Yau kusan two weeks kenan, babu gara babu labarinta. Sosai da sosai hakan ya dami Asim, sai dai ya ɓoye maitarsa, be yarda ya nuna mata komai ba. Ya kan yi ƙoƙarin siyo duk wani abu na buƙata wanda za'aci ko ayi amfani da shi a gidan. Sai dai duk tsawon wannan satin biyu Namra a wahale tayi su dan kullum yana manne da ita, bata da wani dogon hutu indai yana gida.
Bayan sun gama cin abinci ya aje Spoon ɗin hannunsa yana sauke ajiyar zuciya. Kallonsa tayi dan ta lura da yadda yanayinsa ya canja.
“Lafiya dai?”
Ya ɗan kalleta kaɗan ya ɗauke kai yana ɗan murmushi, fuskarsa na nuna alamun damuwa.
“Ba komai”
“Haba Hubby ai ni da kai yanzu mun zama ɗaya, ya kamata ace damuwarka ta zama nawa, babu wani ɓoye-ɓoye”
“Wato bana son nayi maganar ne kiyi mata wani ɗauka, wata ƙila ba zaki fahimce ni ba”
“Idan ban fahimce ka, wa kake tunanin zai fahimce ka? A tunanin ka idan ka ɓoye min damuwarka zan jidaɗi ne?”
Tashi yayi daga ginciren da yake ya gyara zamansa yana tsara kalamanta, ta yadda zasu zaunu a ƙwaƙwalwarta.
“Namra ina gudun ki shiga cikin irin rayuwar ta ne, kin min abubuwa da yawa, zuciyana bata da muradi illah na kyautata miki. A kullum tunani ina zan zam sama mana mafita muyi rayuwar jindaɗi, sai dai gaskiya I'm scared”
Sai yayi shiru be ƙarasa ba yana auna yadda kalamansa zasu kamata.
Ita kuma sai ta tambaya zuciyarta cike da shauƙin kalaman nasa.
“Scared of what?”
“Namra ba ni da wani aiki ko sana'ah mai ƙwari da zan iya riƙe ki da ita, ƴan kuɗi dana ke tunanin zasu ishe ni na kama sana'ah da su na kama hanayar gidan nan 50,0000 per year dan kawai na burge ƴan'uwanki da ke kan ki, nasan ke kika bada kuɗin amman naso nayi saving ɗin su dan mu samu wata madafa, sauran da suka rage min kuma gasu muna cin abinci da su kamin Abbah ya yi mana aike”
Ta ɗan ji babu daɗi da kalmar ta fito daga bakinsa, kusan kullum da tunanin take kwana take tashi, na rashin garar da Abbah yayi mata, a tunaninta hakan da Abbah yayi mata ya mata ne dan ta auri Asim, tun da ba haka yake ma sauran ƴaƴansa ba, ita kam ya kasa sai mata girma.
Can ƙasa-ƙasa ta fara magana, zuciyarta cike da rauni.
“Abbah ba zai aiko mana komai ba, da zai aiko da yanzu ya kawo mana ai, sai dai mu yi tunanin wata mafitar”
Sosai da sosai gabansa ya faɗi, kalamanta sun haddasa masa ciwon kai, har zufa na ƙoƙarin karyo masa. Janta yayi jikinsa ya rumgume.
“Toh Allah yayi mana mafita, ai Abbah ya gama mana komai tun da ya yarda na aure ki, Allah dai ya ƙara masa nisan kwana da ƙyaƙƙyawar rayuwa”
“Ameen”
Ta faɗa tana shafa rigarsa.
“Amman yanzu wace sana'ah kake gani yafi? Nifa da zaka bi shawarana da ka koma makaranta, ka cigaba da karatun ka”
“Bana son karatun nan a yanzu kwata-kwata ya fita rai na, na fi son sana'ar da zata riƙa kawo min ƙuɗi sosai ta yadda zan riƙa kyautatawa matana”
“Wace sana'ah zaka yi?”
“Wai da naso na kama wani shago dake nan Uguru Plaza na zuba atamfa haka da lace da shaddodi na gwada na gani, na ma yi maganar shagon dan akwai wani abokina daya ce babansa yana ba da rancen kuɗi ko nawa kake so kayi sana'ah kuna raba riba, toh shine nake son na masa magana”
Ɗagowa tayi ta kalleshi, damuwa ƙarara a fuskarta.
“Kamar nawa zaka kashe?”
“Zai kai 1.5 million, har kuɗin hayar shagon, indai ana son a saka kaya masu kyau”
“Tau me zai hana na siyar da motana sai na...”
Bata ƙarasa ba yaja wani dogon tsaki, ya tureta daga jikinsa ya tashi ya nufi ɗakin. Da sauri ta rufa masa baya tana karantar yadda ransa ya ɓace nan take.
“Kuɗin ba zasu iya ba ne?”
Ta tambaya lokacin data kunna kai cikin ɗakin. Sai ya juyo kamar a fusace yace
“Ban taɓa sanin baki da wayo da hankali ba Namra sai yau, da badan na sanki ba da sai nace shaye-shaye kike yi, taya zaki ce a siyar da motarki saboda na kama sana'ah? So kike zargin da mutane suke min ya tabbata gaskiya ko? Daman ance na auri ki ne dan dukiyarki, dan Allah dan Annabi ki taimaka wajen shanye raɗa da riƙe amanarki”
Sai yanzu hankalinta ya kwanta, data ji dalilin fushi nasa. Murmushi tayi tasa hannyenta ta laƙamo wuyansa tana kallon hawayen da suka cika masa ido.
“Bana nufi komai sai alheri, kai kan ka yanzu ai abun kunya ne kaje wani guri neman rance bayan ni ina da hanyar samo maka wannan kuɗin. Zai zame kama abun magana ace kana angonka kaje wani guri rancen kuɗin da zaka yi sana'ah, kuma ni Wallahi ba zan faɗawa kowa ba.
Nasan motar zata yi 2.5 ko ma 2 million, kaga idan ka kama sana'ah sauran sai mu siye abinci da sauran kayan gida, ni kai na ina buƙatar ƙuɗi a yanzu”
Kai ya girgiza mata ya cire hannayenta daga wuyansa.
“A'a kima daina wannan maganar dan Allah, kin san ko kuɗin da kika bani na haɗa lefe sai da nayi baƙinciki karɓar su? Nayi nadama sosai da zuciyata ta yaudareni na karɓi kuɗin”
“Amman ai baka da wata mafita Asim, idan ban baka kuɗin ba a ina zaka samo? Wannan ma ai dole ka karɓa”
“Da baki bani ba, da dole zan nemo mafita a duk inda take, ko wane hali zan iya shiga dan na samo kuɗin aurenki”
“Wannan ma ni zan taimaka maka da yardar Allah, kawai ka amince da buƙatata dan Allah, ba ma acan za'a siyar ba, kawai zan yi ma Anty waya nace zaka zo ka karɓa min motana, idan an zo nan sai a siyar Asiri rufe”
Kai ya girgiza mata, irin shi fa sam ba zai karɓa ba, ya nufi ƙofa yana wani huci kamar gaske.
Da kallo ta bishi tana murmushi har ya fice, zuciyarta cike da shauƙin son Asim, tana jin lallai tayi dacen miji.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa22_13.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 23*
NOT EDITED ⚠️
Haka ta cika gidan da ihu sai kuka take duk ta bi ta rikice, zuciyarta na nasaltama Asim ya tafi ya bar. Yarinyar da suke tare ne taje da gudu ta faɗawa Mahaifiyarta, sai gata ta zo da gudu cikin gidan tare da Babbar ƴarta.
Dafa Namra tayi tana girgiza ta.
“Haba ke kuwa sai kace ba musulma ba? Cewa akayi ya mutu ne?”
Cikin kukan Namra ta amsa mata.
“Ban sani ba, sun ce yana asibitin Funtua”
“Yanzu ba kuka ya kamace ki ba, tashi ki wanke fuskarki Mardiya ta raka ki, kuje Asibitin”
Da sauri ta tashi ta shiga ta wanke fuskarta ta ɗauko Hijabinta ta saka, keys ɗin gidan ma sai da Mardiya ta karɓa ta rufe mata gidan, sannan ta koma gida ta shirya sannan ta suka kama hanya Mahaifiyarsu na mata Allah ya tsare.
Keke Napep suka hau ta kai du tasha, sannan suka shiga motar Funtua.
Tun cikin Motar Namra take kuka, har suka isa Funtua, kowa sai tambayar yake lafiya, Mardiya ce kawai take iya amsawa, Namra kan ji take kamar ta yi tsalle ɗaya ta ganta gaban Asim, sam zuciyarta ta kasa aminta da be mutu ba.
Suna isa cikin asibitin suka tambaya, sai a nuna musu emergency ward. Hankali a tashe ta shiga gurin, sai rabon ido take, akwai mutane da yawa a gurin ga kuma ɗakunan bata san wanda zata shiga ba.
Daga gefe ta tsaya ta kira wayar Asim, ringing biyu aka ɗauka.
“Ga mu cikin Asibitin yana ina?”
“Yana ciki suna duba shi, bari na fito yanzu”
Ba a ɗauki dogon lokaci ba, sai gashi ya iso gurin sanye da uniform ɗin road safety. Sai ya miƙa mata wayar hannunsa yana faɗin
“Hajiya ki kwantar da hankalin ki be mutu ba, sai dai ɗan abunda ba za'a rasa ba, ba shi kaɗai yayi haɗarin ba tare da wata babbar mota da kuma ƙananan motaci uku, duk babu wanda be ji ciwo ba, motar ma da yake ciki duk ta ƙone”
Wani sabon kuka ne ya dawo ma Namra.
“Dan Allah da gaske yana da rai?”
“Ko da muka kawo shi nan yana da rai, mutun biyu ne kawai suka rasa rai ciki, amman shi yana da rai”
“Na gode...”
“Ba komai, amman ki kwantar da hankalin ki babu abunda zai faru”
Hawayen idonta ta share, ta fidda wayarta ta saka number Anty Amarya ta kira ta, sai da kiran ya katse bata ɗauka ba, sai ta sake kiranta, sai a uku ta ɗaga.
“Assalamu Alaikum, Namra kin kira ina sallah”
“Anty Asim yayi haɗarin mota yanzu haka muna asibiti”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Da sauki dai ko?”
“Eh sun ce be mutu ba, amman har yanzu likitoci suna kansa”
“Wace Asibitin?”
“Specialist dake Funtua”
“Toh ki kwantar da hankalin ki kin ji? Kin san abunda Allah ya ƙaddara ma bawa baya wuce shi ko? Ki daina kuka ke ma malama ce Namra, ki fawwalawa Allah komai”
“Toh Anty”
“Kin kira mahaifiyarsa?”
“A'a”
“Toh ki kira ta yanzu ki faɗa mata, Allah ya bashi lafiya, gobe zamu zo inshallahu”
“Tau Anty”
Daga haka ta kashe wayar. Ta ɗauki tasa wayar ta kira number Mahaifiyarsa. Ringing ɗaya ta ɗauka tana faɗin.
“Yanzu nake cewa a sawo min kati na kira ka, na ji ko ka isa lafiya”
“Mama ba shi bane Namra ce, yayi haɗari ne a hanyarsa ta dawowa, yanzu haka muna asibitin Funtua”
“Wayyo ni Allah na shiga uku, ya mutu ne? In ya mutu ki faɗa min Namratu”
“Be mutu ba yana da rai”
“Ba shi waya muyi magana”
“Likitoci suna duba shi yanzu, ba zai yiyu ki yi magana da shi ba”
“Kice min kawai ya mutu, wayyo Allah ni Halimatu, na shiga uku na lalace”
Kuka take sosai cikin wayar, Namra na amsa mata da nata kukan. Daga bisani ta kashe wayar, ta risina a gurin tana kuka.
“Haba Namra, ki gode Allah mana da ba mutuwa yayi ba, ki tashi muje muyi Sallah”
Cewar Mardiya tana goge ma Namra hawayenta. Tashi tayi suka nufi wani ɓangare na asibitin suka siye pure water suka yi alwala Mardiya ta shinfiɗa ɗankwalinta tayi Sallah, sannan Namra ta yi.
Ta daɗe tana yi ma Asim addu'ah kamin ta tashi su koma cikin emergency ɗin. Sai kusan goman dare likitoci suka fito da shi tare da wasu mutane maza da mata kusan mutum shida.
Wani ɗakin aka kai shi, irin ɗakin da ake aje majinyata, aka ware masa gado ɗaya, suka saka masa jini. Kusa da shi ta zauna tana kallon fuskarsa. Idonsa a rufe, gefen kansa an saka masa bandeji, an ɗaure ƙafarsa ɗaya, da cinyar hannunsa.
Wani irin tausayinsa take ji, ji take kamar ta cire ciwon ta maida a kanta. Sam bata ji maganar da likitan yake mata ba har sai da Nurse ɗin dake tare da shi ta taɓa ta.
“Kece Matarsa?”
Kai ta ɗaga mata, dan bata jin zata iya magana a yanzu, saboda bakinta kumshe yake da kuka.
“Ki zo likita yana son ganinki”
Tashi tayi tabi bayan Nurse ɗin dan likitan tuni ya tafi duba wasu masara lafiyar.
A kusa da wani marar lafiya likitan yake tsaye yana masa tambayoyi, sai da ya ƙare dashi sannan ya kalle ta ya miƙa mata wata takarda take cikin file ɗin dake hannunsa.
“Ki siyo masa wanɗannan magungunan yanzu, kuma ki siyo masa ɗan ƙaramin wando da riga a saka masa, kin ga yanzu zane kawai aka rufa masa”
Hannu biyu tasa ta karɓa, sai ta koma gurin da Asim yake, Mardiya na zaune a kujerar dake kusa da shi. Namra ta dafa ta.
“Zan je na siyo magani yanzu na dawo”
“Amman kin san guri?”
“Zan tambaya”
“Toh Allah ya tsare”
“Amin”
Haka ta sa kai ta fice ba dan tasan inda zata ba, bata ma jin kuɗin da yake jakarta zai isa ta siye duka maganin. Da tambaya ta isa pharmacy dake cikin asibitin, suka duba magungunan suka ce mata babu irinsu a cikin asibitin sai ta fita waje.
Bata bar gurin ba sai da ya kwatanta mata inda zata samu, can unguwar dake kusa da asibitin. A harabar Asibitin ta hau Napep ta faɗa nasa inda zai kaita. Be direta ko ina ba sai bakin pharmacy ɗin. Sai ta ciro naira ɗari ta miƙa masa. Ta taka da ƙafa ta shiga pharmacy ɗin, sai da aka gama da wasu mutanen sannan ta miƙa musu takarɗar maganin.
Dubawa mutumen yayi ya rubuta kuɗin ko wanne a jikin rubutun.
“Duka dubu shida da dari takwas da naira arba'in”
Gabanta ya faɗi, kwata-kwata kuɗin da yake jakarta be wuce dubu ɗaya da wani abu ba. Wayarta ta ciro ta miƙa masa.
“Dan Allah ka riƙe wayar idan na kawo maka ƙuɗin gobe sai ka bani wayana, mijina ba lafiya kuma bani da kuɗin yanzu, amman nasan gobe Mamana zata zo”
Ba musu ya karɓi wayar, ya miƙawa ɗayan
“Duba mana wannan ba fake ba ce?”
Sai da ya duba gabanta da bayanta, ya ce ta cire mishi password ya duba komai, sannan suka bata maganin.
Tana fitowa cikin pharmacy ɗin, wani ƙaton mutum ya sha gabanta.
“Malama ana magana da ke a can”
Ya nuna mata wata shegiyar Mota mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali. Ɗauke kai tayi kamar bata ji shi ta cigaba da tafiyar tana kallon ti-ti ko zata samu Napep.
Jin tayi ana binta a baya, kuma ba takun mutum ɗaya ba, juyowar da zata yi sai ƙamshin wani daddaɗan turare ya daki hancinta.
Tsayawa tayi cak tana masa kallin jin dalilin binta da yake shi da bodyguards ɗinsa. Shi kuma ya tsaya a gurin yana mata wani kallo mai wuyar fassara.
Mashallah kyakkyawa ajin farko kuma ajin ƙarshen a kyau. Manyan idanuwansa, su suka fi komai kyau a halinta dake fuskarsa, manya ne sosai farin yayi fari, baƙin kuma kamar an shafa masa kwalli, hancinsa ya zauna a tsakiyar fuskarsa kamar anja masa layi, a ƙasan hancin an yanka masa wani hot lip pink color, shape ɗin fuskarsa mai faɗi kamar ƙirginsa. Robe ce a jikinsa mai kyau da ɗaukar hankali.
Ganin be ce mata komai ba, yasa ta juya da nufin cigaba da tafiyarta. Sai kawai yayi kuskuren kai hannunsa ya riƙa hijabinta, da nufin juwo da ita.
Tassssssss. Ta sauke masa lafiyayyen mari a fuska. Da sauri Bodyguards ɗinsa suka zaburo za su kai mata duka, sai yayi saurin ɗaga musu hannu.
“Baka da hankaline da zaka kai hannunka ka taɓa min Hijabi? An faɗa maka kowa wace mace ce ƴar iska? Kasan muhimmancin hijabi da zaka saka wulaƙantacen hannunka ka taɓa min Hijabi? Ni matar aure ce dan haka ka shiga hankalin ka”
Duk balbalin bala'in da take masa, kallonta yake fuskarsa da murmushi, har yanzu sanyin da laushin hannunta yake ji a gefen fuskarsa.
“Nima Mijin aure ne”
Ya faɗa lokacin daya ga tana ƙoƙarin juyawa. Awww Mashallah his voice was soft and sweet, such a nice voice irin ta larabawan nan masu ƙalƙala, wandanda baka gajiya da jin muryar su.
Wani dogon tsaki taja dai-dai lokacin data tsayar da mai Napep ta shiga tayi tafiyarta.
Har cikin ransa yake jin tsakin nata, yana yawo a ƙwaƙwalwarsa kamar wani blood.
“Abdul”
Da sauri wanda ya kira da Abdul ɗin ya matsa kusa dashi yana tsare masa.
“Sir”
“Rubuta Number Mai Napep ɗin can. 771A97K Funtua”
“Yes Sir”
Da sauri ya juya ta nufi gurin da suka yi parking ɗin motocinsu. Shi kam sai da ya daina hango Napep ɗin sannan hankalinsa ya dawo kansa.
‘For the first time in history wata mace ta ɗaga hannu ta mari Abdullah Ahmad Mai-doki’
A zuciyarsa yayi furucin yana mamakin kansa.
“Unique one”
Ya furta a fili. Sannan ya ce su zo da motocin ya shiga suka kama hanya.
Tana isa cikin asibitin ta kai ma likitan maganin yace ta bawa Nurse. Haka suka kwana a kansa ita da Mardiya, ko wanne ya shimfiɗa ɗankwalinsa ya kwanta. Sai dai Mardiya ce kawai tayi bachi Namra kam har safe idonta biyu.
Da safe ita ta bawa Mardiya kuɗi tta siyo abinci a ƙofar asibitin ta karya, ita kam jasa cin komai tayi har likita ya shigo.
Bayan ya gama duba shi ya sake sa masa drip, a cikin drip ɗin yayi masa alluran da aka siyo sannan ya miƙa mata wasu magungunan yace idan ya farka ta bashi.
“Amman likita har yanzu be buɗe ido ba”
“Zai buɗe yana da rai fa, kawai yaji jiki ne, mai yiyu juwa anjima ya buɗe idon, amman inda hali ku kai shi babbar asibitin Katsina dan akwai yiyuwar sai an masa aiki a ƙafarsa, saboda kashinsa na cinya ya shige ciki”
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Ta faɗa tana faɗuwa zaune saman kujerar roba dake gurin.
“Allah ya bashi lafiya”
Wucewa ya yi gurin wasu marar lafiyar ya barta tana aikin kuka. Likitan be yi minti talatin da barin gurin ba, Sai ga Mama ta iso da kukanta. Aiko hankalinta ya tashi sosai da taga yadda fuskar ɗanta ya kumbuɗe kamar an busashi, gaba ɗaya halittarsa ta canja.
Yadda take rusa kuka sai yasa hankalin duk wanda yake gurin ya koma kanta, ƙanwar Asim sai haƙuri take bata tana kuka.
Guraren shaɗaya da rabi Anty Amarya ta iso tare da direban su da Aisha. Namra na ganinta ta fashe ta sabon kuka ta kwantar da kanta jikin Anty Amarya.
Anty Amarya ta danne kukanta, tana lallasar Namra.
“Ki yi haƙuri, Namra ki kwantar da hankalin ki, duk abunda ya kamata ayi masa za'a masa kinji? Idan ma waje ya kamata a fitar da shi za'a fitar, amman ki kwantar da hankalin ki”
Karaf Mama ta tsuma baki, tana mai jin zafin yadda Anty Amarya take lallarsar Namra ita ga ɗanta kwance.
“Ta kwantar da hankali kamar yaya? Ga mijinta kwance ki ce ta kwantar da hankalinta, ta nata ma kike ba ta Ibrahim ba, daman ai nasan ba son ƙwarai kuke masa ba, ni wannan aure bai zo da komai ba sai abun baƙinciki, gashi nan daga shigowarki gidansa ya koma da ƙafa ɗaya”
Da kuka ta ƙarasa maganar. Kallonta kawai Anty Amarya tayi ta ɗauke kai, tana mai jin zafin kalamanta. Bata wani daɗe ba ta tashi ta fito harabar asibitin tare da Namra.
“Allah ya sauwaƙe Namra mu kan za mu koma”
Da sauri Namra ta kalleta
“Yanzu Anty?”
“Eh daman Abbah ki yace min kar na kwana, ƙara mu kama hanya yanzu kin san tafiyar dare bata da kyau, Maryam tace tana gaishe ki”
Nan da nan sai tasa kuka, a zatonta Anty Amarya zata kwana ne. Har suka ƙarasa gurin mota Namra kuka take, daker Anty Amarya ta lallaɓata tayi shiru.
“Anty ba mu da kuɗin biyan Hospital bill, kuma ba ni da ko naira yanzu a hannuna”
Ta faɗa tana ƙara share hawayenta.
“Ai ga mahaifiyarsa can sai ta biya masa”
Anty Amarya ta faɗa tana shirin zama cikin mota. Namra bata ƙara cewa koma, sai idonta dake zubar da ƙwallah.
Sai da Anty Amarya ta rufe motar ta zuƙe gilashin sannan ta ce.
“Zan miki transfer 100k Allah ya bashi lafiya”
“Amin na gode Allah ya kai ku lafiya”
A haka suka yi sallama. Namra ta bi motar tasu da kallo har suka bar asibitin.
____________________________________
Share it please.
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa24.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 24*
NOT EDITED ⚠️
Har Anty Amarya ta koma gida tana jin zafin kalaman da Mama ta yi a gabanta. Sai yanzu take jin zafin rashin mayar mata da magana da bata yi ba.
Bayan Sallah Magariba Hajiya Barau ta shigo ɗakin, tana tambayar Anty Amarya ya mai jikin, a lokacin Maryam da Hindatu har Aisha suna ɗaki suna maganar.
“Jiki da sauki sosai, yaji ciwo a ƙafa da hannu, sai gefen fuska”
“Toh Allah ya ƙara sauki ya tsare gaba, mu kam sai an kwana biyu sannan muje mu ganshi”
“Ai ba komai da sauki ma sosai, ƙaddarori ne kawai idan Allah ya kawo”
“Allah ya sauwaƙe ya ɗauke Wahala”
“Ameen”
Ta tashi ta nufi ƙofa tana faɗin
“Maryam ki zo ki karɓo dambu ɗazu Hajiya Hadiza ta aiko min da shi”
Tashi Aisha ta yi, ta bita suka fita tare. Maryam ta yi ƙwafa tana maimaita maganar ɗazu.
“Amman Wallahi matar nan bata da kirki sam, kuma ta ci sa'ah ba da ni aka je Wallahi da sai nayi mata tasss”
“Hmmm kin san wasu ba su iya yarda da ƙaddara ba, idan abu ya same su sai riƙa ganin kamar wani yayi musu ba Allah ba”
Cewar Anty Amarya, tana gyara zamanta. Hindatu tace
“Ni fa gani nake daman can kamar ba son auren take ba, shiyasa ma ya siye gida can su zauna”
Maryam ta ƙara tsire baki
“Ai mune ma ya dace muce haka ba su ba, dan yanzu na san ita za a bari ɗmda wahala, kuma wannan gidan ba siyen shi yayi ba, sai dai idan haya ya kama, idan ma siye yayi Wallahi Anty Namra ce ta bashi kuɗi, dan ta rance 1.5 million gare ni tace kar na faɗa”
Daga Anty Amarya har Hindatu da Aisha data shigo yanzu kallon Maryam suka yi da mamaki.
“Dan Allah da gaske?”
Hindatu ta amsa da ƙarfi. Maryam ta watsa mata harara
“Haka kawai zan ƙirƙiri ƙarya na faɗa, kuma nasan Wallahi shine ya zuga ta yace ta bashi wai kuma fa ta ƙara masa nata masu yawa, idan ba haka ba taya zai yi wannan lefen har ya samu gidan kai ta”
“Ko Motar nan waya sani ko sai dawa zasu yi ta bashi kuɗin, Wallahi Anty Namra bata da wayo sam”
Cewar Aisha tana ɗire wainar gaban Anty Amarya. Gaba ɗaya yanayin Anty Amarya ya canja, sai ta kawar da fuskarta wani gurin tana ƙoƙarin ɓoye damuwarta, babu abunda take tunani sai lamarin Namra.
NAMRA POV.
Asim be farka ba sai washe garin ranar da la'asar, har lokacin Namra bata sa komai a cikinta ba, dan bata jin yunwa ma a tare da ita.
Daker ya buɗe idonsa kumburarrin idonsa sai kuma ya mayar da sauri ya rufe, saboda zafin da yaji suna masa. Hannunsa ɗaya ta kama, idonta cike da ƙwalla.
“Sannu Asim”
Sai ta tashi da sauri taje ta kira likita. Abun ka da Nigeria sai da likitan ya kusan minti ashiri sannan ya iso tare da abun awonsa.
Sama-sama ya duba sa, ya kira sunan sa kusan sau uku, amman be amsa ba, sai motsa ido yake yana jin abunda yake ji.
Likitan ya kalli Namra yace
“Gaskiya bawan Allah nan yana buƙatar kulawar gaggawa, idan hali zan muku transfer zuwa babbar Asibitin Katsina dan ya samu kyakkyawar kulawa indai kuna buƙatar ransa”
A dai-dai lokacin ne Mama ta iso, sai kawai tasa kuka tana faɗin ta bani ta lalace. Nurse ɗin dake tare da Likitan ta katsa mata tsawa
“Haba Inna muna da wasu majiyanta fa, kukan ki zai iya takura musu”
Namra ta share hawayen idonta tana in'inna tace
“Likita a yi mana”
A take ya karɓi file ɗin dake hannun Nurse ɗin ya fiddo wata doguwar takarda, yayi rubuce-rubuce ya miƙa Nurse ɗin yana faɗin.
“Ki basu takardar biyan hospital bill kuma ki faɗa musu inda zasu je su biya”
Daga haka ya wuce, ya bar Nurse ɗin tana duba adadin abunda aka kashe musu, sai ta ware wata takardar ta daban ta rubuta mata kuɗin ta miƙa mata.
“Idan kin wuce pharmacy zaki ga gurin da ake biya, idan kin biya sai ki zo na baki transfer”
Daga haka ta wuce ta bar Namra da Mama tsaye suna hawaye. Zaunawa Mama tayi a kujerar roba da take gurin. Namra kuma ta fito ita da Mardiya tana duba jakarta.
Kwata-kwata kuɗin da yake ciki be wuce ɗari bakwai ba, saboda abincin data siya ma Mama da Mardiya da kuma ƙanwarsa.
“Amman yanzu kina da kuɗin biya kuwa”
Mardiya ta tambaya tana kallon yadda idon Namra ke zubar da ƙwalla.
“Muje ki raka ni na karɓo waya na”
Shine kawai abunda Namra ta faɗa, taja hannun Mardiya suka nufi gate. Napep suka tare suka shiga, ta sauke su dai-dai bakin pharmacy. Namra ta bashi ɗari biyu sannan suka shiga cikin Pharmacy.
Bata sha wahala gurin su gane ta ba, saboda kayan jiya ne a jikinta. Bayan sun gaisa tace
“Ka gane ni?”
“Eh ba kece ta jiya mai waya ba? Ana ta kiran wayar ta tun jiya”
“Dan Allah wayar zaka bani na kira”
“Tau kin zo da kuɗin ko?”
“A'a waya zan kira naji ko an turo”
“Toh sai dai idan nan a zakiyi kiran”
“Eh a nan zan yi”
Sai da suka yi kamar kar su bata sai kuma ɗayan ya ɗauko ya miƙa mata. Number Anty Amarya ta fara kira, daman ta ga missed call nata a calls list. Ringing biyu Anty Amarya ta ɗauka da sallama.
“Anty ina wuni ya hanya?”
“Alhamdulillah ya jikin Asim ɗin?”
“Ba sauƙi Anty yanzu haka likitan ya tura mu
zuwa babbar asibitin Katsina, kuma ba ni kuɗi”
“Allah ya sauwake, nima kuɗin da nace zan aiko miki ban samu ba, daman ina jiran Abbah ku ya bani kuɗin da nake binsa ne sai na aiko miki”
Wani irin abu Namra ta ji ya daki tsakiyar kanta zuwa cikin ƙafafunta. Ta san da gangan Anty Amarya tayi mata haka ba dan bata da kuɗin ba. Da na gode ta amsa mata ta kashe wayar, tana hawaye.
Number Maryam ta lalabo ta danna mata kira, tana yin pincking sai Namra tasa mata kuka.
“Maryam dan Allah taimako nake nema a gareki”
“Taimakon me?”
“Dan Allah kuɗi nake son ki ara min ko nawa ne dan Allah, Wallahi zan biya ki har da waɗancan ma”
“Anty Namra ban taɓa ara miki kuɗi dan ki biyani ba, duk abunda na baki a kyauta nake baki shi, gaskiya yanzu bana da kuɗi hannu na, amman ki tambayi Anty ba za'a rasa ba”
Namra bata ƙara cewa komai ba, sai kawai ta kashe wayar, ta fashe da wani irin kuka mai taɓa zuciya. Mardiya duk sai ta tsargu ta duƙa a gurin tana bata haƙuri.
Wata Hajiya dake kusa da ita ta kalle tana tambayar lafiya. Sai masu pharmacy suka mata bayani, cike da tausayawa ta kalli Namra tace
“Tashi Bawai Allah zan biya miki, Allah ya bashi lafiya”
Gyalenta Namra ta riƙa tana mata godiya.
“Allah ya saka miki da Alheri, na gode sosai”
Sai ta kalli Mutumen.
“Dan Allah ina ka san za'a iya siyen wayar nan?”
“Gaskiya sai kasuwar Ƴan wayoyi, dan wannan wayar mai tsada ce can ne kawai zasu iya siyen ta”
Yana faɗar hakan Mardiya ta zaro ido tana ƙara kallon wayar dake hannun Namra. Hajiyar ta kalleta.
“Haba ke kuwa kar ki siyar da wayar ki mana”
“Dole ne na siyar kuɗin asibiti zan biya”
Namra ta faɗa cikin kuka. Tun daga sama har ƙasa Hajiyar ta kalli Namra sannan tace
“Nawa ne kuɗin?”
“Dubu ashirin da shida da ɗari bakwai”
Hajiyar ta kalli yaron pharmacy
“Nawa ne kuɗin ka har nata?”
“Ya kama dubu takwas da ɗari huɗu”
Dubu tara ra ƙirgo ta miƙa masa, bata tsaya karɓar canja ba, ta kalli Namra.
“Muje cikin Mota na muga marar lafiyar”
Da sauri Namra ta fita ita da Mardiya, har suka riga Hajiyar isa gurin motar. Sai da ta buɗe ta shiga sannan ta buɗe musu tace su shigo.
Namra ce a front seat Mardiya a baya. Hajiyar tana yi tana satar kallon Namra. Ita kuma natsuwarta bata tare da ita, tambayar da take mata ma sama-sama take amsa mata.
“A nan garin kuke?”
“A'a Katsina nake zama, shine ma suka mana transfer zuwa can”
“Allah sarki wane unguwa a katsina, nima a katsina nake”
“Nasarawa”
Ta amsa mata dai'-dai lokacin data tayi parking, a harabar asibitin. Sai da taje ta duba Asim tayi ma mahaifiyarsa sannu ta suka je tare da Namra ta biya mata kuɗin Asibiti. Aiko Namra da dingi mata godiya kamar wanda tayi mata kyautar rai.
“Ba komai Wallahi, ai yi ma kai ne. Muje ki kai musu takardar su baki wacan sai muje katsina ɗin, dan nima yanzu can zan wuce”
Komawa suka yi, Namra taje ta kai ma Nurse ɗin takardar ta bata ta transfer ɗin, sannan ta dawo ta kawo ma Hajiyar. Ita ta ciri kuɗi a jakarta ta miƙawa Mardiya tace taje ta siyo masa shorts da ƴar riga a saka masa. Sannan taje ta biya dubu biyu aka basu ambulance, wanda za'a kai Asima ciki.
Mama da Hajaru (ƙanwar Asim) ne suka shiga ambulance ɗin tare da Asim. Namra da Mardiya kuma suka shiga motar Hajiyar, Tun kamin motar ta tashi Mardiya ta karɓi jakar Namra wai ta kawo ta riƙa mata. Ba musu Namra ta miƙa mata daman jakar ta yi mata nauyi.
Yadda take tuƙa motar kamar wata fitacciyar direba, dan da ita da ambulance ɗin ba zaka iya gane wanda yafi gudu ba.
Daf da Magariba suka isa Katsina, kai tsaye Babbar Asibitin suka suka wuce. Emergency Motar ta shiga Hajiyar na binta a baya. Suna shiga aka karɓe shi aka wuce da shi Anas room wato ɗakunan da aka tana na marar lafiya shi kaɗai dan bashi kulawa na musamman. Sai da Hajiyar ta biya dubu goma sha shida na ɗakin sannan aka aje shi, nan take suka soma bashi kulawar gaggawa abunka da babbar asibiti.
Godiya sosai Namra tayi ma mata har ta rasa yadda zata nuna mata jindaɗinta.
“Babu komai Allah ya bashi lafiya, ni yanzu zan wuce gida idan wani abun ya taso ki neme ni a wannan address ɗin”
Hajiyar ta faɗa tana murmushi tare da miƙa mata katin ta. Da hannu biyu Namra ta karɓa, ta raka ta har gurin motar ta, sannan ta dawo.
A Dai-dai lokacin ne likitan ya fito daga ɗakin da Asim yake ya nufo Mama yana magana da ita.
“Za'ayi masa gyara a cinyar ƙafarsa, sai kuje ku biya kuɗin, kuma za a siye masa jiki kamar na gora uku, kuje kuma ku biya kuɗin magani”
Ya ƙarasa faɗar yana miƙawa Mama takardun hannunsa guda uku. Da muguwar damuwa Mama ta karɓi takardar irin bani da madafa ɗin nan. Sai Namra tasa hannu ta karɓa, tana kallon likitan
“Idan ya kai gobe ba komai?”
“Ba matsala, amman dai ku ƙoƙarta kar ya wuce goben”
“Tau mun gode”
Bayan likitan ya wuce Namra ta shiga kwantar ma Mama hankali
“Mama ki shiga ki zauna da shi, ni zan je gida naga ko akwai abunda zan samo”
“Tau”
Ta faɗa da muryar kuka sannan ta shiga ɗaki. Namra ta juya ita da Mardiya suka nufi gida.
Mai Napep na sauke su Mardiya ta miƙawa Namra jakarta, ta nufi gidansu. Cikin kasalar jiki Namra ta buɗe ƙofar gate ɗin ta shiga. Ta daɗe a tsaye jikin ƙofar falon tana kuka, sannan ta buɗe ta shiga.
Wanka ne abunda ta fara yi, ta saka wasu tufafin sannan ta shiga kitchen ta ɗora indomie, a gaggauce ta dafa ta zuba a kula, ta haɗa ma kanta tea kaɗan ta sha, sannan ta dawo ta fito da tabarma da filo da bargo guda biyu, ta aje falo ta ɗauko plates huɗu da spoons da kofuna ta saka a basket, ta aje a falo. Duk abunda take Asim ne a ranta, tunani take inda zata samo kuɗin da za'ayi masa aiki, har kuma ta gama bata samarwa kanta wata mafita ta bayan ta siyar da wayarta.
Mayafinta ta ɗauka ya saka ta fita ta nufi gidansu Mardiya. Da sallamarta ta shiga, mataɓ gidan suka amsa mata, suna mata ya mai jiki. Sai da ta gama gaisawa da su sannan ta wuce ɓangaren su Mardiya, kasancewar gudan irin tsohon gidan nan ne da ake na dangi mai ɗakuna da yawa.
Bata tararda Mamarta ba, sai Mardiya dake sallah. Zaunawa tayi saman simintin ɗakin tana jira ta gama. Bayan ta sallame ta juyo ta kalli Namra.
“Namra har kin yi wanka?”
“Tun ɗazu, dan Allah so nake ki kai ma Mama abinci da wasu abubuwan da za su buƙata, kuma dan Allah idan kin san inda ake fansar da waya ki kai ni ina son siyar da wayar ne”
“Kai yanzu kam sun tashi kin ga har tara ta gota fa, sai dai gobe, sai na rakaki ki kai”
“Abincin fa?”
“Muje na kai musu”
Ta faɗa tana ƙoƙarin tashi. Tare suka fito gidan. Tun da suka fito Mardiya take abu kamar mai jin kunya, har suka shiga cikin gidan. Namra ta bata kayan ta ɗauko sauran canjin dake jakarta ta miƙa mata wai tayi na okada da su.
Bayan ta wuce, Namra ta sake buɗe jakarta ta ɗauko waya, sai taga wayam, babu waya babu alamunta, a nan fa hankalinta ya tashi, sai ta zazzage jakar gaba ɗaya, bata ga wayar ba.
Jikinta be bata ta jefar da wayar a cikin gidan ba, amman haka tabi ta yamutse gidan tana neman wayar.
Har Mardiya ta dawo bata ganta ba, idonta duk ya rine tana jin kamar tayi kuka ba hawaye.
Ita kanta ta lura da yadda Namra ta ƙara firgicewa.
“Na kai musu, tace wai na faɗa miki likita ya sake zuwa”
Hannu Namra ta ɗora saman kai ta fashe da kuka
“Kai Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, kin ga wayar ma da nake son saidawa ban ganta ba, ko kin ga inda na jefar”
Wani irin dakan ƙirji Mardiya tayi
“Baki gani ba? Wallahi ban ga inda kika jefar ba, kuma tun da na karɓi jakarki ban ma buɗeta ba, yau ko na shiga uku, da wayar mutane”
A take tasa kuka. Sai Namra ta share hawayenta tana faɗin
“Ƙila ko na jefar a motar matar nan ne ban sani ba”
“Lallai ba zai wuce can ba, amman ni ban ɗaukar miki waya ba Wallahi, sai idan kuma a asibiti kika jefar”
“Bana zargin ki Mardiya, da zan samu rancen kuɗi da sai naje gida ta yanzu, dan hankalina ba a kwance yake ba”
“Amman yanzu dare ne, da kin haƙura har da safe, kin ga ma baki san gidanta ba”
“Ai ta bani addireshinta, dan Allah ki ara min ko ɗari biyu ne naje na duba, kin ga halin da mijina yake ciki”
“Ina da wasu ɗari takwas da aka bani ajiya sai idan sun zan aro miki”
“Aro min dan Allah”
“Bari na ɗauko miki ɗari biyar”
Tashi tayi ta fita, bata daɗe ba ta dawo, ta kawo mata kuɗin. Sai Namra ta ɗauki Hijabita ta saka.
“Dan Allah Mardiya ki zauna nan har na dawo, ina son ki taya ni kwana”
“Tau ba komai Allah ya tsare”
Ta ɗauki katin ta fice, hankalita a tashe. Napep ta tara ta shiga. Su kusan tafiyar rabin awa sannan suka isa unguwar GRA ring.
Gidajen gurin duk masu kyau ne da ɗaukar hankali, abun ka da wanda hankali ba kwance ba haka suka kai ƙarshen unguwar bata gane gidan ba, dan numbobin gidajen sun ɓace mata. Har sai da suka yi tambaya, saɓnan aka nuna musu gidan Hajiya Saratu.
Sai ta da buga ƙofaɗ gate ɗin mai gadin ya buɗe mata, ta tambaya yace mata gidan nan sannan ta sallami mai napep ɗin, shi ma ɗaker ya karɓi ɗari biyu da hansin.
A bakin gate ɗin ta tsaya sai da mai gadin yaje ya faɗawa Hajiyar sannan yayi mata iso.
Tana saka ƙafarta cikin falon ƙashin turare ya fara mata marhabun.
Haka tayi ta doka sallama amman ba a amsa mata ba, sai ta samu guri ta zauna, zuciyarta sam bata natsu da gidan ba.
ta ɗauki tsowon lokaci sannan matar ta fito cikin wata rigar yadi mai shara-shara, kusan ana ganin underwears ɗinta.
Tun da Namra ta kalleta sau ɗaya ta sadda kai bata sake kallonta ba, duk gaisuwar da suka yi idon Namra na ƙasa.
Cikin wani irin karairaiya taje ta ɗauko ma Namra lemu da snack ta kawo mata. Namra bata ci dan basu ne a gabanta ba, kuma ta kasa ɗaga ido ta kalli Matar. Ganin hakan yasa matar ya taso ta dawo kusa da Namra ta zauna, ta kai hannunta dafa Namra tana shafa bayanta duk da kasancewar Namra na cikin Hijabi ne.
“Ki kwantar da hankalin ki miji zai samu sauƙi nayi miki alƙawarin duk abunda tmya dace ayi masa za a masa, dan ya samu lafiya, yanzu me likitocin suka ce ne? Dan daga ganin ki akwai wani a ƙasa”
“Na gode sosai, yanzu sun ce sai an biya kuɗin aiki dana magani, kuma suna buƙatar jini gora uku, shine naso na siyar da wayana na duba ban gani ba, nace ko na manta a motar ki ne”
Wani ƙasaitattacen murmushi tayi, ta girgiza mata kai.
“Baki jefar da komai a mota na ba, amman bari na baki keys ki duba, saboda cire kwankwanto”
Bata jira komai ba, ta tashi ta shiga ɗaki ta ɗauko mata keys ɗin ta miƙa mata.
“Muje ki duba, amman na faɗa miki ba dole sai kin siyar da wayarki zaki iya taimakon mijinki ba”
Namra ta karɓi keys ɗin tana faɗin
“Ba ni da wata mafitar ne sai wannan”
“Kina da mafitoci ba ma ɗaya ba”
Ta faɗa yayinda suke fitowa daga cikin falon suka nufi gurin motocin da suke gidan. Ita da kanta ta nuna mata motar da suka shigo, cikin rawar jiki Namra ta nufi motar ta buɗe tana dubawa. Zuwa Hajiyar tayi bayan Namra ta tsaya tana shafa mata duwawu, tare da faɗin
“Duba da kyau ki gani, amman ni bana tunanin kin bar wani abu a gurin”
Da sauri Namra ta juyo ta fito da jikinta cikin motar tana yima matar wani mugun kallo.
“Miye haka? Ya zaki riƙa taɓa min jiki kamar wata karuwa, ko an faɗa miki ni irin waɗannan mata nan”
Murmushi Hajiyar tayi kamar bata ji zafin kalaman Namra ba.
“Ɓana nufi komai da ke sai Alheri, kina da kyau da duk mace data kalle ki sai tayi sha'awarki, balle kuma namiji, dan haka kiyi amfani da damarki ki taimaki kan ki”
“Ke kuma haka kike? Tirrr da ke daman taimakon da kika min ba dan Allah kika min ba? Saboda wani mugu nufi naki? Toh Allah ya fiki, jikina bana mata irin ki bane, ba kuma na wasu mazan bane, na mijina ne shi kaɗai halalina”
“Hmmm kije kiyi tunani Namra, matuƙar kika amince da buƙata zan miki duk abunda kike so a duniyar nan, idan ma waje ya dace a fitar da mijinki zan sa a fitar da shi”
Namra ta girgiza mata kai.
“Dukiyarki bata burge ni, arzikin gidan mu ya ninka naki sau dubu, ƴan'uwana ne suka juya min baya shiyasa kika ganin a halin da kika tsince ni”
Hawayen ya gangaro daga idon Namra. Hajiyar ta matsa kusa da Namra tana ƙoƙarin dafata.
“Kaicon ki, haƙiƙa ina tausayin rayuwarki, wallahi wata mace bata taɓa burge ni ba kamar ki”
“Ba nice a abun tausayi ba, kece a abar tausayi a ranar da zaki yi nadamar da bata da amfani”
Namra ta buge mata hannu ta juya ta fice daga gidan tana hawaye. Ta daɗe tana tafiya a estates ɗin kamin ta samu Napep. Har ta iso gida hawaye take zuciyarta a cakushe.
Ɗari biyun da hasin da suka yi saura ta miƙawa mai Napep ɗin, ya so yayi magana, sai dai hawayen daya gani a idonta yasa shi tausayinta, ya kaɗa napep ɗinsa yayi gaba.
Mardiya na gani hawaye a fuskar Namra, hankalinta ya tashi, da sauri ta riƙa ta suka zauna saman kujera.
“Lafiya ? Ba acan kika jefar da wayar ba?”
Sai kawai Namra ta fashe da kuka tana riƙe Mardiya kamar ta shige cikin jikinta.
*** *** ***
Ganin dare ya lula Namra bata dawo ba, yasa Mama har zuƙa sosai, a ganinta abun kamar be damu Namra ba. Tun da tana da hanyoyin da zata iya biyan wannan kuɗin. Ita ganin take kamar ma da haɗin kai aka yi masa wani abu yayi haɗari motar, so that idan ya mutu sai ta auri wanda take so.
“Mama ko kuɗin adashe zamu karɓo a biya ina ganin fa kamar bata da kuɗin nan”
Cewar Hajaru, Mama ta kai mata wani mugun zungura
“Duk naji bakin ki yayi maganar adashen nan sai na kusa halaka ki, taya zata ba mu kuɗi bayan mun riga mun zuba, kina ganin kullum zogaron kuɗin zubi take mana. Ai ita ta fimu sanin hanyoyin samo kuɗi, ta nemo ta biya a itace silar komai tun da tasan be wani iya mota ba, tasa ya jawo ta tun daga sokoto har katsina dan kawai su ga bayan shi.
Ni Wallahi ɗana ko mutuwa yayi sai nayi ƙararsu”
Hajaru dai tayi shiru bata sake cewa komai ba, Mama kam sai cika take tana barsewa, ita mai ɗa.
KALSOOM POV.
Babu abunda ta ɓoye Salma na zamantakewar auren da suke yanzu da Hilal.
Ita tafi raja'a akan Hilal baya son haihuwa, daman Asmee takan nuna mata alamun hakan tun lokacin data shigo cikin gidan. Sai dai tunaninta ya sha banban lokacin da Salma take nusar da ita akan wasu abubuwan data manta.
“Haba Kalsoom ke kan ki yanzu ba zaki iya gane wani abu a tare da shi ba? Taya za ace dan kin yi ciki sai ya sauya miki? Baya son haihuwa zai bar matarsa ta haifi yara uku kuma tana aiki?Sherin kishiya yana da yawa Kalsoom musamman na zamanin nan”
“Naga sauyi a ɓangarenta dan duk wani kishi data ɗauka yanzu ta aje shi, bana da matsala da ita”
“Wannan ma kaɗai ya isa ya nuna miki akwai abun da tayi, ki bita a sannu kuma ki yi taka tsantsan da ita. Sannan a duk lokacin da mijinki yake fushi yana hawa sama karki tanka shi, kisa mishi ido, saboda maganar zai iya zama miki illah.
Cigaba da addu'ah, idan zaki iya kiyi alwala a zama ɗaya ki karanta Yasin ƙafa goma sha biyar, ki roƙi Allah, ko kuma ki karanta ayatul kursiyu ɗari uku da sha uku Wallahi duk kika roƙi Allah sai ya amsa miki, ki daure kiyi na tsawon sati acikin kwana uku Allah zai biya miki buƙarta ki.
Sannan ki samu ruwa mai kyau ki watsa a saman rufin ɗaki, idan ya gangaro ki tara abu ya zuba a ciki, ki taceshi ki sha ki wanke kanki, Wallahi indan Asirine akayi miki sai ya karya kuma sai Allah ya nuna miki wanda yayi miki haka a bachin ki, maƙukar kika yi har sau uku”
“Na gode sosai Salma, Allah ya bar zumunci”
“Amin Allah ya baku zama lafiya”
Daga haka ta aje wayar, ta jingina da gadonta tana sauke ajiyar zuciya.
“Kai kayi auren baka huta ba, idan kuma baka yi baka huta ba, da wannen zaka ji”
Yadda ya turo ƙofar ɗakin ya shigo ne yasa ta zabura ta tashi zaune, tana kallon yanayinsa.
“Ina kuɗina dake cikin closet?”
Wani kallon mamaki tayi masa.
“Kuɗi kuma? Ni ban ɗauki kuɗin ka Doc, ban ma san ka aje kuɗi a gurin ba”
“Babu wanda zai ɗaukar min kuɗi bayan ke, dan ke kaɗai kike goge gurin”
“Amman ai ba ni kaɗai bace a gidan nan”
“Mata ta bata taɓa min sata ba, ƴara na kuma basu ɗaukar min kuɗi, sannan basa da wayon da zasu iya ɗaukar dubu ɗari uku da hansi”
Hawaye ya silala a idonta. Ta nuna kanta
“Ni kake zargi kenan, ni na ɗaukar maka kuɗin ko? Haba Doc taya zan ɗaukar maka kuɗi abunda ban taɓa yi ba”
Ƙara haɗe fuska yayi kamar an aiko masa da mutuwa, ya ɗaki mirror ta yana ƙara jadadda mata.
“Bari kiji na faɗa miki, ko ki nemo dubu ɗari uku da hansi ko kuma a bakin auren ki!”
Bata san lokacin data kwantar da kanta gefe tana masa kallon da ita kanta bata san tana masa ba, ta kasa tantancewa shi ne ko ba shine ba.? Fuuuu ya bar ɗakin kamar walƙiya yana wani irin huci.
________________________________
I need more and more comments. 🙌
Bari na ga suwa suke son nayi long chapter gobe 🤔
BEST REGARDS 💖
Khadeeja Candy 😘🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Masu Tambayar Labarin Uzair da Amira zai zo muku a gaba, tare da nasu Zagon ƙasa. Just keep moving komai zai zo daki-daki.
*PAGE - 25*
NOT EDITED ⚠️
KALSOOM POV.
Ta daɗe a gurin tsaye duniyarta na juya mata, kunnuwanta sun kas ɗaukar abunda suka ji Hilal ya faɗa mata, idonuwanta kuma sun kasa yarda da ba mafarki take ba.
Makomar aurenta take tunani, yadda zamanta a gidan zai kasance yake mata yawo a ƙwaƙwalwa, taya zata biya abunda bata ɗauka ba? Akan me zai nuna dubu ɗari uku sun fi aurenta daraja a gareshi? Dan me idonsa zai rufe har yayi mata wannan furucin?
Ta kasa zaɓa tsakanin igiyar aurenta da kuɗin da idan har ta bashi zai iya tabbatar masa da lallai ita ɗin ce ta ɗauka.
Hawayen dake idonta ta share, ta tashi ta ɗauko akwati ta buɗe wardrobe ta ɗauko tufafinta ta saka aciki, ta ɗauki jakarta ta saka wayarta da duk wasu abubuwa da tasan zatayi saurin buƙata, ta zari mayafin ta yafa ta jayo akwati ta fito. A lokacin Hilal yana zaune falon ya ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya.
“Ina zaki je?”
“Gidan mu, ba kace na kawo kuɗi ba ko kuma a bakin aure na? Ni ba zan iya biyan abunda nasan ban ɗauka ba, amman Allah yana nan baya bachi baya angaje zai bayyana gaskiya, amman ni ba ɓarauniya bace”
Tasowa yayi ya ƙaraso kusa da ita.
“Look Kalsoom ...”
Sai kuma yayi shiru ya kasa magana, ya kuma kasa kallonta. Ganin hakan yasa t share hawayenta ta cigaba da jan akwatin. Sai ya riƙe ya kai hannu ya riƙota, kuma ya kasa mata magana, shi dai ji yake babu daɗi ya rasa abunda ke damunsa, sai yanzu yake jin nadamar furucin da yayi mata, mamakin yake yadda ya alaƙanta sakinta da kuɗin da basu taka kara sun karya ba a gurinsa, bayan kuma baya da tabbacin ita ɗin ce ta ɗauka.
“Ban aureka dan dukiyarka ba, balle har ya kai ni ga yi maka sata, nayi tunanin kasan darajar aure, ashe na yi kuskure, daman an faɗa min baka son haihuwa kana son kayi amfani da wannan damar ne ka wulaƙanta ni ko? Zan bar maka gidan ka sai ka zauna da wanɗanda ba ɓarayi ba!”
Kalamanta sun harzuƙa shi matuƙa, sai kawai y saki hannun nata.
“Kije duk inda zaki je, amman bari na faɗa miki duk wani abu ya samu cikin nan na ki, Wallahi sai kin yabawa aya zaƙinta”
Cikin wani irin ɓacin rai ya nufi ɗakinsa, ita kuma ta bishi da wani kallo na takaici na baƙinciki, kamin ta saka kai ta fice.
Ɗakinsa ya koma ya zauna, rasa yayi abund ke masa daɗi, dawowar da yayi ɗaukar kuɗi sai ya kasa komawa. Ba shi ya fito ɗakin ba sai da lokacin ɗauko yaransa daga makaranta yayi har ya gota, sannan ya fito daga ɗakin.
Kukan Rafiq yaji da yaji yasa shi ya nufi ɗakin Kalsoom dan shi sam ya manta da Fariq na bachi.
Ɗaukarsa yayi ya ɗora a kafaɗa yana jijjigashi, ya fito ya buɗe motarsa ya saka shi gidan gaban, sannan ya zagaya ya shiga ya tashi motar.
Ko da ya isa ɗaukarsu duk sun ƙosa, ga Rafiq sai kuka yake masa, har suka dawo gida.
Da gudu suka shiga falon, sai suka tsaya a gurin da Kalsoom ta saba nuna musu su aje safunan su suka aje sannan suka nufi ɗakinta suna rigangan.
Ganin bata ɗakin yasa suka fito suka nufo kitchen da gudu, nan ma basu ganta ba, sai suka nufo dinning gurin da Hilal yake tsaye yana haɗawa Rafiq madara.
“Daddy ina Anty?”
Yi yayi kamar be ji su ba, har sai da suka ƙara tambaya sannan ya kalli Ezzah kasancewar ita ce babba.
“Anty ku taje unguwa”
“Yaushe zata dawo?”
Ulfah ta tambaya. Sai da ya sawa Rafiq madara a baki sannan ya amsa musu.
“Ni ma bata faɗa min ba”
“Daddy ta dafa mana abinci?”
“A'a bari Rafiq ya gama zan muku takeaway yanzu”
“Anty tace mu daina cin takeaway sai abincin gida”
Kallonta Ezzah yayi da kyau.
“Amman yau Anty ki bata nan na ce zaku ci takeaway”
“Daddy ka dafa mana Indomie”
Ulfah dake ƙoƙarin cire uniform ɗinta ta turo baki tace
“Ba za mu ci indomie ba ai da safe Indomie muka ci, Daddy ayi mana takeaway”
Ezzah ta nufo a fusace tana faɗin
“Allah kuwa duk Anty ta dawo sai na faɗ mata nace kin ci takeaway”
Ita kuma sai ta taɓa hannayenta alamar ma shiryawa masifar.
“Nima na faɗa mata na ce kin yi faɗa da wata a makaranta, ai ta ce ki daina faɗa a makaranta”
Hannu Ezzah ta kai zata daketa sai Hilal ya katsa mata tsawa.
“Ezzah karki dake ta, zan dafa miki indomie, ke kuma zan miki takeaway is that okay?”
Duk suka haɗa baki gurin amsa masa.
“Yes Daddy”
“Come and take your brother”
Ezzah ce taje ta karɓe shi, sannan ya nufi ɗakinsa kansa na masa wani mugun zafi.
NAMRA POV.
Tare suk kwana a gidan ita da Mardiya. Sai dai ita batayi bachi ba, har safe Asim take tunani da halin da yake ciki.
Tasan ita kaɗaice a duniyar nan zata iya taimakonsa, idan kuma har bata masa ba waye zai masa, tun da mahaifiyarsa bata da hali.
Babu abunda ya fi ɓata mata rai kamar abunda Anty Amarya da Maryam suka mata, kuma bayan su bata tunanin akwai inda zata iya zuwa ta kai kukanta.
Tun da tayi sallah asuba ta shiga kitchen ta haɗ ma Mama abun kari, sannan ta shigo ɗakin da suka kwana da Mardiya ta tasheta.
Tashi tayi zaune tana murtsikar ido.
“Ina kwana har kin tashi?”
“Ba dole na tashi ba, har na haɗa muku abun karyawa,dan Allah shiga ki wanke bakin ki ki karya, idan kin san gidan wat dillaliya ki kai ni ko kuma ki kira min ita ta zo ta siye gadona”
Mardiya ta daki ƙirji
“Gadon ki kuma? Haba Namra karki siyar da gadon ki mana”
“Idan ban siyar da shi ba, kai na kike son na siyar ? Ko sata zan yi? Ba ki ga hali da mijina yake ciki ba”
“Amman ba ku da ƴan'uwan ne da za su iya taimaka muku?”
“Ƴan'uwana sun juya min baya, shi kuma ƴan'uwansa ba wani hali ne dasu sosai ba, nasan ko da za a samu ba zai wuce ayi karo karo ba, kuma kin ji abunda likita yace kar ya wuce kwana biyu ba'ayi masa aikin ba”
Sosai Mardiya ta ɓata rai tana nuna mata rashin jindaɗinta akan siyar da Gadon da Namra zata yi.
“Gaskiya ni ban jidaɗin haka ba”
“Ba komai Allah zai bani wani, tashi ki shirya ai kin san wata mai siye ko?”
“Eh akwai wata a nan unguwar mai siye sosai”
“Dan Allah ki min magana da ita yanzu kar rana yayi, kuma ina son kije ki kai musu abincin su”
“To bari na tashi”
Ƙoƙarin tashi take tana wani kare-karen zane, kar sarƙar dake jikinta ta faɗo. Ita kam Namra bata ma kula ba sai ta tashi ta bar mata ɗakin.
A haɓar zanenta ta ƙulle sarƙar sannan ta shiga banɗakin, ta wanke fuskarta, koda ta fito har Namra ta kawo mata taliya a plate da ruwan sanyi ta aje mata.
Haka ta riƙa aika abincin kamar wata tsohuwar mayunwaciya, nan da nan ta ƙare ada plate ɗin, ta sha ruwa sannan ta fito falon tana faɗin
“Bari naje na kira miki ita”
“Toh dan Allah ki yi sauri”
Namra ta faɗa tana shan tea ɗin dake hannunta, idonta duk sun wani zurun-zurun kamar ita ce marar lafiyar.
Mardiya bata ɗauki dogon lokaci ba ta dawo tare da matar, sai da suka gaisada Namra sannan Namra ta ta shiga da ita cikin ɗakin ta nuna mata gadon. Tana ganinsa tasan sabo ne, amman duk da haka sai da ta gama duba ko ins nasa sannan ta kalli Namra tace
“To nawa aka masa kuɗi?”
“Babu wanda ya taya, ki siya kawai”
“Toh ai ba siyen ba, kin san irin wannan manyan kayan ba ko wace mai keya ke siyen su ba, sai su daɗe baka sai da ba amman ke nawa kika ga zaki iya sai da su?”
“Ni dai miliyan ɗaya har da wani abu Abbah ya siya min su, ke kuma sai ki kwatanta”
“Kai kai aiko an daki hancinsa, dan wannan kayan yanzu wasu ma sun daina yayinsu, ai sun faɗi sosai. Sabin ma ba zasu wuce ɗari bakwai ba”
“Tau ki bayar da haka ɗin”
Tayi ma Namra wani kallo tana taunar goron dake bakinta.
“Ni ko ai ba zan ci riba ba, magana ta gaskiya zamu yi, dan ni bana son nakkasa mutum, ƙara ayi ciniki babu cuta babu cutarwa, indai zaki iya bari ɗari, shima dai ƙoƙartawa zan yi dan ba duk dillaliya ke zuba kuɗi da yawa ta siye kayan data san ko ta sai da ko karta sai da ba”
“Haba baiwar Allah, Wallahi lalura ce tasa zai sai da abu na, ba kiga sabo ba ne”
“Na gani amman ai kin san duk abunda aka riga aka fitar indai kuɗi kake so sai ka faɗi, amman yanzu zan yi miki magana ɗaya idan yayi miki na siye ɗari uku da ashiri”
Kallon gadon Namra tayi ta sake kallonsa ta kalleshi sannan ta kalli Matar tace
“Kawo kuɗin”
“Amman fa sai naga mai gidan ki, dan wani lokacin ana siyen kaya sai kuma miji ya zo yace shi ba za'a siyar da kayan matarsa ba”
“Mijina ba shi da lafiya kuɗin magani nake nema shiyasa zan siyar da wannan gadon, yanzu haka yana asibiti aiki za a masa”
“Allah sarki, Allah ya sauwaƙe, amman duk da haka zan zo da ɗana sai yayi mana takarda guda biyu saboda gudun matsala”
“Ba matsala, kuɗin fa?”
“Kuɗi gaskiya sai zuwa gobe na kawo miki sai na ɗauki gadon, dan yanzu ƙuɗin da suke hannuna ba su wuce ɗari biyu ba”
“Bani haka gobe sai ki kawo min sauran ki ɗauki gadon”
“To ba matsala amman sai kin biyo ni gida na baki ga ban ƴan gidan mu saboda shedu”
Sai da Namra ta bawa Mardiya abincin da za a kai ma Mama sannan ta saka hijabinta ta kulle gidan suka fita tare.
Gida matar suka shiga, ta ƙirgo kuɗin gaban mutanen da suke gidan ta bawa Namra bayan ta faɗa musu yadda suka yi, da Namra tun a gida. Sannan tasa ɗanta ya ɗauko takarda yayi shedu guda biyu ya bata ɗaya ya bawa Namra ɗaya.
Tare da Mardiya Namra ta fito gidan, suka tare napep ta kai su Asibiti. Mardiya ce ta wuce kai musu abincin Namra ta nufi gurin biyan kuɗin magani. Dubu ɗari da talati ta biya na aikin, sannan ta biya na magani suka zo suka ɗibi jininsa suka auna sannan suka tura ta lab gurin siyen jini, tayi sa'ah an samu irin wanda ake so, gora uku ta siyo sannan ta dawo ta kawo musu.
Cikin dubu ɗari biyu, kuɗin daya rage be wuce dubu bakwai da ƴan canji ba. A kasale ta shiga ɗakin da yake, sai ta tararda shi cike ƴan'uwan Asim na Sokoto da Bakori sun zo dubiya.
Cikin far'ah da ƙarfin hali ta gaisa da su, sannan tayi ma Mama ina kwana. Sai kusan azahar wasu suka koma aka bar mutum biyu su wai ba yau zasu ba.
Ganin azahar tayi yasa Namra ta ba Mardiya makulli taje ta girka mata abincin rana, ita kuma ta dawo kusa da Asim ta zauna, ta zuba masa ido kamar ba gobe. Daker ya ɗaga ido ya kalleta ya sake rufewa ji yake kamar ba duniya yake ba.
Ita kuma wani irin tausayinsa take ji take ciwon kamar a jikinta yake.
Uku dai-dai nurses suka shigo suka fita da shi zuwa ɗakin da za'ayi masa aikin.
ABDOOL POV.
Hannu ya kai ya kunna air conditioner dake ɗakin sannan, ya rage tufafin jikinsa, ya buɗe freezer ya ɗauko power horse ya sha.
Sai ya dawo saman sofa ya zauna, yana kallon window. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ya miƙa gurin windowdake garden yana sauraren birds singing.
Yana jindaɗin saurarensu sosai da sosai, hakan yasa lokuta da dama idan ba shi da wani aikin ya kan tare a garden dan kawai sauraren sautin na su.
Hannayensa ya zuba a aljihu ya tashi yana wani irin taku na sarauta da ƙasaita ya nufi window, Peacock ɗin dake ƙarƙashin apple tree yana sha'aninsa ya tsurawa ido. Kamar wanda ya tuno wani abu sai kawai yayi wani ƙayataccen murmushi ya wanda ya sanya dimples ɗinsa fitowa, lumshe ido yayi yana shafa fuskarsa.
“Because of her, half the time I don't even know that I'm smiling, she insult me but i still need to see, who's she?”
Abund ya furta kenan a fili sai kuma ya bawa kansa amsa.
“The Unique one”
Murmushi yayi mai sauti, ya rumgume hannayensa yana ƙara saita tunaninsa.
Taya akayi ya zure haka? Mema ya kai shi kula wata har yayi ƙoƙarin mata magana, shi da bay da lokacin wasu mata. Hannu yasa a aljihun wandonsa na Army, ya ɗauko wayarsa ya kira wata number, bugu ɗaya ya ɗauka.
“Ali ya ake ciki?”
“Naje har gurin shugaban masu Napep ɗin na bincika, sai aka kawo min mutumen yace shi be santa ba kuma a bakin babbar asibitin funtua ya sauke ta, wai yana ganin jinya take”
“So what's the solution?”
“Sir want i think is better mu shiga cikin asibitin mu bincika”
“No”
Ya girgiza kai alamar shawarar bata masa ba, ya ɗan ɗauki dogon lokaci, be ce masa komai ba, ba dan kuma baya da abun cewar ba, sai dan isa da izza.
“Ka cire kuɗin da zai isa, a shirya takeaway da five thousand sai muje mu raba ma Patients ko Allah zai sa mu samu ganinta”
“Okay but Sir Akwai meeting da zaka je gobe Abuja, kuma the next day akwai meeting ɗin Mr President ya shirya za ku yi akan matsalar tsaron nan na Maiduguri da Zamfara”
Lumshe ido yayi ya buɗe.
“I know that, nasan end of this month ina da free days, a cikin wannan rana ku zamu je, sai ka saka mana date”
“Alright Sir zan duba the most expensive free day na ka”
“Good of you”
Sai kawai ya kashe wayar, ya mayar aljihu. Da ƙarfi aka banko ƙofar ɗakinsa, sai kawai yayi murmushi.
“Hey Dude”
Wanda ya kira da sunan ta fito daga cikin labule tana dariya, yarinya matashi wanda ba zata wuce fourteen to sixteen years.
“Yarima Ummi na kiran ka”
Ta faɗa tana taɓa hannayenta. Hannayen nata ya riƙa yana murmushi.
“Dude Yarima has finally found his princess”
Ta zaro ido
“Wow, when? How? Who?”
“At funtua i don't know who's she”
“Is she really cute?”
Wa wara manyan idanuwansa.
“Yeah she's so pretty, she had that diamond eyes, her lips is so cute, i like her face, she's tall, she wearing Hijab and she's black, Dude you know how i love black girls huh?”
“Yes Dude so how are we going to meet her?”
“I don't know, she slap me Dude”
Ya wani ɓata fuska kamar ƙaramin yaro. Itama ta ɓata fuska kamar tayi kuka.
“So heart touching”
“Don't worry i will slap her heart when i have a chance, but i still feel her soft fingers on my cheek”
“ I will be the first one to tell Ummi”
Ta faɗa tana dariya. Sai yayi saurin rufe mata baki
“No Dude wannan sirrin mu ne, no one will ever know”
“Yes I won't tell”
Ta faɗa tana ɗaga hannu sama alamar tayi alƙawari.
“So tell me why Ummi take son gani na?”
“She want you to go and meet Cute Eysha, daughter of Hajiya Saratu”
“What? Please tell her I'm sick”
Har ta buɗe baki sai kuma ta rufe ta saki hannunsa ta fita. Batayi minti biyar da fitar ba yaji alamun shigowar Ummi.
Da sauri ya haye saman gado yaja bedsheet ya lulluɓe ya makore kamar da gaske ba shida lafiya.
“Ai dole ka riƙa ciwo, kullum baka da hutu kai ne agogo sarkin aiki, idan an maka maganar aure kamar ance ka faɗi ka mutu, duk yaran garin nan kace basu maka ba, ko so kake ni da Mai martana mu mutu ba muga auren ka ba?”
Ɗan ɗagowa yayi kaɗan yana pretending like he's really sick.
“Ummi yanzu kuma miye nawa? ”
“Ƴar wajen Hajiya Saratu nace kaje ka gani, tace min jiya ta dawo daga Kaduna”
“Ummi ko na yi aure babu wanda zata zauna da ni, saboda ina da lalura ta rashin lafiya yanzu haka Dr Alex ya ɗora ni akan magani”
Ya faɗa yana ƙoƙarin mayarda ƙaryarsa ta zama gaskiya. Ita kuma sai ta amsa da ƙarfi.
“What?”
Sai kuma ta kalli ƙanwarsa.
“Afrah go and watch your favorite channel”
Sai da suka yi ido biyu da yayan nata sannan ta fice.
ANTY AMARYA POV.
Ji take bata kyautawa Namra ba, idan har bata mata ba babu wanda zai mata sai Allah, soyayya irin ta ƴa da uwa ta hana Anty Amarya ƙyale Namra har sai da tasa Maryam ta tura mata dubu ɗari da Hansi.
A gajiye Maryam ta shigo falon ta zauna kusa da Anty Amarya tana miƙa mata atm ɗin ta.
“Kai yau nasha wahala Wallahi, sai kusan 4 muka tashi lacca, naje back kuma na tararda layi”
“Kin tura mata?”
“Eh but her phone is still switch off ”
“Maybe ta siyar ita ma”
“Kai why not su dawo nan garin? Zama acan zai mata wuya”
“Leave here ita ta so ai, sai taje tayi abunda take ganin yafi mata”
“Amman Anty Namra zata sha wahala tun da tana gudun zuciyar mutane”
Ajiyar zuciya Anty Amarya ta sauke, tana wani nazarin na daban.
_________________________________________
Five words for this chapter... 😻
Waiting for your comments... 😘
Best regards to you all... 💖
CANDY🌺
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
This page is for Birthday Girl Salwees. Happy Birthday Dear 💖
*PAGE - 26*
NOT EDITED ⚠️
Hankalin Namra be kwanta ba har sai da aka fito da shi daga ɗakin da aka masa aikin.
Sai suka dawo da shi, ɗakin da yake, anyi aiki cikin nasara da taimakon Allah.
Sai da yamma Mama ta je gidan Namra ita da Hajara dan yin wanka ta kuma ɗan huta, Mardiya Namra ta bawa keys ɗin gidan dan ta taba musu abinci kuma ta taya su zama. Ita kuma ta kwana da Asim a asibitin.
Babu irin inda Mama bata shiga ba a gidan, sai baya kyau gidan take da girmansa. Mardiyace ta faɗa mata Namra ta siyar da gadon har an bata wani abu daga ciki.
Babu irin tsinuwar da Mama bata yi ma iyayen Namra ba, a zatonta sune suka turo mata da kuɗin aiki dana magani, a nan ne Mardiya ta ƙara fayyace mata matar data taimaka ta kawo Asim asibiti ba yar'uwarsu bace, nan ma Mama ta cika da mamaki, dan a zatonta ita yar'uwarsu.
“Kai tirr da wasu mutune Wallahi, wato su babu ruwansu da lamarin mijinta tun da ba ita bace ko? Hmmm ni ban taɓa ganin iyaye irin nata ba, daman ba son auren su ke”
Taja wani godon tsaki sannan ta fito daga ɗakin, ta shiga kitchen ta fito ta shiga ɗayan ɗakin. Mardiya dai na biye da ita har ta gama duba gidan. Shikafa da miya Mardiya ta dafa tare da Hajara.
Washe gari ma wani abincin Mardiya ta sake dafa musu, bayan sun ci ta zuba wanda zasu tafi dashi a asibiti, sannan suka wanka suna cikin shiri Dillaliyar ta zo Mardiya tace mata bata nan, sannan ta rufe gidan suka nufi asibitin.
Namra suka tarar zaune a kujerar dake ɗakin tana bawa Asim tea. Ba laifi alamun sauƙi ya bayyana a yanayinsa, wanda a ada ma idan ya ɗaga ido sai yayi saurin rufewa yanzu kuma gashi har yana shan tea.
Farinciki gurin Mama ba'a magana, sai ta zauna saman gadon kusa da shi, tana murmushi
“Mashallah Ibrahim, Allah ya ƙara maka lafiya”
Ɗan murmushi yayi kaɗan irin yana jin zafin ciwon nan yana ƙarfin hali. Mama ta kalli Namra
“Yaushe ya farka?”
“Tun da asuba, har likita ya duba shi ya bada wata takardar ta gani yace allura ce za a masa guda bakwai, kullum ɗaya saboda jinin daya bugu a kansa”
“Allah yasa dai babu tsada”
“ Pharmacy asibiti sun ce duk ɗaya, dubu tara ne, ga kuma maganin da suka rubuta shima sai yaci dubu biyar”
Mama ta rafka uban tagumi.
“Tau ai fa kaji matsalar babbar asibiti, yanzu ina za a samu wannan kuɗin kuma? O Allah”
Namra ta saci kallon Mardiya da idonta ke kansu, tace
“Mardiya kuje waje ke da Hajara”
Tashi tayi ta fice ita da Hajarar. Sannan Namra ta kalli Mama tace
“Akwai kuɗin da zan siya da su, amman da abinci naso mu siya dan abincin mu ya ƙare”
Kai Mama ta girgiza
“Wai Namra iyayenki haka zasu zura miki ido, babu wani taimako? Naga dai suna da shi, amman ko ɗan abincin nan ai sa taimaka muku da shi, amman ace kayi ta sai de sai de anya haka yayi?”
Wani kallo Namra tayi mata.
“Iyayena sun yi iya ƙoƙarinsu duk kan abuɓda zasu min a yanzu kyautatawa ce, amman ba dole ba, balle kuma mijina ”
“Haka ne, daman can ai ba son auren su suke ba, sun fi son ku yi ta wahala kamar ba ƴarsu ba”
“Mama ya kamata ki kina tauna magana kamin furta ta, iyayena, iyayena kuma sun min komai tun da har suka bar ni na auri Asim”
“Amman idan ga mutunci ai da ke da shi kun zama ɗaya, ki duba kiga ko dubiya har yanzu babu wanda ya sake leƙowa daga danginku, Kuma wallahi inda wani guri ne dole ne su ɗauki nauyi naganinsa tun da da motar gidan yayi haɗari, amman sun ɗauki ƙiyayyar duniya sun ɗora masa akan auren ki kamar wanda ya kashe musu wani abu”
Zuciyar Namra ta kawo sosai, a take idonta ya cika da ƙwalla.
“Asim yayi haɗari da motar gidan mu saboda an rubuto zai yi haɗarin, wai Mama mi na tare miki ne? Miyasa kike abu kamar wanda bata yarda da ƙaddara ba, miyasa zaki ɗauki laifin haɗarin motar da Asim yayi ki ɗora min?
Kin manta da ni matarsa ce wace mace ce zata so mijinta ya kasance a halin da Asim yake? Duk abunda na masa baki gani ba? Mahaifiyarsa ce ke amman sisi ban tambaye ki na siyer da kayan ɗakina na biya masa kuɗin magani, amman duk wannan be isa a goge laifina ba? Kin kira aure na da ƙaddara kina tunanin hakan yayi min daɗi? Me kike son na masa ne? Rai na kike son na cire na bashi ko kuma ciwon kike son na maida jikina?
Haba Mama ku bar ni na ɗaya mana, da matsalar iyayena zan ji ko da ta mijina, ko kuma wanda kike ƙoƙarin sani, ke uwace wata maganar be kamata tana fitowa daga bakin ki”
Mama ta cika da mamakin jin furucin da Namra tayi mata, wani dogon numfashi taja ta sauke tana taɓe baki.
“Kin goge ladarki Namra, daman kin masa duk abunda kika masa ne dan ki faɗa kin masa, ai kaji tsiyar taraiya da mai arziki, so kike ace ɗana ya cinye miki komai ko? A ƙaƙaba masa, kamar yadda aka masa na satar ki ko? Ni da zuciya ɗaya na bar ɗana ya aure ki ba da wata manufar ba”
Ta ƙarasa maganar da kuka har da hawaye. Uffan Namra bata ƙara cewa ba, sai kawai ta ɗauki jakarta ta fice.
Sai da ta biya gurin da su Mardiya suke ta karɓi keys sai Mardiya ta biyo ta suka yi gida tare. Tun a Napep Namra ta soma yi ma Mardiya faɗa.
“Dan me zaki faɗawa Mama na siyar da gado na ? Ina ruwanki da rayuwata tana mijina? Jaka zaki tallata ni a unguwa? Ko akai na farau? Abunda ya shafi mijina da mahaifiyata nawa ne babu ruwanki a ciki, dan haka ki iya bakin ki”
Ta ƙarasa dai-dai lokacin da mai Napep ɗin ya sauke su ƙofar gida, Namra ta miƙa masa kuɗinsa ta nufi gate ɗin ta buɗe ta wuce cikin gidan a fusace. Mardiya ta rufa mata bayana tana ƙoƙarin wanke kanta.
_______________________________________
Yau yayi kaɗan ko? Bana son na bar ku babu post ne. Idan Allah ya bani iko zan yi dogon page gobe.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 27*
NOT EDITED ⚠️
Namra na saka ƙafarta cikin falon Mardiya ta saka nata, ta zauna kusa da Namra ta marairaice tana ta ƙoƙarin kare kanta.
“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, Wallahi Dillaliya ce ta shigo lokacin da zamu fita da su, nace mata baki nan shine tace ga cikon kuɗin ki kuma tana son ta ɗauki gadon, shiyasa har ta ji, idan ma baki yarda ba zan iya zuwa na kira Dillaliyar ki tambaye ta ki ji”
Namra ta sauke ajiyar zuciya tana son danne fushinta.
“Na ɗauka ke kika faɗa, da nace baki min amana ba”
“Haba Namra nikam miye ruwana da sha'aninku tsakanin ki da miji da yan'uwansa babu ruwana a ciki. Dama tazo nan babu irin maganar da bata yi ba a kan iyayenki amman uffan ban ce mata ba, ke ma kuma ban faɗa miki ba”
Wani ɗogon numfashi Namra taja ta sauke, tayi shiru kamar mai nazari.
Mardiya ta tashi tana kaɗe jiki.
“Ni kam na tafi sai wata rana kuma”
Namra ta yi saurin riƙe mata hijabi.
“Haba Mardiya ki yi haƙuri mana, rashin fahimta ne kin ga ai ko kece ba zaki jidaɗi ba”
“Haka ne amman kin ga zama da rashin aminta da mutum ba daɗi, matsalar mijinki ma kawai ta isashe ki”
“Shine abunda ya fi damu na, yanzu ma wani maganin suka rubuta min, ina ganin sarƙa na zan siyar na haɗa da kuɗin da suke hannun dillaliya na siya masa maganin abunda ya rage mu siye abincin”
Gaban Mardiya yayi dakan uku-uku jin Namra ta ambaci zancen sarƙarta, take taji natsuwar dake tare da ita ta tafi. Sai ta tashi tana karkaɗe jiki
“Bari naje gida, daga can zan yi ma dillaliya magana nace kin dawo”
“Yauwa dan Allah ki faɗa mata, ai kin san inda ake sai da zinari ko?”
“Gaskiya ban sani ba, amman zan bincika miki”
“Yauwa na gode kin ci abinci ai ko?”
“Eh na ci, sai an jima”
Kamar walƙiya haka ta fice daga falon, zuciyarta kamar zata fito daga ƙirjinta saboda tsoron kar Namra ta nemi sarƙar ta, bata gani ba, kuma tasan ita kaɗai zata zarga tun da ita ta saba shigar mata ɗaki.
Bayan fitar Mardiya Namra ta tashi a gajiye ta shiga ɗakinta, tufafin jikinta ta cire ta ɗauki tawul ta ɗaura ta shiga wanka.
Ta daɗe tana wankan sannan ta fito cike da jindaɗin jikinta, ta buɗe lalulayen ɗakin kasancewar babu nepa, ta kwanta saman godon ba tare data saka wasu tufafin ba, saboda gajiya da kuma bachin dake cikin idonta. Nan da nan bachi yayi gaba da ita.
ANTY AMARYA POV.
“Nifa na damu da rashin kiran Namra, idan an kira ba a samu ita kuma bata kira, Allah dai yasa lafiya”
“Lafiya ƙalau Inshallah, kin san halin da Asim yake maybe ta siyar da wayar”
Cewar Hindatu tana dannar wayar dake hannunta.
“Amman kin san ba mu kyauta ba? Rashin sake zuwa duba shi da kuma kira a ji ya jikinsa? Ko a kan Namra ya kamata mu yi haka”
“Toh ai matsalan ba a samun wayarta”
“Ki je gidan su Asim gobe ko anjima ki karɓo min line sa, ko shi mu kira sai muyi magana da Namra ɗin”
“Amman ba Mamarsa taje Katsina ba?”
“Eh amman ai ba a rasa mai number ba a gidan”
“Zan je anjima inshallah”
Maryam dai na jinsu amman uffan bata ce ba, sai karatun ta take.
NAMRA POV.
Da ƙarfi taji tsawar mota a harabar gidan. Da gudu ta fito daga kitchen ta nufi gurin da motar take tsaye. Ga mamakinta sai ta ga Asim ya fito daga motar jikinsa ƙam kamar be taɓa ciwo ba, wani irin tsale ta daka ta dire saboda murna, tana shirin gudu izuwa gareshi sai kawai wasu karnuka suka taso ta bayansa suka yi cikinta suna ƙoƙarin cizonta.
Hakan be hana ta gudu da isa gare shi ba, ta rumgume shi, sai kawai taji ya ƙyalƙyale da dariya ya luma mata wata ƙatuwar wuƙa dake hannunsa. Wani irin ihu ta saka ihun da bata san har a fili tana yinsa ba. Kirgigi ta farka daga bachin tana wani irin haƙi da ambatar sunan mahallincinta.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, A'uzubillahi”
Har yanzu jikinta rawa yake, kanta sai rasawa yake, saboda mummunan mafarkin da tayi. Ta daɗe a haka sannan ta yi unƙurin tashi tana kallon agogon ɗakinta. Har biyu da rabi ta gota tana bachi bata yi Sallah.
Da sauri ta nufi banɗakin dan yin alwala, kamin ta ƙarasa ta tsaya cak, saboda abunda ta ji yana zubo mata daga ƙasanta zuwa ƙafafunta, dubarwa da zata yi sai ta ga jini sare-sare yana zuba kamar an tunkuɗo shi.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un”
Shi ne abunda ta furta da ƙarfi tana mai jin tsoron halin da take ciki, kamin ta ankaro ta soma jin wani irin mugun ciwon mara marar misaltuwa, a gurin ta zube tada dafe ƙasan marar nata dake mata wani irin mugun zugi.
Mulmula ta fara yi tana kuka, tawul ɗin dake jikinta ya kwance amman bata kula ba sai neman ceto take gashi gidan babu kowa.
Sai kusan biyar na yamma hankalinta ya dawo jikinta, har ta gane inda take kwance, gurin duk ya bace da jini, sai dai har yanzu mararta na mata ciwo da zuji ga wani uban nauyi da take jin cikinta yayi.
Daker ta unƙura ta shiga banɗakin, nan ma zubewa tayi ƙasa saboda rashin ƙarfin jiki, haka sare-saren jini ya riƙa fita daga cikinta tana kuka. Bata samu sassauci ba sai gaf da magariba, sannan ta samu ta tashi ta wanke jikinta ta gyara gurin cikin rashin kuzari ta dawo ɗakinta ta kwanta ƙasa idonta har wani lumshi suke.
Daker ta iya amsa sallamar da Mardiya da Dillaliya suke, sai dai bata iya tashi ba har Mardiya ta samu meta a gurin.
Yanayin yadda ta ga Namra yayi matuƙar ɗaga mata hankali, da sauri ta ƙarasa kusa da ita ta tashe ta zaune.
“Subhanallah, Namra me ya same ki?”
Cikin dauriya da ƙarfin hali Namra tayi mata magana.
“Jini ne yayi min zuba, kuma marana ciwo take sosai”
“Ko ki tashi muje asibiti?”
“Ba zan iya tafiya ba”
“Zan riƙa ki, tashi ki saka tufafin ki muje, kuma dillaliya tana falo tana jiran ki”
“Ki ce mata ta shigo”
Ta faɗa tana wani irin dantsar baki. Mardiya taje ta shigo da ita. A tsatsaye suka gaisa da ita ta miƙawa Namra kuɗin tana mata sannu.
“Allah ya sauwaƙe amman gara kuje asibiti, daman nace bari na kawo miki cikon kuɗin ne, inya so gobe sai na zo na kwashe kayan”
Kai kawai Namra ta iya ɗaga mata, ta juya ta fita tana mata Allah koro sauƙi.
Ƙyar idon Mardiya kan kuɗin da Dilalliyar ta bawa Namra. Namra ma bata kuɗin take ba ta lafiyar ta take.
“Ki tashi ki shirya bari naje na kira mai Napep”
“Amman za a same su da daren nan? Kin ga magariba tayi kar muje asibitin ba kowa”
“A'a Asibitin Malam Yakubu zamu nan kusa take kuma shi ko yaushe yana karɓar marar lafiya, musamman irin wannan”
Ta kai Hannu ta ɗauki kuɗin da suke gefen Namra ta saka cikin bed side drawer.
“Bari a aje kuɗin nan har mu dawo”
Bata tsaya jiran abunda Namra zata ƙara cewa ba, ta juya ta fita da sauri. Cikin ƙarfin hali Namra ta tashi ta saka pad ta zura doguwar riga, ta saka Hijabi ta fito falo ta zauna, yana sauraren yadda kanta ke tsarawa ga jikinta duk yayi mata babu daɗi.
Tana haka Mardiya ta dawo.
“Tashi muje gashi can ƙofar gida”
Ta riƙa suka fita tana mata sannu, a hankalin Namra take takawa kamar mai koyon tafiya har suka isa bakin gate ɗin, da taimakon Mardiya ta shiga Napep ɗin. Sannan Mardiya ta kalleta tace
“Ina Keys ɗin a rufe gidan?”
“Na manta shi yana can gefen dinning, dan Allah ki ɗauko min jaka na, ki ɗauko dubu biyar cikin kuɗin nan da Dillaliya ta kawo”
Da Tau ta amsa ta koma cikin gidan zuciyarta cike da saƙe-saƙe. Lokacin data shiga Kitchen ta fara shiga ta ɗauki ashana, sannan ta shiga ɗakin ta ɗauko jakar data san Namra na saka atm ɗinta, kuɗi da kuma wasu abubuwan a cikin sannan ta bude dorowar ta ɗauko kuɗin ta ciri kubu biyar ta saka a jakar Namra, sannan ta ɗauki sauran ta saka wata ƴar ƙaramar jaka dake jikinta mai kamar pose ɗin tsofi, sai ta warware zagenta ta ɗaga pant ɗinta sa saka jakar cikin pant ɗinta sannan ta ɗauki ɗankwalin Namra ta ƙyasta ashanar ta liƙa masa ta jefa saman gadonta.
Sai ta fito da sauri ta ɗauƙi keys ɗin ta rufe falo, sannan ta nufi gate gabanta na mugun faɗuwa ƙirjinta kamar zai fito.
Nan ma sai da ta tsaya ta rufe gate ɗin, sannan ta shiga Napep ɗin tana miƙawa Namra jakarta. Har mai Napep ɗin ta tashi Napep ya fara tafiya idon Mardiya yana kan gidan, zuciyarta cike da wasi-wasi. Namra kam idonta a lumshe yake ta jinginar da kanta jikin Mardiya tana yadda Mararta ke mata zugi.
KALSOOM POV.
Har ta isa gida tana tunanin abunda zata faɗawa iyayenta, taya zata iya faɗa musu dalilinta na dawowa gida? Bata samu mafita wata ƙarya da zata musu ba, hakan yasa taja bakinta tayi shiru duk juyin duniyar nan da Momi tayi akan Kalsoom ta faɗa mata dalilin na dawowa gida sai taƙi, bata ce shi yace ta dawo gida ba, kuma bata musu wata ƙaryar ba.
“Bari Dady kun ya dawo idan ni baki faɗa min ba, shi ai kya faɗa masa, haka kawai ki ɗauko akwati ziƙi-ziƙi ko kunya ki tafo gida, auren an samu daker anyi yanzu shine kike son ki kashe ko? Tau baki isa ba Wallahi”
Duk irin faɗan da Momi tayi Kalsoom bata yarda ta faɗa mata abunda ya faru ba, hakan yasa Momi kira Dad a waya ta labarta masa abunda yake faruwa. Cikin ƴan mintuna ya baro office ya dawo gida. Ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, ya rufe Kalsoom da faɗa akan ta faɗa masa dalilinta na dawowa gida amman ta ƙi.
Da kansa ya ɗaga waya ya kira Hilal yace yana nemansa, a lokacin Hilal yana tsakar aiki ne hakan yasa ya nemi Dad yayi masa lamani har zuwa dare.
Daren na yi sai gashi ya zo gidan, a nan ma yayi sallah isha'i, sai fira yake da Dad kamar Abbansa. Har suka shigo cikin falo sannan Dad yake tambayarsa ko akwai abunda ya shiga tsakanin su da Namra. Murmushi Hilal yayi ya wayance sosai kamar ba shi ba.
“Dad ni ai nayi mamakin da kace min Kalsoom ta zo gida ɗazu, dan gaskiya ni ban san wani rashin jituwa daya shiga tsakanin mu ba, sai dai ɗan abunda ba a rasa ba na kishi tsakanin ta da abokiyar zamanta, amman kasan rai ajizine ban sani ba ko nayi mata wani abun da ba zata iya faɗa min ba shiyasa ta kawo ƙarana”
Dad yaja tsaki yana girgiza kai irin nasu na manya.
“Kai sha'anin mata sai haƙuri, ni Wallahi na ɗauka wani abun akayi ma, babu yadda ba muyi ba amman yarinyar nan taƙi tayi magana”
Dad ya tashi ya shiga ciki gurin kiran Kalsoom. Hakan yasa Hilal gyara zamansa yana mai jindaɗin da Kalsoom bata faɗi abunda ya faru ba. Dad be daɗe ba sai gashi ya dawo falon tare da Kalsoom da Momi.
A kujera ɗaya ya zauna da Momi Kalsoom kuma ta zauna ƙasa kusa da Momi.
“Tau gashi nan shi dai yace be san wani abu ya shiga tsakanin su ba, ke sai ki faɗa idan akwai abunda yayi miki wanda be sani ba, ko kuma yayi miki shi cikin kuskure”
Ɗagowa tayi ta kalleshi, shi ma sai ya tsare ta da manyan idonsa, har sai da taji ba zata iya ɗaukat kallonsa ba, ta kawair da nata idon. A hankali ta kira sunan ta.
“Kalsoom, Dan Allah kiyi haƙuri ki yafe min, idan har akwai abunda nayi miki a cikin rashin sani ko da kuskure, koma da gangan kin san ɗan'adam aziji ne”
Ji tayi kamar yasa sarƙa ya ɗaure dukanin ilahirin jikinta, sai ta kasa sake ɗaga ido ta kalleshi, kuma ta kasa furta komai. Har Dad ya gama faɗansa da yake mata akan zamantakewar aure da haƙuri. Momi ma ta ɗora da nata sannan suka tashi suka basu guri.
Tasowa yayi daga inda yake zaune ya zauna ƙasa kusa da ita jikinsa na gogar nata, yasa hannunsa ya riƙe nata, fuskarsa kuma daf da nata ta yadda suna iya shaƙar numfashin juna.
“Babe tashi muje gida, na gode sosai da baki faɗawa Dad abunda ya faru”
“Ba zan iya bin ka gida ba, saboda ka riga ka furta duk ban biya ka ba, a bakin igiyar aurena”
“Kuskure na, na san nayi amman dan Allah ki yi, ba zan sake ba”
“Ni ba zan zauna ba, ai ka riga ka nuna kuɗin sun fi rayuwar aurena daraja”
“Shiiiiiiiiiii”
Ta ɗora lips ɗinsa saman nata, yana goga mata hancinsa.
“Ba haka nake nufi ba, zuciya na ne ya kawo har nayi wannan furucin kuma yanzu ina nadama”
Kawarda fuskarta tayi ta unƙura zata tashi, sai ya danneta da dukan ƙarfinsa.
“Don't try me, ba ki da wannan karfin bana son Dad da Mom su san halin da muke ciki, dan Allah Kalsoom kiyi haƙuri idan ma zuciyarki bata natsu ba, idan mun koma zaki iya biyana”
Be sake ta ba har sai da yawun bakinsu sukayi taraiya. Sannan ta tashi ta koma ciki, shi kuma ya fito waje yayi ma Dad sallama. Ita kuma ta ɗauko akwatinta ya karɓa ya saka a mota sannan suka tafi.
Tun da suka kamo hanya ta kalli inda take yake ba, idonta na kam gefen gilashin motar gurin ti-ti. Murmushi yayi ya kai hannu ya shafi fuskarta.
“Na san abunda na yi ban kyauta ba, amman dan Allah kiyi haƙuri, i love you so much”
Uffan bata ce masa ba, bata kuma sakar masa fuska ba, har suka isa gida. Shi kuma duk ya damu, wani irin sha'awarta yake jin tana masa yawo a jiki ga shi be ga alamun sauƙi a tare da ita ba.
Suna shiga cikin falon ta wuce ɗakin. Yayi kamar ya bita sai kuma wata zuciyar ta hana shi, sai kawai ya nufi ɗakin yaransa inda yake jin ihunsu. Da gudu suka zo suka rumgune shi.
“Eyyyy Daddy welcome”
Ɗaya bayan ɗaya ta riƙa shafa kansu, daga bisani ya kai hannu ya ɗauki Rafiq ya rumgume.
“Daddy Ammyn Rafiq ta fita wai gurin aikinta suna nemanta, tace mu zauna har ka dawo”
Ezzah ta faɗa tana wasa da ribon ɗin dake hannunta.
“Kuma tace idan ka tambaya mu faɗa maka ita ce ta ɗauki kuɗin dake cikin closet na ka”
Wani irin abun ɓacin rai ya taso yayi matsa tsaye a zuciya, yana auna irin rainin da Rashida tayi masa, taya zata fara yi masa abunda bata saba ba har tasa ya zargi Kalsoom.
Rufe ido yayi saboda wani mugun ɓaci rai da yaji ya rufe shi,
“Daddy are you okay?”
Yayi murmushin ƙarfin hali yana kallon Ezzah.
“I'm fine, Kuje ɗakin Anty ku ta dawo”
Da gudu suka nufi ɗakin suna ihu da murna.
Kamar zasu ɓalla ɗakin haka suka tura ƙofar ɗakin Kalsoom suka shiga suna mata sannu da zuwa. Yanayin yadda suka ga Kalsoom tayi musu da fuska yasa suka yi tsaye cirko-cirko suna kallonta.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Meaning of POV. Point of view: used especially in describing a method of shooting a scene or film that expresses the attitude of the director or writer toward the material or of a character in a scene.
*PAGE - 28*
NOT EDITED ⚠️
“Bana ce ku daina shiga ɗaki da gudu ba? Ban hana ku ban kar ƙofa ba? Sai kace ball”
Duk kama kunnensu suka yi kamar yadda ta koya musu.
“Auntie we sorry”
“Sorry for yourselves, aya kowa ya riƙe ƙafarsa ɗaya”
Duk dariya suka saka suka rumgume.
“Allah kuwa ba zamu sake ba, Auntie da baki nan Ulfah tace Dady ya siyo mata takeaway”
Ezzah ta faɗa tana zare idon, sai murƙususu take kamar ta shige jikin Kalsoom.
“Ke kuma kika yi faɗa da wata a School”
“Eyye 2+2 kowa taje ta kama ƙafarta na ce”
“A'a ai kince ba zaki sake mana horon dare ba, yau mun yi missing ɗin ki Auntie ina kika je?”
“Wani guri na je”
Ta faɗa tana jan hancin Ulfah, har ga Allah tana son yaran, haka take jin su kamar itace ta haifi su, sam basa sakewa da Mamarsu kamar yadda suke sakewa da ita, saboda ta kan basu lokacin ta.
“Aje a kwanta gobe akwai makaranta, kar a makara”
“Okay Auntie”
Duk kiss suka mata a gefen fuska sannan ta shafa kan su.
“Idan za a kwanta a yi alwalah, Ezzah ki yi addu'ah sai kiyi ma Ulfah, ke kuma Ulfah kiyi ma Rafiq, kuma zan shigo na ga wanda ya kwanta ba dai-dai gobe akwai kama ƙafa”
Ulfah ta tsuke baki ta girgiza kai
“A'a bana so yawunta be da tsarki”
Dariyar Hilal ce ta ɗago ta duka hankalinsu izuwa garesu, ashe yana tsaye jikin ƙofa yana kallon su.
Kalsoom ta ɗan sha masa mur, irin har yanzu fa fushi nake kai, ta kalli yaranta.
“Good night sweethearts”
“Good night Sweet Auntie”
“Ku saka kayan bachi, sauran ku watsar da wannan kayan idan kun cire”
Dariya kawai suka yi, suka je suka ma Daddyn u sai da safe suka fice. Shi kuma ya mai da ƙofar ɗakin ya rufe ya nufo ta yana murmushi.
“Yanzu shi kenan, daga fitar su sai kuma ki ɗaure min fuska, ni da su waya fi cancanta da far'ar nan naki?”
“Su kasan ana canja miji ba a canja ƴaƴa ba”
Dariya yayi ya rumgumota.
“Haba ni da nazo miki da albishir kuma”
Ta tsire baki tana ƙoƙarin zamewa daga jikinsa.
“Wallahi da gaske na ke, nayi shawara zan fara baki 50k duk month, tun da ita Rashida aiki take, ina ganin kamar ban yi adalci ba idan na bar ki haka”
“Dan Allah da gaske”
Ta tambaya cikin murna da jindaɗi, sai kawai ta saki jiki ta rumgume shi.
“Yauwa yanzu da kika ji maganar kuɗi sai na samu rumguma ko? Ko kunya baki ji ba”
Ta rufe kanta cikin ƙirjinsa tana dariya.
Duk wannan maganar da Hilal yake Rashida ya tsaye jikin ƙofa tana jinsa, wani ƙashin baƙinciki ne ya taso ya zo yayi mata tsaye a wuya, har ta kasa jurar tsayi a gurin ta wuce ɗakinta.
Har ta cire tufafin da suke jikinta, tsanar Kalsoom sai ƙaruwa yake a ranta, gani take duk ta zo cikin gida ta hana ta tsukuni ta ƙauce mata miji. Tawul ta ɗauka ta shiga bathdroom tayi wankan tsarki sannan tayi na sabulu ta ɗora da alwalah ta fito. Ta rama sallah magariba sannan ta yi na Isha'i.
Sai kusan goma saura Hilal ya leƙa ɗakinta. Ƙiri-ƙiri tayi kamar bata ganshi ba, ta cigaba da chatin ɗin da take a waya. Shi kuma ya tsaya a kanta.
“Bayan kin dawo aiki sai kika sake fita baki faɗa min”
“Amman ai kasan idan ba aiki ba, babu abunda zai sake fitar da ni ko? Kuma na ga kai ka bani damar nayi aikin, ita wacan da yake ƴar gatan ka ce ai sai ka hanka mata albashi tana zaune a gida ko?”
Murmushi yayi mai sauti.
“Kalsoom bata nufin komai dake sai alheri, ki duba kiga yadda take kula da yaran nan, ke kanki baki kula da su haka, a ganin ki kema kan ki be ci ace kin yanka mata albashi ba, naga ke kina aikin ai”
“Ƙwarai aikin kam yanzu na fara saboda abunda mahaifina ya koya min kenan, be nuna min na zauna a nema a bani ba nima na san Freedom ɗina”
“Good of you, amman idan har aikin yana da rana a gare ki be kamata ki saka hannu ki ɗaukar min dubu ɗari uku ba ba tare da sani ba, bayan kuma babu nauyin da ban ɗauke ba na cikin gidan nan, kin san iya abunda na aikata a rashin ganin kuɗin nan?”
Cikinsa tayi da masifa tana kuka.
“Ka yi min duk abunda zaka yi Hilal, ka kira ni da ko wane irin suna ka siffanta ni da duk sunan da yayi maka a duniyar nan, saboda kayi amarya, daman haka halin ku yake a duk lokacin da kuka aure mune abun wulaƙantawa, mune banza mune wofi”
Kallonta yake har ta gama faɗan ta koma gefen gado ta zauna tana cigaba da kuka. Sai ya sassauta zuciyarsa, duk wani abu da yake ji sai ya aje shi gefe, ya zauna kusa da ita ya jata ya rumgume.
“Bana da niyar wulaƙanta ki dan na yi aure Rashida, i love you so much”
Ƙara narkewa tayi.
“Hilal ina kishin ka, ina kishin ka kwana da wata Mace ba ni ba, Hilal i can't deny it and i can't take it, please divorce her Hilal”
“I can't and won't, ita amana iyayenta suka bani, son da nake miki ba zai sa na rabu da ita ba a kan ki, ke ma kuma ba zan miki haka ba, so karki yaudari kan ki”
Ganin ba zata daina kukan ba, yasa ya ɗaga ta ɗaga jikinsa, ya tashi cikin rashin daɗin rai ya nufi ɗakin Kalsoom.
NAMRA POV.
Sun yi sa'ar samun likitan har ya duba ta, ya sanar mata ciki ne amman ta samu miscarriage, ya rubuta mata gani da allurai sannan ya bata gado. Sai bata yarda ya kwanta ba sai tace mishi sai taje ya faɗawa mijinta. A cikin asibitin ta siye wasu maganin nikan.
A bakin gate ɗin suka samu Napep, Namra kamar jira take, suna shiga ta fara kuka. Ita sam bata jidaɗin ɓarewar cikin ba, gashi har yanzu zugi mararta take mata.
Ba karamin ƙarfin hali Mardiya tayi ba, wajen bata haƙuri dan ita gaba ɗaya hankalinta ya tattara ya koma gida, zuciyarta sai yaye yaye take mata. Ita kanta tana jin bata kyauta ba idan har gidan Namra ya ƙone, sai dai bata da mafita sai wannan.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ”
Ta furta a razane lokacin da mai Napep ya sauke su cikin jama'ar da suke gurin. Da sauri Namra ta buɗe idonta dake rufe ta fito daga Napep ɗin ta nufi gida a ruɗe.
Mardiya ce ta sallami mai Napep ɗin ta rufa mata baya, tana ta innalillahi. Haka Namra ta ƙira kusa mutane da suke tsastsaye suna kallon wutar, har ta shiga cikin gidan. Da sauri wani daga cikin yan fire service ya tare ta sai matan unguwar suka zo da gudu suka riƙe ta.
Wani irin fisge-fisge take take tana son ta kuɓuce ta shiga cikin wuta, sai ɗakinta take nuna musu tana wani irin kuka mai ban tausayi.
Wani irin tuma take tana direwa ƙasa, kamar sabuwar mahaukaciya. Sai kuma ta koma can gefe ta rumgume kanta, jikinta sai rawa yake kamar mai sabon fever.
“Allah na gode maka Allah, mijina ya kare, cikina ya ɓare yanzu kuma gidana ya ƙone, Allah ka sassauta min haka nan Allah, Allah ka yafe min na san ni mai yawan zunubi ce mai yawan saɓa maka Allah”
Wani irin ajiyar zuciya ta sauke sai jiri ya kwasheta, ta soma ganin mutane biyu-biyu sai ta jinginar da kanta, tana numfashi a hankali. Mardiya na can gefe tana kuka sosai, kamar gidan nata ne ya ƙone, idonta har ya kumbura ya daina hawaye.
Haka wutar ta ci ta cinye, ba a samu nasarar kasheta ba, sai da ta ƙone ilahirin gidan gaba ɗaya, ya rage saura BQ kawai. Har kuma lokacin Namra sama-sama take ganin mutane, komai ya zame mata kamar mafarki, yanzu kam bata da gabas bata da yamma, bata da madafa, bata da mafita sai ta Allah. Gashi babu abunda ya fita nata sai tufafin da suke jikinta.
A tunaninta kuɗin da Dillaliya ta kawo mata ya ƙone, ga sarƙarta ga tufafinta kayan ɗakinta da kayan kallo freezer da sauran kayan kitchen, yanzu bata da komai sai rai, gashi lafiyar jikinta ma bata isheta ba.
Mutane sun yi ta bata haƙuri suna nuna mata yarda da ƙaddara, da mata fatan Allah mai da alheri, a gidansu Mardiya ta kwana, ba kuma dan kwanan bachi ba, dan a zaune ta kwana, tana jinjina lamarin Ubangiji.
Da safe Mahaifiyar Mardiya ta siyo mata koko da ƙosai, Namra ta kasa sha, ta aika a siyo mata tea shima ta kasa sha. Sai tayi zaune jigum, tunani ya taru yayi mata tsaye a rai.
Tunanin yadda zatayi da Dillaliya, da kuma yadda zata faɗawa Asim gidansu ya ƙone, bata tunanin faɗawa Anty Amarya, saboda a ganinta sun juya mata baya, ita kuma ta ɗauki alƙawrin ba zata sake nuna musu tana buƙatar wani abu ba.
Sallamar Dillaliya sata ta razana sosai, kamar ance mata ga baƙon mutuwa. Sumi-sumi Dillaliya ta shigo ɗakin fuskarta ɗauke da damuwa da kuma tausayi.
“Allah sarki Baiwar Allah, haka Allah ka kawo miki wannan ƙaddarar ke kuma?”
Ta faɗa yayinda take ƙoƙarin zaunawa. Idon Namra ya cika da ƙwallah.
“Kin dai gani, duk abunda Allah ya kawo ba a iya guje mishi, Wallahi komai ya ƙone”
“Haka na ji ƴar nan, ai ni jikina duk yayi sanyi na haɗa ɗan jarin na miƙa miki har da kuɗin mutane gashi komai ya ƙone”
Ta fara hawaye. Dubu biyar ma Dillaliya jin su take kamar ranta balle har dubu ɗari uku da hansin.
“Ni ko yau ina zan samu wannan kuɗi, ba kaya ba kuɗi mutane ba haƙuri ne da su ba, yanzu wanda na karɓar wa kuɗin nan ba yafewa zata yi ba, nima ɗan jari masu son ganin baya na yau burinsu ya cika, na shiga uku na lalace”
Namra tayi mata wani kallo wanda ita ka ɗai ta san fassararsa.
“Allah satki Dillaliya, ke dubu ɗari uku kawai kika rasa, ni ko mijina ya karye cikina ya zube yanzu kuma gidan ya ƙone gaba ɗaya komai be fita ba, kuma yanzu ki zo kina min wannan maganar, ba sai kin yi lunƙe-lunƙe ba, ki kwantar da hankalin ki zan biya ki, sisinki ba zata yi ciwon kai ba Inshallah”
Namra ta ƙarasa maganar da kuka. Wani daɗi da Kunya ya lulluɓe Dillaliya a lokaci ɗaya, daman ita tana ganin alamu tasan Namra ƴar masu kuɗi ce, kuma haka da Namra tace ya ƙara tabbatar mata da zancenta. Sumi-sumi ta tashi tana share hawaye.
“Ba haka bane ƴar nan, Allah dai ya sassauta miki amman ba shine nufi na ba”
Tana ficewa Namra ta rafka uban tagumi tana tunanin rayuwarta. Babu wanda ta faɗo mata a rai sai Hajiya Saratu matar data taimaketa lokacin da Asim be da lafiya, sai dai zuciyarta bata yarda da zata taimaketa dan Allah ba. A ɗayan ɓangare na zuciyarta kuma Anty Amarya take tunani, su biyu nan sune kawai mafitar ta a rayuwa.
KALSOOM POV.
Kwana biyu nan ta miƙa lamarinta ga Ubangiji, nafila dare da Karatun suratul yaseen da Salma ta faɗa mata shi kawai ta sawa gaba.
Yau ma da wuri ta tashi ta shirya musu komai na karya. Amman Rashida bata tsaya karyawa ta fice, yara kuma tasa musu nasu a kula suka tafi makaranta.
Sai da ta sawa Hilal ruwan wanka yayi wanka sannan suka fito dinning sai tsokanarta yake.
“Ni duk gajiyar da ni, sai fama nake, Allah dai yasa ina da juriya ba zan iya zama da ke ba”
Ya kashe mata ido ɗaya, yana ƙoƙarin zaunawa saman kujera. Ita kam ido ta sakar masa tana kallon ikon Allah, daman yasan abunda zata faɗa ne shine ya rigata faɗa.
“Kai dai Allah be raba ka da abun magana ba”
“Ba wani magana sai gaskiya kema ai kin san ina ƙoƙari in ba haka ba ai sai abun yayi min yawa”
Dariya kawai tayi ta cigaba da haɗa masa tea. Shi kuma ya kwantar da kai yana kallon rigar bachinta dake buɗe.
Tana gama haɗa masa tea aka buga ƙofar falo, saurin miƙewa yayi yana faɗin bari na duba, dan nasan ki da shegen salo zaki iya cewa bari ki duba, har wani yaga halalina.
Kai kawai ta girgiza tana dariya, shima dariyar yake har ya isa gaban ƙofar ya buɗe.
Mai Gadi ne jikin ƙofar riƙe da wani farin abu kamar wasiƙa, ya miƙawa Hilal.
“Alhaji, gashi aka ce a bawa Auntie su Ulfah”
“Waya kawo?”
Doc. Ya karɓa yana tambaya.
“Wani ne a mota har ya tafi ma”
“Okay”
Ya mai da ƙofar ya rufe. Sannan ya juyo ya nufo dinning inda take Kalsoom take zaune yana faɗin.
“Ga saƙo aka ce a baki”
“Saƙon me?”
“Oho sai kin buɗe”
Sai da ya zauna sannan ya miƙa mata. Ita kuma ta karɓa da hannu biyu, ba tare da fargabar komai ba ta yage takardar.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Da sauri ta miƙe tsaye tana zaro ido, sai hotuna suka faɗo tare da kofin tea dake gabanta.
“Subhanallah”
Hilal ya faɗa lokacin da idonsa ya sauka kan hotunan.
____________________________________________
#Share
#Comment
#Candy
#Blog
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 29*
NOT EDITED ⚠️
Shiru-shiru Mama bata aga an kawo musu karin safe ba, gashi har rana tayi kuma babu wani labari, ga yunwa tana ji ita da Asim.
Dan yauzu sauki ya fara zo masa yana son abinci sosai har fira ya kan yi sama-sama.
“Hajara tashi na baki kuɗin achaɓa ke je ki karɓa mana abinci wata ƙila na yanzu zata zo ba,marar lafiya kuma sai da abinci, wannan zunzunzun ba amo ba labari,
Ko tana nufin ba zata ake zuwa asibitin bane dan nayi magana?”
Ta ciro naira hansi ta miƙawa ƴarta Hajara.
“Ungo idan kin je ta baki na dawowa”
Da kallo Asim.ya bi ƙanwar tasa, sai da ta fice sannan ya kalli Mama yace
“Wallahi ko maƙiyinka ya faɗa a hali dana shiga sai an tausaya masa, ki duba ki gani ace ina sirikin su amman har yanzu ba su sake zuwa duba ni ba, ai ko wani na kashe musu sa duba ni tun da ƴar su nake aure”
“Hmmm ai Wallahi mutane nan basa son ka da alheri, su fa basu ƙi ka mutu ba, nifa ina zargin kamar ma da sa hannunsu a haɗarin nan da kayi”
“Nima haka nake tunani saboda lokacin dana je karɓar motar sai da suka sa Direban su, ya duba motar gaba da baya sannan aka ba ni key ɗin, sannan idan har ba plan ba taya daga haɗari mota zata kama da wuta haka kawai”
“Ato nifa na faɗa maka ba su ƙi ka mutu ba, sai ƴarsu ta auri wanda take so, daman can ba a banza aka baka ita ba”
“Amman Namra sai naga kamar tsakani da Allah take so na”
“Hmm ai wannan hidumar da tayi maka, saboda itace silar komai shiyasa tayi maka, kuma yanzu kaga ta kama kayan ɗakinta ta sai da dan ace kai ƙa canye komai sai a fara cewa ta sai da komai dalilinka, ai ba zata rasa kuɗin da za'a maka komai a bankinta ba amman ta zaɓi ta siyar da kayan ɗakinta ai kasan da walakin goro a miya”
“Kayan ɗakinta ta siyar?”
Ya tambaya a wahale dan ciwon kan ya fara dawo masa.
“Eh ba shine ka ji jiya ina magana ba, har kake ganin laifina”
Shiru yayi be sake magana ba, sai ciwon kan yake saurare.
NAMRA POV.
Ta ci kuka sosai har sai da ta goɗe Allah, ba tare da ta bari kowa ya gani ba, dan wuni tayi a ɗakin su Mardiya, duk wanda ya zo mata tanzanko sai yayi mata a cikin ɗakin ko kuma daga bakin ƙofar.
Guraren Uku da rabi Hajara ta shigo ɗakin da sallama, Namra ta amsa mata murya can ƙasa-ƙasa.
“Wa'alaikissalam Hajara”
“Na'am Anty naje gidan naga duk ya ƙone aka ce min kina nan”
“Wallahi jiya ne muna dawowa daga asibiti muka tarar ana kashe wutar”
“O'o wannan abun be yi daɗi ba, nima Mamace tace na zo na karɓo abinci tun safe bata gan ki ba shiru, ashe abunda ya faru kenan, Wallahi ba mu sani ba”
Ta faɗa cike da tausayawa.
“Ina Asim ɗin yaji sauƙi?”
“Ya samu sauƙi sosai ɗazu ma har fira muke yi da shi, har shi ma yace na zo na karɓa abincin”
“Bari na baki ƙuɗi ki siya masa na hanya”
Ta tashi cikin rashin kuzari, suka fita a tare daga cikin ɗakin. Kular Maman Mardiya ta ara tana cikin wanke wa, wata maƙociyar su ta shigo tace kiran Namra.
“Kin yi baki masu gida sun zo su duba gidan su”
A take ta aje wankin kular da take ta gyara tsayin Hijabinta ta fita. Manyan motoci ne fake a ƙofar gidan.
Cikin faɗuwar gaba ta nitsa ta shiga cikin gidan tana musu sallama.
“Wa'alaikissalam ke ce matar gidan?”
Hajiyar ta tambaya tana cire gilashin dake zaune a idonta.
“Eh Nice ance masu gida sun zo”
“Eh ina mai gidan na ki?”
“Yana asibiti ba shi da lafiya ne”
“Ayyah so sorry, amman kin san musabbabin tashin wutar ne?”
“A'a wallahi nima asibiti naje ko da na dawo na tarar wuta na ci”
“Allah sarki Allah ya maida alheri, daman mun zo ne mu duba ance muna anyi wuta”
Ta faɗa tana picking ɗin wayar dake hannunta.
“I'm my way Abdool, har na ga gidan ma”
Sai kuma tayi dariya, ta kashe wayar. Tasa hannu a jaka ta ɗauko kuɗi masu ɗan dama ta miƙawa Namra.
“Ga wannan Allah ya tsare gaba”
Har ƙasa Namra ta ɗuka mata.
“Na gode Allah saka miki da alheri”
Murmushi farar Hajiyar tayi
“Ba komai”
Har gaban mota Namra ta raƙa ta ta shiga motar ta wuce, sannan Namra ta koma gidan ta ɗauki kular da plates da cibi, suka fito ita da Hajara.
A bakin titi ta siya musu shinkafa da miya da nama na 1k. Sannan suka tari Napep suka hau.
Daga ita har Hajara sululu suka shiga ɗakin, kama kamar ita dake ta sun-sun da kai bata son a ga kumburin dake fuskarta.
Sai da ta gaisa da Mama sannan ta nufi gurin da Asim yake ta zauna, yana kallonta.
“Ya jikin ka?”
“Alhamdulillah”
“Likitan ya duba...”
Jin abunda Hajara take faɗa yasa ta kasa ƙarasawa. Mama ta ɗora hannu a ka, tana faɗin
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Asim kuma ya kalli Namra cike da tashin hankali. Ita kuma babu abunda take sai kuka.
“We lost everything Asim, i lost my baby, shine naje asibiti ko da na dawo na tarar gidan ya ƙone”
Rumtse ido Asim yayi, zuciyaraa ɗauke da abubuwa biyu, jindaɗin ɓarin da tayi, da kuma baƙincikin ƙonewar da gidan yayi.
Ringing ɗin wayar Asim dake hannun Mama ne yasa ta share munafukan hawayenta ta danna picking tana kara wayar a kunne.
“Wa'alaikissalam.
Lafiya ƙalau
Alhamdulillah”
Shiru ta ɗan yi kamin tace
“Allah sarki. Namra karɓi ga Maman ki”
Hannu Namra ta kai ta karɓa sai ta fice daga ɗakin. Mama ta kalli Asim cikin ruɗu tace
“Ibrahim idan kaji sauƙi ka rabu da yarinyar nan, ina ganin babu alheri a zaman auren ku, wannan irin bala'i haka”
Shi dai be ce mata komai ba, shi ta kansa yake abunda duk yake tunanin zai zame masa alheri yana ƙoƙarin koma masa sheri.
Yanzu da wannen zai ji ciwon jikinsa ko wannan rashin da suka yi?
“Kuma ina ganin abunda yafi kawai ku koma gida, a can ma dole ta samu wani abu saboda a gaban iyayenta take”
Har lokacin be ce komai ba, Hajara tace
“Ni Wallahi duk ta bani tausayi”
“Ai ba itace abun tausayi ba, Yayanki ne shi da ba shi da kowa sai Allah ita kau har iyayenta suna da abun hannun su”
“Ita ai da tausayi Wallahi”
“Hmmm Allah dai ya kyauta kawai”
Namra na fita ta ƙara wayar a kunne tana dda ƙoƙarin gyara muryarta kar Anty Amarya ta gane tana cikin damuwa.
“Anty”
“Na'am Namra y jikin mijin na ki”
“Ya ji sauƙi”
“Allah ƙara lafiya Wallahi Abbah kin ya hana na dawo duba shi, ko jiya sai da nayi masa magana sai ma masifa ya riga min, Abban ki ya kira ki?”
“Ba komai ai yaji sauƙi, be kira ni ba wayana ya faɗi ban sani ba ko ya kira”
“Har yanzu baki daina halin ki na sakarci ba ko? Ya faɗi ko dai kin siyar?”
“Wallahi faɗuwa yayi”
“Namra ki yi hankali da mutane, ba kowa ne yake son ya gan ka a cikin alheri ba, wani yana baƙincikin yaga kana jindaɗi, wasu fa hassadarsu ba ƙarama bace, kowa abunda yake ƙoƙarin yi ya ture ka daga jindaɗin shi ya shiga, ko kuma ya ture ka duk ku rasa, ba kowa bane zai so ki tsakani da Allah ba, idan kina da shi kowa naki ne, sai ranar da kika rasa komai zaki gane masu son ki da gaskiya
Wani ƙiyayyar tasa a ɓoye take ba zaki taɓa ganewa ba, haka zai ta miki zagon ƙasa har sai ya ga kin rasa komai sannan hankalinsa ya kwanta, dan haka kiyi tunani sosai da duniya, idan baki da hankali mutanen duniya za su miki shi, ki rage damuwa a ran ki ki sawa ran ki sassauci”
“Na gode Anty”
Ta faɗa har cikin ranta, kalaman Anty sun mata daɗi, sai dai tasan ba kowa Anty ke nuna mata ba, sai Asim dan tana tunanin kamar da biyu ya aureta, gani take har yanzu Anty bata yarda da Asim ba.
“Allah ya ƙara masa lafiya, na kira wayarki ban samu ba, shine Maryam ta karɓo min number Asim”
“Eh ai naga line Maryam ne, na gode sosai”
“Tau Sai anjima”
“Okay
Daga haka suka yi sallama. Wayar na yankewa wa Namra ta tsara text ta tura mata Anty Amarya a wayar Maryam.
“Maryam... Zo ki karɓi wayar ki”
“Na'am”
Ta aje system dake jikinta, ta taso ta nufo ɗayan ɓangaren inda Anty Amarya take. Tana karɓar wayar text na shigo, Anty Amarya bata kula ba, ta miƙa mata wayar ta nufi gurin sha'aninta.
_Anty ina cikin matsala, bana iya faɗa miki a waya nasan faɗa zaki min, dan Allah ki taimaka min da kuɗi ko kaɗan ne_
Maryam ya gama karanta saƙon taja wani dogon tsaki ta danna deleted ta goge saƙon.
“Ai fa kullum haka zai riƙa saki kina yi, tun da yaga be samu abunda yake so ba, kai mutanen duniya nan da abun haushi da mamaki suke, ala dole dan auri yar masu kuɗi kai sai kayi arziki, to sai kaje ka ci ubanka, ya mayar da ita saniyar tatsa”
Ta koma mazauninta tana mai jin haushi Namra da Asim ɗin.
KALSOOM POV.
Hilal na kallonta ta girgiza masa idonta da hawaye.
“Wallahi ban aikata ba, ban san wannan mutumen ba Wallahi”
Hannu Hilal ya kai ya ɗauki hotunan yana kallo. A-uzubillah hotunan babu kyau kallo, Kalsoom ce tsirara ita da wani, wani gurin yana kissing ɗinta wani gurin kuma tana kissing ɗinsa.
Ɗaya bayan ɗaya ya riƙa duba hotunan har ya gama sannan ya kalleta yace
“Kin san wannan mutumen”
“Wallahi ban san shi ba, ban taɓa ganinsa ba”
Ta faɗa da kuka.
“Daga ganin wannan ma ai haɗi ne, i trust my wife's ba zaki aikata irin wannan abun ba, duk yadda akayi wannan abun shirya sa akayi”
Ta ƙara fashewa da kuka
“Wallahi sheri ne kawai, na rantse da Allah ban taɓa ganin wannan mutumen ba”
Shiru Hilal yayi kamar mai nazari.
“Ina suka samu hoton ki?”
“Wallahi ban sani ba, dan Allah ka yarda da ni Wallahi sheri ne”
“Na yarda sheri ne, daga gani ma ai kasan haɗi ne, daɓ ga fatar fuskar ta banbanta dana jikin hoton, kuma miyasa ba a kawo lokacin da bana nan ba, sai da ina nan? za a iya haɗa irin wannan hoton a computer? But i can't believe is taya suka samu hoton ki?”
“Wallahi ban sani ba”
“Baki sani ba kamar ya? What kind of nonsense is this? Aljani za a turo ya ɗauki hoton ki ko me?”
Durƙushewa tayi ƙasa tana kuka.
“Wallahi ban sani ba Hilal na rantse da Allah ban aikata ba”
“Naji baki aikata ba, faɗa min ta ina suka aka samu hoton ki?”
Ya faɗa a tsawace irin zuciyarsa ta fara kawowa ɗin nan.
“Wallahi ban sani ba, ni ban turawa kowa hotona ba”
Ɗuƙawa yayi a hasale ya kwashe hotunan ya nufi ɗakinsa da su. Wani irin zugi zuciyarsa ke masa, baƙin kishi ya taso masa.
Haka ya tiƙa duba hotunan kamar wanda zai haddace su, shi dai what he believe Kalsoom ba zata aikata haka ba, sai dai kuma kansa ya ɗaure har yana jin tunaninsa na ƙoƙarin canjawa.
Bedside drawer sa ya buɗe ya zuba hotunan ya rufe, sannan Shirya cikin ƙananan kaya ya feshe jikinsa da turare ya ɗauki atms ɗinsa ya saka a aljihu da wasu ƴan canja, sannan ya ɗauki wayarsa da keys, ya fice daga ɗakin fuska babu annuri.
Sheshekar kukanta ya ɗago da hankalinsa i zuwa gareta, ashe duk tsawon lokacin tana a gurin tana aikin kuka, jikinsa ya mutu yaji ba daɗi ganin kamar shine silar hawayenta. Ƙarasawa yayi kusa da ita ya ɗafa ta
“Kalsoom Calm down, nima fa wayayyen mutum ne nasan za a iya haɗa wannan, amman kin ƙi ki bawa zuciyata damar yarda da hakan”
Ɗagowa tayi ta kalleshi tana kuka fuskarta da majina nashe-nashe.
“Wallahi ban sani ba, ni ban turawa kowa hoto na ba”
“Kina da grp ɗin da kika chat da maza ko?”
Ta ɗanyi shiru tana tunani.
“Grp ɗaya ne, shima kuma na koyon sana'ah ne, kuma ban taɓa magana a grp ɗin ba Wallahi, Instagram ɗina da Facebook tun da nayi aure ban sake hawan ko ɗaya ba Wallahi”
“Good indeed, kina instagram ba? Kina facebook?”
“Amman tun da nayi aure ban sake shiga ba”
Zaunawa yayi kusa da ita yana cire password ɗin wayarsa.
“Ba ni handle ɗin ki”
“Kalsoom_Miss-Arewa”
Instagram ya shiga yayi searching sunanta, sai ga account ɗinta. Yadda ya riƙa ganin hotunan ta sai wani baƙin kishi ya motsa masa.
“Duba nan, yanzu miye amfanin waɗannan hotunan? Kina tallar kan ki kamar ba mace ba, miye abun burgewa a sakin jiki wasu mazan na kallo, ke a ɗaukar ki duk wayewa ce ko? Dole ne sai kin sa hotunan ki a instagram ko facebook?”
“Wallahi ni ba da wata manufar na yi ba”
“Nasan ba wata manufar kika yi ba, su yanzu waɗanda suke da wata manufar ai sun ɗauka sun yi yadda suke so da shi. Duk abunda addini yake hana ƙu baku ganewa, duk abunda kika ga musulunci yace a bar shi barin shi yafi alheri amman baku ganewa, dubi wannan abun wani gurin ma ai rabin jikin ki a waje, ba editing kaɗai ba har asiri sai a ɗauki hoton ki ta nan aje a miki”
Yaja tsaki yana mai miƙewa tsaye.
“Kamin na dawo ki tabbatar kin goge duka hotunan ki da suke facebook da Instagram, ban hana ki yin chat ba amman ban yafe ki yi da wani namiji ba da aurena, duk mazan nan nan friends ɗin ki yi unfriend ɗin su, kuma Wallahi kar na sake ganin hoton ki a social network”
“Wallahi ni daga yau ma na daina chat ɗin gaba ɗaya, amman ka yarda da ni dan Allah”
“Idan ban yarda da ke ba, zan zauna ina magana da ke haka? Very soon an gano wanda yayi wannan abun, akwai mai son shiga tsakanin mu ne”
Gabansa ta dawo ta risina ta riƙe ƙafafunsa.
“Na gode Allah ya saka mana”
Ɗagota yayi ya rumgume. Zuciyarsa cike da kishin hotunan can daya kalla, duk da yasan cewar ba haɗi ne amman yana kishin hakan.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 30*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan ƙuɗin da suka mata saura a jakarta, da kuma dubu ashirin ɗin nan Hajiyar gidan ta bata, su ne take ta maneji ta su tana siyen abinci.
A kullum gidan su Mardiya take kwana, wani lokacin har zanenta take ɗaurawa, kamin ta ɗinka kala biyar a cikin kuɗin. Tayi ta zuba ido tana jiran kuɗin Anty Amarya har ta gaji, tun tana sa ran zata ta kira wayar har ta gaji da jiran ta fara tunanin wata mafitar.
Da ta fito daga gida kai tsaye ta nufi gidansu Hajiya Saratu, har ta isa zuciyarta na nuna mata illar abunda zata yi, ko ba komai zai nisanta ta da Ubangijinta, sannan duk wanda yasan abunda ta aikata mutuncinta zai zube a idonsa, ashe Allah zai jarrabeta da wani matsi har kuma ta nemi tsaɓa masa, idan har ta yi haka bata kasance cikin nagartaccin bayi ba.
Juyar da fuskarta tayi gefen ti-ti tana kallon motocin dake kai da kawo, hawaye na silalawo daga idonta, wani bangare na zuciyar yana ƙoƙarin rinjayarta akan idan har ba ita ba, bata da wata mafita, babu kuma wanda zai taimake ta sai ita. Haka ko wane bawa zuciyarsa take nasalta masa alheri da sheri duk ɓangaren daya rinjaye ka shi zaka aikata.
Hannu ta kai ta share hawayenta, tana mai jin ƙyamar abun a ranta, yanzu idan taje garin aikata ta mutu fa? Me zata cewa Allah? Haƙiƙa an jarrabi wasu gabaninta da suka yi haƙuri kuma sai Allah yayi musu mafita, kuma bayan ita za a jarrabi wasu a bayanta, haka Ubangiji yake jarraba bayinsa dan ya auna imaninsu da kuma yarda da ƙaddara.
“Haƙiƙa za mu jarrabe ku da wani abu na tsoro da yunwa da tawayar dukiyoyi da rayuka, da ƴaƴan itatuwa , ka yi albishir ga masu haƙuri (Wajen jure waɗannan jarabce-jarabcen) Waɗanda idan masifa ta same su sai su ce INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN ma'ana :- mu ga Allah muka fito kuma a gare shi za a maiyardar mu. Wanɗannan gafara da kyakkayawan yabo daga Ubangijinsu sun tabbata gare su, da rahama kuma waɗannan sune shiryayyu.” (Baƙara: 155-157)
Tuna waɗannan ayoyin ya ankarar da ita abubuwan data manta, ji tayi kamar an tsikareta, gashin jikinta ya tashi, a nan ta soma tambayar kanta, dan me zata yarda zuciyarta ta rinjayeta ta tsaɓi Ubangijinta? Ta fita daga waɗancan bayin da Allah ke yabo? Ashe Ubangijinta be mata dukan gata ba? Ashe daman Imaninta ƙanƙane ne?
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ta furta a fili, har sai da mai Napep ɗin ya kalleta.
“Hajiya lafiya dai?”
“Lafiya ƙalau dan Allah juya da ni ka kai ni babbar Asibiti”
“To amman fa wasu kuɗin zaki sake biya”
“Na ji mu tafi”
“Tau Hajiya lafiya kike kuka?”
Sai a lokacin ta tuna da hawayen dake fuskarta, sa sauri ta share hawayen ba tare data ce masa komai ba har suka isa asibitin, sannan ta fita ta ciro kuɗinsa ta ba shi.
Ko da ta shiga cikin ɗakin Asim na zaune, kamsa ya kumbura sosai har idonsa ɗaya ya liƙe, hankalinta ya tashi dan yanzu wannan kumburin ya fi na jiya.
Kusa da shi ta zauna zuciyarta cike da tausayinsa, har idaniyarta na ƙoƙarin zubar masa da ƙwalla.
“Asim kaga har yanzu Anty bata kira ba, kuma bata aiko ba, ni kuma bana da wata mafitar, ga kuɗi da ake bina ma ban san yadda zan yi ba, wannan kumburin naka yana tsorata ni”
Ya matse ƙallah data cika masa ido.
“Namra ko gida za mu koma ne?”
“Idan mun koma za su ce mun kwaso ciwo mun dawo”
“Likita yace idan ba allura nan aka min ba yana da wahala naji sauƙi da wuri”
Hannayenta tasa ta rumgume shi tana kuka. Shi kuma a take yaji sha'awarta ta saukar masa, ya kai hannu yana ɗan shafa ta. Data anƙaro da abunda yake nufi da ita sai tayi saurin ɗagowa daga jikinsa.
“Ina Mama?”
“Tana waje”
Ya sake miƙa hannu yana shafa fuskarta, yana ƙoƙarin ɗaga hijabinta ya zura ɗayan hannunsa ciki.
“Asim asibiti muke fa, kuma dubi halin da kake ciki”
Yawun bakinsa ya haɗe, ba tare daya daina abunda yake mata ba. Ana taɓa ƙofar ɗakin tayi saurin tashi tsaye, shi kuma ya bita da kallo idonsa har sun fara canja kala.
“Mama ina wuni?”
“Lafiya ƙalau ya rana?”
“Alhamdulillah”
Ta ɗan kalleshi cike da kunya, dan gani take kamar Mama ta lura da abunda suke.
“Bari naje gurin Hajara”
Bata jira abunda zai ce ba ta fice. Sai Mama ta zauna a kujerar dake kusa da Asim tana faɗin
“Lamarin nan naka fa ƙaruwa kawai yake yi”
“Tau Mama nayi maganar kuɗin adashen nan kin kawo wasu hujjoji na daban, ko mutuwa na yi ai ke kika rasa ni tun da su ƴar su wani zata aura”
“Shawara da nake kenan a zuciyana, zan je nayi mata bayani sai na karɓo kuɗin daman dubu ɗari uku ne, idan Allah yasa ka samu sauƙi sai a shiga wani kuma”
“Haka yafi, tun da kin ga har yanzu basu saje kira ba ma balle su aiko. Yaushe zaki je?”
“Gobe nake son naje, nima kuɗin da suke hannun na duk sun tafi gurin siyen abinci, ga tufafin nan ƙala ɗaya kullum ƙara naje ya ɗauko wasu tun da waɗanda muka zo da su sun ƙone, da Hajara zan koma in yaso sai na dawo ni kaɗai, daman Haruna ya matsa da maganar yaushe zata dawo”
“Ni Wallahi inda da hali ma da kin tafi yanzu, sai ki dawo gobe da wuri, dan ni kaɗai na san halin da nake ciki, kuma kin ga yanzu aka yi ƙarfe ɗaya, nasan zuwa yamma kin isa”
Ta ɗan yi shiru tana nazari.
“Rana be yi ba?”
“Be yi ba Wallahi, tun da kin ga ma Namra ta zo sai ta zauna nan har ki dawo”
“Tau bari na gani, ai duk na natse ma da wannan kumburin na ka”
Ta tashi ta fita cikin yanayin damuwa. Wayar Asim dake hannun Hajara Namra ta karɓa, ta saka number Babban Yayansu ɗan Hajiya Barau, sai ta matsa can nesa da Hajara ta kira shi.
KALSOOM POV.
Ba itace da girkin ba, amman sanin halin Rashida yasa bata tsaya jiranta ba ta shiga kitchen ta ɗora musu breakfast, daman wani lokacin ita take shirya musu tun da Rashida aiki take zuwa.
Sai da ta shirya komai, na karyawa sannan ta ɗauko kulolin su ta zuba musu abincin su, sannan ta kira su ɗaya bayan ɗaya ta miƙa musu kulolin.
“Ku je gurin mota zan tashi Daddyn ku yanzu”
Ta nufi ɗakinsa, tana buɗe maɓallan rigar bachin ta. A tsakiyar gado yake kwance yana lulluɓe irin yana jin tsayi ɗin nan.
Air conditioner ta fara kashewa sannan ta nufi window ta buɗe su duka ta ɗage labulayen sannan ta nufo inda yake kwance ta yaye bedsheet ɗin tana taɓa masa kunne.
“Likita tashi safiya yayi fa”
Hannu ya kai ya janyo ta saman gadon ya rumgume ta
“Ban gaji da bachi ba”
“Yara suna gurin mota suna jiran ka”
“Ya salam”
Ya ƙara rumgume ta tsamtsam ƙirjinsa, kamar ba zai tashi ba, sai faman lumshe ido yake alamar bachi na masa daɗi.
“Doc. Doc. Doc”
Shiru be motsa bama balle ya amsa ta, hannu ta kai ta murɗa masa kunne, har sai da tayi ƙara ya kama hannunta ya ciza sannan ya tashi, yana jan kitson ta.
“I hate dis Morning”
“Really”
Ta tsire baki tana koyonsa.
“I hate dis Morning”
Ya zare ido, lokacin da idonsa suka kai kan ƙirjinta.
“Wow”
Ya kai hannu zai taɓa ta, ta fisgi kanta cikin zafin nama, ta sauka saman gado ta fice daga ɗakin tana masa dariya.
Tashi yayi ya shiga bathroom ya wanke bakinsa da fuskarsa sannan ya fito ya kai yaran makaranta. Ko da ya dawo babu kowa falo, sai kawai ya nufi ɗakin Rashida dan yaga motarta waje alamar yau bata fita da wuri ba kenan.
Tana ganin ya shigo ta juya kwancinta ta bashi baya. Hakan be da me shi sai ma dariya da yayi ya ƙarasa kusa da ita ya juyo da ita, hawayen daya gani a idonta ya tashi hankalinsa.
“Lafiya Pyar?”
“Bana jindaɗi ne”
“Me ke damun ki”
“Nima ban sani ba”
“Amman miyasa baki faɗa min ba?”
“Taya zan faɗa maka bayan ta shiga haƙƙina taje ta tashe ka, kuma ta san yau ba girkin ta bane”
“Ta riga ta saba ne, saboda kina fita sa sassafe ba tare da kin damu da tashi na ba, balle haɗa mana abun karyawa”
“Ni gaskiya ta daina shiga min haƙƙi bana so”
“Shikenan zan mata magana, amman yanzu faɗa min me kike ji yana damun ki”
“Fever, sneeze, headache and nauseous”
“Zan diɓi jininki da fitsari idan zan fita, yanzu tashi mu karya sai ki sha magana”
Ta ƙara manne masa a jiki.
“A'a ni bana so cin komai”
“Tea fa?”
“Sai dai idan kai zaka haɗa min da kan ka”
“Yes ni zan haɗa miki ai”
Ya faɗa yana murmushi, sannan ya tashi ya fice. Ajiyar zuciya Rashida ta sauke, ranta yana mata ba daɗi, idan har zarginta ya tabbata gasjiyar tana da ciki, tana cikin matsala dan bata iya tantance na waye ne,
‘Taya wani zai gane idan ba ni ma faɗa ba?’
Tambayar da tazo mata kenan a zuciyarta, sai kawai ta tashi ta shiga banɗaki.
Hilal sai da ya shiga ɗakinsa ya ɗauko maganinka sannan ya nufo ɗakin Kalsoom, a lokacin tana zaune gaban madubi tana shiryawa dan fitowarta daga wanka kenan.
Daga bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yace
“Wifey Yau madam babu lafiya, ba zata fito ba tea kawai zata sha, ni ma kuma bana jin cin komai”
Kai ta ɗaga masa tayi murmushin da be kai zuci ba. Har ya wuce, sai kuma ya dawo ya tsaya bakin ƙofar ya miƙa mata hannu.
“Taso na haɗa miki breakfast”
Ba musu ta taso ta miƙa masa hannun ba dan ranta na mata daɗi ba. A kujerar data saba zama ya zaunar da ita, ya ɗauki kofi biyu ya haɗa tea, ya aje mata ɗaya gabanta ya zuba mata ƙwai da sauran abubuwan da suke gurin, sannan yaƴi mata kiss ya ɗauki tea ɗin ya nufi ɗakin Rashida.
Da kallo ta bishi, zuciyarta na sosuwa da lamarinsa, tabbas yana son matarsa fiye da yadda yake son kansa, yanzu ya kasa karyawa saboda bata da lafiya, ta lura da yadda yanayinsa ya canja a take, taya zata shiga rayuwar irin waɗannan ma'auratan sannan tace zata samu farinciki?
Hannu ta kai ta shafa cikinta, hawaye masu zafi suka silalo daga idonta.
Sai da ya bata tea ɗin tasha sannan ya bata magani, sai ya sake fita yaje ya ɗauko wasu robobi guda biyu ya miƙa mata babbar.
“Kiyi fitsari a wannan”
Hannunsa sanye da safa, ya ɗibi jininta ya zuba a ƙaramin robar sannan ya manna mata kaɗa ya lunda mata, ya kwance robar daya ɗaure mata hannun da shi, kwashe kayan yayi ya fice. Bayan kamar thirty minutes ya dawo ɗakin da shirinsa na zuwa office.
Robar fitsarin ya ta bashi, ya karɓa yayi mata kiss, sannan ya fice. Ɗakin Kalsoom ya shiga, tana jin motsinta ta lafe kamar tana bachi, itama kiss ɗin yayi mata sannan ya fice.
Rashida na jin tashin motarsa ta janyo wayarta ta danna number Asmee, ringing huɗu tayi sannan ta ɗauka.
“Asmee an tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau ya gidan?”
Ya amsa mata muryarta da alamar damuwa.
“Asmee yau ba zan samu fita ba, bana jindaɗi, sai dai kr kije idan da hali”
“Me ke damun ki?”
“Abubuwa da yawa ga jikin duk ya min nauyi”
“Ko dai ciki ne?”
“Haka nake tunani nima”
“Allah ya raba lafiya”
Jin ta faɗa ba da wani jindaɗi ba yasa Rashida Tambaya.
“Ya naji muryar ki ba daɗi?”
“Ba komai, nima bana jindaɗin ne, amman zan daure a haka naje”
“Yauwa na gode sosai, kin ce dai yana aiki sosai ko?”
“Sosai Wallahi kamar yan kan wuƙa, duk yadda mu kayi zan faɗa miki”
“Okay na gode”
Rashida na kashe wayar Asmee ta fashe da kuka.
‘Allah kasa ba gaske bane Allah, idan har da gaske ne ya ci amanata, tun da yasan yana da shi kuma ya nemi ya kwana da ni, Wallahi dana sani ni dama ban je gunsa neman magani ba, mugun Malami kawai’
Abunda take ta tunani a zuciyarta kenan, a fili kam kuka kawai take, kamar ta cire idonta.