaya sagare tana kallo.
Bak'aramar tarwatsewa jirgin yayiba, ga mutanenan kwance, wasuma Kansu yacire, wasu k'afa, wasu hannu, wasuma babu ta yanda za'a shaidasu dan duk sun canja kamanni. d'aya bayan d'aya akebi ana nunasu dan ana kwashe gawawwakinne da duba masu rai, dukda babu alamun akwai wani mahaluki dake numfashi acikinsu. gawar mahaifinsu lubna aka nuno, cikin amincin ALLAH shikam kamanninsa na nan, saidai jini dukya 6atashi, sannan hannunsa d'aya yafita.
Ya Umar yaruntse idonsa hawaye na kwarara, mama kanta kuka takeyi, (bak'aramin abune yake raunana jarumtar gwarzo namiji irin ya Umar ba) zuciyarsa da kwakwalwarsa suka Shiga tuno masa waye dady?, mutumin kirki maison talaka da son k'yautata masa, ya tuno ranar daya fara ganinsa shida direbansa, alkairin daya masa ya d'aga darajarsa fiyema da 'ya'yan cikinsa, wasu zafafan hawaye suka k'arayo ambaliya akumatunsa.
Mamace tayi k'arfin halin kama hannunsa ta zaunar akujera, a hankali take shafa kansa tana lallashinsa, ita kanta tasan miye matsayin dady azuciyar ya Umar, kosu sukace sun manta da halaccinsa akan d'ansu sunyi butulci ba k'aramiba.
Lallashin ya Umar takeyi sosai Wanda yake kuka harda shashshrka, kansa yana saman cinyar mama.....Umaru yanzu ba kuka yake buk'ataba, yana buk'atar addu'a ne daga garemu, babu abinda zamu sakanka masa dashi aduniyarnan inba addu'aba, Wanda ya haliccesa shine ya kar6i abinsa, muma nan duk irin wannan ranar muke jira Umaru...... Da ire-iren wad'annan maganganun ta kwantar masa da hankali.
Ahankali yafara sassauta kuka nasa saidai ajiyar zuciya, haka su Rafi'a suka dawo daga gidan inna suka samesu.
Suma sungani agidan inna dan haka basa buk'atar k'arin bayani, saidai ya Umar yabasu tausayi ainun.
Baibar gidanba saida aka kira sallar magriba.
Atsakar gida yatarar da Asma'u zaune saman kujera 'Yar tsugunno. Ta rabga tagumi.
Ko motsin shigowarsa batajiba barema sallamarsa, shima bashida k'arfin mata magana, saikawai yajingina da bango yazuba mata idanu tamkar mai nazarin wani abu.
Sunkai minti20 ahaka sanan ALLAH yabama Asma'u ikon d'agowa danjin kamar alamar mutum tsaye akanta.
Tarazana sosai, dan haka tayi shirin takewa da gudu, muryarsa a sanyaye ya ce, "Asma'u ninefa."
Gabantane yay azabar fad'uwa danjin muryar ya Umar dakuma sunan daya kirata dashi, Wanda zata iya rantsewa bata ta6ajin sunan abakinsaba sai yau.
Ya Fharuk lfy kuwa?.
Ajiyar zuciya ya sauke wadda yayita sau babu adadi, muryarsa hard'an rawa takeyi ya ce, "dadai sauk'i Husna."
Shiru tayi tana nazarinsa, saikuma yabata tausayi, gashi sunyi azumi, takama hannunsa suka shiga ciki.
A babban falo ta zaunar dashi bisa tabarmar data shirya kayan shanruwan.
Baice mata komaiba, tazuba zo6o mai sanyi tamik'a masa, kai ya girgiza mata alamar a'a ya k'oshi. Tuni idanunta suncika tab da kwalla, ganin haka sai kawai ya kar6a ya shaya kusan rabi, daganan yajingina da bango yay shiru.
Itama Asma'u shiru tayi, tasan bak'aramin abune yata6a zuciyar mijin nataba.
Haka sukaita zaman shiru har aka kira sallar isha'i.
Bai iya fitama masallaciba yayi sallar agida. itamadai Asma'u tayi tata sallar.
Har k'arfe kusan goma babu Wanda yazubama cikinsa komai. Cikin Asma'u ne yafara kiran Ciroman yunwa, dama 'yan kwanakinnan bata iya jure zama da yunwa saboda cikinta yafara girma, azuminma dak'yar take kaishi aduk ranar litinin da alhamis dasukeyi yanzu.
Zamewa tayi ta kwanta akan abin sallar, ya Umar yabita da kallo saita bashi tausayi daya tuna bafa ita kad'ai baceba, gakuma azumi dasukayi.
Tasowa yayi daga inda yake zaune yadawo kusada ita, ya had'a shayi mai kauri akofi, yazuba soyayyen dankali afilet da kwai (dan yanzu alhamdulillahi, basuda Matsala a a6angaren abinci. Ko abayama dasuka Shiga halin ha ula'i suna samu suci koda baikai yanda suke soba).
batareda yamata maganaba yakamata yatayar zaune, jinginata yayi da jikinsa sannan yad'akko kofin shayin daketa turiri kad'an-kad'an yakai bakinta.
Kauda kanta tayi gefe alamar bazata shaba. Bayason yawan magana yanzun amma yakula saita sakashi yayi akan dole. muryarsa asanyaye ya ce, "kidaure koda shayinne kisha mana, kinga bake kad'ai baceba.
Itama idanunta tad'ago tana kallonsa, yaya Indai kanaso naci to saidai muci tare. Ahankali ya girgiza mata kansa alamar shi ya k'oshi.
Itama saita kauda NATA kan ta ce, " Nima nak'oshi, tayunk'ura zata tashi daga jikinsa.
K'ara rik'eta yayi dak'yau dukda jikinsa babu kwari, kinga to zauna zanci.
Babu musu tazauna da k'yau, yana bata tana bashi harsuka d'anci babu laifi.
Asma'u tagyara wajen tsaf, lokacin data dawo yashiga d'akinsa, itama saita wuce NATA d'akin cikeda tunanin mike damun ya Umar ne?.
Saida tayi wanka tai shirin barci, zaman jiransa ta zaunayi, ganin lokaci yanata tafiya kuma ko alamarsa babu yasakata mik'ewa takashe komai tafice, tasaba kwanciya ajikin ya Umar dan haka bazata iya barciba ayanzu idan baya a kusada ita.
d'akin tatura tashiga da sallama, turus tayi dan ganin ya Umar kwance bisa katifa a yanda yashigo, ko Riga bai cireba barema asaran yayi wanka.
Jikinta asanyaye tak'arasa gareshi, jin motsinta da k'amshin turarenta yasakashi tashi zaune.
Idanu yakafa mata kamar mai hango wani Abu, tazo ta zauna ajikinsa tana tambayarsa abinda ke damunsa.
Awanan karon bai 6oye mataba yafad'a mata komai.
Itama har kuka tayi dukda bawani saninsa tayiba sosai, ranar ma dasukazo da family d'insane har ya Umar yamari Lubna, aranar tafara ganinsa. tundaga ranar kuma bata kuma ganinsaba.
Daga k'arshe sai ya Umar ne Yakoma lallashinta.
Ta ce, "ALLAH yajik'ansu yagafarta musu ya yafe musu.
Ameen ya Umar yafad'a yana kuma rungumeta da k'yau........
_____________________
Washe gari yazeed yazo sukaje gaisuwa shida abbansu dakuma baban Asma'u, da muktar, Harris, Sadam.
Sun sami gidan cike da al'uma kala-kala, dan yaune ake jana'izarsa, sarakuna, 'yan siyasa, 'yan kasuwa, masu madafun iko a gwamnati, harda mutane daga k'asashe daban-daban. Dan shi d'an kasuwa babu inda babushi, musammanma irinsu dady dasuka zama manya dolene adama dasu ako ina.
Suma su ya Umar anyi jana'izarsa dasu, sai yamma lik'is suka sami damar ganinsu safwan, sannan mutane sunragu sosai.
Har cikin gidan akai musu iso sukayi gaisuwa, saidai su ya Umar basuga Lubna ba. Amma ya hango 'yan biyu ajikin momynsu Lubna d'in.
Ko magana basuyi masaba dan ayanzukam summa manta dashi. Shima baice dasu komaiba tunda ana cikin rud'anine.
Kwana uku suka jera suna zuwa kullum.
Sai'a rana ta k'arshene ya Umar yaga Lubna tsaye aharabar gidan tayo rakkiyar wasu 'yan uwansu dazasu tafi.
Sanye take da dogon hijjabi mai hannu haryana Jan k'asa, balaifi tarame sosai dan mutuwar tarazanasu ainun, tanata jan carbi.
Suna had'a ido da ya Umar gabanta yafad'i, shima kansa saida yaji wani Abu.
d'auke kanta tayi daga garesu, tamaida hankali wajen yin sallama da 'yan uwan nasu dasuka shiga mota. Saida motocinsu suka fice sannan tajuya zasu koma itada Suhaima, da Jiddah matar Ameer.
Yazeed ne yay k'arfin halin kiran lubna d'in.
Tatsaya cak itasu Suhaiman, amma babu Wanda yajuyo acikinsu saidai Jiddah.
Su yazeed basu damuba, dan yauma subiyune kawai, dagashi sai ya Umar.
K'arasawa sukayi inda suke. su ya Umar suka gaishesu tundasu sungaza gaisheau. Jiddah ce kawai ta amsa da arzik'i, amma Suhaima da Lubna sai wani yatsine-yatsine sukeyi.
Sudai su ya Umar basuwani biye musuba sukai musu gaisuwa.
Fuuu suka shige ciki, jiddah kuma tatsaya ta amsa musu harda musu godiya da fad'in ALLAH yabada ladah.
Haka sukabar gidan, tsakanin ya Umar da yazeed babu maicewa uffan. Har k'ofar gidan yazeed ya sauke ya Umar, sukayi sallama.
Yazeed ya ce, "yakamata kashirya gobe idan ALLAH ya kaimu muje wajen saida motoci Umar. Baikamataba ace kacigaba dayawo hakaba.
d'an murmushi ya Umar yayi, karka damu yazeed kasan abinda yasa kaga inata zamewa gameda sayen motarnan, kayi hak'uri na kwantar dawata k'ura sannan, kasan babu Wanda yasan halin da ake ciki har yanzu.
Hakane kuma, namaka uzuri, ALLAH yakaimu lokacin, ubangiji yagyara mana komai cikin hikimarsa da ikonsa.
To ameen ngd sosai abokina, ka gaidamin madam da yara.
Zasuji insha ALLAHU, Nima ka gaidamin madam.
Sallama sukayi yazeed yaja mota yatafi, shikuma yashiga cikin gidan.
Asma'u na kichin tana k'ok'arin had'a kayan bud'a baki. Jin motsinta akichin shima saiya nufi can. yad'an zaro idanu waje dan ganin tana cin k'osan datake soyawa, madam ina azumin?.
Hannu tasa tarufe fuskarta tana murmushi, ALLAH yaya na karya, jinayi bazan iyaba, ga cikina yanata juyamin.
d'an murmushi yayi, dan yau babu laifi yad'an saki jikinsa, sa6anin kwana biyu dasuka wuce bashida walwala ko kad'an.
Yakuma matsowa kusada ita yana fad'in lallai kinzama ragguwa to.
Yaushe kika karya?.
ALLAH yaya ba ragwantaka baceba, tun sandasu Rafi'a sukazo.
Sune suka sakaki kika karya kenan?.
Idanu tazaro lah bafa subane wlhy, kayarda dani ALLAH.
na yarda dake, cigaba da aikinki to, k'osan zai k'one.
Da sauri takoma kan aikinta tafara kwashewa danya soyu.
Yaukam babu laifi bayan shanruwa ya Umar yazauna sunyi hira, acikin hirar tasunema yakecewa tadakata da azumin tahuta hakanan.
Ta ce, "aii zata iya, yau d'inma dan and'anyi ranane.
A'a kibarshi haka, dama inada niyyar tsaidaki saboda babyna baya samun isashshen abinci awajenki.
Hannu tasa tarufe fuska tana fad'in kai yaya.
Dariya yayi yana kwanto da kansa bisa cinyarta tareda tura hannunsa arigarta yana shafa d'an matashin cikin NATA dayayi d'as ajikinta, ya ce, " my baby ALLAH yakawoka, ko yakawoki duniya lafiya. Kullun mafarkin isowarka nakeyi.
Asma'u dai shiru tayi tana kallonsa yanda yake magana da ciki tamkar maiyi da mutum............
_kunjini shiru. Babana ne babu lafiya wlhy, amma Alhmdllh jikin da sauk'i, muna buk'atar addu'oinku plss._🙏🏻
*_(((S))).......2017_*
*_I Love you all_*
[12/27/2017, 4:01 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→57-58_*
..........Bikin Mufida ya kankama sosai, hidima akeyi babu kama hannun yaro.
Ya Umar dai baice dasu komaiba, ko kwayar shinkafa baikai gidanba, dukda mama tamasa magana.
Cemata yayi baida kud'i, kuma ba yaya Abubakar duk yace zaiyibane?.
Shiru tayi dantasan inda maganar tasa tadosa.
Har ana gobe d'aurin aure babu wani abin arzik'i daya sauka gidan.
Babu kayan miya bare nama kokuma wanidai Abu daya danganci abinci har hud'u na yamma kuwa.
Ana nan zaune jigum-jigum.
Kowadai yasan al'adar makwafta da danginka nakusa sukan shigo domin rage aiki ana gobe d'aurin aure.
Gakuma gida cike damk'an da dangi na nesa wad'anda tun ajiya suka fara sauka gidan.
Ana nan zaune jigum-jigum kowa yana raba idanu yaga ta inda abinda ake jiran zai 6ullo. Cikin amincin ALLAH saiga yi anfara shigowa da kayan gado na Mufida.
Nan take kallo yakoma sama, mamaki al'ajabi yacika mutane, kayan gadone irinna da-da d'innan, kuma kallo d'aya zaka musu kagane tsofaffine akaima kwaskwarima kawai. abin mamakin baigama k'arewaba saida aka dire rabin kwandon tumatur, da attarugu da tattasai acikin yellow d'in leda mai layi-layi, sai alayyahu buhu guda maicin arba'in🙊.
Saikuma ga garin tuwon dabai wuce kwano ashirinba, gefe kuma da shinkafa 'Yar Hausa mai tsakkuwar tsiyarnan dabata wuce kwano ashirinba itama.
Kowa yayi cirko-cirko yana kallon ikon ALLAH, Saiga ya Abubakar yashigo saiwani bud'awa yakeyi yana washe hakwara, shi a adole yayi abin arzik'i yau.
Sai gaida mutane yakeyi washeda baki, amma ganin kallon dasuke masa saikuma jikinsa yayi d'an sanyi.
Yakai dubansa kan mama da inna, sumadai kallonsa sukeyi cikeda mamaki, amma a can k'an zuciyar inna tana fad'in ALLAH ya k'ara.
Inda suke yak'araso, har yanzu bakinsa awashe yake, dukda jikinsa yayi la'asar. Mama inna! gafa kayannan sun iso, kunata kirana mutane suna jira sufara aiki ko?, wlhy inacikin kasuwa nayi matuk'ar busy, gashi dak'yar nasami motar data d'akko yakayan gadonnan, kiranma dakukemin yasakani azamar tahowa, kaji na nan za'a kawo guda Biyar manya-manyanema wlhy.
Inadai fata komai zai wadatar da kowa?, kuzo kuduba kayan gadonma, kafintan ya iya aiki wlh...........
Hannu mama tayi saurin d'aga masa dan surutunsa yafara addabar kunnenta.
Hawaye suka zubo bisa kumatunta, cikin shashshekar kuka ta ce, "Amma Abubakar kaji haushin rayuwarka, kaje, nidai kawulak'anta ko? babu komai ngd.
ALLAH sarki Umaru ALLAH yayi maka albarka. Basai mutum yamutuba ake tuna alkairinsa.
Dama duk Wanda yagaza godema ALLAH na tabbata zai godema azabarsa.
Banga laifinkaba abubakar saidai nawa, yau ga abinda halina ya jazamin, ALLAH kamin ni'ima maimakon nagodemaka saina butulce, ya ALLAH ka gafarceni, natuba ALLAH, wlhy natuba.
BakI ya Abubakar yata6e waike mama miya kawo wad'annan surutan ne haka?.
Ubankane yakawosu matsiyaci kawai.......
Bata k'arasaba inna ta to she mata Baki tareda janyeta suka koma baya saboda idon mutane, ya Abubakar baifasa bin bayansuba. Shima ya Umar saiya biyo bayan ya Abubakar dan shigowarsa gidan kenan shima, amma yaga dukkanin kayan dake zube a tsakar gidan, harma yayi gamo damai kawo kaji ak'ofar gidan.
Lafiya kuwa inna? Maganar ya Umar tadaki kunnuwansu.
Atare suka d'ago suna kallonsa, mama tasake fashewa da kuka tana koroma ya Umar bayani dalla-dallah.
Shiru yayi yana saurarenta, tausayinta yacikama masa ciki, kafin ya ce, " wani abu saiga Abba yashigo shima afusace.
Ganindai komai zai kwa6e agaban mutane inna ta ce, ''sushiga d'akin Abba.
Zaune suke suduka a falon Abba, wannnan karon harda Harris da mufida da Rafi'a.
Inna ce tayi magana duk tana bin kowannensu da kallo.....
Ita gsky d'ayace, kuma daga k'inta said 6ata, lallai inamai jaddada muku Abubakar bashida wani laifi, laifinkune wanan, tunda tun farko kune kuka d'ora yarannan akan wannan mummunar tarbiyyar.
Kuna Nuna banbanci akan 'ya'yanku saboda wane yanadashi, wane bashidashi. Kund'auki dukiya tamkar itace jigon rayuwa. Kudubafa halin da Umaru yashiga a watannin baya, amma acikinku babu Wanda yata6a waiwayarsa yasan yaya yaci, balle ya yaciyar da iyalinsa. Bak'aramin tashin hankali yaronnan yashigaba, badan mai tawakkali bane Aida yanzu an mance kamanninsa ko?.
Amma maimakon kujawoshi jikinku, kuringa kwantar masa da hankali, saikukayi watsi da labarinsa kuka kama Abubakar mai kud'i kuka rik'e ko?.
Wannan wace iriyar rayuwace haka?, aurenfa mufida aka saka agidanna amma Umaru baison komaiba akai saboda son zuciya irin naku. Kuji tsoron had'uwarku da ALLAH mana, kufa iyayene masu tarbiyyantarwa bamasu ruguzarwaba, ALLAH fa baya d'orama bawansa abinda bazai iyaba.
Shin ku'a tunaninku kunada wata dabara ta gujema talauci kenan?.
Hummm shidai Ubangiji aiba abokina wasan wani shege bane.
Ai yanzu ba tsinar Abubakar zaku hauyiba, hak'uri zakuyi da abinda yakawo ayi bikin haka, arurruma akaita kowa yahuta......
A'a inna idan ya Abubakar zaibani rancen koda dubu d'ari biyarne sai ayi komai yanda suke buk'atar d'in......
Carab ya Abubakar ya kar6e zancen, a INA naga wata dubu d'ari Biyar in? Kokuwa kud'in kasuwata zan gird'e nabaka rance saboda kanaso ayi biki waje-waje?.
Wlhy Umar kafita idona narufe, yanzu wannan siyayyar dakuke rainawa tawajen dubu d'aricefa. Ko kayan gadonnan hallidu kafinta a dubu arba'in da Biyar yayimini su babu Ragin ko sisi wlhy.
Ince yanzudai inna tagama wa'azi akan rashin godiyar ALLAH ko?....
Ba godemakane ba a yiba ya Abubakar, kawaidai INA buk'atar rancenne.
To banidashi d'an jonin masifa, kaid'in baca akayi ka saida mall d'inkaba? Ina kakai kud'in? In ba neman alagidigo da hankalin mutaneba kakeyi?.
Ajiyar zuciya ya Umar ya sauke, ya marairaice murya, (amma a can k'asan zuciyarsa dariyace ke bal'in cinsa, daurewa kawai yayi ya gimtseta) ya Abubakar bawai inayin Alagidigo da hankalinku baneba, har yanzu wad'anda suka sayi wajennan basu bani kud'in baneba.
Amma munyi alk'awarin nanda wata shida zasu bani adunk'ule, dan banason kud'i gutsin-gutsin.........
Kai dallah sauraramin, wlhy Umar kafita sabgata nasha iska, inbanda raini taya zanyi nad'auki dukiyata nabaka har tsawon wata shida, nikuma nazauna fanko, saboda inajin tsoronka, angaya maka nid'in sallamammene ko shashasha?........
Mamace tak'atse musu zance cikin raunin murya, kabarsa Umaru Shiba sallamamme baneba, nasan babu yanda za'ayi nunkufurci irinna Abubakar yabarsa baka bashi.....kuka yahanata k'arasawa.
Abbah dai yayi shiru, dan tsorone fal ransa, idanfa Umar baisamu kud'innanba dolene shizai nemosu, tundadai mufida diyar cikinsace, atsarima shiya halatta yayimata kayan d'akin. Wani haushin Abubakarne ya kuma tunik'e zuciyarsa.
Agefe kuma dariya na cin zuciyar inna da Harris, dan sunsan ya Umar yanayin pretending ne kawai.
Rafi'a da mufida kam sai ballama ya Abubakar harara sukeyi, karma mufida taji labari, dan zuciyarta akuntace take, wai itace za'akai gidan miji da kayan gado nawajen halladu kafinta?.
Ita bamatasan yanda ya Abubakar ya tsanetaba. Tafashe dakuka Wanda yadawo da hankalin kowa akanta, cikin kuka ta ce, "Abba aidai kai kanada kud'in yimini, kowadai yasan halin da ya Umar yake aciki? Inhar ba'a tausaya masaba to ai ba'a tsine masaba. Niko wlhy Indai kayan wajen halladu kafinta za'a kaini dashi to na hak'ura da auren, ta tashi fuuuuu tafita tana kuka.
Babu wanda ya iya cewa komai, daga nan ma suma taron ya watse.
Ya Umar ma gidansa yakoma yay kwanciyarsa, dama kansa namasa ciwo.
Asma'u kam tana gidan bikin, bama tasan wainar da'ake toyawaba.
Sudai makwafta suka hau gyara abinda yasamu, masu gulma nayi masu tu'ajjibi nayi, harda masu dariyar mugunta dan kowa yasan mugun halin mama a anguwar.
Zuwa bayan isha'i aka kammala miyar dataji uban alayyahu ko kayan miyar ba'a gani saboda yawan alayyahun.
Tun adaren aka kusa shanye rabin miyar ma, mama tamkar tayi hauka dan bak'in ciki, tarasa inda zata tsoma kanta taji sanyi, gashi batada ko sisi, dan bata ta6a tunani ajiye wasu kud'iba saboda aurennan, tasaki jiki komai Abubakar zaiyi.
Abba madai hankalinsa atashe yake, dukda shida yanada 'yan kud'insa amma mak'o da ganin k'yashi yahanashi fiddosu afita kunya.
Adaren mama da inna sunkira ya Umar yafi sau hamshin-hamsin amma yak'i yad'aga, hakama Abba yakirashi yafi ak'irga amma bai d'agaba.
Hankalinsu dukya tashi, musamman ma inna.
Ita duk zatonta ya Umar yayi pretending ne, fitar dayayi zaije yayo sayayyane, amma har shad'ayan dare babushi babu alamarsa.
Ya Umar kam yana kwance agidansa, kuma duk kiran dasuka masa yana kallo ya sharesu.
Duk kiran daya shigo saiyayi murmushi sannan ya ce, "inna mama Abba kufayi hak'u wannan ba Umar d'in dakuka Sani bane, na yanzu ya canja, yasan dad'in dukiya shima, ni babu abinda zan muku, koma wajen d'aurin auren babu mai ganina.
Wannan zai zamemuku izina aii.
Inna ki gafarceni wannan karon kema bazan saurarekiba.
Dayagaji dajin wringing d'in wayar saikawai yamaida wayar salient........
*_washe gari_*
Har kusan 11 babu wani canji agidan, mutane sun sami abun tsogumi sai gulma sukeyi, harda cikin 'yan uwan mama danasu inna.
Zuwa yanzu mama tayi lak'e-lak'e, tayi kuka da nadama har babu iyaka, tasandai yau kunya zasu shatane bata wasaba kam.
Amaryama kuka takeyi rurus, ko wanka tak'i yarda tayima, ta tubure akan tafasa aurenma gaba d'aya, anyi lallashin duniya tak'i sauraren kowa.
Har shabiyu babu wani bayani, gidakam haryama fara d'inkewa da mutane, wasuma badan ALLAH sukazoba, sunzo ganin kwakwafne tunda tun ajiya labari yafara zaga anguwar.
Mutane na tsaye tsirko-cirko akan mama data suma. Dan tashin hankali, ko abincin daza'aci agidan babu to, d'an Wanda Ya Abubakar yakawo ana gama dafawa tun'a gindin murhu mutane suka kwasheshi. Wannan 6acin ran yasaka mama zubewa.
Ana cikin haka sai akaji k'ugin motoci ak'ofar gida. Kafin mutane suyi wani yunk'uri anfara shigowa da manya-manyan kuloli na abinci. gefe kuma ana shigiwa da kayan gado na gani na fad'a.
Ai sai mama ta tashi tashiga jerin 'yan kallo.
Saida aka shigo da kula kusan d'ari ta abinci, gakuma kayan gado na nunawa a sa'a, saikuma ga kayan kichin suma akwalayensu.
Inna dai data kasa hak'uri saida tamatsa tana tambayarsu waya aikosu?............
Kuyi manage da wannan.
*_(((S)))........2017_*
*_I Love you all_*
[12/28/2017, 6:35 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→59-60_*
..........Kai daga ina? Waya aikoku kuma?.
Wani a cikin masu sauke kwalayen ya ce, "Alhaji Umar ne.
Kowa baki ya hangame sama dan mamaki, tuni fuskar mama da inna ta washe, mama kukan farinciki takeyi sa6anin da datakeyin na bak'inciki.
Sunan tsaitsaye tamkar an dasasu saiga ya Umar yashigo, sanye yake cikin kananun kaya, yayi k'yau sosai, kwarjininsa da k'yawun haibarsa sunk'ara bayyana saboda gyaran fuska dayayi.
Mama tak'araso da sauri ta rungume ya Umar. Shima dai yau ya kar6i Maman tasa 100%, kukan dad'i takeyi, haka shimad'in hawayene kebin kumatunsa.
Innace tamusu magana sannan suka koma ciki.
Acan k'uryar d'akin Abba ya Umar ya ce, " mama inna dan ALLAH kugafarceni saboda rashin d'aukar wayarku danayi jiya.
Wlhy mun yafe maka, mun yafe maka umaru, mamace take maganar a cikin kuka.
Inna ma ta ce, "tayafe masa."
Ana haka Abba ya iskesu a d'akin, cike da farinciki ya rungume ya Umar. albarkadai yashata har babu adadi.
Daga nan hidimar biki tacigaba da gudana cikin farin ciki, bakin mak'iya, masu gulma da dariya kuma anrufeshi ruf🤐.
Mufida kam jitayi aduk duniya batada kamar ya Umar.
And'aura aure da k'arfe 2:30pm.
Ango yayi shar dashi, sai washe baki yakeyi yana gaisawa da jama'a.
Hakama amarya mufida a cikin gida, tayi k'yau harta gaji, dangi da k'awaye suna zagaye da ita.
Mama da inna ma dai suna cikin farin ciki mara musali.
Hakama Abba ba'a barsa abayaba, shima yau ya aurar da d'iyar farko a cikin 'ya'yansa.
Ya Abubakar kam bak'aramar k'ullatar ya Umar yayi ba, ko'a awajen d'aurin aure da sun had'a ido saiya d'auke kansa.
Shidai ya Umar saidai yayi murmushi kawai.
Zuwa yamma taro yarage na mata a cikin gida.
Can na hango muku Asma'u itama taci kwalliyarta cikin wani ubansun less pink da ratsin milk, bak'aramin k'yau tayiba gsky, tana tareda matar yazeed da Anty Saddiqa matar muktar.
Zuwa dare aka mik'a amarya d'akinta dayasha Jere da su Anty sa'a da Anty Saratu, saikuma wasu a cikin danginsu na uwa dana uba dasuka biyosu, tun wajen k'arfe d'aya akayi, dukda dai sai yamma lik'is suka gama, ko d'aurin auren basu halartaba.
6angaren abinci kuwa babu Matsala, anci har an barsa, komai ya wadatar da jama'a, dan abincine kala-kala aka kawo, tundaga jalof d'in shinkafa, fankasu, waina, tuwo, gurasa, alala, kai komaidai yawadata, ga ruwa shima, hakama lemuka kowa yasha iya gwargwadon iko.
Bayan ankai amarya akace sushirya za'a dinner da abokan Ango suka shirya.
Su Asma'u anata shiri saitaji wayarta na wringing, d'agawa tayi da hanzari dan ganin ya Umar.
Ko amsa sallamarta baiyiba ya ce, "kin shirya?."
Eh, tafad'a cikin rawar kai.
Cikin dariyar mugunta ya Umar ya ce, "kisameni awaje to."
Aida hanzarinta ta kammala shirinta tafito. Waige-waige taketayi dason hangoshi.
d'it-dit taji motar kusada ita ana mata horn.
Kallon motar tayi saita hango ya Umar aciki. Idanu tad'an fiddo waje dan mamaki, ko'a ina yasamo mota?.
Da wannan tunanin tak'arasa inda yake.
Zagayo mana yafad'a tana bud'e mata k'ofar gefensa.
Babu musu tazagaya ta Shiga ta zauna, wani k'amshin dad'i da sanyi suka ratsata, ta shak'a talumshe idanunta.
Duk ya Umar yana kallonta, dariya kuma nacinsa azuciya, ga wani k'yau da kwalliyar tata tamasa.
d'agowa tayi tana kallonsa, ya Fharuk wannan motarfa?.
Gira yad'age sama yana kallonta da ido d'aya, ta aroce yafad'a cikin wani salon magana.
Amma fa motar tahad'u wlhy cewar Asma'u tana shashshafa kujerun motar na baya.
Saida yatada motar sannan ya ce, "kokinasone?."
Asma'u tarik'e ha6arta, ya Fharuk rufamin asiri, inani ina Mota? Nida ko keke ban iyabama.
'Yar dariya yayi yana k'ara dafe sitiyari dan harsun fara tafiya.
Kedai inhar kinaso kifad'a kawai?..
Tab indai maganar soce kam aii inaso, amma a ina zan samu? anan gizon ke sak'a aii.
Murmushi yayi kawai batareda ya ce, "da ita k'alaba.
Daga nan motar tayi shiru nawasu mintuna.
Wani gurin hutawa yakaita, yasa aka kawo musu abubuwan motsa baki, itadai Asma'u cikawai takeyi, amma hankalinta nacan wajen dinner, kad'an-kad'an saita kalli agogon hannunta.
Duk abinda takeyi idon ya Umar na kanta, amma saiya basar yanata danne-danne awayarsa.
Candai Asma'u takasa daurewa, tad'ago tana kallon ya Umar daketa murmushi yana latsa waya, dan hotuna yaketa mata batareda tasaniba, wajen yak'awatune da hasken lantarki tamkar rana. Itafa dabadan kar ace ta zura k'aryaba dasai tace ba'a 9ja sukeba.
Wajen babu hayaniyar, mutane ma d'ai-d'aine keta shawagi awajen, daka gansu kuma kasan masoyane, saidai asamu banbanci namasu aure da masu zuwa sa6on ALLAH.
ya Fharuk tara saurafa?.
batareda yad'agoba ya ce, "kingaji mutafi kenan?."
Bawai nagaji baneba, amma nasan yanzu anfara dinner d'in.
Fuskarsa yad'an yatsine, ad'age ya ce, "dinner kuma? A ina kenan?.
Sosai tawaro idanunta waje, saikuma ta kwa6e fuska, kai ya Umar kafasan za'aje dinner, kuma nazatama ka d'akkonine dan mutafi.
Kai! Shima yafad'a yanad'an zaro ido. Husna yaushe nacemiki wajen dinner zan kaikai? Nibammasan za'ayi dinner ba gsky.
Shiru tayi masa dan tak'ulu sosai, jitake tamkar tamakeshi dan haushi.
Dukda yakula dayanda tacika tayi fam dan haushi, saiya share, dariya yayi cikin zolaya ya ce, " dinner aii ta 'yammatace bawai cus irinkuba.
Baiyi zatoba saiyaga hawaye sun gangaro akumatunta, wai ita ya Umar kekira da cus!.
Tashi tayi zata bar wajen ya damk'o hannunta. Ta tirje tana fad'in nika sakeni, badai nice cus ba?.
Ina bafa dake nakeba, haba ma'una sorry yeee. Yafad'a yana jawota tafad'o saman cinyarsa, dukda mutsu-mutsun kwacewa datakeyi amma takasa, yaymata k'yak'yk'yawan rik'o, ganin zata tara masa mutane saikawai yafara💋 d'inta.
Muk'us kakeji Asma'u tayi shiru.
Dasalon soyayarsa da wayo irin nasa ya lalla6ata tahak'ura da zuwa dinner d'in.
Dama bayaso taje shiyyasa yaje ya d'akkota.
Sai wajen goma suka bar wajen.
Gida suka nufa, amma tun amota Asma'u tayi barci.
Koda suka isa gida saiya d'auketa cak yashiga da ita ciki.
Tayi matuk'ar gajiyane, dan duk yau batayi barciba, rabonta dashi tunna dare, tundaga sallar asuba batasake komawaba.
Da kansa yacanja mata kayanta zuwa nabarci, yayi mamakin dabata farkaba, dan yasan Asma'u batada nauyin barci. dukda yanatareda uzurinsa haka yahak'ura shima yay shirin barcin ya rungume matarsa suka lula duniyar barci..........
_______________________
A6angaren su Lubna kam an raba musu gadonsu, saboda matsawar dasu Safwan sukayi, ran momy ya6aci matuk'a, amma babu yanda zatayi tunda hak'k'insune.
Tunda akayi addu'ar arba'in suka addabi kowa, dole aka raba kowa yad'auki kasonsa.
Ba k'ananan kud'i da kaddarori suka samuba kuwa, dan mahaifinsu babu laifi yatara musu.
Hummm tunda kowa yakwashi kasonsa saiya kama alk'ibilar data dace dashi kuwa.
Babu Wanda yanemi Sana'a acikinsu kuwa. Dan basu iyaba, ba'a koya musuba, abinda suka Sani kawai shine sukashe kud'i komin yawansu, dasunzo dady zai basu wani. To yau babu dady, yatafi yabarsu cikin babban fili na gwagwarmaya, wato duniya.
Basu Lubna ba kawaiba, hattada mama karenta takeci babu babbaka, sunkoma rayuwarsu tamkar da, kamarma babu abinda yata6a zuciyarsu abaya.
Su Lubna kam aii likafa taci gaba itada Suhaima, murzar kud'insu sukeyi tamkar babu gobe. Sun sayi motoci na garari, hakama sitturu yanzu sai shigar dasuka gadama. To mom dake musu fad'a ada itama ayarta take shek'ewa ayanzu, tataka Wanda taso babu mai abin fad'a tunda tanada 'ya'yan banki masu magana da kowa.
Maganar aurema babu ita a ajandar rayuwarsu, daga bin club sai bin k'awayen banza da boy friends masu tatsesu cikin dabara.
Mom bata bincikar kowa akan dukiyarsa dan acewarta hankali yazoma kowa, idan ka6ata kaikasani, idan ka adanama nakane.
Safwan dayafi kowa rawar kai kam aii inasa-inasa ya had'a yabar k'asarma gaba d'aya. acewarsa yawuce da ajin zaman 9ja yanzu.
Ameer ne kawai zamu iya cewa ALLAH ya taimakesa, ya had'a shi da mace tagari, nuna masa tayi yaraba hannun jari kawai tundashi bai iya kasuwaba.
Dayake yana sonta saiyabi shawararta kuma taimasa amfani. Dama ko a bayan aurensu dataga tarbiyyarsa bata cikaba saita duk'ufa wajen gyarawa, dukda tasha hantara da wulak'anci awajensa hakan baisa tabariba saida taga yadawo hanya d'od'ar. To yanzu haka tanada tsohon ciki haihuwa yau ko gobe.
Lubna da Suhaima ne ke sakkowa daga saman benen gidansu suna taku d'ai-d'ai. Jikake kwas! Kwas!! Kwas!!! Takalmansu nabada sauti.
Ba mamaba hattada Amrah da Afrah dake zaune a falon saida suka d'ago suna kallonsu.
Sanye suke cikin matsatstsun kaya, wandone mai mannewa ajikin nan, sai wata 'Yar mitsilar riga wadda dukansu dazasuyi kwakwkwaran motsi duk sai anga cibiyoyinsu.
Lubna tad'an yane k'aramin gyale, amma Suhaima ko'a jikinta dan ko hula babu a kanta.
Suduka cingom ne abakinsu, kowa nata tauna k'as-k'as. Idan ka gansu basuda maraba da karuwai😥.
Mom ta d'auke kanta cikin matuk'ar 6acinrai, amma batada damar musu magana.
Afrah da Amrah ne suka taso suna fad'in momy muma zamuje.
Lubna ta yatsine fuska tana harararsu, zakuje gidan ubanwa?!! Kujimin yara da d'aukar dala babu gammo.
Dallah kutashimin agaba kafin jikinku yay tsami.
Jiki a sanyaye Amrah da Afrah suka matsa baya.
Lubna da Suhaima suka d'agama mom dake zaune tamkar gunki tana kallonsu, hannu, mom bye...
Basu jira cewartaba suka fice, kowa motarsa yashiga yanufi inda zaije.
Amrah da Afrah kam dasuka fara wayo sosai, dan ayanzu haka shekarunsu takwas, gefe suka koma suka zauna, zuciyarsu cikeda sha'awar abinda sukaga momynsu da k'anwar tata sunayi.
Mom kam hawaye takeyi sosai, jitake mutuwar mijinta tadawo mata sabuwa fil yau.
Afrah da Amrah kam saisuka cigaba da wasansu hankali kwance........
*_duk naga sak'onninku na addu'a ga baba, ngd sosai ALLAH yabada ladan zuminci, masu kiranama ngd sosai wlhy. Kuyi hak'uri, wad'anda sukamin maganaba ta groups zasuga ban amsasuba, messages ne sukamin yawa ta PC wlhy, kunsan nakwana biyu bana online. Kumin afuwa duk naga messages naku INA godiya harbabu adadi 'yan uwana._*
Luv you so much all💋
Bilyn Abdul d'inkuce👌🏼
*_(((S)))........2017_*
*_I love you aall_*
[12/30/2017, 4:54 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→61-62_*
..........A daddafe Asma'u tayi sallar asuba takuma zamewa akan abin sallah ta kwanta. Kafin ya Umar yadawo daga masallaci tuni barcinta yayi nisa awajen.
Kansa kawai ya jinjina yad'auketa cak yamaida kan katifa tareda zame mata hijjabin, shima barcin Yakoma.
Sai kusan goma suka tashi, Asma'u cema tafara tashi. a gaggauce ta afka kicin tana k'ok'arin had'a musu abin kari mai sauk'i.
Cikin 'yan mintuna kad'an kuwa ta kammala, sosai talura da yanda gidan yay datti amma takasa d'aukar tsintsiya tayi koda sharace. Wannan k'azantar data aureta a kwanakinnan tana damunta, tasan ya Fharuk ko kad'an bayason k'azanta. Dantasha ganin 6acinransa sanda yana tareda Lubna kafin ita kuma ya aureta.
Tana zaune afalo sai k'ulla wasik'ar jaki takeyi na yanda zata tashi tarage aikin. Motsin datajine abayanta yasakata juyawa, ya Umar sanye cikin wando dogo da vest yacire jallabiyar dayaje masallaci kenan.
Asma'u ta ce, "Yaya katashi?."
Bai bata amsaba, saidai bin ko'ina na falon yakeyi da kallo a yatsine.
Duk sai Asma'u tasha jinin jikinta.
fuskarsa da alamun 6acin rai, saidai kwarjininsa ya6oye kaso mafi tsoka a 6acin ran nasa. Husna wai wane sabon hali kikeson koya akan tsaftar gidannanne?.
Kallafa kigani, gida Yakima tamkar turken dabbobi, nifa banason k'azanta kuma kinsani sarai.
Sosai idanunta suka cikada kwalla, amma tayi jarumtar rik'esu......cikin rawar murya ta ce, "kayi hak'uri Yaya zan gyara, insha ALLAH bazan sakeba daga yau.
d'an k'aramin tsaki yaja yashige d'akinsa, shima kansa d'akin a harmutse yake, yakai kwana biyar rabonsa da shara. Ananma tsakin yaja mai k'arfima kuwa, Dan har Asma'u tana jiyo sautinsa saboda gidan yakasance babu kayan dazasu hana girmamar sauti komai k'ank'antarsa.
Runtse idanunta tayi Dan harcikin ranta tsakin yashigeta sosai. Tashi tayi akasalance tad'an fara aikin, da k'yar tagama gyaran d'akinta, shima ko morphing bata gamaba taji k'irjinta yafara zafi.
Ajiye morpher d'in tayi tazauna dafeda k'irji. Abaya batama tuna tanada ciki inba fad'a akayiba. Amma acikin watannan ko kad'an batada cikakkiyar lafiya, dauriya kawai takeyi, ciwon k'irji da kasala suke addaba mata, gashi yanzu tadainama yawan barcin bakamar daba dasaita wuni tanayi bata gajiba.
Shigowar ya Umar yasakata d'ago kanta da sauri, kallo d'aya taima fuskarsa ta maida kanta k'asa.
Tunkafin ya tuhumeta tafara magana cikin rawar murya, Yaya kayi hak'u wlhy k'irjina ciwo yakemin.......tak'arasammaganar tana dafe cikinta da k'irjinta dake zafi.
Tausayi tabashi, Dan yagane balaifinta baneba, shi abinda yabashi haushi dabata nuna k'azantar na damunta.
Durk'usowa yayi gabanta yadafa bayanta yana shafawa ahankali, sund'an ja lokaci ahaka kafin yad'ago fuskarta datayi sha6e-sha6e da hawaye.
Gogemata yashigayi amma baiyi maganaba, itakuma tamkar yana zugata sai kuma matso wasu takeyi.
Ganin haka ya Umar ya ce, "kukan ya isa haka kuma malama."
Sassauta kukan tayi saida ajiyar zuciya lokaci-lokaci.
d'agota yayi suka koma bakin katifar, saida yaga tanutsu sannan yay gyaran murya, idonsa akanta ya ce, "zansa asamo miki mai aiki kawai, Dan bazai yuwu mucigaba datafiya ahakaba gsky, inada k'yank'yami Husna kema kinsan haka, kokad'an banason k'azanta.
Amarairaice take kallonsa, muryarta adashe ta ce, " a'a Yaya nidai banason mai aiki. Saidai idan Rafi'a ko Fatee da Hasiya cikinsu wata tadawo nan.
Hannunta yakamo ya rumtse anasa, idonsa nakan fuskarta, husna bazai yuwu mud'aukema mama Rafi'a ba a irin wannan lokacin, kinsan yanzu babu mufida, Fatee kuma tana sana'a itama zamu takurata gsky, saidai idan Hasiya, itama sai idan baba ya amince yabamu tunda dolene tazauna harki haihu, kinga kuwa wata wajen hud'u kenan zuwa biyar.
Kanta ta jinjina tana godiya.
Yad'an murza yatsunta yana murmushi, to amin dariya mana, wannan d'aurewa haka.
Dariyace ta su6ucema Asma'u, tarufe fuskarta tanayi.
Jawota yayi jikinsa ya rungume shima yana murmushi, hannunsa nakan cikinta yana shafawa, murya k'asa-k'asa ya ce, "ALLAH dai yasa kada yarona ko yarinyata suyo gadon wanan saurin kukan naki.
Kanta na bisa cinyarsa tayi 'yar dariya tareda turo baki gaba, tokaima dai karsuyo halinka d'innan na mazurai.
Dariya yayi sosai, cikin dariyar ya ce, " nihar wani mazuraine dani?.
Tab ya Fharuk aii wlhy idan kad'aure d'inan yanda kasan wani soja haka kake.
Yatsansa yasa ya d'alli bakinta yana fad'in mashe ranciya kawai.
Da sauri tasaka hannu tadafe tana fad'in wayyo zafi. Fuskarsa d'aukeda murmushi ya janye hannunta daga kan bakin, o sorry, namanta zan fasa d'an bakin rage zafin.
Hararar wasa tasakar masa, ta yunk'ura zata tashi, ya maidota, sorry my Queen.
Baki tabud'e zatayi magana ya manna nashi.
🚶🏻♀
_______________________
Tare suka wuni agida suna shan sharafin soyayyarsu, da k'yar Asma'u ta lalla6a ya Umar yakaita gidan bikin, yanzuma amotar jiya suka tafi.
Asma'u tayi masa tambayar duniya akan motar wage? Amma yak'i yabata amsa, saidai ya ce, "takice."
Daga baya saita tsuke bakinta.
Ak'ofar gidan Mufida ya sauketa, tareda gargad'in da anyi magriba zaizo sukoma gida.
Ta ce, "to."
Sanda tashiga gidan cike yake da danginsu, Dan harsunzo walima.
Gaisuwa taitayi da dangi, wasu har tsokanarta sukeyi wai sai yanzu take zuwa?.
'Yar dariya kawai takeyi cikeda jin kunyarsu.
Ahaka harta k'arasa d'akin Mufida, a can ta iske Anty Saratu da Anty Sa'adatu.
Bayan sun gaisa, Anty sa'a ta ce, ''o ke ma'u sai yanzu kike zuwa? Halan Umar ne?....
Hannu tasa ta 6oye fuskarta tana fad'in a'a fa Anty, banajin dad'ine.
Dariya duk 'yan d'akin sukayi, mufida dake zaune taci kwalliya da'akasan amarya dashi ta ce, "a'a Asma'u fad'i gsky dai, jiyafa agabana yakiraki, runda ya d'aukeki bamu sake ganinkiba dagake harshi bakuje dinner ba.
La'ilah, Anty Mufida munfaje.
Fatee ta ce, "ki rantse kunje Anty Asma'u!." 'Inafa kallonku kuka tafi amota.'
Hararta Asma'u tayi, to 'Yar saka ido anji.
Yanzummadai dariyar akayi.
Haka akacigaba da gudanar da biki, manyan iyaye irinsu inna sunacan suna rabo, su Asma'u kam ana d'aki anashan shargalle.
Shaf tamanta da sharad'in oga, saida taji anata kiraye-kirayen sallar isha'i sannan ta tuna. Jikinta har rawa yakeyi tajawo Handbag d'inta tafara laluben wayarta. Wayyo ALLAH ni Asma'u naga banu, tafad'a yayinda idanunta suka sauka akan screen d'in wayar. Missed call d'in ya Umar har 7.
Anty Saratu dake gefenta ta ce, "k lafiyarki kuwa?."
Yaya Saratu inafa lafiya, ya Fharuk yacemin da anyi magriba zaizo mu wuce gashi har isha'i tayi. 'Ashe kuma yamin kira har 7 ban d'agaba.'
Yanda tarud'e saitabama Anty Saratu tausayi, duk mace tasan tashin hankalin da ake shiga idan kashiga irin wannan k'angin.
Wayar Anty Saratu ta kar6a, itadai Asma'u tayi sagale tana kallonta. Anty Saratu ta kira ya Umar sau uku amma bai d'agaba, tunawa tayi ko yana masallaci, saita d'an dakata da kiran.
Ana idar da sallah takuma kira, shima saida rakira sau biyu sannan yad'aga. Bata bari yayi maganaba ta ce, "Assalamu alikum, yaya ina yini."
Kamar bazai amsaba, saikuma ya ce, "lafiya."
Tundaga yadda ya amsata tasan akwai Marsala. Amma saita dake zuciyarta ta ce, "dama sonake naji kokun tafine? Asma'u ce ta manta da wayarta awajena, kuma tunda aka kira magriba tafito dankarkaita jiranta.
Ta fito!? Zuwa ina?. 'Ya Umar yay tambayar.'
Jin muryarsa tad'an sassauta Anty Saratu ta gyara zama, k'ofar gida tafito, saidai ban saniba kotana tsakar gidan, danni ina d'aki.
Ajiyar zuciya ya Umar ya sauke, Dan d'azun ransa amatuk'ar 6ace yake, azatonsa Asma'u tak'i d'aga wayarne saboda batason tataho...... Ya ce, " kifito tsakar gidan ki dubamin ita, ganinan zuwa gidan.
To. Anty Saratu ta fad'a tana murmushin nasara.
Asma'u ta rungume Anty Saratu dantaji komai, ngd yaya Saratu, wlhy kin taimakeni, ya Umar d'an barazanane sosai.
Dariya kawai Anty Saratu tayi, ta ce, "kinga tashi muje k'ofar gidan yasamemu a can kawai.
Asma'u taima kowa sallama, sannan suka fito k'ofar gida.
Suna zuwa ya Umar na isowa kuwa. Asma'u ta shagwa6e fuska, kai yaya ina kashige inata zaryar lek'oka tun d'azun kamar nayi k'arya.
d'an hararta yayi ya ce, ''ai ita kika zura, dakina lek'owa dabaki ganniba, tunkafin magriba nazo wajennan inata kiranki amma baki d'agaba.
Lah namanta wayarne awajen yaya Saratu, kumani ALLAH ban gankaba.
To naji shiga mutafi nagaji nikam.
Motar tashiga sukayi sallama da Anty Saratu akan saitazo.
Ya Umar ya harareta, wato haryanzu kina yawon tsiyar nan naki ko Saratu.
Anty Saratu tad'an Sosa gefen wuyanta, ALLAH yaya banayi, zanzo zumincine kawai, nakwana biyu banzo mungaisaba shiyyasa.
To shikenan, kigaida yaran. Yabata dubu biyar.
Godiya tamasa sannan takoma cikin gidan, shikuma yaja motar suka tafi.
________________________
Haka rayuwa tacigaba da shurawa, tun bayan bikin Mufida Hasiya tadawo gidansu Asma'u tanad'an taimaka mata da ayyuka.
Asma'u anata jan ciki, saidai ad'an tsakaninnan tana d'an wahala Dan yanzu ita take nata laulayin cikin.
Sosai take samun kulawa daga ya Umar da danginta, hakama Anty Saddiqa tana iya k'ok'arinta.
Akwana atashi babu wuya, yanzu Asma'u kam tashiga watan haihuwa. Zuwa yanzu tazama alalla6a, sai shagwa6a da rakin tsiya, Abu kad'an sai kuka, wani lokacinma dariya take bama ya Umar, kullum tunaninsa randa Asma'u zata tsinci kanta ad'akin haihuwa.
Yasandai zasusha raki ainun....
A6angaren mall nasa abubuwa nata tafiya dai-dai Alhmdllh, har yanzudai baya zuwa sai lokaci-lokaci, shima saiya faki idanun mutane.
Komai yazeed yatsaya akai, gakuma muktar dasu Harris.
Yanzukam kud'i nashigo masa Alhmdllh.
A6angaren haihuwa kam yatanadi komai, har kayan gado yasiyo da kujeru daza'a zuba agidan, amma Asma'u bata saniba, dan bai kawosu gidanba.
Aranar wata Alhamis da yamma Asma'u tafara nak'uda.
Ya Umar na shago Hasiya taje a hargitse.
Hasiya lafiya kuwa?.
Yaya Anty Asma'u ce, gatacan tan.....
Baibari tak'arasaba ya afako cikin gidan.
Sosai Asma'u tafara jigata, hakan yasa baisaurari komaiba ya sungumi kayansa yakai mota. Hasiya ce tai k'arfin halin d'akko akwatin dasuka shirya kayan haihuwar.
Suna isa asibitin aka kar6esu da gaggawa.
Dr Al-ameen sai kwantar masa da hankali yakeyi.
Wasa farin girki, har wayewar garin ranar Asma'u bata haihuba, sai bak'ar wahala datakesha, duktayi laushi ko nishi bata iyawa.
Zuwa sannan 'yan uwa duksun cika asibitin, hardasu mama, dayake yanzu ta canja hali sosai.
Ya Umar kam aii kamar shima nak'udar yakeyi, dukaya fita hayyacinsa.
Ganin yanda Asma'u ta jigata ko motsin kirki takasa Dr Al-ameen yabada shawarar amata CS kawai.
Kowa yabada goyon baya, ya Umar yasaka hannu a takardar.
Babu 6ata lokaci akayi shirin shiga yima Asma'u theater.
Addu'a da fatan nasara 'yan uwa suka bita dashi. Ya Umar kam saiyayi Alwala yashige masallacin dake asibitin, alkur'ani yad'auka yayta karatu da mik'ama ALLAH kukansa...............
*_Asma'un ya Umar! ALLAH yasa afito lafiya kihaifama ya Umar d'inmu d'a ko 'ya maikama dashi😥._*
Ameen
_kowa yay shiru na second 1 Dan nuna jimami😂_
*_(((S)))........2017_*
*_Luv u all._*
[1/1, 3:05 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→63-64_*
..........Sai wajen 1:30pm su Dr Al-ameen suka fito, kowa yana yarce gumi. 'Yan uwa sukayi Kansu suna tambayar Asma'u harma da abinda ta Haifa.
Hannu kad'ai Dr Al-ameen ya iya d'aga musu, cikin hanzari yashige office d'insa. Ya Umar dake binsa abaya ya ce, "Dr matatafa?.
Karka damu, muna fatan nasara, amma muna neman jini da gaggawa.
Dr kud'ebi nawa kawai. Ya Umar yay maganar cikeda hanzari.
Wasu Abubuwa Dr Al-ameen ya d'auka suka fice, kai tsaye wajen d'ibar jini suka nufa. Cikin amincin ALLAH jinin yazo d'aya kuwa, d'iba akayi aka tace sannan cikin hanzari Nurse d'in tad'auka ta kaima Dr Al-ameen......
Yamzuma saida suka kwashe kusan minti 40 sannan suka fito. Yanzukam akwai canji dan fuskokinsu a sake suke.
Duk mik'ewa sukayi ayanzunma, tunkafin suce wani Abu Dr Al-ameen ya ce, "Alhmdllh congratulations, ansami baby boy." 'Yay maganar yana matsawa gefe, Nurse d'in dake d'aukeda babyn ta bayyana.'
Gaba d'aya sukayi cahhh akan Nurse d'in, kowa nafad'in Alhmdllh.
tamik'a musu k'aton jaririn Wanda kallo d'aya zaka masa ka gane dolene yabama mamarsa wahala saboda girmansa. 'Yar rige-rigen d'auka akeyi, ALLAH dai yabama mama nasarar amsarsa.
Ya Umar kam wajen Dr Al-ameen yamatsa, Dr matatafa?.
Murmushi Dr Al-ameen yayi masa tareda dafa kafad'arsa kwantar da hankalinka baban baby, madam ma tana lafiya, yanzu haka anashirin maidata d'akin hutune danta huta.
Ajiyar zuciya ya Umar ya sauke, Ahankali yafurta Alhmdllhi Ala kulli halin. Dr zan iya ganinta kuwa?.
Babu damuwa muje narakaka dai ka ganta, inaga hankalinka zaifi kwanciya.
Ya Umar baice komaiba sai murmushin dakan k'awata fuskarsa dayayi.
Atare suka shiga d'akin da akakai Asma'un, su hud'une ad'akin, ya Umar yama sauran sannu sannan yak'arasa gaban gadon da aka kwantar da Asma'u.
d'aure take da bedsheet fari sal, said'an d'igo-d'igon jini dayad'an 6atashi, amma ansaka mata k'aramin hijjabi shima fari, idanunta biyu kuma tana iya magana, Nurse natsaye agefenta tana saka mata jinin da aka d'iba ajikin ya Umar Dan k'ara mata.
Ya Umar yak'arasa gaban gadon, yaja farar kujerar dake gefe ya zauna, hannun Asma'u yakamo yarimtse anasa, my Asmah sannu kinji.
Bata iya amsashiba, saidai idonta na kansa, sai hura hanci takeyi. Yamatso sosai yashafa kanta yana fad'in ALLAH yayi miki albarka kinji. Kad'an tad'aga masa kanta, muryarta can k'asa-k'asa take magana. Bayajinta, Dan haka yamatso da kunnensa kusada bakinta.
Ta ce, ''Yaya k'afata nanan kuwa? dubamini."
Murmushi yamata, yakuma shafa kan nata, k'afarki nanan My Husna. bakijintane?.
Yanzuma saida yamatsar da kunnensa sannan yaji mitake fad'a. ALLAH jinake kamar babu k'afar.
Ya Umar ya kalli Dr Al-ameen dake tsaye yana gyarama Nurse d'in yanda zatayi.
Dr kaji wai jitake kamar k'afarta bata a jikinta. Ko akwai matsalane?.
No, babu wata matsala, allurar da akamatace takawo hakan, zuwa safiya zatajita daidai insha ALLAH.
Ya Umar ya ce, "tokinji."
Nanma kanta tajinjina tanad'an lumshe ido.
Dr Al-ameen ya ce, "mubarta inaga zatayi barcine".
Ok ya Umar yafad'a yana mannama Asma'u kisses agoshi. Sannan suka fice.
Zuwa yanzu kowa yad'auki baby daketa barcinsa, suna zuwa mufida amarya ta mik'ama ya Umar babyn tana fad'in Yaya ga bak'on duniya.
Murmushinsa ya fad'ad'a, yakar6i yaron maicikeda lafiya, kiss uku ya manna masa afuska sannan yarungume abinsa yanajin wani farinciki na ratsa dukkan ga6o6in jikinsa.
Yakai minti kamar 5 ahaka, kowa yanata kallonsa cikeda tausayi, sunsan yanadason yara, amma aka rabashi danasa.
Bakinsa ya manna akunnen yaron yaymasa hud'uba, a la66ansa ya furta ALLAH ya raya *_Usman Fhodeeyo_*.
🤗nikad'ai najishi, Dan haka na ce, " Ameen ya Umar🤓.
Babu Wanda aka bari yashiga gunta har magriba, bayan magribane kuma ya Umar ya ce, "duksu tafi hakanan."
Badan sunsoba suka fara shirin tafiya, Anty Saratu, Anty Sa'a, mufida, Anty Saddiqa, fatee, Rafi'a, hasiya.
Mama kad'ai za'a bari anan, Rafi'a da hasiya ance subi fatee gidan inna, Dan ita batazoba, tama mama kara.
Kowa yaje yaga Asma'u dahar yanzu take barcinta sannan suka tattafi.
9:30pm
Mama ta kalli ya Umar da Harris, muktar, Sadam, yazeed da matarsa dasukazo suma tun bayan magriba, ta ce, "yakamata kutafi hakanan dare yayi, bakamar su yazeed kuda kuka baro yarama.
Yazeed yay murmushi mama aisuna tareda mai aiki babu damuwa.
Eh dukda hakadai yakamata kutafi, ALLAH yasaka da alkairi, yabada ladan zuminci.
Gaba d'aya suka amsa da Ameen.
Muktar yamik'ama mama jaririn daketa barcinsa nannad'e a showal. Sallama sukai mata suka fice, amma dana kalli fuskar ya Umar sainaga bahaka yasoba. Amma babu yanda ya iya, dan maza basa jinyar mata awajen, saidai mace 'Yar uwarka. Shima namiji haka.
Saidasu yazeed suka tafi sanan suma suka shiga mita suka tafi......
Ya Umar duk saiyaji gidan babu dad'i, amma fuskarsa cike take da fara'a na farincikin k'yautar da ALLAH yamasa yau. Aikam kusan kwana yayi yana sallah da mik'a godiyarsa ga sarkin sarakuna.
★★★
Washe gari tundaga sallar asuba ya Umar ya koma gida yay wanka a gaggauce yay shirin tafiya asibitin, kai tsaye asibitin yanufa. Saida yafara zuwa suka gaisa da Dr Al-ameen sanan yatafi d'akin da aka kwantar da Asma'u.
Tana zaune akan gadon, tajingina da filon wata Nurse tana taimaka mata wajen bama babyn nono.
Mama kuma na zaune akan kujera tana shan shayi (su mama babu juriyar yunwa😉lol).
Kamshin turarensa yacika d'akin, Asma'u dabatasan da shigiwarsaba tad'ago kanta. Murmushi yamata Wanda yasakata jin wani sanyi aranta, saima tadainajin zafin shan nonon da yaron keyi.
Rissinawa yayi yagaida mama sannan yakoma yabi sauran gadajen suma yana gaishesu.
Abakin gadon yazauna kusada k'afafun Asma'u, yad'auki yaronsa da'aka kwantar agefe bayan yasha nono yak'oshi. My Husna! Ya jiki?.
Cikin sanyin murya ta ce, "Alhmdllh, ina kwana?."
Lfy lau, kuntashi lfy?.
Kanta ta jinjina batareda tayi maganaba.
Ya Umar yamaida kallonsa kan mama yana fad'in mama babu dai wata matsala ko?.
A'a wlhy, lafiya lau muka kwana, shima yaron yanata barcinsa, yanzuma yatashi babu jimawa yad'an fara kuka, saikuma ga Nurse take kowa? tace yunwa yakeji abashi nono yasha, shinema kasamesu suna bashi.
To Alhmdllh, ALLAH yak'ara lafiya.
Ameen ya rabbi.
Ya Umar yakuma kallon Asma'u data zuba musu ido shida babyn cikeda sha'awa. Maman baby k'afar tadawone?..
Fuskarta tarufe tana fad'in kai ya Fharuk babu wani Maman baby.
Dariya yayi k'asa-k'asa dan yagane tanajin kunyar mamane.
Suna nan zaune Dr Al-ameen yashigo, saida yafara duba sauran marasa lafiyar d'akin, sumadai duk theater's aka musu, sanan yak'araso gadon Asma'u. Kan yaron dake hannun ya Umar yashafa yana fad'in my son katashi lfy a sabuwar duniyarmu?..
Ya Umar yay dariya, gashinan k'alau yanata k'yalla idanu.
Dr Al-ameen yak'arasa kusada Asma'u yana fad'in aii yaran yanzu da wayonsu ake haihuwarsu. Ya gaida mama sanan yayma Asma'u ya jiki?. Ta ce, "da sauk'i, saidai bayanta namata ciwo kad'an-kad'an da kanta.
Sannu yamata sanan yasaka Nurse d'in dake binsa amma bata d'azu baceba, takuma d'aurama Asma'u k'arin ruwa. Mama ta ce, "Ameenu bazataci komaiba ita Ma'un?.
A'a mama sai zuwa yamma za'a bata ruwan Lipton tasha kawai.
To ALLAH yakaimu lafiya.
Daga nan Asma'u takoma barci, dan anaso tahuta saboda kanta datace yana mata ciwo. Mama da ya Umar kam suka cigaba da hirarsu.
Kafin wani lokaci asibitin yacika da dangi, yaukam harda inna da baba da Abba akazo, matar ya Abubakar ma tazo, shima hardashi..........
*_bayan sati d'aya_*
Da safe aka rad'a sunan yaron bayan an idar da sallar asubahi a masallaci. Yaro yaci sunan Usman mahaifinsu ya Umar (ALLAH ya gafarta masa, ameen) amma za'ana kiransa Fhodeeyo. To ALLAH ya albarkaci rayuwar Duk wani jariri ko jinjira ameen.
Har yanzu Asma'u na asibiti ba'a sallamesuba, amma suna sakaran sallama ayau d'innan, Dan Alhmdllh jikinnata yayi k'yau. Batada k'an jiki, kuma kowadai yasan CS d'in yanzu ba'a wani dad'ewa a asibiti musamman idan anhad'u damai jarumta.
Tana zaune akan gadon abinci takeci (Dan yanzun tanacin abinci), yaron kuma yana hannun Anty Sa'a, mama da Anty Saratu da mufida sunata hirarsu.
Ya Umar yashigo shida yazeed da Muktar, saida suka gaida d'ayar matar data rage ad'akin, Dan yanzu su biyune kawai, ansallami sauran biyun.
K'arasowa sukayi, kowa ya ajiye ledar hannunsa sannan suka rissina suna gaida mama. Su Anty sa'a ma suka gaishesu, itama Asma'u haka, suka tambayeta ya jiki?. Ta ce, "Alhmdllh.
Mufida tatashi tajawo musu kujerun dake d'akin suka zauna.
Jaririn aka basu, har anmasa wankansa, yana cikin kayan sanyi masu laushi jajaye. Yazeed daya d'aukeshi ya ce, ''masha ALLAH Fhodeeyo".
Mama tawashe baki Dan farincikin sunan dayaci, ta ce, "lallai Ashe wanan mijin na katakone bana robaba?."
Dariya aka sanya duka, mama tad'ora dafad'in to ALLAH yaraya Usmanu.
Ameen suka amsa.
Muktar ya ce, "mama aidama na k'arfenema koda baici sunanba."
A'a rabanifa muktar, indafa baici sunanba tona robane, amma yanzu kun k'ara masa girma yazama na katako baikai na k'arfenba. Dan nasan bazaiyo jarumtar nawa Usmanun ba.
A'a mama karfa ki fidda rai, nangabafa shine mai kama miki sanda, Cewar mufida.
ALLAH ya tsareni mama tafad'a tana kaima mufida duka.
Kaucewa mufida tayi suna dariya.
Asma'u data d'ago ido saita kama ya Umar na kallonta. Baki ta murgud'a masa daga k'arshe. Ya nuna Kansa wai shi takema murgud'e?.
K'ara murgud'a masa bakin tayi sanan tad'aga kai alamar eh.
Shima Kansa ya jinjina wai aii zasu had'une.
Mufida da Anty Saratu dake kallonsu suka tuntsure da dariya.
Mama ta ce, "kai kukuma lafiyarku kuwa?.
Cikin dariya sukace k'alau mama, wata drama muke kallone.
Kudai kuka Sani mama tafad'a tana maida hankalinta wajen hirarsu yazeed da Anty sa'a.
Da yamma aka sallamesu. Kowa yayi farincikin faruwar haka kuwa, bakamar Asma'u, jitake kamar tayita tsallen murna.
Da mama ta ce, "awuce da ita gidanta, amma ya Umar yayta rok'onta akan a'a shidai sutafi gidansu, har itama mamar saita zauna kodan tasakama gidan albarka.
Da wanan dad'in bakin nasa mama ta ameence aka wuce da Asma'u gidan ya Umar.
Sun Tatar da gidan tsaf, dansu Rafi'a sunje sun gyara, nanfa makwafta sukaita shigowa dubata da jariri.............
*_(((S))).......2017_*
*_I love you all_*
[1/1, 3:05 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→65-66_*
..........Shiru momy tayi tamkarma bataji abinda Lubna tafad'aba.
Lubna tak'ara maimaitawa, Dan atunaninta mom batajitane.
Mom zanyi aure kwanannan nacefa.
Mom ta sauke ajiyarzuwa tareda maida dukkan hankalinta akan Lubna da Suhaima. Baby kinsandai banason shashanci, idan kinsan wanan maganar taki ba gsky baceba karki sake maimaitamin ita anan.
Suhaima da Lubna suka kalli juna suna murmushi, mom ALLAH kuwa da gsk baby takeyi, aure zatayi.
Murmushi mom tasaki awanan karon, Dan tagaji da gantalin da 'ya'yan natakeyi ana gulmarsu a anguwar. Ta ce, "Alhmdllh, aii aure shine mutuncin d'iya mace, naji dad'i sosai, kema Suhaima saiki fiddo da mijin ahad'a gaba d'aya ayi, nikaina mamarku auren zanyi Dan kare mutuncin kaina.
Atare Suhaima da Lubna suka had'a baki wajen fad'in mom aurefa kikace!?.
Mom tayi 'Yar dariya, kai kajimin yara, shin nawuce da aurenne?.
A'a mom, amma yakamata kima dad kara gsky, kik'arasa rayuwarki haka, tunda dai duk abinda kike nema ALLAH yabaki. Shiru tayi batace komaiba, zuwa can kuma tayi ajiyar zuciya, shikenan zan duba naga mai yuwuwa, shima Ameer idan yazo zamuyi maganar dashi. Amma ke baby waye mijin?.
Lubna tayi d'an tsaki, abokin wancan fak'irinne nada, Umar!.
Abokin Umar kuma baby?.
Eh mom, ammafa ada, Dan yanzu ko hanya basa had'awa dashi, Dan babu yanda za'ayi mai Arzeek'i da fak'iri suzauna a inuwa d'aya.
To, amma kina gani babu matsala baby?.
Wlhy babu wata matsala mom, Dan nikam ina sonsa, kuma kodan nak'ara haddasa bak'in ciki arayuwar Umar saina auri Hafiz.
Shike nan, ALLAH ya Sanya alkairi, saiki gaya masa yayi k'ok'ari su Gana da uncle d'inku Abdullahi, Dan banaso aja dogon lokaci, idanma san samune ayi bikin nanda k'arshen wata.
Lubna ta turo baki gaba, kai mom bagwara yaje wajen uncle habeb ba, kinsandai mugun halin uncle Abdullahi nan, 'ya'yansama bawani dad'insa sukejiba, sai ak'idar tsiya, shi adole (Ustaz).
Humm baby kenan, amma idan baki mantaba aii Abdullahi shine babba, yanagaba da mahaifinkima bare habibu. Nidai mom dukda haka uncle habeeb naza6a, yau kwana tarafa kenan Uncle Abdullahi yazo yagama mana cin mutuncin agidannan, kuma hardake, amma shine harkin manta, zaki d'au ragamar 'ya'yanki kibasa.
Baby aiba cin mutunci yamanaba, gsky yafad'a, kumanikam koda bazan d'auka dukaba zan d'auki tayin aure, kema Suhaima kifito danaki ahad'a duka kawai. Daga Suhaima har Lubna baki suka cuno gaba, ciki-ciki Suhaima ta ce, "nima aii Ramadan yace zaituro iyayensa."
Alhmdllh, amma naji dad'i sosai, insha ALLAH zan sanarma su habebun dakaina.
Daga nan taron ya watse, baima Lubna da Suhaima dad'iba....
Washe garin ranar mom dakanta ta shirya taje har gida suka tattauna da uncle Abdullahi. Yanuna jin dad'insa sosai, shima uncle habeb sun sanar masa. Shima sosai ya nuna farin cikinsa, Dan sungaji da zagin da'ake musu agari akan gararin da yaran sukeyi. (Sukuma harga ALLAH ba laifinsu baneba, suna iya bakin k'ok'arinsu). Amma ko kad'an su Lubna basa saurarensu, Dan tun mahaifinsu nada rai bawani ganin girman Uncles d'in nasu sukeyiba, tunda sunsan babansu dukya fisu kud'i. Hasalima alfarmarsa sukeci.
Sun yanke hukunci akan sati mai zuwa zasusa akawo kud'i, amma saisunyi bincike akan yaran tukunna.
Mom tamusu godiya sannan tatafi............
________________________
Suna zaune afalo kasancewar lokacin zafine, ko ina abud'e yake. Mamace takema Asma'u fad'a akan shan kunu dabata sonyi. Itadai Asma'u tayi luk'us Dan tasan batada gsky. sai Hasiya dake dariya k'asa-k'asa, Dan babu lalla6ar dabataima Asma'un ba akan shan kunun d'azu da rana amma tak'i, ai gashinan yanzu yahuce tanasha da tsiya ko.
Harara Asma'u tasakarma Hasiya tana tura baki gaba, mama kinganta ko?.
Nagantafa, cewa mama, amma babu abinda zance da ita tunda kece kika jama kanki. Ku yaran yanzu babu abinda kuka iya sai shan shayi da wainar kwai, yo ALLAH natuba ni nata6a ganin jego haka?. Shidai jegon farko inbaka ingantashiba aibazaka inganta nagababa ko? Kuma kayi wasa ahaka zaka taso sakaka, harma mijin yaringa gudunka, kullum ayita fama akan shan kunu, inbanda lalata bashine zaikawo ruwan nonoba yaro yasha yak'oshi.
Anty Sa'a tafito daga d'akin Asma'u tana dariya, dama tun d'azun suna aciki itada Anty saddiqa da anty Saratu suna saka sababbin punches da ya Umar yasa aka kawo d'azun da safe.
Tun d'azun suna jiyo diramar mama da Asma'u sunata musu dariya acikin d'akin. Yanzuma Anty sa'a tafitone tabama Hasiya kayan Fhodeeyo dazata wanke wad'anda sukad'anyi datti.
Yauwa Hasiya ga kayannan, tashi yamma nayi kok'yayi kigama.
To anty, Hasiya ta amsa tana kar6ar kayan.
Mama ta kalli Anty sa'ar, yo harkun gama jeren?.
A'a mama sauradai kad'an, inagama munkusa tashinku daga falonnan dan munkusa dawowa kansa.
To idan kun kammala ai saimu koma falon Umaru tundashi aii kun gama ko?.
A shikam mungama tun d'azun shida kicin.
Asma'u ta ce, "anty sa'a sannunku."
Yauwa ma'un mama sannu kema, tad'an rissina tana lek'en fuskar Fhodeeyo dake bayan mama. Mama! ALLAH kuwa kamannin fodeyo da Umar sako fitowa sukeyi, yaronnan haske kawai zai nunama Umar.
Mama tayi 'yar dariya, yoni sa'a aii kallon Usmanu nakeyi kamar sanda na haifi Umaru, har d'an banzan kukannan nashi na dare dayake hana mutane barci, haka Umaru ya wahalar dani da kukan dare nida mahaifinku, to d'an kwal uban shima gashinan yayo gado.
Dariya anty sa'a da Asma'u sukayi, Anty sa'a tashafa kan fodeyo, kanata barcinka sai dare yayi kahana mamummu barc.......
Shigowa ya Umar tahanata k'arasa maganar.
Ya rissina yana gaida mama, Asma'u tamasa sannu, suka gaisa da Anty sa'a itama. Yad'ora da fad'in anty sa'a sannunku da aikifa.
Yauwa Umar, ya shagon?.
Alhmdllh wlhy, dama zan tambayekine midami kuke buk'ata na hidimar sunan?.
Ai dukma mun rubuta komai, takardarma na d'akinka.
Okey babu damuwa.
Mama ta ce, "tonifa inaga zuwa gobe zan koma gidan mijina gsky."
Suduka suka kalleta cikin alamun tambaya. Ya Umar daya kasa daurewa ya ce, "haba mama miyasa?."
A'a babu komai Umaru, bazan zauna ananba har ranar suna aii, kumama alhmdllh jikin Asma'u yayi k'yau, inama laifi, yau kwananafa Tara agidanan, ga zaman asibiti damukayi na sati d'aya, aii abin ba hauka baneba.
Ya Umar yay murmushi batareda yace komaiba.
Anty Sa'a ta ce, "shikenan mama, amma kibari sai jibid'in da safe, tundadai sunan sai rana."
A'a insha ALLAHU gobe da daddare zan tafi.
Shiru duk sukayi, Dan sunsan halin kafiyar mama sarai.
Zuwa yamma lis suka gama gyara gidan fes, puneches d'in sunyi k'yau sosai, dukdadai basukai tsadar nada da Lubna takwasheba, amma wad'annanma babu laifi kam. Na d'akin ya Umar kujerune na leda bak'ake, da labuloli green, hakama carpet shima green, sai madaidaiciyar TV plasma dasuka ajiye zuwa gobe za'a nemo mai sakawa. Hakama cikin bedroom d'in komai kamar na falonne. d'akin Asma'u kuwa, lemon green & Orange ne, itama komai tsaf. A babban falo kuwa kujeru jaa da milk d'in labulayene dakuma ratsin jaa kamar kujerun, nanma kowa yagani dolene ya yaba saidai mak'iyi.
Mamace ta ce, "aidabasu saka na babban falon ba, dasun bari taro yatashi sannan, inba hakaba kuma duk za'a 6atasune. Sunyarda da shawarar mama kuwa, Dan haka sukace zuwa gobe da yamma sai a kwashe Dan yau sungaji ainun.
Bayan anyi magriba harris yazo ya maidasu Anty sa'a amotar da har yanzu Asma'u batasan tawayeba, Dan shima ya Umar d'in yakan had'a wata guda bai shigetabama, yafi hawa mashin lifan daya saya bayan bikin Mufida.
Yauma kamar kullum Hasiya taje takaima ya Umar abinci d'akinsa, akan sentar table d'in tsakkiyar falon ta shiya masa yau, sa6anin da datake jerawa akan tabarma. Sosai falon ya birgeta Dan haka takebin ko ina da kallo. Shigowar ya Umar tasakata saurin waigowa, sannu tamasa ya amsa shima yanabin falon da kallo, Hasiya falon yayi k'yaune?.
Wlhy kuwa yaya ya had'u, yamafi na yaya Asma'u kyau.
Dariya ya Umar yayi yana zama, ya ce, " kidai dage tajiki."
Itama dariyar tayi tana dafe bakinta, aikodai yaya bara nayi shiru, Dan yanzu Abu kad'an zakama yaya Asma'u tahau mutum da masifa.
Murmushi kawai yayi, amma baice komaiba yashige bedroom d'insa. Daga ciki ya ce, "rediyo jeki kiramin Husna, kuma tataho da fodeyo."
Fita Hasiya tayi tana zum6ura baki, dama idan tana zabga surutu haka yake cemata redio. Data tuno wani Abu kuma saitayi dariyar mugunta, tasan dawuya mama tabar Asma'u zuwa wajensa musamman yanzu da daddare, ko kad'an bata barinsu su k'e6e sukad'ai. batasan miyasaba itama.🤷🏽♀
Afalo ta iske Asma'u zaune a inda ta barsu, amma yanzu tanama fodeyo shirin barcine. Mama kuma tana kwance a doguwar kujera, harma barci ya d'auketa.
Zama hasiya tayi kusada Asma'u, cikin magana k'asa-k'asa ta ce, ''yaya Asma'u! ya Umar na kiranki, yace kuma kije da fodiyo.
Da sauri Asma'u ta kalli inda mama take, Alama tayima Hasiya data fad'a ahankali. Hasiya tak'unshe baki tana dariya k'asa-k'asa.
Asma'u batace da ita komaiba tak'asa sakama fodeyo famfas, tasaka masa riga mara nauyi saboda yanayin zafin garin, hoda ta shafa masa ta k'uraje, a wuyansa da goshinsa sannan ta nad'eshi a showal ta sa6ashi akafad'a tafice cikin sand'a da waugen mama dabatasan sunayiba.
Hasiya ta guntse baki tana dariyarta.😂
Yana zaune abakin gado, dagashi sai tawul, da'alama yanzu yafito daga wanka. Mai yad'auka yad'an shafa sama-sama saboda zafi. Yana cikin fesa turare Asma'u tashigo da sallma.
Fuskarsa d'aukeda murmushi ya amsa mata. Yamik'e tsaye yana saka gajeren wando. Yayinda Asma'u ta zauna abakin gadon tana kwantar da fodeyo.
Ya Umar yagama saka wandon yadawo bakin gadon shima, Rankwafawa yayi yayma Fodeyo kiss akumatu yana fad'in my son rigima, ya shafa kan yaron daketa barcinsa, yanzu gaka kana barcinka? Sai anjima kahanamu barci ko?.
Asma'u dake kallonsu tayi d'an tsaki, kabari wlhy ya Fharuk, yaronnan yana d'aukar hankalinmu, shi yasha barcinsa da rana, mukuma yahanamu dadaddare.
Ya Umar yazauna akusada ita yana rungumota jikinsa, acikin kunnenta ya ce, "sorry momy zamu daina wata rana aii?."
Baki ta tunzuro gaba, o bama zaka masa fad'aba? Saidai ka goyida bayansa kenan?.
Dariya tabashi sosai, Dan haka yadara, yakuma matseta sosai yana dariyarsa, kai my Husna kinada abin dariya wlhy. Yanzu miye abin fad'a ga Fodeyo Dan ALLAH.
hummm zaka fad'i haka kuwa, tunda bakai yake hanawa barcinba, wani lokacinma saiyayi wajen Rabin kukan kake zuwa.
Hannayensa yasa yaruk'o fuskarta suna kallon juna. lumshe idanunta tayi Dan hango buk'ata kwance a idon mijin nata. Aii tama yabama k'ok'arinsa sosai wannan karon, Dan rabonta dashi tun ana jibi zata haihu. Kusan sati uku kenan......
Jin bakinsa akan nata yasaka tunaninta tsayawa cak waje d'aya.
Hummm su ya Umar fa andad'e ba'a gamuba🤐.
Ganin zai zarce gona da iri yasakata rik'e hannunsa. Shima saiya dakata da zagayen dayakeyi da hannunsa ajikita d'in, Dan yatuna akwai d'inki tareda ita. Wasa yaciga dayi da bakinta harya d'an rage zafi sanan yazube akatifar yana maida numfashi. Ahankali tazame itama ta kwanta gefensa, 'yan dabaru take masa irin namu na mata dakakanyi idan kana al'ada. Luf yayi dan sak'wanninta na isa agareshi.
Saida ta tabbatar yasami nutsuwa sannan tabarsa, gefe takoma tana kallonsa, yayinda shikuma ya duk'unk'une waje d'aya yana sauke numfashi.
Yad'an bata dariya amma tadake dankarta tsokanosa.
Bayan kamar minti 10 yad'ago yana kallonta da rinannun idanunsa, ahankali ya ce, "ngd my Husna, ALLAH yayimiki albarka.
Murmushi tamasa mai kwantar da hankali, tareda wani salon kallo, saikuma tarufe idonta, Dan taji kunya.
Yasauke ajiyar zuciya yana murmushin shima, mik'ewa yayi ya ce, " ina zuwa."
Ganin yanufi hanyar bayi ta ce, ''yaya mukam tafiya zamuyi kafin mama tafarga bama nan."
Juyowa yayi ya kalleta, babu wani mama taga bakwa nan, to tayaya kuka fito yanzu.
Yaya wlhy barcifa takeyi, kuma nasan zata iya tashi tunda bata kwanta gaba d'ayaba.
Dawowa yayi yana dariya, ya d'auki fodiyo ya manna masa kiss, my son kafad'ama kakarka iyayenkafa suna buk'atar jin d'umin juna.
Idanu Asma'u tazaro waje tareda mik'ewa zumbur, yaya wa kake gayama hakan?.
Dabaki yanuna mata fodeyo.
Kanta kawai ta jinjina tana fad'in kaga banishi mutafi, saida safe.
Bai bata fodeyon ba, amma yad'an rage fara'a, towai saurin mikeyine? Koma maganar dana kiraki Dan ita bamuyibafa, jiba agogo ko tara batayiba.
Asma'u ta langa6e kai gefe, kai yaya ka tausaya mini plss, ALLAH inajin kunyar mama ainun.
To naji muje falo muyi maganar saiki tafi.
Babu yanda zatayi dole tabishi falon dantaji maganar dazasuyi d'in...........
*_(((S))).....2018_*
*_I love you so much my fans_*
[1/2, 7:48 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→67-68_*
..........Su Uncle Abdullahi sunyi bincike akan mazajen nasu Suhaima, duk dadai binciken yad'an nuna musu matsaloli.
Dan haka suka kira mom dasu Lubna suka shaida musu. Lubna da suhaima suka bad'ama idonsu toka babu kunya sukace sudai zasu auresu ahaka. Babu yanda su Uncle habeb suka iya dasu Dan aganinsu auren yafi yawon gararin dasukeyi.
Cikin sati d'aya komai ya kammala, antsaida biki sati biyu kacal. Sai alokacin Ameer yaji labari, masifa yaytayi, ya ce, "kuma babu abinda ya shalleshi. Ransa a6ace yatashi yana fad'in mom dama nazo na sanar miki jiddah ta haihu d'azun, amma 'yar batazo bada raiba.
Baki mom ta ta6e ta ce, " ALLAH ya k'yauta gaba."
K'ala baice da itaba yakad'e rigarsa yafice.
Suhaima & Lubna suka raka bayansa da harara suna zagi. Mom bata hanasuba, Dan itama yanzu haushi. ameer d'in takeji ainun, musamman yanda ya janye kansa daga garesu, komai saidai matarsa.........
★★★
Afalon suka yada zango, ya Umar yazauna saman 2sita, ita kuma Asma'u tanufi kujera mai kallonsa zata zauna.
Hannunta ya kamo, tajuyo tana kallonsa, da ido yay mata nuni da gefensa. Itafa harga ALLAH fitinarsa take gudu bawani abuba, amma babu yanda zatayi dole tazauna kamar yanda ya umarceta.
Juyowa yayi yana kallonta sosai, itama saita nutsun, ya sauke ajiyar zuciya yana murmushi.... Kuma yak'i magana.
Ganin haka Asma'u tad'ago ta kalleshi, muryarta a sanyaye ta ce, ''Yaya ina saurarenka.
Kauda kansa yayi daga gareta yana dariya k'asa-k'asa, zuwa can ya ce, "to abani abinci mana."
Batareda ta tanka masaba tasauka k'asa ta shirya masa abincin, Dan tasan yafison cin abinci ak'asa.
Fodeyo ya mik'a mata sannan ya sauka k'asan.
Anutse yakecin abincinsa, lokaci-lokaci yakan d'ago yakalleta yana murmushi. Itakuma ta zun6ura baki gaba tana nuna masa agogo, dan bata k'aunar mama tagane tannan.
Ga ya Umar yanata wani cin abinci a yangance tamkar mace.
Yana kammalawa tafara gyara wajen, kwanukan ta kwashe tafita dasu zata kai kicin sukai karo da mama a babban falo.
Kallon tuhuma tabi Asma'u dashi, itakuma tayi k'asa da kanta tashige kicin, duk kunya ta rufeta.
K'in fitowa tayi, har saida tajiyo mama tashiga d'akin ya Umar sannan. A hanzarce tashige d'akinta. Hasiya tabita da kallo tana fad'in yaya Asma'u lfy kuwa?.
Bata bata amsaba tashige cikin bathroom.
Dariya ta kufcema Hasiya, ahankali ta Ce, "ALLAH yak'ara muku aii."
Har mama tadawo d'akin d'aukeda fodiyo Asma'u takasa fitowa daga bathroom. Itama mamar batabi ta kantaba ta kwantar da yaron ta kwanta.
Saida Asma'u tagaji Dan kanta sannan tafito cikin sand'a tayi shirin barci ta kwanta, dama mama afalo take kwana..........
*_bayan kwana biyu_*
Bayan kwana biyu akasha suna. Anrakwashe an kwalle kuwa, munsha bidiri harda bired'e.
Mama kuwa tunda daddare tagudu, aka maye gurbinta da inna baito k'anwar maman.
Asma'u taji dad'in hakan, Dan Dama tana tsoron ya Umar gsky. Kar ganin babu kowa agida yamata aika-aika, gata da d'inki ajiki🤪.
Zuwa dare taron suna yatashi lafiya, su Asma'u sun samu alkairi sosai, fodiyo yayi goshi.
★★★
Su Lubna ma anata shirin biki na garari, tamkar wata budurwa🤭.
Hakama mom bikin ake shiri sosai, aranar alhamis aka sakasu a lalle, juma'a sukayi kamu, ranar Asabar d'aurin aure.
____★______★______★_____
Ranar juma'a da daddare ya Umar yana gidansa wajen 8pm. Yabarsu Harris a shago Dan harsun dawo sunbar muktar da yazeed a mall, saikuma ma aikata sababbi da aka zuba masu dutyn dare.
Asma'u da Hasiya, inna baito duk suna afalon, ya Umar da inna baito dai hirarsu sukeyi akan rayuwa. Asma'u da Hasiya kam hankalinsu nakan kallon film d'in Kalan dangi, sai dariya suketa zubawa.
Fodeyo na goye abayan Hasiya, tunda aka masa wankan yamma yaketa barcinsa.
Sallama suka jiyo daga k'ofar falon, ya Umar ya amsa tareda bada Umarnin shigowa, Dan yaji muryar Sadam Ce.
Sadam yashigo ya gaida inna baito, ya gaida ya Umar da Asma'u.
Hasiya ta gaidashi.
Wata farar ✉ ya mik'ama ya Umar, Yaya gashi wanine yakawo yamzu wai abaka.
Ya Umar yakar6i yana jujjuyawa cikeda mamaki, shikam wazai kawo masa letter yanzu?.
Sadam yaymusu sallama yakoma shago.
Ya Umar ya ajiye takarda yacigaba da hirarsa da inna baito. Saidai k'asan zuciyarsa nata zungurarsa akan ya duba. Warwarewa yayi yabud'e saiga IV ya fad'o, yazaroshi yafara dubawa.
Murmushin takaici yad'anyi Dan ganin sunan Luban da Hafiz ajiki, wai harma gobe d'aurin aure su.
Acan k'asan zuciyarsa kam abin ya k'ona masa ransa. Amma yadake, Dan bayaso su Asma'u su fahimci komai.
Tundaga nanma saiyaji hirar ta gunduresa. Sallama yayma inna baito yashige d'akinsa.
Asma'u kam tuni ta karanto damuwa afuskar mijin nata, tunda aka kawo masa takardar dama hankalinta na kansa, so take tabishi dantaji matsalarsa, amma kunyar inna baito ta hanata.
Inna baito babu ruwanta, bakamar mamaba, bakomai take saka musu idoba. Saidai idan taga rawar kan Asma'u tayi yawa saita taka mata birki, ta hanyar tuna mata takula da kantafa. Wannan yakansa Asma'u kama kanta.
Ya Umar kam yana d'akinsa cikin damuwa, da bak'in cikin abinda Lubna da Hafiz sukai masa. gawani k'arin bak'in ciki Asma'u bata shigo d'akinba har yanzun. Yaja wani dogon tsaki, tareda kai dubansa akan agogon dake manne a bangon d'akin.
Wayarsa ya d'auka yafara Neman layin yazeed. Saidai harta yanke ba'a d'agaba, tsaki yakumayi Dan yasan shegen saurin barcin yazeed, duk inda 9 tayi saika sameshi a gado nad'e......
Wringing d'in wayar tasane takatseshi daga dogon tunanin, ganin yazeed ne ya d'auka da hanzarinsa. Kai kasa halan kanacan kana barci?.
Dariya yazeed yayi, cikin sigar zolaya ya ce, "malam wanefa barci, inadai shan sharafin soyayyane."
d'an iska naji, ya Umar yafad'a cikin 'yar dariya.
Shima yazeed dariyar yayi, o namantafa Ashe kai yamzu gwaurone, karna tada maka da hankali.......
K'atseshi ya Umar yay saurin yi, malam saurareni ba wannan bane agabanani.
Cikin dariya yazeed ya ce, "to miye agabanka Alhaji?.
Ya Umar yashiga zayyanema yazeed zancen iv da aka aiko masa. Wata dariya yazeed ya k'yalk'yale da ita, saida yayi mai isarsa sannan ya ce, "haba abokina, kaifa jarumine, yanzu wannan d'an abinne yatayar maka da hankali? Miye Hafiz balle Lubna?. Kaida ALLAH ya azurta da samun nitsatstsiyar mata kyakykyawa, gashi har ALLAH ya baku k'yautar fodiyo. Ai kamata yayi wannan sak'on yabaka dariya ba 6acin raiba.
Nidai nasan waye Hafiz, kuma tabbas dawata manufa yakeson auren Lubna, humm itama bazan tayata jajeba Dan ta had'u da daidai itane.
Ajiyar zuciya ya Umar yasauke, murya a sanyaye ya ce, "ngd yazeed na fahimta."
Yauwa abokina, yanzu abinda nakeso dakai, ka shirya cikin wanka iyaka wanka mu halarci d'aurin auren gobe, kasanarma muktar shima.
Sannanfa lokaci yayi dazaka fito kanunama kowa kaima kaine. Dan duk wani 6oye-6oye yakamata yak'are hakanan.
Gsky ne yazeed, nima nayi wannan tunan.
Hira suka cigaba dayi, yazeed ya kwantar masa da hankali, ahaka har suka koma hirar kasuwancinsu kuma....
Sai wajen 11 ya ajiye wayar, bayan yakira Muktar shima ya sanar masa. (Dan yanzu sun k'ulle tamau su ukunnan, komai nasu tare yake). Harya kammala wayar Asma'u bata lek'oba.
Itakam alokacinma tuni tayi barcinta.
Abin yabashi haushi, yay shirin barci ya kwanta.....
★.....★......★.......★.......★
Washe gari wajen k'arfe sha biyu ya Umar yashigo gidan, daga shago yake.
Asma'u da Hasiya ne kawai a tsakar gidan, Hasiya tanadaga kicin tana girki, Asma'u kuma tana zaune akujera 'yar tsigunno tana d'auraye kayan fodiyo.
Hirar Fatee sukeyi suna dariya ya Umar yashigo gidan. Asma'u tamasa sannu, amma saiya d'auke kansa yashige.
Ta cije le6enta na k'asan, Dan ita batasan laifin dataima ya Umar ba, tunda safe yaketa wani ciccije mata, lafiya lau yake magana da kowa agidan amma banda ita.
Cigaba tayi da wankinta batareda tabi takansaba.
Wani haushine yakuma turnik'e ya Umar, haryayi wanka yafito Asma'u bata shigoba.
Inna baito ce talek'o daga windown falo takira Asma'u.
Asma'u ta amsa tana mik'ewa, hannunta ta d'auraye aruwa mai k'yau sannan taje.
Inna baito ta mata dak'uwa, kinci gidanku Asma'u, yanzunan mijinki yashigo amma bazakizo kiji matsalarsaba.
Baki Asma'u ta d'an turo gaba, amma batace komaiba. Inna baito ta nuna mata hanyar d'akin ya Umar tana mata fad'a, kudai yaran yanzu saiku haihu goma amma babu hankali ajikinku?, badole kusa mazanku 'yan kalle-kalleba awaje. Yo ALLAH natuba aii yanzu ake gidadanci agidan aure ba daba.
Itadai Asma'u tanajiyo mitar inna baito amma tashige d'akin ya Umar.
Abakin gado ta iskeshi yana shafa mai.
Ko motsi baiyiba barema yad'ago ya kalleta. Tana nan tsaye harya gama shafa mansa, shiri yafara cikin wata dakakkiyar milk d'in shadda wadda tasha Brown d'in sirfani, sabuwa dal, yad'akko sabon takalmi sau ciki Brown ya saka, hularsa zanna Bukar itama Brown da ratsin milk ya kwama, bak'aramin k'yau na d'aukar hankali ya Umar yayiba, yana cikin fesa turare Asma'u tamatso kusadashi, ta madubi ya hangota, Dan haka yakuma tsare gida.
Matsawa tayi kusadashi ta amshi turaren zata fesa masa, amma saiya kauce, idonta cikeda da kwallah tarik'o hannunsa, yafara k'ok'arin kwacewa tasaki kuka. Tsayawa yayi cak amma bai juyoba, cikin muryar kuka ta ce, "haba ya Fharuk! Laifinmi namaka haka da zafi? Dahar na cancanci irin wannan hukuncin daga gareka?.
Ni bakimin laifin komaiba, yafad'a yana k'ok'arin zame hannunta daga nasa. Kuma rik'ewa tayi sosai tana kuma k'ara sautin kukanta.
Bayason jin kuka ta ko kad'an, amma dolene ya nuna mata kuskurenta kodan gaba ta gyara.
Kuma k'ok'arin zame hannun nasa yayi, tayi saurin k'ank'amesa ta baya. Ya cije le6ensa sannan yajuyo da ita gabansa, cikin tsare gidan nasa ya ce, "keda laifin, amma kinfi kowa raki?." Kinga kibarni natafi, su muktar na jirana ak'ofar gida.
Nidai saika fad'amin laifina.
Hummm tom kibari idan nadawo saimuyi maganar, yanzu d'aurin aure zamuje kuma bani kad'ai baneba, gashima sai cud'emin kaya kikeyi ni.
Kuma narkewa tayi ajikinsa tana raira kukan.
Yasan halin kafiyar Asma'u sarai, rungumeta yayi cikin sigar lallashi ya ce, "tom kiyi hak'u idan nadawo zan fad'a miki laifinki, kuma nayimiki hukumci, yanzudai kimin uzuri na tafi kimji my Queen. Yay maganar yana d'ago fuskarta, Sumba mai k'yau yabata akumatu da goshinta. Dak'yar tayarda tabarsa yatafi.
Afalo sukayi sallama da inna baito, yafice sai zabga k'amshi yakeyi abinsa.
Sun halarci taron d'aurin auren, Wanda mutane da dama suka halarta. Amma wannan karon akwai banbanci, babu manyan mutane kamar lokacin aurenta da ya Umar, dakuma na Ameer. (Kunsan yanzu rayuwar wani abumma na ganin ido akeyi, dak'asa tarufe idonka wani ya shafeka a babin sabgoginsa kenan). To su Lubna dai sunga dahir, Dan duk manyan k'asarnan abokan mahaifinsu awannan karon babusu kwata-kwata.
Ahaka aka shaida auren Lubna & Hafiz, Suhaima & Ramadan.
To ALLAH yabada zaman lafiya.
Lokacin da aka kammala d'aurin auren, ya Umar, Yazeed, muktar, suka doshi gungun na abokansu, wato Hafiz, salman, Dr jafar, alkasim, Kabeer, Tasi'u dadai sauransu, suna tsaitsaye sunsha anko cikin faraen shaddoji, su adole abokai masu had'inkai da k'ud'i...............
Nikam bilynku nace hummmm. 🤫shiiiiiiiiii!!!!!!!.