Wanka yayi ya shirya cikin wata gizna, maroon color, sannan ya ɗauki hulla mai kyau ya saka, ya ɗauki agogon hannu ya saka ya feshe jikinshi da turare, sannan ya buɗe wardrobe ya ɗauko sababin kuɗi ya saka a aljihu, sannan ya dawo gaban madubi ya sake kallon kansa, ya tabbatar da kwaliyarsa ta fito, sannan ya ɗauki keys ɗinsa ya saka baƙaƙen takalmi, ya fice.
Ko da ya fito falo, Rashida na gaban dinning tana shirya musu dinner, su Ulfah zagayeta suna nuna mata assignment ɗinsu.
Kusa da ita ya ƙarasa yana leƙon abincin da take zubawa.
“Pyar a zubawa yara nasu nawa sai na dawo mu ci”
“Ina zaka je?”
“Ango zamu je rakawa ba zan daɗe ba”
Juyowa tayi ta kalleshi daga sama har ƙasa, yadda kyau nan nasa ya fito ya bata tsoro. Shi kuma sai yayi kamar be ga kallon da take masa ba sai ya kalli agogon hannunsa.
“Bari naje kar nayi latti, ni kawai suke jira”
Hannu yasa ya rufe idon Ulfah sannan yayi mata kiss a baki, sannan ya nufi ƙofa sai ƙanshi turare yake.
“Allah ya tsare min kai ni dai”
Ta faɗa lokacin da zai fice. Murmushi kawai yayi ya saka kai ya fice.
Motarsa ya shiga yayi horn mai gadi ya buɗe masa, ya hau ti-ti zuciyarsa cike da nishaɗi.
Cikin ƴan mintuna ya isa estate ɗin su Kalsoom. Numbers ɗin gidaje ya riƙa dubawa har ya kai ga number.
Dai-dai gate ɗin ya tsaya yayi horn yayi mai gadin gidan ya leƙo sannan ya buɗe masa, sannan ya shiga harabar gidan yayi parking. Sai ya fito ya nufo mai gadi ya bashi hannu suka gaisa sannan yace
“Dan Allah ko nan ne gidan Alhaji Faruk Kafinta?”
“Eh nan ne”
“Dan Allah mai gidan yana ciki?”
“Eh yana ciki”
“Dan Allah kayi min sallama da shi”
“To wa za'ace masa?”
“Ce masa Doctor Hilal ne”
Da sauri mai gadin ya nufi cikin gidan. Doctor Hilal kuma ya dawo gurin motarsa ya tsaya yana ƙarema gidan kallo.
Hilal ya kusan minti goma tsaye a gurin sannan Abban Kalsoom ya fito, yana ganin Doctor Hilal ya washe baki.
“Maraba da bokan turai, yau likita a gidana na”
Da sauri Hilal ya miƙa masa hannu suka gaisa, har da ɗan risina masa yana murmushi.
“Wai daman nan ne gidan ka?”
“Nan ne kasan abu ga talaka”
Ya faɗa yana dariya, yasan Doctor Hilal sosai dan shine likitan da yake dubashi a duk lokacin daya je asibiti, sai dai Doctor Hilal be waye shi sosai ba, sai yanzu.
“Shigo ciki mana”
A falonsa ya shiga da Hilal ya ɗauko masa lemu da kansa, zai zuba masa Hilal yayi saurin karɓa ya zuba da kansa.
“Ya fama da jama'ah”
Daddy ya faɗa yayin da ya zauna saman kujera.
“Al-hamdulillah da fatar dai na same ku lafiya”
“Lafiya ƙalau, yau dai sai ga likita gidana, ina ji dai hanya ce ta biyo da kai, ni dai nasan Likita be san gidan ba”
Doctor yayi dariya.
“Yanzu ma dalili ne ya kawo ni, akwai wacce na gani naga ta shigo nan gidan”
“To, kuma bata faɗa maka sunanta ba? Ta yiyu ma ƴar maƙota ce”
“A dai yadda nake tunani ƴar nan gidan ce, sunan ta Kalsoom wata doguwa haka”
Daddy yayi murmushi.
“Kalsoom ai ƙanwar ka ce Likita”
Hilal yayi ƙasa da kanshi
“Ina fatar ba'ayi mata miji ba?”
“Ba'a mata ba, amman akwai manema”
“Ina fatar shiga cikin su, amman idan kayi min izini, dan ni da gaske nake yi idan Allah ya yarda”
“Ba ni da matsala Likita, inda har kun dai-dai ta kanku, ni da Kalsoom ai duk mallakin ka ne, tun da ni Patient ɗin ka ne”
Ƙasa Hilal yayi da kansa cike da jindaɗin maganar Daddy, be ɗago ba har sai da Daddy ya tashi yana faɗin
“Bari na kira maka ita”
Daddy na ficewa ya miƙe tsaye ya ƙara karkaɗe shaddarsa, sannan ya zauna a natse yana kallon ƙofa. Sai gata ta fito cikin hijabi tana tafiya a hankali, sallama ta fara masa sannan ta nemi guri ta zauna, tana gaishe shi.
“Lafiya ƙalau, ina fatar Gimbiyar tana nan lafiya”
“Al-Hamdulillah”
“Mashallah, na zo mun gaisa da Daddy ki sai yace ze kira min ke mu gaisa, ina fatar ban takura ki ba, kuma in babu matsala zan so ki gabatar min da kan ki”
“Sunana Kalsoom ni budurwace ina aiki a MTN Service, nan ne gidan mu kuma ina ƙarƙashin kulawar iyaye na ”
Gabansa ya faɗi, jin tana aiki, shi da yake son ƙara aure saboda aikin da matarsa take sai kuma ya sake karo da wata ma'aikaciyar. Sai dai be nuna mata ba, sai kawai yayi murmushi yace
“Mashallah, ni kuma sunan Doctor Hilal Abubakar Mai-lafiya, ina aiki a American Hospital dake nan Kaduna, ina da mata ɗaya da yara uku, ina fatar zan samu karɓuwa, duk da kasancewar na san muna da yawa”
Murmushi kawai tayi masa, ta shiga murza hannunta.
“Ba zan cikaki da surutu ba, dan na fahimci kamar Gimbiyar tawa bata son yawan magana, ni kuma gani kamar wazirin aku, zan nemi alfarma ɗaya zuwa biyu”
“Allah yasa zan iya”
Ta faɗa da murmushi.
“Ina farko ina son ki bani damar zuwa muna gaisawa, bace kullum ba gudun kar na takura miki, amman zan riƙa kwatantawa, sannan ina son ki samin number wayarki”
A take ta karanto masa number, sai da yasa yayi saving sannan ya kalle ta
“Amman fa ni bana son na kira naji User busy, dan ni ina da kishi sosai, ba kamar sauran samarin ki bane”
Nan ma murmushi tayi, sai ya tashi tsaye yana faɗin
“Bari na zo na tafi, kar Daddy yace zan sace masa ƴa”
Sai a lokacin tace
“Ai Daddy ya san be kawo ɓarawo gidansa ba”
“Kar kiyi saurin yanke hukunci, Wallahi sata na zo nayi masa”
A kaikaice ta kalleshi zuciyarta na raya mata abunda ze fito bakinsa.
“Zuwa nayi na sace zuciyar ƴarsa, daga nan sai na sake sace gangar jikinta, na kaita gidana na aje”
Fuskarta da murmushi ta lumshe ido yana girgiza kai. Yau kam Allah ya haɗa ta da Mutum me son raha.
“Ba dan kar na takurawa Sarauniyar ba, dana nemi izinin a rakani ”
Lumshe ido tayi ta buɗe
“Ai duk umarnin da sarki ya bada, da shi baiwa zata yi amfani”
Hannunsa ɗaya yasa aljihu sai ya nuna mata ƙofa da ɗayan.
“Zan so Sarauniya ta wuce gaba, gudun kar bafade yayi mata ba dai-dai ba”
“Amman ai ko a fagen yaƙi, Yarima ne yake sharewa Gimbiya hanya”
Wani irin murmushi Hilal yayi murmushin daya ƙara fito da kyaunsa. Sai kawai ya shiga gaba ta rufa masa baya.
A tare suka isa gurin motar sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro sabbin kuɗi ya miƙa mata.
“Nasan wannan ba ze siye kalamai da kuma tsadadden murmushin ki ba, amman zai iya zama tukuici ga rakiyar da kika min”
Naɗe hannayenta tayi
“Ai wanda ya cika da yaƙi, ya mallake ka duka kai da iyalan ka”
Yasan me take nufi sai kawai yayi murmushi yace
“Zan yi farin ciki idan kika karɓa”
“Ni kuma zan fika farin ciki idan baka cilastani na karɓa ɗin ba, kuma nasan farincikin na naka ne”
Mayarda kuɗin yayi aljihu.
“Na gode da wannan karramawar Kalsoom, ni zan tafi ki kula min da kanki”
“Ni kuma ka kula min da Anty na da duk yarana, kuma ka miƙa min kyakkyawar gaisuwa na a gare su”
Ya buɗe baki
“Baki ce min na kula da kai na ba”
Murmushi tayi masa as respond ta juya ta shige cikin falon, tana mai jin sonsa a zuciyarta.
Shima murmushi yayi ya buɗe motarsa ya shiga.
Ko da ya isa gida, Rashida na zaune falo tana jiransa, duk ta haɗe rai sai kallon agogo take, jikinta na bata ba gurin kai ango yaje ba, gurin wata yaje.
Yana yin sallama ta amsa masa
“Wa'alaikassalam, amman pyar ba gurin kai Amarya kaje ba ko? Gaskiya wannan fitar daga gani gurin wata kaje”
Kusa da ita ya zauna yana murmushi.
“Na gode Allah daya sa matana ta iya karantar mijinta har haka, inda zuciyarki ta raya miki can naje kinsan ba zan iya ɓoye miki ba, ɗa zun ma dan bani da tabbacin zan karɓu ne shiyasa ban faɗa miki inda zanje ba”
Ta masa wani kallo
“Ka karɓu kenan?”
“Sosai ma har da tukuici”
Nan da nan idonta ya cika da hawaye.
“Doctor wasa dai kake”
“Banker da gaske nake, ba tuni nake miki waƙen zan yi aure ba kika ganin kamar wasa nake ba”
“Wallahi baka isa ba, ba a gidan nan ba”
“Toh ai sai ki hana idan gidan ki ne, ni dai tashi ki zubo mana abinci yunwa nake ji”
“Ba zan zubo ba, sai ka koma can kaje ta baka abinci”
“Toh ai ba'a ɗaura mana aure ba, amman dai idan na aure ta zaki ga soyayyah ba ni ba har ke sai tayi feeding ɗin ki”
“May God forbid ,kuma Allah ya tsine mata albarka”
Ta tashi ta nufi ɗakinta da kuka, shi kuma ya bita da murmushi yana jin son matar tasa har cikin ranshi.
UZAIR POV.
A mota ɗaya suke zaune shi da Najeeb, suna jiran fitowar Amira.
Sai ta ɓata musu lokaci, sannan ta fito sanye da abaya, tazo tayi musu tsaye tana hararar Uzair.
“Me ya kawo ka gidan mu?”
“Shiga mota zamu yi magana”
Ba musu ta buɗe motar ta shiga gidan baya ta zauna. Sai da ya gabatar mata da Najeeb sannan ya faɗa mata abunda ya kawo su.
“Lallai Uzair ban zaci zaka iya zuwa da wata buƙatar a gare ba, kira nawa nayi maka amman baka ji ba, yanzu ka haɗa ni da ƙawata har ta fara zargina”
Najeeb yayi murmushi mai sauti.
“Wannan ita kaɗaice mafita a gareki a gare mu kuma gaba ɗaya, kin ga idan mun aikata haka har ke asirinki zai rufu, amman idan asirinki ya tonu zaki fi kowa shiga cikin matsala”
Shiru tayi tana tunani.
“Amman nawa zaka biya ni?”
Uzair yayi murmushi.
“Zan baki 100k yanzu idan aiki ya yi zan baki 300k har abunda ya yi sama, amman ki tabbatar ta saka rigar”
“Taya zan iya tabbatar wa tun da ba tsare ta zan yi ba?”
“Ko ya ya zakiyi a kin sani tun da ke mace ce kuma Aminiyarta, idan ta kama sai ki kwana a gidan, yanzu dai kije ki karɓo mana rigar da dare zamu zo mu karɓa”
Cewar Najeeb.
“Naji amman ni ba zanje gurin wani Malami ba, kuje ku yanke min kai”
Duk dariya sukayi, sai Uzair yace
“Mun ji amman dai ki tabbatar rigar data taɓa sakawa ce, zan miki transfer 100k an jima”
Uzair be yarda ya faɗa mata abun ze iya dawawa idan be kamata ba, sai kawai ya ƙaleta har ta buɗe motar tayi ta fita.
Su kuma suka yi kwana suka wuce, daman baki gate suka tsaya basu shiga ciki ba.
Cikin gidan ta koma, a tsakar gida ta samu Ammy da Yayanta a tsaye suna magana, sai ta wuce ciki ta ɗauko handbag ɗinta sannan ta cewa Ammy zata je ta duba Namra.
“Kice ina gaishe ta dan Allah”
Cewar Ammy, sai ta fice tana faɗin
“Toh zan faɗa mata”
Waje ta fito ta tari mai napep ta shiga. Lokacin data shiga falon Anty Amarya ce kawai a zaune, su Maryam da Hindatu duk sun tafi makaranta, Mama Zainab kuma tun jiya da yamma suka kama hanya.
Har ƙasa ta risina ta gaishe da Anty Amarya sannan ta tambayi Namra, Anty Amarya tace mata tana ɗakinki sai ta tashi sun-sun ta nufi ɗakin.
Namra na kwance saman gadonta tana hawaye.
Kusa da ita ta zauna ta kai hannu ta riƙa hannunta.
“Haba Namra yanzu kina ganin kukan naki maganin ne?”
Tasowa Namra tayi ta rumgume Amira.
“Amira kowa fushi yake da ni, ina jin tsoro Amira”
“Tsoron me?”
“Ina tsoron kar ace sun taɓa min mutunci”
Amira ta fara hawaye.
“Nima ina wannan tunani Namra, kuma idan har haka ta tabbata kika yi ciki kin gama wulaƙanta a rayuwarki ta duniya”
Ƙara fashewa Namra tayi da kuka.
“Wallahi duk na gano wanda yayi min wannan abu sai na kashe ki, sai na masa wulakacin mafi ƙasƙanci a duniya”
Gaban Amira ya faɗi, ji take kamar da ita Namra take.
“Mafita ɗaya ce Namra, ki gwada shan magani da haila zata zo miki, kin ga ko da kina da cikin sai ya zube, tun ba daɗe ba”
Namra ta ɗago ta kalleta
“Amman ba ni da tabbaci”
“Shiyasa nace ki sha ɗin, kin ga idan ma anyi ko ba'ayi ba ke dai kin san babu ciki a tare da ke”
“Ina zan samu maganin?”
“Zan nemo miki, zan bincika na siyo miki”
“Na gode sosai Amira Allah ya bar zumunci, amman har yanzu baki da labarin Asim”
“Wallahi har yanzu, amman ki kwantar da hankalinki na san zai dawo komai daren daɗewa”
“Allah yasa”
“Amin, ni bari na tashi na tafi, daman gurin ɗinki zanje sai nace bari na biyo na duba ki, daga nan na ari rigarki ta atamfa”
“Gashi can je ki duba wanda kike so”
“Na jikin ki zaki ara min, dan bana son ɗinki mai hayaniya”
Ba tare da tunanin komai ba, Namra ta tashi ta cire rigar ta miƙa mata tare da zane sai ta saka wata gown.
“Ai dama kin bar Zanen tun da ba shida wani style, rigar kawai nake so”
Mayarda zanen Namra tayi ta aje, ta ɗauko mata jaka ta saka rigar, sannan ta tashi tana faɗin.
“Bari na je kar Ammy ta ga na daɗe tace na gaishe ki”
“Ina amsawa yaushe zako dawo?”
“Da na siyo maganin zan zo na kawo miki, amman ki kwantar da hankalin ki kinji?”
Kai kawai Namra ta ɗaga mata.Sai Amira tayi mata sallama ta fice.
Bayan fitar Amira Anty Amarya ta shigo ɗakin. Ɗaga bakin ƙofa ta tsaya tace
“Uzair ya janye zancen Auren shi dake yace shi ya haƙura, Abbah ki yace shi ba zai sake miki zaɓi ba ki kawo Asim ɗin zai ɗaura miki aure da shi”
Anty Amarya na kaiwa nan ta juya ta fice. A maimakon ta ji farinciki, sai kawai ta ji wani kalar abu ya baibaye ta, shi ba farinciki ba kuma ba baƙinciki ba. Sai kawai ta rushe da kuka.
Amira na fita gidan ta kira Uzair ta faɗa nasa yadda sukayi da Namra, ya jidaɗin abunda Amira tayi tun da yana ganin ta nan zasu samu mafita. Da dare yazo ya karɓi rigar, yace mata jibi ze kawo mata tare da maganin.
RASHIDA POV.
Tun da safe tayi shirin office, wace ke fita takwas ko takwas da rabi yau tun shida ta bar masa gidan, tun jiya da dare kuma ta ƙi sake masa sai fushi take dashi.
Kai tsaye gidan su ta nufa, Mahaifiyarta tayi mamakin ganin ta tun da sanyin safiya, ga fuska duk hawaye.
“Ke lafiya?”
Sai kawai ta faɗa jikinta tana kuka. Sai duk ta rikita mahaifiyarta a zatonta ma ko sun yi faɗa da Hilal ne ko kuma wani ne ya mutu. Sai da tayi kukanta mai isarta sannan ta faɗa mata abunda ya faru.
“Mom wai Hilal aure ze ƙara”
“Amman shine kika zo kika ta da mun hankali na ɗauka ko wani abun ne ma? Toh dan ze yi aure hana shi zakiyi ko me? Ke kaɗai aka ce masa ya aura?”
“Mom kishiya fa ze min ko baki gane ba”
“Na gane mana, ba'a aure ke aka aureki? Tun yaushe yake miki zancen ƙarin aure?”
“Mom wannan karon da gaske yake”
“Toh idan da gaske yake sai me? Hana shi auren zaki yi? Ke idan mai hankali ce ai da kanki ma kyace masa yaje yayi aure, duk irin haƙurin da yake da ke, idan ma yayi auren ai sai ki samu me riƙa miki yaranki”
Ɗaukar gyalenta tayi ta yafa ta ɗauki jakarta
“Ai daman nasan ba zaki goya min baya ba”
“Oh so kike na goya miki baya ki yima mijinki rashin mutunci ko? Shine kika wani ɗauko gyale kika zo gida ko kunya baki ji, kuma Wallahi bari jiki na faɗa miki kar ki biye son zuciyarki kije ki kawa kanki, kar naji wata matsala ta shiga tsakanin ki da mijinki akan auren nan”
Ficewa tayi tana hawaye tana faɗin
“Ba zan sake zuwa gidan nan ba”
Mom taja tsaki ta tashi ta nufi bathroom.
NAMRA POV.
Haka Anty Amarya ta kwashe kusan kwana huɗu babu ruwanta da Namra, ita kuma tana cikin ɗaki ta kasa fitowa kullum sai kuka take da ƙaratun Ƙur'ane, abun duniya duk ya isheta ji take kamar ta kashe kanta ta huta.
Bayan sauko Sallah Jumma'ah Namra ta tashi ta shiga banɗaki tayi alkwala ta fito ta gabatar da Sallah Azahar, bayan ta ƙare ta ɗauko Ƙur'ane tana karantawa.
Ta tsagaita karatun ne lokacin data ji sallamar Amira, sai da bata tsaya ba sai da ta kai ƙarshen aya, sannan tayi addu'ah ta rufe Ƙur'ane, ta juyo ta kalli Amira.
“Amira”
“Na'am”
A kasale Amira ta amsa mata, dan jikinta ya gama mutuwa tun ɗazu, gashi ko ɗazu sai da Uzair ya jaddada mata baya son a samu matsala.
Sai da Namra ta kai Ƙur'ane mazauninsa ta aje sannan tazo ta zauna kusa da Amira.
“Amira tun ranar ban ganki ba, gashi bana da waya balle na kira ki”
“Wallahi ban samu zama bane kinsan ga makaranta, wai miyasa kika daina zuwa ne mutane sai tambayarki suke”
“Amira kunyar shiga makaranta nake yanzu, a gida ma na kasa sakewa balle makaranta”
“Amman da kin daure ai tun da gani, zai riƙa cire miki kewa, kin ga yanzu fa kina ajin ƙarshe idan kika ce ba zakije ba duk wacan karatun naki zai tafi a banza fa”
Namra ta sauke ajiyar zuciya.
“Ni dai ba wannan ba, kin kawo min magani?”
“Na kawo miki gashi a jaka na, amman ban zan baki ba har sai kin min alƙawarin zaki saka atamfar nan mu fita tare da ke, dan zaman nan ke kaɗai shi ke ƙara miki tunani”
Ta ƙarasa ta ciro rigara daga jaka.
“Ba zan iya ba Amira bana iya fita ko ina yanzu”
“Ni dai ko cikin gida ne”
“Naji yanzu ina maganin?”
“Gashi nan”
Ta ciro ta miƙa mata.
“Gashi amman yace idan kina son yayi sauri zo miki toh ki sha huɗu, kuma yace idan kin sha ki ɗan yawata”
A take Namra ta karɓa ta ɓare huɗu ta shiga bathroom ta sha. Tana fitowa Amira ta miƙa mata rigar.
“Tun jiya na wanke miki ita, ɗinkin nan yaɓa fitar dake ke, je ki saka sai mu fita ko garden ne mu zagaya”
Bata zaton da wata manufar Amira take son ta saka rigar, dan ko a mafarki bata zaton Amira zata iya cutar ta ko kuma a haɗa kai da ita a cuce ta. Sai kawai ta kai hannu ta karɓa, a gaban Amira ta ɗaura zanen rigar kuma da zata saka sai da tayi Bismillah, hakan kuma ba ƙaramin tsoro ya bawa Amira ba, sai dai bata yarda ta nuna ba, har suka fito tare suka nufi garden ɗin.
Wayarta ta ciro ta aika ma Uzair da text.
‘Ta saka yanzu, amman Haila be zo mata ba, na san dai ze zo mata tana sanye da ita’
Ƙarkashin bishiyar mangoro Namra ta zauna, kasancewar ta riga Amira isa gurin, kamin ta zauna taji wayarta tayi ƙara alamar saƙo, sai kawai ta fasa zaman sai ta koma gefen tana ƙoƙarin buɗe saƙon.
‘Amira you fuck up’
Ba shiri ta zaro ido ganin irin reply ɗin da yayi mata.
http://www.khadeejacandy.com.ng/2019/02/zagon-asa12_28.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 13*
Hankalinta ya tashi sosai, har ta kasa jin kiran da Namra take mata, sai da ta yi mata kiran kusan sau huɗu sannan ta amsa kamar a firgice ta juyo ta kalleta.
“Lafiya?”
Namra ta tambaya ganin yanayinta duk ya canja.
Ƙasarowa tayi kusa da ita ta dafa ta tana faɗin.
“Ba komai, Yaya ne yayi min text ina jin Ammy ba lafiya bari naje gida”
“Ko na raka ki?”
“A'a No yi zamanki da sauƙi ai”
Bata tsaya jiran abunda Namra zata ƙara cewa ba, ta nufu hanyar fita da sauri. Hankalin Namra sai duk ya tashi tana jin kamar mahaifiyarta ta ce, har ta unƙura zata tashi sai kuma ta koma ta zauna hango Maryam da tayi tafe ta doso inda take. Kusa da ita ta zauna ta aje hangout ɗinta gabanta tana ƙoƙarin cire hijabinta.
“Anty Namra yanzu shikenan kin yi watsi da karatun ki ko?”
Namra ta sauke ajiyar zuciya.
“Haba Maryam kina min wannan maganar kamar ba kisan halin da nake ciki ba?”
“Allah ya kyauta! Amman ai ke kika jawa kan ki, ya dai kamata ace kin fara yima kan ki karatun ta natsu, ba wai azo a zuga ki kawai ki hau kan layi ba”
“Maryam babu wanda ya zuga ni, kawai kisan bawa baya wuce kaɗɗararsa, dan Allah ki daina ganin laifin Amira”
“Ba laifi ta nake gani ba, amman dai ina tunatar da ke kiyi hankali da yarinyar nan, jikina yana bari babu alheri a abotar nan taku, dan ni tun ba yau na lura da irin shigo-shigo ba zurfi da Amira take miki, dan tana kishin ki”
“Amira bata da wannan Maryam baki fahimce bana”
“Bata da wannan, take kishin ki? Yai Amira tana baƙinciki ta ga kin ɗinka sabon kaya ita ata ɗinka ba, Amira tana baƙincikin ace kin fita zarra a jarabawa, Amira bata ƙaunar a tare ki a hanya ita ba'a tare ta ba, in yau kika saye sabon takalmi sai Amira ta siye, idan aBun farin ciki ya same ki a take Amira take canja fuska, idan wani abu kika samu sai tasan yadda ta shiga ta fita kika hallakarda da shi sannan hankalinta ya kwanta, ke duk baki lura da hakan ba?
Anty Namra ƙarshen duniya muke fa, kuma Annabi da kansa ya faɗa a cikin alamomin ƙarshen duniya akwai rashin amana da cin amana da rashin yarda, Wallahi kiyi hankalin da mutane.
In ma wani sirrin ki ne karki ƙara faɗawa Amira, dan daga lokacin da ke da kanki kika kasa ɓoye sirrinki a cikin cikinki, har kika faɗawa Amira Wallahi kamar kin faɗawa duniya ne”
Namra tayi shiru tana kallon yadda Maryam take tsire baki tana faɗin maganganun, zuciyarta na nazarin kalamanta. Ita kanta a yanzu tana zargin Amira tun daga abunda ya faru da ita, sai dai yadda Amira take nuna mata akwai Aminci a tsakanin su ya kan rikita zarginta.
“Forget about Amira, yanzu dai Abbah yace ki kawo Asim ze aura miki shi how do you feel?”
“I don't know, amman ina jin kamar ban kyautawa Abbah ba, kuma ba zai fahimce ni ba, idan kuma na kawo wani wanda ba Asim na aura Asim zai cigaba da kallo a matsayin mayaudariya, ban san yadda zan yi ba”
“Yanzu dai Uzair ya fasa auren ki, dan haka duk wanda zaki aura babu ruwan Abbah ba kuma ze karɓi wani excuse daga gare ki ba, kinga ƙara ma ki auri Asim ɗin, in yaso sai kiji da Abbah”
“Maryam ban san inda Asim yake ba, Mahaifiyarsa ma tace min bata san inda yake ba, saboda ni ya bar garin nan”
“Ƙarya take tace bata san inda yake ba, shi Asim ɗin yaro ne da zai gudu be faɗawa mahaifiyarsa ba? Baya gari ya akayi Amira ta ganshi?”
“Nima ban sani ba, tace min kiranta yayi a waya”
“Kin gani ko? Wannan Amirar munafukace. Ni zan taya ki nemansa, har gurin uwarsa zanje idan kuma tayi min maganar banza na ci mata mutunci”
“A'a ni dai dan Allah karki mata rashin mutunci, ki bita da lalama”
“Ke fa Anty Namra kina da matsala, mutanen duniya in ka sake sai su ci maka tuwo a ka, kawai idan mutum ya maka zuma sai ka masa wuta, idan kuma ya maka yayyafi sai ka masa ruwa”
“Nidai na ji amman ban da rashin mutunci kinji?”
Ta tsire baki gefe.
“Naji tashi mu shiga ciki, ni yunwa ma nake ji ganin Amirar yasa na shigo nan”
Miƙewar da Namra zatayi sai taji abu ya gangaro mata a ƙafa, tana ɗaga zagen taga jini. Lumshe ido tayi ta buɗe ta kalli Maryam dake kallonta sannan ta riƙa hannunta suka shiga ciki.
Suna shiga Maryam ta nufi kitchen, Namra kuma ta nufi ɗakinta, ta cire kayan jikinta ta gyara jikinta ta saka pad sannan ta saka wasu tufafin.
UZAIR POV.
Sai safa da marwa yake, hankalinsa ya kasa kwanciya, tun lokacin da Amira ta masa text ɗin shirmen data aikata. What if aikin ya dawo gareshi? Tun da malamin yace indai akayi aikin dole ne ya ci.
Najeeb ya dafa shi
“Uzair ka kwantar da hankalin ka mana”
“Haba Najeeb wane irin kwantar da hankali kamar baka san yadda abun nan yake ba, kuma kana ganin taje ta aika mana shirme, ban san abunda yake damun ƴar iskar yarinyar nan ba”
“Ka natsu mana sai mu kira malamin mu faɗa masa abunda yake faruwa”
Sai a lokacin ya zauna, tashin hankali ƙarara a fuskarsa. Kira biyu Malamin ya ɗauka, sai Najeeb yayi masa bayanin komai. Malamin ya daɗe yana jimamin abun sai tambayar yadda akayi suka yi wannan kwaɓar yake.
“Yanzu dai mu saurara nan da kwana biyu mu gani”
“Yanzu Malam babu wani abu da za'a iya yi, babu wata mafita?”
“Mafita ɗaya ce, a nemo kurciyar nan acire layar da aka laƙa mata, kasan kuma mun riga mun saki kurciyar kamunta yanzu ba abu ne mai yiyu ba, sai dai kasan ai da sunan ita yarinyar mukayi dan haka ku ɗan dakata tukuna mai yiyuwa ya iya kamata”
“Ko asa ta cire rigar?”
“A'a duk ta cire rigar ba tare da aikin ya shiga jikinta ba, zai iya dawowa, kasan lamarin iska”
“Okay toh mun gode”
Najeeb na kashe wayar Uzair ya miƙe tsaye yana faɗin
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah ka cece ni Allah”
Jafar ya aje wayar hannunsa ya kalli Uzair yace
“Haba be a Man mana, ai ko aiki zai dawo ba akanka zai koma ba akan Amirar zai koma”
Uzair ya kalleshi
“Amman ai ba ita tayi aikin ba”
“Easy Man ai ita tayi kuskuren, kirata muji yadda tayi wannan banzan shirmen”
Jafar na gama maganar, Uzair ya ciro wayarsa ya danna mata kira.
AMIRA POV.
Kuka take sosai, tun da ta baro gidan su Namra take kuka har ta iso gida. Bata bari Ammy taga shigowarta ba, sai kawai ta shige ɗakinta ta hau kuka baji ba gani. Ita kanta idan za'a tambayeta bata san dalilin kukan ba, ita dai tana jin kuka yana zo mata kawai.
Ganin Number Uzair ce yasa ta ɗauka ta kara a kunne.
“Amira taya kika yi wannan shirmen? Ban faɗa miki ba a son a samu matsala ba?”
“Ai tasa rigar”
“Toh Uban wa yace ki bari tasa ba tare da haila yazo mata ba? Wace irin mahaukaciya ce ke?”
“Yanzu idan ba a yi dai-dai ba me zai faru?”
“Ban sani ba”
Sai ya kashe wayar. A take zuciyarta ta soma raya mata Namra haukacewa zatayi. Kuma ita za a zarga tun da anga shigarta gidan gashi Maryam ta haɗu da ita, hakan yasa ta fashe da kuka zuciyarta na raya mata lallai asirinta na daf da tonuwa.
Haka ta wuni ta kwana da tunanin abunda ze samu Namra, gashi kukan yaƙi ya tsaya mata, ta takure kanta a ɗaki, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin inda zata samawa kanta mafita, dan ji take kamar wani zai faru da Namra, tun da batayi dai-dai ba, kuma ba makawa ita za a zarga. Ji take duk ta tsani kanta, zuciyarta na raya mata ta gudu kawai kamin asirinta ya tonu.
MARYAM POV.
Daga Makaranta ta wuce gidan iyayen Asim. Cikin ladabi tayi sallama ta shiga. Sai Mahaifiyarsa ta amsa mata dan ita kaɗaice yau a gidan. Har ƙasa Maryam ta risina ta gaishe ta. Ta ta ɗan kawarda fuskarta dan ta gane ƙanwar Namra ce tun da sun taɓa zuwa tare da ita.
“Lafiya ƙalau”
“Dan Allah ko Asim na nan?”
“Baya nan yayarki ta zo nan na faɗa mata baya nan, ni ma ban san inda yake ba”
Daga nan sai Maryam ta canja salo.
“Kin san inda yake kam, dan babu yadda za'ayi ace uwa kamar ki bata san inda ɗanta yake ba, shi Asim ɗin yaro ne da zai bar gida yaje nesa ba tare daya faɗa miki ba”
“Au toh ko ƙarya zan miki, macuta maciya amana, bayan kun gama cin moriyar ɗana sannan zaku watsa masa ƙasa a ido, yanzu dan munafurci ne za ku wani zo nemansa kamar ya ci bashin ku?”
“Bashin mu yaci mana, yaje ya ɗaukewa ƴar'uwata hankali ta haukace tace shi take so, yace ta kawo shi a aura mata, shine kuma dan rainin hankali zaki ce baki san inda yake ba, Wallahi sai kin nemo shi duk inda yake ko kuma naje na faɗawa Abbah yasa a kulle ku dake da danginki har sai Asim ɗin ya dawo, dan ba zaku sa muna ƴar'uwa a matsala ba”
“Eh ai zamu iya, tun da ku ƴan siyasa ne ku keda gwannati, amman bari kiji na faɗa miki ni ɗana ba zai aure ƴar marasa mutucin ba”
Maryam ta matso kusa da ita tana zare ido.
“Ooo.... Uwata ce marar mutunci ko?”
“Ni ban ce ba, salon kije ki ƙulla min ƙullaliya, Toh ta Allah ba taki ba”
“Ni dai na faɗa Wallahi ko ki nemo inda ɗanki yake ko kuma duk abunda ya faru dake ke kika ja”
Mahaifiyar Asim ta nuna Maryam da yatsa.
“Ke wannan da ganin ki ba zaki gama lafiya ba”
Maryam ta tuma ta dire.
“Ƙwarai ba zan gama lafiya saboda da kika hallice ni ai baki yi dan na gama lafiya ba, ta yadda idan an je lahira zaki jidaɗin ƙoneni a wuta ko? Ai ke cw ba zaki gama lafiya ba tsohuwa dake kina ƙarya baki san inda ɗan ki yake ba ko kunya baki ji ba”
Ta daki ƙirji.
“Ke ni kike faɗawa wannan maganar?”
“An faɗa ɗin, biri ai a hannun malami ya kan yi guɗa, a hannun bamaguje sai kuka, kuma Wallahi ko ki nemo ɗanƙi ko ki shiga a matsala”
A nan Maryam ta tofar mata da yawu ta wuce, tana bankaɗar mutanen da suka fara cika gidan gurin kallon faɗa.
_____________________________________
Me kuke tunanin ze faru a shafi na gaba?
Anya Asim zai dawo? Da gaske Mahaifiyar Asim bata san inda yake ba?
Ya rayuwar Amira da Uzair akan kuskuren da sukayi? Me zai faru da Namra?
Masu ziyarta shafina, a ƙasan blog ɗin zaku ga gurin subscribe, a nan zaku saka email address ɗin ku ta yadda da nayi sabon updated zaku samu notification, na kan fara sauke post ɗina a can kamin na kawo shi whatsapp.
Ina son ku duka fisabilliah 😘
Best regards 💖
Khadeeja Candy 🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa-14.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
*PAGE - 14*
Sai da aka kwana biyu sannan Maryam ta labarta ma Anty Amarya da Namra yadda suka yi da Maman Asim.
Ran Anty Amarya ya ɓace sosai, daga ita har Namra basu jidaɗin abunda Maryam tayi ba.
“Ke ke Maryam ba wata ba, Allah ya sauwaƙe miki bakin mutane, kullum ana miki magana amman kamar ba'a yi, rashin kunya an faɗa miki abun ƙwarai ne? Ai gashi nan baki mutane akan ki Wallahi Allah ya sauwaƙe miki wannan rayuwa”
Maryam ta ɓata rai sosai, daman tasan za'a rina dan tasan sai Anty Amarya tayi mata faɗa, tun da bata taɓa yaba ma masifar ta ba.
Anty Amarya kam sai harararta take tana jin kamar ta dake ta.
“Aure dai zakiyi kuma mace kike Wallahi ki canja rayuwa dan baki san inda zaki faɗa ba”
“Naji Anty yi haƙuri kin san ni yarinya ce har yanzu”
Namra tayi mata wani kallo
“Kece yarinyar?”
Sai kawai tasa dariya ita da Aisha. Anty Amarya ta ɗauke kai tana amsa sallamar da Ammy tayi.
Cikin tashin hankali ta doso inda Anty Amarya take gyalenta ma a bai-bai ta yafashi.
“Hajiya Amina lafiya na ganki haka?”
Ta zauna saman kujera tana kuka.
“Wallahi ba lafiya ba, Amira ce tun jiya ba mu ganta ba, ba musan inda take ba”
Gaban Namra da Anty Amarya ya faɗi. Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Shine abunda yake fitowa a bakin su. Namra tace
“Amman an bincika ko ina? Kuma bata ga inda zata ba?”
“Bata ce ba, tun ranar data fita tace min nan zata zo inda kike ban sake sata a ido ba sai da safe, ko na na shiga ta tarar tana ta kuka wai kanta ke mata ciwo, sai ce min take tana jin tsoro, na bata magani ta sha sai tayi bachi, ko da na sake leƙawa ɗakin na dubata sai naga bata ciki, na duba ban ga jakarta ba da wayarta, sai na ɗauka ko tazo nan ne, har dare shiru, sai da Abbah ta ya dawo muka yi ta nemanta ba mu ganta ba idan an kira wayarta kuma kashe, haka muka kwana cikin tashin hankali”
Da kuka sosai ta ƙarasa maganar. Sai hawaye suka silalo daga idon Namra a take ta fasa kuka. Anty Amarya tace
“Wallahi rabonta da gidan nan tun shekaran jiya ranar laraba, ban sake sata a ido ba, Allah ya a gaji wannan yarinya ko ina ta shiga?”
Namra ta share hawayen idonta
“Ammy baku mata komai ba? Ba faɗa tayi da wani ba? Kuma babu wanda yayi mata sallama ko da a waje?”
“Wallahi bamu mata komai ba, kuma ni dai ban san wani yayi mata sallama ba, amman dai Babanta ya kai ma ƴan sanda report ko Allah ze sa a gane inda take, amman ke Namra baki san inda Amira zata iya zuwa ba?”
“Wallahi ban sani ba, ranar ma data bar gidan nan naga kamar anyi mata saƙo sai tace min wai kece ba kida lafiya bari tafi gida, washen garin ranar ne ma nace Maryam taje ta duba ki, sai tace min ai sun haɗu da Amira tace mata kin ji sauki”
“Wallahi ni ban yi wani ciwo ba lafiya ta ƙalau, na shiga uku yau ina Amira ta shiga?”
Da kuka ta tashi ta nufi ƙofa. Anty Amarya na bata haƙura har gurin har gurin gate.
Lokacin data dawo ne Hajiya Barau ta tare ta tana tambayar lafiya. Itama salati tasa lokacin tada ji abunda ya faru, suna cikin maganar sai ga Namra ta fito sanye Hijab tana hawaye.
Tana ƙarasowa kusa da su Anty Amarya tace
“Namra ina zaki ?”
“Anty zama be gan ni ba, tun da Amira ta ɓata”
Hajiya Barau ta riƙota
“Wallahi babu inda zaki, kije nemanta kema a ɗauke ki, ko kin manta abunda ya faru ne? Allah dai yasa ba Asim ɗin ne ya sace ba itama”
Namra tayi saurin girgiza kai.
“Wallahi Hajiya ba shi bane, Asim ba ze haka ba, Asim ma baya garin nan gaba ɗaya”
“Uhmm Aifa sai kiyi kuma, irin abunda aka miki ne za a mata, Inshallah mutun ɗaya ne yake muku wannan abun”
“Wallahi ba wanda zuciyarki take zargi bane, Asim baya garin nan”
“Toh a ina yake?”
Hajiya ta tambaya tana mata wani makirin kallo.
“Nima ban sani ba, amman dai ba shi bane”
Anty Amarya ta kasa mata tsawa
“Ai sai ki tsaya nan kina gardama da uwarki akan abunda baki da tabbaci, wuce ki koma ciki babu inda zaki je”
Ba dan taso ba, ta juya ta koma ciki tana kuka. Anty Amarya ta rufa mata baya tana ta mata faɗa wai tana gardama da Hajiya kamar ma uwarta.
Hajiya Barau ta tsire baki ta shige part ɗinta zuciyarta na raya mata Namra ta san inda Amira take.
Bedroom ɗinta ta shige ta ɗauki waya ta kira Uzair tana labarta masa abunda ya faru. Ya kaɗu matuƙa shi kansa ya kwana biyu yana kiran wayar Amira amman baya samu. Sai dai wani ɓangaren hankalinshi ya kwanta ganin kamar asirin kan Amira ya koma ba kansa ba.
Bayan ya gama waya da Hajiya ya kira Najeeb ya labarta masa ɓatan Amira.
“Kaga abunda nake faɗa maka ko? Ai daman nacw maka aikin ba akan ka ze dawo ba akan Amira ze koma”
“Ban sani ba ko nawa na nan tafe Najeeb, amman ina cikin tashin hankali”
“Ka kwantar da hankalinka babu abunda ze faru, amman kuma ka rufe wannan maganar”
“Ya za'ayi ma an faɗa, Allah dai ya sauwaƙe, Ni wallahi ba zan sake irin wannan abun ba”
Najeeb yasa dariya.
“Uzair ka cika tsoro da yawa, shiyasa ka yi sake har waɗannan abubuwan suka faru”
“Ni dai naji”
Daga haka ya kashe wayar, ya nufi ɗakin matarsa.
Hajiya na gama waya da Uzair sai ta kira wata ƙawarta wace take taubashiyar Ammy. Bugu ɗaya zuwa huɗu ta ɗauka.
“Assalamu Alaikum”
“Wa'alaikissalam Hajiya yanzu nake labarin ki, nace ko kina da labarin abun da ya faru?”
“Wallahi bani da labari sai yanzu nake jin abunda ya faru, shima fa dan Ammy tazo da kanta ne dan Wallahi sam ni Amarya bata faɗa min ba”
“Au kina nufin sai yanzu kika ji?”
“Wallahi sai yanzu shiyasa ma nakira ki, Namra ta ɗaki ƙasa ta rantse ita ba Asim bane ya sace Amira”
“Wanene Asim kuma?”
“Ina wani tsohon Saurayin Namra wanda na taɓa baki labari nace miki mahaifinta ya mata miji amman tacw bata so sai shi ko kin manta?”
“A'a na tuna ɗan makarantar su ko?”
“Allah ya bar ki, shi ne fa, toh ai kinsan shine ya sace Namra kwanakin baya har shiyasa ma mijin da zai aureta yace ya fasa”
“Ke ya sace fa kika ce?”
“Wallahi ya sace ko kuma ta bishi ba, kuma kinga ita Amira ta faɗa tace shine yazo ya tafi da Namra ɗin kuma duk nan mutane unguwa sun shedi haka dan sunce sunji lokacin da yake magana, har fa iskanci yayi da ita”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un toh wai ko sha ya sace Amirar?”
“Nima dai shi nake zargi, kuma magana ta gaskiya Namra tasan inda Amira take saboda tasan inda shi Asim ɗin yake, saboda ɗazu take take ƙoƙarin kare shi wai baya garin nan me me magana babu kai babu gindi”
“Amman wannan magana ai bata kyalewa bace, indai har haka ne dole ne a nemi Namra ɗin kuma ita da kanta Ammy tace min Namra ce mutum na ƙarshe da Amira ta gani”
“Ai ke dai bari ƙawayen zamani ai sai a hankali, Allah dai ya bayyana ta”
“Amin bari na kira Ammy yanzu”
Hajiya Barau tayi saurin cewa.
“Dan Allah karki ce gare ni kika ji, kinsan halin Alhaji balle kuma baka kake iko da gida ba, sai ace kayi ma ɗan kishi shaeri”
“Haba dai Hajiya sai kace wata ƙaramar yarinya da zanje nace ke kika faɗa? Ai babu wannan tsakanin mu”
“Toh na gode sai na jiki”
Daga haka ta kashe wayar.
KALSOOM POV.
Kwata-kwata Hilal be yi zuwa huɗu ba Daddy yace ya turo iyayensa. Shi kuma daman haka yake son yaji, satin daya zagawo iyayen Hilal suka neman auren Kalsoom, farin ciki gurin mahaifiyar Hilal kamar ta zuba ruwa ƙasa ta sha.
Iyayen basu bar gurin ba har sai da Daddy da ƴan'uwansa suka yanka musu sadakinta dubu saba'in suka biya sai Daddy yasa musu rana dan ba so yake aja abun da nisa ba, shirin da biyar ga watan huɗu. Cikin farinciki da jindaɗi suka bar gidan.
A ranar Rashida bata yi bachi ba saboda baƙinciki, kwana tayi kuka Hilal na rarrashinta. Washen garin ranar da akayi abun Kalsoom taje aiki sai suka riƙa taya ta murna suna ce mata amarya. Tayi mamakin inda suka samu labarin tun dai ita ban da ƙawarta Salma bata san ta faɗawa kowa ba, da Momy tace mata ƙara kawai mutane suji za'a ɗaura mata aure.
Sai daga baya suka faɗa mata ai Asma'u ce ta faɗa musu. Kalsoom ta kalli Asma'u tana dariya
“Asmee ina kika ji?”
“Abun sheri ma be ɓoyu ba balle na alheri”
“Ni ina mamakin ta ina kika ji”
“Ai tuni ni na sani dan har a wayar mijin naga hoton ki, ido na sa miki dan naga indan zaki faɗa”
Sai duk suka sa dariya. Suka mata barka da Allah yasa alheri.
Bayan ta wuce office ɗin ta Asmee ta bita tana zolayarta
“Amaryar mu amarya mu”
Kalsoom ta ɗora jakarta saman tebur tana dariya.
“Wai daman Hilal ɗan'uwan ku ne?”
“A'a unkuwar mu ɗaya dai da shi, kuma mijina abokin shi ne”
“Allah sarki ke haka unguwarku daya ba”
“Amman Wallahi kin yi dacen miji, gaskiya Hilal yana da mutunci sosai, gashi bawon mata sai yadda kika yi dashi, matarsa ma ba daɗinta yake ji ba amman sai juya shi take”
“Kin san matarsa kenan?”
“Sosai ma, amman wallahi ƴar banza ce sai kin shirya zama da ita hmmm amman aje aikinki zakiyi ko?”
“Haka yace wai baya son aiki”
“Ai saboda aikin matarsa zai ƙara aure dan ya son ya hanata aiki amman ba dama”
“Saboda me?”
“Ai ma'aikaciyar banki ce ƴar gidan su Dr. Ayuba matsayi, kin san ai ƴaƴan gidan ba daga baya ba, haka ake cewa wai aba a musu kishiya, uwarsu ma duk masifar Uban sai tun da ya aure mui”
Ta ƙarasa tana shafa baki. Ganin yadda Kalsoom ke kallonta yasa ta tsargu sai ta tashi daga saman kujerar da take zaune tana dariya tace
“Bari na koma gurin zamana kar MD ya tararda ni a nan ina tsiyaya”
Nan ma Kalsoom murmushi kawai tayi. Sai ta nufi ƙofa tana faɗin
“Mu dai ayi auren nan da wuri aje ayi mana rainon ƴan ɗiyan mu, Allah ya sanya alheri”
Da Amin Kalsoom ta amsa ta bita da kallo tana nazarin maganganunta.
NAMRA POV.
Wuni Namra tayi addu'ah tana ba Allah cigiyar inda Amira take. Duk hankalinta ya tashi ji take kamar ita ce ta ɓata, abu ɗaya zuciyarta ke ayyana mata wato Uzair, sai dai ta kan tambayi kanta da kanta ma zai haɗa alaƙa tsakanin Uzair da Amira.
Kiran da taji Maryam tana mata yasa ta tashi daga saman sallayar da take ta nufi falo.
Tsatsaye ta tararda su Anty Amarya da wasu police biyu mata tsaye a falo. Gaban Namra ya faɗi, da sauri ta ƙaraso kusa da su.
“Lafiya?”
Sai ɗaya daga cikin ƴan sandar ta nuna mata id cart ɗinta.
“From Marna Police station, Muna zargin da a hannu gurin kidnapping ɗin Amira, abokan aikin mu suna waje, zamu je da ke a station”
Ba shiri Namra ta daki ƙirgi tana nuna kanta.
“Ni....?”
Da sauri Maryam ta nufi part ɗin Abbah tana kuka. Anty Amarya ma kuka take ita da Aisha. Kamar an jefo Hajiya Barau sai gata cikin ɗakin tana salati da sallami.
____________________________________
THERE WORDS FOR THIS CHAPTER...!
WHAT DO YOU EXPECT NEXT?
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 😘💖🌺
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa12.html
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 15*
Suna fitowa waje Abbah na kawowa. Sai ya tsayar da ƴan sanda yana tambayarsu.
“Miya faru haka?”
“Sir muna tuhumar Namra ne da sa hannu a gurin sace Amira”
Abbah yayi ma Namra wani kallo. Sannan ya kalli ƴan sanda yace
“Ɗaya daga cikin ku zata biyo ni muje cikin motana”
Ba su musa masa ba, ɗaya daga cikin police ɗin ta bi Abbah suka shiga mota ita da Namra baya, Anty Amarya a front seat.
In banda kuka babu abunda Namra take har aka isa station ɗin. Sannan Abbah ya fita suka shiga cikin station ɗin. Ammy da ƙanwarta na tsaye a gurin idonta A kumbure.
A take wani police ya karanto masa abunda ake zargin Namra da shi, sannan yayi musu jaga zuwa office ɗin dpo. Sai da ya gama da wasu cases sannan ya su Namra suka iso gurin ya gaisa da Abbah cikin mutumci yana girmama shi.
“Ranka ya daɗe Ashe kai ne”
“Nine Wallahi ya aiki ya kwana biyu”
Abbah ya faɗa ba dan ya waye shi, sai dai shi ɗin yasan Abbah kasancewarshi sanannen ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa.
Bayan Abbah ya zauna, Namra ta zauna a kujera dake kusa da Abbah, sai Ammy ta zauna a kujarar dake gefen Namra ita da ƙanwarta.
DPO ya kalli ya dubi takarda take gabansa ya kalli Namra yace
“Amm Namra Usman ana zargin ki dasa hannu gurin ɓatan ƙawarki Amira...”
Kasa magana Namra tayi sai kuka take. Abbah ya katsa mata tsawa.
“Ki buɗe baki kiyi magana mana”
Sai kawai ta ƙara rushewa da kuka kamar zata tsuƙe. Anty Amarya tace
“Taya zata iya magana? Bayan irin ƙazafin da aka mata, a rasa wanda za'a zarga sai ita, lokacin da Namra ta ɓata miyasa bamu zargi Amira ba, ko ita Namra ba ƴa bace? Ko kuma ni ban san zafin ta ba? Faɗa min ɗa ya fi ɗa ne? Wallahi Allah sai ya saka mata shikenan dan anga yarinya bata magana komai aka kwaso sai a dire a kanta, dan kin rikice akan neman ƴarki sai ki ɗauka ki ɗorawa wani, me kuke da shi da har Namra zata sa a ɗauke Amira, wallahi ke kinsan Namra ta fi ƙarfin Amira nesa ba kusa ba...”
Dpo ya miƙe tsaye yana ɗaga ma Anty Amarya hannu.
“Dan Allah Hajiya ki saurara, an zo nan dan a sasanta ba dan faɗa ba”
Bayan ya zauna ya kalli Namra yace
“Ki kwantar da hankalin ki ba wani za'a miki ba, nan guri ne na...”
Ƙwanƙwasa ƙofar da akayi ne ya hana Dpo ƙarasa maganarsa.
“Yes come in”
Wani ɗan sanda ne ya shigo ya sare masa sannan yace
“Sir Alhaji Haruna is here to see you”
“Let him in”
“Yes Sir”
Ya sake sare masa sannan ya juya ya fice. Sai ga Abbah Amira ya shigo cikin ɓacin rai, idonsa be sauka ko ina ba sai akan Ammy, nunata yayi da yatsa.
“Amman Wallahi Asiya baki jin magana, yanzu duk maganar da na miki baki ji ba, sai da kika aikata? Yanzu miye amfanin haka? Ki zubar da kanki mutuncin kawai”
Ya ƙarasa yana miƙawa dpo hannu suka gaisa.
“Wannan maganar bata ma kamata ta fito bakin ki ba, dpo ban kawo maka rahoton ɓatan yarinyar nan ba? Babu inda ban kai rahoton nan ba”
Dpo ya ɗaga masa kai yana murmushi. Abban Amira ya miƙa Abbah hannu suka gaisa
“Alhaji Usman, yau dai mun yi zumunci dole, mata sun haɗa mu”
Abbah yayi dariya.
“Kasan sha'anin mata sai haƙuri, ba tunani suke ba idan zasu yi abu”
“Wallahi basa tunani yanzu miye amfanin wannan abun? Yanzu haka sai da aka kira ni daga gwuiwa station aka ce min ance anga Amira a tashar mota amman basu san motar data shiga ba”
Ammy ta fashe da kuka.
“Wallahi babu abunda ze sa Amira ta gudu tun da ba wani abu muka mata ba”
“Toh aljana ce aka gani kenan? Ko kuma ƙarya suke, tashi ki wuce gida bana son maganganun banza”
Cewar Alhaji Haruna Abban Amira. Abbah yace
“Karka ga laifin ta duk haka muke fama dasu inda mata ne sai haƙuri”
“Magana ce da bata da toshe balle makama ban san inda ma wannan maganar ta fito ba”
Cikim kuka tace Ammy tace.
“Hajiya Barau ce ta faɗa kuma ai ba zata yi ƙarya ba”
Abban Amira ya nuna ta da hannu yana kallon Abbah.
“Kaji ko? Jita-jita ne kawai”
Abbah yayi shiru yana motsa baki alamar nazari. Alhaji Haruna ya kalli Ammy da Ƙanwarta yace
“Ku tashi muke gida”
Da kuka Ammy ta tashi ta fice, sannan ya kalli dpo ya ciro wasu ƴan kudaɗe a aljihunsa ya aje gaban teburin dpo
“Dan Allah aka kashe maganar nan dpo, matsala ta cikin gida ayi haƙuri”
“Ba matsala, muma ai mun fi son haka”
Tare da Abbah suka fito. Anty Amarya na riƙe da Namra har suka fito harabar station ɗin. Sun ɗan daɗe suna fira da Alhaji Haruna sannan sukayi sallama cikin mutunci ya wuce Abbah kuma ya nufi Motarsa.
Har Abbah ya iso gida Anty Amarya masifa take, tana kiran Hajiya Barau da munafuka.
“Ai itama ta haifi ƴaƴa mata, zata jidaɗi idan aka mata haka? Me Namra ta tare mata ne? Ai Wallahi duk mace data ɗuka ta haifi mace tace wata macen ba zata jidaɗi ba sai Allah ya gwada mata akan ƴaƴanta”
Sai da Abbah yayi parking sannan ya kalli Anty Amarya yace
“Bana son ƙananan maganganu, ki wuce part ɗin ki ki bar ni da ita kawai”
Bata sake cewa komai ba, dan tasan halin Abbah zai iya juyarda faɗan akanta. Sai kawai ta buɗe ta fita ita da Namra suka nufi part ɗinta Abbah kuma ya nufi part ɗin Hajiya Barau.
Tana ganin Abbah hankalinta yayi mugun tashin, kamar tasan asirinta ya tono, ko da yake ta karanci yanayinsa shiyasa zuciyarta ta ayyana mata lallai akwai laifin da tayi masa.
Abbah be kula jikokinta da suke falon ba ya hauta da faɗa, daman haka yake idan ya tashi matsifa babu ruwanshi da wanda yake zaune. Ta inda Hajiya barau take shiga bata nan take fita ba, tun tana ƙoƙarin kare kanta har ta kai ga fasa kuka tana faɗin
“Ni Wallahi ba da wata niya nayi ba, kuma tun da daɗewa mukayi wannan maganar fa”
“Ni dai na faɗa miki, ki iya bakin ki ko kuma duk abunda ya same ki ke kika ja, Namra dai kin kusa jikanya da ita, dan haka ba dai-dai bane ki zauna kina faɗan mugaye kalamai akan ƴarki”
Kuka take sosai tana faɗar wai ƙazafi aka mata, har jikokinta suka dafata suna bata haƙuri. Sannan Abbah ya tashi ya nufi part ɗinsa.
Namra na kwance jikin Anty Amarya tana sauke ajiyar zuciya Maryam tace
“Wallahi Allah sai ya saka miki daga Ammy har tsohuwar makirar can Hajiya”
Anty Amarya ta katsa mata tsawa.
“Ke matar uwanki zaki cewa makira ko dan darajar tsufanta kya ce mata haka, balle tana auren uban? Kin gani ina ja miki kunne akan rashin kunyar nan kina ƙarawa ko? Wallahi kika kai ni ƙul sai na ɓata miki rai”
Miƙewa tayi tsaye cikin fushi ta miƙawa Namra takardar dake hannunta.
“Ke ni dai karɓi, Asim ya zo baki nan yace a baki”
Da sauri Namra ta ɗago ta kai hannu ta karɓi takardar, sai ta share hawayenta ta tashi ta nufi ɗakinta, zuciyarta cike da zazzanar son sanin abunda takardar ta ƙumsa.
__________________________
Wannan shafi na ƴan TASKAR KHADEEJA CANDY ne, da CLASSIC LADIES, tare da NAMRA FANS GROUP. I really appreciate your comments 💖💖💖
https://chat.whatsapp.com/LHd6gwdQQWZKNeHU9z4qf0
Masu tambayan grp ga link nan. Amman ban da maza ❌
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 16*
Natsuwa tayi sosai ta tattara dukan hankalinta ta mai da gurin takardar, sannan ta buɗe ta soma karantawa.
_SALAM_
MY DEAR NAMRA.
Na zo gidan ku ance min baki nan, na kira wayarki ban samu ba, mahaifiyata kuma ta shaida min kina nema ma, ban san ta yadda zan iya ganin ki ba amman ga sabon number waya na ki kira ni dan Allah.
Urs ASIM.
Wani dogon ajiyar zuciya ta sauke, ta rumgume takardar a ƙirjinta ta lumshe ido, tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta ɗauki daƙiƙa goma zuwa shabiyar kamin ta buɗe idon, ta tashi ta nufi ɗakin Maryam.
Dariya ta tararda Maryam na ƙyalƙyala kamar wata sabuwar mahaukaciya, har ta zauna kusa da ita bata san ta zauna ba, tana taɓa ta ta zabura.
“Wayyo Allah na”
“Ke lafiyan ki?”
“Wallahi wani littafi ne nake karantawa mai shegen dariya”
“Littafi kuma ai ke Allah be raba ki da karatun littafai ba”
“Wallahi Anty Namra yayi daɗi kamar me, da zaki karanta kema da kin sha dariya”
“Idan na samu time zan karanta, meye sunan littafin?”
“Noor na Khadeeja Candy”
“Okay ni dai ara min wayarki wani abu”
“Ke dai ce zaki kira Asim ba wai kiyi wani abu ba”
“Naji ni dai bani”
Sai da tayi saving ɗin page ɗin, sannan ta miƙa mata wayar tana zolayarta. Namra dai bata ce mata komai ba ta tashi ta fice tana faɗin.
“Ina fatar da Akwai kuɗi a ciki”
“Kai kaji ki da wata magana, manyan Babe's irin zasu zauna waya ba kati, taf mune tare da manyan samarin garin nan fa, kin san ko dan karya dole a saka mana manyan kati ”
Da dariya Namra ta fice, ta koma ɗakinta. Takardar ta ɗauko ta saka Number ta danna kira. Ringing biyu zuwa uku yayi picking da sallama.
Sai da ta lumshe ido ta buɗe da murmushi sannan ta amsa masa.
“Wa'alaikassalam. Asim”
“Namra...”
Daga cikin wayar tana jin lokacin daya sauke ajiyar zuciya, sannan yace
“Namra wai Abban ki ya yarda na aure ki?”
Kai ta ɗaga masa kamar yana gabanta, hawaye suka silalo mata.
“Ya yarda Asim, shiyasa na neme ka”
“Alhamdulillah”
“Ina kaje Asim? Ashe zaka iya tafiya wani guri ka bar ni?”
“Namra idan mun haɗu zamu yi magana”
“Yaushe zaka zo?”
“Ba zan iya zuwa gidan ku da sunan hira ba, sai dai mu haɗa ta layin su Azeema”
“Okay gobe da ƙarfe tara dan Allah”
“Allah ya kai mu I Love You”
“I Love You More”
Daga haka ya kashe wayar. Sai ta rumgume phone ɗin tana murmushi tare da hawaye.
KALSOOM POV.
Kusan kullum sai Doc. Hilal ya kirata a waya sun gaisa, sai dai fira ce be cika zuwa ba sai jefi-jefi. Sau biyu ya taɓa kawo mata ƴaƴansa suka gaisheta ita kuma tayi musu goma na arziki.
Ana sauran sati biyu biki Doc. Hilal ya nemi ta bashi list ɗin abubuwan da zata yi na biki. Bata rubuta wasu abubuwa masu yawa ba, bayan abubuwan da al'ada ta tana da.
Batayi wata hidima ba duk da kasancewar ƙannenta sun so tayi, amman bata biye musu ba, wai ita ta girmi wannan yanzu.
Kala kusan arba'in da huɗu yayi mata, duk masu kyau da ɗaukar hankali, kowa ya gani sai ya yaba, wasu na faɗin haƙurin da tayi yanzu zata ci riba.
Ranar laraba aka saka amarya lalle a daren ranar akayi wankin amarya, washegari alhamis akayi ƙunshi da kitso, friday akayi walima, Assabar aka ɗaura aure Kalsoom da Doc Hilal.
Daddy yayi mata nasiha mai ratsa jiki, gwaggwanin suka mata jan kunne akan rayuwar gidan aure kamin Momy ta ɗora da nata. Kuka sosai Kalsoom tayi a lokacin da aka fito da ita za a saka ta mota zuwa gidan mijinta. Duk wanda ya gani zai yi zaton bata son auren ne.
Da ƙafar dama ta shiga gidan aurenta tana ƙorar shedan kamar yadda Momy ta faɗa mata. Sai da aka zaunar da ita a saman gadon aurenta sannan ta tsagaita kukan.
Batayi zaman minti ashirin ba abokan ango suka shigo tare da ango, sai zolayarsa suke, anyi siyen baki da wasu abubuwa da al'ada ta tanada sannan suka yi musu addu'ar zama lafiya.
Har gurin ƙofa Hilal ya raka abokansa, yayi ma ƴan'uwan amarya da wasu daga abokanta sallama sannan ya rufe ƙofar.
A maimakon ya koma ɗakin Kalsoom, sai ya nufi ɗakin Rashida dan duba halin da take ciki.
Zaune ya tararda ita ƙasan carpet tana wani irin kuka kamar ranta ze cire, wata cousin ɗinta na kusa da ita tana bata haƙuri.
“Habiba ɗan bamu waje”
Ya ƙarasa faɗar yayinda yake zaunawa kusa da ita, janta yayi izuwa ƙirjinsa ya rumgume ta sosai.
“Shiiiiiiiii. Wannan hawayen ban ga dalilin zubar da su ba Ammyn Rafiq, kin san ba ɗan bana son ki bane yasa nayi aure sai dan sauwaƙe miki wasu abubuwan, a maimakon kiyi farin ciki sai kuma kiyi kuka?”
“Ina son Hilal ina kishin naga wata a tare da kai, zan iya mutuwa Hilal”
Ta faɗa tana ƙara narke masa a jiki. Saman kanta ya shafa ya sumbanci shi sannan yace
“Allah ya sassauta miki wannan kishin Pyar, I Love You so much amman ina son ki so abunda nake so”
Kuka tayi sosai har sai da maƙoshinta ya bushe sannan ta sassautama kanta, har kuma lokacin Hilal na rumgume da ita yana rarrashinta.
“Pyar”
Ta ɗago kai ta kalleshi da kumburarin idanuwanta.
“Karki sa damuwa a ranki kin ji? Mijinki yana son ki matuƙa, kuma baya da niyar cutar da ke”
Ta ɗaga daga jikinsa.
“Tashi kaje kar na shiga mata haƙƙi”
“Zanje amman sai kin yi min alƙawarin zakiyi bachi!”
“Zan yi”
Babbar rigarsa ya cire, da ita ya gyara mata fuskarta, ya goge majinar data ɓata mata gaban riga sannan ya kai bakinsa cikin nata yana kiss.
Ya ɗauki lokaci mai tsawo yana kiss ɗinta da shafa wani ɓangare na jikinta, har sai da ya tabbatar ya kashe mata jiki, sannan ya ɗaga ya kalleta.
“Good night Pyar”
“Good night”
Sai ya sumbaci goshinta.
“Dream me i love you”
Ɗan murmushi ta sakar masa kaɗan. Sannan ta sake shi ya tashi, ya baro mata ɗakin zuciyarsa cike da zumuɗin zuwa gurin Amaryarshi.
Da sallama ya shiga ɗakin yana murmushi, sai ya zauna kusa da ita ya kai hannu ya yaye lulluɓin dake kanta.
“Wannan Amaryan bakinta da tsada yake, har ta kasa amsa sallamar angonta”
Hawayen daya gani a fuskarta ya tada hankalinsa. Dan be yi zaton macen data kai kamar Kalsoom idan anyi mata aure a zamanin nan zatayi kuka ba.
“Wannan hawayen na minene My Queen? Ashe yau ba ranar farincikin mu bace? Ai kamata yayi mu gode Allah ko?”
Ita kanta bata san hawayen minene take ba, na farincikin yau Allah ya gwada mata aurenta, ko kuma na yanayin da take ciki na baƙincikin rabuwa da iyayenta.
Matsawa yayi daf da ita sai ya kai tattausan hannunsa ya share mata hawayen, ya kwantar da ita jikinasa, yasa babban yatsansa da mai bi mata yana mata saƙa a jiki.
“Ranar yau ba ranar kuka bace ranar murna ne, ranace da zaki gode Allah kuma ki shirya karɓar angonki da kyakkyawar tarba”
Notse kanta tayi cikin ƙirjinsa, jikinta na amsa saƙon da ƴan yatsunsa suke kai mata. Tana jin wasan ya canja salo sai ta zame jikinta, idonta cike da nauyin kallonsa.
Murmushi yayi yana wani lumshe ido yana buɗe, sannan ya janyo ledar dake gefensu ya buɗe ya ɓalle lemun dake cikin kwali ya ɗauko cup ya zuba mata. Duk yadda taso ta ci da kanta ƙin yarda yayi a dole ta haƙura yayi feeding ɗinta, ba dan tana jindaɗin yadda yake bata ba, abun ka da wanda be saba ba.
Bayan sun gama, ya riƙa hannun tana mursa lallen dake hannu tare da yaba.
“Amman wanda tayi miki lallen nan ta iya lalle gaskiya, yayi kyau sosai”
Yadda yake taɓa hannun nata yasa tsigar jikinta tashi. Duka hannayensa yasa yana luddar hannun nata, a ɗan space ɗin dake tsakanin fingers ɗinta yasa one finger ɗinsa yana mata tafiyar tsusa, sai kallon yanayinta yake, gaba ɗaya idonsa sun koma kamar ba nashi ba.
Janye hannunta tayi ta miƙe tsaye.
“Bari mu tashi mu yi sallah”
Murmushi yayi ya dantsi bakinsa, sannan ya tashi ya nufi bathroom ɗin.
Tun da sunayi sallah godiya be yarda ya kai hannunshi ya sake taɓa jikinta ba, in banda kayan bachi daya ciro a closet ya miƙa mata sai shima ya saka nasa. Sannan ya hau saman gadon ya kwanta ya bata baya, be juyo ba sai asuba.
Bayan sun yi Sallah, ta hau gado ta kwanta, shi kuma ya fita dan duba uwargidansa.
A kitchen yaji motsinta, hakan ba ƙaramin bashi mamaki yayi ba, da sauri ya nufi kitchen ɗin ba dan zuciyarsa ta yarda da ita ɗince a kitchen ba.
“Wow Pyar me kike yi?”
Ta juyo ta kalleshi da murmushi, fuskarta acan-acan da kwalliya kamar ita ce amaryar.
“Breakfast nake haɗa muku”
Ya zagaye ƙugunta da hannayensa, zuciyarta cike da jindaɗi.
“Seriously Pyar? Amman gaskiya kin kyau mana, so faɗa min jiya kin yi bachi?”
“Nayi bachi mana, ai nasawa rai na zan iya ne”
“Good girl”
Yaja hancinta, wanda hakan yasa ta dariya.
“Amman ni dai Doc Ina jin tsoro, kar yarinyar nan ta amshe min kai, wasu ba aure Allah suke ba burinsu kawai su fitar da matar gida su maye gidan da ƴaƴanta”
“No no no, wannan yarinyar ba irinta na auro miki ba, tana da tarbiya fiye da tunanin ki”
“Allah yasa”
“Amin”
Sai ta ɗago kai ta miƙa masa bakinta sukayi kiss, sannan ya rumgume ta a kafaɗa kamar wani ƙaramin yaro.
Har ta gama soya dankalin rumgune yake da ita ta baya, sai da ta fara jera kayan abincin sannan ya sake ta da nufin zuwa ya tashi Kalsoom.
Har lokacin bachi take hankalinta kwance. Da murmushi ya ƙarasa kusa da ita, zanen bachinta ya fara yayewa, yasa hannunshi ta ƙasan wandon bachinta ya soma shafa ƙafarta zuwa cinya.
Wani yarrr taji, sai tayi saurin buɗe ido ta tashi tana kallonsa. Murmushi yayi ya hau saman gadon ya ɗora kansa saman wuyanta.
“Good morning Queen ina fatar kin tashi lafiya?”
Kamin ta amsa ya zira halshensa yana lasar wuyanta, ya kai hannunshi saman ƙirjinta, ya soma murza breast ɗinta a hankali, lumshe ido tayi zuciyarta cike da ƙyamar abunda yake mata. Tana jin ya fara ƙoƙarin ɓalle bottom ɗin rigar bachinta tayi saurin riƙe hannunsa, ta buɗe ido ta tashi.
Sai shima ya miƙe tsaye yana murmushi.
“Je kiyi brush zamu ci abinci”
Bata tace komai sai kawai tayi murmushi, ta nufi bathroom, shi kuma ya fice ya nufi nashi ɗakin dan wanke bakinsa.
Bayan ta fito ta ɗauki mayafinta na jiya ta rufa a jikinta sannan ta nufi falon. A lokacin Hilal har ya hallara a dinning yana riƙe da hannun uwar gidansa.
Yadda taji abu ya soki zuciyarta sai taji kamar karta ƙarasa kusa da dinning ɗin, sai dai tayi ƙarfin halin ƙirƙirar murmushi ta ƙarasa tana gaisawa da Rashida.
Rashida da kanta ta zuba ma Hilal abinci sannan ta zuba ma Kalsoom, sai ta zuba ma kanta.
“Ina Ezzah?”
Ƙalsoom ta tambaya. Sai Rashida tayi murmushi tace
“Suna bachi around tara da rabi zasu je islamiya, idan na tashe su yanzu zasu dame mu ne kawai”
Ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin zaunawa, zamanta keda wuya sai hawaye ya gangaro ta idonta ya wanke mata fuska, da sauri ta tashi.
“Am sorry”
Sai ta nufi ɗakinta. Sai Hilal yayi saurin tashi ya rufa mata baya. A take yanayin Kalsoon ya canja har ta haɗiye wasu yawu da ƙarfi, ta sauke ajiyar zuciya tana kallon yadda abincin ya fita ranta.
NAMRA POV.
Tara saura mintuna Namra ta saci jiki, ta nufi gidansu Azeema. Sai da ta kusa ƙarasa sannan wani tunanin yazo mata.
Sai ta yanke tafiyar ta dawo gida, a lokacin an buɗewa Abban gate zai fita, taji kunyar ganinsa sosai sai dai sa'arta ɗaya dawowa ne tayi ba fita ba da fita ne da me zata ce masa?
Lokacin data kawo kusa da shi ya zuƙe gilashin motarsa yana mata wani kallo.
“Daga Ina mike?”
Ta ɗanyi jikiri gurin bashi amsa saboda tunanin ƙaryar da zata masa.
“Az- Azeema ce bata da lafiya shine yaje na dubata”
“Da izinin wa?”
“Anty”
“To kar na sake ganin kin fita ke kaɗai”
Be jira amsar ba ta ya ɗagarda gilashin motarsa, direba ya jashi yayi suka yi gaba.
Ta hanyar kitchen ta biyo ta shigo falo, sai rabon ido take idan wani be ganta ba.
Al-hamdulillah falon ba kowa hakan ya sata jindaɗi, cikin natsuwa ta nufi ɗakin Anty Amarya.
“Wa'alaikissalam”
Ta amsa sallamar Namra a yayinda ta aje kofin tea dake hannunta saman bedside drawer.
Kusa da ita Namra ta zauna tana tauna maganar da zata mata.
“Anty kin ga jiya ai Maryam ta bani wasiƙa ko?”
“Uhm”
“Asim ne ya bar min ita wai yazo be same ni ba, shine ya rubuta min number wayarsa, sai na kira da wayar Maryam, yace min mu haɗu a gefen gidansu Azeema”
Anty Amarya ta girgiza mata kai
“A'a ke yanzu girman ki ne a ganki a ƙofar gidan wa su kina fira? Yazo gidan ku mana, sai kace wani baƙo”
“Wai shi yana jin ba daɗi idan yazo nan gidan”
“Cinye shi zamuyi? Ai ko yanka namansa ake dole ne yazo nan indai yana son ki”
Shiru Namra tayi tana nazari. Anty Amarya ta mire baki.
“Uhm- Allah dai yasa kina son Asim ɗin nan yana son ki kamar yadda kike son sa”
Murmushi kawai Namra tayi, ta kai hannu ta ɗauki wayar Anty Amarya dake gefenta.
“Bari na kira shi”
Sai ta tashi ta fita. Ɗakinta ta dawo ta sake ɗauko takardar ta saka number ta kira. Ringing tayi har ta katse be ɗauka ba, sai da ta ƙara kiransa sannan yayi picking.
Tana yin sallama ya gane ta.
“Namra gani a gurin ban gan ki ba”
“Ina gida Anty tace ba sai dai kazo gida”
“Namra ina jin tsoro, bana son zuwa gidan nan naku kallon wulaƙanci ake min”
“Kazo mana babu koma ma, Hajiya tana part ɗinta, Maryam da Hindatu sun tafi makaranta, Abbah ma ya fita”
“To gani nan zuwa”
“Gidan ka shigo kaje gurin Garden”
Daga haka ta kashe wayar, ta mayarwa Anty Amarya.
“Anty ga wayarki na gode”
“Ke kin hallaka taki wayar ko?”
Murmushi tayi, ta juya ta fice. Firjin ta buɗe ta ɗauki lemu da kofuna, sannan ta nufi garden zuciyarta cike da zumuɗin son ganin masoyinta.
A-ƙalla ya ɗauki mintuna goma shabiyar, sannan ya iso, da faɗuwar gaba ya buga ƙofar gate ɗin. Sai mai gaɗinsu ya buɗe masa yana tambayar wanene.
“Nine ko Namra na ciki?”
“Eh tana ciki”
Mai gadin ya buɗe masa ƙofa, yana mamakin ganinsa.
Gidan ba baƙonsa bane, dan haka be sha wahala ba gurin ɗaukar hanyar da zata sadashi da garden ɗin. Namra na hango shi ta miƙe tsaye ta rumgume tana murmushi, ta hannayenta, idonta ya cika da ƙwallah.
Shima murmushin yayi yana kallon yadda ta rame tayi baƙi kamar ba ita ba.
“Namra ashe zan ƙara ganin ki?”
Bata bashi amsa ba sai kawai ta nuna masa kujerar dake facing ɗin nata. Bayan ya zauna sai ta zauna tana share hawayenta.
“Asim ina ka tafi?”
“Katsina naje gurin wani Ƙanen Mahaifina ina riƙa masa aikin jima da yake yi”
“Haba Asim shi kenan sai ka gudu ka bar ni kana ganin kamin adalci kenan?”
“Namra idan kika aure wani ba niba, mutane zasu min dariya, ban san da wane ido zan ɗaga kai na kalli mutane ba”
“Matuƙar kace zaka biye ma dariyar mutane ba zaka iya aikata komai ba Asim. Nima dana biye dariyar mutane da ban yarda na aure ka ba, yanzu ka watsar da karatun ka, abunda nake da yaƙinin shine zai taimaki rayuwarka”
“Ba karatu ne a gaba ba yanzu, faɗa min da gaske mahaifinki ya yarda muyi aure?”
“Ya yarda shiyasa yace na nemo ka, kuma ina jin ba zai sa mana date da nisa ba”
“Al-hamdulillah Allah mun gode maka, amman Namra kina ganin zaki iya zama da ni?”
“Ba zan iya zama da kai ba na amince zan aure ka? Ya kake wannan maganar kamar ba Namra ce a gaban ka ba?”
“Ina ganin kamar yanayi na da naki ba ɗaya bane”
“Ba mu da banbanci ai duk mutane ne. Asim Amira ta ɓata”
“Haka naji kuma ni ake zargi da sace ta ko? Kamar yadda aka zarge ni da sace ki”
Ta share hawayenta.
“Waya faɗa maka?”
“Ai abun duniya baya ɓoyuwa Namra, kuma kin san akwai munafukai da yawa a duniyar nan. Shiyasa na yanke shawarar barin garin gaba ɗaya, ko da mun yi aure a Katsina zamu zauna tun da ban da gurin aje ki a nan, amman can family house ne akwai ɗakuna da yawa, sai dai na ƙasa ne”
“Amman Asim kana ganin zaman mu a can zai yiyu? Karatun ka fa?”
“Na riga na yafe karatu Namra. Kuma zaman mua can zai fi, saboda har ga Allah nan bana da gurin aje ki, kuma kin ga nan idan mun ci za'a gani, idan ba mu ci ba ma za'a gani, kuma abu kaɗan za a zo gidan ku a faɗa, can kuma babu wanda ya san ki, kuma kin ga ɗan zuwan nan da nayi, ina kama masa aikin jima nima ina samun nawa, kin ga ko dashi zamu iya cin abinci kamin Allah yayi mana wata hanyar”
“Amman Asim shi yace zai baka gida a can? Ni dai zan fi jindaɗi mu zauna nan”
A take ya canja fuska.
“Ko be yarda ba ni zan roƙe shi ya bamu gurin zama, kuma ni a tunani na Namra ko a ciki wuta nace ki zauna zaki iya zama in har kina so na”
“Ina son ka Asim, kuma zan zauna a duk inda ka aje ni, yanzu kaje ka samu magabatan ka suzo su ga Abba”
Murmushi yayi ya sauke ajiyar zuciya.
“Zan yi haka Inshallahu, na gode sosai”
Ba suyi wata doguwar hira ba suka yi sallama, ko lemun da ta kawo masa be sha ba.
Cikin rashin jindaɗi ta nufi shiga falo, har ta nufi kitchen ta aje lemu na ɗauke da kalaman da Asim yayi mata. Idan tace ba zata iya zama a can ba zai zargeta, sai dai har ga Allah bata jin zamanta acan ɗin zai fi.
Bata yarda ta labarta ma Anty Amarya komai ba, sai kawai ta shige ɗakinta tana shawarta zucuciyarta, da nema musu mafita.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa17.html
🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺
Wattpad @
KHADEEJA CANDY
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
Wannan shafin sadaukarwa ce ga SANAH S MATAZU. Namra da Kalsoom sun ce a gaishe ki😘
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 17*
KALSOOM POV.
Sun ɗauki dogon lokaci kamin su fito. Ko da suka fito har Kalsoom tayi nisa da cin abincinta.
“Sorry mun bar ki kina cin abinci ke kaɗai”
Rashida ta faɗa tana ƙoƙarin zama. Kallonta kawai Kalsoom tayi ta cigaba da cin abincinta. Hilal ya lura da yadda yanayin Kalsoom ya canja hakan yasa ya zauna a kujerar dake daf da ita ya ɗauki abincin ya mai da agurin.
Sosai da sosai hakan ya sosa ran Rashida, for the first time in history jikin mijinta yana gugar jikin wata mace. Wasa da riƙayi da abinci ta kasa ci. Hilal ya lura da yanayinta amman be kulata ba har ya gama cin abinci tare da Rashida. Tashi Rashida tayi zata kwashe kwanukan sai ya riƙe mata hannu.
“Bar su kawai je ki shirya kan ki zan kwashe kayan, nima na iya aikin ai, amman kamin nan zauna zamu yi wata magana”
Ba musu ta koma ta zauna. Sai da yaja dogon numfashi sannan yace
“Rashida Kalsoom ina son ku bani aron hankalinku, Ban auri Kalsoom ba dan na wulaƙanta Rashida, kuma ban auri Kalsoom ba dan bana son Rashida ba, yanzu nauyin ku duk ya hau kai na, dan haka ina fatar zaku taya ni sauke nauyin da Allah ya ɗora min, ba wai ku tada min hankaliba, zan fu kowa jindaɗi idan kuka haɗa kanku.
Zan iya zama abun kwatance idan kuka kwantar min da hankali, ba zan iya gane wace tafi so na ba sai ta sai ta hanyar kwantar min da hankali da kuma kyautatawa. Bana son wani rashin jituwa ya shiga tsakanin ku, kuma ban da ɗauka anyi ance duk wanda take ganin ba ayi mata dai-dai ba zata iya magana”
Kalsoom ce ta fara magana bayan ya kai aya.
“Inshallah zaka same me mai biyayyah, ni ɗai indai gefe na inshallah ba za a taɓa samun matsala ba, kuma ina fatar wasu abubuwan da zanyi a cikin rashin sani Ammyn Rafiq zata tunatar da ni”
“Inshallah ina fatar nima zaki tunatar da ni Allah ya bamu haƙuri zama da juna, sai dai sai kin yi haƙuri dasu Ezzah saboda basa jin magana”
Rashida ta faɗa tana mai jin sassauti a zuciyarta.
“Ba komai Ai yara na kowa ne, yaran ki ai nawa ne”
Hilal ya jidaɗin yadda yaga sun ɗan sake da juna, yasan nan gaba komai ze wuce kishi ne kawai wanda ba a rasa ba.
Bayan sun ɗan yi fira ta tashi ta nufi ɗakinta, Rashida kuma ta nufi ɗakin yaranta, dan ta tashesu.
Shigar da tayi a ɗakin ya bata damar kallon irin dukiyar da mahaifinta ya zuba mata, ta jidaɗi matuƙa sai da ta ƙare ma ɗakin kallo sannan ta ɗaga hannu sama tayi ma Allah godiya. Sannan ta nufi bathroom ɗinta tayi wanka, cikin koriyar atamfa ta shirya ta tsaɓa ado. Sannan ta ɗauki wayarta ta kira Momy da Daddy ta gaishe su.
Guraren biyu da rabi Salma tazo gidan, aiko Kalsoom kamar ta haɗeye ta, sai duk taji kamar ta daɗe bata ganta ba.
Ɗakinta ta kaita ta kawo mata abinci da abun sha. Sai da Salma ta ci ta ƙoshi sannan ta kalli Kalsoom tana dariya tace.
“Komai mai lokaci, yau dai gashi na ci abincin gidan Kalsoom”
Kalsoom tayi dariya. Salma tace
“Ya dai zaman ku babu wani matsala dai ko?”
“Eh toh babu matsala zuwa yanzu, ban sani ba dai ko gaba. Amman a yadda na lura kamar yana son matarsa da yawa”
Salma ta saki baki.
“Kalsoom kenan ke kin fi son ki auri mijin da zai riƙa wulaƙanta uwargidansa? Irin wannan mijin ai ba mijin aure bane, idan ya gama da ita akan ki zai yo.
Kuma Hilal ai dole ya so matarsa tun da matarsa ta gina masa sonta a zuciyarsa, kema ki gina naki mana, yana son matarsa cikin bata bashi lokacinta bata kula da gidanta a yadda ya dace, me kike tunani idan ke kika masa duk abunda yake so?
Aure ba abun wasa bane Kalsoom sai kin kai zuciyarki nesa, babu ruwanki da sashenta indai ba har ta kama bane, wani abu da gangan zata yi dan ki gani amman ki riƙa kauda idonki dan samawa kanki masalaha.
Ban da nuna masa ke maki son matarsa, wallahi komai take miki karki nuna masa baki son matarsa balle kuma ƴaƴansa, sai dai idan tayi miki wani abun na laifi ki nuna ɓace ranki ki yi magana dan ƙwatar yancin ki. Karki kuskura zagin matarsa gaban idonsa, kina ida kina haka ko da ita ta nuna masa bata son ki ita zai riƙe da abun a zuciya ba ke ba
Kuma ki kama ƴaƴansa ki riƙe kamar naki, babu ruwanki da ƴan anyi ance, ban da ɗaukar zancen maƙota, ban da biye son zuciya, duk wani kishi da zaki ji ki danneshi ki sawa ran ki sassauci, ban da faɗin sirrin miji, musamman na al'amarin auratayya. A duk lokacin daya buƙace ke ki nuna masa kin fisa buƙatarsa, ki sake jikinki ki yiwa mijinki duk abunda yake so. Ke ai baki da matsala da wannan matar tun da bata da lokacin kanta ma, yara kuma kullum suna islamiya da boko kin ga ai gidan ma kusan naki ne ke ɗaya
Ƴan uwansa ki kama ki riƙe ki maida su kamar naki, ki girmama mahaifansa, ki girmama abokansa, ki tarbi kowa da far'ah idan kina da abun basu ki basu, ki zama mai yawan alheri, gidan ki ya kasance mai ƙamshi da tsafta, abincin ki ko yaushe a ready.
Kin ga waɗannan abubuwan da na faɗa miki? Sune mallaka na musamman wanda mu mata basu san da ita ba, idan kina wannan wata mace ba zata iya gane kan mijinki ba, sai dai kiji ana ta mallake shi ai baya da magana sai nata”
Kalsoom tayi dariya tana mamakin yadda Salma take jero mata waɗannan bayanan kamar wata tsohuwar mace.
“Salma.yaushe kika ɗauki wannan karatun?”
“To ai ke sabuwace mu kuwa mun tsufa a lamarin, ke bari na baki wani sirrin, idan zaki bawa mijinki abinci ki laɓe a inda ba zai ganki ba ki riƙa karanta masa Bismillah kafa shirin da tara ko sha tara, ki tofa masa a ruwa ko wani abu kamar alawa haka ko dabino, a lemu ma zaki iya amman idan kin ƙanƙare, sannan ki karanta masa Hal'ata alal insanu har zuwa samin'an basira, sai maimaita sami'an basira sau bakwai ki tofa masa a abinci, ki yawaita lalle idan mijinki mai son lalle ne, ko kuma ki karanta ayatul kursiyo ki tufa masa a ruwa, kuma ko yawaita cin fruits da tsarki da ruwan ɗumi, ki riƙa masa shagwaɓa dan zama suna son shagwaɓa sosai, hmmm ƙawata sauran soyayyar ki nemeta gurin Allah kawai, amman sai kin ba labari”
Taɓawa sukayi, Salma ta ɗora
“Ai shiyasa bana da shakku akan mijina, nasan ko aure yayi ba dai wata ta ɗauke masa hankaƙi ba, sai dai ma ta rasa gane kansa”
Salma ta daɗe tana yi ma Kalsoom lacca har aka kira la'asar, bayan tayi sallah suka je tare a ɗakin Rashida Kalsoom ta gabatar mata da Salma sannan ta fito, har gurin gate Kalsoom ta raka ta.
NAMRA POV.
Washe garin ranar da sukayi maganar da Namra, Asim ya sanar mata a wayar Maryam cewa iyayensa zasu zo ganin Abbah ya saka musu rana. Ita kuma sai ta faɗawa Anty Amarya tayi masa magana, ya saka musu ranar lahadi.
Ranar lahadin na zuwa suka zo, Abbah yayi musu tarba daidai gwargwado, sai dai basu ga annurin fuskarsa ba ko kaɗan.
Dubu Hansi yayi musu sadakinta, yasa musu date 23 ga wata mai biwa wanda zai shigo, su kuma suka tafi akan sai sun yi shawara.
A Ranar Namra kuka tayi kamar zata mutu, sai dai bata yarda ta faɗa ma Anty Amarya ba, balle Maryam, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin ƙawarta Amira.
Sai da dare Asim ya kirata a wayar Maryam, a lokacin tana zaune falo sai ta tashi ta shige ɗakinta, sannan ta amsa wayar.
“Assalamu alaikum”
“Asim ya kake?”
“Lafiya ƙalau Dear, yau dai kin ga kamar mafarki an yanka min sadakin ki”
“Daman inda haƙuri ai komai mai faruwa ne”
“Haka ne Allah ya bani ikon biya”
“Ameen, amman Asim nace kana ganin zaman a can zai yiyu ko dai haya zamu kama”
“Haya kuma? Haba Namra ina naga kuɗin kama haya a yanzu, ni da nake tunanin sadakin ki da lefe kuma?”
“Ni zan biya kuɗin hayar, kuma zan taimaka maka da kuɗin da zaka haɗa lefe, amman Asim bana son kabar karatun ka”
Wani irin ajiyar zuciya ya sauke.
“Amman gaskiya Namra ba zan bari kiyi gaka ba, ni ban aure dan kiyi min haka ba”
“Ban maka hakan dan wani abun ba, sai dan nema maka mutunci da girma”
“Zan yi tunani a kai, amman gaskiya wannan shawarar bata yi ba”
“Kayi tunani Asim, matuƙat Abbah yaga inda zaka aje ni ba zai bari na aure ka ba”
“Allah yayi mana mafita”
“Amin”
Daga haka suka yi sallama. Sai ta tashi ta nufi falo dan mayarwa da Maryam wayarta. A lokacin ne Anty Amarya tace mata
“Namra wai ya maganar karatun ki? Kin san kwanan ki nawa baki je makaranta ba kuwa?”
Tsaye tayi cak kamar hoto tana kallon fuskar Anty Amarya.
A waje Asim yayi waya da Namra, ya daɗe a gurin zaune yana nazari sannan ya tashi ya shiga cikin gida. Aiko Mahaifiyarsa kamar jira take ta hau shi da masifa.
“Ai sai kaje ka samu kuɗin biyan sadakin kuma, dan babu wanda zai taimaka maka da komai, tun da kai kacw kaji ka gani”
Zaunawa yayi saman tabarma cike da damuwa.
“Haba Mama ai maimakon ki ƙarfafan gwuiwa sai kuma ki riƙa min faɗa?”
“Na ƙarfafa maka gwuiwa kaje ka aure wannan yarinyar? Ai ba da ni ba Wallahi, yarinya data gudu ta bi wani saurayi yayi mata abunda zai yi, mijin da zai aureta ma cewa yayi ya fasa sai aka ɗauko aka ƙaƙaba maka, kai kuma da kake sakare kace kaji ka gani, gudun jin kunyar mutane ko? Waya sani ma ko wani abun aka ganta da shi”
“Subhanallahi irin wannan kalaman sam basu kamata ba Mama”
Tsaki tayi ta tashi ta shige ɗakinta, tana cigaba da nanata maganar.
🌺🌺🌺 *ZAGON ƘASA* 🌺🌺🌺
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
I dedicated this chapter to.
Angel
M Mimi
Mum Khady
Sarwee
Khady U Dome
Husaina daughter.
And all members of ZAGON K'ASA FAN'S grp. And KHADEEJA CANDY NOVELS 💖
I changed my phone so if your massage are still pending please PC me now.
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 18*
Kalsoom na fita tare da Salma, Rashida taja tsaki.
“Aifa an auro min iyani, ina ruwana da wata ƙawarki can”
Wayarta ta jawo ta danna ta nemu number Asmee ta danna mata kira.
“Ke ƴar gari ya akayi?”
“Toh gani nan dai, kin san yau ba'a zuwa aiki”
“Haka ne nima ina gida ai. Ina Amaryarki ance jiya an kawo miki amarya?”
“Tana nan yanzu ta fita raƙa ƙawarta”
“Hmm wai kisan yarinyar nan da taurin kai, babu irin zugar da da ban mata ba amman Wallahi ta tsaya kai da fata ita sai ta aure shi”
“Ai dole ta aure shi mana, babu mace da zata ga Hilal bata so shi ba balle har shi da kan sa yace yana son ta, kuma ance fa kwantai tayi babu mijin aure ba dole ta laƙe masa ba”
“Aiko dai ce ni na faɗa miki gurin aikin mu ɗaya da ita Wallahi, ƙanenta duk sun yi aure ita tana nan, Allah ya agaje ki dai kar tace zata fitar dake a gidan”
“Idan kuma bata fitar da ni ba ta karɓe min gida ba, dan naga yana ta wani rawar kai akanta”
“Ke ma ai kin sani duk mace data daɗe bata yi aure ba idan zata shiga a gidan ai sai ta shirya, kuma irin su ne suke ƙwace maza su tiyar da matar gida”
“Shiyasa fa nake tsoron auren nan na zamani”
“To ai laifin ki ne Rashida, shi kenan dan kana aiki sai miji yaje ya ɗauko maka wata banza da hujjar wai baka bashi lokacin ka! Ai wannan zancen banza ne, ni ɓa gani ina aikin ba amman mijina shiru kake ji ko ƙorafi bayayi”
Rashida tayi dariya tana mire baki
“Asmee kenan ke ai mijin ki be isa yace ze ƙara aure ba, wanda ko kallo mata ba yayi. Ke nima fa da nake matar abokinsa, sai da wani ƙwaƙƙwaran dalili yake min magana balle kuma har ya shiga office ɗina”
Asmee tayi dariyar jindaɗi, daman haka take son ji, kuma Rashida ta kan yawaita faɗa mata mijinta babu ruwanshi da mata, kasancewar gurin su ɗaya da Rashida.
“Kema ai idan kin tashi sai ki zo aka kama miki kan shi, wallahi ba dai wata ta gane kan gidan ki ba, dan kin san ba'a shedun Namiji anjima kaɗan zai canja miki, ballantana kin ga wannan Uwar tasa ba son ki take ba”
“Toh yanzu ya zamu yi kin san ai ba nida lokacin zama ma balle na fita”
“Ba ki da matsala da wannan, indai kin yarda kuɗin ki kawai zaki bada, ba sai kinje ba”
“Haka zai yi, amman ta san muna abota dake ?”
“Bata sani ba ai ban taɓa nuna mata ba, ce mata nayi mijinta ne abokin mijina kuma ni maƙociyarki ce, na nuna mata sam bana ma shiri dake”
“Hakan yayi kyau sai kiyi ta bugun cikinta”
Ƙyaƙyalewa Asmee tayi da dariya. Rashida tace
“Kin ga suna min warning wai kuɗina ya ƙare, ki shigo gobe ganin amaryar mu daman gobe monday bana gida”
“Toh Allah ya kai mu, na gode sai anjima”
Tana kashe wayar ta tashi ta nufi kitchen daɓ ɗora girkin rana.
DOC. HILAL POV
Tun da ya fita be dawo ba sai dare, da ledodi ya shigo gidan, sai da ya fara biyawa part ɗin Rashida ya kai mata nata, sannan ya shiga ɗakin Kalsoom. A bakin ƙofa ya tsaya ya ware mata hannyensa yana murmushi.
“Taso ki tarbe ni mana”
“Ka ƙaraso dai kawai tun da ka riga ka shigo”
Ta ƙarasa da murmushi tana mai sauke idonta daga gareshi. Ba dan yaso ba ya ƙarasa kusa da ita ya zauna, ya aje ledar gefe ya jata jikinsa ya rumgume yana shinshinar ƙamshin turarenta yana wani lumshe ido.
“Wannan ƙamshin na nawa ne?”
Hannunsa ya saka mata a riga, unƙurin tashi tayi sai yayi saurin walƙatowa ya danne ta, a kunne ya raɗa mata.
“Kin fa san daren yau nawa ne, jiya ma dan nasan kin gaji ne shiyasa na ƙyale ki”
Dariya tayi, cikin dabara ta zame jikinta daga nashi ta tashi tana faɗin.
“Bari na haɗa maka ruwan wanka”
Kai kawai ya ɗaga mata ya bi bayanta da kallo a zuciyarsa yana ayyana lalai yau sai ya shiga gonarsa.
Fita tayi daga ɗakinta ta shiga ɗakinsa ta haɗa masa ruwan wanka, sannan ta fito ta dawo ɗakinta ta same shi still yadda ta bar shi.
“Ga ruwan can na haɗa maka”
Kwantawa yayi saman gadon, yana wani nuna jikinsa ya mutu.
“Ni da zaki taimaka min ki ɗauke ni ki kai ni bathroom ɗin kiyi min wanka da na gode Wallahi”
Dariya ta suɓuce mata, sai tayi ƙoƙarin rufe bakinta.
“Na ɗauke ka kuma?”
“Yes wannan ɗan jikin da kike gani ba wani nauyi da ni ba, kina ɗagawa zaki ji nayi sama suuuu”
Kai ta girgiza still tana murmushi.
“Baka tashi wanka ba, bari na ɗauko maka abinci”
“Wait...”
Sai ta tsaya, har ya taso ya ƙaraso kusa da ita ta yadda zasu iya shaƙar numfashin junansu, ya kama hannayenta, yana kallon tsakiyar idonta yace
“Kalsoom I love you with all my heart, ina fatar auren ki ya zame min alheri kuma farinciki”
“Inshallah”
Ta faɗa tana kawar da fuskarta daga kiss ɗin da yake ƙoƙarin aika mata.
Hancinsa ya goga saman nata yana murmushi mai sauti.
“Wannan kunyar ta ki tana burge ni My Queen, shi yake nuna min lallai ke mace ce”
Ya tsunsa yasa cikin nata, sai ta zame jikinta tana dariya.
“Ruwanka yana hucewa”
Cikin sauri ya janyota, ya walƙato da ita cikinsa, ya riƙe ƙugunta kanshi saman wuyanta, ya tura ta.
“Aya muje ki taya ni”
Ƙofar ɗakinta ta riƙe suka riƙa ja-in-ja, shi yana son ta bishi ɗakinshi, ita kuma tana jin kunya, taya zata iya taya shi wanka, daga kawo ta jiya-jiya. Ganin ta kafe masa yasa yace
“Kema kije kiyi wanka yanzu, or else na taya ki idan na fito”
“Nayi wanka fa tun ɗazu”
“Wannan be min ba, a sake wani”
Kai ta ɗaga masa. Sannan ya saketa ya nufi ɗakinsa.
Wanka yayi ya feshe jikinsa da turare ya saka kayan bachi, sannan ya fito falo ya kashe kayan kallo ya nufi ɗakinta.
Zaune ya tararda ita tana cin naman daya shigo da shigo dashi.
“Kai....!”
Ba shiri ta zabura tana masa kallon tsoro. Ya ƙarasa shiga ɗakin.
“Waya ce ki min nama?”
“Ba ni na siyo ma ba?”
“Dana kawo na aje cewa nayi gashi na siyo miki? Aiko dai yau sai kin biya ni”
Dariya tayi ta ƙara ɗaukar wata ciɓyar kazar ta kai baki.
“Anƙi a biya ka ɗin sai kace wani yaro”
Kusa da ita ya zauna ya buɗe mata bakinshi.
“Toh ɗan sammin na ci, amman fa sai kin biya ni gaskiya”
Ledar kazar ta tura masa, sai ya girgiza mata kai
“Na bakin ki zaki ba ni”
Sai tayi saurin haɗewa tana zare ido. Fuskar shanu yayi ya riƙa kunnenta ya murɗa har sai da tayi ƴar ƙara
“Oh ouch that hurt”
“To dan nace ki sammin shine zaki cinye?”
“Ɗauko min abinci ne na ci, ba zan ma ci kazar ba”
Bayan sun gama cin abincin, sukayi shirin kwanciya, sai ya rigata hawa saman gadon ya kwanta yana kallon yadda take ƙoƙarin canja kayan jikinta zuwa na bachi. Ita kuma duk ta tsargu ganin yadda ya sakar mata, tasan jira yake tayi kuskuren saki wani ɓangare na jikinta ta kallah, hakan yasa ta nufi bathroom, sai kawai ta ji an riƙe ta.
“Wallahi ba zaki je bathroom saboda canja kaya ba, ni dodon ki ne hala?”
“To ka sakar min ido kana ta kallo na”
“An kalle ki, ke ya kika yi kika ga ina kallon ki?”
Ta ɓata rai kamar zata masa kuka
“Haba Doc”
“Haba Mrs Doc”
Zata ƙara magana, ya saka mata yatsunsa biyu na dama cikin baki immediately ya soma wasa da halshenta, ɗayan hannunsa kuma a jikinta yana murza fatarta. Ba yadda ta iya daman tasan ƙarshen wasan kenan, a dole ta lumshe ido yana karɓar saƙwannin da yake aika mata.
Da haka yayi nasarar kwantar da ita saman gado, ya ƙarasa cire mata kayan, sai ga komai nata bayyane, wani irin ajiyar zuciya ya sauke tare da haɗe yawun, ya shiga aikama mata da saƙwannin cikin salo na musamman. A take jikinta ya mutu sai dai duk abunda yake mata jikinta rawa yake abun ka da wace bata saba ba, daker ta iya buɗe idonta karaf ta sauke su cikin nasa, yadda taga launin idonsa ya riƙiɗe yasa gabanta faɗuwa, gashi kuma ta ganshi a yanayin da take ganin be kamata ta kalle shi a haka ba, sai tayi saurin maida idon nata ta kulle gam.
Hakan ya bashi damar riƙe kanta yana karanto addu'ar da Annabi ya koyar da mu kamin sexual intercourse.
“بِسْمِاللَّهِ، اللَّهُمَّ جَنِّبْنَا الشَّيْطَانَ، وَجَنِّبِ الشَّيْطَانَ مَا رَزَقْـتَنَا“
Bismillaah. Allaahumma jannibnash-Shaytaana, wa jannibish-Shaytaana maa razaqtanaa”
*** *** ***
Tun da asuba ya tashi ya haɗa ruwan wanka yayi sannan ya tashe ta, duk yadda yaso ya taimaka mata tayi wanka ƙin yarda tayi a dole ya ƙyaleta tayi da kanta sai zolayarta yake, wai jiya duk ta hajiyar da shi.
Ita kam kunyarsa ma take ji, ta gasa kanta sosai gurin wanka saboda yadda ƙasanta yake mata zafi da raɗaɗi, a tare suka yi sallah. Ita kam bata tsaya komai ba suna sallamewa ta hau gado sai bachi.
Bata farka ba sai tara har da tabi, a lokacin Hilal har ya gama haɗa musu breakfast dan yau Rashida da wuri ta fita ko gaisa bata bari suka yi ba, shi ya kai yara makaranta, sannan ya shigo ɗakin ya tashe ta.
NAMRA POV.
Ta daɗe a gurin tsaye tana tunanin abunda zata cewa Anty Amarya, ita kanta tana buƙatar karatun dan tana da yaƙinin zai taimaki rayuwarta, sai dai tana ganin hakan kamar ba me yiyu bane, tun da Asim yana nuna mata alamun baya son ta cigaba da karatun, gashi ma yace ba nan zasu zauna ba.
“Anty naga zan yi aure shiyasa na bar zancen karatu”
Duk kallonta suka yi suna mamakin irin sakarcin da take ƙoƙarin aikatawa.
“Namra kenan, ai karatu baya hana aure kuma aure baya hana karatu, karki yarda ki bar karatun ki”
“Anty yace ba a nan zamu zauna ba, a katsina zamu zauna”
“Katsina kuma?”
Maryam ta amsa, sai ta taso ta dawo kusa da Namta ta zauna.
“Dan Allah, karki yi haka Anty Namra taya zaki bishi zuwa katsina? Kibar karatun ki? Idan shi be san darajar nashi karatun ba ke ya kamata ace kin san naki, yanzu kina son ki zubar da duk shekarun da kikayi ki zubar da su?”
Anty Amarya ta riƙa hannunta.
“Namra karki yi ma kanki zaɓen tumun dare dan Allah, kar kije kiyi abunda zaki yi nadama”
Fashewa tayi da kuka
“Anty idan nace na zan aure shi zai ce naci amanarsa kuma kin ga yanzu har an yanka masa sadaki taya zan ce na fasa? Bayan kuma Abbah ya bani dama, baya da gurin aje ni a nan sai can, ɗan zuwan nan yayi ya samu aiki da zai iya taimakawa kansa da shi”
Anty Amarya ta dafe kanta tana sauke ajiyar zuciya. Zuwa can ta ɗago ta kalli Namra
“Ki masa magana idan ya aminta zan baku gidan da zaku zauna a nan garin, in yaso sai ku cigaba da karatun ku muga abunda Allah ze yi kuma”
Namra ta jidaɗin abunda Anty take ƙoƙarin mata, cikin murna ta share hawayenta tana mata godiya.
“Na gode sosai Anty, zan masa magana anjima inshallah”
“Ba komai Allah ya sanya alheri”
Daga haka Anty Amarya ta tashi ta nufi ɗakinta. Sai da ta shige sannan Namra ta kalli Maryam tace
“Dan Allah Maryam ina son na nemi taimakon ki”
“Na me?”
“Abu nake son ki ara min dan Allah”
“Minene faɗa min mana, kina abu kamar mai jin kunya na”
Sai da ta sosa gefen wuyanta, cikin jin nauyi da kunya tace
“Kuɗi naƙe son ki ara min, zan yi wani abu ne, kuma kuɗin da yake account ɗina be wuce dubu ɗari takwas ba”
“Kamar nawa kike so?”
“Zan samu 1.5 million?”
“Zaki samu kan, ai kin san budurwar Sadiq ba za'a rasa kuɗi a account ɗin ta ba, kullum Sadiq samin kuɗi yake min Wallahi”
Namra ta harareta
“Dan kuma nace ki ara min kuɗi ai ban ce ki min gori ba, muma na mu lokacin yana zuwa ”
Dariya Maryam tayi ta kai ma Namra dudu a baya.
“Dole nayi miki dariya mana, duk manyan garin nan wasu-wasu ne kawai basu nemi aurenki ba, amman kika ƙi kula kowa ke sai Asim, Allah yasa dai ba auren jari zai yi dake ba”
“Dan Allah ki daina zargin Asim mana haba, ni dai kiyi min transfer kuɗin gobe”
Tashi tayi ta bar mata falon cikin jin zafin furucin Maryam.
*** *** ***
Sai da aka kwana biyu sannan Asim ya samu damar zuwa gurin Namra, duk kuwa da damuwarsa da take da waya, sai yace mata wai neman kuɗi yake.
Guraren takwas da rabi na dare ya shigo gidan, bata ɗauki lokaci ba ta fito cikin hijabi. Sai da suka gaisa sannan ta koro masa da bayanin da gidan da Anty Amarya tace zata basu su zauna.
A maimakon ta ga jindaɗi a fuskarsa sai kawai ta ga ya canja fuska kamar ransa be so ba.
“Har yanzu ƴan gidan ku basu yarda dani ba Namra, har yanzu basa son aure na dake, a tunani zaki iya zama a duk inda zan aje ki, kwata-kwata bana da ra'ayin zama garin nan, a can nake da sana'ah”
“Idan mun zauna a nan zamu iya cigaba da karatun mu, kuma a nan ɗin ma ba zaka rasa sana'ar yi ba”
Miƙewa yayi tsaye irin ya fusata ɗin nan sosai.
“Ba zan zauna a nan ba, Katsina nake son zama, idan kuma baki da ra'ayin aure na kawai ki faɗa min”
Ita miƙewa tayi tsaye tana girgiza masa kai
“Abun be kai ga haka ba Asim, magana ce ta fahimtar juna, bana nufin ƙin aurenka ko kaɗan a cikin rai na”
Takardar dake hannunta ta miƙa masa tare da zinarin da Abbah ya bata ranar da aka musu walima.
“Kaje ka cire wannan kuɗin miliyan biyu ne da dubu ɗari uku, nasan ze isa kayi komai, na mai ƙaramin ƙarfi, ba sai kayi lefe mai yawa ba kala ashirin ma ya isa amman kasa me ɗan tsada dan Allah”
Kawar da kai yayi yaƙi karɓar kuɗin.
“Ni bana buƙatar wannan kuɗin Namra”
“Idan baka amsa ba kana da wata mafitar ne? Wallahi ba zan faɗawa kowa kai na ba ba, dan Allah ka karɓa Asim”
Sai da tayi ta masa magajiya har da kukanta sannan ya karɓa. A fuska yake nuna mata baya son karɓa amman a ransa farinciki ne fess shi da be taɓa mallakar dubu ɗari biyar nasa na kansa ba yau gashi ta miƙa masa million biyu har da wani abu.
Bayan sun yi sallama ta samu Anty Amarya a ɗakinta ta faɗa mata yadda suka yi da Asim, akan ƙin amincewar da yayi na zama garin, sai ta nuna mata wai har ƙanen Babansa ya bashi gida a can, kuma sana'ar da yake acan mai ƙarfi ce wai a ƙarƙashin kamfanin Dangote ya samu suka ɗauke shi.
Bayan Allah ya kyauta babu abunda Anty Amarya tace mata, sai ta taso jiki ba ƙwari ta dawo ɗakinta, zuciyarta a cunkushe, tunaninta a kulle, ya rasa abunda yake mata daɗi har wani jiri take jin yana ɗaukarta.
_____________________________________
WHO CAN'T WAIT FOR THE NEXT CHAPTER?
COMMENT LINE BY LINE!
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖💖💖
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa19.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 19*
Baki har kunne Asim ya isa gida da kuɗin, tun daga yanayin sallamarsa Mama ta gani yana cikin farinciki. A ƙuryar ɗaki ya same ta tana zaune saman sallaya ya zauna kusa da ita yana murmushi.
Wani kallo tayi masa ta ɗauke kai, dan ita yanzu wani haushi ma yake bata ji take kamar tayi ta dukansa. Takardar kuɗin dake aljihunsa ya ciro ya aje mata gaban sallaya tare da zinarin da Namra ta bashi.
Ba a ɓoye zinari yake ba, ko yanzu ka tashi daga bachi aka nuna maka shi zaka iya gane shi, musamman irin wannan na Namra da aka siya daga Dubai. Gabanta ya faɗi, sai ta kalli sarƙar ta kalleshi kusan sau huɗu sannan ta ce
“Ina ka samo wannan sarƙar Ibrahim?”
Da dariya ya amsa mata
“Nawa ne”
“Na ka? Sata ka fara ne? Kamar fa zinari nake gani”
“Ba kama bace zinari ne, wannan kuma takardar kuɗi ce na miliyan biyu da dubu ɗari uku”
Ta daki ƙirji ta da ƙarfi.
“Miliyan biyu Ibrahim? Ina ka samo wannan kuɗi?”
Yanayin yadda tayi masa tambayar da ƙarfi, yasa ƙanensa shigowa ɗakin da gudu suna tambayar miya faru.
“Kuɗi na samo mana miliyan biyu da dubu ɗari uku, ga kuma sarƙar zinari”
Ƙanensa ya zauna kusa da shi da mugun mamaki.
“Ya Asim taya ka ɗauko?”
“Ba ɗaukowa nayi ba, Namra ta bani tace nayi hidima da su”
Duk tsalle suka saka suna murnar Yayansu ya samo kuɗi, sai Mama tayi saurin riƙe so
“Dan Allah ku rufa mana asiri, kar aji a dirar mana cikin daren nan”
Sai da suka natsu sannan ta kalli Asim
“Da gaske ita ta baka Ibrahim?”
“Wallahi ita ta bani yanzu nan, sai da ma nayi kamar ba zan karɓa ba, sannan na karɓa kuma tace ba zata faɗawa kowa ba”
Hannu Mama ta ɗaga sama.
“Al-hamdulillah Allah mun gode maka”
Ƙanensa yayi dariya yana faɗin
“Mama ke da baki son ta”
“Ai suma ba dan Allah zasu aura masa ita ba, kai kana ganin masu kuɗi kamar Alhaji Usman zai yarda Ƴarsa tayi aure irin gidan nan idan ba da wani dalilin ba”
Asim ya sauke ajiyar zuciya kana yace
“Wallahi haka kowa ke faɗa, ni kwata-kwata ma ta fitar min a rai, kawai dai zan aure ta saboda na fita kunyar masu ganin kamar ɓa zata iya auren mutun iri na ba”
Mama ta mere baki
“Wallahi ko rantsuwa nayi ba zan yi kaffara ba, da abun nan be faru ba ba zasu taɓa yarda kmsu barta ta aure ka ba, Amman wannan shi ake cewa gobarar ti-ti ko ba komai dole dai a kira ka da surukin Alhaji Usman kuma ko yaƙi ko ya so dole ne ya samo maka wata hanyar, kuma Allah kaɗai yasan ribar da zaka ci akan wannan auren”
“Haka abokaina ke faɗa, wai wata hanyar ce Allah yayi min”
“Sosai tun dai baka ci amanarta ita ta nemi ta ci taka ai dole Allah ya saka maka”
“Yanzu wannan kuɗin tace min aje a haɗa lefe dasu kuma da su zan kama gidan hayan da zamu zauna a katsina”
“Amman Ibrahim zaman ka a nan be fi ba? Karatun ka fa?”
“Can ɗin zai fi Mama, kin ga zan samu sana'ah mai ƙwari, kuma ƴan'uwanta basa zasu sa mana ido a zamantakewar mu ba, idan muna da shi aci idan babu a haƙura, babu wanda yasan mun ci ko ba mu ci ba”
“Haka ne, sana'ah ma yafi, kuma nan kan sai sun sa maka ido har dai wata yarinya na nan marar mutunci kai yarinyar nan bata da kunya kaga yadda ta riga min fitsara sai da ta tara min jama'ah a gida kamar nayi sata! A nan ma saurin kashe auren zasu yi”
“Ai Maryam bata da mutunci ni kaina ina haƙe da ita Wallahi”
Ƙanwarsa ta risino.
“Amman Ya zaka gyara mana gidan nan ko?”
“Gyara gida ai dole ne yanzu kan, bari dai na ciro kuɗin kawai komai ma za'ayi da yardar Allah”
Duk tsalle suka hau yi. Mama na musu dariya zuciyarta ta cike da farinciki.
*** *** ***
Shi da kansa yasa ta faɗawa Abbah cewar ƴan'uwan babansa zasu zo su kawo sadaki da aka yanka tare da lefe.
Sai da Abbah ya sake sa musu rana sannan Anty Amarya ta faɗaata ita kuma ta faɗa masa.
Da daren ranar ne Aisha take faɗawa Anty Amarya irin maganganun da ake tayi a makarantar ta islamiya.
Namra na zaune parlour tana jinsu, har suka yi maganganunsu suka gama bata ce uffan ba, shiru kawai take tana saurarensu ƙwaƙwalwarta na juyawa.
“Amman gaskiya Anty Namra karki bar karatun ki, idan har ba zai iya bari ki ƙare makarantar ba kawai ya haƙura da auren ki, ai ba akanki aka fara cin amanar ba, kuma wallahi duk mai maka son gaskiya dole ne yaso cigaban ka, amman gani nake kamar cin amanarki kawai zai yi”
Maganar Hindatu ce ta ɗago da hankalin Namra har tasa ta kalleta, sai dai bata iya tace musu komai ba ban da ruwan hawaye daya fito daga idonta.
Maryam ta tsire baki
“Ke dai kika sani, tun da baki da ra'ayin kan ki sai na Miji, kuma wallahi kina daf da yin nadama dan duk mace da bata da ra'ayin kanta wahala tana tare da ita, ina tunanin wani abu ne ya ƙire kuma sauran kaɗan ya faɗa miki, ko kuma a ɗaga auren har sai kin ƙarasa karatun ki”
Hannu Namra tasa ta share hawayenta ta tashi jiki ba ƙwari ta nufi ɗakinta tana wata tafiya kamar marar lakka.
Sai a lokacin Anty Amarya ta kalli Maryam tace
“Kar na sake jin kun mata wata magana akan auren nan, kuyi mata fatar alheri kawai, wannan maganganun ba zai haifar mata da komai ba sai baƙinciki, idan kuna mata wannan maganar damuwa zata mata yawa.
Gani nake yi abun kamar zai taɓa ƙwaƙwalwarta, dan Allah karku sake mata magana nan, ita kan ta a yanzu bata iya banbance fari da baƙi, bata daɗe da fita lamarin Uzair yanzu kuma ta faɗo wannan, ko wane ɗan'adam baya wuce ƙaddararsa, no matter how you try baka iya tsallake ƙaddararka,
Kuma ba musan alherin da yake cikin wannan auren ba”
Maryam ta tsire baki.
“Wallahi babu wani alheri a ciki, daga gani ma amanarta zai ci shiyasa yake son yaje can nesa da ita, kuma ya hanata karatun ta tun da shi be san muhimmancin karatun ba”
“Babu alheri a ciki kin san gaibu ne? Idan ma amanarta zai ci ai ita ba yarinya ba ce, idan bata iya karatun duniya ba ai sai duniyar ta karantar da ita, ai kowa ya ƙona rumbunsa, ya san inda toka ke kuɗi”
Daga haka Anty Amarya ta tashi ta nufi ɗakin Namra, zaune ta tararda ita tana aikin kuka. Kusa da ita Anty Amarya ta zauna ta jata jikinta tana rarrashinta.
“Ki riƙa sauraren zuciyarki Namra, Allah yasa wannan auren ya zame miki alheri, kada Allah ya bar ki da kanki Allah ya dafa miki lamarin ki”
Rumgume Anty Amarya Namra tayi sosai tana wani irin kuka mai taɓa zuciya. Anty Amarya bata san lokacin da nata hawayen suka zubo ba.
*** *** ***
Ranar Assabar suka kawo lefen, tarba ta musamman akayi musu, tun daga kan drinks har zuwa abubuwan ciye-ciye, Hajiya Barau ta soya musu kaji da wasu abubuwan. Sai dai wannan karon ba'a tara mutane kamar wacan ba, iya su ƴan gida ne kawai suka tarbi lefen.
Su basu ga wani abun a'zo a gani ba, a lefen tun da abun masu hannu da shuni idan ba an saka tufafin dubu ɗari, ɗari biyu ba su ba ƙimarsa suke gani ba. Sai dai Anty Amarya bata bari sun yi magana a gaban idonta ba, sai dai idan bata nan, a fuska kuma sai tasa suka nuna mata ai yayi ƙoƙari. Ita kanta tasan yaba mata ne kawai suke dan su ƙarfafa mata gwuiwa, amman ba dan sun ga darajar kayan ba.
Tun daga ranar da aka kawo mata lefen Namra tayi sallama da abinci, duk yadda aka tursasata sai tacw bata iya ci, sam bata ma jin sha'awar abincin balle ta ci. Iyakarta abu mai ruwa, ko kuma tea, gashi ta yi baƙi sosai kamar ba farar mace ba, ta rame kamar marar lafiya.
Ita kaɗai tasan abunda yake cin ta a zuciya, tana jin son Asim, wani ɓangaren kuma tana jin kamar ta fasa auren amman babu dama, ta kasa samawa kanta mafita. Haka take wuni a ɗaki kamar wata marainiya, duk wata hidima da ake na zuwa siyen kayan aurenta ba da ita ake yinsa ba.
Da dare Maryam ta samu Namra ɗakinta tana nuna mata pictures ɗin gadaje wato furniture ɗin da za a zuba mata.
“Kin ga wannan miliyan ɗaya da rabi, wannan kuma miliyan ɗaya da ɗari bakwai Abbah yace ki zaɓi wanda kike so”
Kasa zaɓa tayi, ita sam zuciyarta bata mata daɗi.
“Kawai ki zaɓa min wanda duk kika ga yayi miki”
“Amman Anty zaki yi event ko?”
“ Babu abunda zan yi Maryam wanda ya wuce walima”
Kallonta Maryam tayi kamar tace wani abu sai kuma wani tunanin ya zo mata, sai kawai tayi shiru ta shiga nuna mata kujeru.
Sai da suka kai ƙarshe sannan Namra ta riƙa hannunta cikin rashin kuzari tace
“Maryam dan Allah kar ku yi fushi da ni dan na aure Asim, ku yi miki kyakkyawar fahimta dan Allah”
“Babu wanda yake fushi dake, kuma kin yi ma Asim halacci iya halacci Allah yasa kar ya zamo butulu, ya riƙe ki Amana”
“Amin na gode”
Daga haka Maryam ta tashi ta bar mata ɗakin. Ita kuma ta gincira tana sauke ajiyar zuciya.
KALSOOM POV.
Yanzu kam ƙofar farinciki ta buɗe mata dai-dai gwargwado bata da wata matsala a gidan mijinta.
Tun da safe zata tashi ta haɗa yara breakfast, tayi musu shirin makaranta, sannan ta tashi Doc. Sai dai yanzu kusan wata ɗaya kenan, Rashida babu ruwanta da Kalsoom duk kuwa da kasancewar yaranta ne take yima hidima, da ranar girkinta da ba girkin ta ba duk Kalsoom ce take girki, sai dai da dare ne zaka banbance ba ita ke da girki ba, kasancewar kwana biyu-biyu yake musu.
Doc. Hilal kam ji yake kamar ya ɗauki Kalsoom ya haɗeye, saboda yadda take masa komai daki-daki a gidansa, yana jindaɗin yadda take tashi tun da asuba tayi aiki, daman maza basa son raguwar mace. Gashi tana nunawa yaransa so hakan ba ƙaramin daɗi yake masa ba. Sai dai a ɗayan ɓangaren yadda Rashida taƙi ta sake Kalsoom abun na sosa masa rai, dan duk wahalar da zatayi da yaran Rashida ba zata iya ce nata sannu ba, balle na gode, ko kuma ta nuna mata jindaɗinta a kansu.
Yau ma kamar kullum bayan ta gama sallamar yara, sun karya sai ta raka shi bathroom suka yi wanka tare.
Ita ta shafa mishi mai ta murza masa turare, jaka yazo ya zauna ta saka mishi tufafi ko kunya. Har ta ɗora masa hula akai bakinta yake kallon.
“Perfect everything clear”
Ta faɗa tana ƙara gyara masa girarsa. Bakinsa ya miƙa mata.
“Na siye wannan lips ɗin”
“Yau ba za'a sai da maka ba”
Lumshe mata ido yayi, ya langaɓar da kai
“Haba Ma'am... Pity me”
Sai taja kumatunsa.
“No Toy”
Miƙewa tayi tsaye. Ganin da gaske ba zata masa kiss ɗin ba yasa yayi hanzarin fisgota ya jefar saman gado.
“Idan ban samu kiss ba toh zan nemi abunda ya fi kiss ɗin”
Hannu ta ɗaga masa
“Tsaya Wallahi zan baka, amman kiss kawai”
“Naji kiss kawai aya tashi”
Ya faɗa yana nuna mata bakinshi. Kamin ta miƙe tsaye ya buɗe durowa ya ɗauki sweet candy yasa bakinsa. Riƙe ta yayi gam kamar wanda zata tsire masa sai da ta tsosar masa bakin da kyau da kyau sannan ya sake ta bayan ya mayar mata da sweet ɗin cikin bakinta.
Sai ya zaunar da ita.
“It my turn”
Mai ya ɗauka ya fara shafa mata, sannan ya shafa mata hoda, sai janbaki. Sannan ya ɗauki underwears ya saka mata, ya ɗora mata da gown, haka ya mundula mata ɗankwali saman kai sai dariya yake.
Bayan sun gama, ta rako shi har gurin mota, sai da yayi mata side hug sannan ya shiga motar tana masa addu'ah.
“Allah ya haɗa ka da halak komai ƙanƙantar ta, ya nisanta ka da haram komai yawanta”
“Amin I Love You Dude”
“I love you more”
Bayan ya wuce ta dawo falon ta ƙarasa gyarasa. Guraren goma da rabi Rafiq ya tashi, sai tayi masa wanka ta bashi abincin sannan ta ɗauko shi suka dawo falon suka zauna.
Ƙonƙosa ƙofar data ji anyi ne ya ɗago da ita ɗaga kallon MBC2 da take.
“Waye?”
Daga inda take zaune ta tambaya.
“Nice Amarya”
Jin muryar Asmee yasa ta tashi ta buɗe mata ƙofar fuskarta a sake.
“Amarya gida sai ƙamshi yake”
Ta faɗa bayan ta zauna. Kalsoom tayi dariya
“Daman gidan mace a gidan ƙamshi ne, ya aikin ya kwana biyu?”
“Lafiya ƙalau, kina nan kina fama da rainon yara ko?”
Murmushi Kalsoom tayi.
“Asmee ke nan, ai yara na kowa ne, kuma ƴaƴan Hilal ai ƴaƴana”
Asmee ta wani gyara zama tana tsire baki.
“Ke ni dan Allah raba ni da abun haushi, ke kika zama ni nake miki kishi”
“Asmee kenan nikan na so naga kishiyarki”
Kalsoom ta faɗa tana dariya. Da sauri Asmee ta matsa
“A'a Wallahi mugun abin ki ya biki, ke daman Allah be raba bakin ki da tsaɓo ba, bari ma na bar miki gidan daman wani haki ne na siya nace bari na sam miki”
Ta faɗa tana fiddo wani baƙin abu a ƴar ƙaramar roba.
“Kin ganshi ɗan matse ne mai kyau Wallahi, sai kin ban labari, nasan ai kayan amarcin ki sun ƙare yanzu ai”
“Wallahi sun ƙare, duk na kyautar da su ni ba son irin abubuwan nan nake ba, nafi son masu zaƙi ko kuma ƴan fruits haka, kin san suma suna gyara jiki”
“Amman gaskiya kiyi amfani da wannan dan Wallahi yana da kyau sosai”
“To na gode zan gwada”
Bata daɗe ba ta tashi ta fita, har gurin gate Kalsoom ta rakata, sannan ta dawo gida.
Tun kamin Asmee ta isa gida ta buga Rashida tana labarta mata cewar saƙonta ya samu isa yadda ake so. Daga ɗayan ɓangare Rashida tayi murmushi tayi mata godiya sannan suka yi sallama.
Tana aje wayar ta tsire baki. Mutumen dake zaune saman wata huge chair ya kalle a ƙasaice yace
“Wacece?”
“Matar ka ce”
Yayi saurin ɗagowa
“Miya kai ta gidan ki? Bayan baki nan?”
“Ai abokiyar zama na nan, gurinta taje”
Ɗan murmushi yayi
“Mata Allah be raba ku da kicihiba”
Dariya tayi ta ɗauki documents ɗin da suke saman teburinsa, ta nufi ƙofa.
“Ki kai min waɗancan documents ɗin a guesthouse”
Ya faɗa yana kallon mazaunanta dake cikin suit.
“Gaskiya yau ba zan samu shiga ba da wuri zan koma gida”
Daf da zata fice ta amsa masa, sannan ta fice.
___________________________________________
Assalamu alaikum Habibaties💖. To all those that are asking about Amira and Uzair labarinsu zai zo nan gaba, so please wait patiently. And masu cewa kaza ya kamata ayi ba kaza ba, blah blah blah, yen yen yen, this and that, na gode duka amman please ku bar tafiyar nan ta tafi a yadda na tsara ta. Ba ku san dalilin da yasa Yasmeen ta fito a Barrister ba, ba ku san miyasa asiri ya koma kam Amira ba instead of Uzair, so please judge less.
Na gode Sosai Jazakallahu Khairan 🌺
I Love You All Fisabilliah 😘
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa20.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 20*
Ba'ayi wasu events ba, bayan salalle da wanki a Amarya, sai Walima da akayi ranar Jumma'ah. Bikin yayi mutane sosai musamman ta ɓangaren Anty, kasancewar Anty Amarya yanzu ne ta fara aurarwa. Har Ƴaƴan Hajiya Barau da suke nesa sai da suka zo.
Kaɗan daga cikin ƙawayen Namra ne suka samu halartar walimar, kasancewar bata yi gayyatar mutane ba, wasu ma ta hanyar Maryam suka ji.
A babban masallacin Jumma'ah akayi ɗauren aurenta, manyan mutane da dama sun tafi ta dalilin Abbah.
Yadda Asim.yake far'ah da nuna jindaɗinsa kamar ya zuba ruwa ƙasa ya sha. Takeaway na Manyan mutane Abbah yasa aka shirya masa ya rabawa abokansa. Asim kan shimkafa da miya yasa aka shirya masa a gidan wani abokinsa, sai ya tare da Abokansa a can bayana ɗaurin auren sukayi liyafar cin abinci.
Namra na zaune ɗakinta tare da wasu cousins ɗinta, Maryam ta shigo da guɗa.
“Ayyyyyyy Yau an ɗaura auren Namra da Asim”
Wani irin faɗuwa gaban Namra yayi, a maimakon tayi murna sai kawai idonta ya cika da ƙwallah. A take ta soma ganin kamar mafarki take. Farinciki da baƙinciki sai suka taru suka mata tsaye a guri ɗaya.
Yadda ƴan'uwan nata suka riƙa zolayarta yasa ta fito da kukan nata a fili, su kuma suka cigaba da zolayarta. Daker wata Gwaggonta ta lallaɓata ta tashi, tayi wanka lalle ta shirya cikin jar atamfa, mai makeup ta zo ta gyara mata fuskarta.
Sai suka fito da ita harabar gidan inda ake ta kiɗin ƙwarya.
Tsaye tayi a tsakiyar filin riƙe da hannun wata jikar Hajiya, ƴan'uwan Abbah da Hajiya Barau suka riƙa mata ruwan kuɗi suna cashewa, ƴan'uwan Anty Amarya ma sun watsa mata kuɗi sosai. Bata daɗe sosai ba a filin aka dawo da ita dan ta canja wasu kayan, saboda tafiyar da zasu yi, dan tuni motocin da za su ɗauki Amarya zuwa katsina suka iso.
Lokacin da Gwaggwaninta suka fara mata huɗuba akan zamatakewar aure da haƙuri, sai ta riƙa kuka kamar ranta zai fita. Tana faɗuwa tana tashi a aka riƙota aka shiga part ɗin Abbah da ita.
Duk fita suka yi suka barta daga ita sai Abbah, sai Maryam dake riƙe da gefenta itama tana hawayen rabuwa da ƴar'uwarta.
“Maryam tashi ki bamu guri”
Ya faɗa lokacin daya sauke idonsa kar kam Namra dake aikin kuka. Tashi Maryam tayi ta fita. Sai Abbah ya tattara duk kan natsuwarsa ya maida kan Namra.
“Haƙiƙa Khadija ke ƴata ce, kuma ina farinciki da Allah ya gwada min yau na aurar da ke, farinciki ko wane uba ne ya aurarda ƴarsa da ransa kuma ga wanda take so.
Khadija yau igiyar aure ta shiga tsakanin ki da wanda kike so, ina jan kunnenki akan haƙuri zaman aure, duk abunda yayi miki na daɗi ko akasin hakan kiyi haƙuri ki zauna da shi a haka, kar wani tsaɓani ya shiga tsakanin ki da mijinki ki kin tunawa cewa kina da uba! Na ɗaira miki aure da wanda kike so a yau, kuma na sallama masa ke har abada!
Karki kuskura wanke ƙafarki ki zo gidan nan da sunan yaji ko saki. Nayi miki iya abunda ya kamata uba yayi ma ƴarsa na abunda al'ada ta tanada, sai dai kiyi haƙuri ba zan miki gara ba, ba kuma zan ɗora masa kuɗi ba, ke dai yake so kuma ga ki nan na bashi, Allah yayi miki albarka ya baku zama lafiya”
Tun da Abbah yake maganar kan Namra na ƙasa tana wani irin kuka kamar ranta zai fita, duk yadda taso ta tausa muryarta tayi ma Abbah magana sai ta kasa saboda kuka.
Har Abbah ya gaji da sauraren kukanta, ya kira Maryam ta fita da ita. Ko da aka koma da ita part ɗin Anty Amarya numfashinta har rawa yake. Nan ma barinta akayi daga ita sai Anty Amarya. Amman Anty Amarya ta kasa mata magana saboda kukan da take na rabuwa da ƴarta.
Har lokacin da aka bata ya ci ya cinye, Anty Amarya bata iya cewa Namra komai ba, daga ita har Namra suke. Sai da su Mama Zainab da Hajiya Barau suka shigo zasu fita da Namra sannan Anty Amarya ta iya furta
“Na yafe miki Namra Allah yayi miki albarka”
Juyowa Namra tayi ta rumgume Anty Amarya iya ƙarfinta. Har Hajiya Barau da Mama Zainab sai da idonsu ya cika da ƙwallah. Daker suka ɓanɓareta daga jikin Anty Amarya saboda yadda ta rumgumeta.
Yadda Namra take kuka yasa duk wanda yake falon sai da yayi hawaye. Ƙanen Asim da wasu ƴan'uwansa suna tsaye gefe suna kallo.
Muta ɗaya suka shiga da Maryam da Mama Zainab da Hajiya Barau. Ɗayar motar kuma ƴan'uwan Asim suka shiga daman ciki suka zo. Biyun wasu ƴan'uwan Abbah suka shiga, sai ta su Maryam da Aisha da Hindatu da wasu Cousins ɗin su. Ƙarfe uku da ƴan mintuna suka kama hanyar Katsina.
KALSOOM POV.
Yanayin yadda Doc. Hilal ya shiga yau, ya bata tsoro, sai dai bata damu sosai ba, dan tasan haka rayuwa take yau daɗi gobe ba daɗi. Ballantana ma yau ba ɗakinta bane wata ƙila ma uwargidan tasa ce ta ɓata masa rai.
Sai dai hakan be sa tayi ƙasa a gwuiwa ba, wajen zuwa tayi masa kyakkyawar tarba. Sai ta aje Rafiq a falo ta tashi ta nufi ɗakinsa, tana faɗaɗa murmushinta.
Kwance ta kararda shi saman gado ya lumshe ido yana, hannunsa ɗaya dafe da kansa.
Kusa da shi ta zauna, ta kai hannunta ta shafi gefen fuskarsa.
“Ya Omri lafiya kake kuwa?”
Shiru be amsa ta kamar ba zai yi murmushi ba, can kuma ya buɗe ido ya kalleta, sam baya jindaɗin ransa, amman a haka yayi ƙarfin hali ya ƙirƙiro murmushi ya kai hannu ya shafa bayanta.
“Matar Doc. Yau jina nake sai a hankali Wallahi?”
Duk sai taji babu daɗi, daman tasan ba banza tun da taga ya shigo babu ko sallama, kuma be kulata ba ya shigo ɗakinsa.
“Wani abun ne yake maka ciwo?”
“No”
Ya sake lumshe ido.
“Kawai bana jindaɗin rai nane, shiyasa na baro office ɗin”
“Ko wani ne ya ɓata maka rai?”
Idonshi a lumshe ya girgiza mata kai.
“No haka kawai Wallahi”
“Toh Allah ya sauwaƙe ammn idan irin hakan ya same ka, ka riƙa karanta Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, zaka ji sassauci”
Tashi yayi zaune, ya sakar mata ido kamar yau ya fara ganinta, sai kuma yaja ta jikinsa ya rumgume gam-gam, yana maida numfashi.
________________________________________
Yan Katsina ga Amanar Namra nan mun kawo muku 😢
Anya Hilal lafiya yake kuwa?🤔
#Comment
#Share
#Blogger
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa21.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 21*
Ana kiran Sallah magariba suka isa Katsina. Kai tsaye suka wuce unguwar Nasarawa. Sun yi mamakin ganin gidan da aka sauke su da sunan gidan da Namra zata zauna.
Ba dan komai ba sai dan sanin Asim ɗin ba shida halin da zai iya kama hayar irin wannan gidan balle kuma har ya siye. Daman tun lokacin da aka zo jere an labartawa Hajiya Barau irin tsarin gidan. Gida ne plate mai kyau da shike-shike, ga farin fentin daya ƙawata gidan. A can ciki an ware dinning area da kitchen a gefe sai two bedrooms da babban falo, ga manyan kujerun da Abbah yasa aka zuba mata kamar ƴar wani shugaban ƙasa, duk bedrooms ɗin an saka mata furniture masu kyau da tsada.
A ƙaramin ɗaki ta tare ita da ƙannenta, su Hajiya kuma suka fito falo sukayi sallah, bayan sun gama direba ya kawo musu takeaway data aika a siyo musu, sai da suka ci abinci suka ƙoshi sannan Hajiya Barau ta shiga ɗakin da Namra take tana mata sallama, wai zata je gidan wata ƴar'uwarta ita da sauran waɗanda suka zo tare, su Maryam kuma sai idan Ango ya shigo sannan za su je.
Ko da Hajiya Barau ta bar gidan ana kiran sallah I'sha'i. Sai a lokacin Namra ta tashi ta shirya cikin wasu tufafin duk da kasancewar fuskarta a kumbure, ta koma babban ɗakin. Tara da rabi ango ya shigo tare da abokansa, ba a wani yi siyen baki ba, bayan addu'ah da fatan alheri da suka musu. Maryam dai sai ta watsawa abokan nasa wani mugun kallo take, tana Allah-Allah wani yace yana son ta cikin su tayi masa wankin babban bargo.
Tare suka fita da abokan angon, ɗayan yana ƙoƙarin magana da Hindatu dan itace mai ɗan dama a cikin su, sai wata cousin ɗin su Sameera. Lokacin da Namra taji ɗakin yayi tsit sai sabon kuka ya dawo mata, sai dai wannan karon hawaye ne kawai ba kamar na ɗazu ba.
Bayan ya rufe ƙofar gidan ya shigo ya rufe ƙofar falo, sannan ya nufi ɗakin da take da Sallama, bata iya amsa masa ba saboda kukan daya cika zuciyarta, sai shaƙar majina take tana haɗeye yawu da jimmar dannen kuka daya kasa ɓoyuwa.
Kusa da ita ya zauna, ya yaye mayafinta fuskarsa ɗauke da murmushi.
“Namra kukan me kike kuma? Bayan Allah ya cika mana burin mu”
Ɗagowa tayi ta kalle shi, kamar tace wani abu sai hawaye suka silala daga idonta zuwa kumatun ta.
Shi kansa baya buƙatar da faɗa masa dalilinta na kuka tun da yasan iyayenta basa son sa, gashi ya rabo ta da garin su. Shi kan ta ɓangarensa yau take sallah, tun da ya cika burinsa na aurenta ya fita kunya, ga uban dukiyar da aka zuba masa, ga kuma wanda yake jira a matsayin gara a kawo masa.
Jin kawai ta yi ya rumgume ta yana rarrashinta.
“Na san ban kyauta miki ba, dana nesanta ki da iyayenki, amman ni a nawa tunanin hakan shine zai fi mana, Namra a can abubuwa da dama zasu iya faruwa idan muna tare da iyayenki, amman a nan ba komai zasu ji ba, kuma a nan zamu tabbata ba zaman na ɗan wani lokaci ne kawai idan muka ga abunda Allah yayi sai mu koma can, kiyi haƙuri kinji?”
A yanayin da take bata iya magana, sai kawai ta ɗaga masa kai tana sauke ajiyar zuciya, tasa hannayenta ta rumgumeshi.
Har kusan shaɗaya dare suna zaune a gurin, daker ya lallaɓata ta tashi suka yi sallah nafila, kazar ma shi kaɗai ya ci ita kan lemu kawai ta sha ta hau gado ta kwanta. Washe gari guraren takwas na safe ya fita ya siyo musu kayan haɗa tea, ya shiga kitchen ya dafa ruwan zafi a electric, sannan ya dawo ɗakin ya haɗa ya zuba mata nata ya zuba nasa. Nan ma tea kawai ta sha bata ci birede ba, tsakanin jiya zuwa yau ta rame sosai kamar ba ita ba.
Shi kuma be yi matsa mata akan sai ta ci ba, tun da dai ita ba yarinya bace taya zai yi forced ɗinta akan cin abinci, shi duk ma ta cika sa dan yayi hating kuka for no reason, ita kanta ta san babu abunda ya tsana kamar kuka. Daman zuciyarsa ta faɗa masa, dan a rufa mata asiri ne aka yarda aka aura nasa ita, dan yasan babu dalilin da zai sa Abbah ya yarda ya aureta har ya baro garin da ita ya kuma hanata karatunta haka kawai ba tare da wani abu ba.
Sai dai hakan be dame shi, tun da ko ba komai ya taka first step of success, tun da ya auri ƴar masu hannu da shuni, kuma zama da kutuwar uwa dole, a dole dai Abbah ya kyautata masa tun da ya zama surikinsa.
Tashi yayi ya kwashe kofunan ya kai kitchen, sannan ya dawo kusa da ita ya zauna. Sai ya kai hannu ya shafa bayanta, dan tana daga kwance ne.
“Namra ko kina buƙatar wani abun ne? Naga baki ci komai ba”
Tashi tayi zaune hawaye cike a idonta, ta riƙa hannunsa tasa cikin nata, ta kalli ƙwayar idonsa tace
“Asim ka min alƙawarin ba zaka ci amana ta ba, ka min alƙawarin ba zaka taɓa rabuwa da ni ba, ka min alƙawarin ba zaka wulaƙanta ni ba, ka min alƙawarin zaka zauna da ni a duk halin da muka samu kan mu”
Gabansa ya faɗi sosai, a take ya ɗauke idonsa ɗ
Daga kallon da take nasa, yaja jikinsa ya rumgume.
“Taya kika wannan maganar kamar baki san waye Asim ba? Namra bakin ki ya daina furta irin waɗannan kalaman Asim ne naki har abada”
Sallamar su Hajiya Barau da Maryam ne, yasa shu saurin sakinta ya tashi ya fita yana amsa musu, a falo suka yi karo, sai ya kai har ƙasa yana gaida Hajiya Barau, ba laifi Maryam ma ta ɗan sakar masa fuska sun gaisa kamar daman can shiri suke.
Ko da suka shiga ɗakin Namra na gyara fuskarta da hoda, sai ta juyo ta kalli Maryam da murmushi a fuskarta.
“Hajiya Maryam an samu isowa”
“Toh ba dole ba, Hajiya ta sha kai muzo mu kawo miki abinci muyi sallama dake da wuri zamu koma”
Ta faɗa tana dire kular abinci a gaban Namra. Saman gado Namra ta dawo ta zauna tana ɗan ɓata fuska.
“Yanzu tafiya za kuyi ku bar ni?”
“Ahaf to ba aure kika zo yi ba”
Cewar Sameera tana mata kallon zolaya. Zata ƙara cewa wani abu Hajiya Barau ta shigo bakinta ƙumshe da sallama. Duk haɗa baki sukayi gurin amsa mata, Namra ta saukar da kai tana gaishe ta.
“Lafiya ƙalau, Amarya ya tashin ku?”
“Alhamdulillah, ya gajiya”
“Gajiya ta bi lafiya, muna ta sauri a kawo muku breakfast, sai angon yake ce min ai kun karya”
“Eh da safe ne ya haɗa mana tea”
“Toh ai yayi kyau”
Juyawa tayi ta koma falo, Sameera ta bita tana nuna mata abu a wayarta. Sai ya rage daga ita sai Maryam da Aisha. Maryam ta ciro waya a jakarta sabuwa ta miƙawa Namra.
“Gashi inji Anty tace na baki, akwai layi a ciki”
Da murna Namra ta karɓa
“Wayyo Mamana ta kai na”
Cikin zumuɗi ta buɗe kwalin kwayar iPhone 6+ ce golden color yayi kyau sosai. Rumgume Maryam Namra tayi tana rawa.
Sai kusan azahar sannan su Hindatu da sauran mutanen suka ƙaraso. A lokacin ne Hajiya ta shigo ɗakin tayi ma Namra jan kunne akan zamantaewar aure da haƙuri, nan ma kuka Namra tasa mata, bama kamar lokacin da suka fito za su kama hanya. Tayi kuka sosai kamar ranta zai cire, a take taji kewarsu ta kama ta, sai duk taji kamar ta bisu. Tana tsaye bakin gate tana kallon motarsu har sai da ta daina hangota sannan ta dawo cikin gidan da sabon kuka.
Asim kan be dawo ba sai yamma, ya shigo tare da wasu dangin Babansa da suke Bakori, kallo kan kallo suke sun daga kan gidan zuwa kayan da suke cikin gidan.
Da far'ah Namra ta tarbe su, ta zuba musu abincin da Hajiya ta kawo mata ɗazu, waina ce da miya sai doya da ƙwai, sannan ta kawo musu ruwa. Sai daf da magariba suka tafi, ƴar fitar da Asim yayi ya rakasu ya dawo duk tsoro ya kamata tun da bata saba zama ita kaɗai ba a gida.
Ko da ya dawo tana tsaye bakin ƙofar falon tana jiransa, da murmushi ya riƙa hannunta, ya lago ɗayan hannunsa a ƙogunta suka koma cikin falon. A tare suka zauna saman kujera maƙalle da juna
“Aiko.kina da aiki duk kika sakawa ran ki tsoro dan ke kaɗai zaki riƙa rayuwa a cikin gidan nan ƙara ma tun wuri ki cire tsoro a ranki”
Maganar yake yana kallon ƙirginta, rigar lace ce a jikinta, kuma kalar ɗinkin da aka mata ya bayyana breast ɗinta. Ita kanta ta lura da yadda yanayinsa ya canja, hakan yasa ta tashi ta nufi da jimmar shiga ɗaki. Sai yayi sauri riƙe hannunta.
“Ina zaki je?”
“Ɗa... Ɗaki”
“Okay”
Sai ya tashi tsaye yayi mata side hug suka nufi ɗakin tare, har suka isa ɗakin mazaunanta yake shafawa, tana zaunawa sai ya kwanto mata saman jikin ta yadda breast ɗinta zasu shafi ƙirjinsa, ya kai ɗayan hannunsa yana shafa ta.
Lumshe ido tayi ta buɗe tana murmushi, sai ta haɗe bakinta da nashi, duk yadda tayi ƙoƙarin abandoned na ƙin yarda sauri yarda da shi sai ta kasa, saboda yadda ya kashe mata jiki, ga kuma irin kayan mata data sha tun jiya suke damunta, a take ta shiga mayar masa da martanin irin saƙon da yake aiko mata.
Basu samu kansu ba sai kusan asuba. Basu yi bachi daya kai minti ashiriba aka kira sallah asuba, shi ne ya riga ta tashi ya shiga bathroom yayi wanka tsarki sannan ya zuba wasu ruwan yayi alwala. Sai da ya canja ya saka jallabiya sannan ya tashe ta dan tayi sallah.
Daker ta unƙura ta tashi zaune, har ta samu ta ɗauki zanenta ta ɗaura sannan ta tashi tana wata tafiya kamar wanda aka ɓarewa kafafu ta nufi banɗaki.
Shi dai da kallo ya bita zuciyarsa cike da zarge zarge, sam shi be ga alamun budurci a tare da itaba, jinin da aka ce ana ganin idan anyi sex da virgin shi be gan shi ba, an faɗa musu wasu har kasa tafiya suke amman ita gashi har ta kai kanta banɗaki.
Kuma the way da take mayar masa da kiss da yadda take romance ɗinsa ya nuna ta taɓa sanin wani namiji kamin shi, daman yasan za'a rina, zargin mahaifiyarsa ya zama gaskiya.
A take wani ƙololon baƙinciki ya taso masa, yana ayyana irin cin amanar da Namra tayi masa, zuciyarsa na nuna masa tayi masa zagon ƙasa, shi take son ta yaudara.
Har sukayi sallah suka gama be kalli inda take ba, har sai da ta gama addu'o'inta sannan ta gaishe shi cikin kunya. Duk wani abu da yake ji a zuciyarsa sai ya dannesa ya ƙirƙiro far'ah da murmushi ya yaɓa a fuskarsa.
“Lafiya ƙalau Amarya, ya gajiyar jiya?”
Tayi saurin sauke kanta, tana mai jin kunya, shi kuma ya watsa mata wani kallo ƙasa-ƙasa, zuciyarsa na ayyana masa abubuwa ƙala-ƙala.
Tashi yayi ya je ya siyo musu kayan tea, ita kuma ta hau gadon ta kwanta saboda ta gaji da yawa. Shi ya haɗa musu tea kamar jiya, har yayi ya gama tana bachi abunta.
Bayan ya kawo kayan tea falo wayarsa tayi ringing, ganin number mahaifiyarsa yasa ta fita daga harabar falo gaba ɗaya, ya nufi can bayan kitchen sannan ya ɗaga wayar.
“Mama ina kwana”
“Lafiya ƙalau Ibrahim ya gida?”
“Lafiya ƙalau”
“Kina lafiya dai ko?”
“Lafiya ƙalau muke, ina su Amma?”
“Kowa lafiya ƙalau, nace ba a aiko da komai ba ko?”
“Eh kin san ai yau kwana biyu da auren a ɗan jira tukuna kuma ko zasu aiko a nan gida zasu kawo sai ku aiko mana ko?”
“Eh toh haka ne, kasan dashen da aka shiga ne jiya ta aiko mana”
“A ɗan jira dai Mama na san suna kan hanya”
“Toh Allah ya taimaka, amman dai karka yi wasa da kuɗin nan ana kawo su ka samu wata sana'ah babba ka riƙa”
“Haka zan yi ai, ko abokaina haka suke cewa”
“Toh Allah ya taimaka, ina Namra ɗin take ne?”
“Bachi take”
“Toh idan ta tashi a gaishe ta”
Daga haka suka yi sallama, sai ya dawo falon ya cigaba da haɗa tea, sannan ya shiga ya tashe ta.
Sai da tayi brush shima yayi sannan suka dawo falo suka karya. Bayan sun gama ya kwashe kayan ya kai kitchen, ita kuma ta shiga kiran wayar Anty Amarya suka gaisa.
Kowa dai da ta kira a gida har Hajiya Barau, sannan ta kira Abbah, kira biyu tayi masa be ɗauka ba saboda sabon layi ne, sai a na uku yayi picking, be wani sake sosai ba sama sama suka gaisa, sannan ta kashe wayar.
Duk tsawon lokacin data ɗauka tana gaisawa da ƴan'gidan su Asim na kusa da ita yana lalabenta, tana aje wayar ya shiga saka mata hannu ƙasanta. Sanin abunda yake nufi da ita yasa ta unƙura ta tana tureshi, cikin yanayin damuwa take masa magana tana son ya fahimceta
“Asim, not now please, Wallahi na gaji kuma har yanzu zafi nake ji”
Kallonta kawai yayi ba dan yana da niyar fasa abunda yake yi ba, idonsa sun rikiɗe sun canja sosai, sai wani numfashi yake.
Ita kanta tasan a yanzu ko da wane yare tayi masa magana ba ganewa zai yi ba, a dole ta ƙyaleshi ya riƙa wasa da ɓangare jikinta, kamin ya jata su koma ɗaki.
Har yayi abunda zai yi gama, be ji ya gamsu ba, ita kuma duk ta ƙosa ya fita ma ya bata ɗakin, da ita kaɗai tasan irin azabar da take ji. Daker ta samu ya rabu da ita, ta tashi a wahale tayi wanka dan ta karanta ta gani kuma ta sha ji a wa'azi ana faɗar cewa ba kyau ka kwanta bachi da janaba a jikinka, ko yaya ne ƙara dai kayi wankan. Ta gasa jikinta sosai da sosai sannan ta fito kamar da rarrafe ta dawo bedroom ɗin. Ko tufafi bata tsaya sawa ba ta hau saman gado, sai bachi.
KALSOOM POV.
A cikin ƴan kwanakin nan kwata-kwata ta rasa gane kan mijinta, duk yabi ya birkice mata kamar ba shi ba, abu kaɗan sai ya hauta da faɗa, ko kuma yayi ta haɗe mata fuska yana nuna baya son tana zama kusa da shi. Sai dai a ɗayan ɓangaren ta samu sassauci gurin Rashida yanzu kan zamansu babu laifi tana ɗan sakewa da ita, har ma tayi mata godiya a wani lokacin.
Yau ta kama weekend Rashida bata da aiki, kuma Doc yau a ɗakinta yake. Sai ta tashi tun da asuba ta haɗa musu breakfast, sai ta gama shirya komai sannan yaje ta tasheshi, ta shiga ɗakin Kalsoom ita ta taso ta.
Da gangan Rashida ta ɗauki dinner set mai plantain da kuma mai kifi ta aza gaban kujerar Kalsoom.
Sannan ta shiga haɗa masa tea dan tuni ya iso gurin yana duba chat ɗinsa na whatsapp. Har Kalsoom ta iso gurin ta zauna be kalli inda take ba, gaisuwar da tayi masa ma can ciki ya amsa mata still be kalle shi ba.
Rashida na lure da yanayin Kalsoom da Hilal zuciyarta cike da shauƙi, sai dai a zahiri sai tayi kamar bata gani ba, ta hidimar haɗa masa tea kawai take.
“Maman Rafiq miƙo masa plantain gata nan a gabanki”
Ta faɗa tana dire masa tea ɗin a gabansa. Ba tare da tunanin komai ba Kalsoom ta ɗauki kwanon ta dire masa a gabansa. Ta miƙa masa birede, sai a lokacin ya samu damar aje wayar har ya kalleta, sannan ya miƙa hannu ya karɓa. Yana buɗe kwanon yaga kifi sai yaja wani dogon tsaki ya kalleta.
“Ace ki miƙo min plantai sai ki bani kifi kifi kika san ina ci ne?”
Bata iya cewa komai ba, sai Rashida ce tayi magana.
“Haba Doc toh ai kwanukan biyu ne bata san wannenen a ciki ba”
Kallonta kawai yayi ya tashi a hasale ya nufi ɗakinsa. Daman haka ya koma mata abu kaɗan yasa shi zuciya indai ita ce tayi masa abu. Rashida taja wani dogon numfashi tana kallon Kalsoom da idonta ke ƙasa
“Tashi ki bi mijinki mana, haka halinsa yake sai kin yi haƙuri, nima fama nake da shi”
Murmushi Kalsoom tayi ta nuna mata kamar ba komai.
“Fushi fa yake da ni, dan nace masa ina buƙatar hutu, shine tun ranar yaƙi ya sauƙo”
Ta faɗa tare da tashi ta nufi ɗakin nasa. Hakan da tace ya ɓata ran Rashida kuma ya dagula mata lissafi.
Kwance ta tarrada da shi ya lumshe ido yana dafe da kai.
“Doc...”
Buɗe ido yayi ya kalleta, sai ya tashi zaune ya zaunar da ita.
“Sorry for what i did earlier, i just that... ”
Sai kuma yayi shiru. Hannunsa ta riƙa tasa yatsunta cikin nasa.
“Doc idan akwai abunda nayi maka kayi haƙuri kasan ɗan'adam ajizi ne, amman be kamata ace kullum kana fushi da ni ba, a zamantakewa kullum tattauna ake so da fahimtar juna, idan har wani abun nake maga kamata yayi ka faɗa min zan gyara inshaAllah”
Rumgumota yayi jikinsa.
“Baki min komai ba, kawai ina abu ne a ciki na mai ƙarfi, irin ii can't control myself when I'm angry at you, I'm sorry too”
Lafewa tayi jikinsa kamar wata mussa, sai toshe hanci take, dan warin turarensa yana son sata a mai. Duk yadda tayi ƙoƙarin daurewa sai ta kasa saboda aman daya ci ƙarfinta, da gudu ta tashi ta nufi bathroom ɗinsa. Sai ya rufa mata baya da sauri yana tambayar lafiya.
Amai ta riƙa kwararawa ba ji ga gani kamar zata amaye hanjinta, gashi komai bata ci ba da safen nan. Har tayi aman ta gama yana riƙe da da ita yana shafa bayanta.
Sai da ta gama ya wanke mata bakinta, sannan ya riƙota suka fito yana mata sannu.