Amana duk baccin nan da takeyi a kasa ta kwanta,jiya da ta hau bed jikinta damunta yayi saura kadan ta makara a sallar asuba,shi yasa ta sauka kasa,sabo da Aabid ta kwanta a kan bed,
12:30 pm Amana ta farka,sallah kawai tayi ta fada kitchen ta shirya lafiyayyen abinci sannan tayi wanka ta shirya cikin uniform dinta,sai kamshi take zubawa saboda uniform kala biyar Alim ke bawa ma'aikatansa kuma duk shekara sai an sake musu new,a hankali Amana take tafiya saboda skert dinta bata iya tafiya da shi ba mantawa tayi ta taka kayam kayam da sauri,shi yasa a kullum sai ta fadi wajen sau biyu ko uku,
Wucewa tayi wajen driver zuwa dauko Aabid saboda 1:30pm ake tashinsu,Amana yan gayu har takama takeyi tana kamewa a bayan mota,
Tana zuwa schl din har an tashi Aabid da gudu ya shigo motar yana rungume Amana,schl bag dinsa ta karba suka karaso gida,
A palon sama suka iske Alim zaune cikin 3qtr brown da Riga coffee color,sai kamshi yakeyi part din dama yan aiki sun gyarashi neat ko ina kyalli yakeyi, Suna shigowa suka rafkawa Alim sallama tare da cewa Daddy mun dawo cewar Amana kaji shishigi wajen Amana,
Daya room din opposite Na Alim ta kai Aabid ta cire masa uniform tare da jefa kayan a washing machine,ta hau yiwa Aabid wanka,a towel ta nadoshi ta fito dashi Palo yana bayanta ta zaunar dashi a kujera,komawa tayi ta shanya kayan da ta cire masa,sannan ta fito da sauri tana ta fiyarta zata dakkowa Aabid kaya ji kake timmm skert ya harde ta fadi,wannan karan sai da taji ciwo a kafarta,Alim ko a bai ce ba Aabid ne kadai yayi mata sannu,
Abinci ta dauko musu suka ci abinsu a Palo,Alim sai satar kallonsu yakeyi yanda suke wasa da cokula,
Bayan ta shirya Aabid cikin uniform din islamiyya nan kuwa ba nisa a kusa da gidan Alim Islamiyyar take,a kafa ta kai Aabid ta dawo ta gyara wajen da suka bata kana ta wuce room dinta.
Mum Alim zaune a bakin makeken bed dinta da Alama nazari takeyi a ranta tana ta tunanin yanda zata bullowa Abban Alim domin so takeyi tayiwa Alim aure tana jin tsoron karfa Alim ya hadu da wacce yake so,
Bari zanje gidan Alim da kaina next Wk zamuyi magana dashi dole ya karbi zabina haka ta gama sake sakenta sannan ta fita kitchen wajen masu girki tana zunduma musu ashar basu gama girki a kan lokaci ba,
Gidan baki kuwa yana nan inda yake sai abinda ya karu domin lalacewar tayi yawa,yayyen Amana mata guda biyu an sako su daga gidan miji suna nan an hadu ana sheka tsiya,Baba kuwa wato sulemanu Harka ya shagala wajen wata bakuwar bazawara da ta zo wajen matarsa wato umma Babar Amana kenan sun bude harka a boye suke fasikancinsu a gidan liman abokinsa,wani dakinsa da yake harkar bokanci anan suke kwashewa tare da wannan bazawara me suna Salamatu, har yau matan gidan basu gano ba,har Babar Amana bata sani ba sabo da Salamatu ta kware wajen rike sirri,bata wasa da sirri.
5pm Aabid ya dawo daga islamiyya, 8pm Amana ta dauko abincin Aabid ta zo sama part din Alim,Aabid yana can yana wasansa Alim yana cike wasu takaddu Amana tayi sallama ta shigo dauke da tire,ta kalli Alim Wanda ya ke cikin jallabiya fitted fara tas sai sheki yakeyi,yayi kyau matuka kamar aljani cewar Amana,sai kuma tace barka master asha aiki Lfy master,
Ko kallonta Alim baiyi ba yana jinta,TV Amana ta kalla taga ana nuna wasan Barcelona da Chelsea, da sauri ta ajiye abincin gefe,wata uwar sufa tayi a kasan center carpet kamar zata fada cikin TV din,ta tsura ido tana kallo,
Can Messi ya fara yanke yan wasan Chelsea Ya wuce zai kaita raga Amana da karfi ta fara uhum....uhummm...yawwa....yanke shege....sai Messi.....a....goal.......sai tafi ta fara raf raf tana murna kamar an mata bushara da gidan Aljanna,Alim dake aiki cak ya tsaya yana kallon abinda Amana takeyi,
Can kuma Iniester ya dakko ball Amana tace ehem..good idea mikawa Suares mana ai kuwa Iniester kamar yaji ya mikawa Suares,
Amana ta fara ihu cikin siririyar muryarta tana tafi Suares ya buga sai ta daki pose ta dawo ai Amana tace Oh.....God..tayi kararrawa...shege yayi kararrawa, dakiki Suares ya zakayimana haka dabba shashasha dolo,common ka buga ta ka wani makata sama,
Ana ta ball tayi zafi Chelsea suka farke 1-1 Amana tayi lakwas tana zage zage,Alim kuwa tsayawa yayi yana kallon abinda Amana takeyi kamar tv, ana ball fa can wani lokaci Suares yaci daya,minti kadan messi ya karawa Chelsea,sai ga Amana ta mike tsaye tana ta tafi da tsallen murna,kuma gashi an tashi 3-1 Barcelona sun cinye Chelsea.
Juyowa tayi taga Alim ya kafe ta da ido a tunaninta shima ball din yake kallo shi kuwa Alim tunaninsa anya Amana kalau take kuwa.
Abinci ta jawo tare da cewa Aabid my Boy zo maza muci abincinmu sai wasa kakeyi kana gani munci ball ko murna baza ka taya ni ba,shi dai Aabid dariyarsa yayi ya zauna,
Abincin ta bude wata hadaddiyarr jallop din taliya da doya tasha kifi,ga wani lemon dabino da kwakwa da ta hada me sanyi da dadi,ga wani flask dan karami ta hada coffee lafiyayye,wani plate kuma kankana ce da yawa ta yanka da pork ciki,gefe guda kuma wani farfesun kazane sai kamshin dadi,
Kallon Aabid tayi tace boy da wanne zamu fara?Alim tun a ido yasan girkin zaiyi dadi da ace zasu bashi to da ba shakka zai ci,amma yaga Amana kwatakwata bata iya tayi ba a rayuwarta,idan zata ci mene a gaban mutum baza tace gashi ba,kuji Alim din nan da kwadayi,to Amana a gidansu basawa juna tayi haka suka taso,
Yau kamar Amana tasan Alim me yake sakawa a ransa,taga yanda yake kallonsu,kawai sai tace uhm mutum da yake siyo kayan abinci a cinye a dinga hanashi,ban taba yi masa tayi ba,yau dai bari Na gwada ko zaici,
A plate ta zuba girki ruwa ruwa malam yana tiriri da kamshi ta je har gabansa ta ajiye masa gashi ko zaka iya ci,dawowa tayi ta zauna,a ransa yace to iya taliyar zata bani jibi fa abubuwa,bai gama tunani ba yaganta taje kasa ta dawo dauke da wani glass jug da karamin glass cup,lemon kwakwa ne ciki ta ajiye masa,ta ebo farfesu nan ma ta ajiye,kankana ma ta zuba masa tasa ta ajiye masa,sannan suka cin nasu da Aabid,kafin kace me Amana da Aabid sun cinye girkin su tas komai coffee kawai basu sha ba,
Alim yana gani yagansu sun fara exercise suna motsa jiki sai tsalle sukeyi,suna faman sheka dariya kamar tababbu,can Aabid ya kwanta yayi flat Amana ta danne masa kafafu yana tasowa a hankali yana komawa,sosai sukeyin gym dinsu,shi Alim mamaki yakeyi har yaushe Aabid dinsa ya koyi irin abubuwan nan?lallai in hakane yarinyar nan ta cika shedaniya,su kuwa kala kala suke gym dinsu idan ta kwanta tayi Sai ayiwa Aabid ma,wurin 30mnt sunayi sannan suka gama,bayan sun huta suka fara shan coffee dinsu,
Alim kuwa sai abincin Amana yakeci yana lumshe ido bai taba cin abinci me dadin Na Amana ba a duniya,saida ya cinye komai ya shanye komai,
Aikinsa yaci gaba da yi sai da ya kwashe 1hr lokacin Amana harta kwashe komai ta gyara wajen,coffee ta hado masa shima a cup ta ajiye masa sannan ta fara koyawa Aabid assignment suna gamawa suka tafi dakinsu tare da cewa Alim Good night Daddy Amana ita a dole Aabid take koyawa tarbiya.
Satin Amana Biyu da fara aiki a gidan Alim yanzu sun shaku da Aabid sosai,shi kanshi Alim ya saba da hayaniyarsu a part dinsa,dama Alim indai ya dauki me kula da Aabid yafi so su dinga yawan zama a part dinsa ta yanda zai dinga ganin meke faruwa da dan nasa,shi yasa baya hana me kula da Aabid zama a part dinsa,ganin yanda yan aikin Alim ma Kansu yan gayu ne yasa Amana ta kara wayewa,amma harkar jagaliyancinta yana nan,bata ragawa kowa sai Alim,uniform dinma sai taga dama take sawa,kayanta take sawa,bata mutunci da matan masu aiki,amma duk ma'aikatan Alim maza natane mutunci sukeyi sosai,tafi yin muamula dasu,mata kuwa tsakaninta dasu sai harara,har girki take shiryawa me dadi ta rabawa mazan,watarana har kaji take soya wa ta basu kowanne me yawa,
Shi yasa idan ka dauke Alim to Amana ce ta biyu da suke girmamawa,
Amana kuma duk kula mazanta ko yatsa bata bari ko da wasa wani ya ce zai rike mata,ita duk harkar iakancin nan bata sanshi ba,ba ruwanta da shi,dan yanzu ko american film da finanan soyayya bata kaunarsu,tafi son film din yaki ko Na sojoji,tafi so taga film din tashin hankali,bata son taga film ana zaman lafiya,tafiso taga Wanda ake kashe kashe ana harbe harbe ana Sara suka,ana harba bum.to fa ka gama birge Amana
Yau Aabid tazo dauka a bangaren Alim sai taga ana film din yaki american film wani Na sojoji me taron mutane,kawai wuta ake ba daga kafa,
Kawai sai ta samu waje ta zauna,Alim kuwa da Aabid suna bedroom har 11pm tayi har Aabid yayi bacci a wajen Alim ba Susan Amana tana Palo tana kallon ba,11-30pm aka gama film din akasa 2 dinsa,duk Amana tana zaune a wajen,har bacci ya saceta ta bingire a wajen,ta wani baje skeet din uniform din nata ya tartare ya dawo Rabin cinyarta Allah yasa tana da wando tight gajere shima Rabin cinya amma da ansha kallo,
Alim yaji karar tv ya fito zai kashe sai yaga Amana ta baje a kasa tana ta bacci skert ya kara tattarewa ya kusa komawa kugu,dankwali ya kwance gashi yayi yalala a kasa,juyi ta karayi tana Sosa cinyarta tare da sa hannu ta zuge zip din skert dinta ta zareshi ta jefar,Alim ya saki baki yana kallon inda zallar baiwar kyau da kyan sura yake,cikin jikinta har yafi fuskarta fari ma kal dashi luwai luwai ko gashin jiki bata dasu,
Can ta kara juyowa ta zuge zip din rigarta ta jefar da ita daga ita sai vest da tight dinta,tana ta baccinta,Alim duk ya diririce,maimakon ya kashe tv sai ya kashe ac ya juya dakinsa kamar munafuki ya kwanta yayi lakwas yana ta nazari,tare da tunanin surar Amana,
Da kyar ya samu yayi bacci,Amana kuwa bata farka ba sai da asuba,ganin inda take yasa ta kwashe kayanta ta arce da gudu dakinta tare da banko kofa tana mamakin yaushe ta cire kayanta,
Sallah tayi ta koma baccinta kasancewar yau Saturday ba kai Aabid schl,ba ita ta farka ba sai 11am,da sauri ta fada kitchen ta hadu da Saude ,Saude tace aikin banza dama zuwa nayi Na fada miki Alhaji ya canja min wajen aiki ya mai dani bangaren gyaran swimming pool yace daga yau ke zaki dinga yi masa abinci,munafuka abinda kike so dama kenan,an manne masa ana tsafi mayya.
Tana gama fadi ta sheka da gudu ta bar kitchen din domin tasan Amana ba mutunci gareta ba,ita Saude dadi taji yanzu ta huta da girke girke,
Amana kuwa ko ajikinta tana hada breakfast ta hada harda Alim,sannan tayi wanka,tasa uniform dinta yasha guga sai kamshi takeyi,har part din ta shirya abinci wannan lokacin sabo da Alim ta shirya masu a dining table.
Tunawa tayi da Aabid ko wanka ba tayi masa ba.dakin Alim ta kwankwasa shuru,kofar ta tura a hankali ta shiga ciki,ba kowa a room din karar ruwa taji alama wanka akeyi,kallonta ta mayar kofar toilet a bude taga kofar tare da hango Alim daure da towel iya kugu yana yiwa Aabid wanka,
Gyaran murya tayi daga can nesa tace Daddyn Aabid zanyiwa Aabid wanka,da sauri Alim ya juyo tare da zubawa Amana ido ba tare da yayi magana ba ya yafitota da hannu wai tazo,ai kuwa da sauri ta shiga kamar bazai yi magana ba sai kuma yace gashi nan Na gama masa wankan kiyi sauran aikinki,kallon Aabid tayi taga kunnensa duk kumfa,dariya ta kyalkyale dashi tare da cewa sorry Baabaaa haka akeyin wankan?kai haka kayiwa kanka,pls ka dinga karfafa jikinka kana koyon abin duniya
Komai ka wani langwabe baka iya ba,harara Alim ya watsa mata tare da ficewa daga toilet din,
Yaga alama yarinyar zata rainashi,bayan ta Shirya Aabid dinning suka fito Alim yaja sit ya zauna,Aabid ma haka serving dinsu tayi komai sannan ta kwashi nata ta koma wajen tv kasa ta zauna tare da kamo sport Chanel tana kallon wrestling.
Alim kuwa ya mai da kai sai shan kunun gyada yakeyi,ga wasu girki da ta hada wajen kala 4 bai ma San sunansu ba, dadi kawai yake kwasa,
5pm Amana ta dau wanka cikin kalar kayanta masu kama da Na wizzy ta fito,da yake Amana me kyauce shigar kyau take mata,a palon kasa ta hanyar kitchen wajen sweeming pool ta iske Alim yana hutawa,yana karanta news paper ga lemo yana korawa,
Tana zuwa tace Daddyn my boy?shuru ba amsa,Master kana yawa a kasar nan,key din mota za a bani pls muje yawo da My Boy,Alim sai yanzu ya tuna Amana ta iya tuka mota,ba tare da yayi magana ba ya cilla mata key abin mamaki yaga ta cafe kamar namiji,tace nagode saura ka bamu kudi,ice cream zamu sha da my Boy,
Baice kala ba ya ebo kudu a aljihu bai San adadinsu ba ya mika mata,tace sai master Allah dai ya saka, tayi waje abinta ta dauki Aabid sannan ta dauki motar da ya bata key wata arniyar mota,ta bata wuta tare da fisgar motar irin Na yan tasha ta kotseta tayi gaba,yan aikin gidan sai kallonta sukeyi da mamaki,matan kuwa kamar su kashe Kansu da alama Amana ta samu fada har motar oga ta fara hawa.
Godiya me tarin yawa gareku fans dina.
AsmaBaffa
[6/27, 9:25 PM] +234 808 968 1079: ✳CIRANIN AMANA✳
50-55
By
AsmaBaffa
Wurin wani hadadden park Amana ta kai Aabid wuraren wasan yara,sosai Aabid yaji dadi sai murna yakeyi tare da zubawa Anty Amana surutu, hadadden resturant ta kaisu sukayi ciye ciyensu,ko ina Amana ta gifta sai an kalli motar,
Ga wani hadadden tuki da takeyi,shopping mall ta shiga Aabid ta kwasarwa kayan zaki,da wasu kayan sport,schl bag new design,dasu canvas da tarkacen dai makaranta,wasu panties Na maza 3qtrs da riguna duk ta siyawa Aabid, Wasu singlet ta gani na maza latest masu tsadar gaske da boxers,Kudin ta ebo dungurugun ta siyawa Alim boxers guda biyar singlet biyar,ita kuwa kayan make up ta siya da turaruka masu saukin kudi,
Sai takalmi guda biyu da ta siya,da wasu sabuwar pcap guda biyu, ice cream ta jidar musu sannan ta je can wurin da Alim ke siyo nama,wato wajen manager inda ta taba yin aiki,sai mamaki sukeyi yanda suka ga Amana ta kara gogewa ta kara haske da kiba,ga wata shegiyar mota da tazo da ita,sun zata Amana ce tayi kudi,nama ta siya ta wuce gida,8pm suka shigo gidan,ko kayan basu ebo ba ta ja Aabid room dinta sallah sukayi da wanka suka canja kaya marasa nauyi,sannan ta riko hannun Aabid suka kwaso kayan gaba daya har part din Alim,lokacin 8:30pm suka sami Alim a Palo yana zaman jiransu da tunanin ina suka tafi haka tun 5pm,
Ganinsu yayi da kaya niki Niki,a gabansa suka ajiye komai,a hankali yace dama kun Dade da dawowa?Aabid yace Daddy wanka mukayi da sallah,
Kayan Amana ta fara budewa ta nunawa Alim kayan Aabid gaskiya shi kanshi sun birgeshi ta iya zaben kaya,jawo wata ledar tayi ta nuna masa nata,sai yayi mamaki nata ko kayan make up din ma ba masu tsada bane,ba wani abu special da ta siyawa kanta,daya ledar kuwa mika wa Alim tayi Master kalli naka,Alim yaso gwasaleta amma yayi tunanin hakan ba dadi ayi ma abin kirki kaki yabawa,karba yayi ya duba,komai size dinsa kuma ta siyi masu tsada,
Gasu best Color nasa komai white,
Thnx ya furta a hankali,ledarta ya kalla yace amma wannan shirme kika kwasowa kanki kika dawo,next time ki kiyaye in ba haka ba baza ki kara zuwa ba,ok master cewar Amana.
Alim yace aransa jibeta kamar ta kirki yanzu kaji ana dambe da ita,kayan zakinsu ta diba tace Aabid baka shan wannan yau sai watarana watarana,idan ana shan zaki hakora mutuwa sukeyi su fara ciwo,mata iyaye a kiyaye za kuga yanzu yaro zaije schl sai a sa masa lemon kwali da biscuit a jaka kayan break,ba kudi bane,ba birgewa bace,ba kuma gata da tarbiya bace,saboda illa zai masa hakoransa su mutu da wuri,ko ya fara ciwon hakori tun yana yaro,gwara ki bashi ashirin ya siyi aya,ko taura,tsamiyar biri etc yanda akeyi da,ko ki dafa musu abinci me kyau yafi wannan kayan zakin.a kiyaye pls.
Kwashe kayan tayi ta boye icecream biyu da nama da drinks kawai ta bari,kitchen ta koma ta dauko su plate etc ta bude ta ebi nata Dana Aabid ta zubawa Alim shima
Alim a ransa yace to yau abincinmu kenan,ci yayi sosai yana kora drink yasha icecream kadan ya mika musu abinsu yana kallonsu suna ta cin nasu suma.
News Alim ke ta kalla Amana ta matsu a canja tashar ball amma shuru gajiya tayi tacewa Aabid tashi muje muyi baccinmu,ko kallonsu Alim baiyi ba har suka sauka suka bacewa ganinsa,
Washe gari Sunday da 9pm Alim ya kira Amana ya mika mata schl Uniform irin Na makarantar su Aabid green and white,ba hijab sai hula da mata ke sawa,Riga da skert,skert din irin da kadan ya wuce gwiwa abinka da lagos,
Kayan har kala biyar,sandal dasu canvas,schl bags,littafai komai ya mika mata,yace kuma Ss1 suka baki ba ss2 ba,
Murna wajen Amana ba a magana hakan ma Na gode master,Allah ya biya bukatunka ya kara buda maka,
Gobe sai kiyi shiri idan kinje office din pc zakije,wani card ya mika mata yace ki bashi wannan cewar Alim,karba Amana tayi tana ta murna.
Washe gari kuwa da sassafe ta shirya ta shirya Aabid cikin uniform ba karamin kyau Amana tayi ba, already ta hada breakfast,cin nasu sukayi suka barwa Alim nasa, brush suka karayi suka gyara sannan suka je wajen Alim dake zaune a palonsa,
Gaisar dashi sukayi sai kallon Amana yakeyi yanda ta hade a uniform,key din mota ya mika mata gashi kin iya driving ai no need driver ya tukaku,ki kiyaye ban son ayi tukin ganganci da Aabid dina.
Murmushi kawai Amana tayi ta rike hannun Aabid suka fito compound,ba motar jiya da ta tuka bace,wata motarce har tafi ta jiya kyau da tsada,
Ma'aikata kamar idonsu zai fado ganin Amana a uniform wato matsayinta har oga ya sata a schl,kuma a schl dinma me tsadar gaske irin ta dansa,ga motoci ko wacce hawa takeyi,mazan gaba daya murna suke taya Amana,matan kuwa bakin ciki kamar su kasheta haka sukaji,
Amana tana kallonsu suna shiga motar tayi wani tuki Na yan tasha ta fice daga gidan,Alim yana kallonta ta window,bai San sanda ya saki murmushi ba,tare da furta yarinyar nan bata ji ko Kadan
Tunda Amana ta cinna hancin motar schl ake ta faman kallonsu,an zata yar gidan wani shegen me kudice tazo da kaninta,kowa driver ke kawo su amma Amana ita ke tukin gasu daga Amana har Aabid masu kyau ne,kalar naira da Hutu,saida takai Aabid har class sannan ta wuce office din PC ta bashi card, ya kaita har ss1A tafiyar da Amana takeyi cike da gadara da takama tana cin magani an dauka Naira ce ta hudata,basu San Amana tun tana kauye haka take ba.
Kafin kace me duk mazan Ajin sun saba da Amana,matan kuwa ko kallonsu bata yi,break aka kada anje restaurant Na schl cin abinci,Amana duk yan aji maza da mata sai da ta raba musu maltina kowa daya daya,nan da nan schl ta dauka wata yar gidan wani kusace Amana
Har class din su Aabid taje ta daukoshi ta bashi abinci da kanta Amana tana mugun kaunar Aabid bata son abinda zai bata masa rai,Aabid kuwa yanzu ya daina tsokana da ciwa mutane mutunci ya nutsu sosai,gashi Aabid yafi ma Alim haske ka rantse baturene,shi yasa yake da farin jini.
Amana har malamai take kaiwa drinks kyauta,kwananta 3 da fara schl amma har ta zama popular, kuma ba laifi tana da kokarinta,amma Amana tafi iya mathts duk wani abu Na calculation to Amana ta sanshi ta iya gifted ce,
Matan schl din tsinewa Amana sukeyi bata da mutunci bata kula kowa sai maza,guda dayace yar ajin su Amana wata Rufaida ita kadai ce suke magana da Amana sabo da Rufaida tana son Amana haka kawai,shi yasa ta nacewa Amana tun bata kulata har ta fara kulata.
Shi kanshi Alim dadi yakeji yanda yaga Amana Na kula da Aabid,ga Aabid sai kiba yakeyi yanzu kuma yayi hankali sosai.dan haka Amana ta kara daraja da kima a idonsa,Amana kuwa a schl kullum sai anyi fada da ita a schl,gashi ba a daukan mataki a kanta sabo da ta siye kowa da kyaututtukanta.
Kamar kullum Amana ta fito da mota ita da Aabid zasu je schl ta ware mota tana fella gudu,wata rantsantsiyar mota ta gani ta parker wata kyakyawar dattijuwa ajin farko ta fito daga bayan motar tana yanga da takama tazo zata tsallaka titi tana ganin mota amma sabo da takama irin ta wannan dattijuwa kawai ta hau titi tana tsaida wata mata,Amana ta Riga ta kawo da mota da kyar ta iya take birki amma duk da haka sai da ta bigi dattijuwar nan kadan a kafa,matar ta fadi wanwar,Amana da sauri ta gangare tazo tana yiwa matar sannu tana bata hakuri,matar ta rigada ta rude sosai bata gane wace kawai murya takeji,
Masifa ta fara yiwa Amana dalla matsa dabba yar talakawa matsiyata,sai faman ashar matar nan takeyi Amana Na bata hakuri amma matar nan cewa take wlh iyayenki ma sai sunyi nadamar haihuwar ki,sai Na batar dasu.
Amana haushi taji kawai ta take motar ta suka tafi schl,ta bar matar nata masifa da zage zage,da kyar driver da wannan kawar tata da take kokarin zuwa wajenta suka sata a mota suka kaita asibiti aka dan duba lfyrta suka dawo gida,matar kawai tunani takeyi a ina zata ga yarin yar nan da ta kadeta taci ubanta har iyayenta,gashi ko ta ganta baza ta gane ta ba tana rude bata ga fuskar yarinyar ba,amma zata gane muryar,motar ta tuna sai taga kamar tasan motar,kamar motar Alim danta,amma me zai kawo wata ta hau kai ba ta Alim bace amma taci alwashin nemo Amana dan ubanta,wannan dattijuwa ba kowa bace face Mum din Alim.
Amana kuwa mamakin irin masifar matar takeyi,bayan sun tashi daga schl saloon ta wuce aka gyara mata gashinta wannan karan kasan gashin tasa aka canjawa kala y koma yellow fari fari,sama kuma baki,kaji turawa an waye a lagos.
Aabid ma anma masa wani kala ya kalli sama ka rantse bature ne,dama Aabid gashin turawa gareshi yellow ba black ba,
Amana har islamiyya Saturday Sunday tana zuwa yanzu,Alim tunda yaga gyaran gashin Amana yake mamakinta kamar wata baturiya wayewar tayi yawa,na Aabid kuwa ai kasa magana ma yayi ya rabu dasu kawai,.
Suna zaune a palon kasa, Baban Amana ya kirata a waya,dagawa tayi da sauri tare da cewa Allah bar mana me gida sai Baba,ya kowa da kowa,alhmdlh cewar Baban Amana sannan yaci gaba bakya nemanmu ko, haba Baba ka daina irin wannan kasan ina ji dai kai fa cewar Amana, Baba a gaishe da Umma kace gobe zan kirata pls,Baba hope dai ka daina abin nan da kakeyi ?Allah Baba shi yasa naki zuwa Na ganku ga kudi ina samu.
Baban Amana yaji Amana tace tayi kudi sai murna ta kamashi bai damu da abinda Amana tace ba kawai ya fara haba yar Amanata yaushe zakizo Na ganki yanzu Allah ya kusa shiryata ai Amanata,zan hadaki da Ummanki,Umman Amana dake gefe taji ance Amana tayi kudi caraf ta kwace tace Amana yata yaushe zan ganki dan Allah kizo mu ganki,ki siyo min doya da manja,ki taho min da garin kwaki dan lagos,ki tahowa da kannenki kwakwar manja,da ashobe Na yarabawa zan dinga zuwa biki,
Baba ne ya kwace wayar daga hannu Umma yana harararta tare da cewa matsa banza kwadayayya,yace Amanata Nima ki siyo min leshi dinkin buba zanyi Na yarabawa maza,ki siyo wa Haladu 3qutr Na maza,ga kannenki su Badariya ko T-shirt ki siyo musu kinji,
Matan gidan da yara duk sun rude kowa yana Anty Amana ki kawo min ayaba da lemo,wasu suce naman kaza,wasu suce yohourt,Badariya yan mata kanwar Amana me ji da kanta da tashen fitsara ita ta fisge wayar daga hannun Baba tace ke Amana ni Apple zaki siyo min kin San ni ba kalar kauye bace,amma Baba yana wani wai ki kawo min T-shirt yo Allah Na tuba T-shirt ko ta su Badaru ai Na sa,kin San Baba dan kauye ne wlh,
Zanci Uwarki Badariya Jakar banza dan Ubanki Babane dan kauyen?mahaifinkine fa Allah ya kamaki shegu marasa tarbiya cewar Amana,Badariya ma ta cikin waya tace Badai ni ba kece shegiya wlh,su iyayen namu da kike tarewa Ubanme suka tsinana ma,komai mu mukewa kanmu,ba makaranta hattana sabulun wanki mu ke siya,sannan kuma muyi musu biyayya,Amana tace ke Iyayenmune fa dole mu duba darajarsu garemu,kuma dole mu bisu ko me sukayi mana,iyaye iyayene wlh amma Badariya kodai kina Jan hayakine?
Tun yaushe kuma Amana ai har wiwi ja nakeyi cewar Badariya,shuru Amana tayi.
Badariya tace ke Amana anfa kama Isa yana police station ya saci akuyar gidan shehu me alewa,Zahrau kuma ta cirewa wani yatsa daya ana ta rigima,Goggo uwar gida ita ta karbi wayar tace Amana ni ayabar da ake soyawa zaki kawo min,Amana tace oh Goggo plantain? Eh yawwa inji goggo.to shike nan sai mun kara magana kitt Amana ta kashe waya tare da dafe kai tana maida numfashi.
Sun dameta da surutu kowa nata shirme,tsaki taja a fili tace gidanmu gidanmu baza su taba canjawa ba,hannu ta daga sama tace ya Rab gamu gareka,
Kyalkyalkyal taji dariyar Alim da Aabid har sun tuntsuro kasa sabo da dariyar kauyancin yan gidan su Amana,juyowa Amana tayi taga yanda Alim yake sheka dariya sosai dimple dinshi sun lotsa yayi mugun kyau,
Sakin baki tayi tana kallonsu,ita ta manta Alim yana wajen gashi wayar a handsfree ta sata,
Tsayawa tayi ta shagala tana ta faman kallon dan bakin Alim da hakoransa yar yar ga dariyar tayi masa mugun kyau,
Saida suka gaji da dariyar suka tsaya Alim yace no wonder kike haka,Ashe a hakan kamar ma kece wayayya nutsatsiya a gidanku,wlh Na kusa zuwa kano kece driver komai za a siya musu kar ki damu,nan ya kara sakin dariya,
Amana takaici ya kamata za a raina mata dangi da iyaye a masifance tace don't go there pls dan billahillazi ka zagi iyayena sai nayi butar malam da kai,kai akan iyayena zan iya karyaka,ka San me zaka fada min bana daukan wulakanci gwara ka koreni,dan kana da kudi muma haka Allah yaso ganinmu ehe,
Aabid ne ya matso kusa da ita zai riketa da sauri ta hankadashi baya ya fadi tim,ta zare masa ido kai ni zaka yiwa dariya a haife Na haifeka takalminta ta cire ta Zane duwawun Aabid dashi,
Sai kuka yakeyi yana bata hakuri,Alim yana gefe yana kallonsu yace kinji kunya your Boy kike duka yau,da sauri ta jefar da takalmin ta rungume Aabid tana lallashi,Mum Alim wacce ke labe jikin kofa tana kallon komai akan idonta,banko kofar dakin tayi da karfin gaske.
AsmaBaffa
[6/27, 9:25 PM] +234 808 968 1079: ✳CIRANIN AMANA✳
55-60
By
AsmaBaffa
Mum Alim tana muzurai zata fara masifa tare da bin Amana da wani mugun kallon tsana,amma shigar Amana ta bata mamaki,domin Amana bata sa uniform din yan aikin Alim ba,kayan sawarta ne Na swagg a jikinta,Wani tunanin mugunta ne ya darsu a zuciyar Mum Alim nan take ta saki fuska da fara'a tace Alim wannan yarinyar fa? Alim yace Mum me kula da Aabid ce,ya ban ganta da uniform ba? Yanzu ta cire Mum,Aabid kuma me yayi mata take dukansa?tsokanarta yayi Mum,hmm ba a haka yarinya me raino da hakuri akasanshi,
Alim ne ya kyaftawa Amana ido wai ta gaisar da Mum,da sauri Amana tace Mum An yini lfy?hmm haka ake gaisar da manya a garinku?Baki da tarbiya ne? Amana tana zumburo baki tace sorry fa Ina kwana,
Mum ce tace hmm yanzu ai yamma ce,to ina yini?lfy cewar Mum tare da tabe baki,
Amana kuwa sarai ta gane masifaffiyar matar da ta kade ce a titi,itama Mum ta gane Amanace ta kade ta,shi yasa ta kulla mugunta a ranta,
A fili tace ke yarinya ya sunanki,sunana Amana,wanne gari? Kano state a garin wudil.murmushi Mum tayi tace good tare da cewa Alim dama Aabid nazo gani ni Na tafi gida,
Haba Mum ki zauna mana,murmushin mugunta tayi tace abinda nazo wajenka zan nemo Na samu cikin sauki shiken nan bye ta yi waje cike da shirya mugunta,
Mum murna take taga yarinyar da tafi tsana a duniya,ga laifin ta dukar mata jikanta,gata a gidan danta tana cin arzikinsa,lallai Amana zata ci Ubanta.
Ita kuwa Amana bata kawo komai ba a ranta,Hannun Aabid ta kama take ta faman lallashinsa tare da cewa master pls ka tayani lallashi,tabe baki Alim yayi yace kunfi kusa Amana keda ur Boy.
Bacci Aabid yayi a jikin Amana,kallon Alim tayi dake latsa waya tare da cewa Daddyn Alim wannan dama Mum dinka ce? Itace wacce nake fada maka Na kusa bigeta a mota tana ta fada,Kinyi sa'a da ta iya kyaleki haka ki godewa Allah,shuru Amana tayi tana tunani.bayan sati daya Alim ya samu kiran gaggawa daga wajen Mum, 5pm ya dawo gida cikin tsananin kunci da bacin rai ba a San wacce Magana sukayi da Mum dinsa ba
Amana suna palonsa ita da Aabid sunga lallai Alim yana cikin damuwa,shi kanshi Alim so yake ya samu abin nishadi abinda zai sanyaya masa rai,wayar sa ya dauko tare da mikawa Amana wayar take this kira Daddynki kuyi hira da su Ummanki,da sauran yan gidanku,
Amana cike da mamaki ta kalli Alim tace rannan fa munyi waya dasu kuma,Na sani ai ki kirasu kawai kuyi hira ungo karbi cewar Alim,shi Alim so yake yaji shirmen gidan su Amana ya sha dariya ko zai samu saukin zuciyarsa.
Amana kuwa karba tayi amma sai ta kasa amfani da wayar,karba yayi ta karanta masa number Baba yasa tare da dialing,bugu daya Baba ya dauki wayar tare da cewa Alo...Alo ..da sauri Alim ya mikawa Amana wayar ta kara a kunne tare da cewa Hello Baba Amana ce.
Hhhhh Baba ya kyalkyale da dariya tare da cewa 'yata Amanatullah wannan lambar fa ta waye? Kallon Alim tayi ya yayi mata nuni kawai tace ta saurayinta ce ,Baba number Saurayina ce,wata kara Baba ya saki Amanata yanzu a lagos kinyi farin jini kin samu masoyi,Ashe zanga aurenki a duniya,Amanata duk bakin jininki a lagos kika samu miji,murmushi Amana tayi tace Baba sai ma ka ganshi kamar bature,me kudin gaske,yeeeeeeee ahayye yan gidan su Amana suka dauki shewa da guda tuni yan gidan kaf suka yanyame Baba,Umman Amana ce ta fashe da kuka tace Allahu Akabar kabira,yanzu Yar nan duk bakin jininki kinyi saurayi,Ki gaishe mana dashi idan zaki zo ki taho da shi mu ganshi,Goggo ma ta fisge wayar tare da cewa ice ko yana bada kudi me kyauta ne?Amana tace dubu Dari Dari yake rabawa sai yan gida suka dau tafi da ihu,Haladu ne ya matso ya wafce wayar Amana dan ubanki wayar tarho zai siyo min ki fada masa, wlh kika zo babu wayar sai Na karyaki,kaji Haladu kaifa jarabane karma ka dameni cewar Amana,Badariya daga gefe tace kai Amana shegiyar gari ce,yanzu tana can tana Shanawa.
Jamila tace Amana ki kula mazan lagos HIV ce garesu karki bari ya sa miki ita,gwara ta kama Baba,Baba dake gefe samu yayi ya kwadawa Jamila mari tare da fisge wayar ,nan take matan gidan suka fara fada ana zage zagen juna,kafin kace me gidan ya hargitse ana ta cakaki,gajiya Amana tayi ta kashe wayar cike da bacin rai,
Ga kunya ta lullubeta domin Alim yasa wayar a hands free.
Kallonsa Amana tayi taga shi sai dariya da murmushi yakeyi abinsa.tare da fadin why zaki kashewa Baba waya ana hira yaci gaba da murmushinsa.
Kwanaki kadan akayiwa su Amana hutun makaranta Alim yace su shirya zasu je kano wajen danginsa for 1wk zai kai musu Aabid,su. Dameshi da son ganin Aabid,murna wajen Amana ba a magana zata ga danginta,yauce ranar tafiya Alim yace kuma a motocinsa zai tafi bazai bi flight ba,Amana ce me driving Alim da Aabid, escort suna sauran motocin,
Fitowa sukayi Amana cikin shigarta ta yau da kullum,Alim ne ya Ce ina kayan Dana siya miki aka kai dinki gaba daya Riga da skert ne kala 10 harda dogayen riguna readymade wajen 5,takalma da bags,gyale komai dai me tsada akwati guda Alim yayi mata duk wani kayan tsaraba kuma an jibge a mota basu da matsala
In dai baki canja kaya ba wlh baza ki je ba,ko kunya bakyaji yanda kika zo lagos ki koma haka,
Akwatinta dake mota ta zuge ta dauko wani lace me tsadar gaske milk and brown,cikin gidan ta koma ta shirya sosai ta fito a yan mata,ba karamin kyau tayi ba kamar a saceta,takalmi gyale da jaka duk brown,bata iya daura dankwali ba acuci maza kawai tayi ta yafa siririn gyalen a kanta ta fito cike da takun gadara,wai ai Alim ya kusa suma yanda yaga Amana yar india,ta hadu sosai,shi kuwa wani milk wandon jean ne pencil a jikinsa sai wata T-shirt pupple, takalmi ma milk color yasha kyau,Amana fa an waye sosai key ta karba ta shige mazaunin driver Alim Na gaba ya daura kafa daya kan daya can saman gaban mortar, Aabid a bayan mota,Amana a nutse ta fara sarrafa kan mota sannan suka dauke hanya,tafiya Amana take shararawa ta gaske tun Alim yana tunanin zaiji tace ta gaji amma sai yaji shuru kida kawai takesha tana murza kan mota,Aabid yayi bacci wurin kai Uku,Alim ma sai bacci yakeyi,
Sai da sukayi Rabin tafiya har dare ya kusa yi sannan Amana ta kalli Alim tace Master yunwa mukeji ga my Boy ma sai bacci yakeyi aci abinci ayi sallah, ok kawai Alim yace tare da gwadawa Amana garin da zata tsaya restaurant din,
Abinci da sallah sukayi Amana da escort suka take kan mota har dare yayi har wurin 2am Na dare suka zo Kaduna Alim yace suyi bacci a kd gobe su karasa kano saboda kafafunsa har sun kumbura,Amana tace a'a wlh baza mu tsayaba sai munkai kano,ke engine ce wai bakya gajiya ko namiji ba kowa ne zai iya abinda kike ba,
Ae naji amma ba wani kwana a kd sai munje kano.haka suka dinga sharara gudu 4:50am suka isa kano,wajen ciromawa suka tsaya sukayi sallar asuba Amana harda yin brush a gefen titi,haka tacewa sauran ma duk saida kowa yayi brush har Aabid,Alim ma,sannan suka tsaya zasu dan huta,kafin wani lokaci Masu shayi sun fara yi,Amana har teburin me shayi taje ta zauna aka yi mata hadin kauri da indomie da kwai a wajen taci ta koshi ta shanye tea dinta Allah yasa ma mutane basu fara fitowa ba,haka tayiwa Alim da Aabid take away har mota,su kuma sauran escort sukaje duk suka sha suka ci abinda suke so Alim ya biya kudin,shi kam Alim sabo da yunwa shima cinye nasa yayi,Aabid ma Amana tayi feeding dinsa,Amana harda wanke fuska da sabulu tayi fresh,ta shafa powder da lipglow,Alim ya kalleta tare da tabe baki tare da cewa bafa saurayi zakiyi ba,dama bakin jini gareki,kar muje gidanku wlh kice ni saurayinki ne ba ruwana,
Amana murmushi tayi tace za a gani ai.ni nace kace Na fadawa Baba hakan.
Ci gaba sukayi da ta tafiya a nutse har kano cikin Tudun yola GRA,wani tsantsararren gida suka nufa nan take aka wangale musu gate suka kutsa ciki,matan gidan da sauran wasu mutanen yan uwan Abban Alim,duk suna waje sunzo tarbar Alim da Aabid,abinda ya basu mamaki mace ce driver dinsu,
Basu ce komai ba Amana ta fara budewa ta fito tare da gantsarewa tayi mika tana Hamma da salati,duk an zuba mata ido ganin ta fito ba dankwali gyalen na ta ma a hannunta yake,
Zagawa tayi ta dauko Aabid Alim kuwa daya daga cikin guards shi yazo ya bude masa kofa sannan ya fito a gajiye,danginsa yan mata da samari kowa rungumeshi yakeyi ana masa sannu da zuwa,haka manyan iyaye ma,sannan suka koma kan Aabid,gaba daya securities din Alim sun kwashi gaisu wajen dangin Alim sannan aka basu part guda masaukinsu da masu basu abinci etc,Amana kuwa duk cikin manya samari da yan mata ba Wanda ta kalla da idon rahma,babu Wanda ta gaisar kawai gefe taja ta tsaya tana binsu da kallo,har suka gama rungume rungumensu,
Daya kanin Abban Alim ne yace Alim wannan fa?
Sai lokacin Alim ya yafito Amana da hannu ta karaso wajen,tunawa tayi yace in sun hadu da manya ta dinga gaisar dasu da wannan dalilin tace barkanku da gida tayi shuru Abinta,Alim yace Kawu wannan me kula da Aabid ce,madalla cewar Kawu,kakar Alim ce ta jawo Amana zo muje wannan ta wajena ce da kyar Amana ta danyi murmushin yake,ita gidansu can wudil take so ta tafi,
Alim ta kalla kurrr tace Daddy gidanmu zanje ni dai,nan take Alim ya watsa mata hararar data firgitata, a hankali yace haka ake gaishe da manya gidanku,zan fasa barinki kije gida wlh in kikara irin wannan,kuma kibi kaka kuje can ki zama me tarbiya kina koyawa Aabid why ke baza kiyi ba.
Haj Sameera kanwar Abban Alim itama tazo daga Nassarawa G.R.A gidan mijinta sabo da tarbar Alim,tare da iyalanta yan mata su 4,sai Alhaji Ishaq shima kanin Abban Alim shi tare suke zama da Babarsu wato kakar Alim da yaransa Maza samari manya su 4 mata 2 yara sune suka taru a gidan.
Shuru Amana tayi tabi Kaka suka tafi sashenta Aabid sai kuka yakeyi shi Anty Amana zai bi.
Kaka sai tsokanar Amana takeyi tun Amana bata saki jiki ba har ta saba da kaka, ita kaka dai haka kawai taji tana son Amana,wanka Amana tayi taci abinci ta haura gadon kaka sai bacci,Alhaji Ishaq sai fada yakewa Alim ya wahalar masa da jika tun daga Lagos har kano a mota, ka tabbata sai dai securities su koma da motocin kai da Aabid kubi flight.
Kowanne cikin Wanda sukazo baccin gajiya suke ta kwasa tun safe har 5 sannan suka tashi sukayi wanka da Sallah,Banda Amana domin hutun sallah takeyi,kuma Ita kadaice batayi bacci ba har sukazo kano,Aabid tuni yar Haj Sameera Ikram tayi masa wanka ta shiryashi,Alim ma ya gwangwaje cikin shiga ta alfarma.sunyi sallar isha an hallara ana jiran kaka da Amana amma shuru Alim sai baza ido yakeyi ina sa ran ganin Amana.
AsmaBaffa
[6/27, 9:25 PM] +234 808 968 1079: ✳CIRANIN AMANA✳
60-65
By
AsmaBaffa
Amana ta fito daga wanka a toilet din Kaka ta gama shafe shafenta sannan ta dauko Riga da wando zata sa abinda harda pcap,Kakace ta karbe kayan tare da cewa haba jikata gidan nan maza ne da yawa samari,bai dace kiyi wannan shigar ba kinji,
Babu kyau,kuma daga yau jikata idan kinga manya ki gaishesu sosai ba irin gaisuwar da kikayi dazu ba kinji,ki rusuna ki gaishesu a ladabce,nan Kaka ta zage ta dinga koyawa Amana abubuwa sosai,
Kuma Amana ta gamsu ta yarda maganar Kaka gaskiyace,ita kuwa Kaka ta tabbatar Amana tana bukatar tarbiya,da alama bata samu kulawar iyaye ba,a hankali Amana tace to Na gode kaka kuma zanyi yanda kikace,ki zama mace ta gaske me aji kinji? nan ma jiki a mace Amana tace to kaka domin tunda take arayuwarta babu Wanda ya taba cewa ta gyara halinta sai kaka,nan taji ta kara kaunar tsohuwar,
To dauko atamfa kisa a kayanki muje cin abinci,ba musu Amana ta dauko wata Riga da skert Na atamfa me kyau da tsada red ta saka ta shafa powder harda jambaki red,ba karamin kyau tayiba kamar yar India ga diri da shape ga fadin hips da tudu sosai,komai cib,
Kaka tace masha'allah,to saura daurin Dan kwali,kaka ban iyaba cewar Amana tare da dakko red gyale ta yana Dan siriri,tasa flat shoe red,suka fito tare da kaka gwanin sha'awa.
Palo suka fito karo Na farko kenan da Amana taji kunyar mutane,kowa ya zubo mata ido,Baren ma Alim da yake kallonta kamar me,karasowa tayi a nutse ta tsuguna har kasa gaban Abba Ishaq da matarsa da Haj Sameera tare da cewa Ina yini Abba,kuna lfy?fuska sake ya amsa mata,haka tayiwa su Sameera ma,mazan samari da suke ta faman binta da kallo tace sannunku Ina yini,suma sun amsa da fara'a,ganin yan matan tayi ai sa'anninta ne koma ta girmesu,ga wani kallo da suke mata Na banza kawai sai ta sharesu ta mike tsaye,daya daga ciki wato Ikram tace mu baza ki gaishe mu ba?
Amana ce ta juyo a fusace tace hey mind ur tongue bana daukan nonsense,ta juya wajen Alim abinta sauran kuwa da mamaki suka bude baki lallai yarinyar nan masifaffiyace daga magana,su kuwa mazan birgesu Amana tayi ma,
Huzaifa dan gidan Abba Ishaq dake wajen yace bakuwace fa maybe ma ta girmeku Ku Baku kulata ba, tazo gidanku sai ita zata gaisheku,Kaka da Abba Ishaq sukace kyaleshu shashashai.
Amana kusa da Alim ta koma ta zauna a hankali tace ina Aabid,A hankali shima yace Aabid yayi fushi da ke,ni baza ki gaisheni ba?
Dariya tayi tace Daddy Kakace ta koya min fa,Kallonta Alim yayi yana jin wani farin ciki da ya rasa Na mene,ga kamshinta da kyan da tayi yana wani fusgarshi,
Alim da Amana hirarsu kawai sukeyi a palon an zuba musu ido kowa da abinda yake sakawa a ransa,
Abinci aka shirya kowa ya hau dining banda Amana da Kaka su basa zama a kujera,suna ci suna hirarsu,Huzaifa ma wajen Amana ya koma ya like musu,sai hira suke sha,Dan danan Amana ta saba da mazan gidan gaba daya banda matan,
Suna gama cin abincin Alim ya cillawa Amana Key din mota muje ki kaini gidan su khaleed Frnd dina ne.cafe key din Amana tayi tace wlh ni bacci nake ji ka nemi wani driver din, tun daga Lagos ko bacci banyi ba har kano kuma kace mu kara fita,
Palon gaba daya aka cika da mamaki mace ta tuko mota tun daga lagos har kano ansha mamaki tare da jinjina mata,Haj Sameera tace ke yan mata ya sunanki ma, sunana Amana, great name,Huzaifa yace lallai sunanki Na daban ne Baby Allah sa ki zama me Amana
Kaka tace ke kyaleshi muje kiyi baccinki,shi kanshi Alim fasa zuwa yayi yaje ya kwanta shi da Aabid,cikin dare Aabid ya dinga tsala ihu shi A kaishi wajen Antynsa,
Daukoshi Alim yayi har part din Kaka ya buga mata kofa ta fito,yace Aabid ke Neman waccen yarinyar,sai kaje ka kai mata tana waccen dakin,nan Kaka ta koma dakinta Alim ya shiga dakin Amana,
Da sauri ya runtse idonsa ganinta sanye da short wando da kadan ya rufe duwawunta,sai wata half vest a jikinta ta tale kafafu tana ta bacci,
da sauri Alim ya daura Aabid a bed din ya fice da sauri tare da rufo dakin.
Da kyar Alim ya iya runtsawa a ranar,washe gari da safe Amana ta hada kayanta Dana kaka ta fito can bayan gidan jikin wani panfo daga ita sai wata doguwar Riga me hannun vest,wankin kayanta dana Kaka take faman yi,
Mutanen gidan sai dadi sukeji tana girmamasu tsohuwa,Aabid yana kusa da ita,Alim yana sama yana kare mata kallo ta window,
Kwanansu Amana uku a kano,Alim yace tashirya zasuje ya kaita gidansu,Ta gama shirinta Na tafiya Garinsu wudil sai murna takeyi,
Motocin Alim gaba daya da escort suka jera zuwa gidan su Amana cikin yan tafiyar harda Huzaifa.
Amana tana ta driving dinta sanye take cikin wani rantsatsen lace Golden Colo tayi matukar kyau,Alim yasha arniyar shadda light blue fitted,Aabid kam English wear ne,Huzaifa ma ya chakare,jerawa sukayi har garin su Amana tun a hanya Alim ya fara sa ido yana dariya kasa kasa,zasu sha kallo yau.
Ana zuwa wata majalisa Amana ta tsaya da motar tare da sauke glass kasa tace hi guys Baaabaa Baabaa kuna sha'aninku,kallonta sukayi sosai da kyar suka iya ganewa Amana ce,Alim Huzaifa sai kallon ikon Allah sukeyi,ganin gungun samari sun yanyame motar ana ta kawowa Amana gaisuwa,haka Amana ta dinga tsayawa majalisa majalisa suna gaisawa,tace sai Na nutsu Baabaa akwai labari fa.
Har kofar gidansu ta tsaya sauran motocinma suka tsaya,Ko wa kallon irin rubewar da gidan yayi sukeyi,su Baban Amana suna waje sun zata shugaban kasane yazo wucewa,shi kanshi Baba kasa gane Amana Yayi su Alim gaba daya fitowa sukayi daga motar,mutane sun yanyamesu ana kallon turawa sunzo,wasu suce turawane zasuyi Titin kwalta,wasu suce ai makaranta zasu Gina,wasu sunce ruwan tuka tuka za ayi ko pampo,
Amana tace Allah taimaki Baba, Baba Amana ce fa,ai Baba kamar ya suma, Da karfi yace Amana yaushe kika zama haka ko takarar Gomnan Lagos kika fito kika ci bamu sani ba,ai Alim da Huzaifa Dariya suka kamayi,can sai ga Haladu da gudu yana haki yana zuwa ya dakumi Amana yace arniyar kasa wlh itace Dan ubanki ina wayata?
Matan gari sai leke sukeyi ta Katanga suna gulma gidan Baki sunyi kudi,Amana ta dawo da arziki harda sojoji masu take musu baya,Amana kafin ta shiga cikin gidan yan gidan kaf maza da mata yara da manya sun fito gaba daya kamar yaki,
Hamza babban yaya yazo wajen Amana yace shegiyar ban biyar Amana ta bashi hannu suka tafa tace How far man,Hamza a Abuja yake Cirani kawai sai ya juya harshe suka fara broken English pigeon shi da Amana,
Huzaifa da Alim dariya kamar su mutu,duk shuru shurun Alim kasa dannewa yayi.
Badariya yar kwalisa ita ta matso tace Banza yar kauye to ki shiga cikin gidan mana,kinzo da mutane kin barsu a waje,wajen Aabid Badariya taje tace kaga Bature amma wannan baya jin hausa,Fatar Aabid ta latsa da Sauri ta kalli Alim tace laushi wlh,dariya Alim yayi tare da cewa Badariya ko?tace laaaa dama kuna jin Hausa?a ina kasanni? Huzaifa ta kalla tace kuzo Na Baku wajen zama Ku kyale shashasha Amana,dariya Huzaifa yayi yace antynki cefa ko? Ae yayata ce amma Allah Amana bata da mutunci kaf garin nan an sani,yanzu ta balla mutum,
Amma fa tafi kowa hankali a gidan har Baba dasu Umma cewar Badariya, dauko mana tabarma mu zauna a waje kinga muna da yawa cewar Huzaifa
Wai wanne ne cikinku saurayin Amana?cewar Badariya,Huzaifa bai San me zai ce ba kawai sai ya nuna Alim yace gashi,harara Alim ya makawa Huzaifa,
Cikin gida Badariya ta koma dakin Babansu ta dauko manyan tabarmi sababbi dal dal guda uku musamman Baba ya siya sabo da bakinsa.
Inuwar mangoro me sanyi dake kofar gidan ta shindidawa Alim da Huzaifa,suka ce ta mayar da sauran saboda guards basa bukata suna can jikin motoci,
Baba ne ya karaso wajen Su Alim a mutunce suka gaisa aka kawo musu ruwa pure water leda uku me sanyi,
Amana kuwa tana cikin gidan ana ta labarin duniya,dan ma Amana bata fiye surutu ba,Badariya duk ta fesa cewar Alim ne saurayin Amana sai kallonsa akeyu.
Suna zaune Amana ta fito tana kuyi hakuri Na barku kuzo muje ciki Ku gaisa dasu Umma,Aabid yana makale jikin Alim suka shiga suka gaisa dasu Umma,Alim a hankali ya cewa Amana wace Ummanki? Nan Amana ta nunana musu Ummanta wata fara kwal kamar kwara,suna kama da Amana,gashi yan gidan gaba daya ba laifi suna da kyau sosai Amana ce ta fisu gaba daya,
Alim zai tafi matan manya kowacce dubu hamsim,Umman Amana dubu Dari,Baba ma dubu Dari,sai kayan tsarabarsu yace Na Amana ne ta siyo musu,su doya,manja,dankali,etc harda wayar Haladu,Apple,banana da lemo,su guava, duk abinda suke fada a waya Alim ya siyawa Amana ta basu,gida da makwafta an rude,
Alim sunyi Sallama da Amana cewar jibi za a zo a dauketa zasu koma lagos,Amana tace to ka tafi ni idan nayi 3wks sai Na dawo lagos din,Aabid dinfa? Alim ya furta,baki ta turo gaba to shike nan ka turo jibin a daukeni, Kudi ya bata yace ga salary dinki,
Kin karba tayi to wannan kyautar da kayi a gidanmu ai yafi karfin salary kawai ka barshi,ban son iyayi karba malama kina bata mana lokaci,Karba tayi tare da godiya,baku ci komai ba,tabe baki Alim yayi mungode zamuci a gida, Aabid tayiwa bye bye tare da cewa dama nasan ba ci zakuyi ba Ku yan gayune,Huzaifa yace no ba haka bane Baby Amana, wuce gida tayi aka ci gaba da labarin duniya. Alim sai wurin dare suka koma can gidan su Kaka.
Amana kuwa bata basu labarin halin da ta Shiga a lagos ba,bata fada musu irin rayuwar da tayi a lagos ba,kawai labarin duniya ta basu,haka frnds dinta maza ta ba wasu Dari biyar,wasu 1k,tunda Amana taje take yiwa yan gidansu hudubar Ilmi,cikin kwana daya duk kannenta saida ta sa su a makaranta,
Har alkwari tayi musu indai sunyi karatu to zata sai musu motar hawa,sai murna sukeyi suka sami kwarin gwiwar zuwa Islamiyya da boko,suma yayyen nata sun shiga islamiyyar Matan aure suna jira Amana ta sai musu motoci,mazan kuwa Amana tayi musu alkawarin jari,suma har sun fara nutsuwa,
Iyayensu kuwa tace Makkah zata kaisu suma wannan dalilin yasa ba shiri suka shige islamiyyar matan aure,sunga fa lallai Amana da gaske take,
Baba halinsa yana nan Na banza sai Wanda ya karu a kai,har matan aure bi yakeyi,shi yasa kudin da Alim ya bashi Amana tayi masa wayo ta kwashe kudin ta bar masa iya 20k,sauran kuwa duk ta biya family schl,
Baba yaso yayiwa Amana dukan tsiya kan ta karbi kudinsa amma sai ya tuna alkawarirrikan da tayi masa sai yayi shuru da bakinsa, yaune ranar da Amana zata bar garinsu,kananan kayanta duk ta rabawa su Badariya,su Umma ma sun samu T-shirt dai dai,Aabid ya dami Alim rigimar a kaishi wajen Antynsa ba shiri Alim ya turo driver guda daya da mota da safe da wuri yazo daukan Amana,sai kumburi Amana takeyi sai wajen 5pm sannan ta dauko akwatinta tabi driver suka taho cikin kano city.karfe takwas Na dare suka karaso gidan.
Aabid yana jin sallamar Amana ya fanfaro da gudun tsiya ya dafalfaleta,mutan gidan duk suna Palo banda Alim Wanda sun fita gari da Frnd dinsa khaleed,
Gaishesu Amana tayi ta tafi wajen Kaka can ta ya da zango sai hira sukeyi da Kaka,har tayi wanka Kaka ta kawo mata abinci sukaci tare da Aabid,
Alim kuwa tun safe yake jiran dawowar su Amana amma shuru har khaleed yazo suka fita.Amana har tsarabar Goro ta kawowa Kaka,sai murna Kaka takeyi Goro lafiyayye me yawan gaske,Matar Abba Ishaq kuwa da Haj Sameera kayan miya irinsu su kuka,kubewa bushashiya,gyada danya etc duk Amana ta kawo musu da yawa.
AsmaBaffa
[6/27, 9:25 PM] +234 808 968 1079: ✳CIRANIN AMANA✳
65-70
By
AsmaBaffa
Tunda Alim ya dawo yaga ba Aabid yasan Amana ta dawo,washe gari da safe ma Amana bata fito ba a dakin Kaka taci abincinta,
Har yamma lis Huzaifa yaje yasa Amana tayi shiri sosai cikin wata arniyar shadda sky blue,suka fito sai kyalli sukeyi,khaleed da Alim suka gani a compound,
Da fara'a tace Daddy barka da yamma,ta kalli khaleed kadan tace ina yini tayi gaba abinta ba tare da ta jira amsarsu ba, Alim a ransa yace lallai ma yarinyar nan,
Khaleed yace wannan kyakyawarfa?yar uwarku ce? A Ina ka zama Daddy dinta?
Tabe baki Alim yayi tare da cewa Nanny din Aabid ce fa,Aabid yana ce min Daddy shine itama take fadamin,lallai ka iya zaben Nanny cewar khaleed,sai wurin 9pm Amana ta shigo ita da Huzaifa,yayi mata siyayya sosai,Alim suka gani shi kadai a Palo,ko me yake jira oho,
Yana ganin Amana ya sauke Ajiyar zuciya me karfi hade da mikewa ya bar palon,washe gari 6am escorts dinsa suka kwashi motoci suka dauki hanyar lagos, da Aabid jirgin karfe 5na yamma suka bi,Amana sai murna akeyi ana zare ido an hau jirgi,
Mintuna kadan suka sauka a Lagos wani Frnd din Alim Kamal yazo ya daukesu a airport,ya kaisu har gidan Alim ya wuce abinsa.
Gidan neat kal kal suka samu ko ina kasancewar yan aiki sunayin gyaransu,
Tunda Amana ta dawo ta shige dakinta suka sha bacci da Aabid washe gari ma haka Alim bai ganinsu Sam,
Kwanansu Uku da dawowa amma Amana bata kara sa wani atamfa ko lace ba damunta sukeyi,kayanta ta koma sawa,yau shirin wanka sukayi Amana sanye da Wando legins tight iya gwiwa da rigar ta tshirt armless irin doguwar nan ta kai Rabin cinyarta
Aabid kuwa dan pant ta sa masa ta jashi sukayi bangaren sweeming pool din gidan,
Alim suka gani zaune a kujera daga shi sai short ko Riga babu,yana karanta jarida yana kora lemo,towel dinsu Amana ta ajiye gefe,da fruits salad da ta hada musu,Aabid ta Goya ta shige cikin ruwan nan ba tare da suncewa Alim ci kanka ba,
Tunanin Alim Amana bata iya ruwa ba kawai sai ya hangota ta Goya Aabid tana iyo a ruwa kamar wata kifi,a ransa yace ita wannan komai ta iya kenan.
Aabid kuwa dariya yake ta bangalawa yau ya shiga ruwa,dama bai taba shiga ba,sun Dade ciki sannan ta fito zasu huta su koma,gaba daya bata sa bra ba rigarta duk ta manne a jikinta.
Alim gaba daya ya rude ya shiga wani yanayi ganinta a haka,kafe kirjinta yayi da kallo,yanda ko ya tayi motsi kadawa sukeyi,ji yake kamar ya cafkosu ya shafa,gasu shape dinsu gwanin birgewa,Amana fruits dinsu suke sha bata San me Alim yakeyi ba,Alim gani yayi Amana zata koma cikin ruwa kallonsa zai kare,kiranta yayi da sauri,
Amana! Wani iri Amana taji a jikinta babu abinda ke birgeta a rayuwarta irin taji Alim ya kira sunanta,sai taji kamar ta shide,cikin tafiyarta ta gadara da zafin nama ta karasa wajen Alim,shi kuwa Alim kallonsa yake ta sha yanda Na shanunta suke juyawa,
Ya kwashi wajen 10mnt baice mata komai ba,ita kuwa sabo da tasan yanayinsa baya magana a kan lokaci sai bata damu ba ta tsaya tana juransa,shi kuwa ba haka bane kallon kirjinta yakeyi a hankali saboda ya daga jarida nufinsa ita yake karantawa Ashe wayo ya hada kawai idonsa Na kan Amana ta saman jaridar.
Mikewa yayi daf da Amana kamar zai shige jikinta a zuwan shi tafiya zaiyi,Amana ganin kyaykyawar surar Alim yana kyalli yasa ta jin wani dummmmmm a kwakwalwarta,ta rasa gane mene domin bata taba jin hakan ba,
Alim yana sani yayi luuuu ya tafi zai fadi tare da dafe kansa yace ouch...da sauri Amana ta taroshi ya fado jikinta ragwajaf tare da sakar mata nauyinsa ai kuwa yafi karfin Amana nan take suka fada cikin ruwan gaba daya,
Sai lokacin hankalinsa ya dawo jikinsa sai ya fara tamke fuska yana cin magani tare da tsaki ya fice daga pool din,yana ta faman masifa,aikin banza daga kiranki sai ki jefani cikin ruwa,komai bakyayi A hankali kamar wata sakarai yaja tsaki tare da barin wajen cike da kunya.
Amana kuwa bata kawo komai ba tace masifaffan mutum,shuru shuru dashi sai masifa,Aabid ne yace Antyna Daddy baya masifa fa,to naji muje muyi wankanmu,komawa ruwan sukayi suna ta wankansu har suka gama,
Yau sati biyu kenan hutun makarantar su Amana ya kare sun koma schl,Mum Alim tun safe take damun Alim kan yazo fa akan maganarsu,haka ya hakura yaje har dakin Abbansa,
Bayan sun gaisa Abba yace Alim wata magana nake jin cewar wai ka tsayar da mata za a je Neman aure,kallon Mum Alim yayi,Mum kuwa ta daka masa harara ba shiri yace yeah Abba,amma a kano take shike nan Alim ka turo min driver ka jibi za muje nemo maka aurenta,cike da takaici Alim yace to Abba ya musu sallama ya bar gidan kamar ya kashe kansa tsabar bakin ciki,
Kwana tsakani Abba ya shirya tare da Amininsa da Mum Alim,sai driver dan rakiya,flight suka bi har kano suka dauki Alhaji Ishaq sukaje can garin da za a nemowa Alim aure,
Suka nemowa Alim aure kuma an basu yarinya tare da sa ranar aure nan da 1mnth domin Mum tace bata so a day lokaci sabo da shedan,
Mum Alim koda sukaje Neman auren mutuniyar kirki ta zama tare da kaunar talaka haka ta nuna,gidan Amarya sai yabon halinta sukeyi,basu San Mum tana da dalilinta,akwai abinda ta boye a kasa.su kuwa Allah sarki sai murna sukeyi gida ya rude sabo da jin dadi zasu shiga gidan Naira.
Bayan sun dawo Abba ya sanarwa Alim komai tare da yabon dangin Amarya,Abba yace son sai watarana kafin biki ka kawo min sirikata Na ganta,domin Mum dinka tace kana sonta sosai,Asiya kanwarku ma naji yanda take yabon halinta,haka Nura da Auta Sadiq ma naji sunce sun Santa yarinyar kirkice.
Alim dai cike da mamakin makircin uwarsu yace Hmm kawai,shi kuwa Abba ya zata kunya Ce kawai.
Amana kuwa harkar gabanta takeyi kawai daga schl sai karatu,zama da kawarta Rufaida yar gayu yasa Amana ta fara dan canja halinta ba laifi,
Mum tace baza ayi biki ba kawai aure za a daura amarya ta tare,
Biki ya matso Amana a bakin yan aiki taji ogafa zaiyi aure, wannan matar yana sonta ba zabin Mum dinsa bace,nan Amana taji tarihin Alim har auri saki da Mum ke sashi yi saboda bata so wata ta ci arzikinsa sai ita uwarsa da ta haifi abinta,
Ko yan uwansa Na jini bata kauna Alim ya musu kyauta sai ta dinga nuna kyashi da bakin ciki,
Bare Abbansa bata so ko hira taga sunayi da Alim saboda kar ya bashi wani abu,Abban Alim kuwa shima me arzikine, hassada ce tayiwa Mum yawa,shi yasa bata taba yarda Alim ya auri wacce yake so,shi yasa duk wacce tasan Alim bazai taba kauna ba har a bada to ita zata nemo ta aura masa.
Amana tana gama jin labarin taji wani bakin ciki da bata San Na mene ba ya taru ya cushe mata a zuciya,hankalinta ya tashi ta nemi farin cikinta ta rasa,a ranta saida ta tsinewa Mum Alim yafi dubu kan wanne dalili zatayiwa Daddy aure, bakin cikin Amana kenan.
Amana tana shiga Palo bata kula da Alim ba ta jefar da Jakarta a palon ta cire takalminta ta watsar cike da tsananin bakin ciki ta ja tsaki,nan ta fara zagaya Palon,da karfi tace a'a...wai mene haka ne eh....ina ruwana ma aikin banza aikin wofi,
Minti kadan ta buga kafafu tare da miko hannu kamar damisa zata damki nama tace saina ehhhhhhhhhh......shake tsohuwar nan.....can wani lokaci ta dakko ruwa ta kafa kai kwat...kwat...ta shanye tare da jefar da robar tace sai naci uwar tsohuwa wlh...tambadaddiya.....kodaddiyya.....sokayayya....me suffar hanjin ligidi.... Tayi dakinta da sauri ta fada bed dinta,Aabid ne ya shigo daga baya shi kam yaga Daddynsa wajensa ya nufa.
Ihun Amana su Alim sukaji sai karaji takeyi a dakinta,da sauri Alim ya bude dakin nata a kan bed ya ganta kawai wutsil wutsil takeyi tana karajinta tare da tsine tsine,Allah ya baki lfy cewar Alim yayi waje abinsa.Aabid yana a kafadarsa,
Ranar Amana da kyar ta iya yin wanka haka ta kwana ba bacci,sai asuba ta samu bacci,Aabid sai driver ne ya kaishi schl,amma Amana tace Sam ita bata da lfy.haka Amana ta yini da zazzabi,ga period tanayi,harda su amai tsabar bacin ran za a yiwa Daddynsu aure.
Alim kuwa tun yana damuwa har ma ya gaji gudun kar ciwo ya shigeshi a banza,frnds dinsa ma sun jajanta masa, sun tabbatar auren babu inda zaije.
Yau daurin aure saura 1wk Amana duk ta rame ita kanta bata San dalili ba,Alim kuwa ko a kwalar rigarsa indai irin wannan aure ne ya rigada ya saba dashi.
Mum kuwa burinta ya kusa cika,
Kwanaki fa suna ta ja gobe Saturday gobe daurin Auren Alim,dole ya gayyaci abokansa sosai,Amana kuwa tana Palo tana jira taga wankan auren Alim,itama ta shirya cikin shadda dark brown tayi kyau kamar itace Amaryar Aabid kuwa ya tafi weekend wajen Mum Alim,
Wani gigitaccen kamshi Amana taji ya daketa,Alim ya sakko cikin hadaddiyar shigar wata tsadaddar shadda yar gaske fara kwal,yayi Kyan da bai taba yi ba a duniya,ita kanta Amana gigicewa tayi,
Da Sauri ta mike tsaye tana wani kyafta ido sannan ta fara magana,dan Allah Dan Annabi dan Darajar Allah dan girman Allah kaje dani daurin auren naka kaji,
Pls Daddy kaje dani sosai ta damu Alim sai yaje da ita,je kiyi shiri kwana yini daya zamuyi tunda ma hakane sai Na tsaya mu taho da Amaryata.cikin tawagar angwaye dake flight harda Amana,
Amana burinta idan sunje kano taje gidansu su gaisa da yan uwanta.
Gidan Amarya kuwa an cika makil ana jiran angwaye,Abba da yan uwansa duk Suna can,Mum ma ta tura Aminiyarta Haj Talatuwa da Haj sameera kanwar Abba da matar Alhj Ishaq Aisha. Duk suna gidan Amarya ana jira a daura aure.
Angwaye sun sauka a kano sun kara haduwa a manyan motoci Na alfarma tare da frnds na kano an tafi gidan Amarya daurin aure,Amana tana kusa da Alim,sai tsokanarsu akeyi cewar tayiwa Amarya wayo,Amana dai tayi shuru ita da Alim a bayan mota Khaleed ne driver,ana ta zankada tafiya,zuciyar Amana cike da kunci,shi kam Alim ya rasa dalili jin wannan auren yakeyi daban da sauran da Mum tayi masa,baya jin wani kunci,ya danganta hakan da sabo.
Amana bata kaunar ganin garin Amaryar ma sabo da haka ta kwantar da kanta a jikin kujera tare da lumshe ido,khaleed kuwa sai tsokanar ango yakeyi yaki yin shuru,sauran motocin abokan ango suna binsu a baya,
Garin Amarya aka shigo har unguwarsu da layin gidan su amarya wani dandasheshe gida da duk unguwar babu kamarsa shi aka tsaya da motoci,mutane damkam cikin masallaci da wajensa,dangin ango duk gasu nan,har su Huzaifa, Amana bude lumsassun idanuwanta tayi don kallon unguwar Amarya,ai da sauri ta kara damke idonta ganin wani tsantsararren gida me kyau,gida Na fita kunya,ga mutane sunsha wanka,kamshi Na tashi kowanne cikin shigar alfarma,
Amana sai zare ido takeyi da mamaki tana kara bude idonta sai kallon dangin Amarya takeyi cikin suturu Na gaske,da gani sun samu harka,mamaki cike da zuciyar Amana,sai murza ido Amana takeyi.
Kallo Amana take tayi tana murje ido,ga kwalla ta cika idonta har hawaye ya fara zubar mata ta rasa meke mata yawo a zuciyarta.
AsmaBaffa
[6/27, 9:25 PM] +234 808 968 1079: ✳CIRANIN AMANA✳
70-75
By
AsmaBaffa
Amana bata gama shan mamaki ba sai da taga Babanta ya fito daga gida dauke da Alawa goro da chewgum Na daurin aure domin a kauyen haka akeyi,
Hangame baki Amana tayi domin ganin su Haladu da Hamza tare da sauran yayyenta duk sunzo daga garin da suke Cirani,mamakin Amana shine ganinsu cikin shiga me Kyan gaske,gaba daya sun canja,kyansu ya fito,sunyi fresh,to me ya faru haka,amma ai suna waya dasu Baba me yasa basu bata labarin komai ba,cikin motar da take ta kalla kawai sai taga wayam ba kowa Ashe angwaye duk sun fice an barta a ciki,su Alim ta hango sai hada hada sukeyi,musamman yanda taga Alim da danginta sai wasa da dariya sukeyi,mutumin da ba ya magana shine yake ta wasa da dariya haka.
Ana haka aka fara hudubar daurin aure,Amana sauke glass din window motar tayi dai dai da lokacin da taji ance an daura auren ALIM USMAN MUSA da AMANA SULEMAN HARKA kan sadaki naira million daya.
Amana poster tayi ta kame waje daya tare da hangame baki,shi kuwa Alim ya rasa me yake ji a ransa sai congrat akeyi masa da fatan alkhairi,
Baban Amana baki har kunne sai rabon alawa da goro yakeyi ana masa Allah sanya Alkhairi,Amana kuwa ta matsu mazan su watse ta shiga cikin gidansu taji wannan wanne irin abune,za a min aure ban sani ba,
Wani bangaren kuma wani nishadin dadi ta tsinci kanta ciki,tana ta tunanin duniya bata sani ba har mutane sun waste,angwaye kadai suka rage a kofar gidan su Amana,
A rude Amana ta gyara gyalenta siriri shara shara da ta yana a kanta bata daura dankwaliba sai acuci da tayi,gashi shaddar da tasha kowa ya ganta zaice Amarya ce,
Fitowa tayi daga motar kamar zata tashi sama ta wuce cikin gida ko bangaren angwaye bata kalla ba,Amana doluwa ta zama data shiga hadadden gidansu,kamar a birni,ko ina yasha tiles kofofi da windows masu kyau,cikin dakuna sun sha furniture masu kyau,
Komai Na gidan Na yan gayu,dakuna ta duba bedrooms gasu nan na maza Dana mata,Dana baki,da Na Babansu Palo da bedroom,
Dakin iyayensu ma Palo da bedroom ko wacce,kakarsu ma haka.gida ya kai gida ba jin kunya,mamakinta waye yayi gidan haka,
Yan biki mata sai kallon Amana yar gayu akeyi,ana guda,shewa,tare da tsokanar Amarya,Amana sabo da tsabar gulma dan kar ace tana so sai ta fashe da kuka tare da kallon Badariya tace ke dan uwarki ina dakin Umma,nuna mata badariya tayi ta fada ciki da kuka,
Babane ya shigo dakin shima,Amana cikin kuka tace Baba ya zaka yi min haka,ayi min aure ban sani ba,ko a waya ai ka fada min,Baba yace haba Amana ta ki yafewa Babanki kinji,uwar mijinki ce tace kar Na fada maki sabo da tana kaunarki tafi so tayi abinda zai saki nishadi,kinga gidan nan mijinki shi ya Gina min,kinga kowa Na gidan nan ya basu jari me tsoka,kannenki duk ya biya musu kudin makaranta,kudi da abinci da sutura duk shi ya aiko mana sosai har yayyenki da suke Abuja da cross river yayi musu komai,ta dalilinsa gidan nan an ci gaba,ga ilmi ana samu,
Ga shi kowa yana da aikinyi,yanzu duk iskancin da jahilcin da ake tafkawa a gidan nan Nawa ya fara raguwa, Iyayenku sun fara daina zage zage sabo da islamiyyar da kika ce su shiga,haka duk maza da mata masu shaye shaye da sata da matan ma masu mugun hali ta sanadiyyar makaranta da aikinyi da suka samu duk sun daina sai abinda ba a rasa ba,
Ki duba da kanki ki gani su Hamza duk sunyi hankali,nima yanzu alhmdllh Ina ciyar da iyalaina,to Baba kaifa ka daina daya halin naka?cewar Amana,
Jan numfashi Baba yayi yace kuci gaba da min addua Amana Na kusa dainawa,kuka Amana tasa haba Baba yanzu so kake yayanmu su gajeka,mu gaskiya kana jawo mana abin kunya,
To Amanata sai hakuri ai inji Baba,shi yasa alherin da mutanen nan sukayi mana dole Amana nayi musu abinda suka bukata,amma gaskiya uwar yaron nan mijinki da Babansa mutanen kirki ne,kinyi dace,yanda suka nuna mana kauna gamu talakawa amma suka iya hada zuriya damu ai sai dai Allah ya saka,Allah sa Albarka cewar Umman Amana dake zaune bakin gado,Amana tace nidai kawai ba a kyauta min ba,
Kudin sadakinta Baba ya mika mata dubu dari shida ta dauka haladu yaje banki ya sa mata a accnt dinta Dari hudu kuma ta rabawa iyayenta da danginta,
Gidan su Amana suna da tsafta sosai saboda shi Baba Allah yayoshi me tsamtsami,shi yasa dole kowacce ta zama me tsafta a ko ina,saboda yana ganin kazanta zai iya sakin mace.
Badariya ce ta kawowa Amana wainar fulawa da yaji me dadin gaske,ta kawo mata waina da miya ta bikinta,tuwon shinkafa miyar ganye,ummanta kuma ta kawo mata danwake me zafi,
Tun anan Amana taga canji,da Dane yaushe Badariya zata wani girmamata haka,gashi abin farin ciki Badariya ta daina zuka hayakin sigari,Umma ma da ace da ce yaushe ma zata wani saurareta idan ba kudi Amana ta bayar ba gaskiya Alim da iyayensa sun taimaka musu,ko sabo da wannan dalilin ta yiwa mijinta biyayya.
Ta fara cin danwakenta kenan Badariya ta kara shigowa Anty Amana kinga booth din motar angwaye kuwa abincine irin Na hotel da kaji,da ruwan jarka ke harda lemuka sun bude a irin abin take away suna ta ci in fada miki gaskiya yan gayu ne,amma angonki bai ci ba shi,Badariya tace kinga wannan Huzaifan ya bani da yawa Na kawowa su umma,
Anty Amana wai dan Allah nima ina da kyau?kinji wannan Huzaifan sai yace ni me kyauce,nace ai kin fimu kyau yace bai yarda ba Badriya ke ta faman surutu,Amana cike da masifa tace karki dameni dallah,
Sallamar Alim sukaji Umma dake waje tace shiga mana tana ciki ai an zama daya,tana cin danwakenta Alim ya shigo ya zauna a daya daga cikin kujerun palon.
Kwanikan gaban Amana ya shiga Budawa wainar fulawa ya gani tana ta tiriri,dama shi yana son wainar fulawa,gabansa yaja kawai ya fara ci,saida yaci ya koshi ya mike yace ki gama ki fito mu tafi ina jiranki,OK kawai tace da kyar,
Saida ya fita sannan ta sauke ajiyar zuciya tare da shakar kamshinsa,
Saida taci ta koshi sannan ta mike tace Umma zamu tafi, hhhh dariya akayi sosai amarya da ango sunzo daurin aurensu tare sun koma tare,ba a taba ganin irin wannan aure ba,Amarya kamar bata da gatan dangi,
Umma wata katuwar Leda ta mikawa Amana tare da fadin Badriya ta rubuta komai a jiki,wajen Baba Amana taje sukayi sallama,Baba yace to Amana in kayi da kyau kaga da kyau,kibi Allah kibi mijinki Idan kika tsaya wuru wuru ki gani a allonki, muna kallo za a watsaki a jahannama,gidana ba a yaji,idan miji ya sakoki to ki nemi wani gidan ba gidana ba,Amana dai aranta tace wannan ai ba nasiha bace ta kirki,kai Allah shiryi su Baba,a hakanma gwara Baba ya kamanta,Umma ba wata nasiha sai wasu kwalabe manya ta wani bani a Leda,ko mene oho,
A fili kuwa kallon Baba tayi tace ai billahillazi ya sakoni ko nayi yaji dole gidanmu zan taho, ina kakeso naje,Baba ma yace aikuwa kinyi karya in kina wasa ki gwada ki gani,Baba no...zanci Ubanki Amana karki ga ina lallabaki Na fiki iya shege,Amana tace Baba Allah baka hakuri,yawwa tashi maza kuje Allah bada zaman lafiya,
Baba yanzu baza a kaini a matsayin Amarya ba?ke ya isheki Amana tafi gashi duk angwaye sun tafi mijinki ne kadai ya rage a garin nan.
Amana tana cin magani tare da kukan gulma wai dan kar ace batayi kuka ba ta fito har jikin motarsu taje Har khaleed driver yabi wata motar sun tafi cikin kano city,
Alim ne kwal a wajen,key din mota ya mikawa Amana me kuka,a ranta tace wato baima daukeni Amarya ba kenan, karbar key din tayi Alim ya Shiga gaba,ta zauna mazaunin driver ta fara tuki har suka bar garin Amana tukinta takeyi Hawayen karya nata sharara a fuskarta harda shesheka,
Har sukazo airport Amana bata daina kuka ba,Alim yana ta satar kallonta,ga driving ga kuka,frnds tuni suna jirgi ango da Amarya ma shiga jirgi sukayi khaleed ya juya gida da motar,
Amana ana lungu a kujerar jirgi har yau kuka takeyi tare da cewa Ashe tana kaunata,me sonace,Ashe kaunace zunzurutu Na dinga zaginta a banza,Ashe uwata ce nima,
Nima ina kaunarki ta kara fashewa da kuka,Alim bai gane kan zancen Amana ba,
Ashe Amana duk kukan takaici takeyi rannan da taji Mum zatayiwa Alim aure ta kwana tana zaginta kala kala,ashe ma itace amaryar,ashe Mum din Alim tana matukar kaunar Amana tunda har ta iya hada jininta da Na Amana.
Amana tunanin halin Mum ta shigayi yanda take sa Alim yana auri saki,kawai sai Alim ya kara jin kukanta tace shikenan bazanyi lasting ba,bazanyi inganci ba,
Shi dai baya gane me Amana take nufi,masu kula da cikin jirgi sai lallashin Amana sukeyi tunaninsu ko bata da lafiya,
Har suka zo lagos bata sani ba,motocin Alim Jere sun kai bakwai su suka kwashe tawagar ango,har gida wajen Mum dinsa aka rakasu,Har Amana sai wani rufe fuska takeyi saboda kunya
Mum cike da nuna murna da farin ciki Na karya ta tarbi Amana,
Yata kiyi hakuri kinji anyi aure ba tare da amince warkiba Na yaba da halayenki matuka shi yasa naji kwadayin hadaki da Dana,kuma shima Alim ya fada min yana sonki,haka Mum Alim ta dinga shiryawa Amana zancen karya iri iri,har sai da Amana taji ta yarda da Mum,
Su hajiya Talatuwa kawar Mum sun dawo suma,Talatuwa ita kadai tasan dalilin da yasa Mum tasa Alim ya auri Amana,Aabid yana makale a jikin amarya Amana, Mum ce ta sa ma'aikata suka fito da lefen Amana Na gani Na fada har akwati 9 babu abinda babu,wasu ma a Holland Mum ta hadosu,har mota aka shigar da akwatuna,Mum ta kalli Amana tare da kallon ledar da Amana tazo da ita,da wasa da dariya Mum tace wannan kayan fa daughter,Amana murmushi ta saki tare da cewa Umma Na ce ta bani nima ban San mene ba, Mum ce ta karba tare da dubawa kayan gyara Na mata ta gani,ingatattun magunguna,fakar idon Amana tayi ta dalla mata wata uwar harara tare da maka mata banzan kallo,a ranta Mum tace za a mallakemin yarona tsinanniya zaki ga yanda zan mai da rayuwarki,a fili kuwa cewa tayi yata wannan ai sunyi araha da yawa sai su lalata miki mahaifa,ki bari ki zauna yanda Allah yayiki sai mijinki yafi sonki,Amana baiwar Allah to Mum kawai tace,
Bayan sunyi sallar isha Abban Alim ya nemi Alim da Amana yayi nasiha ta gaske sannan yayiwa Alim tasu ta sirri,Asiya ma sai yabon irin kyan Amarya takeyi har sai da Mum ta maketa,
Aabid Alim da Amana haka aka rakasu har mota suka tafi gidan Alim,kowa yana murna da fatan alkhairi banda Mum da kullum cikin kulla sharri take,
Ma'aikatan gidan Alim kaf sun sa ido suga an kawo amarya su ga kalarta su sami abin gulma,sai sukaji shuru kawai Amana suka gani da Aabid da Alim,sai suke tunanin ba yau za a kawo Amarya ba,amma wasu maza daga ma'aikata sunzo da gulmar cewar sunji ance Amana itace matar da Alim ya aura,amma aka karyatasu ba a yarda ba ganin babu wata alama data nuna Amana Amaryace,kuma sunga da safe da ita Alim ya tafi gidan biki,
Amana kuwa suna shiga Palo Alim yace ina ledar hannunki da aka baki a garinku? Mum ce tace Na bata basu da inganci Amana ta fadi,mene a ciki?Alim ya tambaya,hmm nima ban sani ba amma naji Mum tace wai kayan gyaran matane,nan take Alim ya gano wato Mum kwacewa tayi dan kar ma ko ya kusanci Amana yaji wani dadi,
Baki ya tabe tare da cewa ke kuma sai kika tsaya sototo ta karbe ko?gaki da wayo amma kuma baki dashi,sai kiyi tayi ai.ga Aabid karbeshi yayi bacci zanje Na huta
Wanka sukayi gaba daya suka kwanta baccin gajiya Kowanne a dakinsa yake,washe gari dukkansu babu Wanda ya fita,haka sai ga yan aiki sun shugo da lefen Amana gaba daya,Suna zaune sai ga Mum da sassafe tayi sallama a gidan,da sauri Alim yacewa Amana dauki Aabid ki koma dakinki,saida ya tabbatar Amana ta shiga dakinta sannan ya budewa Mum kofa ta shigo tana faman baza ido,ko gaisawa basuyi ba tace ina Amarya,yatsina fuska Alim yayi tare da tabe baki yace Mum pls ki daina hadani da wannan yarinyar bana kaunarta,
Tana can dakinta nifa Mum duk cikin matan da kike aura mun babu wacce Na tsana kamar wannan yarinyar,bana kaunar ganinta Sam,da nasan zakisa Na aureta da bazan taba daukanta aiki a gidana ba,yanzu wlh kin jawo mata masifa da bala'i aiki zata sha ta zama baiwata kawai,.
Wani sanyi da dadi ne ya ziyarci zuciyar Mum,nan take tayiwa Alim sallama driver ya maidata gida,
Wata ajiyar zuciya Alim ya saki tare da kwankwasa dakin Amana ta fito tana fitowa ya sakar mata kayataccen murmushi tare da cewa Amarya yau bazaki hada mana break ba ko hutun Amarcinne,Amana dai kunya ce ta lullubeta,harda nunawa Alim Aabid karfa yajika tare da fadawa kitchen sai Murna takeyi
AsmaBaffa
Ina godiya kwarai readers luv u all,ina ganin sakonninku ta ko ina tnx.
[6/27, 9:25 PM] +234 808 968 1079: ✳CIRANIN AMANA✳
75-80
By
AsmaBaffa
Alim suna ta game da Aabid har Amarya Amana ta gama shirya girke girkenta a dining sannan ta koma dakinta ta shige toilet ta feso wanka tare da cancada kwalliya cikin shigarta ta yau da kullum amma yau ta dabance wani burmemen wando 3qtr red da wata Riga T-shirt karama ko dankwali bata daura ba ta fito,su Alim ta hango a dining tun kafin ta karaso wajen Alim ya mata alama da hannu cewar ta juya ta canja kaya,
Tasan kayan da yake nufi dan haka ta cuno dan bakinta ta juya tana kunkuni ta canja shigar atamfa wata lemon green dinkin Riga da skert sosai tayi mugun kyau ta fito a Amaryarta,yau Amana cewa tayi sai ta daura dankwalinta nan ta fara kici ciki ta kasa kawai sai ta Dora dankwalin kawai a kanta kamar gyale ta fito haka,
Tana zuwa Alim yace ko kefa,zo...zo..da sauri taje wajensa,dankwalin ya zame a kanta,habawa nan yaga zallar baiwar gashi baki sidik yana kamshi da kyalli,
Amana kuwa gabanta sai faduwa yakeyi kasancewar namiji bai taba yi mata haka ba,
Shi kuwa Alim daurin dankwali ya shiga tsantsarawa Amana harda rera wakar barmani choge ....sakarai... bata da wayo,ai Amana dariya ta fara kyalkyalawa,Alim bai taba ganin dariyarta haka ba domin Amana ba komai ne ke bata dariya ba,
Tsayawa yayi har ta gama dariyar sannan ya daura mata daurin zamani kamar ta daura goggoro haka Alim ya Nada mata dauri,da sauri ta shiga bedroom din Alim ta kalli kanta yanda ta zama kamar sarauniya,
Fitowa tayi tare da cewa dan Allah a ina ka koyi dauri haka,ko a mata ban taba ganin wannan kalar ba,ba kin maida kanki namiji ba ta ya zaki San da wannan sakara kawai cewar Alim.tun daga wannan rana Amana ita ba abinda ke birgeta irin ta zauna taga Alim yana nannada mata dauri abin birgeta yakeyi yana bata sha'awa.sabi da haka yasa Amana kullum burinta tasa atamfa ko lace ko shadda ko material tazo wajen Alim tace Daddy ayi min dauri,shiko Alim ya zauna ya tsantsara mata dauri,kuma tayi tayi ya fada mata a ina ya koyi dauri yaki fada mata,
Amana tare da Aabid zaune a kujera tana taje masa gashi,Aabid ne yace Anty ki siyo min icecream gobe idan munje schl,Amana ce ta bige masa baki kar ka sake Na kara ji kace min Anty as from today Na zama your Momy, kunji fa Amana,Aabid kuwa ya rike gam Momy yake ce mata
Yau Amana sauri tayi kafin Alim ya fita Office tayi wanka tasha wani dakakken lace a cikin kayan lefenta ta fito main Palo Alim ma ya sakko cikin shirin sa zai wuce office da sauri tasha gabansa Daddy...Daddyn Aabid pls ayi min dauri,me zakiyi da dauri yanzu ke da Mum ke nemanki,kiyi sauri ki je wlh kafin ki shiga Matsala,cike da shagwabar da bata San ta iya ba tace to Daddy nifa kana gani ko schl banje ba yau saboda Mum tana nemana,kuma nace kamin daurin Na je kaki,kuma ma Allah ni bazan iya Driving ba yau muje ka saukeni a gidan,
Lallai yarinya baki San nufin Mum akanki ba,to ko driving karkiyi ta ganki a motata kinji Na fada miki,muje Jan hannunta yayi har dakinta,tsofaffin kayanta ya duba ya dakko wata doguwar rigar atamfa wacce take karama kuma ta kode ta jeme,yace sa wannan maza,ba musu ta yi hanyar toilet da sauri Alim ya jawota baya yace kut amma kinma raina ni dalla malama sa kayanki anan me zan gani,
Kunya sosai taji haka ta daura zani cikin dabara ta canja kayan,sannan ya dauko wani dark powder sosai ya shafa mata saiga Amana ta dawo baka baka tayi kalar wahala,kowa ya ganta zai rantse a cikin talauci take, oya yi kalar tausayi Na gani Alim ya furta,ai kuwa Amana ta wani langabe kamar Almajira, good ki yi acting ina zaluntarki,ina baki wahala a gaban Mum,karki bari Abba ya ganki a hakan,kuma zamu tafi amma zan saukeki ki hau taxi ta kaiki,duk abinda Mum zatace ki nuna wahala kike sha a hannuna,
Amana to kawai tace tana tausayin kanta haka ta sa hijab har kasa sabo da yan aiki kar su ganta haka,cikin jerin motocin Alim suka fita sun kusa da gidan su Alim aka tsaya,Amana ta cire hijab dinta tare da yafa wani yankwanannen gyale Tsoho kalar talauci,ta fito tare da shiga taxi ta bashi Address din da Alim ya bata,me taxi ya kaita har gidan,
Sunkuyar da kai tayi har sashen Mum,tana shiga palon tayi ido hudu da Mum Alim ana mata tausa,kamar gaske Mum ta mike tsaye tare da rafka salati Yata kece kuwa, haka kika dawo?me ya faru,Alim ne ko?Amana kuwa kawai sai ta fara Kuka wiwi kamar gaske
Tace Mum baya sona,bakiga azabar da yake gana min ba,har marina yakeyi,kuma ko dakina bai taba shiga ba,yanzu kusan aikin gidan kaf ni nakeyinsa,
Ya tsaneni baya kaunata,bauta kawai nakeyi,kayan sawata gaba daya ya kwace har Na lefe,ni dai kice ya sawwake min wlh na gaji,wani dadi da sanyi ne ya lullube Mum Alim,a fili tace ki bari yata zanyi masa magana,wannan ai shirmene,ya zai watsa min kasa a ido,ina zuwa,da sauri Amana ta riko kafafun Mum tana kuka dan Allah Mum karki fada masa, ki rufa min asiri,idan kika fada masa na shiga Uku na lalace,
Mum a ranta tace baki shiga uku ba sai nan gaba,a fili kuwa kan Amana ta shafa tace ina zuwa wani daki ta shiga,Amana ta bita a hankali ta labe a jikin kofar,Mum taji ta fara waya da kawarta tana ta shewa da murna tare da bayyana irin makircin da ta hadawa Amana,da Wanda zata hada mata nan gaba,
Amana ce ta fashe da kukan gaske tana tunanin bala'in daya tunkarota da halin da zata shiga nan gaba,Mum ce taji motsi taji ajikinta Amana ce,da sauri ta katse wayar ta kira Alim tare da sawa a handsfree ta matso jikin kofa wai sabo da Amana taji bakin ciki a ranta tace Son wannan yarinyar me kayi mata haka,gaskiya kaci Amana baka kyauta ba,
Alim kuwa yasan makircin uwarsa kuma ya tabbata wannan nasihar ba tsakani da Allah tayita ba,sabo da haka Alim yace Mum na tsani yarinyar nan,bana kaunarta,bantaba tsanar wani dan Adam a duniyaba kamarta ,kema Mum kin San bazan taba son wannan ballagazar yarinyar ba,kawai biyayya nayi miki,
Amana taji komai da Alim ya fada dama kuma tasan Alim ba sonta yake ba,sai dai batayi tunanin zai ki ta haka ba,duk ta shiga rudu,komawa tayi Palo zuciyarta cike da kunci,Saboda Munafunci Mum driver tasa ya kai Amana gida har tana cewa dama saboda na ga halin da kike ciki yasa na kiraki, godiya tayiwa Mum kawai ta shiga mota,Suna barin gidan ta maida katon hijab dinta.
Fiya fiya fiya Amana ta fada dakinta tare da bugo kofar garam,1pm tayi sallah tare da addua kan Mum da Alim,ta fada kitchen tare da shirya girke girke na alfarma,
Shiryawa tayi a dining,sai ga Aabid ya dawo daga schl yana ta faman kiran Momy am back,wanka tayi masa ta shiryashi cikin kayan islamiyya,sannan ta bashi abinci tare da cewa maza ka huta ka tafi islamiyya,
Wanka ta shiga ta fito tayi shafe shafenta sannan ta bude akwatin lefenta ta zabo wani short wando pink da kadan ya rufe duwawu ya haura cinya,da wata T-shirt karama yellow,ta shirya ta baza gashinta yana sheki da kamshi,ta shafa powder da jambaki pink, tabi jikinta da turare masu matukar kamshi,
Alim kuwa ya Gaza tabuka komai tunani yakeyi me Mum zatayiwa Amana, gida ya dawo direct toilet ya fada ya fara wanka, Amana kuwa tana gama kwalliyarta Palon Alim tazo kunci yayi mata yawa,ji take kamar ta kama da wuta kawai sai Amana ta daddage iya karfinta ta kwalla da karfin gaske tace kinyi........da....yar....Halak.....ni......Amana.....Sulemanu.......Harka.......sai........Alim ne ya fito daure da towel jikinsa duk kumfa saboda magana cikin kara da yaji Wanda baya gane me akace,
Ido hudu Alim yayi da Amana wacce ta dau wankan sugar ta takarkare ta bude dan mitsitsin bakinta tana ganin Alim ta karasa maganarta a hankali da Ni....Amana... Sulemanu...Harka....Allah sai nayi mata biyayya....ina son....Surukata,kunji karyar Amana da wata mummunar kalma zata fada ganin Alim ta canja salo.
Tsaki Alim yaja ya koma ciki tare da rufo kofarsa,
Tana zaune ya fito yana kamshi cikin 3qtr da singlet fara,dining ya nufa da Sauri ta mike taje wajen, cike da shagwaba tace to basai ka tsaya nazo na zuba ma ba,Sabon iskancin da kikazo dashi kenan yau,Alim ya furta
Shuru Amana tayi Ta zuba masa abincin,sannan ta mike da niyar barin wajen,muryarsa me sanyi taji me Mum tace miki dazu zo ki fadamin,wata harara Amana ta watsa masa sannan ta karaso tana turo dan bakinta,ni kike harara? Wani wal ta karayi da idonta sannan tace ba dole na harareka ba kafi kowa sani and u are asking me,what do u want me to tell u to,
Ok marar kunya zageni yanzu fa ni mijinki ne Dole ki min biyayya,au to wacce rashin biyayya nake maka,duk biyayyar da nakeyi baka gani? A hakan kike wata biyayya,yes mana Kai ka sanni ka tuno lokacin da mukahadu a wajen yan fashi da suka taremu,a lokacin zan iya cin kwalarka na balla ma kafa,
Kuma da ace bana ma biyayya da abinda naji Mum dinka ta fada da kuma yanda kace mata a waya to da muna haduwa sai na ragargaza ma hakarkari,
Amma kawai sabo da yanzu ka zama mijina shi yasa kuma da darajar Aabid kar na illata Daddynsa amma ai da tun ranar danazo gidan nan zan kaddamar maka,
Murmushi Alim yayi tare da cewa ke ganinki zaki iya ballani to ko dan yatsa na baki isa kin lankwasa ba,baki San karfin maza ba naga Alama amma zan nuna miki,
Amana juyi tayi Hmm kai mufa mun San what man can do woman can do better,Allah ko?to mu gwada mu gani cewar Alim.da ya daina cin abinci ya mike tsaye tare da tube singlet dinsa yace in kin isa tube haka mu gani a gabana,miki miki Amana tayi,yace sannan idan har da gaskene what man can do woman can do muje toilet kiyi min fitsari a cikin kwalaba ba tare da wani ya zubo kasa ba,
Nan ma shuru Amana tayi,hannunta ya kamo karo na farko kenan,wani shock mar mar sukaji a jininsu tare da zirrr a kwakwalkwarsu, idan kin isa kwace mugani,Amana ta fara kici kici amma ta kasa, wuyanta ya damka ya shaketa kadan,yace taimaki kanki ki kwace na gani,Amana ido ya firfito tana ta kakarin amai saida ya gaji sannan ya saketa,sai murza wuyanta takeyi tana karari da tari,da kyar tace ai zan iya kwacewar kawai dan kaci abinci ne ni kuma banci komai ba,
Murmushi Alim ya saki Wanda yasa dimple dinsa dinsa lotsawa gaba daya,Amana tana tsaye ta faki idon Alim saida ta bari ya sakankance ta zagaya ta bayansa tare da shako wuyansa ta matse Kansa a kirjinsa wai so takeyi ta masa mugunta,shi kuwa Alim ji yayi ta tallafo kansa,laushin na shanunta da yaji a kansa da wuyansa shi yasa ya wani lumshe sexy eye dinsa,tare da tsotsar pink lips dinsa,Amana tunaninta zafi yaji sai kara kankame Wuyan Alim da kansa a kirjinta takeyi, ta kai 20mins a haka sannan ta dago kansa sai taga Alim ma bacci ya fara yi abinsa,zamewa tayi Wanda yayi sanadin budewar idon Alim yayi ja da gani baccine cike a idonsa.
9pm Aabid yayi baccinsa Amana tayi wanka cikin kayan baccinta na lefe sai da ts zabo wata a can kasan akwati wata yar riga fara kar iyakarta cinya me laushi,hannunta karami dashi,turaren jikin da kawarta Rufaida ta bata shi ta shafa sama sama ta sa rigarta,ta kara fesa wani turaren sannan ta kwanta,
Tayi adduar baccinta ta fara bacci amma abin mamaki tunda tasa rigar takeji wani azababben kaikayi na fitar hankali,har yan kuraje kana na suka fito mata,tun tana Susa har ta fara kuka sosai.
Cikin dare Alim yaji kuka da ihun Amana,ta hanashi bacci, fitowa yayi da Sauri ya nufi dakinta,a kasan tiles ya hangota tana ta shure shure da tirje tirje hade da soshe shoshen jikinta,ga kuka kuma tare da ihu.
Hannunta ya kama ke lfy wai burinki kullum ki takurawa mutane,Idan kika dameni part din yan aiki zaki koma.
Ba tare da ta bude ido ba ta fara Susa jikinta tana borin jini borin jini nakeyi, mikewa zaune tayi tare da makale Alim ka Sosa min dan Allah, Alim dubawa bed yayi ya hango Aabid yana ta bacci,daukan Amana yayi cak har bedroom dinsa ya kwantar da ita a bed dinsa, sannan ya fara cirewa Amana kayan jikinta,sai ci gaba takeyi da soshe soshenta ba kakkautawa,ga kuka hade da zullo duk ita kadai take ta faman yi.
AsmaBaffa
Godiya dubu gereku masoyana,ina ganin sakonni ta ko ina .
[6/30, 8:55 PM] 0mmer Farouk: ✳CIRANIN AMANA✳
85-90
By
AsmaBaffa
Tunda Amana ta shige blanket dinsa duk ya rude,ya Shiga wani hali,ya rasa dalilin da yasa yake jin haka a tare da ita Wanda bai taba jin makamancinsa a wajen duk matan da Mum ta aura masa ba,jinta yake a jininsa har bargonsa ganinta yake ita ta daban ce, a hankali Amana ta yi magana Daddynmu pls ka fahimceni wlh kazafi sukayi min ban aikata hakan ba,kasan halina kasan me zan iya aikatawa,muje schl din gobe ka tambaya kaji me ke tafiya,
Tunda Amana ta fara magana kamar tana masa rada a kunne gaba daya hankalinsa ya fara susucewa,hankalinsa ya tashi,gashi sai kara matsowa jikinsa takeyi,
Hannunsa ta rike kaji Daddyn Aabid,wani xirrrrrrr Alim yaji nan take bari jikinsa ya fara sosai,
Amana ta zata ko zazzabi ne ya kama Alim,da sauri ta sakeshi Yaya Alim zazzabi ya kamaka,Amana ita bata San kan komai ba ta dami Alim sai yasha maganin zazzabi,da kyar yaja numfashinsa yace ba...zazzzab..bi..nakeyi ba, gashi jikinka yana rawa,kirjinsa ta taba ta ji temp dinsa,ai da sauri Alim yace wayyo Allah shiiiiiiiii.....tsorata Amana tayi tace jikin ne sannu kaji ko kashinka na kirjj ya goce ne?bari na hada ma tea fuskarta dauke da damuwa,
Yunkurawa tayi da niyyar tashi taji ya riketa gam tare da fadin ina zakije muyi baccinmu kinji,Daddy to bari na kawo ma tea,no ki barshi kawai mu kwanta,to my Boy kar ya farka yaga bana nan zaiyi kuka fadin Amana,ba abinda zai sameshi,kuma Aabid ai baya farkawa ko ya farka bashi da tsoro kawai ki kwanta a nan yau,
Amana ba haka ta so ba amma bata son jayayya dashi kawai sai ta kwanta
Kamar jira yakeyi jikinsa na rawa ya matso jikinta,Amana ta tsorata zuciyarta kawai bugawa takeyi jikinta sai Mazarin tsoro yake,A hankali ya manneta a jikinsa ajiyar zuciya ya saki,tudun mazaunanta na kan sandar girmansa kasancewar ta baya ya rungumota
Rigarta ya kama ya rada mata a kunne in cire miki wannan? Kai ta girgiza masa a'a bana so,shuru yayi tare da fara shafa kafafunta zuwa cinyarta da tasa cinyar,wuyanta ya taba dai dai kashinta tare da lasar kasan kunnenta,cikin sanyin murya yace wannan kashin wuyan naki saura kadan ya cike ranar dana fara ganinki yafi haka,
Ita dai Amana duk a takure take,cike da tsoro tace ae yanzu ai kaga ina gidanka ina cin mai kyau,inci kaji da yohourt,murmushinsa me tsada ya saki,yatsanta na tsakiya na hannun dama ya sa abakinsa yana ta tsotsa Amana a zuciyarta tace kodai maye ne wannan?shi kuwa lasarta ya fara tare da shafa wuyanta a hankali yace ina sarkarki ta rannan wata siririya tana miki kyau,Amana tace ai bana kwana da sarka ko dankunne,gashinta yaci gaba da shafawa yana kullum gashinki kamshi dame kike wankewa,Amana ta fara gajiya da wannan tambaya ta Alim,A gajiye tace shampoo na,
Damammen cikinta ya shafa a kunne ya rada mata cikinki me kyau ko kina gym? Amana ta gaji da tambaya cike da shagwabar da bata San ta iya ba ta furta wai kai Daddyn nan komai sai ka tambaya dan Allah?
Hannunsa na a kan wajen wuyanta yana shafawa yayi kasa wajen kirjinta yana hadowa yana shafo dukiyar fulaninta da suke a ciki,Amana wannan lokacin feeling wani abu ta fara kamar dadi dadi,har wani lumshe ido takeyi idan ya shafo gefen na shanunta sai taji dama ya shafosu duka,
Ta rasa gane mene wannan ke damunta,shi kuwa malamin nata a yanzu wa wuce gefen na shanunta amma baya kaiwa ciki,Amana a fili ta furta a'a ni wai lafiyata kuwa,Alim yayi nisa tsabar santi sai yaji kamar Amana tace ni ayi lafiya,
Tnx dear yaci gaba
Sai wani mika takeyi tana kara mannuwa da jikin Alim,har nishi nishi takeyi kadan,Alim ne ya juyota suna facing din juna tare da tambayar ko na cire miki rigar ga hadarine ma a garin kyafi jin dadin bacci,Amana tana tsoro amma taji tana so ya Murzata ta Riga ta fara nisa itama,
Cike da kunya ta daga mishi kai kawai alamar ae,tana sunne kai tare da rufe idonta kam,
A hankali kamar me tafiyar tsutsa ya cire mata yar fingilar rigar baccinta,ba vest ba bra a jikinta pant ne kawai,
Alim nan ya fara murtsika dukiyar fulaninta masu matukar kyau da laushi hadi da sulbi,magana yaci gaba da yi suna da kyau abubuwan naki ga taushi ko na dan sha miki?da kyar Amana ta iya furta a'a ni dai ban iya haka ba.
Haka ranar ma Alim ya murji Amana yanda yakeso da salon sa lips dinta kuwa kamar zai cire mata su sosai sukayi jajir dasu,Hakan ma bai gaji ba dan Amana taga ya haukace mata ne ta tsorata shi yasa ta fashe masa da kuka,har yanzu Amana ta hanasu bacci kuka takeyi kamar yayi mata wani abu,
Tun yana lallashi ya gaji yace ke ki rufemin baki kamar na yankaki in kika dameni zan yi babban ma yanzu,sai kace kema bakya jin dadin kinfini jin dadin ma,dan mitsitsin bakin ta turo cike da shagwaba Allah ni bana wani jin dadi,haka kikace ko? Ae din abinda dole kake takura min cewar Amana,murmushi Alim ya saki zakiyi bayani zan kamaki,
Uhm naji idan ka kamani kar ka barni da rai ma Amana ta fadi tana fari da ido,dariya Alim yayi sosai yace ok akwai ranar bayani,
Gashinsa ta fara cukwikuya masa tana yamutsashi Daddyn Aabid wai balarabe ne kai? Shuru yayi mata,to wai kai ko dan India ne kuka dawo kasar nan?nan ma shuru yayi,tace watakil ma bature ne kai,Aabid dina yafi kama da Bature,
Cikin Muryar bacci a hankali Alim yace ki daina fada min Daddy yarona dani zakina cemin Daddy da girmanki yaushe na isa na haifi kamarki,
To dama ai dan Aabid ya koya sosai nake fada ma Daddy,amma haka kawai yaushe zan mai da miji uba,
Daddy dafa da nazo gidan nan baka magana sanda muke haduwa a gari kuwa kafi kurma kurmanta ya ,pls kiyi bacci Amana kin dameni,dama kina da surutu haka?
A'a banidashi dan kawai kayi hakuri akan an koreni daga schl ka nemo min wata naci gaba da karatuna shi yasa fa nake ta ma surkulen surutuna,
Dariya Alim ya shigayi tare da fadin kin tonawa kanki asiri ai kuma,naji to kwanta kiyi bacci gobe zamuje schl din ni dama nasan haka banza baza ki bar Aabid ki shigo blanket dina ba,
Wlh kamar ka sani nafi fa son Aabid akan ka,
Da haka bacci ya kwashesu makale da juna,da asuba sukayi Sallah suka sake komawa bacci,Amana ta Riga tashi taje ta hada breakfast lafiyayye sannan ta shirya Aabid itama shirin tayi cikin wata doguwar Riga readymade black me duwatsu Golden,yanzu ta fara sabawa da kayan hausawa har acuci tayi tare da yafa gyale golden takalmi me tsini tasa Golden da Jakarta same color,sai kamshi take zubawa ta fito rike da hannun Aabid ka rantse danta ne,
Sun fara cin abincinsu Kenan kamshin Alim yayi musu sallama,sanye yake cikin wata T-shirt ruwan toka,sai wando pencil ruwan kasa,pcap dinsa ma ruwan toka haka ma takalminsa me tsadar gaske same color,
Wata siririyar sarkar azurfa ta maza ce karama makale a wuyansa, ba karamin kyau yayi baa,tunda ya fito Amana take kallonsa, ta kasa dauke idonta,
Agogon Gucci me tsadar gaske dake hannunsa ya kalla 7am dai dai,
Amana Ce ta kalli Aabid tare da zabga masa harara,Aabid Wanda ya Riga da yasan me Momy Amana take nufi,da Sauri ya furta Daddy ina kwana,
Fuska sake Alim ya Amsa masa,bayan sun gama komai Amana ta mika masa kanta Daddy daura min dankwali,ba tare da ya kalleta ba yace ban iya ba ki dage ki koya da kanki,pls Daddy ka dankwalin ta rike a hannu tare da yafa gyalenta kawai tace muje,Amana kwas kwas take tafiya da takalminta me tsini kamar zata fadi kasancewar bata saba da shi ba,suna compound takalminta ya gurde saura kadan ta fadi Alim ya riko hannunta da karfi ta fada kirjinsa suna shakar kamshin juna,Aabid har ya kai jikin mota,Wai wai Allah ya taimakeni da tuni naci kasa fadin Amana,rankwashinta yayi a kai ai u r too stubborn,kara ta saki tare da kura masa ido kasanfa da zafi Amana ta furta,ke da kike namiji mace me kamar maza kwari ne babu,to idan ni namiji ce kenan kai dan gay ne tunda kana eh yane dani,
Karki kara dangantani da gay uban me nakeyi dake abinda dan Dane kawai nakeyi sai kuka da kike damun mutum dashi,dariya Amana tayi ai Kaine Allah danma mijina na ne kai nake kyaleka amma sai ka dinga sawa ina jin wani abu da ban taba sani ba,kuma ka dawo kamar damisa na Neman nama ni wlh tsoro kake bani,dan dai kawai Baba yace nama biyayya ne,kasan me Baba yace?girgiza mata kai Alim yayi alamar A'a.
Dariya ta karayi hmm waifa cewa yayi kar na sake na koma gidansa idan nayi yaji,kuma ko an sakeni na nemi wani gidan ba nasa ba,jiba dan Allah mutum da gidansu,idan Mum dinka watarana ta koreni dole na koma can ko?
Tunda take surutunta a compound Alim yake kallon Amana sama da kasa cike da shauki,ga wani kyau da tayi masa,a hankali ya furta ki daina tunanin zata koreki,ai ni nake aurenki,ki tabbatar duk abinda kika gani ko kika ji kin fada min,saboda a dau mataki,hannunta ya rike hade da murzawa muje ko,
Duk abinda su Alim keyi a compound Saude na kallonsu ta bangaren yan aiki.a fili Saude ta furta kamar a kunnen Hajiya,cikin jerin motocin Alim sun kai goma suka shiga cikin schl din,sai kallonsu akeyi har office din pc,.
PC jiki na rawa ya gaisa dasu Alim,takadar ya mikawa pc wacce ya kori Amana, cike da izza ya furta yimin bayani kan wannan,
Jikin PC na mazari ya kwashe yanda sukayi da Mum ya fada masa, tunda Alim yaji Mum ce ya cika da mamaki,kawai sai ya ce Aabid yaje class sannan yaja hannun Amana suka bar schl din,wata makarantar Alim ya saka Amana suka bata ss2 sannan suka dawo gida,
Amana zaune a Palo ta zuba tagumi sai tunani takeyi kan me tayiwa surukarta ta tsaneta haka,Alim ne ya fito sanye da short wando da singlet ya iske Amana zaune ta zuba tagumi,karasawa wajenta yayi tare da janye hannayenta yan mata me ya faru,jiki ba kwari Amana tace ba komai idonta ya ciko da kwalla,habarta Alim ya tallabo gashi kamar zakiyi kuka meke damunki? Kuka ne ya kwace mata ta fada jikin Alim tare da kankameshi tana ta kuka,tausayinta ya kama Alim ya shiga shafa gashinta yana dan jijjiga bayanta kamar jaririya,sai da tayi me isarta sannan ta share hawayenta ta mike zaune,hada ido suka hada da Alim sai kuwa Amana ta kyalkyale da dariya ta kara fadawa jikinsa ta boye fuskarta a kirjinsa,
Dago fuskarta yayi tare da kura mata ido wani sabon hawaye ya gani a fuskarta ya gangaro kadan,a hankali Alim yace fada min lfy me ya faru?
Da kyar ta iya furta shike nan na kusa zama bazawara,Mum zata sa ka sakeni ni an lalata min rayuwa ta na zama bazarawa,Alim ne ya kalleta to mene bayan ma ko rayuwar aure bamuyi ba,idaan ma mun rabu wani zaki aura ki manta dani,idon Amana jajir tace to ai kuma shike nan ni bazawara ce kuma sai dai na auri Tsoho me mata,
Murmushi Alim ya saki ai wasu matan sun fi son Tsohon ma,baki Amana ta tabe cike da shagwaba tace taoho me ciki katoto ina zansa rumbun cikinsa,gashi da matarsa yafi son uwar gidansa,ke da kike kyakyawa cewar Alim,kyan banza har wani kyaune dani,komai kyanka maza su ina ruwansu,ci ma mutunci zasuyi wasu har da duka,ai kuwa wlh Daddy ko indai miji ya min ba dai dai ba na masa warning yaki jiki to inba sai na fasa masa kai da tabarya,in samu in karya masa wuya,matarsa ta zaneki ai cewar Alim,mikewa tsaye Amana tayi kut..ai kuwa wllh da sai na cire mata hanci,kasan karfi na kuwa?
Alim ya girgiza kai taya zan sani tunda bamu taba dambe ba,to kaja bakinka ka tsuke mutumina dan kar na gwada a kanka,dariya Alim yayi waye mutumin naki kai mana,yawwa dan Allah dan yimin Sandar rake kaji Daddyn Aabid,mene kuma sandar rake? Alim ya tambaya,a kafada zaka sabani kamar ka dauki jaririya kana zagawa sai kace Sandar rake sai nace Azo a siya,oya tashi muyi ta janyo hannun Alim sai kawai ya mike tsaye,Amana ta zata karfinta ne ya mikar da Alim tsaye ta kalleshi tana tsalle kamar zata buga ball ka gani ba ka gani ko ai na fada ma karfi gareni if not taya zan iya mikar dakai tsaye.
Cak Alim ya saba ta a kafada cikin sigar shagwaba tace Daddy to kace sandar rake,Alim baiyi magana ba da kyar ya iya furta ina zan kaiki?muje bedroom dina,har kan bed dinta Alim ya jefa ta dakin yabi da kallo ko ina tsab tsab gwanin sha'awa kwanciya yayi kusa da ita cike da shauki ya jawota jikinshi,a tsorace ta ja baya tana ya Alim muje sweeming pool,janshi tayi har pool ta famjama cikin ruwa,tayi tayi ya shigo amma yaki,yana bakin wajen a zaune daga shi sai short,