Ƴan seconds ya rage wayar ta fara ringing sai kawai ta kashe, tana tunanin yadda za fallasawa kanta asiri idan har ta yarda ta faɗa masa danuwarta, ba duka ɗan'uwane yake taimako dan Allah ba, ballanta shi data san dole ne ya faɗawa Hajiya Barau, ita kuma fitar da maganar zata yi, sai a fara cewa tana roƙon dangi.
Juyowa tayi ta nufo gurin da Hajara take zaune, ita ma ta zauna tana miƙa mata wayar.
“Har kin kira?”
“A'a ban kira ba na fasa ne”
Ta faɗa tana murmushi, isowar Mama yasa ta sadda kanta ƙasa tana watsa da yatsun hannunta.
“Wai gida za mu koma yanzu”
Daga Hajara har Namra kallonta suka yi
“Gida kuma? Ina ba dai sokoto ba ko?”
Namra ta tambaya cike da mamaki.
“Can fa, wai so nake muje yanzu kamin yamma mun isa sai da gobe kuma mu juyo”
“Amman zuwa lafiya ne?”
Mama ta ɗan yi shiru kamar mai tunanin abunda zata ce mata.
“A'a wai kuɗi zan je na ranto idan har Allah yasa an samu sai a siye maganin da likita ya rubuta ta, tun da naga alamun sauƙi a jikinsa amman kumburin nan na kansa yana bani tsoro. Kuma ina son naje na ɗauko wasu tufafin gashi mai son Hajara shi ma ya damu yaushe za mu dawo”
Namra ta sauke ajiyar zuciya cike da tausayawa, ji take kamar ace tana da mafitar su ta ɗauka ta bada, ba sai taje neman rance ba.
“Amman Mama da zaki yi haƙuri har gobe, saboda yanzu rana yayi sosai, kuma zaku iya zuwa ku tarar da jira a tasha, ƙara ki haƙura har da safe sai ki tafi, amman tafiyar dare ba kyau, musamman lokacin nan na muke cikin matsalar tsaro”
Mama ta ɗan yi shiru, tana nazarin maganganun Namra.
“Nima haka nake gani, ƙara na haƙura har zuwa goben”
Ta faɗa daga tsayen da take tana gyara ɗaurin zanenta, sai kuma ta juya ta koma dan faɗawa Asim zancen canjin tafiyar.
Sai da wuce sannan Hajara ta kalli Namra tace
“Tafiya yanzu sai kace waɗanda aka kora daga gari”
“Nima ai shi na gani, ƙara dai a haƙura har da safe, yau da gobe a duk ɗaya ne wajen Allah”
Namra ta faɗa tana ƙoƙarin tashi
“Lallai kam, nima bana son tafiya irin wannan”
Murmushi kawai tayi ta nufi ward ɗin da nufin ƙara tausasa Mama ta haƙura da tafiyar har gobe.
A bakin ƙofar ta tsaya cak! Tana sauraren muryar Mama da kunnuwanta suke sato mata.
“Na ce amman ai dubu ɗari sun isa ko? Kar mu karɓo kuɗin duka ya zama ba muna da komai gurin mai dashen”
“A'a Mama ki karɓo gaba ɗaya, kin san dole ne mu siye abinci, kuma wata ƙila ba wannan maganin kawai za a siya ba”
“Amman Ibrahim idan muka karɓi kuɗin duka mun fita daga adashen kenan fa, abinci idan har taga babu shi ai dole ta faɗa ma iyayen nata, ni ina mamakin ace ƴarka ta yi wuta irin haka ka kasa taimaka mata, anya wai ƴar su ce tagaske kuwa? Ni bana ganin a kashe kuɗi dika fa”
“Haba Mama lafiya na kama da me? Idan har Allah yasa na ji sauƙi, ai sai a samo wasu a ake shiga kuma”
“Ina za'a samu wasu Ibrahim? Kana ganin yadda suka juya maka baya, Wallahi bana tunanin zaka samu wani abu a auren nan, duba kaga ko fa ƴar garar nan da ake ba su maka ba, yanzu dubi halin da kake ciki ai ko basu fitar da kai waje ba, sa maka iya ƙoƙarin su amman suja ƙyale ka”
Wani dogon numfashi Asim.yaja ya sauke zuciyarsa cike da jin zafin abunda iyayen Namra suka masa.
“Allah dai ya bani lafiya, idan kiɗa ya canja rawa ma dole ta canja, idan su yi dan Allah ba sa yi dan ƴar su”
Kamar an jefar da gilass a ƙasa ya tarwatse haka taji a zuciyarta, lokacin da maganganun Asim suka daki dodon kunnenta.
Da sauri tayi baya tana maida numfashi, tare da haɗiye yawu a lokaci ɗaya. Wani irin mamaki take tana girgiza kai, kamin tayi haramar barin gurin.
Da sauri-sauri take tafiya kamar zata haɗa da gudu, ji take kamar tayi tsalle ta ganta a wani wajen, ta kasa yarda da kunnuwanta sun ji abunda Asim da Mahaifiyarsa suke faɗa.
Ta tari mai Napep tana haƙi kamar wanda aka janye wa numfashi.
“Nasarawa zaka kai”
“To ɗari da Hansi, kuma sai na bi ta Yarima Estate na sauke wannan matar”
Kai kawai Namra ɗaga masa, ta shiga Napep ɗin ba dan hankalinta yana jikinta ba. Yarinyar dake kusa da ita taja wani dogon tsaki, tana matsawa can gefe irin tana ƙyaƙyamin Namra ɗin nan.
“Mtswww ni dama zaka sauke ta, ta nemi wani sai na biya ka kuɗin duka”
“A a haƙura dai zaki yi Hajiya, ai da kamin a ɗauke ta kika ce haka, amman yanzu na riga na ɗauko ta kyayi wannan maganar kuma”
Mai Napep ɗin ya faɗa, yana mai cigaba da tuƙinsa. Sai a lokacin Namra ta kalle ta da kyau.
“A'a ka sauke ni mana ka kaita ita kaɗai saboda ni ba mutum bace, ko kuma Napep ɗin ta gidan ku ce, idan har kin isa miyasa ba'a siya miki mota ba? Ko kuma ayi miki direba na ki na kan ki? Wallahi ƙaryar arziki kike tun da har kika iya shigo Napep”
Ƙasa-ƙasa ta kalli Namra tana wani yamutsa fuska, ita har ga Allah ƙyaƙƙyamin Namra take. Wayarta dake jaka tayi ringing, tayi saurin fidɗo purse ɗin dake cikin jakar ta cire wayar tare da yin picking ta kara a kunne.
“Hello Dude”
Ta ɗan yi shiru kamin ta sake cewa.
“Ni na baro motar can, Ummy ce na faɗa mata, wai bata turo direba tun da ban faɗa mata zan fita ba”
“Eh ina kam Napep n kusa isa, okay bye safe trip Dude”
Ta kashe wayar kamar ta fasa kuka, kamin a isa Estate ɗin nasu har ta tsawala.
Har bakin gate ɗin gidansu ya sauke ta, ta ciro 1k ta miƙa masa, bata tsaya karɓar canji ba ta nufi gidan, da sojoji suke gadi, da sauri suka buɗe mata gate shige cikin, sai ƙyaƙƙyamin kanta take.
Kai kawai mai Napep ɗin ya kaɗa ya wuce da Namra Nasarawa road.
A ƙofar gidan su Mardiya tace a sauke ta, ta ciro ɗari biyu ta miƙa masa ya karɓa ya bata canji sannan ta juya ta nufi cikin gidan, zuciyarta na dawo da maganganun da kunnuwanta suka joyo mata.
A zauren gidan ta tsaya, ta jingina da ginin gurin ta lumshe.
‘Miyasa Asim yake ƙoƙarin ɓoye min sirrin sa? Me suke shiryawa shi da mahaifiyarsa? Kar zancen Anty ya zama gaskiya, kar dai ace rayuwar Asim ta canja, da biyu ya aure ni kenan? Soyayyar daya nuna min a baya ta ƙarya ce?’
Hawaye ya silalo daga idonta, dake lumshe, sai kuma ta girgiza kai tana cigaba da zancen zuci.
‘Amman ya so ni a baya kuma so na gaskiya, miyasa yanzu zai canja? Na juyawa kowa baya saboda shi, ba zai min haka ba, what if i choose the wrong person? No no no it's Asim mutumen da yake son ki so na haƙiƙa mutumen da yace min miki ba dukiyarki ce a gabansa ba’
Ta buɗe ido tana share hawayenta.
“Amman mi yake nufi da idan ba suyi dan Allah sa yi dan ni? Me yake nufi da idan rawa ta canja, Allah ka fahimtar da ni, Allah ka amintar da ni, Allah kar ka saka zancen Anty ya zama gaskiya, Allah kar kasa Asim ya zama cikin mutanen da za su min Zagon Ƙasa, Allah kar kasa ayi ma auren nan na mu dariya”
A fili tayi furucin tana kuka, zuciyarta a karye, tana ji a jikinta ranar nadamar ta tana daf ta ita.
Ganin wata zata fito daga cikin gidan yasa tayi saurin ɓoye kukanta.
“Namra ce a nan tsaye?”
“Eh yanzu na shigo ina wuni?”
“Ya jikin mai gidan na ki?”
“Da sauƙi sosai”
“Allah ya ƙara sauke, har yanzu dai ba mu samu mun koma mu ƙara dubashi ba”
“Ba komai ai, kuna ta sana'ah ba zama”
“Ba zama fa Allah dai ya ɗauƙe Wahala”
“Amin”
Namra ta kunna kai cikin gidan, ita kuma ta fice tana gyara hijabinta.
HILAL POV.
Yau one day da gwajin da ya kai ayi ma Rashida, dan haka yana buƙatar karɓo result ɗin dan tabbatar da zarginsa, duk da alamu sun nuna cikin ne amman ya fi son ya ƙara tabbatarwa.
Lokacin daya gama duba Patients ɗinsa sai ya nufi lab dan karɓar sakamakon.
To his surprise ba abunda yake zato ba kawai ya gani, a cikin result ɗin akwai symptom ɗin HIV. Haka ya riƙa karanta result ɗin ba daɗi, but still abu ɗaya yake gani da biyu yake gani.
Ciki da kuma symptom.
Ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yayi, kar mutanen da suke gurin su zargi wani abu. Cikin rashin kuzari ya dawo office ɗinsa, har ya zauna sai kuma ya tashi tsaye, sai karanta takardar yake numfashinsa na yawo, wani zafi ya riƙa jin yana masa yawo tun daga cikin cikinsa zuwa ƙwaƙwalwarsa.
“Ko dai mistake suka yi? How could this happen?”
Ya kasa yarda, mamaki yake har yanzu, shi dai yasan yana yawan gwada kansa every 6 months da kuma iyalansa, kuma lokacin da aka auna jinin Kalsoom be nuna haka ba, why Rashida?
Gani yake mistake ne suka yi, sai dai baya jin zai iya koma ya tambayesu, abunda kawai zai iya, shine ya sake ɗibar jinin nata, da na ƴaƴansa da kuma na Kalsoom ya kai ward ɗin da ake gwajin cutar, dan tabbatar da zarginsa, idan har da gaske ne ai zai nuna yadda ta samu ciwon da kuma daɗewarsa a jikinta.
Be iya ƙarasa aikin ba ya haɗa kayansa ya ɗauki ƙaramin box ɗinsa ya cire labcoat ya riƙe a hannu ya fice, ba tare daya tsaya kulle office ɗin ba.
Ko da ya isa gida kansa har wani zafi yake kamar an kunna masa wuta, gaba ɗaya kalar idonsa, da fuskarsa ta canja irin kana kallonsa kasan yana cikin damuwa.
Rashida na zaune falo riƙe da plate tana cin abinci, ba laifi yanzu kan ta ɗan samu sauƙi dan ita ma tayi girkin sa kanta. A bakin ƙofar falon ya tsaya yana kallonta wani tausayinta yaji ya lulluɓe shi har idonsa suka cika da ƙwallah.
Ita kuma ta ɗan kalle shi kaɗan ta kauce kai, ba dan bata son kallon nasa ba, sai dan baƙin kishi daya rufe mata ido, gani take yanzu ai ba ita kaɗai ce da shi ba.
Yana sako ƙafarsa a first step ɗin falon, sai ta tashi ta nufi ɗakinta. Shi kuma ya tsaya a gurin ya bita da kallo zuciyarsa cike da tausayinta.
______________________________________________
Assalamu alaikum Habibaties 🌺
Ina fatar kuna cikin koshin lafiya? Allah yasa haka Amin
My dear readers idan Allah yasa muna cikin masu rai da lafiya, idan na yi page 35 tau ZAGON ƘASA na Khadeeja Candy ya koma na siyarwa, daga bakin Page 35 har zuwa karshe na kudi ne, daga page 1 zuwa 35 free ne. Nasan zaku ga chanji yazo muku ba ta yadda kuka zata ba, ku yi hakuri ku min uzuri, haka sauyin ya zo. Kuma ina fatar zaku goya min baya, fiye da yadda kuke min a da, soyayyar ku da haɗin kan ku, shi na ke fata a kullum, Allah yasa ku min kyakkyawar fahimta. 😊👌
Ga waɗanda suke sha'awa. Naira ɗari biyu ₦200 zaku turo ta wannan account ɗin 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.
Ga wanɗanda basa da account kuma za su iya turo katin waya na line mtn na dari biyu da hansin ₦250 ta wannan number 08036126660
Idan kun tura. Sai ku turo da shaidar biyan kudin wato screenshot ta wannan number 08036126660.
NA GODE 😊
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 32*
NOT EDITED ⚠️
Ɗakinsa ya wuce ya aje kayan da suke hannunsa, sannan ya fito ya shiga ɗakinta. Zaune ya same tana taunar naman abincin data gama ci, kusa da ita ya zauna yayi mata ƙuri da ido, kamar mai tunanin abunda zai faɗa mata.
“What?”
Ta tambaya shi sam be san ta lura da kallon da yake mata ba har sai da tayi magana.
“Bana da ikon kallon ki ne?”
Ya faɗa yana murmushin ƙarfin hali.
“Kallo na nawa kuma, ai na gaji da kallon nawa ne shiyasa kaje ka ɗauko wata, kuma ni ka faɗa mata ta daina zuwa min yawo da yara karta lalata su”
“Uhmm, Pyar ki daina sawo zance Kalsoom a gurin da muhallinta ba, ke da ita duka ɗaya kuke a guna, wani abun da kike faɗa akanta ba daɗe yake min ba, and you know what ita bata taɓa wani mugun furuci akan ki ba, balle kuma akan ki ba, sannan tana kula da ƴaƴanki”
Ta taɓe baki ta aje plate ɗin ƙasa.
“Wallahi duk son ƙarya ne, babu kishiyar data zata so ƴaƴan kishiryarta, wannan duk Zagon ƙasa ne”
Ya kai hannu ya riƙo hannunta.
“Naji pyar faɗa min when last nayi miki gwajin jini?”
“I can't remember, ba kai kake min ba?”
Ya ɗanyi shiru.
“Ina ganin anyi shekara biyu yanzu, saboda ba samun zama nake ba, miya faru?”
“Ba komai, zan sake ɗibar wani ne, wacan a mota ya ɓata fitsarin kawai na auna”
“Okay amman yau zaka ɗiba, dan gobe zan je aiki”
“Daga jin sauƙi sai kuma zuwa aiki?”
“Kasan matsalar banki tun yau ma aka so na koma”
Hannu ya kai ya shafa gefen fuskarta.
“Pyar i love you so much ki sa wannan a zuciyarki, mijinki yana son ki sosai”
“Yana son mu dai point of correction”
Ta faɗa tana wani yatsina fuska, shi kuma yayi murmushin da be kai zuci ba, ya tashi tsaye.
“Bari na yi wanka”
“As you wish”
Bayansa ta bi da kallo zuciyarta na mugun tafarfasa, duk yadda take so mijinta idan ta tuna da ba ita kaɗai yake so ba, sai ranta ya ɓace.
Sai da yamma lis sannan Kalsoom ta dawo, dan yau gidan su ta wuni ita da yara, daman duk ranar da ba'a zuwa makarantan ilamiya, ta kan yi amfani da lokacin ta koyar da su wani abu na rayuwa ko kuma addini, sai ya kasance yau kan tana buƙatar zuwa gida gaida du Momy, shiyasa ta kwashi yaran duka suka je gidan.
Tayi mamakin ganin Rashida tayi abinci a yau bayan kuma jiya ta gama koken bata da lafiya, kusan kwana biyu nan ma har cewa take ita ba zata iya cin komai ba.
Ta san yau Doc ba a ɗakinta yake ba, hakan yasa bata damu da dole sai ta ganshi, dan ko da suka dawo, baya gidan Rashida ce kawai, kuma har dare be dawo ba.
Da wuri yaran suka yi bachi saboda gajiya, sai ya rage ita kaɗaice a falon sai tv tada tisa a gaba tana kallo. Saman kanta Rashida ta zo ta tsaya sai wani yauƙi take kamar ance mata Doc ne a gurin zaune.
“Ammyn Rafiq ya idan zaki fita da yara ki riƙa faɗawa Dadyn su, yazo nan yana ta min faɗa wai shi baya son yawo kar a lalata masa yara”
Kalsoom ta ɗago kai ta kalleta tana murmushi
“Ai ni kaina ban fita ba, sai da na nemi izininsa, balle kuma na ƴaƴansa, I'm friendly Rashida feel free to tell me baki son ina fita da yaran ki, is okay sai na tura su duk inda nake so”
Bata tsaya jiran abunda zata sake cewa ba, ta aje remote ɗin dake hannunta, ta tashi ta bar mata falon.
Da wani mugun kallo Rashida ta bita ji take kamar ta tashi taje ta maƙareta, bata san tana kishinta ba ma sai a yanzu data kwana biyu nan a gida, ita dai gani take Kalsoom ta tare mata guri.
‘Ni ban ga abunda matar nan ta fini da shi ba, yaje ya kwaso ta, mace sai baƙin munafurci, Wallahi kin yi kuskuren auren mijina dan mijina mijin Rashida ne ƙadai ba dawata macen ba’
Ƙwafa tayi tana wani huci kamar maciji, ta juya ta koma ɗakinta. Saman gado ta zauna tana sauraren yadda zuciyarta take mata zafi, kishin Mijinta take ji sosai, sai a yanzu take gane abunda wasu ƴan grps nata na whatsapp suke faɗa mata akan kishiya, ya karɓe mata ƴaƴa, yanzu kuma tana ƙoƙarin karɓe mata miji, gashi Hajiya ma tafi son Kalsoom da ita.
Wayarta ta ɗauko ta aika ma da Asmee kira, sai da ta mata two missed calls sannan tayi picking.
“Ina ta kira hala baki kusa?”
“Eh Wallahi ya gida?”
“Gida ƙalau, ni dai ce hankali ba kwance kuma ban ji kin kira ni, Asmee idan mukayi sake fa matar nan ƙwace min miji zata yi”
“Wallahi ban samu naje bane, bana jindaɗi sosai, amman inshallah gobe zan je”
“Ayyah me ke damun ki?”
“Ina jin ƙiba ne sai kuma Infection ya shiga ciki”
“Indai Infection ne ki nemi ɗayyar citta da tafarnuwa ki feraye cittar ki ki jiƙa su, su jiƙu sai ki riƙa sha ko kuma ki nemi maganin nan Cantin yana yi sosai. Na rage tumbi ko kiba kuma ki samu ganyen guava guda bakwai ki tafasa with one liter of water kisha for seven day's mrng before breakfast da kuma last thing kafin kwanciya, shi Momy take kuma wallahi na sauka ta rage ƙiba sosai cikin satina ɗaya yayi mata aiki wallahi, masu ulcer ma zasuyi yana maganinsa, irin wannan yafi na asibitin dan shi ba shida side effect. Allah ya baki lafiya”
“Amin na gode sai kin ji ni”
Daga haka sukayi sallama, Rashida ta aje wayarta tana faɗin
“Garin kwashe kwashen ki dai sai kin kwasowa kan ki, ba ko wane malami bane zai haɗe yawunsa akan ki, ni ko zan yarda ai ba zan malaman ƙauye ba ƙazamai”
Ta ƙarasa maganar da tsire baki, duniyar tunaninta na son dawo mata.
A gogon ɗakin ta sakarwa ido daga seconds zuwa minutes take ƙirgawa har ya kai ga hours, Doc be dawo gida ba, haka ta gaji ta kwanta saman gado idonta a ƙafe, babu abunda take tunani sai Rashida.
Yadda ta shiga cikin gidan da kuma irin rawar data taka tun daga shigowarta zuwa yanzu, bata ankara hawaye suka silalo mata.
Sai yanzu take jin yadda ɗacin zuciya yake, sai yanzu take jin son Hilal na haƙiƙa a zuciyarta, sai yanzu take gane ta tabka kuskure da tabar shi ya ƙara aure, yanzu haka zata kasance ita da wata a cikin gida? Haka itama zata gina nata rayuwar ta karɓe mata kowa?
Tafiyar daƙiƙa biyar zuwa shida numfashinta yayi kamin ya dawo izuwa gareta har ta ankaro da duniya take, ta samu damar amsa sallamar mai gidan nata.
“Wa'alaikassam”
Sautin muryarta ya isar masa da saƙon damuwarta, ga kuma hawaye dake kwance a fuska. Ledar dake hannunsa ya aje ya zauna kusa da ita gabansa na faɗuwa, har zuciyarsa ta fara raya masa wani abun na dabam.
“Miya faru kike kuka?”
“Kawai ina tunanin rayuwa ne, da kuma irin sakamakon da kayi min, bayan nayi maka dukan hallacin”
Masauki yayi mata a ƙirjinsa, ya kai hannu ya dafa cikinta, zuciyarsa na hasaso masa wani tunanin na daban.
‘i just can't believe that, taya wannan cutar zata kusance mu? Allah kar ka jarabe mu da abunda zai sa rayuwar mu data ƴaƴansu cikin damuwa’
A can cikin duniyar tunaninsa, kunnuwansa suka cinto masa wasu kalamai da Rashida take ta maimata masa.
“Ni kar ta sake fitar min da yara, kar taje ta lalata min su, kaji”
“Ba zata lalata su sai dai ta gyara tarbiyarsu, bakin ki ya daina furta mummun kalamai a kan Kalsoom, zamana take ba zaman ki, dan haka babu ruwanki da ita”
Da gautsi ya ƙarasa mata kalam, wanda har zuciyarsa haka take, dan kawai yana son ta ba zai yarda ta da aybanta masa amarya ba, dan shi ya san darajarta, kuma yasan gidan data fito.
“Ƙara ma ku haɗa kan ku dan ni ba zan ɗauki irin wannan abun ba, mu taru mu gode Allah akam kyautar da yayi mana, kuma ku yi fatar Allah ya sauke ku lafiya”
Kalamansa basa buƙatar fassara, kai tsaye ta san inda suka dosa, daman ita ta san ciki ne da ita, to Kalsoom fa ita ma cikin ne.
A take yawun bakinta suka tsinke, cikinta ya ɗauki kuka, ba ƙaranin ƙoƙari rayi ba wajen ƙawata fuskarta da murmushi, dan ta nunawa Hilal ta jidaɗin.
“Mashallah Kalsoom ita ma tana da ciki? What a blessed”
“Tana ma har ya riga na ki, bata da matsala sosai ne shiyasa ba za a gane tana da cikin ba”
Amsarsa ta tabbatar mata da zarginta, daman dalilin tambayar kenan. Wata duniyar take ƙoƙarin kai shi dan ta nuna masa farincikinta, ta kuma ɓoye masa baƙincikin da ke son bayyana a fuskarta.
Zuwana Kalsoom yasa ya daina takura akansa a kanta, duk magiyar da yake mata yake nuna mata maitarsa yanzu ya daina tun da ya samu wani halalin nasa, sai dai daren yau da raya masa shi fiye da yadda yake zato, a yau tayi masa abunda ta shekara goma bata masa ba, ta sakar masa jikinta sosai, har sai da shi kansa ya gaji dan kansa ya bar.
Tare suka yi wanka, suka ci abinci da kuma dan abun taɓawa daya siyo musu ɗazu, a lokacin ƙarfe biyun dare yayi. Suna gamawa ta kwanta dan ba gado haƙƙinsa, shi kam be kwanta ba sai yayi nafisa raka'ah biyu, raka'ar farko ya karanta fatiha da ayatul kursiyu sai ya dora kulhuwallahu sama, a raka a ta biyu kuma ya karanta fatiha da amanar rasulu ya ɗora kulhuwallahu sama, sannan ya zauna yayi zaman tahiya kamin ya sallame a cikin tahiyar ya faɗawa Allah buƙatarsa, sannan ya sallame.
Sai da yayi salatin annabi da godiya ga Allah da istigifari ƙafa ɗari ɗari sannan ya sake ɗaga hannu yayi kirari ga ubangijinsa ya nemi yafiyarsa, sannan ya sake koro da buƙatarsa.
A cikin ɗauko abun ɗibar jini ya ɗibi jininta dan yasan da safe ba zai samu damar ɗiba zata ce masa aiki.
Washe garin da zai kai yaransa makaranta suma ya ɗibi nasu, Kalsoom kam sai daf da zai fita sannan ya ɗibi nata sai raki take masa tana masa shagwaɓa, wai da zafi ita zai ƙarar mata da jini, haka ta riƙa narke masa a jiki har yayi lattin zuwa aiki.
NAMRA POV.
Kwata-kwata bachi ƙaura yayi mata daga ido, bata ma jin alamunsa balle har tasa rai zai so mata, abu ɗaya zuwa biyu yayi mata tsaye a rai, maganganun da Asim yayi shi da mahaifiyarsa, wata zuciyar na shawarta akan ta bayayyana masa ta kuma tambaye shi abunda yake ƙoƙarin ɓoye mata, yayinda ɗayar kuma take ce mata ta haƙura taga iya gudun zuwansa dan tabbatar da zarginta.
Babu amfani da raya dare da tunani bayan Ubangijinta yana kallonta, kuma yana shirye ya amsa buƙatunta, tayi haramar ƙorar sheiɗan sannan ta samu kuzarin fita tayi alwalah, sannan ta dawo ɗakin tayi nafila ta ɗora sa salatin Annabi.
Firgigit Mardiya ta farka daga dogon bachin da take a farkigice har tana ihu. Namra ma dake kusa da ita sai da ta ji tsoro kowa dake cikin ɗakin ya matsa, Mahaifiyarta ta tashi tana kallonta.
Gabanta ta fara kallo kamin ta kalli bayanta, sai kuma ta bi ko'ina na ɗakin da kallo, ajiyar zuciya ta sauke yafi ashirin, sannan ta haɗe yawun bachin da suka cika mata baki, ba dan tasan tayi ba.
“Ke lafiyarki?”
Ashe dai duniya take, jin muryar mahaifiyarta ya ƙara tabbatar mata da a farke take.
“Wallahi wani mumunan mafarki na yi, wai wuta tana bina”
“Subhanallahi, ke kuwa ai addu'ah zaki yi”
Namra ta faɗa, tana rufe ƙur'anen dake hannunta, sannan ta nufi gurin bachinta tayi addu'ah bachi ta kwanta ba dan tana jin bachin ba, sai dan tana buƙatar jinginar da jikinta da tabar suka saba mata shimfiɗa da ita.
Washe gari...
Da sassafe ta siye tea da buroɗi ta nufi asibiti, dan bata son su Mama su kama hanya bata isa ba, tun da babu wanda zai kula da Asim sai ita. Duk yadda take ganin ta doka sammako sai taga har sun fi ta, dan tana shiga ɗakin taga alamar sun kama hanya.
Bata yarda ta nunawa Asim komai ba, ta gaisheshi sannan ta masa ya jiki ta soma zuba masa tea ɗin.
“Jiya kika tafi baki faɗa ba”
“Eh pad ɗina ne ya lalace shine naje gida na canja, su Mama sun kama hanya ko?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yanzu kam hankalinsa ya kwanta, daman can yana tunanin ko ta ji maganar sune yasa taje ba tare data faɗa musu ba, ashe shi da Mama ba su canka dai-dai.
“Eh tace da wuri zata je yadda zata tararda matar da za a ranto kuɗin gareta”
“Allah yasa a dace”
Ta faɗa tana miƙa masa tea, kallon da tayi masa da kuma maganarsa sun zari zuciyarta, miyasa Asim yake ɓoye mata? Wani tunanin ne ya zo mata sai ta kawar da fuskarta gefe.
_______________________________
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 33*
NOT EDITED ⚠️
Washe garin ranar da Mama ta tafi ta dawo, guraren uku da rabi na rana. Ita kaɗai ta dawo ba tare da Hajara ba, Namra bata nuna mata komai ba ta tarbeta da far'ah tana mata sannu da zuwa.
Tana son tayi labari Namra ta tsare su taƙi ta tashi, shi kansa Asim yana son magana da ita amman ba dama, tun da Namra tana gurin.
Kamar ta san Namra bata tanadar mata komai, tun a hanya ta tayi gurin biredin ta da lemu, sai ta ta ci ta ƙoshi, sannan ta tashi ta fita.
Da kanta taje ta biya kuɗin maganin dan kar taba Namra.
Ta dawo daga biyan maganin ne, Namra ta tashi tayi musu sallama ta baro asibitin.
Har ta iso gida kuka take, tana tunanin yadda Asim yake ɓoye mata lamarin, dan ta lura da yadda suke kallon kallo da Mama, hakan ya soma tabbatar mata da abunda Anty Amarya ke faɗa mata.
“Idan har ta tabbata Asim na son yaudarata....”
Sai kuma tayi shiru ta share hawayenta, ta miƙawa mai Napep kuɗinsa ta shige gida.
*** ***
“Thank you”
Ta faɗa tana murmushi tare da kallon mutumen daya tashi daga saman kujerar ta ya nufi ƙofar fita. Sai da ya fice sannan ta kalli wayarta dake ringing, sannan ta kai hannu ta ɗauka zuciyarta na raya mata irin labarin da Asmee zata bata.
“Ƴar gari kamar kin san yanzu nake tunanin ki nace ko kin samu zuwan kuwa?”
Kuka ta fara ji kamin Asmee ta ɗora mata da zancen dalilin kiran nata.
“Rashida ina ciki matsala”
“Lafiya miya faru?”
“Wani malami ne da muke zuwa gurinsa, yana ba mu taimako, shine yanzu ake ce mana malamin yana da ciwon nan na zamani, shine tun ranar na kasa sukuni ban ma sama naje gurin matsalar ki ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Asmee garin yaya? Ya taɓa sex dake ne? Ko me?”
Kuka tayi sosai har ka kasa magana.
“Ki faɗa min mana ki daina kuka”
“Ya taɓa lokacin da je neman wani taimako sai yace min sai na kawo sperm ɗin wani wanda ba mijina ba, da jinin al'ada da shi za a haɗa, ni kuma na ce masa ban san inda zan samo ba, shine....”
Ta ƙarasa da kuka
“Ke yanzu kin je an gwada jinin ki ance kina ɗauke da ciwon ne? Stop crying and tell me Asmee”
“Ban je ba, tsoro nake ji ban san wanda zan faɗawa ba sai, dan bani da ƙawa irin ki, na rasa yadda zan yi tsoron gwajin na ke, aiki ma na daina zuwa yanzu”
“Innalillahi Ya salam Ya salam”
Ta soma zagaye office ɗin tana dafe kai, da wayar a kunnenta.
“Ki kwantar da hankalin ki kinji karki faɗawa kowa, kuma karki yi abunda zai sa mijin ki ko wani ya zargi wani abu, i will call you back”
Tayi saurin kashe wayar tana tuna jininta da Hilal ya ɗiba, idai har Asmee ta kamu da cutar to itama zata iya kamuwa da ita tun da har suna using mutum ɗaya.
Faɗuwa tayi zaune zumi na keto mata ta ko'ina, hannu ta kai tana shafa kanta, tana girgiza shi kamar wani ne a gabanta.
“Ko shiyasa ya sake ɗibar jinina? Amman kuma ai da ba zai kusance ni ba, amman yanzu idan ya auna dole ya gano idan akwai shi”
A fili take furucin zuciyarta a karaye, jikinta har tsimi yake, yanzu kam hannaye biyu tasa ta dafe kanta tana tunanoma kanta mafita.
“Dole ne na dakatar dashi daga yin gwajin, kuma dole ne nima naje na bincika kai na, indai har da gaske ne Asmee kin cuce ni”
Da sauri ta tashi ta kaɗe jikinta ta fiddo hoda a jakarta ta gyara fuskarta sannan ta ɗauki jakar ta fita. Sai da ta biya ta faɗa musu fitar gaggauwa ta kamata, sannan ta fito harabar bankin ta shiga motar, ta ɗauki hanyar Asibiti.
Akwai ƴar tazara tsakaninta da asibitin, amman yadda ta sakarwa motar wuta yasa ta isa cikin ƙanƙanen lokaci. A harabar asibitin tayi parking, ta fito ta duba gurin da aka tanadarwa manyan likitoci dan faka motocinsu.
Motar Doc Hilal ce ta uku a gurin, that's means yana cikin asibitin, safa da marwa ta fara yi tana tunanin ta inda zata fara. Lab ne ya faɗo mata a rai. Da fargaba ta kutsa kai cikin asibitin ta ɗauki hanyar da zata hada ta da lab ɗin, ƙasa-ƙasa take kallon mutane, tana fargabar haɗuwa da Hilal, dan ko ganinta yayi bata san me zata ce masa ba.
Ta tararda mutane da ɗan yawa a gurin da aka tana da dan karɓar results ɗin jini da fitsari, hakan yasa ta zagaya ta shiga ciki tun da ita ba baƙuwar asibitin ba ce.
Biyu daga cikin mutanen da suke gurin sun gane, tun da sun san matar Doc ce, cikin mutunci da far'ar ta gaisa da su tana yi tana kallo ƙofa.
“Habib na ce kun gama gwajin jinin da Doc ya kawo? Za a tafi dashi wani garin ne”
Wanda ta kira da Habib ɗin ya amsa da.
“Eh tun ranar muka shi ba ai”
“Ba yau ya kawo ba?”
“A'a ina jin tun monday ne, Monday or Tuesday? Abbas kai ka bashi ko?”
Wanda aka kira da Abbas ɗin be ma kula.da zancen su ba sai rubuce-rubucen sa yake, Habib ɗin ya kalleta.
“Ina jin Monday ne, an dai kwana biyu yanzu”
Gabanta ya faɗi sosai.
“O'o nasan ya jefar da results ɗin wani wajen shiyasa ya ƙi ya faɗa min, amman yau be kawo maka wani ba?”
“Gaskiya be kawo ba, dan mu muka yi duty safe yanzu zamu tashi”
Nauyi zuciyarta sosai tayi mata har sai da ta tsayi ya gagareta, ta zauna a kujerar dake gurin.
“Amman dan Allah ya za'ayi na samu results ɗin wacan gwajin? Tun da ya ɓatar nasan ba zaku rasa a littafin ku”
“Wallahi da an fito da results ɗin an rubuta a littafi ansa a paper na results ɗin ake kai su ɗakin ajiya, sai dai shi Doc zai iya zuwa yayi ma Doc Omar magana, sai ya bincika masa, amman nan results kawai muke badawa”
“Okay Thank you bari na koma gurin Doc ɗin nayi masa magana”
“Okay a gaida yara”
Ya faɗa yana kallon bayanta, irin ƴan iskan samarin nan ne da basa gani su kauda idonsu.
Ƙafafunta sun mata nauyi, ga idonta dake son ciki da ƙwalla tana mayarwa, akwai ƴar tazara tsakanin office ɗin da lab, hakan ya bata damar tunanin abunda zata cewa Hilal idan ya ganta, idan kuma ta koma bata shiga ba ta san zai iya samu labarin ta shigo cikin asibitin tun da akwai waɗanda suka santa, kuma zasu iya faɗa masa.
_Thank you so much my tomatir my albasa my daddawa my miyar kuka_
Yana dannawa Ƙalsoom reply ɗin ta whatsapp. Rashida ta turo ƙofar office ɗin ta shigo da murmushi a fuskarta.
Tashi yayi daga jinceren da yake saman kujera ya kalli da dariya.
“Surprise surprise surprise”
“Yes Darling, na biyo ta nan baya ne shina nace bari na biyo na ga farinciki na”
Ya ɓata rai sosai lokacin daya lura da yanayin tufafin dake jikinta. Suit ne mai wando ta riga sai ɗan ƙaramin hijabi dake kanta.
“Daman Haka kike fita daga office? Ba mun yi maganar nan dake ba dan me zaki fito baki ɗora abaya a sama ba, a cikin office ɗin ki kawai na yarda ki riƙa zama haka, kika ce kin ji ashe ni kike ma ko? Yana ɗaya daga cikin dalilin daya sa bana son aikin nan na ki, bana son wani na ganin matana abun nan yana min zafi”
Sai a lokacin ta kula da tufafin da suke jikinki, tsabar hankalinta baya jikinta bata ma san ta fito a haka ba. Hannayenta tasa ta laƙamo wuyansa.
“Im sorry Wallahi fitar gaggauwace shiyasa amman ba zan sake ba i promise”
“Yanzu haka kika shigo a asibitin nan kowa na kallon ki? Haba Rashida idan an girma a san an girma mana, kefa uwace kamata yayi idan kin ga Ezzah tayi wannan shigar kiyi mata faɗa ba wai ki yi ba”
Ta saki wutan nasa ta nufi freezer dan ita ba faɗan da yake mata bane a gabanta, abunda ya kawo ta take ƙoƙarin yi, tsayawa tayi ta duba da kyau drinks ɗin da tasan babu a freezer ɗin tace masa tana so.
“Nidai nace kayi haƙuri, kuma ina son nasha coc”
Ta faɗa tana marairaice masa, daman tasan baya shan coca-cola saboda irin abubuwan da ake faɗa akanta, kuma ta san yadda ya tsani kayan yahudawa.
Kamar zai ce mata babu, sai kuma ya ƙyaleta tun da yasan tana da ciki wani abun dole ya ɗaga mata ƙafa, sai dai be sakar mata fuska ba dan har yanzu ransa a ɓace yake, sai kawai ya juya ya fita.
Da sauri ta nufi teburinsa ta fara duba takardun da suke gurin, bata ga abunda take nema ba, hakan yasa ta nufi wata ƴar ƙaramar wardrobe dake gefen kujerar, har ta kai hannu ta buɗe sai kuma wani tunanin ya zo mata.
‘Idan na yamutsa masa takardu dole zai zargi wani abu’
Sai kawai ta fasa buɗewa ta koma ta zauna a kujerarsa ta ɗauki ƙafafunta ta ɗora saman teburin kamar babu abunda yake damunta, alhalin a can cikin zuciyarta tashin hankaline da tunani suka taru suka mata katutu.
Yadda ya fita haka ya dawo fuska a haɗe kamar be taɓa dariya ba, ransa ya sosu sosai da ganin irin dress ɗin data shigo dashi cikin asibitin.
Miƙa mata Coc ɗin yayi ya nufi windows ɗin office ɗin ya rufe. Tashi tayi tare da Coc a hannu daman can ba shanta zata yi ba, bata ma jin zata iya saka wani abu a cikinta yanzu.
“Ni zan wuce”
Ya watsa mata wani kallo.
“Haka zaki fita?”
Ta ɗan kalli jikinta
“To ya zan yi?”
“Ban sani ba”
Ya nufi hanger ɗinsa ya ɗauko labcoat ya ɗora mata sama.
“Kuma kar ki cireta har office”
“Doc zan bi ta lab na karɓi results, nayi mafarkin na haifi ƴan'biyu”
Dariya yayi sosai, wanda be shirya yi ba
“Toh ai ba a jini ake ganin twins ba, kuma ban ma kai awon jinin ba”
“Miyasa?”
“Ba nan za min ba, Asibitin Alex zan kai, saboda asibitin su tafi ta mu kayan aiki”
“Okay”
Ta faɗa zuciyarta cike da jindaɗin jin inda zata kai jinin, wani gurin kuma ta jidaɗin da be riga ya kai ɗin ba.
“To ina ka aje shi? Karka sake ce min ya ɓata kuma”
“Ba zai ɓata ba yana nan cikin mota na”
Ya faɗa yana jan hancinta, ita kuma ta kai bakinta dai-dai nashi tayi masa kiss.
Har gurin mota ya rakata sai da ta shiga yaga tashinta sannan ya koma office ɗin.
A maimakon ta koma asibitin sai kawai ta jiya pharmacy ta siye abu sannan ta ɗauki hanyar da zata kai ta gidan Asmee.
__________________________________________
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 34*
NOT EDITED ⚠️
ASIM POV.
“Naje na biya kuɗin har na magani, sun ce Nurse zata riƙa baka”
Ta faɗa tana hita da ɗan ƙaramin mafecin dake hannunta.
“Mashallah har nawa aka biya ne?”
“Dubu ɗari da goma sha ɗaya, ni ban san dalilin yasa ta kawo ka wannan asibitin ba, ace allura guda dubu tara magani ma shegen tsaɗa”
“Asibitin kuɗi ce fa, ba kiga ɗaki suka ware mana ba”
“Allah dai ya baka lafiya mu bar Asibitin nan, ni ban ma ƙi mun koma gida ba gaba ɗaya”
“Gaskiya ni ba zan koma gida yanzu ba, ana kallo kayi aure ka auri masu abu sai kuma aga yadda na dawo da ciwo, kuma a can ai sai ma mun fi jin kunya tun da ƙyale ni zasu yi, maƙiya sai su mana dariya”
“Ai ba za a maka dariya ba kam sai dai a zagi iyayenta”
“Ni dai na fi son zamana nan, a cikin kuɗin ki bani dubu ɗari na bata sai ta siye wasu abubuwan, tun da tace BQ ɗin be ƙone ba sai mu zauna a cikin”
“A'a wane irin dubu ɗari kuma? Dubu shirin ai ya isheta ta siye komai”
“Mama har katifa fa da sauran kayan aiki, ashirin ba zasu isa ba”
“Ni zan je na siyo katifar, da kai na haka kawai za a ɗauki har dubu ɗari a bata, idan an bata nawa ya rage ni bana da lalurar ne? Ban ga dalilin da zata ci amfanin ka kai baka ci nata ba, wallahi tallahi na tsani yarinyar nan saboda iyayenta, sam basu da mutunci”
Asim ya sauke jiyar zuciya.
“Ni bana ma son tunawa da su Wallahi, rai na har ɓaci yake, hmmm Allah dai ya bani lafiya, na warke na tashi garau, Wallahi sai na basu mamaki”
“Ai kana da maƙiya kam Ibrahim Allah dai ya baka lafiya”
Da Amin ya amsa yana gyara zamam ƙafarsa.
RASHIDA POV.
Cikin mintuna ta isa gidan Asmee, tana fito mota Asmee na fitowa daga falo ta tarbeta.
Tashin hankalin dake fuskar Rashida ya ɓatar da na Asmee dan yadda taga Rashida ta rikice ta damu sai ita ta sassautama kanta, a tunaninta Rashida ta damu da matsalar ta ne har haka.
Da suka shiga falo kowanne kasa magana yayi sai kallon kallo suke, Rashida na tunanin ta ina zata fara, Asmee na fargabar irin amsoshi da zata bata.
“Wai ke ya akayi kika yi wannan kuskuren, Asmee dan me zaki cuci kan ki ki cece mu?”
“Rashida na faɗa wani haɗi ne yayi min wanda dole sai an samu sperm ɗin wani”
“Amman ke yanzu dan baki da hankali sai ki bar shi yayi amfani dake? A maimakin kije can waje ki samo wani? Yanzu kin ja mana masifa Asmee”
Rashida ta ƙarasa maganar da kuka.
“Ba ni da tabbacin ina shi ɗin ko bana da, an ban yi gwaji ba, wata mata ce da take zuwa gurinsa aka ce ta kamu”
“Amman yayi ta neman ki ne har da yawa ne?”
“Kin san duk lokacin da kaje da buƙata dole ne sai sun nemi su kwanta da kai”
Kuka ta fara, yana ta dana sanin abunda ta aikata. Sai kusan azahar Rashida ta bar gidan bayan taja mata kunne akan karta kuskure da bari kowa yaji ciki har da mijinta.
Banki ta dawo zuciyarta cike da tunani kala-kala, masu sokanar tama ganinta da rigar likita, dariya kawai take musu ba dan ta kula da zancen su ba. Ta shiga office ɗinta sai zama ya gagareta, ga takardun data tarar an kawo ma tayi sigh ko kallonsu ba tayi ba. Ta juya ta fita, office ɗin Alhaji Bashir ta nufa. Bata nemi izinin shiga ba ta tura office ɗin ta shiga.
Hannunta ta miƙa masa kamar yadda ta saba yayi mata kiss, sannan ya zauna saman teburin ta ɗora sama ƙafarta ɗaya saman ciyarsa tana masa wani irin abu, kamar wata gwaggwazajiyar karuwa.
“Security Camera, dai a kashe take?”
“Ai nasa an cire min ita tuni saboda ke”
Ta ƙara matsarda ƙafarta, izuwa cikinsa.
“Bashir akwai wanda ka sani a Alex Hospital, ɓangaren Lab?”
Hannu ya kai ya naɗe wandon suit ɗin nata, ya fara shafa ƙafarta.
“Ba za a rasa wanda na sani ba, miya faru ne?”
Shiru ta ɗanyi tana tunani, idan har ta yarda ta faɗa masa, asirinta zai tono, tun da dole ne yayi ma matarsa magana, wata ƙila ma ya sake ta.
“Wallahi wata friend ɗita ce za'ayi ma gwajin kasan asibitin sun fi ƙwarewa, sama data su Hilal”
Ya ɗauko wayarsa yana wani lumshe ido
“Bari na kira Doc Sabo sashen jini yake aiki”
Ta sauka daga saman teburin ta dawo saman cinyoyinsa.
“Kar wani ya shigo fa”
“Babu wanda zai shigo sai ya nemi izini”
Sai da suka gaisa da likitan sannan ya haɗa shi da Rashida. Gaisawa kawai tayi da shi sannan ta sanar masa zata karɓi number sa, su yi magana.
Sai da ta saka number a wayarsa sannan ta sauka daga saman jikinsa, daman tayi samana hakan ne dan kar ya gano damuwarta tun da ta saba masa a duk lokacin data shigo office ɗin.
Duk da irin kibar da yake da ita bata hanashi saurin unƙurawa ba ya riƙo hannunta ganin zata wuce.
“Yau da wuri zamu tashi babu aiki da yawa”
“Eh amman zan je gida akwai abunda zan yi”
“Aiko dai yau na so mu haɗu”
“Gaskiya akwai abunda zan yi, yanzu fa haɗuwar mu zata riƙa wuya, ƙara kaje gurin matar kawai”
Bata tsaya jiran abunda zai ƙara cewa ba ta fice daga office ɗin.
Lokacin data dawo office ɗinta zaunawa tayi ta ƙare duka aikin dake gabanta, sannan ta ɗauki wayarta ta kira likitan. Bayan sun gaisa ta gabatar masa da kanta.
“Sunana Aisha bee Omar, akwai wani cousin ɗina dake fama da matsala sai yaje asibiti aka bashi gwajin jini, to ina son idan ya kawo ka min a yi masa a kira ni a sanar dani dan Allah”
“Amman miyasa Hajiya?”
“Idan ka kawo ka sanar min zan faɗa maka ko minene, ka turo min account number ɗin ka”
“A wannan Asibitin bama yin abunda ya tsaɓa doka, hakan kan iya ja mana ɓacin suna a asibitin nan”
“Ba taka doka zaka yi ba, ceton rai ne idan har ya kawo ka faɗa min dan Allah”
“Miye sunan shi?”
“Sunan shi Hilal”
“Okay”
“Karka Manta ka turo min account number ɗin”
“Alright”
Yana kashe wayar ya turo mata account number ɗin. Ta jidaɗin ganin number, ga dukan alama zai yi saurin bata haɗin kai, jiki na rawa ta tashi ta fita daga office ɗinta, ta je ta cikin bankin ta masa transfer 100k.
NAMRA POV.
Yau ba laifi ta samu bachi dare, duk da ba mai nauyi bane sosai, minti goma ashirin zuwa ashirin da biyar take farkawa.
Sai dai a duk farkawar da take, a zaune take ganin Mardiya tana kallonta kamar wata mayya, tun Namra tana dauriya ta koma bachi har ta gaji ta tambaye dalilin rashin bachin nata.
“Wallahi na kasa bachin ne mafarkin tsoro nake, kusan kwana biyu yanzu haka na ke”
“Kiyi addu'ah kawai ki kwanta, babu abunda zai same ki, ki karanta Ayatul kursiyu ƙafa uku ko wace da bismillah wallahi har garin Allah ya waye babu abunda zai same ki”
“Toh na gode zan gwada”
Ta faɗa da damuwar a muryarta. Komawa Namra tayi ta kwanta ba ita ta fake farkawa ba sai asuba.
A kulolin gidan ta ɗauka ta zuba musu ɗumamen tuwo da Maman Mardiya tayi, sannan tayi wanka ta ɗauka ta nufi asibitin.
Ko da ta isa ta tarar har sun siye tea a bakin asibitin sun karya. Mama bata wani sake da Namra sun gaisa ba, ciki-ciki ta amsa masa gaisuwarta, ta fice tama watsa mata wani kallo a kaikaice kamar wata kishiryarta.
Hakan be dame Namra ba, dan ita ta san muhalin data aje ta a yanzu, tun da ta fara fahimtar tafiyarsu.
Bayan kamar minti talatin da fitar Mama Asim ya ɗauko dubu goma sha biyar ya miƙa ma Namra.
“Ga wannan ki siye wasu abubuwan na gida, Mama zata siyo katifa da wasu kayan”
Namra ta jidaɗi sosai, daman zama gidan su Mardiya ya fara isarta, duk da tasan kuɗin ba zasu isheta hakan be hanata nuna farincikinta ba.
“An biya kuɗin maganin ne har wasu sun rage?”
“Eh ɗari biyu matar ta ara mana, Allah dai ya ba ni ikon biya”
“Amin, amman Asim shabiyar zasu isa siyayya kuwa? Ba mu da komai fa kasan komai ya ƙone”
“Haka nan za a matsa ayi Namra, bafa irin siyayar gidan ku zaki yi ba, ta talakawa zaki yi, kamin mu ga abunda Allah zai yi kuma”
“Toh Allah ya taimaka”
“Amin, likitan yayi min allurar ɗaya ɗazu, kuma yace ya kamata na ɗan fara taka ƙafar, koda ina riƙa wani abun ne”
“Aiko ya kamata ka fara tun yanzu”
“A'a sai nan gaba, gaskiya ni tsoro nake ji”
Ta ɗanyi dariya, tana mamakin irin rakin da Asim yake da shi. Asibitin ta wuni sai da yamma ta koma da zimmar taje Mardiya ta raka ta kasuwa suyi siyayya. Bayan tafiyarta Mama ta siyo abinci a bakin asibiti ta ci, ta kawo mo Asim, dan kwata-kwata ƙwara tayi daga ɗakin har sai da Namra ta tafiyarta, sannan ta dawo, Mama irin mutanen nan ne da basu iya samun arziki ba, waɗanda idan abu ya same su a take suke canjawa mutum, ga shegen son su yi kuɗi kamar hauka, tana daga cikin mutanen da suka tsani masu arziki, suna ganin kamar Allah ya fi son su da su, ita a nata rayuwar bata ƙi Asim yayi arziki ba ta kowa ne hali, ko dan ya rama abunda iyayen Namra suka masa.
ABDOOL POV.
A hankali yake tsotsa bakinsa kamar mai shan minti, sai wasa yake da drink ɗin dake gabansa ya kasa sha.
“Saboda Mai Martaba yace yana son ganin ka shiyasa ka wani damu ko?”
Ya ɗan ɗaga kai kaɗan ya kalli Ummi da idonsa na marar gaskiya.
“Eh mana, na san ba zai wuce yayi min maganar aure ba”
“Ai dole yayi maka maganar aure, tun da kai baka san ka girma ba, ace ko wace mace baka so, kwana ki har ƙaryar ciwo kayi min sai gashi likitan ya ƙarya ta ka, wai anya ba aljana take auren ka ba?”
Yayi dariya yana kallon ƙannensa mata su huɗu da suke zaune a ɗayan ɓangaren na falo suna sha'aninsu.
“Abdool ya kamata ace kana yi ma kan ka faɗa, mahaifin ka yana son ka, kar kayi abunda zai sa kyaunka ya ɓace a gare shi, kasan ƴan da matan uban nan naka suke, basun ka suke su kuma zuga shi zasu yi ta yi har sai sun ga taren ku ya ɓace, duk kuma wanda bashi da uwa a cikin gida yana cikin matsala dole ne yayi taka tsantsan”
Ya shafa kansa, yana jingina da kujerar dinning ɗin.
“Ummi Mai Martaba na da wani buri akai na, shiyasa ya natsa nayi aure, ni kuma bana son sarautar nan, ni kwata-kwata ma ba dan shi ba Wallahi da ba zan zauna ƙasar nan ba”
“Amman ai ba kai kaɗai ya haifa Namiji ba, amman kai ne mafi soyuwa a ransa, to dan me ba zakayi masa abunda zai sa ya ƙara son ka ba? Indai baka fitar da wanda kake so ba sai ya kai ga ɗaukar wata a cikin gidan nan ya haɗa ku, idan kuma ka ƙi yarda kasan abunda zai biyo baya”
“Ummi wanda nake so ban san inda zan ganta ba, ban san yadda za'ayi na haɗu da ita ba”
“Kamar ya?”
Ta tambaya tana kai ƙwallon anabi a bakinta.
“A Funtua na ganta bakin wani pharmacy, na fita nayi mata magana, tace min matar aure ce ita”
“Ta faɗa maka ita matar aure ce kuma zaka so ta?”
“Sam bata min kama da matar aure ba mai igiya uku, sai da matar aure kalar aure, ina ganin wannan take nufi, irin ƴan matan nan ne masu aji sosai, har marina tayi fa”
Ummi ta gyara zamanta, irin na mutanen nan da naira ta zauna a jikinsu har ta nuna kanta, ga kuma milkin dake cikin jininta, na ƴaƴan sarakai.
“Wayw Uban ta a garin nan?”
“Wallahi nima ban sani ba, irin yaran nan masu mugun ji da kan su, kuma na rasa yadda zan yi na same ta, duk wata hanya da zata sadani da sake ganin ta nabi amman ba nasara, har abinci naje na raba a inda ake sa ran zan ganta amman ban ganta ba, kuma ni Wallahi ita nake so”
“To sai yaya kenan?”
“Sai na nemota duk inda na ganta zan gane ta, ba zata min marin banza ba sai na rama, kuma gaskiya ba zan haɗu da ita hakan nan ba ga dukan alamun ita ce, dukan matan da nake haɗuwa da su ban ji komai akan su ba sai ita”
Ya faɗa yana mai tashi tsaye.
“Anya ba aljana ka haɗu da ita ba Abdool?”
“Ba aljana bace Ummi”
A faɗa yana dariya, zuwa yayi ya mata side hug, ya ɗauki anabi ɗaya ya kai a bakinsa, na biyu kuma ya jefe ƙannensa da shi.
“Ummi ki tsara min yadda zan cewa Mai Martaba”
Be tsaya jiran abunda zata ce ba, ya fice daga falon yana murmushi. Da kallo Ummi ta bishi tana mamakin yadda ɗan nata yake ƙoƙarin zame mata aljani.
ANTY AMARYA POV.
Tun da Abbah yake maganar bata ce uffan ba har sai da ya kai aya. Sannan ta sauke ajiyar zuciya tace.
“Zan musu magana, ai dukan su suna da manema, daga Hindatu har Maryam ɗin”
“Ƙara ayi musu magana su fitar da wanda suke so, da ba zan sake zaɓawa kowa miji ba”
“To, Alhaji nacw har yanzu baka je ganin Mijin Namra ba, ya kamata ko a waya ne ka kira shi ku gaisa”
“Ko Namra ce bata da lafiya ba zan kira ba, balle mijinta, ki daina kawo min wani bato daya shafi Namra, baki san irin baƙin cikinta daya ke cikin zuciyata ba”
“Toh ni idan ka min izini ina son na koma naje na ganshi”
“Ba zaki koma ba, idan be gode da ganin da kika masa ba, ya bar shi, ba familyn ta ya aura ba ita ya aura, kuma na sallama masa ita har abada, babu hannuna babu ƙafata a lamarin Namra, ta zaɓi wanda take so sai taje ta zauna da shi”
Ko kaɗan kalaman Abbah basu yi ma Anty Amarya daɗi ba, nan take ta canja fuska, ɓacin rai dake zuciyarta ya bayyana.
“Haba dai, wannan wane irin magana ne? Shikenan bata da damar ta zaɓi mijin da take so? Wannan sam ba adalci ba ne, baka ƙaunar yarinyar nan kamar ba kai ka haife ta, ɗan abu ƙanƙane sai ka ɗauki karan tsana ka ɗora mata”
Ta ƙarasa maganar da kuka.
“Ke kin fi kowa sanin na yadda na nunawa Namra so, ai ke ya kamata kiyi tunani kiga rashin dacewar abunda Namra tayi min, ko da ace ba ni na haife ta, ya kamata ace tayi min biyayya tun da nina raine ta har ta kai inda take yanzu, be kamata ta zaɓi wani ta bar ni”
Kukan Anty Amarya ta cigaba da rera masa. Shi kuma ya ɗauki jaridarsa ya buɗe yana karatu, ba dan kuma yana son karatun ba, sai dan yayi avoiding kukan na Anty Amarya, tana da matsayi a zuciyarsa, ba kasafai yake son kukanta an itace mafi soyuwa a zuciyarsa, duba da yadda take masa biyayya da kuma yadda take da ƙuruciya, sama da Hajiya Barau data kwana biyu.
Idan kuma ya biye mata yasan halinta yanzu ne zata birkice masa, har ya rasa gane kanta.
Data gaji da kukan ne, ta share hawayenta, ta tashi ta bar masa ɗakin.
Tana shigowa part ɗinta duka ƴaƴanta suka lura da yanayinta, ba ma kamar Maryam data fi damuwa da ita sosai.
“Anty Lafiya?”
“Lafiya ƙalau, kawai ina tunanin Namra ne, ban san halin da take ciki ba babu waya hannunta, kuma Abban ku yaƙi ya bar ni naje na duba su”
“Inshallah tana cikin ƙoshin lafiya Anty, kwana ki ma sai da ta turo da text wai ki taimaka mata da kuɗi, ni kuma na goge text ɗin dan nasan Asim ne zai sata”
“Amman miyasa baki faɗa min ba? Baki san halin da take ciki ba, ƙaddara ce ta riga ta faɗa mata babu yadda za muyi”
“Nayi tunanin ko shine yasa ta”
“Nawa tace a bata?”
“Bata faɗa ba”
“Gobe kije ki tura mata 300.000k sai ki kira wayar Asim ki faɗa mata, kuma kice ta siye waya tasa layin ta, kwana kin nan mafarkin ta nake ta yi, ban san halin da ƴata take ciki ba”
“Inshallah zan tura mata”
“Abbah ku ba ban saƙo gare ku, amman sai gobe zan faɗa muku”
Tana kai wa nan ta tashi ta nufi ɗakinta, tana share hawayen da suka zubo mata.
RASHIDA POV.
Tana gama aikin office ɗin ta dawo gida, tasan abunda ta shirya ma kanta shiyasa ta dawo da ƙarfe shida tsaɓanin tara na dare data saba dawowa.
Ɗakinsa ta shiga tana masa bincike ko zata ga takardun results ɗin ko kuma jinin daya ɗiba tun da yace mata be kai, amman bata ga komai ba. Har ta gaji ta dawo dakinta .
Duk da tasan yau ba a ɗakinta Doc take ba, hakan be hanata chaɓa ado ba, dan ta ɗauki hankalinsa. Daman ya saba duk wacce yake ba girkinta ba yakan shiga yayi mata sai da safe, sannan ya wuce ɗakin da zai kwana.
Tun kamin ya shigo ɗakin, ta haɗa masa tea da lemun tsami dan tasan yana son haka, ta kuma saka masa zuma a maimakon sugar, sai ta ɗauko maganin dake jakarta ta buɗe ta kaɗa masa cikin tea ɗin har kusan guda biyar.
Tana mayarda jakar ta aje yana turo ƙofar ɗakin ya shigo, gabanta ya faɗi, abun ka da wanda bata saba ba, sai dai ta wayance taje ta rumgume shi.
To her surprise sai ya sauke hannayensa daga saman wuyanta, yana ɗan murmushi. Bata damu da abunda yake mata ba, dan a tunaninta fushin ɗazun ne na dress ɗin ta tayi. Cup ɗin tea biyu ne sai ta ɗauki ɗayan ta miƙa masa.
“Ga tea”
Hannu ya kai ya karɓa ya furta
“Thank you, good night”
Har ya juya, sai kuma ya juyo ya kalleta kamar zai ce wani abu, sai kawai ya sakar mata murmushin irin na fatar faki, ya juya ya fice.
Ɗakin Kalsoom ya nufa, ko da ya shiga ciki be ganta ba, ya duba bathroom bata ciki, sai kawai ya nufi ɗakin su Ezzah dan yasan ba wuce tana can ba.
A tsakiyar gado ya tsame ta tana ta tofawa yaransa addu'o'i, su kuma sai bachi suke tayi abun su. A bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yana murmushi, har ta gama ta taso ta nufo shi.
Hannu ya kai ya laƙƙamo kunkurunta, jikinta ya haɗe da nashi, ita kuma sai haɗiyar yawu take tana kallon kofin dake hannunsa, ƙamshin tea ɗin yana kai ma hancinta ziyara.
Kaɗan ya kurɓa ya kai mata kofin a baki, ɗan tsami tsamin data ji yasa ta jidaɗin tea, ta riƙe kofin da hannu biyu har sai da ta shanye tea ɗin gaba ɗaya.
Tana shanye tea ɗin ta saki kofin tayi masa kwance a jikin, wani irin bachi mai bala'in nauyi yayi gaba da ita.
“Hey...”
Ya faɗa yana girgizata, amman ina, tayi nisa har ƙoƙarin zubewa take a ƙasa, hannayensa yasa ya ɗauke ta cak, ya nufi ɗakinta da ita. Saman gado ya kwanatar da ita ya kwanta gefenta yana shafa fuskarta, zuciyarsa cike da mamakin abunda yake cikin tea ɗin.
Ya kusan minti talatin a gurin kwance, sai yaƙi yake da bachin dake son sace shi, yana unƙurin tashi yaji an turo ƙofar ɗakin, ƙin motsawa yayi sai ya lumshe ido kamar yayi bachi, sai ga Rashida ta ƙaraso har gurin tana leƙen fuskarsa, har da sa hannunta tana masa yawo da shi dan ta inda gasken yayi bachin.
Da sauri ta juya ta fita ta nufi ɗakinsa, keys ɗin motarsa ta ɗauka, ta fito waje ta buɗe motar tana masa bincike, seat ɗinsa na gaba ta buɗe ta fara bincikar takardun da suke gurin. Jikinta ne ya bata ana kallonta, da sauri ta fito daga motar, sai taga Doc tsaye ya rumgume hannayensa yana kallonta.
Kasa motsawa tayi, numfashita mai sai da yayi nisan zango sannan ya dawo, jin tayi kamar ƙasa ta buɗe ta shige ciki, a take mararta ta cika da fitsari.
___________________________________________
One free Page remained 🙌
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 35. Last Free Page*
NOT EDITED ⚠️
Bata taɓa sanin gume na da zafi ba, sai a wannan lokacin, wani irin nauyi ta ji kanta yayi kamar an ɗauki duniyar nan an ɗora mata, yau ganin Hilal take ya cika ko ina na duniyar idanunta.
Yau kam ba ranar kuka ba ce, tashin hankalin daya same ta ya fi ƙarfin kuka, hakan yasa hawaye ba kusanci idonta ba, ashe abu mai sauƙi ake ma kuka, ta kasa yarda yau ita ce Hilal ya kama dumu-dumu ba.
“Kin san kina da HIV kike ƙoƙarin ɓoyewa Rashida? Do you know what lokacin dana ɗibi jinin ki result ɗin ba ɓata yayi ba, nace miki haka ne saboda ban yarda da abunda idona ya gani ba, na dawo na ɗibi jininki da na yarana da na Kalsoom nawa dan na gwada, so that na tabbatar idan da gaske kina ɗauke da cutar ne, amman ke kin san kina ɗauke da cutar kika bar ni ina kusantar ki?
Da ba dan wanann cikin ba, da sai mu ɗauki dogon lokaci a tare da dake baki faɗa ba right? What if all of us mun kamu da cutar nan?”
Ƙiri-ƙiri tayi masa da ido, cikin ƙarfin hali ta cira ƙafarta da tayi mata mugun nauyi ta tako ta ƙaraso kusa da shi.
“Kana tabbacin ni ce kaɗai nake ɗauke da cutar? Kasan ta ina cutar ta shige ni? Miyasa idon ka zai rufe har haka?”
“Ke da kan ki kike zargin kan ki, dan me zakiyi ma Doc Sabo transfer 100,000k? Dan me zaki ce idan ya kawo jinin kamin ya auna ya kira ki? You late Rashida ko da kika kira shi na riga na kai jinin amman yaƙi ya faɗa miki saboda ya san ni kamin ya sanni kuma ya san aikinsa, daman nasan ziyarar da kika kawo min ɗazu a office bata banza bace cox na lura dake kwata-kwata hankalinki baya jikin,
Bincike da kika min da tambayoyin da kika min ya tabbatar da akwai wani abu, and now what kin sa abu a tea ki bani nasha so that kiyi iya binciken ki ko? To bari na faɗa miki if something happens to my wife hmmm you're in trouble”
Sai a yanzu hawaye suka samu damar cika idonta har suka silalo zuwa kumatunta.
“Saboda na san idan kasan ina da HIV ba zaka faɗa min ba, idan har ya tabba ina da HIV Hilal to ta hanya ɗaya na same shi, wato sex kuma wani namiji be taɓa kusantana ba sai kai, a lokacin dana bar ka ya kusance ni ban san komai ba, sai a ɗazu nasa an nemo min Doc Sabo saboda na tabbatar idan har da gaske ina cutar ne, do you know who i try to protect? You and your dirty wife, Asmee told me everything about your bride but very soon gaskiya zata yi halinta, kuma ba zan taɓa yafe mu ku ba, aje ayi gwajin”
Tana kai nan ta raɓa gefensa ta wuce cikin falon. Juyowa yayi ya bita da kallo zuciyarsa na raya masa abubuwa da dama.
Kalamanta basu kama zuciyarsa ba, amman suna ƙoƙarin zaunawa akansa, what he believe shi dai yana da protection ɗin da ba kasafai cutar zata yi saurin kama shi ba, ko baya da protection, he's Doctor ya san cutar bata saurin kama namiji kamar mace, dan namiji ɗaya mai hiv zai kwanta da mace goma to dukkan su sun zama patient living with hiv, wato sun shiga sahun masu dauke da HIV acikin al'umma.
Amman mace ɗaya mai HIV zata kwanta da namiji 10 a rana, abu ne mai sauki namiji 2 ko 3 suka mu da wannan ciwon mai karya garkuwar jiki. Namiji zai iya daukan HIV kawai idan yana da wata kafa a gabansa abunda ya shafi kurji, yanka ko tsaga.
“He's lie”
Ya furta a hankali, yana murza saman goshinsa, zuciyarsa ta kasa yarda da zancen ta, duk da yasan Kalsoom take nufi, dan ita daya auna jininta be nuna haka ba, amman yasan result ɗin zai fito kuma dole gaskiya tayi halinta.
Shigowa yayi cikin falon cikin tunani da sarƙaƙiya, a saman babbar kujera ya zauna, ya dafe kansa, ɗaurewar da kansa yayi shi ya hana shi bachi har safe.
Har yayi sallah asuba ya dawo, be ji motsin Kalsoom ba, ita daya san wani lokacin ma takan riga shi tashi, a falon ya zauna yayi addu'o'insa sannan ya shiga ɗakinta, yadda ya tararda ita kwance rigingim har sai da ya tsorata, wani irin ninshari take kamarmacijin nan mesa na bachi, yayi mata girgizar duniyar nan amman ina, in ma ban da ƙara nauyin bachi babu abunda take.
Da sauri ya fita ya shiga ɗakinsa duba keys amman be ganshi ba, sai a lokacin ya tuna da suna guri motarsa da Rashida ta saka su jiya, da sauri ya fita daga ɗakin ya nufi gurin motar, ashe ma buɗe ta kwana, shiga kawai yayi ya kunna ta ya bar gidan.
Rashida na jin tashin motarsa ta duba agogon ɗakinta, 6:55am ya nuna, bata damu da rashin warewar gari ba ta tashi ba tare data tsaya wanka ba, ta canja tufafin jikinta zuwa atamfa ta ɗauki abaya ta ɗora sama, sannan ta ɗauki handbang ɗinta ta fice daga ɗakin.
Cikin sauri ta shiga motarta tayi mata keys gudun kar Hilal ya dawo, dan yanzu kam sam bata son haɗa ido da shi.
Gidan su Asmee ta nufa, cikin ƙanƙanen lokaci ta isa, haka ta riƙa musu horn har sai da mai gadin ya buɗe mata gate, kusan da motar Alhaji Bashir ya faka motarta, daman tasan yana nan dan yanzu be isa fita ba. Ƙofar falon ta riƙa bugawa tana sallama kamar zata tashi gidan.
Alhaji Bashir ne ya buɗe mata ƙofar yana tambayar lafiya, dan tun da yaji muryarta hankalinsa ya tashi, a tunaninsa ko tazo tayi masa wani abun ne.
Tun daga samansa ta kalle shi har zuwa ƙasan shi, daga shi sai guntun wando, sai da ta kai zuciyarta nesa sannan ta iya ƙirƙiro murmushi ta yaɓa a fuskarta.
“Matar ka na nan?”
“Lafiya kika mana sammako haka?”
“Lafiya ƙalau, sirrin mu ne, saƙon zan bata”
Kamin ya ƙara cewa wani abu har Asmee ta ƙaraso gurin tana tambayar wanene.
“Nice na doko muku sammako, saƙon ki zan baki”
Rashida ta amsa da kanta, tana mata murmushi. Wani kallo Asmee ta watsa ma Alhaji Bashir, irin ya zaka zo daga kai sai guntun wando haka. Sai kawai ya juya ya shige ɗakinsa.
Asmee ta riƙo hannunta suka shigo falon.
“Ke lafiya kika zo haka?”
“Taimakon ki nake nema, idan har baki taimake ni ba, zamu iya rasa ran mu ni da mijina”
“Subhanallahi miya faru?”
“Mijina ya aiko ni zuwa gare ki, maganar da zan faɗa miki sirri ce bana son kowa yaji, ko da kuwa mahaifiyarki ce ko mijin ki”
“Ban taɓa sirri dake ba na faɗawa mahaifiyarta ba, balle kuma mijina taso muje ciki”
Dar ƙarshen gadonta, Asmee ta kai ta suka zauna, sannan ta kalle ta tace
“Faɗa min damuwarki, matuƙar ina da maganinta wallahi zan miki”
“Irin samarin nan nake nema kidnappers”
Asmee ta daki ƙirji.
“Aka yi da wani ko za'a miki?”
“Wani muke son a a ɓoye mana shi, saboda ta hanyar shi ne kaɗai ne, mijina zai cigaba da rayuwa da ni, dan Allah idan kin san inda irin mutanen nan suke ki faɗa min”
“Ni ɗan maye ma miye haɗina da shi balle kuma ɗan kidnapped, Wallahi ban san wani mai wannan aikin ba”
Rashida ta kama hannayenta ta riƙe ta fara kuka.
“Ko cikin ƙawayen ki ba kisan wacca tasan mai irin wannan aikin ba? Dan Allah Asmee ki ceci rai na”
“Bana da ƙawar da zata iya faɗa min sirrinta har haka sai ke, ko da suna da irin waɗannan mutanen ba zan iya sani ba, sai idan gurin wannan Malamin zaki je, sai ya haɗa ki da wani cikin masu zuwa gurinsa, dan yana basu taimako sosai”
“A ina Malamin yake? Dan Allah ba ni addireshinsa”
“Ba a cikin garin nan yake ba, a ɗan dutse yake da kin shiga garin ɗan dutse kika ce Malam mai gobe da nisa ko ƙaramin yaro yasan gidan sa, bari na baki number wayarsa, kamin ki isa zan kirashi na faɗa masa”
“Na gode Allah ya saka miki da alheri, samin number”
Ta faɗa tana miƙa mata wayarta. Sai da Asmee ta saka mata Number sannan tace
“Amman kin san garin kuwa?”
“Karki damu zan tambaya har na isa garin, ai bada motana zan je ba, gidan mu zan bina na aje motar, saboda gudun sa ido”
“Allah yasa a dace, amman ina jin tsoro Rashida”
“Babu abunda zai faru, ba mummunan abun zan aikata ba”
“Dan Allah aro min niƙab ɗin ki da Hijab”
Ba musu Asmee taje ta ɗauko mata ta saka.
A gaggauce ta fice da daga gidan, zuciyarta har wani ɗar-ɗar take, tana ayyana irin rashin mutuncin da zatayi Doc Sabo, lallai yau zata nuna masa ta fishi zama yar duniya, Zagon ƙasan da yayi mata ƙarami ne, yanzu zata masa babban.
Kamar yadda ta tsara, a gidansu ta biya ta aje motar, ko cikin gidan bata shiga ba, balle su gaisa da Momi, tana rufe motar ta fito ta tari Napep ta shiga, ya ɗauki hanyar tasha da ita.
HILAL POV.
Be daɗe ba ya dawo, daman allurai kawai yaje ya ɗauko, yana shiga ɗakin ya haɗa allurar yayi mata, sannan ya ɗauko tawul ya jiƙa shi da ruwa, ya riƙa dafa mata a goshi.
A hankali ta fara motsi tana nishi da miƙa irin ta gaji sosai ɗin nan, hankalinsa ya ɗan kwanta lokacin daya ga ta buɗe idonta, sai ya sakar mata murmushi.
Daker ta unƙura ta tashi zaune, saboda nauyin da jikinta yayi mata.
“Wane irin bachi nayi haka?”
“Magani na saka miki a tea ɗin, tashi kiyi sallah”
Ta ɗan kalli window taga yadda rana ta fara hudowa, sannan ta unƙura da zimmar tashi tsaye, sai Doc ya kai Hannu ya riƙa hannunta.
“I trust you Kalsoom dan Allah kar ki bani kunya”
Wani kallo tayi masa, irin ban gane ba. Sai kawai yayi murmushi yana ƙoƙarin ɓoye feelings ɗinsa.
“Yanzu idan aka ce ina da hiv zaki zauna da ni?”
Dawowa tayi ta zauna, ta kai hannayenta ta riƙa fuskarsa.
“Idan har kana da hiv zan zauna da kai, kuma idan har kana da shi nima nasan ina da shi, so babu dalilin ƙyamar juna”
“What if aka ce ke kike ɗauke da shi ba mu ba?”
Shiru ta ɗan yi tana nazarin tambayoyinsa, anya Doc zai mata irin wannan tambayar haka kawai.
“Idan har ni nake ɗauki da cutar zan nisanta kai na daga gare ku, gudun kar ku kamu da cutar, har sai ta zama aids, domin wannan kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) bata rayuwa da keu a wajen jiki, saboda haka akan iya kamuwa da ita ta hanyar kissing ko kuma yin anfani da wani abu wanda me dauke da cutar ke anfani da shi, kamar kofin shan ruwa, abun yanke farce, da brush.
Amman da zarar cutar ta kai marhala na karshe ma`ana AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) zan cigaba da mu'amala da ku kamar yadda na saba, saboda ba`a kamuwa da ita ta hanyar kissing, cin abici tare da me dauke da ita, amfani da kayayyakin ko abubuwa da me dauke da ita ke anfani da su, kamar kayan sawa, wayan salula, agogo, wanka a swimming pool, zama a kujera, cizon sauro, ma taci comb, tawul, da kuma tafiya, hada hanu, zama,da yin aiki tare da me dauke da cutar, amman ba zan bari ka kusance ni ba, ko da kuwa zaka na shan magani da amfanin da kororon roba, saboda it's risk.
Sai dai kuma ka sani, rayuwata zata tarwatse zan nisanta da ƴaƴanka, duniya zata ƙyamace ni, kuma dole na rabu da kai”
Ta ƙarasa maganar hawaye na bin fuskarta. Ɗan murmushi yayi ya tashi yana ƙoƙarin ɓoye hawayen da suka cika masa ido.
“Intelligent woman, je kiyi sallah zan haɗa ma yara breakfast”
Har ya fice hawaye take, zuciyarta cike da tunanin abunda yasa Doctor yayi mata wannan tambayar.
NAMRA POV.
Ko ta koma gida, ta samu duk sun tafi walimar aure, ta wata maƙociyarsu, da ake yi yau jumma'ah. Mardiya ce kawai a gidan, ta zauna cikin ɗakin ta rafka uban tagumi.
Sallamar da Namra tayi ma sai da ta firgita ta.
“Ke lafiya kike kuwa? Ke kaɗai aka bari a gidan?”
Namra ta tambaya tana zama kusa da ita. Ajiyar zuciya mardiya ta sauke.
“Kawai ina tunanin rayuwa ne”
“Rayuwa kuma kamar ya?”
Shiru tayi tana tunanin irin ƙaryar da zata yi ma Namra, dan bata son faɗa mata asalin abunda yake damun ta.
“Inna ce duk ta bi ta dame ni akan rashin auren nan, kamar ni nayi ma kai”
“Ayyah wai wani abun ba'a kusa yake ba, komai yana da lokaci”
“Na sani matsalar iska ne yake damuna, ina ganin kamar shine ya hana ni aure, amman ita inna ta kasa ganewa”
Ta bijiro da damuwarta a fuskarta kamar da gaske abunda yake damunta ɗin kenan. Ita kuma Namra sai tausayinta take.
“Ki riƙa azkar kina faɗawa Allah damuwarki, inshallah zai miki magani”
“Ina yi Wallahi babu inda ba mu shiga akan neman taimako ko ina sai ace mana Aljani ne ya aure ni”
“Subhanallahi, amman Mardiya, ai dole aljani ya aure ki tun da kina yawo babu ɗankwali, gashi kina yawan sauraren waƙe-waƙe, da ace baƙara kike yawan karantawa nayi imani ba zai samu nasara akan ki ba”
Ajiyar zuciya Mardiya ta sake saukewa, a karo na biyu, ta ƙara gyara zamanta.
Namra ta kalleta cike da tausayawa tace
“Ki samu allo ki rubuta suratul azari, daga farkon ta har ƙarshe, idan kin yi alwala la'asar kika rage ruwa sai kiyi amfani da su ki wanke rubutun ki shanye har kwana uku, indai matsalar aljani ne mai hana aure inshallah zai rabu da ke”
“Na gode sosai Inshallahu zan gwada”
“Allah yasa a dace, da naso ki raka ni kasuwa amman naga kamar kina cikin damuwa bari mu bari har gobe”
Kamar kar Namra tayi maganar nan da nan Mardiya ta kai idonta gurin ƙaramar jakar da Namra take riƙe da ita, sai kuma ta kawar da kai.
“Mu bari har goben dai yanzu yamma yayi”
“Eh nima ai haka na gani”
Ƴar nokiyar dake hannun Mardiya ce tayi ƙara, sai ta tashi ta bar ɗakin tana amsa wayar.
Tashi Namra tayi ta cire hijabinta, ta rataye, sannan ta ɗauki jakar wanda kuɗin suke ciki ta saka a cikin akwatin Mardiya na kaya, da zimmar ta aje a cikin dan kar taje ta jefar da ita wani gurin, sannan ta fita ta kama ruwa.
RASHIDA POV.
Data isa tasha, shatar motar ta ɗauka ita kaɗai, ya kai ta ƙauyen. Bata sha wahala ba gurin gane gidan, tambaya ɗaya suka yi aka nuna musu gurin, gidan ne mai kyau kamar ba ƙauye ba. Sun tarar da layin mata sosai a gurin haka ta samu guri ta tsaya har aka kai gareta. Sannan ta shiga.
Ƙaton ɗaki ne mai cike da kayan alatu, ba dan rawanin da taga ni a kansa ba, da zata iya rantsuwa da Allah tace wani attajiri ne ba malami ba, sai dai hakan be bata mamaki ba, dan tasan duk mutumen dake aiki da manyan yan siyasa dole ne ya tara komai.
Kallo ɗaya yayi mata ya soma gyara ƙasar dake gabansa yana faɗin ta cire niƙabin ta, ba musu ta cire niƙab ɗin tana gaishe shi. Be amsa ba har sai da ya gama bugun ƙasar sa, sannan ya kalleta yace.
“Kin zo nan ne dan a haɗa ki da wani yayi miki wani aiki”
“Haka ne ni ƙawar Asmee ce, tace zata kira ka”
Sai da ta ciro dubu hansin ta aje masa a gabansa, sannan ta koro masa da bayani. Sai da ta gama sai yayi murmushi yace
“Zan haɗa ki da wani, saboda kawai Asma'u ce ta turo ki, amman ba dan haka ba, babu abunda zai sa na haɗa ki da shi, saboda shegen mutum ne, ni kaɗai zan iya sashi abu yayi nan take”
“Na gode Malam, idan har aiki yayi kyau, kai ma zaka jidaɗi inshallah”
Wayarsa ya ɗauka ya kira, yayi tsowon minti ashiri yana lalasar mutumen sannan yaba Rashida waya suka yi magana ya faɗa mata inda zata same shi.
Bayan sun gama malamin ya kalleta yace
“Idan buƙatata da biya ki dawo ina son ganin ki, dan gaskiya akwai matsala a tare da ke, kuma akwai abunda yake shirin faruwa da ke, dole ne sai kin nemi taimako”
“Inshallah, zan dawo”
Da tsoro tayi masa sallama, tana ta tunanin wane irin matsala ne, zuciyarta nata raya mata lallai wannan malamin yana aiki kam.
Tafiyar mintuna arba'in suka yi, suka dawo cikin gari, kai tsaye tace direban ya nufi American Unique Estates da ita, a dai-dai inda ya kwatanta mata ta tsaya, ta kira number da Malamin ya bata ta mutumen tace masa tana gurin, sannan ta sallami direba fiye da yadda suka yi jingar.
Tsaye kawai take a gurin amman babu natsuwa a tare da ita, ji take kamar wani zai zo ya ganta. Bayan kamar mintuna asirin da biyar wata ƙafirar mota ta faka gabanta.
Wani Namiji ne mai shigar mutunci ya fito cikin motar tare da Amira.
“Ke ce Rashida wacca Malam ya aiko?”
Namijin ya tambaya.
“Eh nice”
Amira ta buɗe mata Motar.
“Shiga muje”
Da tsoro ta shiga motar, zuciyarta duk bata natsu da su ba.
___________________________________________
Assalamu alaikum as i said yau na kai Page 35, that's means na gama free pages kenan. Dan haka duk mai son ƙarashin wannan labari zai iya turo ₦200 zuwa wannan account 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.
Sai ku turo da shaidar biyan kudin wato screenshot ta wannan number 08036126660.
Zan saka ku group inda zan riƙa updated littafi kullum inshallah.
Na yi haka ne duba da yadda wasu suke ci da gumi na, akwai wanda ya ƙirƙiri grp a whatsapp ana tura masa naira ɗari yana tura littafan marubutan online cikin har da nawa, sannan akwai wanda ya ɗauki littafina na MAIRO ya maida shi application ya ɗora a Google play store, wanda duk yayi downloading ɗin app ɗin sai google sau biya shi, idan kuma suka ɗora talla a app ɗin kuma wannan shima sai sun biya shi, ni da nayi rubutun ban ci ba shi ya ci. Bayan haka an ɗauki littafina na SALEENA an saka a okadabooks, ba tare da izini na ba, wanda idan aka siye kuɗin zasu je ga wanda ya saka littafin ne ba gare ba, idan kukayi searching duk zaku ga abunda nake faɗa muku na Application da okadabooks.
Dan haka ya sa na canja wannan littafin uzuwa na kuɗi, dan nima na ci amfanin abuna, da wani ya ci da gumminka ƙara ka san kai ka ci, ko yayane, dan baka san ta rai ba. 😀
Ina roƙon duk wanda na ɓatawa rai sanadin canjin nan ko kuma littafin nan, dan Allah ku yafe min, nima ban za ci sauyin zai zo ba, sai daga baya, da tun farko na faɗa. Ina roƙon alfarma dan Allah kar wanda ya mai da min da Littafi document.
Na gode da shawarwari da ƙauna, Allah ya sakawa kowa da Alheri. I love you all
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 36*
NOT EDITED ⚠
Nitsa kai suka yi tayi cikin unguwar, sun yi tafiyar mintina goma zuwa sha uku, sannan suka isa ƙarshen unguwar, a bakin wani makeken gate black color.
Tsoron dake cikin zuciyar Rashida ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a jikinta, gani take kamar wani abun zasu mata har ta buɗe baki tayi magana, sai ta tuna da abunda ya kawo ta gurin, kuma ta san bata da wata mafita sai wannan.
Sai kawai tayi shiru da bakinta ta sakar musu na mujiya har suka faka bakin wata babbar ƙofa. Amira ce ta fara fita tana faɗin
“Fito muje”
Buɗewa Rashida tayi ta fito, sai mutun ya ja motar ya nufi wani ɓangare na gidan da ita.
Amira tayi gaba, Rashida ta rufa mata baya sai kalle-kallen gidan take.
Cikin wani ƙaton falo suka shiga, wanda aka ƙawata da kayan alatu, kallon falon tayi sosai ba dan ya birge ta ba, sai dan ɗaukar rahoto ta karanci wane irin gida ne aka a kawo ta.
Kamar daga sama ta ji Amira na mata magana.
“Idan baki yarda da gidan ba, miyasa kika shigo? Ko kina tunanin za mu miki wanin abun ne?”
Kasa cewa komai, tayi har Amira ta gaji da tsayi a gurin, ta isa gaban wata babbar kujera ta zauna tana cire gyalen abayarta.
“Guy Son!”
Ta ƙwala mishi kira, tana nuna ma Rashida kujera.
“Zauna idan zaki iya”
Rashida ta zauna zuciyarta na ɗar-ɗar, wani tunanin ne ya zo mata. What if tafa mutumen data sani? Ko kuma gidan yana tare da Dr Sabo fa?
Fitowarsa yayi dai-dai da sauke ajiyar zuciyar da Rashida ta yi, a yanayin shigarsa da kamalarsa, bata zace shine Guy Son ɗin ba har sai da ya zauna kusa da Amira, jikinsa yana Gugar na Amira.
“Wa kike son ayi miki garkuwa?”
Ya tambaya, fuska babu alamar murmushi balle wasa.
“Wani mutun ne, sunan shi Doc Sabo a asibin Alex yake aiki sashen jini”
“Cire Niƙab ɗin fuskarki kiyi mana bayanin komai”
Tasa hannu ta cire Niƙabin ta gyara zamanta sannan tace
“Mijina ne ya ɗibi jinina dana yara na ya kai masa akan yayi mana gwaji, bana da tabbaci amman ina jin kamar ina ɗauke da cutar hiv kuma ina tunanin mijina da kishiyata basa da shi, na karɓi numbersa gurin abokin aikina na kira mun yi magana akan zai faɗa min idan mijina ya kawo jinin, har na tura masa dubu ɗari, sai gashi ya yaudare ya faɗawa mijina na bashi kuɗi”
Ya kai hannunshi ya riƙa hannun Amira yasa yatsunsa cikin nata.
“So kina son ayi forcing ɗinsa ya canja result ɗin ko?”
“Haka nake so, matuƙar ya faɗi gaskiya, mijina zai rabu da ni, kuma duniya zata ƙyamace ni, zan ba ku ko nawa kake so, dan Allah ku taimaki rayuwata”
Amira ta ɗan yi murmushi.
“Ba shi kike son ayi a ɗauke miki ba, ƴaƴansa za'ayi kidnapped sai asa shi dole ya faɗi abunda kike so”
“Koma yaya ne ni dai yi min zan biya ko nawa kuke so”
Ta faɗa tana karyar da murya irin tausayin nan. Wayar dake hannu ya karɓa, ya saka wata number ya kira, ana picking yace
“Zo nan ina neman ka”
Be fi mintuna uku da aje wayar ba, sai ga mutumen ya shigo cikin ƙaƙanan tufafi, yazo dai-dai shi ya tsaya, Rashida na kallonsa gabanta ya faɗi saboda jan idonsa.
“Ka bincika min addireshin Doc Sabo yana aiki a Alex hospital sashen jini”
“Okay Boss”
Sai ya juya ya fice. Guy son ya kalli Rashida ya ce
“Bani addireshin ki, kuma karki kuskura ba ni na ƙarya dan zan gano ki”
Gabanta ya faɗi sosai, kuma ta tsorata, bata son bashi na ƙarya tun da har ya gargaɗeta, sai dai kuma idan har ta ba shi adireshin na gaskiya, bata san abunda zai faru ba.
“Sunana Rashida Abdullahi Kardam ina aiki a Stanbic Ibtc Bank, mijina babban likita ne, yana aiki a Kaduna special hospital, muna nan GRA magaji road”
“You can go, zaki ga motar data kawo ki zata maida ke inda kike”
“Thank you”
Ta saka niƙabinta ta saka sannan ta ɗauki jakarta ta fice. Amira ta tashi ta nufi gurin window falon ta tsaya, tana kallon harabar gidan. Tana sinkayar motar har suka fice, sannan ta sauke ajiyar zuciya, ta jingina da gurin ta rufe ido.
Hannunshi yasa cikin jikinta yana murza fatar jikinta, ya fara shinshinar gefen wuyanta. Buɗe idon ta yi ta ture shi da dukan ƙarfinta.
Kallon da zai yi sai hawaye ya gani sun silalo daga idonta. Yarfarda hannu yayi ya cije fuska.
“So nawa zan faɗa miki bana son hawayen nan”
“Ka bar ni nayi kuka na, ai ina da dalilin kuka”
Hannu ya kai ya riƙe fuskarta iya ƙarfinsa ya matse ta.
“Ba dalili bane, idan har kina son iyayen ki dole ne ki koma gare su, amman kin kasa kuma kin ƙi ki faɗa min gaskiya, saboda kin san mugun abun da kika aikata”
Yana kaiwa nan ya wurgar mata da fuska gefe, ya wuce ciki. Da kallo kawai ta bishi idonta na hawaye, wani irin zafi zuciyarta ke mata, ita kaɗai tasan irin abunda take ji.
Bata ganin laifin kowa sai Uzair da Namra, dan sune suka rusa mafarkinta, suka gurɓata duniyarta, suka canja tunaninta, sun salwantar da farincikinta, sune sanadin barin gidan iyayenta, sune suka sa duniya ta zage ta, sun yi nasarar sauyata daga mutum zuwa mutum mutumen da kowa ke kallonta.
Lallai bata da maƙiya kamar su, bata da wani buri illa na ganin bayan su. Har yanzu zuciyarta bata lurar da ita illar abunda ta aikatawa Namra ba, bata ganin asirin ne ya koma mata, gani take kamar da haɗin bakin Namra Uzair ya cuce ta.
Tana son komawa gida amman hakan sai ya gagareta, idan ta tuna yadda ta bar kowa nata, ta watsar da karatun ta, ta dawo nan ta zauna, sai taji kamar ta haɗiye zuciya ta mutu.
Rayuwarta ta zame mata kamar mafarki, yadda sauyin yazo mata, sai yayi mata kamar a shirin fim ko littafi, silar su ne take a cikin halin da take ciki. A yanzu kan bata da mafarki sai na Namra da Uzair bata da buri sai na su.
Ƙarar buɗe ƙofar gidansu da tayi ta fita ne ya dawo mata sabo, yadda ta kai kanta har tasa ta bar garin sokoto ne ya riƙa mata yawo a ƙwaƙwalwa.
Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da wani irin mahaukacin kuka, tana yagar fuskarta. Da sauri Guy son ya fito daga ɗakin daya shiga yazo ya rumgume ta yana rarrashinta.
“Shiiiiiiiiiii, I'm sorry Amira, I'm so sorry”
Ya ɗora kansa saman na ta yana girgizata, alamar lallashi, har cikin kansa yake jin kukanta, son ta na masa yawa a ko ina na gaɓoɓinsa.
RASHIDA POV.
A inda suka ɗauke ta ɗazu, mutumen ya sauke ta, sai ta tari Napep ya kai ta unguwar da iyayenta suke. A nesa da gurin tasa ya sauke ta ta sallame shi, sannan ta taka da ƙafa ta ƙarasa cikin gidan.
Sai da ta buɗe motarta ta saka jakarta sannan ta, ta shiga cikin gidan, bakinta ƙumshe da sallama. Da far'ah Momy ta amsa mata.
“Ma'aikatan kuɗi yau a gidan na mu?”
“Wallahi kuwa, yau kin san babu aiki”
“Yau kuma har da hijabi! Aiko kin ga yadda ya fitar da ke, mashallah”
Zaunawa tayi tana murmushi.
“Momy kenan, shi saka Hijabi har wani abun ne?”
“Wani abun ne mana, shiyasa abokiyar zaman ki take burgeni saboda ta san kanta sosai, duk inda zaka ganta da hijabi zaka ganta, kin ga irin wannan matar? Da wahala wani namiji yayi mata maganar banza, Hijabi ne abu ne mai muhimmanci Rashida tun da har ki ga musulunci ya koyar da mu saka shi ai kinsan yana da kyau”
Ta ɗanyi murmushi, wanda be kai ciki ba murmushin rashin jindaɗin maganar da Momy tayi na Kalsoom.
“Nikan bana burge ki ko Momy?”
“Ba haka nake nufi ba, yadda ɗabi'unta da halayenta yake haka na so naki ya kasance, amman sai ki ari wata rayuwar ta daban kika ratayawa kanki, kika ɗauki wani hali wanda ban san inda kika samo shi ba kika laƙabawa kan ki”
“Uhmm Momy ban yi breakfast, yunwa nake ji sosai”
Ta faɗa da nufin kawar da wacan maganar ta Momy, shiyasa bata cikin son zuwa gidan ba, duk lokacin da tazo sai ance tayi wani abu ba dai-dai ba, yanzu ma abun ya wuce guri har abokiyar zamanta Momy take yabo, ita kam bata taɓa ganin uwar dake yabon kishiyar ɗiyarta ba sai nata uwar.
6ana ɗaya daga cikin dalilin dayasa Kalsoom ta zame mata ƙashin wuya, amman wannan matsalar da take ciki yasa ta ma manta da ita sai yanzu da Momy take tsokaro mata tsatsar ƙiyayyar da tayi mata katutu a zuciya.
A gidan da wuni, duk irin tambayar da Momy tayi mata na barin motar ta da tayi taje wani gurin, ƙin faɗar inda taje tayi, balle ma har ta faɗawa Momy dalilin zuwan nata.
Tasan bayan sallah magariba Hilal baya gida, dan a masallaci yake sallah magariba kuma baya shigowa gida sai anyi isha'i, hakan yasa ta dawo gida a lokacin, dan bata son ta dawo lokacin da yake nan.
Ta jidaɗin rashin ganin ɗaya daga cikin motocinsa hakan ya tabbatar mata da baya ma unguwar kenan, sai da ta cire hijabin ta bar a mota sannan ta fito, ta nufi hanyar falo.
Ɗora ƙafarta da zatayi sai gabanta ya faɗi, maido ƙafar tayi tayi baya-baya tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta kusan minti biyar a haka, sannan ta kai hannu ta tura ƙofar ta shiga, bata ga alamun motsin kowa a gidan ba, hakan ya tabbatar mata da dukansu basa nan. Sai da ta leƙa ɗakin yaranta, taga babu kowa sannan ta nufi ɗakinta.
Jakarta ta fara ajewa tana sauke gajiya, sannan ta cire tufafin jikinta, ta shiga banɗaki tayi wanka, ta fito.
Dressing mirror ta nufa, ta shafa mai da turare sannan ta zauna tana nazarin duniyarta, idan har ta aikata abunda take da niya, to asirinta ya rufu, sai ɗayan kuma tana tunanin makomarta, akan abunda take ƙoƙarin aikatawa. Wani dogon numfashi taja ta sauke. Sam bata lura da takardun dake saman gadonta ba har sai da ta unƙura zata tashi.
Gabanta ya faɗi, a iya tunaninta bata san ta bar komai a saman gadonta da zata fita ba, sannan yanayin takardar be yi kama da documment ko file ba. Matsawa tayi kusa da gando ta kai hannu cikinn rawar jiki ta ɗauki takardaun.
Tana fara karantawa ta ji kamar an mata shocking, wani abu yazo mata tsam tun daga saman kanta har zuwa cikin ƙafafunta, bata ankaro da duniyar da take ciki ba, har sai da jini ya fara bin ƙafafunta.
NAMRA POV.
Sai da yamma sosai ƴan gidan suka dawo, abun walima ɗaya Inna ta bawa Mardiya tace su raba ita da Namra. A tare suka ci, lemun da yake ciki Namra tacw ba zata sha, ta bar ma Mardiya.
Bayan sallah magariba, ɗaya daga cikin matan gidan ta kawo ma, Namra tuwon masara da miyar ganye, haka Namra tayi ta tura abincin ba dan tana so ba, abun ka da wanda be saba ba.
Kaɗan kawai ta ci ta bar ma ƙannen Mardiya saura, ta wanke hannunta, sai ta koma kusa da Maman Mardiya ta zauna tana labarta mata zasu koma BQ, Inna tayi mata murna sosai, har tana cewa zata ƙara mata da wani abun.
A daren sun sha hira, ita da Inna sai labarin rayuwa take bata, irin gwargwarmayar da ta sha kamin ta kawo yanzu, da kuma labarin ƙurciyarsu ta ƙauye, wani abun na dariya wani na ban haushi, wani kuma na ɗaukar darasi.
Sai kusan goman dare Namra ta kwanta, har kuma lokacin Mardiya bata gidan, kuma sam hankalin Inna be tashi ba, bata ma nuna damuwarta akan rashin sanin inda Ƴarta take ba. Sai kusan shabiyun dare ta dawo gidan, tana ta wani ƙunshen-ƙunshe, suna sun-sun ita da Inna a tunaninsu Namra tayi bachi.
Sai kawai ta warware Mardiya da ta zo da shi. Har suka ci suka cinye Namra bata motsa ba balle ta nuna musu idonta ba, sun tana bachin ƙarya har na gasken yayi gaba da ita.
*WASHE GARI*
Inna ta bada aka siyo musu koko da ƙosai, sai ta siyo ma Namra waina, dan ta lura sam bata son koko, tun farkon kwananta gidan. Sai da ta ci ta ƙoshi, sannan ta nufi akwatin Mardiya dan ɗauko kuɗinta, da zimmar ta siya ma Asim abinci ta kai musu.
Bata ga jakar a inda ta aje ta ba, sai ta sa hannunta tana ta lalabawa, wayan bata ji komai ba, wale akwatin tayi tana duba sama-sama ko zata ganta, amman bata ganta ba.
Zata canye hannunta kenan sai taji abu ya zargi hannunta kamar an soke ta da allura, da sauri ta janye hannun tana raki.
“Waisss Ina jakar nan ta shiga ne”
Sai ta soma ɗaga tufafin ɗaya bayan ɗaya, tana dubata, ganin tayi kamar be dace ta ya mutsa mata kaya ba, saboda neman jaka wata ƙila ma ta ɓoye mata a wani gurin, ƙara kawai ta tambaye ta.
Har zata mai da kayan sai abu ya faɗo daga cikin ɗankwalin atamfar Mardiya, dubawar da Namra zata yi sai ta ga wayarta, da sauri ta kai hannu ta ɗauka.
No it can't be her phone, ta duba wayar gaba da baya.
“Wayata ce wannan this is my phone, how... ”
Sai kuma tayi shiru, tana nazari. Da sauri ta barkata kayan ta kai har ƙasan akwati, sai ga sarƙarta, da wasu manyan ƴan kunne nata, da agogon ta. Da sauri ta ɗauki ta miƙe tsaye tana mamaki.
Cikin wani irin bachin rai ta fito waje ta isa har inda Mardiya take zaune suka fira da Matan gida, ta ɗauke ta mari. Namra bata damu da matan da suke cikin gidan ba haka ta shararawa mardiya mari har huɗu tana hawaye.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 37*
NOT EDITED ⚠
Sare saren jini ne ya fara zubar mata, amman hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma gurin takardar.
‘Ga result ɗin da kike nema nan, da kuma wanda Doc Sabo ya bani jiya, ranar Monday, na biyun zai fito, idan har baki tsallake ba, za'a sake miki na uku, bana son kowa ya san sirrin mu, na yi alƙawarin rufa miki asiri saboda ƴaƴanmu, amman ba zan zauna dake ba Rashida idan har hakan ya tabbata, kar ki kuskura canja komai kar kiyi unƙurin yin komai, har sai gaskiya ta bayyana kuma na baki damar zuwa gida idan kina da buƙata, bana son wata alaƙa ta sake shiga tsakanin ki da su Ezzah a yanzu’
Taya zai mata katanga da yaranta? Taya asirinta zai tono tun yanzu, ba zata iya jure rashin Hilal ba ta shirya sadaukar da rayuwarta a gareshi, tana son mijinta, miyasa zata farka daga bachi tun yanzu? Baya mafarkinta be ƙare ba?
Wani irin ihu ta saka ta silale a gurin.
NAMRA POV.
Faɗuwa Mardiya tayi ƙasa daga kan turmin da take zaune, tana kallon Namra da mugun razana a fuskarta.
Gaba ɗaya matan gida sai hankalinsu ya tattara ya ya koma kan Mardiya da Namra. Babu wanda yace uffan har Inna da take Mahaifiyar Mardiya, dan tasan Namra ba zata mari Mari Mardiya haka kawai kawai ba.
“Ashe baki da zuciyar Imani? Duk zaman amanar da nake dake Zagon ƙasa kike min? Kina ganin yadda na yi ta neman wayar nan, ashe tana gareki kika ƙi faɗa min? Taya kika ɗauki sarƙa ta da ƴan kunne na? Faɗa!”
Namra ta faɗa a tsawace tana mai jin kamar ta kama Mardiya ta ɓanlata gida-gida, ta watsar. A nan matan gidan kowa ya fara sun-sun da kai suna kallon-kallon ma junansu, daman sun daɗe suna jiran zuwan wannan ranar, tun da sun san Mardiya ta na ɗan ɗauke-ɗauke kuma sun san ba zata rasa yi ma Namra ba, tun da halinta ne.
Murje ido Mardiya tayi, ta mayarda hawayen da suke son zuba mata, wani dakewar zuciya ta samu kanta da ita, na mayarda ƙaryarta ta zama gaskiya.
“Namra ya kamata ace kina bincike kamin ki aikata abu, kuɗin ki na canja musu muhalline, sannan ni ban ɗaukar ka miki waya ba balle kuma sarƙa, sai idan wani sherin zaki min”
Tassss Namra ta sake marinta ta turata can baya har ta faɗi.
“Munafuna mai siffar ƴan wuta, nayi farinciki da Allah ya nuna min ko wacece ke tun a yanzu, na yi nadamar sanin ki a rayuwarta, baki da imani ba ki da tausayi Mardiya, duk irin halin da nake ciki sai da kika ƙafe zuciya kika min sata? Ɗaukar haƙƙin wani? kuma ki jira sakamakon ki”
Wannan karon Mardiya hawaye take. Mahaifiyarta ta matso tana hantarar Namra, magangannunta sun ɓata mata rai sosai, tana ganin dan me Namra zata musu haka.
“Amma ke kam ba ƴa bace sam baki da mutunci, ai komai Mardiya tayi miki ya kamata ace kin taushe zuciyarki kin ɗaga mata ƙafa, balle ma bayi ba dan ban haifi ɓarauniya ba”
Namra ta kalleta da jajayen idanuwanta, ta yarfe ta da hannu.
“Kin ji kunya Wallahi, tirr da uwa irin ki mai ɗaurewa ƴarta gindi tana abunda take so, uwar da ƴarta zata sa ƙafa ta fita ba zata dawo sai taga dama kuma hankalin ki kwance, sai murna kike tana kawo miki abunda daɗi, kina da tabbacin inda take zuwa? Idan har kin san hallaci ba zaki bar ƴarki ta ta ɗauki abu na ba, ko da kuwa yana zuba a ƙasa”
Maman Mardiyar ta jinjina kai
“Lallai ɗan adam butulu, lallai mun yi kuskure yi miki masauki min yi kuskuren yarda dake, a nan da kika yi gobara babu uban da yayi miki masauki sai mu, mu baki ci mu baki sha amman shine zaki watsa mana ƙasa a ido ko tafiyar yawon asibitin nan duk da Mardiya akayi shi, amman ki rasa abunda zaki saka mata da shi sai sata”
“Kune kukeyi kuskure, ni nadamar sanin da na yi mu nake, in mamakin bushewar zuciya irin na ƴarki, na yarda da ita ace ita macuciya ce”
Hawaye take kamar an buɗa fonfo, sai ta shiga ɗakin ta kwaso kayanta ta fito da su waje, sannan ta sake komawa ta ɗauke komai nata a ɗakin ta fito dashi waje, sai a sannan matan gidan suka fara saka baki a maganar, suna bata haƙuri tare da Mahaifiyar Mardiya.
“Wallahi ba zata sake kwana a gidan nan ba, indai ƴar halak ce ko ƙofar gidan nan karki sake bi, shi kenan dan anga yarinya bata magana sai a riƙa cin amanarna kowa ya kwaso shararsa sai ya zube akanta, to ta Allah ba taku ba Wallahi, Mardiya nan gani nan bari kashe di uku lahaula bakwai”
Namra ta nuna ta yatsa.
“Karki soma wulaƙanta ni akan wannan gidan, nima rayuwa ce ta canja min da ko a hanya kika haɗu da ni ba ki isa ki faɗa min magana mai ɗaci ba, kuma ni ƴar halak ce zan tabbatar miki da hakan ”
“To mu zuba mu gani, ai mu kujera ne, muna nan zaune zaki dawo”
Namra bata sake ce mata komai ba, uffan ba saboda baƙinciki, da taimakon yaran gidan ta kwashe ƴan tsomakaranta ta kai BQ ɗin gidan ta , sai ta zauna a balcony ɗin gidan ta tsurawar main house ɗin gidan ido, tana hawaye.
Miyasa Mardiya zata mata haka bayan ta yarda da ita? Miyasa duk wanda ta yarda da shi sai ya dawo yana mata Zagon Ƙasa? Ji take kamar ace akwai wani a kusa da ita ta faɗa masa matsalarta ta labarta masa damuwarta, ta faɗa masa abunda Mardiya tayi mata ko zata samu sassauci a zuciyarta.
Tashi tayi ta ɗauko wayarta, ta riƙe a hannun tana juyata, itace last kyautar da Anty Amarya tayi mata, jin son wayar take ya shige ya, lallai tana buƙartar mahaifiyarta a kusa da ita.
Ƙoƙarin kunna wayar take amman abun ya gagara, ta danna power bottom ɗin amman wayar taƙi ta tashi, sai ta juyar da gefenta da bayan ta tta duba ko ina, bata ga wani matsalar ba, amman wayar taƙi ta tashi.
Riƙe wayar tayi tana ta kallonta, kamin ta saka ta ajaka, ta tashi ta canja Hijabinta ta fito harabar gidan. Yau kam sai da tayi tafiya mai nisa sannan ta samu Napep, kai tsaye tace ya kai ta asibiti.
Lokacin data shiga asibitin ta yi ta ƙoƙarin ta ɓoye damuwarta, amman abun ya ci tura, saboda baƙin cikin abun da Mardiya tayi mata ya tsaya mata a rai.
Ko da ta shiga ɗakin ta tararda likita na duba Asim, yana wasu ƴan rubuce-rubuce, bayan ya gama ya miƙa mata takardar.
“A siyo wannan maganin anjima za a bashi”
Hannu kawai tasa ta karɓa tana kallon likitan har ya fice, sannan ta zauna kusa da Asim ta ɗora kanta saman kafaɗarsa, ta fara hawaye.
“Miya faru?”
Kuka ta fara rarewa a hankali.
“I just need someone to tell everything will be okay”
Zungurarta yayi da kafaɗarsa ta ɗaga daga saman ƙafaɗar tana kallonsa, shi kuma ya wani ɓata fuska.
“Namra miyasa kike abu kamar wata ƙaramar yarinya, ya kamata ace kin san kin girma fa amman sai ki riƙa abu kamar wata ƙaramar yarinya, haba Namra baki ga halin da nake ciki ba, yanzu fa wani maganin ne likita ya rubuta min, ni wannan zaman asibitin ban san ranar da zai ƙare ba, da nasan wannan ƙaddarar zata same ni da ban je ɗauko motar nan ba”
Furucin da Asim yayi a yanzu, sai ya ninka ɓacin rai tazo da shi, tayi tunani zai barta ta faɗa masa damuwarta ne har ya rarrashe ta, amman sai ya ƙara mata wani.
“Miyasa kowa baya fahimtar damuwata, miyasa kowa baya jin abunda nake ji? Miyasa ba a ganin ƙoƙarina? Be kamata ka biye Mama ba, be kamata ace kana irin wannan furucin ba”
“Be kamata ba? To idan ban biye mata ba wa zan biyewa? Ai gaskiya take faɗa, komai ƙaddara ne amman kuma yana da sanadi, nan gaba idan ba bara ba me kike tunanin zamu koma yi? Tun ana baka rance wata rana ai hana ka za'ayi”
Kallonsa kawai take, tana mamakin kalamansa, taya Asim.ya juya ya koma ba shi ba? A yau ita Asim yake kallon tsabar idonta ya faɗa mata irin wannan maganar?
Turo ƙofar da Mama tayi ta shigo ne yasa tayi saurin share hawayenta, ta sanda kai ƙasa, zuciyarta na mugun ƙona.
“Ga waya mamanki ta kira”
Hannu ta kai ta karɓa, sai ta tashi ta bar ɗakin da saurin saboda kukan dake son cin ƙarfinta.
Mama ta bita da wani kallo.
“Me kuma aka mata?”
“Oho kukan data saba ne ta zo ta min”
“Hmmm wannan matar ita da iyayenta ba son ka suke ba, duk ta bugo wayar nan ƴarta take kira,ƴar wayar kiran ma ta kasa ta siya mata, ni wallahi ban san me suke nufi da kai, ni Wallahi da zaka bi ta nawa da ka saki yarinyar ka huta ma kan ka”
“Mama idan na sake ta a yanzu wace mace ce zata zauna da ni a haka? Bana da kuɗin auren wata, sannan kina ganin halin da nake ciki, ai ƙara ma na zauna da ita duk wahalar da zamu sha mu shata tare, komai zai ci ni sai ya ci ƴarsu”
“Hmmm Allah ya kyauta, amman wannan sun nuna maka ƙiyayyah zallarta, Allah dai ya azurta ka ya baka lafiya”
“Amin”
Ya amsa fuska a haɗe kamar ance iyayen Namra suna gurin. Lokacin da Namra ta fita, sai tayi can gefe nesa da inda masu jinya suke shinfiɗa dan shan iska, sannan ta riƙe wayar tana kuka. Sai ga kiran Anty Amarya ya shigo, cikin sauri ta ɗauka ta kara a kunne, tana cigaba da kuka.
“Lafiya Namra? Miyasa ki?”
“Ma....Ma...”
Yau kam da Mama ta kira Anty Amarya, sunan da be taɓa zuwa a bakinta ba tun tashinta, saboda sabo da yadda kowa ke kiranta da Anty Amarya.
Anty Amarya jin kukan ƴarta take har cikin ranta, bata san abunda yasa Namra kuka ba, sai kawai ita ta fashe da kuka tana dafe zuciyarta.
“Namra faɗa min minene? Miye damuwarki ƴata faɗa min? Indai kuɗi ne na turo miki 300,000k a account tun jiya, ko ba za su isa ba na ƙaro miki?”
“Mama ina son ganin ki, i miss you”
“Okay ki faɗa ma mijin ki idan ya bar ki zan turo direba ya ɗauko ki kin ji? Akwai wani abun ne? Jikinsa dai ƙalau ko?”
“Ya..ji sauƙi”
Ta amsa da in'innar kuka.
“Namra ki kwantar da hankalin ki kinji? Komai zai wuce? Rayuwa bata tabbatuwa haka nan dole ne za a jarraba bawa”
“To Anty na gode”
“Ki sayi waya ki saka layin ki, ki kira ni kin ji”
“Tau”
Ta kashe wayar, sai ta duƙa a gurin ta riƙa rusa kuka kamar wacca akayi ma mutuwa. Ko da ta tashi har hijabinta ya ɓace da hawaye, sai ta cire ɗankwalinta ta ɗora saman hijabinta, ta koma ward ɗin.
HILAL POV.
Tun bayan fitar Rashida daya gama shirya ma yaransa abun kari, sai ya ɗauko tsohon result ɗin ya ɗora a saman gadon Rashida tare da takardar rubutun da yayi mata. Sannan ya koma yayi wanka ya kwashi yaran suka wuni gidan Hajiyarsa, tayi farinciki da murna sosai, sai da suka yi sallah isha'i sannan yace ma Kalsoom ta tashi tayi shirin zuwa gida. Ita kuma sai ta riƙa kiran yaran da zimmar su zo suje gida sai ya riƙe mata hannu ganin babu kowa falon.
“Ba da su zamu je ba”
“Amman....”
“Don't talk gobe da yamma direban hajiya zai mai da su gida, suna jindaɗin zaman nan let them enjoy themselves”
“Amman suna zuwa islamiya da safe fa”
“Just for one day, please a daga musu kafa mana, yau bana son jin muryar yaran nan a gida”
“Saboda me? Wai Doc miyake damun ka?”
Ya kwanto da kansa saman jikinta, kamar wani ƙaramin yaro.
“Ke kike damu na? Son ki ne yake wahalar da ni”
“Ba so na bane wannan, wata damuwar ce ta daban, dan Allah ka faɗa min abunda yake damun ka”
“Tashi muje kar muyi dare”
Ya tashi da zimmar kawar da maganar dan baya son faɗa mata komai.
Shi ya fara zuwa yayi ma Hajiya sallama sannan ita ma tayi masa, suka kama hanya, tun da suka hau titi bata ce masa komai ba in ban da ido ta da sakar masa tana kallon yanayinsa, a fuskarsa take karantar damuwarsa, zuciyarta na nasalta mata lallai akwai abunda yake damun Mijinta.
Parking taga yayi a gefen ti-ti, sai ya juyo ya kalleta yana murmushi, kamin ya kai hannu ya jaka izuwa ƙirjinsa, ya rumgumeta. Ya ɗauki dogon lokaci a haka sannan ya tashi motar suka ƙarasa.
Jikinsa ne ya bashi ba lafiya ba, tun daga lokacin da yayi parking ɗin, sai kuma ya soma jin rashin dacewar abunda yayi ma Rashida, ko ba komai uwar ƴaƴansa ce, sai dai babu yadda ya iya tun da hiv indan be zama aids ba, akan iya kamuwa dashi ta hanyoyi da dama, tun da a yanzu shi dai ya samu tabbacin shi da Kalsoom da ƴaƴansa basa ɗauke da cutar.
Sai dai ya san Rashida ba zata iya rayuwa babu shi ba, yasan yadda take ƙaunarsa, amman zai gogeta a ransa matuƙar result ɗin ƙarshe ya fito, kuma ya tabbatar da a sex ta samu cutar.
Sai da ya raka Rashida har ɗakinta, sannan ta fito ya shiga ɗakin Rashida. Yanayin yadda ya ganta ya tsorata sosai, tana kwance cikin jini babu numfashi. Be san lokacin daya ɗauke ta ya fito da ita da gudu ya nufi mota.
AMIRA POV.
Daga rarrashin da yake mata, sai wasan ya sauya salo, ya fara bin jikinta yana wasa da dukan ɓangarorin jikinta, har yayi nasarar jan hankalinta, ya biya buƙatarsa.
Sannan ya nufi ɗakinsa ya kwanta, ita kuma ta nufi wani ɗakin, tayi wanka ta shirya cikin wasu tufafin ta fito kamar ba ita ba.
A falon ta dawo, ta buɗe freezer ta ɗauki lemu tasha tana ƙoƙarin kawar da damuwar dake cikin ranta dan samawa kanta nishad.
Ta zauna, saman kujera tana ƙoƙarin canja MBC bollywood, zuwa AIT, program ne suke akan yadda za'a magance matsalar tsaron data addabi Nageria, har zata canja sai channel sai kuma ta tsaya tana kallon yadda Abdool yake watsa turanci yana koro bayani kamar wani ba'amerike, hakan ya ɗauki hankalinta har ta kula da kyausa, da kuma muƙaminsa, kamin su sake naɗo sunansa.
“Major General Abdullah Ahmad Mai-Doki, wow nice guy, nice work, nice name, everything perfect”
Ta furta a hankali tana mai maida hankali ga kallonsa sosai. Dif nefa suka ɗauke wuta, wani irin buga ƙafa tayi, ta sosa hancinta.
“Oh they Fuck up”
Zata tashi sai ga mutumen ɗazu ya dawo, yana bata rahoton Doc Sabo. Dafe kai tayi tana tashi tsaye.
“Eyyyyyy karka cika ni da wani magana, ga wayana nan ka duba number ta ansa banker ka tura mata text ɗin abunda zata biya, sannan kace Samuol ya tada mana injin”
Tana kaiwa nan ta nufi ɗakin da Guy son ya shiga ɗazu.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 38*
NOT EDITED ⚠
Ko da ta shigo ɗakin ta same shi tare da Mama suna magana, bata iya zago zancen da suke amman jikinta yana bata kamar maganar ta ne suke. Cikin Ladabi ta miƙawa Mama wayar.
“Kun gama maganar ko?”
“Eh mun gama”
“Tau madallah”
Yanayin yadda ta tayi maganar ya tabbatar ma da Namra da biyu tace haka ɗin, sai ta tashi ta fice daga ɗakin ta basu guri.
Da kallo Namra ta bita har ta fita sannan ta zauna kusa da Asim
“Anty ta aiko min da 300,000k, zan bawa Dillaiya su in yaso sai ta bini hansin ɗin”
Asim yayi shiru be ce komai ba, sai ma yayi kamar ba dashi take magana ba, baya son nuna mata be jidaɗi ba, sai dai a can kasa zuciyarsa rashin jindaɗin ne, ganin ba shi Anty ta aikowa kuɗin ba, tun farkon fara rashin lafiyarsa har zuwa yanzu babu wani abu daya fito daga hannunsu izuwa gare shi da sunan yayi lalura da su.
Hannunshi ya kai ya riƙa nata hannun.
“Namra ya zaki ji idan aka ce yau Mama bata son ki kuma kina auren ɗan ta?”
Tayi shiru tana nazarin inda maganarsa ta dosa, tambayace yayi mata mai ma'ana ɗaya, dan kai tsaye ta san da ita yake.
Sai kawai tayi murmushi tace
“Be zai dame ni ba, saboda Kai na aura ba Mama ba, sannan ban aure ka ba dan wani abu naka sai dan son da nake maka, to dan me wani abun zai rufe min ido har na zarge ka?”
“Uhmm”
Ya janye hannunsa, yana kallon ƙofar ɗakin kamar mai jiran shigowar wani.
Can kuma ya kalleta
“Ina ganin idan an gama min allurar nan, ya kamata ace mu koma gida saboda asibitin nan in ban da kashin kuɗi babu abunda suke ja mana”
“Gidan ma sai an gyara za'a zauna, saboda gate ɗin ya ɓangale gefe ɗaya, kuma BQ nan tsoro take bani”
“A haka dai zamu daure mu zauna”
“Da ace da hali da an gyara gate ɗin, in yaso BQ ɗin sai a share a wanke”
“Sai ki gyara da kuɗin da Anty ta aiko ai zasu isa”
“Amman ba kaji nace bashi zan biya ba? Sai dai na siyar da sarƙa na gold a gyara”
Ya kalleta a kai-kaice
“Ina kika samu sarƙar gold? Ba kin ce komai ya ƙone ba?”
“A hannu Mardiya na gani ɗazu har da wayana ma, ita ce ta satar min”
“Mardiya? Ya akayi kika gani?”
“A ƙasan a kwatinta, saboda jiya na saka kuɗin daka bani a cikin kayanta, gurin nema ne sai na wayar har da sarƙar ma, da wasu ƴan kunne da Hajiya ta taɓa raba mana lokacin data dawo makka”
“Amman ya akayi Mardiya ta shiga har ciki ta ɗaukar miki sarƙa har da waya ma?”
“Ban san yadda ta ɗauka ba wallahi kawai dai na kamata da su ne a yau, kuma nayi mata masifa ita da Mamanta”
“Aikowa baki kyauta ba, yarinyar duk hidimar da ake ta zuwa asibiti da ita ake yinta, anya ma ita ta ɗauka? Dan gaskiya yarinyar nan tana da natsuwa da tarbiya”
“To idan ba ita ta ɗauka ba ya za'ayi na gani a akwatin ta? Kuma fa taji lokacin da ina nema”
“Yanzu idan kin siyar me zaki yi da kuɗin? Namra wai kin faɗawa Abbah mun yi wuta kuwa?”
Ƙasa tayi da kanta.
“Ban faɗa ba, babu wanda ya sani”
“Nima bana son kowa ya sani dan muna da maƙiya za su mana dariya, amman dai su ai kamata ace sun sani, rayuwa tayi haka? Namra ki duba halin da nake ciki, babu wani taimako sai na Allah, yanzu idan kuɗin nan da muka ranto suka ƙare kina tunanin akwai inda za mu sake dubawa? Ban san miyasa rayuwa ta zo mana a haka ba, kana neman ka ɗaga kayi gaba, amman sai baya kake abubuwa suna ƙaruwa”
Ya ƙarasa maganar idonsa cike da hawaye.
“Inshallah zan faɗa mata idan na je, tace na tambaye ka idan ka bar ni sai naje”
“Gurin me?”
“Tace tana son gani na ne”
Har zai ce wani abu, sai kuma yayi shiru yana nazari, idan har ya barta yaje be san abunda zata samo ba, musamman idan ta faɗa musu halin da suke ciki.
“Amman ba zaki daɗe ba ko? Kije amman kwana biyu za kiyi ki dawo”
Hannayenta tasa ta rumgume shi, tana murmushin jindaɗi.
“Na gode daman nima ba zan wuce kwana biyun ba, Allah kara maka lafiya”
Har cikin ƙasan zuciyarta take jin son Asim, sam bata iya gani illarsa, saboda zuciyarta tana muradinsa, a take zuciyarta ta fara raya mata ya ɓoye mata maganar kuɗin wata ƙila saboda karta sa ci suna da kuɗi, kuma ita kanta bata san yadda yayi ya samun kuɗin adashen ba, sai dai abunda ya faɗa a wacan lokacin ya tsaya mata a rai, a duk lokacin data tuna sai ta ji babu daɗi, har zuciyarta ta zarge shi akan haka.
HILAL POV.
A haukace ya isa asibiti, dan a tunaninsa Rashida ta mutu, shi da kansa ya kai ta emergency room, tare da taimakon wasu Nurses ya shiga neman numfashinta.
Da taimakon Allah komai ya daidaita, sannan ya ɗaura mata drip, yayi mata allurar. Tsaye yayi cikin ɗakin yana kallonta bayan Nurses ɗin sun fita.
Wayarsa ya shiga lalabe sam ya manta da tana ciki mota, sai yanzu. Fita yayi be daɗe ba ya dawo tare da rigar asibiti da wasu kayan aiki, sai ya canja mata tufafin jikinta, ya gyara mata jikinta sannan ya saka mata rigar, sai ya kira wata ma'aikaciyar gurin mai share-share ta kwashe kayan.
Zaunawa yayi a gurin ya ɗafa kansa, sai ga wasu daga cikin abokan aikinsa sun shigo duba ta, sama-sama ya amsa musu, suma sun ga damuwa ƙarara a fuskarsa, sun lura da yanayinsa, duk a tunaninsu saboda Madam bata da lafiya ne.
Fatan sauƙi suka mata sannan suka fita, shi kuma ya tashi yaje gurin motarsa ya ɗauki wayarsa ya kira Hajiyarsa ya faɗa mata, sannan ya kira Momy ita ma ya faɗa mata.
A cikin motar ya shiga ya zauna ya tasa abunda ke masa daɗi duniya, baya son yaransa su san komai a tsakanin su, kuma be san wane bayani zai yi ma Hajiyarsa ba da Momy, sam baya son duniya tasan abunda Rashida ta aikata, sai dai kuma be san yadda zai yi yayi ya ɓoye ba, cox he's no more to her.
Be ɗago kansa daga tunanin da yake ba, wayarsa tayi ringing, number Momy ce a rikice take tambayarsa wane ɗaki Rashida take.
Sai da ya buɗe Motar ya fito sannan ya amsa ta.
“Kin shigo Asibitin ne ?”
“Eh ina emergency”
“Okay tsaya a gurin zan ƙaraso yanzu”
Ya kashe wayar tare da rufe motar, sannan ya nufi gurin da yake zaton take. Tun daga nesa ya hango ƙannenta biyu. Cikin rashin kuzari ya ƙarasa inda suke ya gaishe ta, su kuma ƙannen suka gaishe shi. Sannan ya wuce dasu zuwa ɗakin da take.
Ganin halin da take cikin yasa Momy har ta fara hawaye, kallon ta kawai Hilal yayi yana ayyana irin abunda zata ji idana kace mata ƴarta na ɗauke da cuta mai ƙaryar garƙuwar jiki.
“Momy karku taɓa ta, ko da ta farka ne”
“Toh amman mi ya same ta haka ne?”
“Ta samu Miscarriage ne”
“Subhanallahi Allah ya bata lafiya”
“Amin”
Ya koma ya jingina da bangon ɗakin yana kallonta, ɗaya daga cikin ƙanwarta ta warware carpet ɗin da suka zo da shi ta shinfiɗa a gurin. Ta miƙawa Hilal Kujera, sai kawai ya girgiza mata kai.
“No Thanks”
A gurin yayi ta tsayi har Hajiya ta iso, ita sai da ta kira shi, yaje ya taho da ita sai suka gaisa da Momy, ta duba ta tayi mata fatan sauƙi sannan ta fito. Tare suka jero da ɗanta sai gaisuwar girmamawa ake mata, dan kowa ya ganta ya ga Hilal yasan itace mahaifiyarsa.
“Yanzu haka baƙin kishi ne ta sawa kanta, gashi yanzu kun yi losing wannan baby”
Shi dai be ce komai ba, ya buɗe mata Mota. sai da ta shiga, ta zauna sannan yayi mata sai da safe direba ya wuce da ita, shi kuma ya juyo ya dawo cikin asibitin.
Lokacin daya dawo, sai ya zauna saman gadon kusa da ita, babu abunda yake kallon sai fuskarta, rayuwarta da tasa yake ta tunani, irin yadda suka so junansu har suka haifi ƴaƴansu, yanzu kuma lokaci ɗaya komai yana shirin sauya musu, he just can't believe ace Rashida ta ci amanarsa da wani, haƙiƙa yana da tambayoyin da suke buƙatar amsa daga gareta.
“Ai da ka tashi kaje gida, tun da ga mu muma ai mun isa mu kula da ita”
Can ciki ya ji muryar Momy tana masa magana. Sai ya tashi cikin rashin ƙwarin jiki yayi musu sai da safe ya fice.
NAMRA POV.
Daga asibitin sai ta wuce bank, layi ta bi sai da ka kai gareta sannan tayi checking balance ɗinta, dubu ɗari huɗu ta hansin ta gani, a tunaninta ko Anty Amarya ta ƙaro mata wasu ne, sai kawai ta cire kuɗin gaba ɗaya, cikin farinciki da jindaɗi.
Kamin ta isa gida sai ta ta fara biyawa ta gidan dillaliya, ta ƙirga kuɗinta ta bata, sannan tasa a kira mutumen da yayi musu wacan rubutun yayi masu sheida saboda wata rana.
Sauran kuɗin daya rage mata sai taje kasuwa ta siye kuloli, da ƴan wasu kayan aiki da basu kai sun kawo ba, data dawo gida sai ta wanke kuloli ta siye abincin ta nufi asibitin da shi.
Ta jidaɗin ganin Asim a tsaye yana ɗan takawa, Mama na tiƙe da shi, suna zuwa ƙarshen ɗakin suna dawowa, wani farinciki ne ya mamayeta, bata san lokacin data aje kulolin ba ta tsaya tana kallonsu.
Hamdala take yi ma Allah cikin ranta, tana jindaɗin yadda taga mijin nata yau ya fara taka ƙasa, Mama ma farinciki take sosai daman ta fi kowa son haka dan zaman asibitin ya isheta.
Sun kusa minti latalin suna, suna zagaye ɗakin sannan Mama ta zaunar da shi saman gado.
“Allah ya bi da lafiya ya ƙara sauki”
Ita da Asim suka haɗa baki gurin amsawa da Ameen. Sannan ta zuwa ya fice.
Namra ta kalli Asim da far'ah a fuskarta.
“Da nice nace za kayi wannan yawo zaka ce min ba aka iya ba”
Ɗan murmushi yayi, shi kansa yana cikin jindaɗi a yau.
“Alhamdullillah, ban zaci zan iya ba”
“Ai babu abunda za a iya matuƙar aba'a gwada ba, Allah ya nuna min ka tashi ka koma kamar yadda kake”
“Ameen”
Ta kwantar da kanta saman jikinsa. Shi kuma yayi shiru yana nazarin rayuwarsa, irin mutanen da sukajuya masa baya yake lissafi a zuciyarsa, ace har abokansa da yake ganin sun kai amman kowa ya kasa takowa ya zo ganinsa
“Hmmm”
Ya furta a fili, yana sauke ajiyar zuciya. Sai Namra ta kalleshi
“lafiya?”
“Lafiya ƙalau, kawai ina tunanin tafiyarki ne, Mama tace karki je yanzu, idan ma wani abun ne ai aiko miki kawai, kuma ki faɗa wata komai ta waya kawai, tama kira ba ki nan”
Shuru Namra tayi bata ce komai ba, sai dai maganar tasa bata mata daɗi ba. Hannu ya kai ya shafa ta.
“Namra have you ever noticed that Anty bata taɓa kira kai tsaye da sunan jin jikina ba? Haba Namra ai ko wani na kashe musu sa ɗaga min ƙafaa balle auren ƴar su na ke, abun nan ya ɓata ran Mama sosai, nima shiyasa a duk lokacin dana ga ɓacin rai a fuskarta sai nawa rai ya ɓace, daman irin wannan ake gudu aje ayi aure a kasa samun kwanciyar hankali”
Shiru tayi tana taɓin hannunta, ita kanta tasan iyayenta basu kyauta ba, akan abunda aka yi mata kuma Asim yana da gaskiya kan abunda yake faɗa, tasan Abbah kam ba zai zo ganinsa ba, amman ya kamata ace ko Maryam ce ta zo ganinta, ganin yadda suke da ita jini ɗaya, amman ko waya bata taɓa bugo mata ba.
Anya ta cancanci su juya mata baya har haka?
Ba su da wani excuse akan haka, sai dai a yanzu bata son ta zurfafa amincinta ga Asim tun bayar maganar su da taji da Mama.
Kamar ya san abunda yake ransa, sai kawai ya rumgume ta.
“Ina son ki, kuma bana tunanin akwai abunda zai raba ni da ke, ina son na ɗanɗana miki rayuwar da baki taɓa mfarkin shigarta ba, irin rayuwar jindaɗin da tafi ta gidan ku, sai dai ina gudun ranar da zaki rabu da ni saboda wani baƙin talauci ko mugu abu ya same ni”
“Ba zan taɓa rabuwa da kai ba Asim na maka alƙawari, ko a wane hali na samu kai na, zan zama mai biyayyah a gare ka, zan maka sadaukarwar da ba kowa ce mace ce zata iya ba, son nuna maka son da ba kafai ake samun irinsa ba.
Sai dai ni zuciyarta ta kasa Aminta da kai, kana ɓoye min wani abu naka Asim”
Gabansa ya faɗi, yana Allah-Allah idan ba wani zancen nasu ta ji ba.
“Me zan ɓoye miki? Miyasa zuciyarki ta manta da waye Asim a duniyarta, taya Asim zai cuce ki, Asim be aure dan tsinkayar wani abu na gidan ku ba, shiyasa tun farko ban so na aure ki saboda na san zaki yi tunanin saboda haka na aure ki”
Jikinta ya mutu, hawayen da taga yana zuba a idon Asim ya tsayar da nata hawayen, a take ta manta da zargin da take masa, wani irin son sa da ƙaunarsa suka mamaye mata zuciya.
MORNING UPDATED
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 39*
NOT EDITED ⚠
Ko da ya isa gida, Kalsoom na zaune a balcony tana zaman jiransa, hankalinta ya tashi sosai, ji take kamar itace a halin da Rashida take ciki.
Tana ganin yayi parking, ta tashi da sauri ta ƙarasa inda yake ta buɗe masa motar.
»“Ya jikinta? Da sauƙi?”
Ido ya sakar mata kamar yau ya fara ganinta, be ce mata komai ba kuma be kashe motar ba, balle ma ya fito. Ita kuma duk ta tsorata, gabanta sai faɗuwa yake kar ta ji mummunan labari.
“Dan Allah ka min magana mana”
Ta masa maganar irin tana daf da yin kuka. Sai a sannan ya kashe motar ya fito, ya ɗora kansa saman na ta, ya kai hannu ya riƙe hannunta yana sauke ajiyar zuciya.
“Da sauƙi ta samu bachi”
“Amman ka kira gida ka faɗa musu?”
“Na faɗa”
“Sun zo?”
“Sun zo”
“Allah ya bata lafiya, amman dai be zube duka ba ko?”
“Ya zube”
“Ayyah Sorry”
“Sorry too”
Duk maganar da take masa yana amsa mata, kansa na saman nata ne, sai a sannan ya riƙa hannunta, ya matsar da ita daga jikin motar ya rufe motar, ya jata zuwa ciki.
A falo ya zauna, sai ta zauna kusa da shi, tana ɗan shafa bayansa, a tunaninta zubarwa cikin ne be masa daɗi ba.
“Doc kayi haƙuri Allah zai sake baka wani”
Ya kalleta.
“Haka ne, Kalsoom do me a favor”
“Na me?”
“Ki min alƙawarin zaki kula da yarana zaki basu kyakkyawar tarbiya, and komai suka yi ba zaki gundura da su ba”
“Baka da buƙatar na maka alƙawari, amman miyasa kayi min wannan maganar na?”
“Zan raba muku gida ne, da Rashida zan wareta daban, ke zaki zauna a nan tare da yara”
“Miyasa?”
“Ita ta buƙaci haka”
“Kuma ta yardar ta bar min yaran?”
“Eh amman ba na son ki faɗa musu hakan, ni zan yi magana da su, ko da sun dawo karki faɗa musu Mamansu ta kwanta asibiti”
“Okay”
Ta faɗa a sanyaye, ita dai ta san ba lafiya ba, yanayinsa da kuma hukuncin daya yanke ya tabbatar mata haka.
“Bari na haɗa maka tea”
Ta tashi ta nufi kitchen, zuciyarta da tunani kala-kala, ko dai Rashida ce take da hiv! Shiyasa yake ta mata tambaboyi a baya? Kuma yanzu zai raba ta da ƴaƴanta, ai ba zai raba ta da su haka kawai ba, kuma yadda take ganin damuwar nan ta masa yawa ta san ba'a raba ɗayan biyu ba.
Har ta haɗa masa tea ta kawo masa tunanin take.
Fuskarsa ta tsurawa ido sosai, lokacin da zata miƙa masa tea, tana son gano gaskiyar zarginta, idonsa sun rine irin na ɓacin rai ɗin nan da damuwa idan sun yi ma mutum yawa.
Har zata ce masa wani abu, sai kuma wata zuciyar ta hana ta, sai kawai ta zuba masa ido har gama shan tea ɗin ya tashi ya nufi ɗakinsa.
Ita kam sai da ta gama abunda take sannan taje tayi wanka ta saka kayan bachi ta nufi ɗakin nasa, daman yau girkinta ne, ganin be shigo ɗakinta ba, ba zai hana ita ta kai kanta ba.
Washe gari har Kalsoom ta haɗa musu breakfast, idonsa biyu amman ya kasa tashi, jikinsa ya ɗibge kamar marar lafiya.
“Doc breakfast is ready”
Ta faɗa tana tsaye daga bakin ƙofa. Da ker ya ɗago kai ya kalleta.
“Je kiyi yau bana jin yunwa”
Ya unƙura ya tashi, ya nufi banɗaki. Ita kuma ta juya cikin rashin jindaɗi, ta fice. Wanka yayi ya fito, ya shiryar cikin ƙananan tufafi, ya feshe jikinsa da turare sannan ya fito falo cikin wani yanayi marar misaltuwa.
Ummu Faisak ya gani a falon zaune tana gaisawa da Kalsoom, tana ganinsa ta fara masa wani kallo ƙasa-ƙasa, sannan ta gaishe shi.
“Lafiya ƙalau ya ma su jiki?”
“Da sauƙi, ita ma tace na zo na ɗauko mata wayarta”
“Ta farka kenan?”
Kalsoom ta tambaya.
“Eh ta farka”
Kalsoom ta kalli Hilal
“Bari na tashi na shirya sai mu wuce tare na ganta”
“Ba yanzu ba”
Ya faɗa fuska ba yabo fallasa. Ba jira abunda zata sake cewa ba ya fice.
Kalsoom sai duk ya ji babu daɗi, Ummu Faisak ta buishi da kallon tana ayyana irin mallakar da Kalsoom tayi masa, har yake ƙoƙarin mantawa da Rashida a nan take, da ada ne aka ce bata da lafiya da duk ya bi ya haukaci amman yanzu dubu yadda rana ta fito be je ba, sannan ya hana Amaryarsa taje.
Wani dogon numfashi taja ta sauke irin an gulma ta tashi ta nufi ɗakin Kalsoom.
A hanyarsa ta zuwa Asibiti, Hajiya ta kira shi ta tambayi jikin Rashida, ya amsa mat d taji sauƙi, sai kuma g kiran Alhaji Bashir ya shigo, sai da Hilal yayi parƙing sannan ya ɗauki kiran suka gaisa sannan ya tambaye jikin Rashida.
“Ya Madam da jiki?”
“Jiki Alhamdillah, jiy ne ta samu miscarriage”
“Ayyah Allah ya bat lafiya”
“Amin Amin na gode”
“Dan Allah idan ka shiga, ka bani ita mu gaisa, Asma'u zata zo anjima Inshallah”
Ya kashe, sannan ya buɗe motar ya fita, duk inda y bi gaishe shi ake har ya isa ɗakin.
Wasu ƴan'uwanta ya tarar suna mata sannu ciki har da wasu Nurses da suke aiki gurin. Sai da ya fara gaida Momy sannan ya amsa gaisuwar da ƴan'uwan nata suke masa, ya nemi guri ya tsaya ya kafe Rashida d ido.
Momy ce ta fara fita sannan suma duk suka fita, ka barsa cikin ɗakin shi kaɗai sai ita, jin tayi kamar tace kar su fita, dan bata da idon kallon Hilal balle bakin yi masa magana.
Shi kuma ya tsare ta da ido kamar mai auna hawa da saukar numfashinta.
“Yanzu ba ki ji kunyar kan ki ba Rashida? Kina da aure ki bi wani namiji a waje? Wannan wane irin ƙazanta ne? Miyasa kika ɗauki zina ba komai ba? Idan kika mutu a yau mi zaki cew Ubangijinki? Me na rage ki da shi? Wanda kika bi miya fi ni da shi?
Ko kum kawai sheiɗan ne ya ƙawata miki yin haka? Kin manta ke uwar yara uku ce? Miyasa Zina ta burge ki Rashida? Ashe son da kika nuna min duk na ƙarya ne tun da har zaki iya ba wani halalina, kin lokacin da kike hana min kan ki a baya? A haka nake haƙuri ina bin ki har Allah yasa na haɗu da Kalsoom na aure, amman ko d mafarki ban taɓa tunanin aikata zina ba.
Tsakanin jiya zuwa shekaran jiya tausayinki nake, ina tunanin halin da zaki shiga idan babu a rayuwarki, amman yanzu nayi tunani baki buƙata na, sam ni da ke ba mu dace ba, nayi baƙinciki nayi nadamar da kika zama uwar ƴaƴana, faɗa min wanene wannan mutumen?”
Tun da yake maganar, bata balle shi balle tace wani abu, hawaye kawai take, irin hawayen nan da wani ke bin wani. Ya matsa kusa da ita ya ciro takardar take aljihunsa ya aje mata.
“Aure na da ni da ke yau ya ƙare, na sauwaƙe miki kije ki auri wanda kike ganin ya fi ni, ki dauwama ke da shi a duniyar da kuke son kasancewa”
Ɗagowa ta yi tmda sauri ta kalleshi, irin kallon nan da bata san tana masa ba, yau ta rasa gane duniyar da take, sama take ƙasa take, mafarki take ko gaskiya ne? Da gaske Hilal ne ko waninsa? Taya zata rayu ba da Hilal ba? Gidan ta da ƴaƴanta a yau sun zama mallakin kalsoom ba ita ba.
A saman gadon ta matsa can nesa ya rumgune kanta tana zubar ido kamar mai ganin aljanu. Ko kaɗan tausayinta a yanzu kam be ziyarci zuciyarsa ba, dan yasan ta cancanci fiye da haka, sai kawai ya juya ya fice daga ɗakin, cikin wani irin zafin rai da baƙinciki.
NAMRA POV.
Bata jin ko ta faɗama Anty Amarya sun yi wata, zat yarda dan ganin take kamar cewa zatayi shi ma haɗi ne, kuma bata iya tambayarta wani kuɗin, sai kawai ta kira ta da wayar Asim tace mata be bari ba yace ta bari har yaji sauƙi sai su zo tare, Anty Amarya bata jidaɗin hakan ba, sai dai babu yadda ta iya tun da mijinta ne.
Da dare Namra kasa, bachi tayi har sai da taje wani BQ dake maƙota ka d nasu ta nemi ƴar fulanin data zo ta taya ta kwana. Duk da haka har safe ba yi bachin kirki ba dan hankalinta be kwanta da gurin ba.
Da safe sai ta aika yarinyar ta siya musu ice su ɗora girki, a abun da bata taɓa ba a rayuwarta yau gashi zata yi. Kamin yarinyar ta dawo, sai taje waje ta ɗauko duwatsu ta haɗa murhu, kamin yarinyar ta dawo sai ta zauna saman bolcony tana kallon gidan.
Tunani take na ranakun baya, lokacin da Anty Amarya take saka ta girki da gas ko electric amman ta ƙi yi ta riƙa faɗin wahala, yau gashi zayi da abund bata ma taɓa gwada kunna wutar da shi ba, yau ga ta a ɗakin da babu katifa balle gado, duk wani abu mai muhimmanci a rayuwart i zuwa yanzu ta rasa shi.
Hawaye ne suka silalo mata sai tayi saurin gogewa, ganin ƴar fulanin ta doso inda take ɗauke d icen.
Sai kusan 12 ta gama girkin abun ka d wacce bata saba ba, sai ta zuba ma yarinyar ta zuba ma su Mama na su sannan ta zuba sauran a kula, sai ta janyo ruwa a rijiya, ta shiga banɗakin BQ ɗin tayi wanka, sannan ta fito ta shirya cikin atamfar jiya ta saka Hijabi ta ɗauki kular ta fito, yau kam a bakin gate ma ta samu Napep, tayi sa'ah an sauke wata ne, sai kawai ta shiga ya ɗauki hanyar asibiti da ita.
Suna kaiwa Babban titi, aka riƙa musu hannu akan su tsaya, amman ta hana mai Napep ɗin tsayawa, har sai da suka isa bakin asibitin. ta fito tana miƙawa mai Napep ɗin kuɗinsa, ta tsaya jiran ya bata canji, sai ta motar ta faka kusa da ita. Abdool ya fito ya nufo ta jiki na rawa. Kamin ya ƙaraso har Mai Napep ɗin ya bata canjinta ta kunna kai cikin asibiti, shi kuma sai sauri yake ya ci gabanta.
Mama na gurin zamanta ta sinƙayo yadda Abdool ya biyo Namra har cikin ward yana ƙoƙarin cin gabanta, sai ta tashi tsaye, ta matsa can baya tana leƙen su, ta tattara hankalinta gaba ɗaya ta mayar gurin.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Written by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 40*
NOT EDITED ⚠
“Haba baiwar Allah, Wannan wane irin jan'aji ne? Dan Girman Allah ki tsaya ki saurare ni”
Abdool ya faɗa yana haɗe hannayensa, alamar yana roƙonta. Girman Allah daya haɗa ta dashi ne yasa ta tsaya har ta ɗaga kai ta kalle shi.
“Malam ni Matar aure ce”
“Matar aure mai igiya uku ko kuma matar aure kalar aure”
“Matar aure mai igiya uku, dan haka kar ka sake bina”
Wani irin faɗuwa gabansa yayi, a take gumi ya fara zubo masa, a take launin idanuwansa suka canja.
“Inshaallah ba zan sake ba, dan Allah ki yi haƙuri ban san kina da aure ba”
Sai a sannan ya janye ya bata hanya, ta raɓa gefensa ta wuce, shi kuma ya juya jiki a sanyaye ya nufi hanyar fita, kallonsa ake tayi a gurin saboda wasu sun san Namra tana da aure, wasu kuma suna masa kallon sani tun da akan nunasa a tv akan matsalar tsaro, kuma sun san ɗan sarki ne, tun da ga fuskar Mai-matarba nan a fuskarsa.
Sam be ji maganar da wani likita ke masa ba har sai da likitan ya cira ƙafa ya cin masa ya dafa shi.
“Manjor ina magana fa”
Ya ɗan kalleshi yana murmushin ƙarfin hali
“Doc Husaini ya aiki?”
“Lafiya ƙalau, ka zo ganin wani ne?”
“No... Eh.. Oh.. Yeah.. Yeah.. Naga wani Cousin na mu ne”
“Allah sarki, tau ya aiki ya kwana biyu? Kun yi kuɗi kun ɓoya”
“Kai ina wani kuɗi aiki ya samu gaba ba sauƙi”
Haka suka jera suna tafiya, suna ɗan taɓa fira har Abdool ya isa gurin motarsa. Jikin sashin kuzari ya buɗe motar ya shiga yana yima Doc Sallama.
“Tau ni kan zan wuce”
“Yanzu kan ganin ka sai manya, tun da baka ma zama garin”
“To ya muka iya, aikin ne a haka ko ina jefa mu ake”
“Allah ya taimaka, sai mun yi waya”
Daga haka ya rufe motarsa, shi kuma ya juya ya koma cikin asibitin. Ribas yayi ya juya hanyar gidan daya baro.
Tuƙin kawai yake jikinsa ba kuzari, kansa yayi zafi sosai, sai hannu yake sawa yana murza goshinsa, lokaci zuwa lokaci yake sauke ajiyar zuciya har ya isa gida.
Ya daɗe zaune cikin motar, sannan ya buɗe ya fito, yayi yaƙi sosai da ƙafafunsa kamin ya ci galaba akansu har su samu ƙarasawa da shi falon Ummi.
Be damu da farar shaddar dake jikinsa ya zube saman carpet, ya lumshe ido yana sauraren bugun zuciyarsa. Ya samu minti ashirin zuwa ashirin da biyar a haka, sannan Ummi ta fito cikin wata bugaggar shada ya nufo inda yake hankalinta a tashe.
Saman carpet ɗin itama ta zauna kusa da shi ta kai hannu ta riƙa kansa.
“Son tell me what happen? Larai tace min ba lafiya ba, talk to your Mom please”
Sai a lokacin ya buɗe manyan golden eyes nasa ya kalleta.
“Mom i saw her today”
“Who?”
“The woman i have been dreaming of, i finally saw her in a hospital”
“And...”
“Ummi matar aure ce”
Wani dogon numfashi Ummi taja ta sauke, tana tunanin ta inda zata fara kwantar masa da hankali.
“Abdallah, be patient one day your princess will surely come, miji baya aure sai matarsa, mace ma bata aure sai mijinta”
“I know, but what i don't understand is duk mace da na gani bata kwanta min, sai wannan ita kuma yanzu matar wani ce, zuciyata tana son wahalar da ni”
“Karka damu, komai zai wuce, i will talk to Mai Martaba, zan faɗa masa ya baƙa time, har Allah ya baka wacca kake so, bana son ka auri wace baka so ina son ganin farincikin ka”
“Thank you”
“Anything for you”
Ya ɗan kwanto jikinta, babu abunda yake gani a idonsa sai Namra.
“Allah ka shiga tsakani na da zuciyata, Allah ka min tsari da sherin zuciya”
Be ankaro da fili yayi maganar ba har sai da yaji Ummi ta amsa masa ta Ameen, dan shi duk a tunaninsa a zuci yayi wannan addu'ar.
Ummi tana son ɗan ta sosai, ta kan damu da damu damuwarsa, ta fi kowa son farincikinsa, saboda ta san zafinsa.
Abdallah Ahmad Mai-doki. Ɗa ɗaya namiji gurin Hajiya Zuwaira. Kuma ɗa na uku a jerin ƴaƴanyen Mai Martaba sarkin katsina na uku III, wato Alhaji Ahmad Abdallahi Mai-doki, jiki gurin Isma'il Mai-doki sarkin Katsina na farko.
Shine ya gaji sarautar kakansa, tun bayan da sarautar ta bar gidansu, sanadin rasuwar kakansa. Bayan rasuwar Sarkin Katsina na biyu, sai aka ɗauko sarautar aka bawa mahaifin Abdallah, wato Ahmad Abdallah Mai-doki.
Matan sa biyu a yanzu, bayan fitar Ummi ya auro Hajiya Salamatu, wace ta kasance ita ta biyu a yanzu. Hajiya Zuwaira (Ummi) Ta sha gwargwarmaya da uwar gidansa Hajiya Shafa, dan zame mata tayi muguwar kaza, mai hana shiga akurki. Hajiya Shafa ta haifa masa ƴaƴa bakwai, Mashkur ne na farko, sannan Salwee wace ita ce ta biyu, sannan Ummi ta Haifi Abdallah, wanda mai martaba ya saka masa sunan babansa, hakan yasa bata taɓa faɗar sunansa sai dai ya kira sa da Yarima ko Babana.
Mar martaba yana matuƙar son Ummi ganin ita ce ƴar'uwarsa kuma itace tafi kula da shi sama da Hajiya Shafa, hakan yasa zaman gidan ya gagareta, saboda irin son da yake nuna mata.
Babu inda Hajiya Shafa bata shiga ta fita ba, har sai da taga ta raba aurensu da Mar matarba, ba tare daya sani ba yayi mata saki uku lokaci ɗaya, kuma ya karɓe ɗansa, Abdallah a lokacin yana ɗan shekara biyu da wata uku. Son duniya nan Mai Martaba ya ɗauka ya ɗora masa, saboda son da yake ma uwarsa, sai kuma akayi sa'ah ya zama ɗa na gari gurin iyayensa, duk kuwa da faɗi tashin da yasha kamin ya kawo inda yake yanzu. Mai martaba ya so ya kaishi waje karatu amman Hajiya shafa ta hana, tasa aka kai ɗanta.
Haka tasa aka riƙa tura masa kuɗi da sunan karatu ashe yana can yana holewa da ƴan matansa, har yayi karatun ya gama be dawo gida da kyakkyawan results ba. Abdallah da yayi karatu a Nigeria sai ya fishi ƙoƙari da basira, sosai hakan ya ƙarawa Mai matarba ƙaunarsa, bayan ya gama degree a nan sai ya turawa waje yayi Master's. Hakan yasa Hajiya Uwani ma da tazo daga baya ta ɗauki ƙiyayyah ta ɗora masa, kowa cewa yake Mai Martaba yafi son sa da kowa.
Bayan fitar Ummi a gidan Mai Martaba, sai auri Alhaji Dahiru, mahaifin Haleema da Meesha da Fauza, tana da goyon ƴar autar ta, Amal ya rasu. Tun daga lokacin bata sake aure ba, sai tayi zamanta a gidan da take ita da yaranta, daman ba guri ɗaya suke da abokiyar zamanta ba. Da aka raba musu gado sai ta riƙa juya dukiyar tana business da ita har abun ya bunƙasa.
Abdallah mutum ne mai tsantsan da kai, da kuma taka tsantsan da duniya, duk da irin tarin dukiyar mahaifinsa da ta mahaifiyarsa da kuma sarautar da suke da ita, be taɓa sa yayi unƙurin wulaƙanta kowa akan hakan ba.
Yana yawan samun matsala da Ƴan'uwansa a lokacin da yake gurin mai martaba, ganin irin son da yake masa, da kuma irin rufin asirin da Allah yayi masa, ga kuma aikin da shine sillar ɗaukaka a duniya.
Baya son fitina ko tashin hankali, hakan yasa ya tattara ya dawo gurin Mahaifiyarsa, sai ya warewa kansa part ɗaya a gidan, daman can ya zuba musu securities. Ko kaɗan Mai Martaba be so hakan ba, amman dole ya haƙura ganin hakan shine mafita a garesu gaba ɗaya.
Kuma hakan be rage ƙaunarsa a zuciyar Mai martaba sai ma ƙaruwa da tayi, dan a yanzu ne Abdallah yake nuna masa kulawa da biyayyar fiye da da. Ga kuma zumuncin daya ƙaru tsakanin Mai Martaba da Ummi, kasancewar Kakansu ɗaya, daman can auren gida ne aka yi. Idan har zai cilasta Abdallah yin abu to sai dai ya kira Ummi ya faɗa mata, dan baya tun karar Abdallah kai tsaye da abunda ya san zai iya sosa zuciyarsa.
Ya kan zauna yayi fira da shi kamar abokinsa, shine yafi kowa sanin sirrin Mai martaba, gashi ya karanci mahaifinsa sosai, da ido kaɗai zai oya gane abunda Mai martaba yake so ko ƙi.
A duk lokacin da suke tare baka taɓa ganin danuwa a fuskar Mai matarba, idan ba su yi labarin zamanin baya ba, tun Abdallah zai ɗauko masa firar matsalar tsaro da kuma sauran matsalolin da suke damun ƴan negeriya, ko kuma na siyasa.
Wani lokacin kuma idan ya shiga faɗar Mai martaba, zai zauna a kusa da shi ya riƙa karatun alƙur'ane, Mai martaba na sauraro, hakan kuma ba ƙaramin daɗi yake masa ba. Ga shi kuma Major abunda Mai martaba ya daɗe yana mafarki Allah be ƙaddari zai yi ba, ɗansa yayi.
Major General Abdullah Ahmad Mai-doki, an officer of very high rank in the army. Sunan ma kawai idan an faɗa daɗi yake ma Mai maraba.
*Back to Story*
****
Sai da ya bar cikin asibitin gaba ɗaya sannan Mama ta koma ta zauna, sai taɓe baki take, ita dai bata san ko waye ba amman zuciyarta na nasalta masa babban mutum ne, sai dai alaƙar dake tsakaninsa da Namra ne ya tsaya mata a rai.
Bata jiyo abunda suke cewa ba, amman dai ta ga Namra ta tsaya ta yi magana da shi, rai ta ya sosu tana jin kamar tana taya ɗanta kishi, sai yanzu take jin rashin natsuwa a lamarin Namra ya saukar mata.
‘To idan bata san shi ba, ya za'ayi tayi magana da shi? Miye ma na wani biyota har asibiti? Ko ƙe tsakanin su Allah masa ni’
A baɗini take zancen, a zahiri kuma sai taja tsaki, ta gyara zamanta, tana kalle-kalle kamar baƙuwar asibitin.
NAMRA POV.
Tsaye ta tararda shi jikin window, yana kallon wani ɓangare na asibitin.
Har Sallamarta daya amsa be sa ya juyo ba, jar sai da aje abincin ta ƙarasa inda yake tana murmushi.
“Haka ake so Allah ya ƙara lafiya”
Ya kalleta a karkace, yana mai jindaɗi har cikin ransa, shi kansa ya san yana daf da komawa dai-dai, dan yana jin kuzari a jikinsa sosai, ga kumburin kansa nan duk a cire.
Shi kan sa ya san he has to fight for his life, just to achieve his goal, he needs so many things and many things need him, so there's no point of giving up.
“I'm just trying na ga samu sauki sun sallame mu Next week”
“Inshallah indai har kana takawa haka zasu sallame mu da wuri”
Ta faɗa tana shafa bayansa, daɗi har fal har cikin ranta. Bayan ya ci abincin ta zuba masa ruwa ya sha, sannan ya ɗauko masa zancen gyara gida.
“Har yanzu Mama bata je kasuwa ba”
“Eh wai cewa tayi tun da ga wannan kuɗin Anty ta turo miki, ta ce a bar wacan a siye magani da shi, kin ga daman rantuwa tayi abunda yayi saura sai ta mai da mata”
“Kuɗin da Anty ta tura min har na biya bashin gado da su, sauran zan siye tufafi ne da wasu abubuwan kuma Anty tace na siye waya”
“Amman ai kin ci kin ga zinarin ki? Da kin siyar sai a ƙara ayi lalura, idan Allah yasa na warke sai na siya miki wani, wanda ya fishi ma zan siya miki”
Ta ɓata fuska tana kallonsa.
“Ni gaskiya ba zan siyar da zinari na ba, shi ƙadai ya rage min na kuɗi, kuma ko na siyar sana'ah zanyi da kuɗin, dan ba zan riƙa zuwa ina roƙon kowa komai ba”
Ya taɓe baki yana mata wani kallon.
“Hmmm Namra kenan, kina min kallon talaka ko? Har zan ce ki ranta min zinarin ki yi min complain, an faɗa miki zan dauwama a talauci ne hala? Kina ganin bana da mafitar da zan biya ki ko? Nima zan yi kuɗi Namra, zan yi arxiki irin kuɗin da baki taɓa mafarkin Asim zai yi ba, akwai buƙatar nayi kuɗi ko dan na rama bikin da aka min”
“Idan nayi magana zaka ga laifi na, haba Asim shikenan sai ace kullum nice zan riƙa biyar dangi ina roƙon su abu? Yau da gobe sai Allah, na rasa komai dana mallaka, sauran kuɗin nan daya rage min da shi nake cefane, kuma siyen abinci ba haƙƙina bane, kai Allah ya ɗorawa amman ka ɗauki kuɗin nan ka bawa Mama, idan nayi magana kace rantowa kayi alhalin kuɗinka ne na adashe!”
Dammm ya wulga mata wani kallo da mugun faɗuwar gaba. Ya akayi ta sani? Ina ta ji?Ko dai Mama ce tayi subul da baka ta faɗa mata. Ƙoƙarin kare kansa yake yana naɗe tabarmar kunya da hauka.
“Allah sarki rayuwa, talauci be yi ba, a yau har ni kike tunanin na ɓoye miki wani abu, yau ni kike yi ma gori akan kin siye abinci, ai ban san ba dan Allah kika aure ni ba sai yau, kina ganin kamar ba zan iya rayuwa babu ke ba ko? Kina ganin kamar da arzikin ki nake ci ko? Kina ganin ke kika min magani ko? Da gaskiyar Mama yanzu cewa za ayi duk ni na ƙarar miki da komai na ki, daman haka kike so ace na auro ki na zo na aje ki ina cin amanarki ko? So that ki samu damar fakewa da na yaudare ki, daman na san ba dan Allah kika aure ni ba”
Tun da ya soma kwarara zantukansa kallonsa kawai take tana mamakin kalamansa, wasu zantukan ma bata san inda suka dosa ba. Yau kam ya fara fito mata a kowaye shi, ya bayyana mata abunda zuciyarta ta soma zargi akansa.
“Na bar jindaɗin gidan mu, na zabe ka. Na watsar da karatuna na bika, saboda kar kace na yaudare ka. Na sadaukarda komai nawa saboda kai, amman duk ban tsira ba? Irin kallon da kake min kenan? Nice ya kamata ace na zarge ka tun lokacin da na ji abunda kuke magana kai da Mama amman na taushe zuciyata ina ƙoƙarin yaƙi da ita akan ka, ka kan nuna son iyayena su taimaka kama amman duk be sa na zarge ka ba, miyasa baka tausayina ne? Yanzu na gano dalilin rashin son da Mama take min, kuna min kallon wawuya wacce bata san ciwon kanta ba.
Son ka ne Asim shine ya rufe min ido na kasa ganin laifin ka, babu irin furucin da ba amin ba akan ka, amman na dage sai na aureka, a tunani na kana min irin son da nake maka ne”
Ta ƙarasa maganar murya ƙasa-ƙasa irin kifi musulmim nama, tana hawaye. Shi kam tsire baki yayi ya kalleta
“Kowa ya sani ba tsakani da Allah kika aure ni ba, sai da wanda zai aureki yace ya fasa sannan aka nemo ni, yanzu kuma kina son yin amfani da damar da kike da ita na rashin lafiya ki kula wasu mazan a waje”
“Me kake nufi?”
“Kin fi kowa sanin abunda nake nufi, waya kawo ki yanzu cikin asibitin nan? Ina kallon yadda ya rako ki ya koma, ko kin maidani mahaukaci ne, talauci ba yin kaina bane Namra, dan ina talaka ba zaki wulaƙanta ni a banza ba”
Ta miƙe tsaye tana masa kallon mamaki, har kofin ruwan dake hannunta ya zube.
“Ka zarge ni da komai, amman ban da Zina, dan ban sha nono ba, mahaifina be yi da ƴar wasu ba, dan haka ba za'ayi da ni ba, ban aikata zina ina budurwa ba, ba zan aikata da aurena ba. Kai butulu ne Asim wanda be san hallaci ba, ɗan bushiya mai soke uwar goyonsa a baya....”
Tasss ya watsa mata yatsunsa biyar a gefen fuskarsa, a zaune da yake, sai wani zanzana yake kamar ya riƙota yayi ta dukanta.
“Kim fita da ainahin kalar ki Namra, daman kin min duk abunda kika min ne dan wata rana ki min gori? To mina samu a auren naki? In banda baƙar ƙaddara miye ke bi na?”
Dafe kuncinta tayi ta juya a guje tana wani irin kuka mai taɓa zuciya, ta fice ɗaga ɗakin.
RASHIDA POV.
Kukanta ne ya shigo da su Momy a ɗakin. Duk tambayar da suka mata kasa amsawa tayi sai kuka take kamar wace aka cirewa rai.
“Ya sake ni Momy ya sake ni! Na shiga uku na lalace na ba ni Momy mutuwa zan yi, Wayyo Allah na”
“Me kika masa?”
Momy ta tambaya hankali a tashe. Ta kardar kawai ta iya nunawa Momy tana kuka sosai.
Da sauri Momy ta ɗauki takardar ta buɗe.
“Ni Hilal a yau na saki Rashida saki ɗaya”
Momy na gama karantawa ta rufe takardar tana faɗin
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Sai ta riƙata, ta zaunar saman gado tana girgizata, ganin tana ƙoƙarin fita hayyacinta.
“Ke Rashida kwantar da hankalin ki zan sa ya maida ke kin ji?”
Ta rirriƙe Momy gamgam tana zare ido.
“Da gaske Momy?”
“Da gaske mana, ki kwantar da hankalin ki kinji? Zan yi magana da shi”
“Toh”
Tayi zurun kamar sabuwar mahaukaciya. Sai kallon Ummu Faisak take wace ta shigo yanzu.
“Lafiya miya same ta?”
Ta ƙarasa da sauri tana tambaya. Momy bata iya faɗa mata komai ba ta fita ta kira likita, yayi mata allura, cikin ƙanƙanen lokaci ta samu bachi.
Sai da suka fito sannan Momy take labarta mata abunda ya faru cikin yanayin damuwa.
“Af ai da sauƙi tun da sakinta kawai yayi be kashe ta ba, ai a yanayin yadda ya bar gida na ɗauka yana zuwa zai kashe ne ma, kin ga yadda yake ji da matar nan? Hmmm”
“Aiko idan ka ganta kamar ta ƙwarai, ƙo dai wani abun ne ya haɗa su?”
“Ai haka ƴan matan zamani suke, suyi miki laflaf su kwace miki miji sannan su koreki, ai wannan saki daga gani bana banza bane mace na ciwon zubar ciki kuma asibiti gurin iyayenta? Hmmm”
“Ai yanzu sai an bincika za a ji ko minene, bari na faɗa ma Daddyn”
Cikin yanayin damuwa da ɗaurewar kai Momy take maganar.
Hilal ko da ya koma gida ya tarar yaransa sun dawo, daga gidan Hajiya, ko wanne fuskarsa babu walwala sun saka Kalsoom gaba, kamar su mata kuka.
“Hey kids”
Ya faɗa yana ƙokarin zaunawa sound so cool and funny. Sai duk suka nufo shi suna faɗar.
“Daddy wai Hajiya tace mana Ammyn mu ba lafiya tana asibiti”
Ya ɗan sosa kansa, sam ya manta yace kar Hajiya ta faɗa musu. Kalsoom dake ɗauke Rafiq ta nufo shi tana faɗin
“I try to explain but.. ”
Da ido yayi mata alama da tayi shiru yaja hannunta ya zaunar da ita kusa da shi, ya kalli yaran.
“Listen kids Maman ku ta ji sauƙi sosai, har ma tace na gaishe ku”
“Daddy ina son na ganta”
“Ba zaki ganta yanzu ba, amman ajima zan kira miki ita a waya ku gaisa”
“Tau”
Ulfah ce ta wayance, jin ance taji sauƙi, Ezzah kam ƙin sakewa tayi sai ƙoƙarin kuka take.
“Duk sun ci abinci, amman ita ta ƙi ta ci”
Ƙalsoom ta faɗa tana kallon Ezzah. Hilal ya kai hannu ya riƙo hannunta.
“Sweetheart ki ci abinci kin ji? Mamanki tana nan lafiya”
Kai kawai ta ɗaga masa ta share hawayen da suka zubo mata, ta nufi ɗakinsu.
******
Rashida bata farka ba sai dare, tea aka bata ta sha sannan ta kora da magani. Yanzu nen abunda ya faru ɗazu yake dawo mata, a ƙwaƙwalwa, da sannu-sannu take tuna komai, sai ta gane ashe ba mafarki ne take ba.
A hankali hawaye masu zafi suka fara sauko mata, zuciyarta na ƙona kamar garwashi.
Taya zata juye rayuwa babu Hilal? Taya zata bar ƴaƴanta a hannun Kalsoom? Yanzu me zata faɗawa iyayenta? Ga kuma ciwon dake jikinta, da wannen zata ji? Wani irin kuka take irin kukan nan na baƙinciki da baka son kowa ya ji.
Wayarta ta janyo ta buɗe password ɗin, kamin ta taɓa komai sai ga saƙwanin sun taso sama, na mutane da kuma mtn.
Na number Amira ta fara buɗewa, cikin ƙarfin hali ta ƙaranta, ta yi reply sannan ta aje wayar gefe tana kallon ƙanwarta Sa'adatu take bata haƙuri.
“Momy tace zatayi ma Daddy magana sai su yi magana da Hilal ɗin”
“A'a bana da buƙata nice nace ya sake ni, karki bari Momy ta kira shi, kije kice nace karta kira shi”
“Amman Adda...”
“Kawai ki faɗa mata, nice nace ya sake ni, kije ki faɗawa Momy”
Sa'adatu ta tashi ta fice tana hawayen tausayin ƴar'uwarta. Rashida ta share hawayen da suka zubo kata tana kallon wayarta dake ringing.
Number Hilal ta gani, har tayi kamar karta ɗauka, sai kuma ta danna picking ta kara a kunne, muryar Ulfah ta ji tana mata ya jiki kamin Ezzah ta karɓa.
“Ammyn wai kin ji sauƙi?”
Cikin yanayin damuwa Ezzah ta tambaya, sai kawai Rashida ta fashe da kuka.
“Na ji sauƙi Ezzah, amman ba zaki sake ganina gidan ku ba, Abbahn ku ya sake ni ya zaɓi Antyn ku a kaina, yace baya so na Antyn ku yake so, ita zata zama mamanku daga yanzu, Abban ku yace kar na sake shigo masa gida....!”
Hilal be san me Rashida take ce nata ba, amman hawayen da ya ga suna zuba a idon Ezzah y tabbatar masa ba lafiya ba. Da sauri ya ƙarɓe wayar ya kashe, yana kallon ƴarsa dake wani irin ɗaukar numfashi tana kuka.
Kamin yace wani abu kiran Hajiya ya shigo wayarsa, cikin sauri ya ɗauka.
“Hello Hajiya”
“Ka zo yanzu ina neman ka”
Bata tsaya jiran abunda zai ce ba, ta kashe wayar, hakan ya tabbatar masa da ranta a ɓace yake.
MARDIYA POV.
Tana suɗar yatsun hannunta ta kalli Inna tace
“Wai Inna baki san wata addu'ah da ake karantawa ba, wallahi sai nayi ta mafarki wuta na bina, kullum sai na farka a firgice”
“To ni wata addu'ah na sani, kawai ki riƙa anbaton Allah dai idan kika firgita, kina fa cikin maƙiya, kowa ya saki gaba, ko wannan yarinyar Namratu ba ta iya miki sheri ba”
“Hmmm Wallahi ta Allah ba ta su ba, kuma abun duk ba a so sai gan shi gare ni wallahi, kuma Wallahi tallahi indai ina numfashi, sai na rama abunda Namra tayi min, sai na ɗasa mata baƙincikin da har ta mutu ba zata manta da ni”
“Ai ko ita zata so ki haukace, ni wallahi kin baɓ mamaki karma wace aka ɗaurewa baki kin ki shiru tana ta cin zarafin a gaban mutane,
Kuma ko abunta kika ɗauka ai dole ki ɗauka mace sai rowar tsiyar, ko gobarar da tayi ai zakkace ta fita, sai ƙaryar banza wai ita ƴar masu kuɗi ce ƴar masu kuɗi zata zauna nan a wulaƙance”
“Ƙaryar banza ce kawai ba wani ƴar mai kuɗi, ni ko cikin nan nata sai naga kamar zubar da shi tayi wallahi”
“Saboda me? To ko bana mijin ba ne”
“Waya sani, daga maƙota ta ɗauki ƙiyayah ta ɗora min, ai ko abunta na ɗauka be dace ta ci min mutunci cikin mutane ba”
“Ke ai wauta kika yi da ace tun lokacin kinje kin siyar ya za'ayi ta gani”
“Toh ai ina jin tsoro ne kar naje siyarwa asiri ya tono”
“To ai yanzu kin tonawa kan ki asirin”
“Uhmm”
Mardiya ta unƙura ta tashi ta fice riƙe da kwanon. Inna ta bita da kallon tana tsakin abun haushi.