GABATARWA*
Wani ɓangare na labarin nan ya faru ɗa gaske, sai dai an ƙara da wasu abubuwan dan ilmantarwa da nishaɗi. Labarin na iyalai uku three family.
NAMRA FAMILY.
DR. HILAL FAMILY.
KALSOOM FAMILY.
Sunan Novel ɗin *ZAGON ƘASA*
Green snake under green grass, people with two colors. A tension, Schemed Novel of slut.
Witness to regret.
Witness to love.
Witness to tears.
Witness to drunken.
Witness to revenge
*MEANING OF THE NAMES*
NAMRA - Delicious water
UZAIR - Name of a prophet
HILAL - Crescent
KALSOOM - Name of Prophet Muhammad (pbuh) daughter
EZZAH - A person who give the honor, respect
RASHIDA - Intelligent sober
IFHAN - Respectful, nice, precious
RAFEEK - Friend
YASMEEN - Flower
ABDULLAHI - Servant of Allah
ASIM - Person who keep away from sins.
*SADAUKARWA*
Na sadaukarda wannan littafin ga (Daughter) RASHIDA ABDULLAHI KARDAM kin cancanci fiye da haka a gareni
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandycom.ng for your updated.
FIRST FAMILY...
*1.......* Ƙarfe biyar da minti arba'in da takwas na yamma, ta faka Motarta a parking space, ajiyar zuciya ta sauke ya fi sau uku, sannan ta kalli takardun da ke gefenta kamar mai tunani, daga bisani ta kai hannu ta ɗauka, ta buɗe motar ta fito.
Jiki a sanyaye ta nufi harabar gidan, gurin da Mahaifinta yake zaune yana shan iska, daman a al'adarsa ya kan zauna a habarar gidan da yamma, wani sa'in ya kan duba jaridu wani lokacin kuma ya leƙa yanar gizo, dan sanin me duniya take ciki.
Da kamar fargaba Namra ta doshi gurin da yake, zuciyarta na raya mata abubuwa da dama.
talkamin ƙafarta ta fara cirewa tun kamin ta ƙasara kusa da carpet ɗin da aka saba shimfaɗa masa, sallama ce ta fito bakinta kanta na ƙasa kamar mai jin nauyin kallonsa.
“Assalamu Alaikum”
Bai amsa sallamar ba, sai dai ko kaɗan hakan bai bata mamaki ba, daman bata tsammaci zai amsa mata ba, sai kawai ta ɗora da gaisuwa.
“Abban sannu da hutawa ya aikin?”
Ya yi jinkirin amsa mata na daƙiƙon da zai kai ashiri zuwa ashirin da biyar, sannan ya amsa mata can ƙasan maƙoshinsa
“Al-hamdulillah”
Bata yarda wata kalmar ta ƙara fito daga bakinta ba, sai kawai ta tashi jiki ba ƙwari ta saka takalminta, ta nufi hanyar da zata sadata da part ɗin Mahaifiyarta.
Sai da ta share hawayen da suka zubo mata kamin ta kai hannu ta murɗa ƙofar falon ta shiga. Babu kowa a parlor sai air conditioner dake ta aikinsa, Kai tsaye ɗakinta ta wuce zuciyarta cike da rauni.
Saman gadonta ta zauna ta lumshe ido tana sauraren bugun zuciyarta, kalaman da Mahaifinta ya yi mata ɗazu da safe suƙa riƙa dawo mata, irin yadda ya riƙa aibanta ta, yasa ta ta yi saurin dafe kanta, sai kuma ta fashe da kuka tana murza zoben dake hannunta.
Haka ta zauna a ɗakin bata fito ba har sai da aka yi sallah Magariba, bayan ta yi sallar ta fito ta nufo parlor fuskarta babu yabo babu fallasa.
Duk ƙannenta suna zaune parlor suna kallon Dadin kowa, babu wanda ya lura da fitowarta sai Mahaifiyarta. can nesa da Mahaifiyarta ta zauna tana gaisheta.
“Anty barka da dare”
Bata amsa mata ba, sai kallonta take tana karantar irin halin da ƴarta take ciki.
“Tunda kika dawo daga makaranta Namra kina cikin ɗakin, so kike yi damuwa ta yi miki yawa ko? Yau ranar girkina ce amman saboda ke Abbanku bai leƙo nan ba, na shiga sashensa na rasa gane kansa, so kike ki kashe min aure ko Namra? kin fi son ki rayu da son zuciyarki fiye da farincikin iyayenki? bana ƙin zaɓin ki Namra, amman tun da mahaifinki ba ya so barin shi ya fi alheri”
Matsewa ta yi cikin kujerar tana wani irin kuka da ba zata iya fitarwa ba.
Sai yaushe Abbah ta zai fahimci halin da take ciki ne, sai yaushe zai tausayawa rayuwarta? ji take idan har ta yarda ta rabu da Asim zata iya mutuwa, bata jin zata iya rayuwa da wani Namji da ba Asim ba, kuma idan har bata aureshi ba, ta san Allah ba zai yafe mata ba, mutane zasu masa dariya, daman an daɗe ana masa kirarin ita ɗin ba sa'arsa bace, ta san irin son da Asim yake mata, ta ya zata iya sanar da shi ba zata aurensa ba? Yayyu ta Mata da Maza Tara Mahaifinta ya aurar, duk kuma a cikinsu babu wanda ya yi ma zaɓin miji ko matar aure sai ita.
Sallamar Barrister Yasmin da Mijinta ne, ya ankarar da ita ta yi saurin share hawayenta, tana gyara fuskarta dan kar su gane ta yi kuka.
Anty Amarya ce ta amsa musu fuska a sake kamar yadda ta saba tarbonsu.
“Maraba maraba da Lauyoyi, cikin daren nan ake tafe”
Yasmin ta zauna a kujerar da Anty Amarya take zaune, yayin da Uzair ya zauna a kujerar da ke kusa da ƙofa, idonsa na kan Namra wace ta banye ɗaurin ɗankwalinta tana ƙoƙarin magana da matarsa.
“Anty Barrister ina Afnan?”
“Yanzu na biyo uban daren nan na miƙe hanya ki rasa wanda zaki tambaya sai Afnan? amman yarinyar nan akwai ki da rainin hamkali”
Kusa da ita Namra ta dawo ta zauna tana faɗin
“Kaji Anty da wata magana, toh ai ita ce Ƴata dan haka ni ita zan tambaya”
“Idan kina son ganinta kawai ki je gidan Gwaggo ki ganta, amman indai tambaya zaki yi, ki riƙa cewa ya na ke ni da Mijina”
“O'oh masu miji manya, toh ni ban ga mijin na ki ba ai”
“Ni ai na ganki”
Uzair ya amsa daga inda yake zaune yana kallon ƙugunta zuwa saman ƙirjinta.
“Jar uban nan, ka ji min wata magana! saboda ke fa muka biyo ta nan amman zaki wani ce baki ganshi ba”
Duk suka sa dariya Maryam ta ce
“Toh mijin na ki ai tsoron mutane yake shiyasa ya maƙure gurin kamar wani ɗan fashi”
Anty Amarya ta kai mata dudu
“Wai dan kun ga baya magana shiyasa kuka raina shi ko?”
Dariyar suka sake yi, sannan Anty Amarya ta shiga tambayar Barrister ya aiki. Namra kuma ta nufi hanyar kitchen dan ta ɗauko musu ruwa, tun da ta tashi Uzair ya bi bayanta da kallo har ta shige kitchen ɗin.
Bayan sun sha ruwan ne Barrister ta ce
“Anty Mun zo aron Namra ne, Uzair zai yi ɓaƙi daga Abunja,kuma yana son ayi musu wainar kaza kinsan Namra ce ta iya shiyasa muka zo mu faɗa miki”
“Aa ni ba ruwana ga ku ga Namra”
Cewar Anty Amarya tana kallon Namra da ta ɗan ɓata fuska kaɗan, dan sam yanzu bata son zuwa gidan Yasmin, Hakan kuma ya samo asali ne tun lokacin da Uzair ya soma nuna mata maitarsa a fili.
“Kai gaskiya na so nayi tilawar haddata, dan Saturday nan ne walimar mu fa”
Yasmin ta ɗan zungureta
“Ke uwar kuiya, just for one day ne fa zaki mana, ai yau Wednesday, zaki iya yi Friday”
“Haba kije mana idan kin gama musu da wuri ma ai zaki iya dawowa”
Anty Amarya tasa baki. Yasmin ta ce
“Kuma ni kin ga fita zan yi ba gida zan wuni ba, ina da cases har huɗu ƙila sai yamma zan dawo balle ki ce zan dame ki da surutu, Uzair kuma sai biyar yake dawowa, ke kaɗai ma za'a bari a gidan”
Ta amince ba dan ta so ba, sai dan babu yadda zata yi, indan har ta ce ba zata je ba, Yasmin zata zargeta, Anty Amarya kuma zata mata faɗa, sa'arta ɗaya gobe ba su da lacca.
ba su wani daɗe sosai ba, suka yi ma Anty Amarya sallama suka fice. Har gurin Mota Namra ta rakasu, Yasmin na laƙame da kafaɗarta tana mata tambihi game da haƙuri, dan ta fi ƙowa sanin halin da Namra take ciki, kasancewar shaƙuwarsu, Namra bata ɓoye mata ƙomai.
Bayan sun wuce ne ta dawo jiki a sanyaye ta shigo parlor.
“Ni wallahi bana son zuwa gidan Anty Yasmin”
Ta faɗa tana ƙoƙarin zaunawa saman kujera. Maryam ta kalleta ta ce
“Saboda me?”
Kamar zata ce wani abu sai kuma ta yi shiru ta kalli tv.
“Tashi kije ki ci abinci”
“Bana jin yunwa”
“Ai gaki nan, duk kin bi ki koɗe sai fama kike da rama kamar wata marar lafiya”
“Wallahi Allah bana jin yunwa Anty”
“Ta ya zaki ji yunwa kin ɗauki damuwa kin sawa ranki, Allah ya sauwaƙe miki wannan rayuwa”
Shiru ta yi ba tare da ta ce komai ba, dan ta dan duk yadda zata yi ma mahaifiyarta bayani, ba ganewa zata yi ba.
Annur ne ya shigo ya tsaya daga bakin ƙofa hannunsa riƙe da lemu ya ce
“AntyAmarya wai Abbah ya ce ki zo tare da Anty Namra”
Gabamsu ya faɗi dukansu, bama kamar Namra data ja wani dogon numfashi ta sauke, kamin ta kalli Mahaifiyarta. Ba tare da ɓata lokaci ba suka tashi suka nufi part ɗinsa, kishingiɗe suka tararda shi, kofin tea na gefensa yana sanye da madubi fuskarsa babu annuri yana duba wasu documents.
Namra ta zauna ƙasa cikin ladabi, Anty Amarya kuma ta zauna saman kujera tana faɗin
“Annur ya ce kana kiran mu!”
Bai ce uffan ba, har sai da ya ƙare duba takardun da yake sannan ya cire gilashin idonsa, ya kalli Namra babu alamun wasa a tare da shi ya ce
“Kin san Alhaji Madu Sanusi?”
“Eh”
Ta amsa ƙasa-ƙasa gabanta na ɗan faɗuwa, aikan ta san Alhaji Madu akan farin sani, mutumen da kwana biyu, uku yana gidansu, aminin mahaifinta.
“Shekaran jiya ya yi min magana akan ki, saboda yana son ƙara aure dan ki zame masa first lady tunda sauran matansa basa jin turanci, kuma a takarar da yake akwai buƙatar ya auri mace ƴar boko, mun gama magana da shi gobe da dare zai zo ku gaisa”
Tun da ya soma maganar hawaye ke zuba a idonta har ya ƙare, daker ta iya amsawa da
“Allah ya kai mu”
Anty Amarya ta amsa da “Amin” Tana sauke ajiyar zuciya, sam bata jindaɗin yadda Abbah yake yi ma ƴarta sai dai babu yadda zata yi, ko magana ta yi cewa yake ita ke ɗaure mata gindi tana yadda take so.
Cikin sauri Namra ta taso, ta baro falon zuciyarta cike da zulumi, tana tsaron abunda zai je ya dawo, ta rasa ƙwaƙwaran dalilin da ya saka Mahaifinta ba ya son tarayyarta da Asim.
Har ta shigo ɗakinta kalmar Alhaji Madu ce take mata yawo a kunne, saman gado ta kwanta hawaye na bin fuskarta, sai ta kai hannu ta janyo wayarta, gallery ta shiga ta kamo hoton Asim tana kallo.
“Miyasa Ƙaddarata zata min haka? kin san ba zaki barni na yi soyayyah da shi cikin kwanciyar hankali ba kuma kika haɗa mu? kinsan ba zan auresa kuma kika sa na sansa, Allah kayi min mafita karka ka bar ni da kaina”
Rumgume wayarta ta yi sosai tana kuka da tuna kalaman daya faɗa mata yau a makaranta.
‘Ina son ki sosai Namra duk da jikina yana bani lallai ba zaki aure ni, saboda ni da ke ba ɗaya ba Namra, ga shi mahaifinki baya son na, Mahaifiyata tana yawan faɗa min wai zaki ɓata min lokaci ne kawai ba zaki aure ni ba, Namra ina gudun ranar da zan wayi gari kin zama matar wani magauta suyi min dariya...’
Kuka take sosai har da karkarwa, tana matsar idonta da buga ƙafafunta.
**********
Manjo Usman Zamau tsohon soja ne, mai mata biyu Hajiya Barau wanda ake kira da Mama da kuma Hajiya Larai wanda ake kira da Anty Amarya. Gidan Alhaji Usman babban gida ne mai ɗauke da part uku, part ɗin uwargidan sa da kuma na Amaryarsa sai nasa.
Uwargidansa na da ƴaƴa tara hudu mata biyar maza kuma dukansu sun yi aure, wasu suna tare da ita wasu kuma aure ya kai su nesa, a yanzu bata da ɗa ko ɗaya a gidan sai jikoki da ƴaƴan ƴan'uwa.
Anty Amarya ce aka auro daga baya, ita ce mai yara huɗu dukansu mata, Namra ce babba sai Maryam dake binta da kuma Hindatu da Aisha. cikakkancen sunan Namra shine Khadija mahaifiyarta ta kan mata Alkunya da Namra ne kasancewarta ita ta fari gareta. Namra na 100l a jami'ah ta haɗu da Asin, suka ƙula soyayyar da babu wanda ya sani har suka kai 300l, sai a yanzu ne abun ya zame musu matsala kasancewar Asim ba ɗan kowa bane face talaka mai neman abunda zai sa a bakinsa.
Ita kuma ƴar masu arziki ce musamman yanzu da Mahaifinta yake takarar Senator, daman can mutun ne mai abun hannunsa dan yana da kamfanoni da dama ciki da wajen ƙasar nan.
A duk familynsu da shi suke tinƙaho dan Allah ya yi masa rufin asiri ta ko ina.
Gashi shi ƙaɗai mahaifiyarsa ta haifa a duniya, a duk familynsu ya fi shaƙuwa da Mahaifiyar Yasmin da Kuma Mahaifiyar Uzair kasancewar kakanninsu guda, kuma yana ganinsu mata, yana tausayinsu sosai.
WANNAN KENAN
*********
SECOND FAMILY...
Tun da ta dawo daga aiki take cikin damuwa, abun duniya ya fara isarta komai ya taru ya yi mata katutu a rai, kullum ta fita ta dawo sai anyi da ita a unguwa, ƙawayenta su zolayeta familynsu ayi ta tambaya, kamar ita ta ɗorawa kanta rashin aure.
Kallon kanta take ta madubi tana hawaye, ta ko'ina Allah ya yi mata sura, mace ce abunda ake cewa mace, amman babu mai neman aurenta sai mutanen banza, duk acikin manemanta babu na ƙwarai da zata ware da sunan wanda zata aura, duk wanda ta yi ma maganar aure ba zai sake dawowa ba, sai dai su nuna suna son jikinta.
Sa'aninta duk sun yi aure, sun barta sai kace wanda ta zagi maza, tun tana sa ran idan ta gama karatu ta samu wanda zata aura yanzu ga shi har ta gama ta samu aiki amman ba shiru, ada abun ba ya damun iyayenta amman yanzu ya zame tunaninsu, suna addu'ah amman kamar basa yi, sun aurar da ƙannenta biyu mata ita shiru, babu mashinsshini balle malashi.
Faɗi tashi na neman magani babu irin wanda bata yi ba ita da iyayenta, amman ba wani labari. Yanzu kan har ta fara fidda rai daga samun mijin aure.
Kallon kanta take sosai da sosai a gaban madubi tana mamakin yadda take ƙokarin kare kanta daga zina da alfasha, tana ƙokarin sallah dare da sadaka, amman ta kasa samun mijin da zai aureta.
Hawaye ne suka zubo mata tana tuna irin yawan ƙawayenta, amman babu ko ɗaya duk sun yi aure sun barta.
Ƙarar da wayarta ta yi ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, sai ta kalli Screen ɗin wayar Salma ce rubuce a fuskar wayar, cikin sauri ta share hawayenta ta ɗauki wayar ta kara a kunne.
“Hello Salma”
“Na'am Kalsoom ya kike?”
“Lafiya ƙalau, ya Ahmad?”
“Lafiyarsa ƙalau, idan kina da time gobe ki shigo da wuri zamuje wani guri”
Da toh kawai ta amsa mata ta aje wayar, ta san tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, ko bata faɗa ba ta san ba zai wuce ta kai ta gurin wani Malamin ba, dan duk cikin ƙawayenta ita ce ta fi kowa damuwa da rashin aurenta, ita ce take ta faɗi tashi akan taga ta yi aure.
Kiran da ta ji ana mata downstairs ne yasa ta motsa ta tashi ta nufi ƙofar fita. Karo suka yi da Momy sai ta ja baya da sauri tana faɗin
“Kirana kike yi?”
“Eh yanzu mijin Zainab ya kira wai bata da lafiya tun shekaranjiya”
“Subhannallah miye same ta?”
“Wai maleria ce, amman dai na san ba zai wuce ciki ba, shine nace ki shirya gobe kije can ki yi mata ko da kwana uku ne idan ta ɗan sarara sai ki dawo”
“Haba Momy ni kuma? miyasa Saleena ba zata je ba ni fa yayarta ce kuma ace na koma can na zauna”
“Toh miye a ciki? ai ansan lalura ce ta kai ki, Saleena Exam za su fara gobe kinga ba zai yiyu ta je can ba, amman ke tunda aiki ne ai idan kin dawo sai ki ɗan taya ta aikin gidan da dafa musu abinci”
“Amman Momy ai yana da ƙanne mata kuma za a iya ɗauka mata ƴar aiki”
“Ya san da ƙannensa amman ya zo nan ya faɗa mana, idan mutum yana mutunta ya kamata kai ma ka mutun tasa, kwana uku kawai zaki yi ki dawo kin ji?”
Ta ɗaga mata kai alamar toh, zuciyarta cike da damuwa.
“Allah ya yi miki albarka”
“Amin”
Daga haka Momy ta juya ta sauka ta barta a gurin tsaye. Jinginawa Kalsoom ta yi jikin ƙofar tana addu'ah
“Ya Allah idan mijina yana nesa da ni Allah ka kusan to dashi a gare ni, idan yana kusa da ni Allah ka haɗa mu”
Juyawa tayi ta shiga ɗakinta tana cika ma bakinta iska.
***********
THERD FAMILY....
A-hankali ya ke shafa lallausar fatar jikinta da hannunsa, idonshi a lumshe yana hura mata iska a kunne, daga bisani ya fara tsosar kunnen nata hannunsa ɗaya yana saman ƙirjinta. A take ta lumshe ido tana maida numfashi, tana ƙoƙarin mayar masa da martani, hannayenta tasa cikin gashin kansa kamin ta juyo ta soma masa kiss a ƙirji, ɗayan hannunta na cikin cibiyarsa, da sauri ya kwantar da ita ya zare tawul ɗin jikinta ya soma murza fatarta bakinsa cikin nata suna maida numfashi. Ringing ɗin wayarta ne yasa ta walƙato shi cikin dabara ta dawo saman ta, sai ta yi saurin sauka tana dariya
“Am sorry Sweetheart na yi latti, ka ga har an fara kira na”
Daker ya iya ɗaga jajayen idanunsa ya kalleta yana haɗiye yawu
“No Please karki min haka Ammyn Rafiq, i need you”
Tawul ɗinta ta ɗauka ta ɗaura tana faɗin
“I need you too Babe, but there's nothing i can do, you know how my work is”
Babu abunda zai ce mata, haka take masa time to time, ta kan hana sa haƙƙinsa saboda aikinta, idan ta dawo da dare ta ce ta gaji bachi idan kuma da safe ne ta ce zata yi latti, babu kuma yadda zai yi ya hanata aikin tun da mahaifinta ya tsaya kai da fata akan lallai sai ƴarsa ta yi aikin banki.
Yana kwance a gurin har ta yi wanka ta shirya yana kallonta, sai daf da zata fita sannan ta zo daidai kunnensa ta yi masa kiss
“Take care of yourself okay, idan Rafiq ya tashi ka shirya shi idan zaka je aiki ka aje shi kurin Hajiya, zan ɗauko shi idan na dawo, idan kuma su Ulfah sun dawo abincin su na nan a flask, love you my hubby my Doctor”
Daga haka ta fice tana murmushi, da kallon ya bita har ta fice, sannan ya ɗauke kansa yaja bargo ya lulluɓe ya soma sana'arsa.
_______________________________
Hello my beautiful people, ina fatar kuna lafiya kuma ina fatar wannan tafiyar zata muku daɗi zaku kuma bani haɗin kai kamar ko yaushe.
Wannan tafiyar ba irin wacan bace ce, ba zan baku kunya ba In'shallahu, iyana gayyartar ku a sabon shafina wanda zan riƙa zuɓa duka littafaina a can, zan riga yin update a can sama da ko'ina zaku iya samun shafuka na akan kari Just click the for your updated.
www.khadeejacandy.com.ng
Zan cigaba idan na ji ra'ayoyinku 08036126660 na gode ☺
Best regards 💖
Khadeeja Candy🌺
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa03.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 2*
NAMRA POV.
Yadda Namra ta ga rana haka ta ga dare, dan kwana ta yi kuka da tunanin Asim, da safe ma bata fito ba sai da ta yi shirin fita, sannan ta leƙa ɗakin Anty Amarya dan gaishe ta, daga bakin ƙofa ta tsaya tana miƙa mata gaisuwar tana ɗan kare fuskarta.
“Anty Ina kwana?”
Yanayin muryarta kaɗai ya isa ya karantar Anty Amarya halin da ƴarta take ciki, daman ta san za'a rina, ko babu dalili Namra ta kan yi kuka balle yanzu da kuka ya zame mata jiki.
“Ba zan hana ki kuka ba Namra, dan kina da dalilin yinsa, amman nasan kin sauke Alƙur'ane kuma kin haddace hizo arba'in daga cikin Alƙur'ane, ashe ko ya kamata a'ce idan kin shiga damuwa ki riƙa faɗawa Allah buƙatarki kina kai kukan ki a gareshi”
Daga inda take tsaye ta amsa da
“Na gode sosai Anty In'shallahu zan yi, zan je gidan su Anty Yasmin”
“Allah ya kiyaye hanya, amman ki tabbatar kin ci abinci ka min ki je”
“Toh”
Bayan ta amsa da to ne ta juya ta fice, dinning ta nufa ta haɗa tea kaɗan ta sha, dan bata jin cin komai, ta daɗe a gurin zaune sannan ta ɗauki handbag ɗinta ta rataya ta fice daga palour, direct ta nufi gurin da Motar ta take.
Bayan ta yi addu'o'in data saba, sannan ta yi ma Motar key ta yi horn Mai gadi ya buɗe mata ta fice.
Tuƙi take kamar marar lakka, gashi zuciya ba ƙwari, sai tunane-tunane take.
Hannu ta ga ana mata gefen hanya alamar ta tsaya, tana ganin Asim ta yi saurin taka burƙi ta yi ribas ta dawo dai-dai inda ya ke ta faka, buɗe Motar tayi ta fito jiki na rawa ta ga masoyinta.
Matsowa ya yi kusa da ita yana murmushi
“Namra”
“Asim”
Haɗa baki suka yi gurin kiran sunan, sai ko wannensu ya yi shiru yana kallon ɗan'uwansa.
Da sauri Namra ta kawarda fuskarta saboda hawayen da suka cika mata ido. Hankali Asim ya tashi sosai ganin hawaye a idon Sahibarsa.
“Jiya na kira ki ya fi a ƙirga amman baki ɗaga ba, yanzu kuma ga hawaye a idonki, hakan ya tabbatar min da akwai abunda yake damunki”
Ta share hawayen da suka zubo mata.
“Babu komai, ba abunda ya ke damuna”
“Kina ɓoye min wani abu Namra, kina son tunani ya yi min yawa ko, ina tunanin halin da muke ciki, ga halin talaucin da nake ciki ga rashin aikin yi da ke damuna, Namra da wanne zan ji?”
“Faɗa maka bashi da amfani Asim, zai ƙara maka damuwa ne kawai”
“Saboda ba zan iya miki maganinsa ba ko Namra?”
“Ba haka bane, Asim zan baka wasu kuɗaɗe da zaka ja jari da su...”
Hannu ya ɗaga mata
“Tun yaushe nake faɗa miki ba dukiyar ki nake so ba Namra, ke nake so ba abunda yake cikin gidan ku, ko abunda kika mallaka, kawai ina son ki yi min alƙawari duk rintsi duk wuya ba zaki rabu da ni ba, ki min alƙawarin zaki aure ni Namra shi kawai nake so”
Kai ta girgiza masa tana wasu irin zafafan hawayen
“Ba zan iya ba Asim, ka gafarce ni ba zan iya ba...”
Dammm! Ya ji kamar an jefa masa dutse a zuciya, a take idonsa suka rine suka cika da ƙwallah, sai ya yi saurin sadda kansa ƙasa yana zauke ajiyar zuciya.
“Ashe gaskiya Umma take faɗa min, ashe yaudara ta kike ba zaki aure ni ba, amman kin ban mamaki Namra, ban tsammaci haka daga gareki ba”
Ta yi saurin kama hannunsa tana kuka
“Ba laifi na bane Asim, iyaye ne...”
Ya katsa mata tsawa
“Iyaye? Ni bana da iyayen ne Namra? Mahaifiyata bata son tarayyata da ke amman na tsaya kai da fata akan sai na aure ki, sai ke? kin fi ni sanin darajar iyayen ne ko me?”
Kasa cewa komai tayi, daman ta san ba zai fahimce ta ba, ba zai mata uzuri ba, zai zargera da da cin amana, ita kam ta san bata kyauta masa ba, sai dai babu yadda zata yi.
Hannunta ya ture, ya share hawayen da suka zubo masa ya juya a fuce ya kama hanya.
“Asim!Asim!! Asim!!!”
Haka ta bishi da kira tana kuka, amman ko waigowa bai yi ba balle ya amsa mata. Zubewa ta yi a gurin tana kuka, kukan tausayawa kanta da zuciyarta, dan ita ma kanta ta san tana son Asim, zata yaudari zuciyarta ne kawai idan har ta ce zata iya rayuwa da wani namijin da ba Asim ba.
Ta kusan minti goma shabiyar a gurin tana kuka, sannan ta buɗe Motarta ta shiga. Hanyar da zata sadata da gidansu ƙawarta Amira ta ɗauka tana wani irin gudu na fitar hankali.
Cikin ƴan mintuna ta isa gidansu Amira, daga wajen gidan ta faka motar ta dan ba zata iya jira mai gadi ya buɗe mata ba, sai ta fito ta taka da ƙafa ta shiga cikin gidan still tana kuka.
Mahaifiyar Amira ta yi mamakin ganin ta haka, sai tambayarta take lafiya, ita dai bata yarda ta faɗa mata komai ba, ta wuce ɗakin Amira kasancewar gidan ba baƙonta bane.
“Ke lafiya miya same ki?”
Amira ta tambaya cike da tashin hankali tana girgiza Namra. Bata ɓoye mata komai ba, tun daga yadda suka yi da Abbah, har abunda ya faru tsakaninta da Asim a yau.
Wani dogon tsaki Amira taja ta ɗauke hannunta daga jikinta
“Ke dan Allah duk kin tayar min da hankali, ni na ɗauka ma wani abun ne”
Kallon rashin fahimta Namra ta yi mata da idanunta da suka rine saboda kuka.
“Ban gane ba, Amira ko baki fahimci abunda na faɗa miki bane?”
“Na fahimta sarai, ai da hausa kike magana, naga dai babu wani abun tada hankali a ciki, tunda kina da mafita”
Namra ta ƙara kallonta
“Wace irin mafita? Ai nima mafitar nake nema”
“Kawai ki bishi ku gudu kuje can wani guri a ɗaura muku aure, daga baya iyayenki zasu yafe min idan suka fahimci irin son da ke tsakanin ku”
“Wannan ba mafita bace Amira, ni ba zan iya wannan ba, duk son da nakewa Asim bai kai wanda nake yi ma iyayena ba, ko wanne muhallinsa daban”
Amira ta taɓe baki
“Ashe ko ba son ƙwarai kike masa ba, tun da har ba zaki iya sadaukar da kan ki a gare shi ba”
Shiru Namra ta yi kamar mai tunani, sai kawai ta share hawayenta ta ɗauki jakarta ta rataya tana faɗin
“Bari na wuce akwai inda zanje, sai mun yi waya”
“Toh, Allah ya kiyaye hanya”
Lokuta da dama haka Amira take nata yaɓen maganar duk data zo bakinta, ta kan bata shawara tsaɓanin tunaninta, sai dai babu wanda zata faɗawa damuwarta kamar ita da Anty Yasmin.
Da wani mugun kallo Amira ta bita tana harararta, can kuma ta taɓe baki.
“Wahalalliya, ashe ƙaryar so kike tun da ba zaki iya barin iyayenki ba”
Wayarta ta jawo ta soma danne-danne, kamin ta tashi ta nufi ɗakin mahaifiyarta dan labarta mata abunda ya faru.
Har Namra ta fito daga gidan nazarin kalaman Amira take, sam bata ganin dacewa akanta guje iyayenta, saboda saurayin da zai iya barinta ya ɗauki wata, taya zata iya gudu mutanen da suka shekara ashirin da biyu suna bata gudummawa, akan saurayin da haɗuwarsu bata wuce shekara uku ba, idan har ta yi hakan ta yi babban butulci wanda ta cancanci ko wane irin sakamako. Sai dai wani ɓangare na zuciyarta, yana karantar da ita akan abunda Amira ta faɗa mata shine mafita, dan idan ba haka ba mahaifinta ba zai taɓa bari ta auri Asim ba.
Har ta isa gidan Barrister Yasmin wannan tunanin take, tana hangowa kanta illa da kuma alfanun da ke tare da ita idan har ta zaɓi guduwa ta bar iyayenta.
Ta daɗe a cikin motar tana kiran wayar Asim, amman yaƙi picking at the end ma sai ya kashe wayar gaba ɗaya, cikin rashin kuzari ta buɗe motar ta fito tana kallon balcony ɗin ƙofar Yasmin, sai a lokacin ta lura da Motoci uku da aka faka a gurin.
‘Waɗannan ba Motocin Ya Uzair bane, kar dai ace baƙin har sun iso, ko da yake abuja ba nesa bace idan sun shigo jirgi’
Shine abunda take rayawa a zuciyarta tana ƙoƙarin duba agogon hannunta, 11:23am ya bata hakan yasa ta saki jiki ta nufi ƙofar, tana isa ta kai hannu ta murɗa ƙofar. Abunda ta yi arba da shi yasa ta mutuwar tsaye, zaro ido ta yi ta rufe bakinta da sauri taja baya.
Cikin sauri Uzair ya ture Mutumen da ke samansa ya tashi ya nufi inda take, har ya iso kusa da ita jikinta rawa yake, gashi be da riga daga shi sai gudun wando. Shima hankalinsa ya tashi sosai bai tsammaci a buɗe ya bar ƙofar ba, mamakin kansa yake ma yadda bai ji buɗe gate ɗin gidan ba da fakawar Motar ta.
Da hannu ta nuna shi, sai kuma ta kasa magana. Cikin zafin hannu ya kai hannu ya cafko hannunta ya jefa ta cikin parlor.
Baya-baya tayi tana neman mafita sai kawai ta shige kitchen da samawa kanta makami, tana shiga ta nufi inda wuƙa take ta kai hannu ta ɗauka. Shi kuma ya kunno kai cikin Kitchen ɗin zuciyarsa na bugawa da ƙarfi.
“Ba zan miki komai ba Namra, matukar kika rufa min asiri, wallahi kuskure ne ba a son raina bane cilas ta ni suka yi”
Nuna shi ta yi da wuƙar da ke hannunta tana girgiza kai
“Ba zan rufa maka asiri ba Ya Uzair, tun da ba rufin asirin kake so ba, tun ba yau ba na taɓa ganin wani video a wayarka, Namiji na kissing ɗin Namiji ɗan'uwansa sai kace min sabon Memori ne ka siye baka san da video ba, yanzu kuma na kama ka da ido na.
Kai wane irin Namiji ne dan Allah? Matarka ta yarda da kai ta baka amana amman kana cutar, cutar ma bata tsaya akan ka har sai ka neme ni! Kuma miye abun son ga Namiji ɗan'uwanka? Tirrr da kai Ya Uzair, na yi baƙinciki da ka kasance mijin Anty Yasmi, sam bata cancanci zama matarka ba”
Murmushi ya yi ya jawo ƙofar Kitchen ɗin ya rufe.
“Na nemeki ne saboda naga abunda nake so a jikinki, lokacin da nace na aureki ai cewa kikayi kina da wanda kike so, daman nima ban shirya zama da mata biyu ba, shiyasa na nemi yin sex da ke.
Amman yanzu bari kiji na faɗa miki, duk kika kuskura kika bari maganar nan ta fita, kika faɗawa duniya cewar ni ɗan homo ne sai na tarwatsa rayuwarki, ki rubuta ki aje”
Ya faɗa mata haka fuska a ɗauri babu alamar wasa a lamarinsa, sannan ya buɗe ƙofar kitchen ɗin
“Zo ki fice, amman ki rubuta ki aje duk kika kuskura fitar da wannan maganar sai na salwanta rayuwarki”
Daga haka ya fita ya bar mata kitchen ɗin.
Ita kam bata yarda ta fito ta nan ba, sai ta buɗe ƙofar baya ta kitchen ɗin ta fita gabanta na mugun faɗuwa, har ta shiga Motarta jikinta rawa yake, zuciyarta na raya mata karta ɓoyewa ƴar'uwarta kuma aminiyarta abunda mijinta keyi, gani take idan har tayi haka bata yi mata adalci ba.
Tana fita daga gidan ta faka gefen ti-ti ta dannawa Yasmin kira, three miss call tayi mata amman bata ɗaga ba, ta san ba zai wuce tana cikin kotu ba, sai kawai ta yanke shawarar tura mata saƙo.
Ko da ta isa gida Anty Amarya bata nan, part ɗin kuma babu kowa, ƙannenta duk suna makaranta, hakan ya bata damar shiga ɗakinta ta baja kolin hajar tunaninta.
UZAIR POV.
Lokacin da Uzair ya ga Namra ta fita sai ya gargada ƴan iskan friends ɗinsa, ya gyara gidan tas kamar komai bai faru ba. Ba ayi minti Arba'in ba, sai ga Yasmin ta dawo gidan, cikin sauri ta shigo parlor tana dube-dube.
Uzair na zaune saman kujera yana kallonta, hankalinsa kwance kamar ba komai, sam be yarda ya nuna akwai wani abun a fuskarsa ba, tashi yayi ya tare ta, tare da rumgumeta yana kissing
“Lafiya wife?”
Ta sakar masa jikinta sosai
“Wallahi miss call ɗin Namra na gani da text ɗin ta, wai na yi sauri na zo gidana, shine duk hankalina ya tashi”
Dariya yayi sosai a zuciyarsa yana jinjina ƙarfin hali irin na Namra.
“Haba dai sai kace baki san Namra ba? Zata iya disgaki fa ai ba yau ta saba ba, karki tashi hankalinki”
Juyowa tayi sukayi kissing ɗin junansu sannan ta ce
“Ta katse min aiki na, ina fatar dai tayi maka kosan kazar?”
Hancinta ya laƙata
“Namra bata ma zo nan gidan ba, friends ɗina kuma har son kama hanyar Abuja daman ɗaurin aure suka zo”
Da haka ya shammace ta ya cigaba da kissing ɗinta.
NAMRA POV.
Duk yadda ta so ta labartawa Anty Amarya abunda ke cikin ranta na game da Uzair sai ta kasa, haka ta wuni tana tunanin abunda ya faru tsakaninsu da Asim, da kuma shawarar da Amira ta bata, a ɗayan ɓangaren kuma ƙwaƙwalwarta na ɗauke da hoton abunda taga Ya Uzair yayi.
Har bayan Sallah Isha'i tana kiran wayar Asim amman ya ƙi ya ɗaga, ta tura masa massage no reply, abun duniya duk ya bi ya dame ta.
Shigowar Anty Amarya ne yasa ta tsaita natsuwarta, har tana ƙoƙarin gyara zamanta.
“Abbanki yace na faɗa miki baƙonki ba zai samu zuwa ba”
Anty Amarya ta faɗa yayinda take ƙoƙarin zaunawa saman gadon kusa da ita. Namra ta ɗan kalleta kaɗan
“Miyasa?”
“Nima ban sani ba, amman na naji a waya yana cewa wai kin masa ƙarama, kuma yana jin nauyinki”
Namra ta ɗan yi murmushi ƙaɗan ta kwanta jikin Anty Amarya.
“Shima dai yasan ni ba sa'arsa bace”
Anty Amarya ta shafa kan ƴarta.
“Allah dai yayi miki zaɓin da yafi alheri, ya yaye miki damuwarki”
“Amin Mamana”
KALSOOM POV.
Around eight thirty Kalsoom ta fito ɗakinta, a lokacin Saleena har ta wuce makaranta. Ita ta haɗa musu breakfast bayan ta gama, ta zuba ma Dad da Momy nasu ta ɗauka ta nufi part ɗinsu.
Bayan ta gaishe su, ta aje musu abincin tana ƙoƙarin rasowa Momy tayi mata tuni da zuwa gidan ƙanwarta Zainab.
“Ban manta ba Momy, yanzu idan na shirya can zan fara zuwa na aje kayana sannan na wuce aiki”
“Hakan yayi Allah ya kawo miki naki mijin”
Sai da ta amsa sannan ta tashi ta fice. Kala biyar ta ɗauka a maimakon uku, dan tasan sai ta fi kwana uku a can, cikin ƙaramin akwati ta saka su, sannan ta shirya kanta ta fice.
Kamar yadda ta tsara sai da ta fara biyawa gidan ta aje kayanta sannan ta wuce gurin aiki. Biyu da rabi ta tashi daga aikin direct gidansu ƙawarta Salma ta wuce.
Ta taki sa'ah, tana shiga mijinta na fita. Sai da tayi Sallah Salma ta ɗebo mata abinci ta ƙoshi sannan ta ɗauko mata zance.
“Kalsoom wani gari ne nake son muje tare da Ruƙayyah ita zata kai mu, ance malamin yana aiki sosai dan mutane da dama suna dacewa”
Kalsoom ta sauke ajiyar zuciya
“Ni wallahi har na gaji da irin wannan shige-shigen, kullum ana abu kamar ba'ayi, wani gurin ace aljanu ne wani su kuma su ce sihiri ne, na rasa gane kan matsalar nan, Wani lokacin har ji nake kamar na kashe kai na”
Salma ta dafata
“Subhanallahi, haba Kalsoom ki daina wannan maganar mana, Allah ya baki aikin da zaki iya taimakon kanki, Allah ya rufa miki asiri aure ne kawai Allah bai kawo miki ba, shine kuma kike ƙoƙarin butulce masa, kina wannan maganar sai kace ba musulma ba?”
Kalsoom ta lumshe ido ta buɗe ta kalli Salma cike da damuwa ta ce
“Salma duk abunda Allah ya ban da wanda zai ban bai kai kamar aure ba, aure shine cikar mutuncin ko wace ƴa mace, ni fa ba dotse bace Salma ina da sha'awa ina tsoron abunda zai kai ni ga halaka”
Salma ta riƙata tana ƙoƙarin kwantar mata da hankali.
“Roƙon Allah baya faɗuwa ƙasa Kalsoom, komai zai zo ya wuce kamar ba'ayi ba, kuma ba asan inda rabo take ba wata ƙila mu dace”
“Ni dai ba zan sake zuwa ko ina ba, na haƙura ballantana kinsan Ruƙayya ba a sirri da ita, kuma ko munje ba wani dacewa za muyi ba, tun da babu wanda zai iya matso maka da nesa kusa, babu wanda zai iya goge abunda Allah ya rubuta maka, sai dai kawai su ci kuɗinka, na fawwalawa Allah komai daman da shi na dogara”
Duk yadda Salma ta so ta lallaɓa Kalsoom su je, sai taƙi dan ita yanzu ta riga ta sadaƙar. Sai da Yamma Kalsoom ta bar gidan Salma.
__________________________________
How about dis journey?
#threefamily
# Vote
#Comment
#TeamNamra
#TeamKalsoom
#TeamHilal
#Candy
#Blog
Always check my website for more.
BEST REGARDS💖
Khadeeja Candy 🌺
www.khadeejacandy.com.ng
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 3*
DOCTOR HILAL POV.
Bayan ya gama abunda yake ya shiga ya yi wanka, sannan ya fito falo ya yayi breakfast, sai kuma ya sake dawowa ya tashi Rafiq ya shiya sannan ya fice.
Kamar yadda ya saba gidan Hajiya ya nufa dan kai Rafiq ɗin, kasancewar Hajiya na da ƴan aiki da yawa masu kula da shi, wani lokacin ya kan aje shi a falo yace a shiga dashi gudun kwankwamin Hajiya, ko kuma ya aje mata shi ya yayi saurin barin gidan.
Sai dai yau bai yi sa'ah dan yana shiga ya ci karo da ita cikin falon tana karyawa, sun-sun-sun yayi ya gaisheta.
“Hajiya Barka da tashi”
“Barka dai mijin Hajiya, har ta tafi aikin ko? Bari dai kaji na faɗa maka na kusa barin rainon ɗan ku”
Maganar tayi masa zafi, sai dai babu yadda ya iya tun da mahaifiyarsa ce, kuma idan sabo ya saba da irin waɗannan kalaman daga bakin Hajiya da Alhaji, Murmushi yayi ya shafa kan sa.
“Hajiya haƙuri dai za'ayi, kisan ƴan rainon nan ba tsoron Allah suke ba”
“Kai ai kana tsoron Allah, tun da har kakr barin Matarka tana shiga cikin maza tana gogaiya, ace mace idan ta fita takwas na safe ba zata dawo ba sai cikin dare? Bata da lokacin mijinta balle na ƴaƴanta”
“Hajiya kin san aikin banki ne, kuma ita ce Manager ta banki dole ne ta riƙa bada lokacin can”
“Toh ta bar aiki mana dole ne? Amman ace mace ta bar Yaro ƙarami mai shan nono dan kawai ta je aiki”
Murmushi kawai yayi ya tashi yana shafa kai yana faɗin
“Bari na wuce”
Har ya kai ƙofa bai ji tace masa komai ba, sai ya juyo yana murmushi yace
“Hajiya ni fa bana son fushin nan da kike da ni”
Wani kallo ta watsa masa
“Yaushe na ce ina fushi da kai?”
“Toh ai ban ji kince Allah ya tsare ba”
“Ko ban ce ba ai Allah tsare ka zai yi”
Wata irin dariya yayi, ya dawo yayi mata side hug
“Allah ya bar mana ke Hajiya, i love you”
Dariya tayi tana faɗin
“Jeka ka aikinka kamin Alhaji ya fito, kasan nashi faɗan babba ne”
Ficewa yayi yana dariya, zuciyarsa cike da shauƙin son mahaifiyarsa.
Uku da ƴan mintuna ya tashi aiki, sai da ya biya ya ɗauko Yaransa daga makaranta sannan ya dawo gida, sai da suka yi sallah sannan ya zuba musu abinci suka ci, wani lokacin lokacin ta kan tashi da wuri ta dafa musu abinci, wani lokacin kuma sai dai yayi musu takeaway. Bayan sun gama ci suka shirya suka tafi Islamiya.
Haka Doctor Hilal yake fama da irin wannan kaɗaicin kamar marar mata, gashi shi ba mutun ba ne mai son yawa fita, indai ba gurin aiki ba kullum zaka tararda shi a gida.
Matarsa kuma ota da gidan sai dare, babu yadda ya iya tunda babanta ya tsaya kai da fata akan lallai sai tayi aikin banki kasancewarta babbar ƴarsa, tana da ƙanne maza amman ya tsaya akanta dan kawai yaga ya kashe mata aure, tun asali ba Doctor Hilal ya so ta aura ba, shiyasa baya ƙaunar surikin nasa ko kaɗan, shi kuma baya jin zai iya rabuwa da ita saboda yana son matarsa ita kuma tana sonsa.
Ulfah da Ezzah na dawowa daga makarantar islamiya, suka ɗauko Homework ɗin su Doctor Hilal ya yi musu.
Gimbiyar tasa kan bata dawo gida ba sai bayan Isha'i. Da sallama ta shigo amman ko inda take bai kalla ba balle har ya amsa mata sallamar, sai ta kwanto jikinta tana masa shagwaɓa
“Yanzu zan yi sallah ka kasa amsa min haba Dear”
“Yaran ki har sun gaji sun yi bachi, yau kwatakwata Rafiq bai sha nono ba, idan ni ina iya haƙuri na su kuma ba? Rashin ba su lokacin ki da kike shi zai sa ki kasa karantar wane hali ƴaranki suke ciki”
Bata yi mamakin kalamansa ba, daman yakan yi fushi da ita wani lokacin, kuma ta lura da hakan tun daga lokacin da samu promotion. Yana tashi tayi saurin sakin handbag ɗinta ta riƙo shi, sai ya ture hannunta
“Zaki iya fushi da ni?”
“A'a ni Wallahi ba zan iya”
Ta faɗa a marairaice
“Toh ki koya daga yanzu, ta yadda za mu iya yin sati ba muyi magana da junan mu ba”
Rumgume shi tayi tana kukan shagwaɓa.
KALSOOM POV.
Ko da ta isa, Zainab na kwance falo tana bachi. Mayafinta ta aje ta ɗauki hijabi ta saka, ta bi gidan gyara tass, sannan ta ɗora musu girki.
Haka ta kwana huɗu tana musu aiki, cikin rashin sakewa dan gani take kamar Zainab ɗin da Mijinta zasu raina ta, ta kan abuɓda bai dace ba amman bata magana, sai dai kwallafawa zuciyarta idan har ta je gidan sai ta faɗawa Mony irin zaman auren da Zainab keyi. A kwananta na huɗun ne Momy tayi ma Mijin Zainab magana ya kawo ƙanwarsa dan ta taya Zainab zama, Ranar da zata dawo ranar ce Zainab ta fara awo cikin, dan haka dole ita ce ta rakata bata je aiki ba a ranar, asibitin ta je aka yi ma Zainab komai, sannan suka dawo gida tare, da zimmar ita Zainab ɗin zata koma gidanta da yamma.
Bayan sun gama cin abinci rana ne, Kalsoom ta ɗauko labarin dan Momy ta ja mata kunne.
“Gaskiya Momy ayi ma Zainab faɗa, ya kamata ace ta canja rayuwa ta riƙa lurar da mijinta abunda ya dace da wanda bai dace ba, kinsan mijinki fa kece makarantarsa ta farko, gareki zai fara ɗaukar darasi”
Momy tace
“Mi akayi?”
“Sam sam sam mijinta baya son alheri kuma baya son yan'uwansa suna zuwa gidan, sannan idan za ayi girki sai dai komai yaje ya siyo ƙire-ƙire kamar ba mai kuɗi ba, idan fa kika saba masa da wannan rayuwar ita zai riƙa miki ko can gaba”
Zainab ɗin ta haɗe rai sosai irin bata ji daɗin maganar ba.
“Nifa gaskiya bana son haka, daga zuwa jinya sai kuma kizo kina faɗar sirrin gida na”
“Ba ina faɗar sirrin gidanki bane, gaskiya nake faɗa miki”
“Toh ya kike son nayi masa? Ai halinsa ne idan yaga dama zai canja, Anty Kalsoom kefa ba auren nan kikayi ba balle kice kinsan yadda abun yake, ki bari har kiyi auren sannan ki faɗa min abunda da zan yi da wanda ba zan yi ba”
Saleena tayi farat tace
“Haba Anty Zainab daga an faɗa miki gaskiya”
Zainab ɗin ta yatsene fuska.
“Wane irin gaskiya, so take na masa bala'i ne ya sake ni nazo na zauna tare da ku”
Momy ta kalli Kalsoom tace
“Ki daina irin haka ba kyau, koma minene ki kyale ta can ita ta sani, ba kyau kana faɗin sirrin ɗan'uwanka, ita fa rayuwar aure sai da haƙuri kuma ke baki yi ba balle ki gane haka, ku daina wannan maganar bana so”
Duk maganar nan da Momy take kan Kalsoom na ƙasa saboda idonta daya cika da ƙwalla, daga bisani ta tashi ta nufi ɗakinta tana hawaye. Saleena ma ta tashi ta bar musu gurin tana harar Anty Zainab.
NAMRA POV.
Ranar Assabar aka yi walimar kamar yadda aka tsara, Namra na cikin ɗalibai talatin da uku da suka haddace wani ɓangare na Alƙur'ane, da ban aka ware su aka karramasu, aka kira manyan mutane suka yi musu kyauta.
Maryam na cikin Ɗaliban da suka sauka bana, bayan walimar makaranta sai da Anty Amarya ta shirya nata walimar a gidan dan karrama ƴarta.
Ƴan'uwa da abokan arziki da dama sun samu halarta, cikin har da Anty Yasmin da Ya Uzair. Anci ansha nama kam kamar mayankansa, ga uban takeaway da Anty Amarya ta
shurya gwanin ban sha'awa.
Ana sallah la'asar Ya Uzair ya tashi zai wuce dan Yasmin tace ita kam sai dare. Anty Amarya ta ɗauko masa takeaway, ƙin karɓa yayi sai yace a bawa Namra ta kai masa. Ba dan ta so ba ta karɓa ta nufi gurin Motarta fuskarta babu annuri. Shi ko yana cikin motar ya hakince yana kallonta.
“Ba nace karki faɗa Yasmin ba? Shine har da buga mata waya ko?”
Ya faɗa bayan ya kai hannu ya karɓa.
“An faɗa mata ba, amman zan faɗa mata very soon dan ba zan bar ta ta cutu da kai ba, ba zai yiyu ka laƙa mata cutar HIV ba ina zaune ina kallo”
“Wai miyasa idonki ya buɗe haka? Alaƙar dake tsakanin ki da Yasmin ita ce tsakani ɓa da ke, kuma Yasmin matata ce babu ruwanki da lamarin mu”
“Idona ya buɗe ne tun daga lokacin dana fahimci kai fasiƙi ne, kuma wallahi sai na tona maka asiri, har nema da kayi sai na faɗa”
Wani dogon tsaki taja, ta juya ta nufi hanyar falo.
Da wani irin kallo ya bita yana jin kamar ya kamo ta ya shaƙure, ƙwafa yayi ya rufe motarsa.
Sai bayan sallah isha'i kowa ya watse, a lokacin ne Maryam da Namra suka samu damar duba kyaututukan da suka samu, Ba wanda suka fi murna kamar na Abbah da yayi musu kyautar Zinari, ihu suka riƙa yi kamar zasu tashi gidan dan murna, ba ma kamar Marya data daɗe tana roƙon Abbah ya sai mata zinari.
A tare suka nufi part ɗinsa dan yi masa godiya, sai suka tararda shi zaune tare da Hajiya barau fuskokinsu shimfiɗe da murmushi.
Guri suka samu suka zauna suna masa godiya, sai ya amsa da far'ah kamar ba shine yake fushi da Namra ba, ita kanta abun ya bata mamaki sai dai kuma ta jidaɗin hakan.
Daf da zasu tashi ne Abbah ya kira sunan Namra
“Khadija”
“Na'am”
Da faɗuwar gaba ta amsa, ta dawo ta zauna tana jiran ta ji abunda zai ce. Sai da yayi gyaran murya sannan ya ce
“Kisan yadda nake da Uzair ko?”
“Na sani Abbah”
“Toh ya aiko Hajiya gata nan zaune ne yace yana son ƙara aure kuma ke yake so ya aura idan na amince masa”
Dakan shida-shida gabanta yayi saɓanin uku-uku dana kowa ke yi, da sauri ta kalli Abbah sai kuma ta sadda kanta ƙasa kamar wanda bata gane abunda suke faɗa ba.
Can ƙasa-ƙasa ta tsinkayo muryar Hajiya tana cewa
“Uzair kam ko wani gurin yaje neman aure ai mu zamu shige masa gaba, balle yace yana son ƴar mu”
Abbah yayi murmushin jindaɗi yace
“Sosai kan, wallahi yaron nan yana da tarbiya, ga hankali”
“Kuma ina fatar Khadija ba zaki bamu kunya ba, zamu yi matuƙar farinciki idan har kika amince da wannan auren”
Cewar Hajiya Barau. Abbah ya kalli Namra fuskarsa babu alamun wasa yace
“Zan baki kwana uku kije kiyi shawara, but lemme remind and warning you for the last time, kar damar dana baki na shawar ki zo ki ce min ba ki amince da Uzair ba”
Bata iya cewa komai ba har na tsawon lokaci, sai kawai ta tashi tayi baya-baya ta ƙara baya baya tana dafa kai kamar wanda zata faɗi, har sai da Maryam ta riƙa ta suka fita.
____________________________________
Yauwan Comments din ku yawan typing dina, comments din ku gwarin guiwa ne a gare ni.
#DOCTOR HILAL TEAM
#NAMRA TEAM
#KALSOOM TEAM
#UZAIR TEAM
#Comment
#Share
#Vote
#Blog
#Threefamily
BEST REGARDS 💖
Khadeeja Candy 🌺
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa04.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 4*
NAMRA POV.
Da kuka Namra ta shiga part ɗin Anty Amarya, sai ta zube ƙasa, ta jefar da sarƙar da ke hannunta cikin parlor.
Hindatu da Aisha duk suka kalleta, Anty Amarya kuma ta nufo ta da sauri tana tambayar ba'asi. Maryam ce ta faɗa musu abunda ya faru, dan Namra kuka kawai take kamar wacce za'a cirewa, zaunawa Anty Amarya tayi kusa da ita, ta kai hannu ta riƙa fuskar Namra idonta cike da ƙwallah ta soma magana
“Namra mi yake damun ki ne? Saboda Uzair yace yana son ki shi ne kike wannan kuka? Ni kike sakawa a damuwa, ni kike son jama matsala, duk rashin biyayyar da zaki yi ma mahaifinki laifin a kaina yake, ƙaurin suna zaki yi Namra, matuƙar kika ce ba ki son Uzair, kuma ni za'a zaga, miyasa a duk lokacin da za'a miki maganar wani Namiji sai kiyi kamar ki kashe kan ki? Namra mi yake damunki? Ke ce babba a gareni ke ya kamata ace kina nunawa ƙannenki dai-dai da rashinsa, haba Namra haba, haba, haba”
A take ta ji kukanta ya yanke, sai ta share hawayenta ta unƙura ta tashi, ta nufi ɗakinta.
Saman kujera ta zauna tana tunanin dalilin Uzair na faɗawa Abbah cewar yana son ya aure ta.
‘Miyasa yaje ya faɗa Abbah? Ko ma ya aure ba auren Allah da Annabi bane zai min, baya tunanin zumuncin mu da Anty Yasmin zai iya lalacewa? Ko dai wani abun ya ke nufi da ni ne?’
Tashi tayi ta nufi gurin gadonta tana cigaba da tunani
‘Tabbas idan har na ƙi yarda da auren shi ni za'a zaga, Abbah zai iya ɓatawa da ni, zan saka Umma cikin damuwa,
Wata ƙila yayi hakan ne dan na rufa masa asiri, ta yadda babu wanda zai san abunda yake aikatawa’
Saman gado ta zauna tana murmushin takaici
“Idan kasan wata, baka san wata ba Uzair, kaine zaka zanje maganar auren ka da kan ka, ko kuma na tona maka asiri Wallahi, ba zaka ci riba biyu a kai na ba”
Wayarta ta jayo ta shiga contact ɗinta ta nemo number Ya Uzair ta danna masa kira, ringing tayi har ta katse bai ɗauka ba, haka ta jera masa kira kusan tara amman be yi picking ba at the end sai mai ya kashe wayarsa.
Jin wayar a kashe ya matuƙar harzuƙa Namra sai kawai ta yanke shawarar kiran wayar Yasmin, dan tana tunanin ko saƙo ta tura masa ba zai karanta ba.
Yasmin na kwance jikin Mijin mijinta wayarta ta yi ƙara, sai da tayi kamar ba zata tashi sai kuma ta tashi a kasale ta nufi gun da wayar take.
Da far'ah tayi picking tana mata zolayar data saba mata a duk lokacin data kira ta
“Ke miyasa zaki kira ni yanzu, mijina baya son wayar dare fa”
Namra bata jin wasar, sai kawai ta ce
“Anty Yasmin Ya Uzair na kusa da ke?”
“Yana nan manne da ni mana, ya akayi?”
“Ba shi wayar zanyi masa magana ne”
“Okay”
Ba tare da kwan-kwanton komai ba, ta nufi inda yake ta miƙa masa wayar.
“Gashi Namra na son magana da kai”
Gabansa ya faɗi, ya kusan five seconds yana kallon wayar kamin ya karɓa ya kara a kunne
“Ina jin ki”
Cikin fusata Namra ta soma magana
“Ai daman so nake ka ji ni kuma ka maida hankali akan abunda zan faɗa maka. Uzair ina jan kunnen akan kayi saurin janye maganar aure na, ko kuma na tona maka asiri, ka je ka faɗawa Abbah cewar ka janye zancen aure na ko kuma ni naje na faɗawa Abbah waye kai.
Uzair zan iya kiran family meeting dan kawai na tona maka asiri, kaga har Anty Yasmin sai ta gujeka, kuma ka kunyata a idon duniya”
Murmushi yayi mai sauti
“Amman mi yasa ba zaki iya haƙuri na kunna wayana ba Namra? Wannan wane irin matsuwa ne haka? Be kamata kina min haka ba, sai ki bari har komai ya kama sannan kowa ya sani”
Be tsaya jiran abunda zata ƙara cewa ba ya kashe wayar yana girgiza kai, sai ya kai hannu ya janyo Yasmin ta faɗo jikinsa ya shiga mammatsa breast ɗinta yana hura mata iska a kunne.
“Bloody me Namra tace maka ne?”
Sai da ya kai hannunsa saman wandonta na bachi sannan yace
“Idan na faɗa miki zaki fahimta? Zaki min Uzuri?”
“Uhm”
“Bloody Son Namra nake kuma yanzu haka har na yi ma Abbah magana akan hakan, sai dai ita tana jin kunyar ki”
Ɗauke wuta tayi na ƴan daƙiƙu, sannan ta zare hannunsa daga jikinta ta juyo ta kalleshi
“Kasa a duniya babu wasan dana tsana irin wannan, dan Allah ka daina bana so”
Dariya yayi ya gyara zamansa ta yadda zata iya fahimtar zancensa
“Wallahi kin ji na rantse miki ko? Abunda na fada miki gaskiya ne, ƙara aure zan yi kuma Namra zan aura”
Tashi tayi ta matsa baya tana masa wani kallo kamar ta ga dodo
“Karka haukata ni Uzair, karka raba min hankali gida biyu”
“Ai na rantse miki, kuma idan har baki yarda ba ki kira Hajiya Barau ki ji, dan ita na aika ta faɗawa Abbah”
Kasa magana tayi, sai kawai ta rufe bakinta tana kallon wani gurin kamar mai tunani, zuwa can kuma ta jiya ta bar ɗakin, shi kansa Uzair ɗin bata nata yake ba, kalaman Namra yake tunani da nemawa kansa mafita.
A falo Yasmin ta dawo ta zauna, tana tunanin kalaman Uzair da son tantance gaskiyarsa
‘Idan har ba da gaske yake ba, mi zai sa yayi min wannan furucin? Ni kaina ina zargin irin yadda Namra take kula Uzair’
Bitar kalaman zuciyarta kawai take, wani ɓangaren tana ganin kamar Namra ba zata iya mata haka ban, bayan ma ta san babu wanda Namra take so kamar Asim, ko kuma dai tana yaudarar take dan ta karkatar mata da hankali?
Har garin Allah ya waye Yasmin bata iya tsayar da ƙwaƙwaran dalilin da zai sa Namra ta iya cin amanar ta ba, kuma ta kasa gasgata cewar Uzair ba da gaske yake ba.
Tun da tayi sallah asuba, ta koma saman gado ba dan bachin ba, sai dai kanta da ta ji yana sarawa, kuma bata jin haɗa ma Bloody ɗinta breakfast a yau, dan tun jiya ta warewa kanta ɗaki daban ta bar masa wacan ɗakin dan zuciyarta ta soma ɗasuwa da ƙiyayyarsa.
Shi kuma be bi sawunta, dan yasan she need a space, ta yadda zata gasgata kalamansa kuma ta san da gaske yake, shi kanshi da ace ya biyeta da be samuwa kansa mafita ba.
Tun bakwai na safe yayi shirinsa na zuwa office, be damu da breakfast ba ya fito ya nufi ɗakin da Yasmin take, yana taɓa ƙofar ya ji ta kulle, be tsaya komai ba ya sauko downstairs ya buɗe Fridge ya ɗauko ruwa ya sha, sannan ya fice.
Ba tare da fargabar komai ba ya nufo gidan Abbah, tun da yayi parking ya sauya yanayinsa zuwa na damuwa da ɓacin ciki.
Part ɗin Hajiya Barau ya fara shiga har wani sauke ajiyar zuciya yake. Murya ƙasa-ƙasa yayi sallama, Jikokinta suka amsa masa. Be yarda ya zauna ba dan be ga alamun Hajiya a falon ba.
“Ina Hajiya?”
Sai duk suka haɗa bakin gurin amsa masa
“Tana part ɗin Abbah”
Be tsaya komai ba ya juya ya nufi part ɗin Abbah yana ƙoƙarin ƙirƙiro ƙwalla. Ƙwanƙwasa ƙofar ya fara yi sai da aka amsa masa daga can ciki sannan ya tura ƙofar ya shiga da sallama.
Guri ya samu ya zauna ya natsu, yana sauko da kalaman da suke ƙwaƙwalwarsa zuwa bakinsa.
Ya kusan minti biyar zaune sannan Hajiya Barau ta fito, tayi mamakin ganin Uzair da wannan safiyar, a zatonta ma ko cikin yaran gida ne suka zo karɓa wani abu hannun Abbah, zaunawa tayi tana kallon yadda damuwa ke shimfiɗe a fuskarsa ƙarara.
“Uzair lafiya kuwa?”
“Hajiya lafiya ba ƙalau ba”
“Toh mi ya faru?”
“Abbah yana nan?”
“Yana nan”
“Dan Allah ki kira min wata magana nake son mu yi”
Ba musu Hajiya ta tashi ta nufi ɗakin Abbah. Bata ɗauki wani dogon lokaci ba sai gata ta fito tare da shi. Guri Abbah ya samu ya zauna yana amsa gaisuwar da Uzair yake masa
“Lafiya ƙalau, lafiya dai kayi mana sammakon nan?”
Jimmm yayi kamin ya ɗago kai ya kalle Abbah ya ce
“Abbah ka gafarce ni, kuma ka fahimci dan Allah”
“Mi ya faru?”
“Abbah...”
Sai kuma yayi shiru, kamar mai jin nauyin furta, har sai da Abbah ya ce
“Am... Uzair ni mahaifinka ne, kuma ina tunanin kasan da hakan, so ka faɗa min damuwarka kawai let your voice out”
“Abbah akan maganar dana aiko Hajiya ne na neman auren Namra, shine nake son a yanje...”
Wani kallo Abbah yayi masa yana karantar yanayinsa.
“Daman kace kana son ta dan ka dawo daga baya kace ka janye?”
“Ko kaɗan babu hakan a raina Abbah, kawai na lura kamar bata so nane kamar akwai wanda take so”
Abbah ya kalli Hajiya.
“Ke kika faɗa masa akwai wanda take so?”
“A'a Wallahi mi zai sa nayi haka?”
Cewar Hajiya tana ƙoƙarin kare kanta. Sai Abbah ya kalli Uzair ya ce
“Waya faɗa maka haka?”
“Abbah jiya ta kira ni da dare, gaban Yasmin tana min kalamai da basu dace ba, babu irin zagin da bata min ba, sannan tayi min barazanar ɓata min suna matuƙar ban janye maganar aurena da ita ba, tace min Asim take so kuma shi zata aura”
Abbah yayi murmushi yana gingina kai.
“Kurciya ho, ai Khadija ba ita zata aurar da kanta ta ba, kar wannan ya ɗaga naka hankali, sai dai ina son ka tabbatar min da zancen ka, shin har yanzu kana nan akan kuɗirinka na aurenta?”
Ɗagowa yayi ya kalli Abbah ido cikin ido.
“Abbah da bana son ta babu abunda zai sa na nemi aurenta, idan har zata amince da aure zan fi kowa farinciki, sai dai idan bata so kar a cilastata gudun abunda zai je ya dawo”
Abbah ya tashi tsaye yana faɗin
“Kar ka damu Uzair, kawai kaje ka fara shawarar date ɗin da kake so a saka musu na aure”
Murmushi Uzair yayi ya sauka ɗaga kan kujera ya ɗuka yana yima Abbah godiya.
“Abbah na gode sosai Allah ya ƙara rufa asiri yaja nisan kwana”
Sannan ya kalli Hajiya yana faɗin
“Hajiya a taya ni godiya”
“Ba komai Uzair, ai kai ɗan mu ne”
Cewar Hajiya. Cikin farinciki yayi ma Abbah sallama. Uzair na ficewa Hajiya ta kalli Abbah tace
“Amman ita kam Namra mi yasa tayi hakaɓ”
Abbah be ce mata komai ba ya kaɓe rigarsa ya nufi part ɗin Anty Amarya a fuce.
Haka ya shiga falo babu ko sallama sai sunan Namra yake kira iya ƙarfinsa. Duk fitowa suka yi har Hindatu dake kitchen da Maryam da Aisha, Anty Amarya ta nufo shi tana tambayar lafiya.
Wata harara ya watsa ma Namra sai da ta haɗe yawu da ƙarfi tayi ƙasa da kanta.
“Ni zaki watsawa ƙasa a ido? Ni zaki tozarta? Ɗan ƴar'uwata zaki kira ki ciwa mutunci dan kawai yace yana son ki?”
Kasa magana tayi sai kawai ta fara kuka. Anty Amarya ta girgiza ta
“Namra kin kira shi ne?”
Kai ta ɗaga. Anty Amarya ta shiga salati. Cikin kuka Namra tace
“Wallahi bana son sa ne, na zan iya auren sa ba, haba Abbah da wane ido zan kalli Anty Yasmin idan na aure shi”
“Da idon da kika kalle ni kika ce min kina son Asim”
Abbah ya faɗa a fusace yana zare mata ido. Anty Amarya tace
“Amman Namra ban taɓa sanin baki da hankali ba sai yau, Uzair ɗin ne kike faɗin ba zaki iya aurensa ba? Da me kika fishi toh?”
Karkato fuskarta tayi ta kalli Anty Amarya tana kuka
“Wallahi Uzair ba mutumen kirki bane, yace yana so na ne da wata manufa”
Anty Amarya ta nuna ta da yatsa
“Ke ai mutuniyar kirkice tun da Mahaifinki ya shimfiɗa miki tabarma, kika naɗe kika jefar”
“Wallahi Uzair ɗan homo ne Abbah, maza ya ke nema ƴan'uwansa”
Lokaci ɗaya ta ji ɗaukewar wutar cikin kanta, wanda hakan ya haddasa mata ganin waɗansu ƙananan taurari sakamakon wani irin mari da Abbah yayi mata, bata ankaro ba ya ƙara mata wani, be tsaya komai ba ya sake marinta, kamin kace kwabo sai ga jini ya gangaro ta hancinta kamar mai haɓo.
____________________
#Blog
#Comment
#Share
#Three-family
#Three-Team
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa05.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 5*
NAMRA POV.
Cikin takaici da jin haushi, Abbah ya nuna ta da tsaya.
“Ke baki isa kisa nayi magana ta tashi ba, a duk cikin ƴaƴana babu tsagerarra irin ki, bari kuma kiji na faɗa miki weather you like or not sai kin auri Uzair, idan kin haihu ranar da aka ɗaura miki aure da Uzair ki kashe kan ki”
A fusace ya juya ya fice. Anty Amarya ban da hawaye babu abunda take, sam bata ga laifin Abbah ba, dan tana ganin duk abunda yayi mata ita taja, ita ma kanta kwatankwacin abunda zata iya yi mata kenan, dan bata ga dalilin aibanta Uzair ba dan kawai bata son sa, kasa cewa komai ta yi ta juya cike da baƙinciki ta nufi ɗakinta.
Namra kan na risine gurin tana kuka, Maryam da Aisha na bata haƙuri.
Babu wanda zai fahimce ta saboda babu wanda yaga abunda ta gani, kuma bata da wata sheda da zata nuna.
Hajiya Barau ce ta ɗauki zancen tana yayatawa, wai Namra ta yi ma Uzair ƙazafi dan kawai bata son ta aure shi. Cikin sati maganar ta zagaye familyn su. Wasu kan sun yarda duba da irin kuɗin da suka taso masa lokaci ɗaya, sai dai kyakkyawan halinsa da mutane ke gani ya shafe wacan baƙin fentin da wasu suke ganin Namra ta shafa masa.
Hakan da Namra tayi ba ƙaramin sosa ran Uzair yayi ba, ko ba komai ta ɓata masa suna ta wani ɓangare, ga kuma rashin jutuwa daya samu da Matarsa Yasmin.
A ƴan kwana kin nan sai shiga cikin dangi yayi masa wuya, gani yake kamar sun yarda da abunda Namra ta faɗa, a waya wasu ke kiransa suna nuna masa abunda Namra ta yi bata kyauta ba, wasu har da yi mata Allah ya isa. Amman ita kan Yasmin ko a jikinta, sai ma sha'aninta take kamar abun be dame ta ba.
Babu irin faɗan da mahaifiyarsa bata masa akan ya janye maganar auren nan, amman ya ƙi saboda Abbah yaƙi bashi damar hakan.
“Uzairu ka janye zancen auren nan, ka faɗa maka, duk fa mutumin da yayi maka haka toh ko kashe ka zai iya yi, wannan ƙazafin data maka zai iya shafar har aikinka, ni ban taɓa ganin maƙiyiyi kamar Namra ba, ace ɗan'uwanka,
Aiko kama da gaske ne ka rufa masa asiri”
“Babu komai Umma Allah zai saka min, sai ta ga abunta inshallah”
“Allah dai ya isar maka, amman abun nan ya ɓata min rai matuƙa Wallahi, kai ma dai da hange-hange kake mi Namra take da shi daya fi na Yasmin har kake son aurenta”
“Wallahi Umma tun lokacin dana auri Yasmin ina jin son Namra, kuma wannan walimar da akayi na haddatan ƙur'ane kin san har da ita ciki, shiyasa naji na kwaɗaitu da zama mijinta dan na samu mai bawa ƴaƴana tarbiya, tun da ni da Yasmin ba wani dogon ilmin Islama ne da mu ba, sam ban tsammaci abun zai zama haka ba”
“Toh ai ko ilminta ya zama na banza tun da har ta iya yi ma ɗan'uwanta wannan ƙazafin”
Haka dai suka yi ta hirar Namra Hajiya Binta na tsine mata har aka kira Azahar.
A masallacin gidan yayi sallah, sannan ya koma ciki yayi ma mahaifiyarsa sallama ya fice. Babu abunda yake ji a ransa sai tsanar Namra, ji yake ko kashe ta yayi ba zai huce abunda tayi masa ba.
A dai-dai gate ɗin gidan su Amira yayi parking, sai ya fita ya taka da ƙafa, ya ƙwanƙwasa ƙofar gate ɗin. Mai gadi ne ya leƙo yana tambayar.
“Wanene?”
“Dan Allah Amira na ciki?”
“Eh tana ciki”
“Dan Allah yi min sallama da ita”
“Toh wa zan ce mata?”
“Ce mata manager ne”
Daga haka ya juyo ya dawo gurin motarsa, ya ciro wayarsa yana ƴan danne-danne. Ba a ɗauki dogon lokaci ba sai ga Mai gadin ya dawo yana faɗin
“Wai tace tana zuwa”
Tsayuwarsa ya gyara, yana kallon ƙofar gidan har ta fito.
Cikin rangwaɗa da isa take tafiya har ta ƙaraso kusa da shi da sallama.
“Maraba da sarauniyar kyau, gimbiyar mata, kuma adon mata, nasan ba ki san ni ba amman ni na san ki”
“Na sanka mana, ba kai bane Cousin ɗin Namra”
“I'm glad you remember”
“So what brought you here?”
“Ke ai ba sai kin tambaya ba, mace kyakkyawa irin ki mai hankalin da tarbiya, ai dole ne ta riƙa samun masu ziyartar ta a duk lokaci, son ki ne ya kawo ni, zuciyata ta kasa haƙura da ke na kasa haɗeye yawuna a kan ki, shiyasa kika gan ni a ƙofar gidan ku”
Cikin salon jan hankali yake maganar yana murmushi. Ita kuma sai wani yauƙi take abun ka da mata.
“Na ji matashin darasin ne kawai amman ban fahimcin karatun da yake cikinsa ba”
“Zan miki bita, na kuma fassara miki inda baki gane ba idan har mafaraucin zai samun ganin Gimbiya anjima?”
Shiru tayi tana fari da ido.
“Sai ka shigo, kuma idan ka zo karka tsaya a waje ka shiga harabar gidan, kar ka wuce ƙarfe tara”
“Consider it done my lady”
Buɗe motarsa yayi ya ɗauko bandur ɗin 1k ya miƙa mata.
“Ki shiga da wannan, zan yi farinciki”
A yadda ya karanceta be yi zaton zata karɓa ba, a take murmushi ya bayyana a fuskarta, tasa hannun biyu ta karɓa tana masa godiya
“Na gode sosai”
“Never mention it again, my regards to mom please”
Fari ta ƙara masa da ido
“Sure”
Ta juya ta shige. Wani shu'umin murmushi yayi ya buɗe motarsa ya shiga.
KALSOOM POV.
SIX MONTHS LATER.... Tun da ta dawo daga Seminar take bachin gajiya, ta taje aiki ta dawo sai bachi. Ga kuma ɓacin ran dake tare da ita, da tunani, dan ko ranar da zata tafi seminar ɗin sai da Dad yayi mata jan kunne akan ta kame kanta, ya sake maimata mata irin zagin da ake masa na yaƙi aurar da ita ya barta tana aiki sai yawa take gare gare, Babu kuma yadda zai hana ƴarsa aiki, dan da shi take yima kanta wasu laluraron ba dan kuma ya kasa ɗaukar nauyinta ba, sai dan rashin auren da bata tayi ba, idan har yace zai hanata aiki sai yaga kamar be mata adalci ba, kuma zai tauye mata haƙƙi damuwa zata mata yawa.
Sai dai burin iyaye ne suga sun aurar da ƴarsu sai idan hakan be samu ba, yadda zamani ya lalace komai girman ɗan ka dole ne kasa mishi ido gudun kar ɓata gari su lalata maka shi, musamman ƴa mace.
Ita kanta wani lokancin ba son zuwa seminer take ba, sai dai babu yadda ta iya tun da haka kamfamin MTN ya tsarawa ma'aikatansa.
A ɗayan ɓangare kuma tana ganin kamar iyayenta ba su yarda da ita bane, shiyasa suke takura mata da da yawan tambihi a duk lokacin da zata nisanta da su.
Tana ji a ranta har yanzu iyayenta ba su gama karantar ta bane, dan ta ɗaukarwa kanta alƙwarin duk irin sha'awar dake damunta da son auren da take ba zata taɓa aikata zina ba.
Da yamma ta tashi bachi, bayan ta ci abinci ta koma ɗakinta ta buɗe system tana duba wasu abubuwan. A ɗakin Momy ta same ta tana labarta mata hukuncin da mahaifinta ya yankena haɗata aure da Cousin ɗin ta Abubakar.
Gabanta ya faɗi, duk yadda take son aure bata jin zata iya auren Abubakar, mutumen da duk a familynsu an buga masa tambarin neman matan banza, neman mata kawai yasa ma gaba shiyasa auren ma kwata-kwata baya gabansa gashi yanzu har ya girmi tazurai, ba dan kuma ya rasa matar aure ba.
A cikin yanayin damuwa ta kalli Momy tace
“Amman Momy mi yasa ba'a nemi shawara na ba, kamin ku yanke wannan hukuncin?”
“Yayi hakan ne dan yasan ba zaki bashi kunya ba, kuma ba mahaifinki bane yayi masa magana, mahaifinsa na yayi ma Abbanki magana da amincewar Abubakar ɗin”
Girgiza kai tayi
“Gaskiya ni ba zan iya aurensa ba”
Wannan maganar da Kalsoom tayi ta fusata Momy har tasa ta canja fuska.
“Haba Kalsoom ana son a samu kiyi aure sai kuma kice ba zaki iya aurensa ba? Toh idan ba shi ba kina da wani wanda zaki iya fitarwa a yanzu ne? Ba zaki bar ruwan idon nan ba ko?”
Hannu biyu tasa ta dafe kanta. Sai yaushe Momy zata fahimcin matsalarta ne? Kullum cewa take tana ruwan ido, taƙi ta tsayar da miji, alhalin ba ruwan ido bane, duk mazajen babu na aure ko wanne da tasa matsalar.
Dagowa tayi ta kalli Momy tace
“Yanzu dan kawai ina son aure sai ace duk wanda ya zo min sai na aura? Abunda nake it not calling ruwan ido it calling carefully planning for the future”
Momy ta taɓe baki
“Yanzu dai idan kunya zaki bawa mahaifinki sai kiyi, naji ma yana faɗar baya son aja abun da nisa ina jin ba zaki wuce wata biyu a gida ba idan har kin yarda, kuma ni ban san Abubakar da wani mugun hali ba, yana da rufi asiri yana da kyau kuma baya shaye-shaye, neman mata ne kawai shi ma kuma bamu tabbatar ba tun da bamu taɓa kama shi yana yi ba,
Kuma yanzu ai da wahala ace maza basu san mace ba, ko kuma basu taɓa aikata zina ba, wata ƙila ma idan ya aure ki zai daina”
Idon Kalsoom ya cika da ƙwallah, ganin yadda Momy take gyara Abubakar dan kawai ta aure shi.
“Idan kuma be daina ba, ƴarki zata cutu, Momy kisa wannan a zuciyarki”
Momy ta dafata
“Kiyi auren dan ibada Kalsoom, kuma ki auri Abubakar da zuciya ɗaya”
Tashi Momy tayi ta fice, ta bar Kalsoom cikin tunani da neman zaɓin Allah.
____________________________
Masu karantawa a blogger ina ganin ku fa, amman baku comments, sometimes zan samu mutum 200+ sun leƙa website ɗin amman ba ku comments. Yadda kuka ga Wattpad haka Blogger yake zai nuna masu karantawa, amman babu Comments, ina fatar zaku gyara.
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa06.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
Ƴan Taskar Khadeeja Candy wannan shafi na ku ne. Ina jindaɗin Comments ɗin ku keep it up.🌺
*PAGE - 6*
NAMRA POV.
Har yanzu Asim baya ɗaukar wayarta, ta masa text ya fi a ƙirga, amman ba reply, kuma tun ranar da suka samu matsala bata sake saka shi a idonta ba, scul ma ya daina zuwa.
Hakan yasa ta yanke shawarar jan ƙawarta Amira su je gidan iyayensa, dan dubasa.
Haka kuwa akayi bayan an gama lacca, sun fito ita da classmates ɗin su, sai ta riƙa hannun Amira ta nufi hanyar library da ita.
Amira biye kawai take da ita, amman hankalinta na can wani gurin, sai tunani take.
Saman balcony suka zauna, kamin Namra ta yi magana sai Amira ta fara yi mata tambayar da ke cikin ranta.
“Namra kin ce da Uzair aka sa muku rana ko? Kuma kin ce baki son sa right?”
“Uhm”
“Ba taimakon ki zai yi ba?”
Namra ta yi mata kallon rashin fahimta
“Taimako kamar ya?”
“Haka dai na ji ana faɗa wai taimakon ki zai yi, dan Abbah ya bari ki auri wanda kike so”
“Kowa ya faɗa miki haka ƙarya ne, idan har zan nemi taimakon wani toh ke ce zaki riga kowa sani”
“Amman miyasa baki son sa?”
Shiru tayi, tana tunanin faɗa mata gaskiyar lamarin, sai dai tana jin har yanzu Amira bata kai matsayi da zata san sirrin gidan su ba, wannan matsalar ta cikin gida ce kawai, kuma ba komai bane zaka faɗawa ƙawa, dan ba kowa bane zai iya riƙe maka sirrinka, wani kuma zai yi kallon ka da abun ne, duk kuwa da amincin da ke tsakaninku.
“Amira so na ke ki raka ni gidan su Asim”
Ta ɗauko mata zancen ne, dan samun damar kawarda wancan tambayar da tayi mata.
Ajiyar zuciya Amira ta sauke, har yanzu kan ta kulle yake ta rasa dalilin da yasa Uzair ya yi mata ƙaryar yana son ta, kuma ya ƙulla alƙawarin zai aureta, lalai akwai wani abu a ƙasa.
“Zan raka ki mana, kwana biyu ya daina zuwa makaranta, nima ina tunani ko lafiya?”
Ta faɗa lokacin da Namra ta girgiza tana maimaita mata zancen.
“Tashi muje kamin four ta yi”
Namra taja hannunta suka tashi. Har suka isa gidan, Amira tunanin maganar Namra take, wani ɓangare na zuciyar na nuna mata lallai Uzair so yake ya yaudareta.
Namra nayin parking ta dafa Amira, ganin tun ɗazu hankalinta baya jikinta.
“Wai lafiya kike kuwa?”
Saurin buɗe motar ta yi, gudun kar Namra ta samu damar zargin wani abu.
“Lafiya ƙalau, fito muje”
Fitowa Namra ta yi gabanta na faɗuwa, a bakin ƙofar gidan ta tsaya tana tunanin abunda zata ce musu idan ta shiga.
Amira ce ta yi sallama taja hannun Namra suka kunna kai cikin gidan.
Ƙannen Asim ne suka amsa mata, mahaifiyarsa na haɗa ido da Namra, ta sauke kai ta cigaba da ƙullin zoɓonta kamar bata gansu ba.
Har ƙasa Namra ta risina ta gaisheta, yayinda Amira ta gaisheta a tsaye. Can ƙasan maƙoshinta ta amsa musu, fuska a haɗe kamar ta ga mutuwarta. Kasa magana Namra tayi, har sai da Amira ta ce
“Umma ko Asim na nan?”
Ɗago kai ta yi tana musu wani ƙazamin kallo.
“Ai ku zan tambaya, dan yau kusan sati uku kenan, ban saka Ibrahim a ido ba, tun ranar da ya zo nan yana hawaye yace kin cuceshi, ban sake ganinsa ba, ni kaina nemansa nake”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Namra ta faɗa idonta na ƙoƙarin cika da ƙwalla.
“Wani Innalillahi zaki yi? Ashe kin san Allah? Babu irin roƙon da ban miki ba akan ki rabu da Ibrahim amman kika ƙi, duk irin maganar da na masa a banza saboda idon sa, ya rufe akan ki”
Amira ta yi saurin saka bakinta.
“Wallahi Umma ba haka ba ne, ita kanta Namra tana son Asim, laifin mahaifinta ne”
“Ni ban tambaye ku laifin kowa ba, dan Allah ku fitar min daga gida, kuma wallahi sai Allah ya saka masa”
Har suka fito kuka Namra take, kasa tuƙa motar ta yi, sai Amira ce tayi driving ɗinsu.
“Yanzu ina Asim ya tafi? Duk abunda ya same shi ni ce sila, ba zan yafewa kai na ba”
“Namra ki daina kukan nan indai ba so kike muje gida a riƙa tambayar ki me ya faru ba. Ke ni fa ban ma yarda da zancen ta ba, ta ya za'a ce namiji kamar Asim ya bar gidan iyayensa dan kawai ya rabu da ke? Ai wannan fashion ɗin ya wuce”
“Zai iya saboda gudun waɗanda za su masa dariya, kuma ɓacin rai babu abunda ba ya sawa Amira”
“Amman ke dan Allah rabuwa da shi be fi miki alheri ba? Saboda shi kika ɓata da duk samarin ki, kuma mahaifinki ya ɓata da ke, shiyasa ma yanzu yake ƙoƙarin miki auren dole, abunda aka bar yayi tun kakanni”
Shiru Namra bata ƙara cewa komai ba har Amira ta yi parking a bakin gate ɗin gidansu Namra, dan bata jin shiga cikin gidan, ita ma kanta tana da nata damuwar.
“Ni dai zan wuce, idan kin gama kukan sai ki shiga da motar ciki”
Bata jira abunda zata ce ba, ta buɗe motar ta fice. Sai da Namra tayi kusan minti talatin a gurin sannan ta buɗe motar ta fito ta dawo mazaunin direba ta yi ma motar key tare da horn.
Mai gadin na buɗe mata gate, ta shiga da gudu har sai da tayi kaura da wata motar dake gabanta fake.
Buɗewa tayi ta fito, tana cigaba da kukan ta nufi part ɗinsu.
Anty Amarya na tsaye jikin window tana kallon abunda Namra ta yi, tasan Namra da zafin zuciya nan gaba har kanta zata iya jima ciwo da motar, ranta ya ɓace sosai, ita kanta ta damu da halin da ƴarta take ciki, sai dai babu abunda zata iya yi tun da ita ta jawo kanta haka tun farko.
Namra na shigowa Anty Amarya ta miƙa mata hannu.
“Bani makulin motar?”
Ba musu ta miƙa mata, tana share hawayenta, bayan Anty Amarya tace ta karɓi key ɗin tace
“ATM ɗin Abbanki yana nan na aje miki, shi ya aiko yace a baki yace ki ciri ko nawa kike so ki yi lalurarki, kuma yace ki samu ƙawayen ki ku rubuta events ɗin da zaku yi, on Wednesday za'a kawo lefen ki da IV”
Wani irin abu ta ji ya ratsa zuciyarta, idonta cike da ƙwalla ta kalli Anty Amarya.
“A tunani na uwa ce zata fi kowa fahimtar halin da ɗan ta yake ciki. Ke kika haife ni, ke kika raine ni har na kawo yanzu, ashe be isa yasa ki karance wacece ni ba? Ashe za'a iya zuwa a'ce miki nayi kisan kai kuma ki yarda? ”
Anty Amarya ta sauke ajiyar zuciya.
“Namra kin yi furucin ne a idan ba zan iya goge zanen rubutun ba, ba zan iya musu da Baban ki ba, idan har na goya miki baya wajen butulce masa duniya zata zage mu, shi kuma ayi masa dariya ace ƴar waje na tafi ƙarfin sa. Ban san dalilinki ba, amman nasan na za ki yi ma Uzair irin wannan sheirin ba haka kawai ba, amman ni da ke duk babu abunda za mi iya yi”
“Na gode da kika fahimta, na gode da zuciyarki ta raya miki ba ƙazafi na yi ma Uzair ba, Allah ya fahimtar da Abbah”
Anty Amarya tace
“Namra ina nan ina miki addu'ah, idan auren ki da Uzair ba alheri ba ne kada Allah ya bari ayi shi”
Da kuka ta rumgune Anty Amarya
“Na gode”
Anty Amarya ta riƙa hannunta suka zauna, ta soma tambayarta taya ta ga Uzair yana aikata wannan mummunan aiki na luwaɗi, kuma miye hujjarta.
Babu abunda Namra ta ɓoye Anty Amarya, tun daga lokacin daya fara nemanta, har zuwa lokacin data kamashi da friends ɗinsa da irin gargaɗin da ya yi mata.
Anty Amarya taja wani dogon numfashi ta sauke tana jinjina lamarin.
“Lallai Uzair ya cika tantiri, shine kuma ya zagayo ya zo neman aurenki?”
“Ina tunanin yayi hakan ne dan Anty Namra ta rufa masa asiri, tun da mijinta ne ai ba zata tona masa asiri ba, kuma kin ga yanzu data faɗa sai ta zama ita ce mai laifi”
Cewar Maryam tana riƙe ƙoƙarin zama kusa da Namra.
“Amman miyasa baki faɗa min ba tun farko? Miyasa kika kirashi a waya kika masa cin mutunci? da wannan ne ya zagayo yazo ya ɗaure ki a gurin Abbanki, miyasa ba ku shawara idan zaku yi abu?”
Namra ta share hawayenta.
“Ban zaci abun zai zame min haka ba, nayi tunanin zai ji tsoro ya janye maganar auren ne”
“A ƙasashen yahudawa Uzair yayi karatu, ya fiki iya makirci, kuma mai son abun ka ya fi ka dabara”
Maryam ta kalli Anty Amarya
“Yanzu meye abun yi?”
“Abun yi kawai mu duƙufa da addu'ah, daga ke har ita, kuma In'shallahu wannan aure Allah ba zai bari a yi shi ba, tun da akwai zalumci a ciki”
Sun daɗe zaune a falo suna firar, sannan Namra ta tashi ta nufi ɗakinta zuciyarta cike da sassauci. Daf da zata shige Maryam ta kira ta
“Anty Namra”
Juyowa ta yi, ta amsa murya a daƙishe
“Na'am”
“Ki sawa zuciyarki sanyi, Mama na tare da ke, nima ina tare da ke, Allah ma yana tare dake, kuma zai kawo miki mafita”
Daga inda take tsaye ta ɗan murmusa
“Na gode Maryam”
Ko ba komai ƴar hirar da suka yi, da goyan bayan da suka nuna mata, yasa ta samu kanta da ɗan sakewa, tsaɓanin baya da take ganin kamar ita kaɗai ce a cikin matsalar.
Daman komai na duniya yana son tattaunawa, ta haka ne zaka fahimci wasu, wasu kuma su fahimce ka, matuƙar kace zaka kulle sirrinka a zuciyarka, shine mataki na farko wajen gurɓata tunaninka, da jawa kanka ciwo.
Sai dai duk da haka maganar da Mahaifiyar Asim ta yi mata ɗazu ta tsaya mata a rai, cewar Allah sai ya saka masa, yasa jikinta sanyi, da kuma zancen bata san inda ɗanta yake ba.
“Ina ka shiga Asim? Miyasa zaka yi haka? Zaka lalata karatun ka, ka guji iyayenka saboda ni Asim?”
Rumgume filo ta yi, tana tuna ranar da yake labarta mata irin rayuwar da suka taso ta maraici shi da ƙannensa, da kuma irin wahalar daya sha kamin ya samu kuɗin registration, wanda shi ya hana shi shiga makaranta da wuri.
Lumshe ido tayi, tana buga kanta da hannunta. Wayarta ta sake ɗauka ta kira layinsa still switch off, sai kawai ta aika masa da sako.
Sannan ta kira Amira ta labarta mata yadda suka yi da Anty Amarya, da kuma goyon bayanta da suka yi a yanzu.
************
ONE WEEK LATER...
Wednesday tun da sanyi safiya Anty Amarya da Maryam suka fara shirya abunda za su tarbi masu kawo lefe dashi, snacks da meatballs da sauran abubuwa Hajiya Barau ce tace zata yi, dan ɓangarenta za'a kai lefen.
Tun safe Namra ta bar gidan, kasancewar ba su da lacca sai kawai ta yanke shawarar zuwa gidan su Amira. A can ta wuni tana aikin kuka, tun Amira na iya rarrashinta har ta gaji ta zuba mata ido.
Sai bayan sallah Azahar Amira take labarta Namra wai jiya taga Asim. Da sauri Namra ta kalleta.
“A ina kika gan shi?”
“Shi ya zo nan gidan, ya kara ni a waya na fito, kuma yace karka faɗa miki”
“Haba Amira? Baki faɗa masa halin da nake ciki bane? Wai da gaske kike ko wasa?”
“Na saba miki irin wannan wasan ne? Babu abunda ban faɗa masa ba akan halin da kike ciki, kuma nayi-nayi ya faɗa min inda yake zaune ya ƙi, Namra karki so ganin Asim duk ya koma wani iri”
Namra ta dafe kanta
“Wayyo Allah na. Da wace number ya kira ki?”
“Wata baƙuwar Number ce”
Ta ɗauko wayarta tana nuna mata number. Cikin rawar jiki Namra ta kofe number tasa a wayarta ta soma kiransa. Ƙasa-ƙasa Amira take kallonta har kiran ya katse ba'a ɗaga ba. Daga bisani sai aka kashe wayar gaba ɗaya.
Har aka yi Magariba Namra nata trying ɗin Number amman kashe.
“Ki haƙura da kiran nan Namra, idan ya ga dama zai kira ki tun da kin tura masa saƙo”
“Baki fahimci yadda nake ji bane Amira, ni kaɗai na san halin da nake ciki”
“Yanzu dai kin ga anyi magariba, ya kamata a'ce kin koma gida, nima kuma ina son na biki dan naga lefen, zaki ci abinci ko na haɗa miki tea?”
“Tea zai fi dan bana jin cin wani abu”
Tashi tayi ta fice daga ɗakin, sai gata ta dawo riƙe da kofin tea, yaji Lipton da ginger da lemun tsami sosai har ya canja kala.
Ta daɗe riƙe da kofin kamin ta miƙa ma Namra.
“Ki daure ki shanye, tun da baki ci komai ba, nasan kina jin yunwa zai taimaka miki”
Ba musu Namra ta karɓa, tayi bismillah ta riƙa kuɓa tea har ta shanye. Sannan ta tashi sukayi Sallah, sai Amira ta ɗauko Hijabinta ta saka suka fito.
Napep suka tsaida, dan Namra yanzu bata da Mota tun lokacin da Anty Amarya ta amshi key ɗin bata mayar mata ba, ita kuma Amira daman ba Mota ne da ita ba.
Magana suka masa yace zai kai su ɗari biyu, sannan suka shiga.
Be aje su ko'ina ba sai ƙofar gidan su Namra, Amira ce ta biya kuɗin, sannan suka fito suka shiga cikin gidan.
A falon Anty Amarya suka tararda ƙannenta biyu, Hajiya Lariya, da Mama Zainab.
Cikin ladabi Namra ta gaishe su, suka amsa suna mata fatan alheri, sai yaba lefen suke suna shi masa albarka.
Ita dai bata ce komai ba, idonta dai cike da ƙwalla, sai Amira ce take amsawa da
“Amin”
Fitowar Anty Amarya ne yasa Namra tashi tsaye, ta kalleta.
“Kin dawo?”
Nan ma Amira ce ta amsa
“Eh, Anty ina wuni?”
Anty Amarya ta lura da hawayen da suka idon Namra, kuma bata son ta yi kuka har ƙannenta su fahimcin halin da take ciki, sai ta yi saurin cewa Amira.
“Lafiya Ƙalau, Amira ku shiga ɗaki”
Hannun Namra, Amira ta riƙa suka nufi ɗakinta.
Saman gado suka zauna, sai Namra ta kwanta jikin Amira tana kuka, jikinta duk ya mace kamar marar lakka.
Amira ta ciro wayarta dake cikin pose, tayi ƴan danne-danne sannan ta mayarda wayar, ta cigaba da rarrashin Namra tana bata Haƙuri.
Ba'ayi minti ashirin ba, sai ga kira ya shigo wayar Namra, da number da Amira ta bata tace mata number Asim ce.
Cikin rawar jiki Namra tayi picking ta kara akunne tana.
“Asim! Asim!! Asim!!! Dan Allah kayi magana”
Shiru ba a amsa mata ba, daga bisani sai aka kashe wayar. Kira ta riƙa aika ma number amman ba'ayi picking ba, bayan kamar minti biyar sai ga sako ya shigo wayarta.
‘Namra ki fito yanzu, ina son na yi wata muhimmiyar magana da ke, ina nan bayan layin ku ta gurin gidan Alhaji Sani’
Tana gama karantawa ta nunawa Amira, sai Amira ta riƙe ta
“Namra karki je...”
Sai kuma ta yi shiru kamar wacce ta tuno wani abu, sai ta kalli Namra da ke kallonta tace
“Amman idan ba wannan ba, ba ki da wata dama ta ganinshi, kuma idan ba kije ba zai iya fushi da ke”
Namra ta sauke ajiyar zuciya
“Zaki raka ni?”
“A'a ni ba zan je ba, kar a shigo ɗakin ba kowa, kuma idan mun fita tare za'a zarge mu, wata ƙila ma Asim ya kasa yin magana da ke idan yaga muna tare, amman me zaki ce wa Anty idan ta gan ki?”
“Nima ban sani ba, kuma idan har na faɗa mata ba zata bar ni naje ba”
“Toh karki faɗa mata, kibi ta ƙofar kitchen ki fita, zan jira ki a nan har ki dawo”
Ba tare da fargabar komai ba, Namra ta tashi ta nufi ƙofar fita.
Sai da ta fice sannan Amira ta ɗauki wayarta ta kira number, ana ɗauka ta ce
“Gata nan zata fito yanzu”
Namra na fitowa taga Anty Amarya na zaune falo tare da ƙannenta suna hira. Da faɗuwar gaba Namra ta nufi kitchen ɗin, tayi sa'ah babu kowa a ciki.
Hakan ya bata damar buɗe ƙofar a hankali ta fice. Da wage-wage ta isa gate, nan ma a hankali ta soma buɗe ƙofar, sai ga mai gadi ya taso ya nufo ta yana tambayar lafiya.
Dan ya san indai ba dolen-dole ba babu abunda ke fitar da su da zarar anyi sallah magariba, dan Abbah baya son fitar dare.
“Lafiya ƙalau, saƙo zan karɓo nan baya, yanzu zan dawo”
“Toh Allah ya tsare”
Sai ya maida ƙofar ya kulle. Sauri-sauri take tafiya tana wage, sai kiran wayar take amman anƙi picking.
Sai data kai ƙarshen layin, sannan ta karya kwana ta nufi gurin daya kwatanta mata, jiki babu ƙarfi sai jin take kamar ta faɗi, dan ƙafafunta basa iya ɗaukarta.
Kamin ta ƙarasa taji kamar ana binta a baya da mota, ta ɗan ji tsoro daman da fargaba ta fito gida, kasancewar unguwarsu ba kasafai zaka ga mutane ba ko da rana balle da dare, ga kuma fargabar kar wani ya ganta yaje ya faɗa a gida. Tsayawa tayi tana kallon ƙatuwar Bus ɗin mai baƙin gilashi.
Wasu maza ne guda huɗu suka fito ɗaga ciki Bus ɗin suka nufo ta ciki har da Uzair, ganin Uzair ne ya hana ta gudu daman can bata jin ƙarfin gudun, sai ta tsaya tana masa kallon mamaki da tunanin me ya kawo shi nan.
‘Daman yana biye da ni kenan? So yake ya tona min asiri yace ya gan ni na gana da Asim da dare ko me?’
Kiran daya shigo wayarta ne ya ankarar da ita daga tunanin da take. Number ce wanda aka turo mata saƙo da ita da sunan Asim ne. Da sauri ta kalli Uzair daya ƙaraso kusa da ita
“Uzair daman kai ne? Ko kuma wayarsa ka karɓa?”
Ta tambaya a kasale, jiri na ƙoƙarin ɗaukarta.
Murmushi kawai ya yi mata, ya kai hannu ya riƙo ta iya ƙarfinsa.
A nan Allah ya bata ikon yin ihu da dukan muryarta. Cikin sauri mutumen dake tare da Uzair ya fitar da wani ƙyalle ya danne mata hanci dashi, daga nan bata sake sanin inda take ba, sai numfashinta ya ɗauke dif.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa07.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED⚠
*PAGE - 7*
A hannunsa ta suma, sai ya ɗauke ta ya miƙawa mazan da yake tare da su yana faɗin
“Ku shiga da ita, kuma ku tabbatar bata farka ba, har sai na dawo”
“Yes Boss”
Cikin girmamawa suka amsa, suka saka ta cikin Bus ɗin. Sai da Uzair ya ga sun bar gurin sannan ya nufi ƙofar gidan Alhaji Sani inda yayi parking ɗin Motarsa.
Bude Motar yayi ya shiga, ya ɗauko wani turare ya fesa, sannan yayi ma Motar key. Ribas yayi ya dawo ta bayan layin sai gashi a bakin gate ɗin gidan su Namra.
Horn yayi mai gadin ya buɗe masa yana gaisheshi. Guri ya samu a harabar gidan ya yi parking.
Sai ya fita ya taka da ƙafa ya isa part ɗin Abbah, dan yaga motarsa a waje, alamar yana nan kenan.
Hankalinsa kwance ya shiga falo, Abbah na kishimgiɗe yana duba jarida, Uzair ya shigo sai yayi saurin zubewa ƙasa yana kwasar gaisuwa.
Da far'ah Abbah ya amsa, yana nuna masa gurin zaman, bayan sun gama gaisawa, sai Uzair yayi shiru be ce komai ba har sai da Abbah ya kalle shi ya ce
“Uzair kana da wata magana ne?”
Abbah ya tambaya, yana mai jin son Uzair ɗin a cikin ransa, kusan ma ya fi kowa jindaɗin wannan haɗin, dan Allah ya sa masa son Uzair shiyasa komai na harkar kasuwancinsa sai ya saka shi, duk kuwa da cewar shima yana da ƴaƴa maza.
Sun-sun ya yi da kai
“A'a Abbah, akan maganar IV ne na mata, har yanzu Namra bata rubuta ba, kuma lokaci na tafiya, shine Hajiya tace na zo, na mata magana, shine nace bari na gaishe ka”
Abbah ya yi murmushi irin nasu na manya, sannan ya yi gyaran murya yace.
“Uzair sai ka yi haƙuri da lamarin Khadija, har yanzu akwai ƙurciya a tare da ita, kuma ita ba zata gane alfanun wannan auren ba har sai anyi, haƙiƙa ina son Khadija matuƙa sai dai tayi tsalle ne da ɓata rawarta tun daga lokacin data tsaya kai da fata akan lalle ita sai wannan yaron,
na bata dama na fitar da wani ta ƙyale wannan yaron amman sai ta buga min ƙafa a ƙasa ita sai Asim, shiyasa kaga na fita lamarin ta, saboda so da yawa zaka abunda mu iyaye muke hangowa ba shi ƴaƴa ke hangowa ba, a tunanin ta na yi mata hakan ne dan na cutar da ita, tun da ta nuna bata so.
Nasan anbar auren dole a yanzu, amman duk abunda na yi ma Namra ita ta jawa kanta”
Abbah ya ɗaga kai ya sake kallon Uzair da kyau yana mai nuna masa abunda yake faɗi a bakinsa shine a zuciyarsa.
“Uzairu ina fatar zaka riƙa Khadija da amana, kuma zaka nuna mata so da kulawa, irin son da zata san lallai ta yi dacen mahaifinta be mata mugun zaɓi ba, ina son ka sani duk abunda ya samu Namra ni ya sama, kuma zai taɓa mahaifiyarta, ina addu'a wannan aure Allah ya sa masa albarka, ya baku haƙuri zama da junanku”
Jikin Uzair yayi san yi sosai da kalaman da Abbah yayi masa, sai yake jin kamar Abbah ya san abunda yake son aikatawa.
Cikin rashin kuzari ya yi ma Abbah sallama, ya tashi ya fice.
Har ya iso gurin motarsa tunanin kalaman Abbah yake.
‘Abunda duk ya sami Khadija ni ya sama’
Same shi ya fi tsaya masa a rai, tunani yake what if Abbah ya gane gaskiyar dalilinsa na neman aurenta? Shi kuma baya jin yana da wata mafita ta rufa ma kansa asiri bayan wannan, tun shi dai ba zai ce zai kashe Namra ba, gashi ta ce sai ta tona masa asiri.
Ya kwashe minti arba'in a gurin yana tunani, ba tare da ya sani ba. Can sai ya nufi gurin Mai gadin yayi masa magana kan ya shiga yayi masa sallama da Namra.
Cikin girmamawa mai gadin ya nufi part ɗin Anty Amarya, shi kuma ya dawo gurin Motarsa ya tsaya ransa a jagule.
In few minute Mai gadin ya dawo ya shaida masa ance gata nan zuwa. Chanji ya fiddo a aljihunsa ya miƙawa Mai gadin, sannan ya gyara tsayuwarsa yana jiran fitowarta.
Lokacin da Mai gadin ya shigo falon, Anty Amarya, na zaune tare da ƙannensa suna cin abinci, sai tace da Mai gadin yace tana zuwa, sannan ta tashi Maryam ta ce taje ta kirata ɗakinta.
Maryam ta aje littafin dake hannunta ta tashi ta nufi ɗakinta. Tana yin sallama Amira ta zabura kamar marar gaskiya.
“Anty Amira, ina Anty Namra?”
Shiru tayi tana dube-dube kamar mai neman abu, can kuma ta kalli Maryam tace
“Maryam idan na faɗa miki wani abu zaki fahimta ai ko?”
“Uhmm minene?”
“Namra ta fita ɗazu, Asim ne yayi mata texs wai yana son ta zo suyi sallama, shine ta fita tun ɗazu”
Gaban Maryam ya faɗi
“Amman kika barta taje ita kaɗai? Idan wani abun ya same ta fa?”
Shiru tayi tana tunanin ƙaryar da zata ƙaƙaro
“Ba yadda ban yi ba, amman tace ba zan bita ba, wai na tsaya kar a zo nemanta ba'a ga kowa ba, amman bari na kirata”
Cikin sauri ta shiga kiran wayar. Maryam bata tsaya ba, ta juya ta fita.
Daga bakin ƙofa ta tsaya tana kiran Anty Amarya. Daker ta taso saboda abincin da suke ci da kuma firar da suke da ƴan'uwanta.
A tunaninta Maryam zata ce mata Namra taƙi zuwa ne, sai kawai taji wani labari banbaragwai. A take Anty Amarya ta ɗauko wayarta ta shiga kira amman ba a picking.
Sai duk hankalinsu ta tashi, Anty Amarya ta koma ɗakin Namra ta samu Amira zaune tana faman kiran waya.
Anty Amarya ta katsa mata tsawa.
“Ina tace miki zata?”
Jiki na rawa ta amsa ma Anty Amarya dan ta ga ranta ya ɓace sosai.
“Tace min nan bayan layi”
“Amman dai Anty Amira kin yi wawanci Wallahi, shine kika bar ta taje? Maimaiko ki hanata ko ki faɗawa Anty, kuma kika ƙi binta kuje tare”
Maryam ta faɗa tana hararar Amira. Anty Amarya tace
“Ita ma Namra ai da wayon ta”
“Ko da wayonta ai wani abun sai an nuna mata, tun da kinsan yadda Anty Namra take ko ni sai na fita wayo, waya sani ma ko da ke ya haɗa kai kika lallaɓa masa ita ta tafi”
Amira ta kalleta
“Haba Maryam wane irin magana kike haka ne? Kina tunanin ni zan iya cutar da Namra?”
“Waya sani abu a duhu, ƙawayen yanzu ai ba abun yarda bane, kuma Wallahi duk abunda ya samu Namra ki ƙaddara ke ya sama dan ba zan taɓa yafe miki ba”
Amaimakon Amira tayi magana sai kawai ta fashe da kuka, ta tashi ta ɗauki pose ɗinta ta fice tana kuka.
Anty Amarya sai ta hau Maryam da faɗa
“Wai Maryam ba zaki bar fitsarar nan ba ko? Kullum ina miki magana kan shegen bakin nan naki amman baki ji, yanzu miye na wannan furucin fisabillahi? Ita Namra ƙaramar yarinya ce da Amira zata ɗorata a layi ta hau?”
Maryam ta tunzure baki.
“Wallahi zata iya ɗora ta a layi wannan Amirar da kike gani shegen wayo ne da ita, kuma Wallahi tun ba yau na lura kamar tana hassadar Anty Namra, wani fa sam baya son yaga cigaba a gareka sai ci baya, kuma wani maƙiyi na ɓoye ba gane shi ake ba”
Anty Amarya ta katsa mata tsawa
“Zaki je kiyi magana da Uzair, ko tsayawa zaki yi, kina ƙara min ɓacin rai”
Juyawa tayi ta fita tana faɗin
“Wallahi duk wani abu ya samu Anty Namra Amira zan zarga”
Ɗakinta ta shiga ta ɗauki Hijabinta ta saka, sannan ta fito ta nufi harabar gidan gurin da Uzair yake, tana harararsa.
“Bata jindaɗi ba zata iya fitowa ba”
Ta faɗa ba tare data masa sallama ba, kuma bata tsaya jiran abunda zai ce ba ta juya tayi tafiyarta.
Wani kallo ya bita dashi, daman duk cikin Family Abbah Maryam tafi uban kowa tsageranci. Buɗe Motarsa ya yi ya shiga zuciyarsa cike da tunane-tunane, hannu yasa ya shafa kansa, sai ya ciro wayarsa ya nemo wata number ya danna mata kira.
Ana yin picking ya ce
“Tahir kana ina?”
Ban ji me aka ce masa ba, sai kawai yace
“Ok gani nan zuwa yanzu”
Daga haka ya kashe wayar, ya ƙarama gudu. Can kaɗai ne yake jin zai iya tafiya ya fayyace sirrinsa, tun da duk akan layi ɗaya suke.
Sai da ya yi tafiya mai nisa, sannan ya isa bakin wani ƙaton gate.
Horn yayi mai gaɗin ya buɗe masa sannan ya kunna kai cikin ƙaton guesthouse ɗin. Parking ya yi, ya fito ya nufi hanyar shiga gurin. Zazzaune ya tararda su, Tahir da Najeeb. Tun daga ganin yanayin shigowarsa sun san akwai wani abu a ƙasa. Tahir ne ya fara magana
“Lafiya kake Uzair?”
Bakinsa ya cika ma iska ya busar
“Wallahi ina cikin matsala”
“Matsalar me?”
Najeeb ya tambaya, cike da son sanin abunda ke damun amininsa.
Uzair be ɓoye aminansa komai ba, tun daga ganin da Namra tayi ma friends ɗinsa na Abuja har zuwa nemanta da yayi, kuma kalaman da Abbah yayi masa yanzu, sannan ya ɗora da sace ta da yayi.
Tahir ya girgiza kai
“Uzair you Fuck up, ai yin wannan abun da kanka matsala ne, mun riga mun san junan mu toh miye na ɓoyewa kasa kanka a matsala? Yanzu ka sace yarinyar mutane kana ganin asirinka ba ze tunu ba?”
“Nayi tunanin zan iya solved ɗin matsalar ne, da nayi nufin na riƙe ta ne har kwana biyu ta yadda za a yi tunanin ta gudu da bi saurayinta ne. Ga Yasmin ta juya min baya na rasa gane kanta, kuma yanzu idan ta dawo zata iya faɗa asirina ya tonu kuma kasan komai ze iya faruwa, family ni za a zaga kuma.mahaifinta ba zai ƙyale ni ba”
Tahir ya dawo kusa da shi ya dafa shi.
“Ka kwantar da hankalinka, irin wannan yarinyar ta dabara bata musu, kuma irin wannan sirrin ba a sake da shi”
Najeeb yace
“Lallai kam, irin wannan yarinyar malamai za a shiga da ita, fiussss an gama da ita”
Tahir yace
“Shine kawai, yanzu kaje kayi abunda zaka yi da ita, kasa a maida ita gida kamin asuba, zan rubuta maka wani magani ka bata tasha zata manta abunda ya faru, idan Jafar ya dawo zamu zauna mutattauna”
Murmushi jindaɗi yayi, yajin ya samu mafita gurin abokansa.
Cikin kuzari ya tashi bayan Doctor Tahir ya rubuta masa maganin a takarda, ya yi musu sallama ya fice.
__________________________
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖😘🌺
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 8*
Yana cikin mota yana driving zuwa guesthouse ɗinsa, kiran Najeeb ta shigo wayarsa. Picking yayi ya kara a kunne sai ya mai da tuƙin da hannu ɗaya.
“Hello”
“Uzair kana ina? Ka isa gidan ne?”
“A'a gani dai kan hanyar zuwa siyen maganin”
“Karka siyo ka wuce gidan kawai, idan ka isa ka jira ni gani nan zuwa, kuma ka tabbatar bata farka ba, idan kuma ta riga ta farka, karka bari ta gan ka, ina ka aje ta?”
“A guesthouse ɗina”
Sai ya kashe wayar, ya ƙara ma Motarsa gudu. Yana isa, Najeeb na isa. Sai duk suka yi saurin fitowa Motar. Najeeb ya nufi shi yana faɗin
“Yanzu ya kamata mu mai da ita gida”
“Taya?”
Najeeb ya kalli ko ina na gurin, sannan yace
“Ni zan kaita, faɗa min inda ka ɗauke ta, zanje can na maidata, zamu saka mai gadin nan naka ya je a inda take ya riƙa ihu da neman taimako har mutane su taru su, su nuna masa gidansu, zai bamu haɗin kai dai ko?”
“Me zai hana indai an bashi kuɗi”
Uzair ya faɗa.
“Okay zan tsara masa yadda zai yi, miye sunan Saurayin nata?”
“Asim sunan shi Ibrahim, amman anfi saninsa da Asim”
“Good yanzu kira ɗaya daga cikin masu tsaronta ya duba mana idan bata farka ba”
A take Uzair ya ciro wayarsa. Najeeb kuma ya nufi gurin mai gadin.
Ɗaya daga cikin yaran ne suka shaida masa har yanzu bata farka ba. Shi kuma ya nufi Najeeb ɗin ya faɗa masa.
Sai da Najeeb ya gama tsarama mai gadi yadda zai yi, sannan ya juyo gurin Uzair.
“Good yanzu kasa su ɗauko ta, su saka ta a mota na, sai ka shiga taka motar ka nuna mana daidai inda ka ɗauke ta”
“Baba Audu zaka iya ko?”
“Ƙwarai Zan iya ranka ya daɗe ai wannan abu ne mai sauki, kuma taimako ne”
Baba Audu ya faɗa da kansa. Sai Najeeb yayi murmushi.
“Zamu baka dubu ɗari idan aiki yayi kyau, zamu baka wasu dubu ɗari na rufar sirri, ka tabbata dai ba'a samu matsala ba”
Har ƙasa Baba Audu ya risina yana godiya baki har kunne.
“Allah Ubangiji ya saka da alheri, ai ni ko baka bani komai ba, zan iya maka fiye da wannan”
Najeeb ya nuna masa Mota.
“Kaga Mota can je ka shiga gidan gaban”
Sai kuma ya kalli Uzair
“A fito da ita yanzu”
Cikin sauri Uzair ya nufi gurin, be daɗe ba ya fito, wani namiji na ɗauke da ita. Ita kuma ta langwaɓe kamar wacce ta mutu.
Najeeb da kansa ya bude Motar suka saka ta gidan baya. Sannan Najeeb ya shiga driver seat, Baba Audu ya shiga front seat, Uzair kuma ya shiga Motarsa, sai ya shiga gabansu dan nuna musu hanya.
Cikin mintuna suka isa gurin. Can nesa da gurin suka faka, sai Najeeb ya buɗe motar ya fito da ita. Uzair ya nuna dai-dai inda ya ɗauketa sai Najeeb ya ajeta a gurin, yasa car key ɗinsa ya ɓarke mata Hijabi, ya yagashi, ya barƙa rigar afamfar dake jikinta, har rabin breast ɗinta ya fito.
Sanna ya ɗago ya kalli Uzair
“Ta fito da waya?”
“Yes ga wayar ta nan hannu na”
Ya faɗa yana ƙoƙarin cirota daga aljihunsa. Najeeb ya miƙa masa hannu
“Wani wayar zan taka ta da mota, kuma ka bani layin da ka kira ta da shi”
“Why?”
Najeeb yayi masa wani kallo
“Haba Uzair ya kake abu kamar ba wayaye ba? Baka san za'a iya amfanin da wayar a gano sawon hannunka ba? Za a iya gano ka idan kana amfani da layi, kuma yanzu ai amfanin layin ya ƙare”
Kamin Uzair yayi magana, kiran Amira ya shigo wayarsa. Da sauri Najeeb ya tambaya.
“Who's calling?”
“Her Best friend”
“Did she know?”
“Yes tare da ita muka haɗa komai”
“Karka yi picking call ɗin nan it risk, let's go kar wani ya gan mu”
“Da wahala wani ya gan mu, baka ga yanayin gurin ba? Ko da rana ba a cika wucewa ba balle yanzu pass 11 fa”
Najeeb yayi murmushi, irin na har yau baka waye ba Uzair. Sai kuma ya kalli Baba Audu
“Da ka daina hango hasken Motar mu, zaka fara ihun”
“Toh ranka ya daɗe”
Cikin sauri suka nufi motocin su, Najeeb sai wage-wage yake kamar mai neman wani.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa09.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 9*
A lokacin da Baba Audu ya daina hango su, sai ya buɗe dukanin muryarsa ya kwarara uban ihu yana neman taimako.
“Wayyo Allah jama'ah a taimaka mana, a ceto rai, jama'ah ku kawo agaji”
A yanayin gurin, ba kowa bane zai iya saurin fita, saboda yanayi na tsoro da ake ciki, gashi ta bayan layin unguwar ne ba mutane sosai.
Cikin ƙarfi hali da bugawar zuciya, Baba Audu yake ta kwarara ihun yana wage-wagen jiran wanda zai fito.
Tsinta-tsinta aka fara fitowa ana nufar gurinsa, sai tambayarsa suke lafiya. A nan ya soma ƙirƙiro hawayen ƙarfin hali yana faɗa musu abunda Najeeb ya tsara masa.
“Wallahi wasu mutane yanzu suka jefo da wannan yarinyar daga mota, kuma suka zo suna ƙoƙarin taɓa mata mutunci”
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Shine abunda kowa yake faɗa, dan makamacin wannan be taɓa faruwa a unguwar ba. Wani dattijo ya kai hannu ya gyara mata Hijabinta, ta yadda zai suturta mata breast ɗinta dake buɗe.
Waɗanda suka santa sun gane ta, sai dai kowa mamaki yake, yana tunanin suye ne suka mata haka? kuma a ina ta haɗu da su haka.
Wani saurayi ne ya kawo ruwa aka zuba mata, amman shiru bata farka ba, haka akayi ta zuba mata ruwan but still bata motsi. Anan mutane suka ce a ɗauke ta a kaita gidansu
*** *** *** ***
Babu irin kiran wayar da Anty Amarya bata yi ma Namra ba, tun tana ringing har aka kai ga kashe wayar.
A lokacin hankalinta ya tashi sosai, ita da Maryam har Aisha da Hindatu sai da hankalinsu ya tashi.
A take Anty Amarya ta fara kuka, tana tunanin abunda ze samu ƴarta, kuma tana tsoron kar Abbah yaji, sai duk tabi ta rikice ita da Maryam. Aisha da Hindatu suka ce zasu je bayan layi su duba ko Allah yasa zasu same ta.
Anty Amarya ta share hawayenta.
“Babu inda zaku je cikin daren nan, bayan layi da yake da duhu idan wani abun ya same ku fa, ban san abunda yasa Namra ta raina ni ba, ta ya zata saka ƙafa ta fita ba tare data faɗa min ba? Duk abunda ya same ta ita tajawa kanta”
Maryam ta ɓata fuska.
“Gaskiya Anty Namra bata kyauta ba, amman da kin bari munje mun duba ko zamu ganta”
“Babu inda za ku je, idan Abbah ku ya gani kuce masa me?”
“Abbah ba ze gani ba, tun da yana part ɗinsa, kuma ba daɗewa zamu yi ba, dubowa kawai zamu yi mu dawo”
“Babu inda za ku je yanzu goma ta wuce, inda har kuna jin magana ta, toh karku je ko ina nemanta, ai ita ta kai kanta, ina zaune falo tabi ta ƙofar kicin ta fita, ba dai-dai bane tasa ƙafa ta fita ba tare da sani ba”
Anty Amarya na gama faɗar hakan, ta tashi ta nufi falo tana hawaye. Yanzu kan babu abun ɓoyewa dole ta faɗa ma ƙannenta abunda yake faruwa, su kansu basu jidaɗi ba, sai laifin Namra suke gani, wai taya zatayi haka kamar wata ƙaramar yarinya.
Haka suka yi zaune jugum, kowa sai addu'ah yake, babu irin roƙon da Mama Zainab bata yi ma Anty Amarya ba akan ta bari suje su dubota, amman ta hana.
Har kusan shaɗaya babu wani labari, sai shabiyu saura kwata, suka soma jin hayaniya a habarar gidan, sai doko musu sallama ake da muryar maza.
Wani irin faɗuwa gaban Anty Amarya yayi, har sai da ta dafa zuciyarta ta lumshe ido. Mama Zainab da Hajiya Raliya ne suka riga fita, Aisha da Hindatu suka rufa musu baya.
Maryam kuma ta tsaya kusa da mahaifiyarta ganin halin da take ciki. Cikin ƙarfin hali Anty Amarya ta tashi, Maryam ta ɗauko mata hijabinta ta saka sannan suka nufi ƙofar fita.
Ko da suka fito har Hajiya Barau ta isa gurin, Abbah kuma ya fito daga part ɗinsa ya nufi gurin da mutane suke tsaye, riƙe da Hannun jikan Imam jikan Hajiya, da alama shi ya je ya faɗawa Abbah.
Cike da kasala Anty Amarya ta ƙasara gurin ita da Maryam. Tana ganin halin da Namra take cike gabanta ya ƙara faɗuwa, a take kasala ta sauki mata. A nan Maryam ta fara kuka ganin Namra kwance kamar matatta ga Hijabinta a yage.
Abbah ya kalli mutanen cikin tashin hankali.
“Miya faru? Ina kuka ɗauko Khadija?”
Kowa sai ya nuna Baba Audu yana faɗin shi ne san abunda ya faru, tun da yace musu a gaban idonsa akayi. Tun kamin Abbah ya tambaye shi ya shiga yi masa bayani.
“Na fito ne gidan ƙanena can baya, sai na hango wata ƙatuwar mota mai kamar ta ƴan makaranta ta tsaya, a gefen gurin sai aka jefo wannan yarinyar , sai kuma suka fito su huɗu suna ƙoƙarin cire mata tufafi, shine fa sai na fara musu ihu suka gudu suka shige motar, bayan sun wuce ne, na ƙarasa inda take ina neman taimakon jama'ah ganin halin da take ciki, da jama'ah suka fito sai suka ce sun santa a nan gidan take, dan ni ba ɗan unguwar nan ba ne ban san ta ba Wallahi”
Wani irin abu ne ya taso ma Abbah, tun daga kan ɗan yatsan ƙafarsa zuwa ƙasan zuciyarsa, a take kalar idanunsa suka canja, wata jijiyar ɓacin rai ta taso masa, ta ratsa gefen wuyansa zuwa kansa, a hankaɗe ya kalli Anty Amarya.
“Yaushe ta fita?”
“Wallahi... Ban ...san ...ta fita ..ba ...”
Anty Amarya ta amsa murya na rawa. Abbah ya katsa mata tsawa
“Baki san ta fita ba kamar ya? Taya zata fita ba tare da kin sani ba?”
Kamin Anty Amarya ta ƙara bashi amsa, sai mama Zainab ta yi ɓaranɓarama, a ƙoƙarin kare Anty Amarya.
“Wallahi duk muna falo ta fita, babu wanda ya san da ita, ta hanyar kitchen ta bi, wai zata yi sallama da saurayinta”
Anty Amarya jin tayi kamar ta matse bakin Mama Zainab amman ba dama.
“Junaidu!”
Hajiya Barau ta ƙwalawa mai gadin kira. Da sauri ya amsa dan yana kusa da ita, yana kallon Namra dake kwance cike da mamaki.
“Ya aka yi Namra ta fita? Ba dokar gidan nan bace idan anyi magariba ba wanda ze fita?”
Jikinsa ya hau ɓari, yana ƙoƙarin ƙare kansa.
“Wallahi sai da na yi mata magana, sai tace wai saƙo zata karɓo nan kusa, ni sam na manta ma da bata dawo ba sai yanzu”
Abbah ya kalli Baba Audu
“Kasan mutanen ne? Zaka iya gane su?”
Baba Audu ya yi shiru kamar mai nazari.
“Gaskiya ba zan iya gane su ba, amman dai na ji suna faɗin Aasimu ko Ƙasimu, suna ce masa ya yi sauri su tafi”
“Asim..!”
Abbah ya amsa da ƙarfi. Sai kuma ya sauke ajiyar zuciya, ya kalli mutanen.
“Na gode sosai, Allah ya saka ma kowa da alheri”
Sai da suka masa Allah ya kyauta, sannan suka fita kowa bakinsa ƙunce da magana, wasu kuma mamakin fitar da ta yi suke, ga kuma ɓarin zancen da Mama Zainab ta yi.
Maryam ta nufe ta tana faɗin
“Abbah akai ta asibiti, duba fa bata motsi”
Juyawa Abbah ya yi ya nufi part ɗinsa rai a ɓace. Hajiya Barau ta ce
“Daga ta zan ɗauko mota akai ta, ai kisan halin Abban ku sai dai ta mutu a nan”
Hajiya Barau ce taja mota, da taimakon Hindatu da Mama Zainab suka sa Namra a mota, suka nufi asibitin dake kusa da su.
Suka bar Anty Amarya da Maryam suna aikin kuka, Hajiya Raliya na bata haƙuri, sai kawai Aisha ta yanke jiki ta faɗa iskokanta suka taso.
*** *** ***
Suna shiga Uduth, aka wuce da ita emergency, da sauri Nurses suka karɓe ta, aka ɗorata akan gado, suka shiga da ita wani ɗaki, taimakon gaggawa suka shiga bata kamin Likitoci su iso.
Ba a fi minti biyar ba, Doctor Hilal ya shigo cikin manyan kaya, hannayensa zube a aljihu, tare da wani likita, hankalin kwance ya ƙarasa inda take kamar ba marar lafiya ze duba ba.
Duk natsuwa Nurses ɗin suka yi suka ja da baya suka bashi guri. Hannu ya kai ya taɓa gefen wuyanta, yana kallon agogonsa hannunsa, sannan ya kalli drip ɗin da aka ɗora mata.
“Ku cire mata drip ɗin nan sai numfashinta ya dawo, ku kira Doctor Adamu ko wani likitan, da wannan ba aikin Likita ɗaya ba ne”
Yana kaiwa nan ya juya, sai Likitan da suka shigo tare ya yi saurin cewa.
“I'm sorry Doctor, Doctor Adamu is not around, that's why i call you”
Juyowa ya yi ya kallesa
“Wannan ba aiki na ba ne, and you know it, tiyata kawai na zo yi garin nan, ba kuma zan ɓata lokaci na akan abunda ba aiki na ba, jirgi zan bi na koma kaduna a can ma ina da aiki”
Yana kai wa nan ya fice. Da sauri wasu Nurses suka fita dan kiran wani likitan, shi kuma wannan likitan ya shiga bata taimako.
KALSOOM POV.
Tana tashi daga aiki, ta wuce gidan ƙawarta Salam dan labarta mata halin da take ciki.
Bayan Salma ta kawo mata abinci ta ci tayi sallah, sai take bata labarin abunda ya faru.
A maimakon ta ga ɓacin rai a fuskar Salma na taya ta baƙinciki irin mijin da zata aura, sai ta ga Salma na murmushi da yima Allah godiya
“Alhamdullah Allah mun gode maka, haba Kalsoom ko dan daɗewar nan da kika yi ba aure, be isa yasa kiyi haƙuri ki auri wannan ɗan'uwan naki a haka ba? Kina ji fa na faɗin da babbar budurwa ƙara ƙaramar bazawara, ƙannenki biyu a ɗaki ke kina nan, haba Kalsoom ki yi tunani mana”
“Ba auren ne bana so ba Salma, halin Sadiq ɗin ne na ke tsoro, ina gudun abunda ze je ya dawo, tun kamin tafi ake shawara ba sai an dawo ba, Wallahi na tsani mutum ne neman mata”
“Dan Allah ki daina faɗar wannan maganar, kar wani ya jiki ya san sirrinki, nema mata yanzu ya zamo ruwan dare, da wahala ki samu namiji me aure ko marar aure da baya neman mata, ko wace mace da kika gani a gidan mijinta tana da nata matsalar, no married friend of yours will ever tell you her marital problems,no woman will tell you her husband's fault amma karya take tace he is perfect,because no one is, dan Allah kiyi auren ki Kalsoom ke kaɗai ce a cikin kawayen mu kika rage baki yi aure ba”
Wani kallo Kalsoom ta yi mata, tana mamakin yadda ta kasa fahimtar ta.
“I have never blame myself for being single, i know I'm pretty, i'm well behaved, i'm Godly,and yet still single. Salma thats just how nature works, that is how Allah has designed it.
Idan duk a cikin ƙawaye na ni kaɗaice ban yi aure ba so what? Ni nayi kai na? Allah who created me differently and created them differently, surely made you destinies different. Komai lokaci ne Salma i don't want to rush into marriage with just any guy just because i want to be married, babu mai son ya je ya yi aure ya fito”
Salma ta dafa ta
“Haba Kalsoom zaki yi auren ne da niyar ki fito? Your idea is inside you Kalsoom, kiyi tunani me kyau, amman aure nan shi ya fi, kawai ki bawa Allah zaɓi”
Hawayen da suka zubo mata ta share ta ɗauki jakarta ta rataya.
“Na gode Salma zan yi tunani akai”
Har bakin gate Salma ta rakota, suka yi sallama sannan ta koma. Tafiya Kalsoom take tana tunani, sai taji ana mata horn, juyowar da zata yi sai taga wata hadaɗɗiyar mota mai kyau, tana binta a baya. sayawa tayi sai mai motar ya zo dai-dai ita ya tsaya, yana sauke gilashin motar.
Dattijo ne mai yalwatacciyar fuska da cikar kamala ta mai kuɗi.
“Shigo mana”
Ya faɗa yana buɗe mata front seat. Bata kawo komai a ranta ba, sai kawai ta buɗe motar ta shiga. Driving yake kaɗan-kaɗan yana gaisawa da ita.
“Ya kike ya gida?”
“Lafiya ƙalau”
“Ina zaki je ne haka?”
“Gida”
“Kuma kike tafiya a rana haka, kar fa rana ta taɓa min ke”
Ɗan murmushi tayi ta gyara yafin gyalenta.
Ba ko kunya ya kai hannu ya yaye mata gyalen
“Haba ke kuwa ya kiƙe ƙoƙarin rufe min kyau nan naki...”
Be karasa ba ta buge masa hannu tana masa wani kallo
“Sauke ni Malam, ni ba irin waɗannan matan bane”
“Haba kyakkawa daga magan...”
“Ka sauke ni nace!”
Ta faɗa a tsawace. Ba shiri ya ya faka motar ta buɗe ta fita tana tsaki.
“Ku ba za ku ce kuna son mace da aure ba sai lalata, duk Namijin da ka haɗu da shi abunda kawai yake ƙoƙari ya kai ga jikinka, ƴan iska kawai marar mutunci”
Haka tayi ta zaginsa, shi dai be bi ta kanta ba ya ƙaɗa motarsa yayi gaba.
_______________________________
Share it please, and drop your opinion. 🙌
Best regards 💖
Khadeeja Candy 🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa10.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 10*
UZAIR POV.
A guesthouse ɗin suka koma. Bayan Najeeb ya fito motarsa sai Uzair ya fito, suka nufi bayan motacin da suke gurin.
Ta inda suka san ba za'a gansu ba suka tsaya. Sai Najeeb ya kalle Uzair ya ce
“Uzair zaka janye maganar auren nan gobe gobe ba sai jibi ba, ka ce ka fahimcin tana da wanda take so, dan haka kai ka haƙura.
Sai idan ka yanje maganar ne sannan za mu je da kai gurin Malam gobe da nisa, dan ba za a yi mata magani kana auren ta ba”
“Amman idan mahaifinta yaƙi yarda fa?”
Najeeb ya yi masa wani kallo
“Ta ya zai ƙi yarda ? Shi ze aure ta ne? Ya kake abu Uzair kamar ba ɗan duniya ba? Sai wani ɓoye-ɓoye kake ai gashi nan ka jawa kan ka”
“Babu babbar matsala kamar ganin da tayi min, yanzu idan ta faɗa dame zan kare kaina”
“Sai kace ai ta saba maka ƙazafi, kai ma ai kasan kayi kuskure na bari ta ganka, kamata ya yi kasa a ɗauko maka ita”
Uzair ya yi shiru yana nazari, tashin hankali bayyane a fuskarsa. Kiran Amira tana ta shigo masa a waya amman yaƙi ɗagawa.
Ƙarfe ɗaya da rabi na dare kiran Baba Audu ya shigo wayar Najeeb. Cikin sauri ya ɗauka yasa hands-free.
“Hello Baba Audu ya ake ciki?”
Daga ɗayan ɓangaren Baba Audu ya amsa
“Na gama komai, na fito ina babban ti-ti, dai-dai inda kace na tsaya”
“Ina fatar anyi nasara?”
“Komai ya tafi yadda kake so”
“Toh ka jira ni, zan zo nan gurin na ɗauke ka”
Daga haka ya kashe wayar, ya kalli Uzair.
“Yanzu ka wuce gida kawai, ni zanje na ɗauko shi, idan ka taso aiki gobe mu haɗu a guesthouse ɗin Jafar, kuma ka tabbatar da ka sallami waɗannan mutane da suka ɗauko ta in case of”
Be jira abunda Uzair zai ce ba, ya nufi motarsa. Sai bayan ya fice sannan Uzair ya nufi cikin guesthouse. Be daɗe ba ya fito ya buɗe motarsa ya shiga, ya ɗauki hanyar da zata kai shi gidansa.
Tun kamin yana yin parking ya kashe wayarsa, sannan ya fito ya nufi hanyar falon.
Yasmin na zaune falo tana duba wasu takardu da system Uzair ya shigo da sallama.
Sai dai bata amsa masa sallamarba ma balle har ta ɗaga kai ta kalle. Kamar hakan be dame shi ba, sai kawai yazo ya zauna kusa da ita ya rufe system ɗin dake gabanta.
Yana ganin ta unƙurin zata tashi, sai yayi saurin riƙe ta ya zaunar, ya danneta da dukan ƙirjinsa ya ɗora mata nauyinsa, yana ƙoƙarin saka mata hannu ciki riga.
“Haba Bloody miyasa kike min haka ne? Dan kawai zan ƙara aure sai na zama maƙiyinki? Ai badan bana son ki zan ƙaro wata ba, sai dan rufin asirin mu”
A kaɗan-ƙaɗan ya raɗa mata haka, cikin wani irin siga na son tada mata hankali, sai numfashi yake sakar mata a kunne.
Ƙoƙarin ƙwatar kanta take amman ta kasa, ta ƙara haɗe rai sosai.
“Sake ni mana, Uzair bana son haka”
“Zan sake ki, amman sai kin faɗa min idan kin daina fushi da ni, idan kuma baki daina ba toh zan janye maganar auren”
“Maganar auren ka be dame ni ba, babu ruwana da lamarin auren ku, dan haka ka daina saka ni a ciki”
“Babu ruwanki da lamarin aure na kuma kike fushi da ni?”
“Amman dan zaka yi aure sai ka rasa wadda zaka aura sai Aminiyata, kuma ƴar'uwa ta”
“Nima ai ƴar'uwata ce, kuma naga kamar zaku fi zaman lafiya”
Wani dogon tsaki taja, tasa guiwar hannunta ta buge masa ciki. Ba shiri ya sake ta ya dafe cikin.
“Yasmin kashe ni zaki yi?”
Tsaki ta sake masa ta wuce ɗakinta, tana cika da batsewa. Da kallo Uzair ya bita yana murmushi, sai da ta shige ɗakinta sannan ya tashi ya nufi ɗakinsa.
Tun da asubar fari Hajiya Barau ta bugo masa waya ta faɗa masa abunda ya faru. Yi yayi kamar be sam komai ba, duk ya firgice yana nuna damuwa, sai tambayoyi yake zubo mata, yana nuna mata tashin hankalinsa kamar ance masa gata nan gabansa.
“Ban san miyasa Namra ta tsane ni har haka ba, ban san abunda na tsare mata ba, na rasa gane kanta”
“Uzair, inda har ba Allah yayi auren nan naku ba, bana jin zata zauna gidanka ko da ka aureta, kuma Wallahi a yadda zuciyar Namra take ko kashe ka zata iya yi ko kuma tayi maka wata illar, tun da bata son ka”
“Daman abunda Hajiyata take ta faɗa kenan, ni ina ganin gaskiya haƙura zan yi, ƙara taje ta auri wanda take so kawai”
“Da kam yafi maka, dan wannan auren ba zai yi ƙarƙo ba, sannan bana jin wannan yaron daya ɗauke ta ze barta haka nan, kar ayi maka kwashe-kashe”
“Barin ze fi tun da har zuciyarta wani take so, kuma duk macen da zata iya bin saurayinta kinsan ta girma”
“Ashe kai ma kana da tunani, fasa auren akam zai fiye maka”
Daga haka suka yi sallama. shi kuma ya sauka saman gadon ya nufi bathroom.
Sai tara da ƴan mintuna ya shirya, be damu da breakfast ya fito ya nufi parking space. Lokacin Yasmin har ta daɗe da barin gidan. Direct gidan Mahaifiyarsa ya nufa Hajiya Binta. A can ya yi breakfast yana labarta mata abunda ya faru, sai tace masa ai Hajiya Barau ta kira ta ta faɗa mata komai. Ta ji daɗin maganar da yayi ta basa auren Namra, ita daman zuciyarta bata natsu da aurensa da Namra ba, tun lokacin da tayi masa ƙazafi.
NAMRA POV.
Cikin ikon Allah numfashinta ya dawo, sai aka ɗaura mata drip,
Sai dai bata farka ba sai kusan Asuba, a lokacin Mama Zainab ce kawai a ɗakin, dan Hajiya da Hindatu tun cikin dare suka koma gida.
Kuma har garin Allah ya waye babu wanda ya leƙosu sai Amira, ita ma sai goma har da rabi sannan ta iso.
Namra na zaune jugummm tana tunani hawaye na bin fuskarta. Amira na shiga ta je da gudu ta rumgume Namra tana kuka.
“Wallahi da ba'a ganki ba Namra, da kashe kai na zan yi”
Namra ta share hawayenta, ta kalli Amira.
“Amira ina Asim yake?”
Gabanta ya faɗi, har sai da ta haɗiye yawun bakinta ta.
“Ina Asim yake Amira? Taya Asim ya zo gidan ku har ya baki wannan number?”
Nan ma kasa amsawa ta yi sai kukan munafurci take, zuciyarta na tsara mata irin ƙaryar da zata yi Namra dan kare kanta. kamin ta amkaro har Namra ta ƙara mata wata tambayar.
“Amira ki amsa min mana, ina Asim? Amira number da kika ba ni bata Asim ba ce, lokacin dana je ba Asim na gani ba Uzair na gani, faɗa min ta ya haka ya faru?”
Har lokacin Amira shiru take, bakinta sai rawa yake ta kasa magana. Hakan ya tabbatar ma Namra abunda take zargi.
“Uzair ya haɗa kai da ke an cuce ni”
Dam! Dam!! Dam!!! Zuciyar Amira take bugawa har cikin ƙwaƙwalwarta, ja ta yi da baya tana girgiza ma Namra kai hawaye na fita a idonta.
“Ki zargi kowa da cin amanarki, amman ban da ni, har a bada Amira ba zata taɓa cin amanar Namra ba”
Namra ta ɗaga mata kai tana hawaye.
“Asim ma ba zai iya cin amana ta ba, karki yaudari kanki wajen nuna min Asim yana so ya cuce ni. Amman ke Uzair zai iya siyen ki ya biya ki dan ya cimma burinshi, babu wanda ze fahimci ni, na ɓata ran kowa, ban san hali da Mahaifana suke ciki ba, sanadin ke da Uzair”
“Namra karki yanke hukuncin abunda baki sani ba, zan iya dafa miki qur'ane Namra, ban haɗa kai da Uzair ba dan na cuce ki.
Namra ta ya zan haɗa kai da wani ya wulaƙanta ki a titi? Har sai jama'ar unguwarku sun ɗaiko ki su kawo gidanku, Kuma su bada shaidar sun ji muryar Asim kuma sun ji an kira sunansa.
Namra tun da na bar gidan ku, ban rumtsa ba saboda tunanin da kukan rashin sanin halin da kike ciki, kina fita Maryam ta shigo ni ta ɗaurawa laifi tace ni ce silar komai, na yi tunani ke zaki bada shaida akaina ashe na yi kuskure.
Namra ki faɗa min dalili ɗaya, da zai sa na cuce ki, faɗa min Namra? Kinsan a iya zamantakewar mu da ke duk wanda ya ci amanar wani Allah sai ya fitar masa da haƙƙinsa”
Da wani irin kuka ta ƙarasa maganar kamar ta sheɗe. Kalamata sun sa jikin Namra sanyi, sai zargin da take mata ya soma raguwa, sai dai har yanzu bata ji zuciyarta ta natsu da Amira ba.
Kan ta ya kulle, ita dai tasan ba mafarki tayi ba, tabbas ta yi ido huɗu da Uzair kuma ya riƙa ta, sai dai bayan nan bata san wani abunda ya faru ba.
‘Taya Uzair yazo gurin? Miye dalilin da zai sa Uzair ya yi min haka? Taya Amira zata cu ni ta’
Sune tambayoyin da suka tsaya mata a rai, kuma suke ƙoƙari riƙita mata ƙwaƙwalwa.
Jin Amira ta dafa ta ya dawo da ita daga dogon tunanin da take.
“Namra kin fi kowa sanin ni wace ce...”
Bata ƙarasa Namra ta kai hannu ta riƙa hannunta.
“Ki yi haƙuri, kaina a kulle yake, a yanzu bana iya banbance gaskiya da ƙarya, bana iya tantance komai na rasa gane abunda yake faruwa da ni...”
Da kuka ta ƙarasa maganar, sai Amira ta rumgume ta suna kukan tare.
Shigowar Mama Zainab ne yasa suka tsagaita kukan, suka share hawayensu.
“Kuka fa ba zai muku ba, abunda ya faru ya riga ya faru sai dai a tari gaba. Likitan ya rubuta miki wani magani?”
Ta tambaya dan ɗazu Likitan daya shigo ne yasa ta fita, ta basu guri. Namra ta ɗauki takardar dake gefenta ta miƙa mata.
“Bai rubuta min komai ba, ya dai bani takardar sallama, yace bayan sati biyu na dawo”
Mama Zainab ta karɓa tana faɗin
“Masha Allah, sai ki tashi muyi harama, dan yanzu Hajiya Raliya ta kira ni wai tana son ta zo Mamanki ta hanata, kuma ƙara mu koma gida kar a fara mana taro, tun da babu wanda yaji abunda ya faru sai ƴan gida”
Namra ta lumshe ido ta jin wani abu daya tsaya mata a zuciya.
Amira ce taje ta biya komai da komai sannan ta zo ta riƙa Namra suka fita tare.
HILAL POV.
A gajiye ya fito asibitin, daker yake driving saboda gajiya, dan wuni yayi yana aiki, har jin yake kamar fever na son rufe shi.
Yau kan baya iya bin gosulon nan na government house, saboda taron da ake.
Sai kawai ya hanka ta cikin estate dan samawa kansa sauƙi sai dai tafiyar zata masa nisa sosai tun da ya biyo doguwar hanya.
“Subhanallah”
Ya faɗa lokacin da idanuwansa sukayi arba da wata kyakkyawar fuska, dake takowa izuwa hanyar daya fito. Sai ya rage gudun da yake, ya mai cigaba da kallonta.
Tana da kyau sosai mai jan hakali da saka natsuwar zuci, sai dai fuskarta kawai yake iya gani, domin jikinta rufe yake da ƙaton hijabi. Hakan kuma ba ƙaramin burgeshi yayi ba, ganinta cikin kamala ga tafiyarta a natse.
Kamin ta ƙaraso kusa da shi ya faka gefen ti-ti yana ƙare mata kallo.
Tana da tsayi da dogon hanci ga idonta dara-dara, farin fuskarta fes, sai dai a iya yadda ya fahimta kamar bata da jiki sosai.
Dai-dai lokacin data kawo kusa da shi sai ya sauke gilashin motarsa yana miƙa mata sallama.
“Assalamu alaikum Malama”
“Wa'alaikassalam”
Ta amsa mishi da zazzaƙar muryarta sai dai hakan be sa ta tsaya ba, sai ta cigaba da tafiyarta kamar ba ita ta amsa masa sallamar ba.
Da sauri Doctor Hilal ya buɗe motar ya fito ya biyo ta da ƙafa.
“Dan Allah ɗan tsaya na tambaye ki wani abu”
Allah daya haɗa ta dashi yasa ta tsaya, da badan haka ba babu abunda ze sa ta tsaya dan iya yanzu ta sallama a lamarin maza.
“Dan Allah ke matar aure ce?”
“A'a”
“Dan Allah ya sunan ki, kuma ina ne gidan ku?”
Sai a lokacin ta kalleshi, wani faɗuwa gabanta yayi lokacin da idonta suka sauka cikin nasa, kyausa yayi mata kwargiji, wanda yasa tayi saurin sauke idonta ƙasa, tana sauraren bugun zuciyarta.
“Miyasa ka tambaya?”
“I ask you first”
Ba amfanin yin ƙarya, dole ta faɗa masa gaskiya.
“Sunana Ummul-Kalsoom amman ana kira da Kalsoom, gidan mu yana ta nan gaba number 5 gidan Alhaji Faruk Kafinta”
“Toh na gode”
Bata sake ce masa komai ba, ta cigaba da tafiyarta. Shi kuma ya bita da kallo har sai da yaga inda ta shiga, sannan ya shiga motar yana murmushi, a take ya ji duk gajiyar da take tare dashi ta wartsake, cikin farinciki da annashuwa ya kunna motar ya hau ti-ti.
__________________________
What do you expect next?
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa11.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 11*
NAMRA POV.
Keke Napep Amira ta tare musu ta faɗa masa inda ze kai su, sannan suka shiga.
Be sauke su ko'ina ba sai Ƙofar gidan, Amira ta biya shi sannan ta riƙa hannu Namra suka shiga cikin gidan.
Kamar mai nauyin ƙafa haka Namra take tafiya tana hawaye, gaban na bugawa da ƙarfi. Da wane ido zata kalli Anty Amarya? Idan Abbah ya kalleta me zata ce masa.
Mama Zainab ce gaba da sallama sannan Namra, sai Amira ta biyo baya. Hajiya Raliya ta amsa musu sallamar, Anty Amarya kam yi tayi kamar ma bata gansu ba, ta tashi tayi ta nufi kitchin.
Saman Kujera Amira ta zaunar da Namra, sai ta zauna kusa da ita tana amsa ya jikin da Hajiya Raliya take mata.
“Da sauki har an sallamota”
“Wallahi babu yadda ba mu yi ba ni da Aisha da Hindu muje ganin ki amman Larai ta hana, sai gashi Abbanki ya zo shi yace kar wanda ya fita da sunan ganin ki a gidan nan, toh kar ma ya kuskura ya dawo”
Fashewa ta yi da kuka, ta kwantar da kanta jikin Amira dake hawaye.
Shigowar Hajiya Barau ne yasa ta noke kanta, Amira da Mama Zainab suka amsa mata. Idonta kar kan Namra sai kallon jikinta take.
“Namra kin dawo? Wallahi Alhaji ne ya hana mu zuwa ganin ki, ya jikin?”
“Alhamdulillahi”
Mama Zainab ta amsa. Zaunawa tayi kusa da Amira.
“Ince dai babu abunda ya same ki ko?”
“A'a ba komai likita ya bincika yace babu abunda yake damunta”
Cewar Amira
“To Alhamdulillahi, Allah ya tsare gaba”
Sai ta tashi sun-sun-sun ta fice. Hajiya Raliya ta kalli Namra cikin damuwa ta ce
“Haba Namra haka kike so maƙiya su yi ta miki dariya? Ansa ranar aurenki kije ki gana da wani? Haka aka kawo mana ke shame-shame mazan unguwar nan zagaye da ke, shi haka shine daɗi?”
Amira ya share hawayenta
“Dan Allah ku daina wannan maganar, zaku ɗaga mata hankali ne kawai, ita kan ta ba'a son ran ta hakan ya faru ba, kusan babu yadda Namra zata kai kanta ga halaka ko kuma inda ta san mutuncin ta ze zube”
Namra kan kuka kawai take, tana jin wani irin ƙololon baƙin ciki ya riƙe mata zuciya. Kamar daga sama sai ga Abbah ya shigo falon fuska babu annuri.
A take cikin Namra ya ɗauki ƙugi, ko Amira sai da ta razana da yanayinsa, yana katsawa Namra tsawa jikinta ya hau rawa.
“Khadija ki tashi ki koma can gurin saurayin na ki bana son ganin ki a cikin gidan nan!”
Cikin baƙar zuciya Anty Amarya ta fito daga kitchen ta nufo inda Abbah yake tsaye tana faɗin
“Babu inda Namra zata je, ko kisan kai ta aikata idan ta shigo nan gidan ta samu mafaka, dan gidan ubanta ne ciki da waje, komai Namra ta aikata sai ance ƴar Alhaji Usaman ce ko da bata duniya, duk inda aka ga sunan Namra sai anga naka kuma dole ace ƴar ka ce”
Abbah ya nuna Anty Amarya
“Ai daman ke kike goya mata baya take duk abunda take”
Anty Amarya ta nuna kanta tana hawaye.
“Ƙwarai, nina goya mata baya nace ta fita cikin dare taje taga Asim, kuma idan taje ta faɗi ta suma jama'a su ɗauko ta su kawo maka cikin gida ni nace....”
Mama Zainab ta rufe mata baki, tana ba Abbah haƙuri. Da ƙarfi Anty Amarya ta buge mata hannu ta matsa tana faɗin
“Ki ban ni ina faɗi ciwon bakin na, wannan ƙurjin ya daɗe yana min ƙaiƙayi a cikin rai, duk abunda Namra ta aikata gare ni yake dawowa, ni nake tura ta, faɗa min wace uwa ce zata so abunda ya faru da Namra ya faru da ƴarta, amman ni yake ɗorawa laifi”
Shiru Abbah yayi yana kallon Anty Amarya data cika falon da ruwan bala'i tana zazzaga masa rashin mutuncin har yata gama be sake cewa uffan ba.
Hajiya Raliya ce keta bashi haƙuri tana cewa kar ya tanka mata, shi ma daman be da niyar sake ce mata komai, dan yasan Anty Amarya bata iya faɗa ba, idan ta birkice masa babu mai iya tare ta sai Allah, haka take wani lokacin kamar mai aljannu, shiyasa Hajiya Barau ta sallama ma lamarinta.
Tsaye Anty Amarya ta yi masa ƙyam, tana jira ya ce mata kulle ta ce masa chas, dan idonta yanzu a murje yake, zuciyarta kuma ta kawo. Abbah be yarda ya sake ce mata ƙomai ba, ya juya ya fice.
Sannan Anty Amarya ta kalli Amira a tsawace tace
»“Ke Amira tashi ki je gida”
Da sauri Amira ta ɗauki jakarta ta rayata, ko sai ajima bata ce ba, ta fice jikinta na rawa.
Tasss! Tasss!! Tasss!!! Anty Amarya ta sauke ma Namra mari har sau uku, sannan ta nuna mata ƙofar ɗakinta
“Tashi ki wuce ɗakin ki, kin samu farinciki kin jidaɗi”
Zubewa Namra ta yi ƙasa daga kan kujera tana kuka, ta riƙe ƙafafun Anty Amarya.
Riƙo fuskar Namra Anty Amarya ta yi ta sake sakar mata wani marin sannan ta tureta ta fisge ƙafarta, ta wuce ɗakinta cike da ɓacin rai.
Daga Hajiya Raliya har Mama Zainab tsaye suka yi basu yi unƙurin yin wani abu ba, dan sunsan halin ƴar'uwarsu kan akwai haƙuri amman idan ta hasala bata da daɗi.
Sai daNamra tayi kukanta mai isarta sannan ta tashi ta nufi ɗakinta. Saman gadonta ta faɗa ta sake fashewa da sabon kuka.
Har La'asar bata fito daga ɗakin ba, kuma babu wanda ya shiga inda take inba Aisha ba, itama tun da ta fita tayi shirin islamiya babu wanda ya leƙo ɗakin.
Tasan dole ne Maryam tayi fushi da ita, dan Maryam tafi kowa ɗaukar zafi idan wani abu ya faru. Sai da dare Aisha ta shigo ta aje mata abinci ta fita.
UZAIR POV.
Yana tasowa daga gurin aiki kai tsaye ya wuce guesthouse ɗin Jafar, daman tun yana gurin aikin suka sha masa kai da kira, wai duk sun hallara shi kawai suke jira.
Yana shiga ruwa kawai ya sha Najeeb ya tambaye shi.
“Ya Labarin yarinyar?”
“Wai asibiti ta kwana, Kishiyar mamarta take faɗa min ɗazu da safe, sai na nuna mata kamar ban ji ba”
“Amman kaje ka ganta?”
Jafar ya tambaya. Sai ya girgiza masa kai
“A'a na dai je gurin Hajiyata na faɗa mata maganar janye auren tace zata je ta faɗawa Abbah”
Najeeb yace
“Amman ai da kaje ka ganta Uzair sai ka nuna kasan abunda ya faru, anyway muje ciki malamin yana ciki tun ɗazu ya iso”
Uzair yayi sauri haɗiye ruwan bakinsa.
“What? Na ɗauka zuwa zamu yi gurin shi”
“No Ba zamu iya shiga dajin nan ba, sai na aika direba ya ɗauko shi, kasan su kuɗi kawai suke so da sun ga ƙuɗi komai zasu iya”
Cewar Najeeb. Tahir ya aje wayar dake hannunsa saman tebur ya miƙe tsaye.
“Muje ayi abunda za'ayi akwai inda nake son naje”
Sai duk suka ɗugunzuma suka nufi wani ƙaramin falo, da ba kasafai suke zama cikin shi ba.
Dattijo ne sanye da babbar rigarsa, kansa ya sha uban rawani, haƙorasan duk goro, ga wani ƙaton faifai dake gabansa, mai cike da jar ƙasa. Idan ka kalleshi sai kayi masa ɗaukar mutumin kirki, a fuskarsa ba zakayi zaton zai iya aikata wani mugun abu ba.
Duk guri suka samu suka zauna, bayan sun gaisa, Jafar ya kora masa da bayani
“Am daman na faɗa maka tun ɗazu, abokin mu ne yake ciki wata ƴar matsala, wata ƴar'uwarsa ce take ƙoƙarin masa zagon ƙasa, saboda ta kamashi yana aikata luwaɗi, shine take son tona masa asiri, babu yadda be lallaɓata ba amman ta ƙi yanzu haka so take ta rabashi da matarsa, da kowa nasa”
Lokacin da Jafar ya kai aya sai ya zumguri kafaɗar Uzair alamar yayi magana, sai shi kuma ya ɗora.
“Yanzu haka ta ɓata min suna a cikin familyn mu kuma yanzu haka tana nan akan bakanta na cewar ta faɗawa duniya da ƙwaƙwarar hujjah”
Malamin yayi murmushi yana gyara zamansa.
“Yanzu me kake son ayi mana, shin kana son a kulle mata baki ne ko kuma ayi mata kurciya ta bar garin gaba ɗaya?”
Kallo-kallo suka riƙayi, kowa na tunanin abun cewa, can sai Najeeb yace
“A ɗaure mata bakin kawai ta yadda komai ta gani ba zata iya faɗa ba”
“Ko kuma ayi mata kuciya ta bar garin gaba ɗaya”
Cewar Jafar. Uzair ya girgiza kai
“Idan muka mata haka ba muyi mata adalci ba, why not dai ayi mata na rufar bakin”
Najeeb yaja tsaki
“Ita ba naka sunan ta ɓata ba? Idan aka mata kuciyar ta bar gari kana tunanin wani zai zargeka ne? Sai dai ace ai halinta ne, kuma wannan shine kawai mafita”
Uzair yayi shiru yana nazari. Sai Malamin yace
“Minene sunan ta? Sai mu duba muga irin aiki daya dace ayi mata, dan aikin da ke yima wani bashi ke ma wani ba”
“Sunanta Khadija, amman Namra ake kiranta”
A take Malamin ya gyara ƙasar ya shiga bincike, yana wasu tsiface-tsiface.
Ya ɗauki tsawon lokaci yana bincike amman be gano komai ba, can ya ɗago kai ya kallesu yana jinjina kai yace
“Lallai wannan aikin ze ci ƙuɗi da yawa, kuma magana ta gaskiya wannan yarinya akwai tsari tare da ita na musamman, ba lallai bane ko wane irin aiki ya kamata sai dace”
Duk sun cika da mamaki, bama kamar Tahir daya kasa haƙura har sai da ya tambaya
“Saboda me?”
“Ban san dalili ba amman lallai akwai tsari mai ƙarfi a tare da ita, kasan ni bana aiki da munafurci kuma idan har abu baya yi zan fito fili na faɗa maka gaskiya”
Uzair ya sauke ajiyar zuciya
“Yanzu ba wata mafita kenan?”
Lailaya ƙasar yayi
“Bari mu bincika mu gani”
Sai ya koma bincike yana watsa wani farin miski a jikin ƙasar.
Zuwa can ya ɗago ya kalli Uzair yace
“Ta ƙi bayyana a binciken mu, sai dai an samu mafita, za a iya samun sa'arta ne kawai da asuba ko kuma lokacin da take haila”
Lokacin asuba lokacin ne mala'ikun da suke tsare bawa idan yayi addu'ar bachi suke tashi, Idan be yi saurin tashi yayi sallah ba, a lokacin har sheɗan yake samun sa'arsa ya saka masa kasala, da ƙuiyar yin sallah har sai rana ta fito.
Lokacin Haila kuma lokaci ne da ba ko wace mace ba ce take tsare yin addu'ah a wannaɓ lokacin ba, saboda ganin tana al'ada, bayan kuma duk kan addu'o'i an yarda mai haila ta karanta sallah ce kawai aka ɗauke mata, da ɗaukar cikakken ƙur'ane, da kuma ɗawafi.
Dan haka yan'uwa mu kiyaye addu'ah a wannan lokacin, kuma mu kiyaye Sallah asuba a cikin lokaci, tana da muhimmanci sosai.
Najeeb yace
“Amman kana ganin idan har anyi aikin zai ci kuwa?”
“Zai ci dan wannan aikin ba za a yi shi ace ba a ga nasara ba, sai dai ya zamo wanda ake son ya sama ɗin be same shi ba”
“Kamar ya?”
Tahir ya tambaya da sauri.
“Zamu yanka baƙin bunsuru guda biyu, da rago, sai a samo mana tunfafiya da kurciya da su zamuyi aikin, sai a rubutu wasu abubuwan da jinin bunsurun a watsa a riga ko zane da zata ɗaura sai a bata ta saka, inda har ba wanda ya bata ɗin nan bane yayi kuskure toh lallai babu tantama aikin zai kamata, amman fa a lokacin da take Haila ko kuma kamin sallah asuba”
Jafar ya riƙe baki
“Babbar magana, dole sai ta wannan hanyar kawai?”
“Ba dole sai ita ba, amman ita ce tafi ko wace sauƙi”
Tahir ya kalli Uzair
“Toh kai kana da mak maka wannan aikin ne?”
“Akwai wata ƙawarta ina jin kamar zata iya, amman what if ba ayi nasara ba?”
Tahir ya dafa shi.
“Ka yarda kawai za'ayi nasara, karka sawa kanka wannan”
Kai ya girgiza
“Ni dai ko na haƙura kawai na ƙyaleta”
Ganin yadda Uzair ya tsorata yasa Malamin shiga kwantar masa da hankalin
“Za'ayi nasara, karka damu, ka haɗani da wadda zata kai mata rigar na san yadda zan tsara mata komai”
Shiru Uzair be ce komai ba, shi dai sai tunani yake. Ganin hakan yasa Najeeb yace da Malamin
“Shikenan a fara aikin kawai, zan turo maka dubu ɗari a account ina tunanin zasu isa? Idan ma da wani abu sai ka kira a waya”
“Zasu isa inshallah, amman za a kawo rigar da taɓa sawa, dan da ita zamuyi aiki, kuma ina son ganin yarinyar”
“Ba matsala zuwa gobe duk yadda muka yi zaka ji ni”
Daga haka suka yi sallama, Najeeb yasa direba ya maida malamin. Sannan suka ya dawo falo suka shiga tattauna maganar.