Wani kallo Ezzah take yi ma Kalsoom tana hawaye, maganganun mamanta na mata yawo aƙwaƙwalwa. Daga Hilal har Kalsoom ɗin kallonta suke, ba sun dalilin kukan nata ba, amman sun san ba abun ƙwarai ne Rashida ta faɗa mata ba. Doc ya kai hannunshi ya dafa sai kawai ta ƙwaɓe hannu ta juya da gudu ta nufi ɗakinsu.
“Daddy ƙyale ta Mama tace ta ji sauƙi fa”
Ulfah ta faɗa tana lanƙwamo wuyan Kalsoom da Hilal. Ɗan murmushi Kalsoom tayi tana riƙa hannunta.
“Na sani ta ji haushi ne ba a kai ta ta ga Mama ba”
Hilal ya miƙe tsaye zuciyarsa na raya masa akwai abunda Rashida tacewa ƴarsa.
“Bari naje gurin Hajiya tace tana nema na”
“Okay Allah ya kiyaye bari nayi magana da Ezzah”
“No karki yi magana da ita yanzu, bari sai da safe”
“Okay Allah ya tsare”
“Daddy Allah ya tsare”
Ulfah ta faɗa tana tsalle.
“Amin Sweetheart sai na dawo”
Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya fice. Cikin ƴan mintuna ya isa gidan Hajiyarsa, ba tare da fargabar komai ba ya fito mota ya shiga cikin gidan.
Yana shiga falon ƙannensa da ƴaƴan ƴan'uwansa da suke gidan suka soma gaidashi suna masa sannu da zuwa, sai da ya gama gaisawa da su sannan ya nufi ɗakin Hajiya.
Da sallama ya shiga, ta amsa masa ba tare da ta kalleshi ba, sai sarƙoƙin dake gabanta take gyarawa, har ya zauna ƙasan Carpet yana ɗan kallon yanayinta.
“Hajiya ga ni Allah yasa ba laifi na yi ba”
“Au ashe ka san kayi laifi? Yanzu abun da kayi ma yarinyar nan dai-dai ne? Ban samu naje ganinta ba sai da yamman nan ina zuwa suka ce min wai ka sake ta, duk kunya ya kamani”
Ya ɗan shafa kansa.
“Ayyah Hajiya sorry ban nemi shawarar ki ba, nima a kai tsaye sakin ya zo min, kuma bana da wata mafita sai ta sakin ne”
“Amman fisabillillahi baka tashi sakinta ba sai da tayi ɓari? Kai baka ma tsoron ace Kalsoom ce? Na san kana haƙuri da ita, dan kai ne kaɗai zaka iya ɗaukar abunda Rashida take maka, amman ai tuni ya kamata ka yi haka ba yanzu ba”
“Hajiya idan na sake ta a lokacin da Kalsoom bata nan wa zai kula da yaran? Kuma lokacin ba zan iya sakin ta ba saboda bata min komai ba”
“To me ta maka yanzu? Tun tun tun baka gano illarta ba sai yanzu? Hilal bana son ka zama cikin irin mutanen fa”
Yayi ƙasa da muryarsa yana son faɗa mata gaskiyar lamari.
“Hajiya ba zan iya ɓoye miki ba, Rashida tana da Hiv kuma ni da Kalsoom da ƴaƴana duka ba mu da shi sai ita, kuma ta hanyar sex ta samr shi”
Wani abu Hajiya tayi da hannu irin na ƙyama da tsoro idan sun zo ma mutum a lokaci ɗaya.
“Kana nufin Rashida tana bin maza a waje kenan?”
“Ba wai ina nufi bane, haka ɗin ne, tun da ga alamu ya nuna kuma ta tura ma likitan da na ba jininta ya auna kuɗi dan ya ɓoye yace ba haka ba ne”
“Idan ko har haka ne, ba kayi laifi ba Hilal dan irin wannan matar babu mai son ta zamo uwar ƴaƴansa, ni dama can yarinyar nan bata min, ai ƙara ma daka sake ta taje can ta ƙarata ita da uban nata daya tsaya mata”
“Amman Hajiya dan Allah karki faɗawa kowa saboda rayuwar ƴarana, zasu iya shiga wani hali kuma duk wanda ya ji zai riƙa mana wani kallo ne”
“Haba Hilal ai wannan sirri ne tsakanin ɗa da uwa, babu wanda zai ji har abada, amman me zaka faɗawa iyayenta ne?”
“Zam ce ta zubar min da ciki ne shiyasa na sake ta, ai nasan ba zata taɓa faɗa musu gaskiya ba”
“Allah ya kyauta, Mahaifin ka ma be sani ba, dan ban faɗa masa ba, nima haka zance masa. Ai Allah ba azzalumin kowa bane shiyasa asirinta ya tono tun wuri da sai duk ta laƙa muku shi sannan a gano”
“Kwata-kwata matar nan ta fita rai na wallahi, babu abunda bana mata, babu irin haƙurin da bana yi da ita akan zamantakewar mu, akan me zata je ta bi wani a waje? Idan akwai abunda nake mata wanda bata so ko kuma be gamsar da ita ba ai sai ta faɗa min ai tattauna aƙe so zamantakewar aure da fahimtar juna, dan me zata watsar da yaranta taje ta aikata wannan mummunan abu? Allah kaɗai ya san iya tsawon lokacin data ɗauka tana aikatawa, nayi nadamar zama da ita Hajiya.
Da nasan haka zata zama da tun farko ban aureta ba, kuma ban sa laifin kowa ba kamar na mahaifinta dan shine ya tsaya kai da fata akan dole sai ta yi aiki, saboda kawai baya son aurna da ita, yanzu ai sai ya aura mata wanda yake so ”
“Ƙaddarori ne idan Allah ya kawo sai haƙuri, Allah dai ya ƙara tsarewa”
“Amin ni zan wuce”
“To Allah ya tashe mu lafiya, akwai waina a kula idan zaka ci”
“A'a bana son komai yau sai da safe”
Daga haka ya fice, Hajiya na kallonsa cike da tausayawa.
Koda ya koma gida Ulfah da Rafiq sun yi bachi, Kalsoom ce kawai a falo, ta ƙurawa tv ido, duk da hankalinta ba nan yake ba.
Shigowarsa yasa ta ɗago kai ta kalleshi fuskarta da yanayin damuwa.
“Har ka dawo?”
“Eh ke kaɗai ce a falon?”
“Eh me Hajiya tace maka?”
“Tace idan na zo na cire miki kunne guda na kai mata”
Ya faɗa yana jan kunnenta har sai da tayi ƴar ƙara
“Ouuchhh nima tace na kai mata hancin ka”
Taja masa hanci ta tashi da sauri daga gurin. Ƙyalƙyalewa yayi da dariya, yana kallon kunkurunta.
“Kalsoom zo nan”
“No no no”
“Please?”
“No no”
Ta nufi ɗakinta da sauri, sai ya bita yana dariya.
******
Washe gari da wuri Kalsoom ta tashi kamar yada ta saba, sai da ta ciro musu uniform ta ɗora musu saman kujera sannan ta nufi kitchen ta haɗa musu breakfast, har ta gama haɗa breakfast ɗin tunanin Rashida take, tana ganin kamar Hilal be kyauta ba idan be barta taje ta ganta ba.
Sai da ta zuba musu abincin a kula sannan ta shiga ɗakinsu ta tashe su, Ulfah ta fara tayarwa t miƙar da ita tsaye tana girgizata, sannan ta shiga tashin Ezzah
“Ezzah tashi ku yi shirin makaranta na gama muku abinci”
“Ki ƙyale ni ni ba zan je ba!”
Ta faɗa a tsawace tana jan bargota ta ƙara rufa, Kalsoom bata sake taɓa ta sai kawai ta shiga da Ulfah ta haɗa mata ruwan wanka ta fito ta nufi ɗakin Doc.
Zaune ta tararda shi yana karanta saƙon da Rashida ta aiko masa. Daga bakin ƙofa Kalsoom ta tsaya tace
“Doc Ezzah tana ta fushi har yanzu”
Ya ɗago ya kalleta
“Kamar ya me tace?”
“Wai ba zata je makaranta ba”
“What! Ba zata je makaranta ba as how? I hate nonsense”
Ya aje wayar dake hannunsa ya nufi ɗakin nasu, Kalsoom na biye da su a baya, sai dai bata ƙarasa shiga ɗakin ba, ta tsaya daga bakin ƙofa.
Yana shiga ya shiga tashinta, tana jin muryarsa sai ta buɗe bargo ta buɗe ido, fuska a takure tana kallonsa.
“Tashi ki yi shirin makaranta, kika ce ba zaki makaranta ba?”
“Zan je ni bana son tana tashi na ne”
“Saboda?”
“Ni bana son ta Ammyn ta faɗa min itace ta koreta baka son Ammyn Anty kake so kuma ba zaka sake kai mu inda take ba sai dai mu zauna da Anty kuma ba zata sake zuwa nan gidan ba, ni bana son ta Daddy i hate her”
Buge mata baki Hilal yayi, ya katsa nata tsawa.
“Kar na sake jin bakin ki ya furta irin wannan kalamin, tashi kije ki shirya zuwa makaranta ko na zane ki yanzu nan”
Da sauri ta tashi ta shige bathroom tana kuka. Kalsoom dake tsaye jikin ƙofa tayi saurin barin gurin, ta nufi ɗakinta.
A gaban madubi ta tsaya tana hawaye, zuciyarta sai bugawa take,motsin shigowar Doc ne yasa ta saurin juyo ta kalleshi
“Doc ka rabu da Rashida ne?”
Ya saka hannyensa aljihu yana ɗaga mata kai alamar eh.
“Me yasa?”
“Hakan shi yafi dacewa”
“Dan Allah ka dawo da ita ƴaranta suna da buƙatar ta”
Ta faɗa da muryar kuka hawaye na mata zuba. Matsowa yayi kusa da ita ya ɗafa kafaɗunta yana magana a hankali.
“Basa buƙatar ta matuƙar suna tare da ke, i trust you zaki basu tarbiyan daya kamata, kuma zaki kula min da su, ba zan taɓa maida Rashida ba ko da hakan yana nufin ƙarshen rayuwar ƴarana ne”
“Me ta aikata maka ne?”
Ya rumgume ta ƙam-ƙam a ƙirjinsa yana shirin mantar da ita zancen da suke. Sai gurin Takwas saura ya bar ɗakin. Ko da ya fito duk suna falo suna jirana, Ezzah idonta yayi ja sosai daga ganin alamu kuka tayi sosai, amman sai yayi kamar be kula ba har ya kai su makarantar be yi Ezzah magana ba balle ya rarrasheta.
Daga makarantar ya wuce asibiti dan jin kiran da Rashida take masa, sam be ji wani abu a ransa ba, na tsoro ko kuma na tunanin irin abunda ƴan'uwanta zasu masa.
Mahaifiyarta ya tarar a ɗakin dare da Babanta sun sata gaba, ita kuma sai rusar kuka take. Daddyn ta na ganin Hilal yayi kansa kamar zai dake shi.
“Me ka zo yi cikin asibitin nan me ya kawo ka? Marar mutunci marar tarbiya, wanda be san hallaci ba, sai yanzu data gama zazzage maka mahaifarta dan ka auro wata zaka sake ta? Daman can ne bana son auren ku da ita dan ban yarda da tarbiyarka ba”
“To ai yanzu sai aka aura mata wanda ka yarda da tarbiyarsa, idan ta cika idda zata iya auren wanda kake so”
Momy ce tayi saurin riƙe hannun mijinta ganin yadda ya ware zai zabgawa Hilal mari.
“Karka so ma faɗa min maganar banza, ko ba daɗe ko ba jima sai Allah ya jarrabe ka da son Rashida kuma wallahi ba zan bari ta koma maka ba, tun da ka ci amanar ta”
“Nima ba zan koma ba Daddy nice na nemi ya sake ni, kuma yanzu nice na kira shi akwai abunda zan faɗa masa, dan Allah ka bar ni nayi magana da shi”
Rashida ta faɗa cikin kuka. Wata muguwar harara Mahaifinta ya watsa mata kamin ya fice shi da Momy da idonta ke cike da hawaye.
Cikin shesshekar kuka Rashida ta kalli Hilla ta soma magana dashi tana jin zuciyarta kamar zara narke.
“Hilal ka san ina son ka, shiyasa ka yi min haka ko? Duk irin zamantakewar da muka yi da kai haka zaka saka min? Taya kake tunanin zan rayu babu kai”
“Ta yadda kike rayu da wani na a lokacin da nake tare da ke, haka zaki rayu da wani a lokacin da ba ni, ƙaryar so kike min Rashida tun da har kika iya aikata zina da wani namiji bayan ni ban rage ki da komai ba”
“Ni ba dutse bace Hilal, dole akwai lokacin da zan buƙace wani a kusa da ni, a lokacin bana gida, idan nayi kwalliya sai dai mutanen office su yaba min, su za su gani ba kai ba, kuma dole ce tasa na fara aikatawa kamin abun ya zame min jiki”
“Faɗa min dawa kike tarayya?”
“Ba zan faɗa maka ba, amman ina son ka san da wani abu ɗaya, har a bada ba zan daina son ka ba, kuma ina roƙon alfarmar karka faɗawa kowa sirrina”
“Ba zan faɗawa kowa ba, kuma ba saboda ke ba, sai dan saboda Ƴaƴana”
“Ba zaka sake jindaɗin rayuwar aure ba Hilal, iya rayuwar da muka yi itace ta jindaɗin aure, wallahi Kalsoom ba zata mallake min ƴaƴa ba, idan har ban zauna da kai ba babu wata mace da zata zauna da kai a duniya da sunan rayuwar aure, baka isa ka raba ni da ƴaƴana ba, wata mace kuma bata isa ta maye gurbina ba”
Matsowa yayi kusa da ita cikin zafin rai zai mata magana. Sai ga Asmee ta shigo ɗakin. Sai kawai ya juya ya fice ba tare daya faɗa mata abunda yayi niya ba.
Da sauri Asmee ta ƙaraso kusa da ita ta dafa ta.
“Ke lafiya Hilal yake kuwa? Wai jiya bayan na bar nan asibitin na ji mummunan labari da gaske ne kuwa?”
Kwantowa tayi kikin Asmee tana kuka
“Da gaske ne Asmee ya sake ni”
“Me kika masa?”
“Ban masa komai ba haka kawai ya sake ni”
“Hmmm sherin kishiya ne, ai kinsan yadda mijinki yake son ki ba zai sake ki haka nan kawai ba, wani asiri ne aka masa”
“Ba zai mai da ni ba, shikenan ƙarshen aurena da shi”
“Wallahi ƙarya ne, ƙarya ne wallahi Allah ya sa kiji sauƙi da wuri, kin ga malamin nan da na kai ki gurinsa? Wallahi ki koma yayi miki aiki a gigice Hilal zai maida ke”
“Zan koma yayi min aiki, amman bana Hilal ya mayarda ni ba, sai dai na wani abun daban, na riga na yafe Hilal har a bada”
“Kar kice haka Allah dai ya baki lafiya”
Ƙara fashewa tayi da kuka ta ƙamƙame Asmee tana jin wani irin zugi da zuciyarta ke mata.
AMIRA POV.
Daga ita sai tawul ta fito daga banɗaki, ta zo ta zauna gaban mirrow tana taje kanta. Sai da ta gama ta shafa mai tayi kwalliya sannan ta kalli Guy son dake kwance saman gado yana kallonta tace
“Amman kasan matar nan ta raina mana hankali? Sai da tasa muka bincika ko waye likitan sannan zata ce mana wani ta fasa”
“Manta da ita kawai, akwai wani aiki da zamu je yi Abuja jibi, akwai wanda ya kira ni kuma na san zamu samu kuɗi da yawa”
Ta baro inda take zaune, ta nufo inda yake tana wara ido
“Da gaske?”
“Na taɓa miki ƙarya?”
“No I'm just asking, you know how a like Abuja”
“Yeah shiyasa zan je da ke ai”
Rumgume shi tayi cike da jindaɗi, shi kuma ya shiga shafa jikinta.
NAMRA POV.
Cikin wani irin kuka ta isa gida. Yau duk wani tsoro da take na gidan be ziyarce ba, dan baƙinciki dake tare da ita tafi tsoro, yadda ta ga dare haka taga dare, sai ta tashi tayi sallah, tayi addu'ah samun mafita da sauƙi a zuciyarta. Tana gurin bata tashi ba har aka kira sallah asuba, kasa cin komai tayi da safe, ji take kamar ta kashe kanta ta huta, kalaman Asim sun tsaya mata a rai, sai yanzu ta fara gasgata kalaman Anty Amarya, ayau Asim ya nuna mata ko waye shi, ya buɗe mata sirrin dake ransa, sannan ya zarge ta da abunda wani be taɓa mata ba.
A tau ta tabbatar da tayi zaɓen tumun dare, sai a yanzu tana ganin laifin zuciyarta.
“Miyasa kika bar ni na kamu da son wanda ba dan Allah yake so na ba? Dan me baki bar ni na so waninsa ba? Duka yaushe muka yi aure da shi amman yau ya sauya min ya nuna min abunda ban taɓa mafarki ba? Yanzu ya zanyi da rai na? Na bar karatuna saboda shi na zo garin da ban san kowa ba saboda shi amman duk ban masa ba?”
Ita ƙaɗai take magana da kanta, tana wani irin kuka mai taba zuciya. Bata ji a yau zata iya kwana a katsina, dan a yau bata buƙatar kowa a kusa da ita sai yan'uwanta, da mahaifiyarta, tasan ko hira kawai tayi da su zai rage mata damuwa, sama da zaman kaɗaici da take yanzu.
Tashi tayi ta matsa kusa da inda ta aje ƴan komatsanta.
Jakarta ta buɗe taga kuɗin da yayi mata saura, sai ta shiga BQ ɗin ta ɗauko Sarƙa da wayarta ta saka a jakarta ta sauya hijabinta ta jawo BQ ɗin ta fito tana kuka.
Sai da ta tari Napep ta shiga sannan wani tunanin ya zo mata. Idan ta koma gida da wane ido zata kalli Anty Amarya? Me zata cewa Abbah? Masu jiran su yi musu dariya tasan zasu yi. Har ya kai ta tasha bata samawa kanta wata mafita ba, sai dai hakan be hana ta shiga motar sokoto ba, tun da bata da wani gurin zuwa sai can.
ABDOOL POV.
Yana zaune ƙasan Carpet yana cin abinci, Ummi dake zaune saman kujera ta tsare sa da ido tana kallon ɗan nata cike da tausayawa.
Sai da ya gama cin abincin sannan ya kalleta yana murmushi.
“Ummi wannan kallo ai sai ki tsorata ni, gani zanje Abuja gobe ai sai kisa nayi tunanin ko mutuwa zan yi”
Ɗan murmushi tayi ta kawar da kai.
“Kawai ina tausayin ka ne, jiya da zafin jiki ka kwana saboda tunanin nan yarinyar how i wish ina da wani abu da zan yi akai”
“Karki damu, ni ai haka jiki na yake, mutane suna cewa ba komai bane dan kaji mutum da zafin jiki”
“Ba irin naka zafin ba, wacan ɗan ɗumi ake nufi kuma shi ma a mace ne ba namiji ba”
Dariya yayi ya tashi tare da plate ɗin
“Ummi kenan, ni fa bana da wata damuwa yanzu sai ta Mai Martaba”
“Zan yi magana da shi ai na faɗa maka, kawai kai dai ka samu natsuwa kuma ka kwantar da hankalin ka”
“I will try inshallah”
“Ni Allah yasa ma Abujar nan da zaka je ka haɗu da wata wanda zaka so fiye da wannan ma”
“Ai gurin aiki zamuje ba gurin hutawa ba, idan kuma kina son na ɗauko miki soja shikenan, sai na auro soja”
Wani tsaki taja ta ɗauke kai ta mayar gurin tv. Shi kuma yayi dariya ya shige kitchen.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺*
*© Khadeeja Candy*
*PAGE - 42*
NOT EDITED ⚠
Da yamma lis Namra ta sauka babbar tashar sokoto, sai da kowa ya gama fita motar kasancewar ita ce a can baya sannan ta fito jiki a sanyaye, tana kalle-kalle kamar mai tunanin inda zata je.
A hankali ta cira ƙafarta da tayi mata nauyi saboda zaman mota ta fara takawa, ta doshi ƙofar fita tashar gabanta sai faɗuwa yake kamar zai fito, wani abu ta ji ya zo ya tsaya mata a zuciya, yana ƙoƙarin danne mata numfashi.
Ta daɗe a tsaye bakin ti-ti sannan ta tari Napep ta shiga, sai da ya fara tafiya da ita suka yi nisa sannan ta ɗan karkato ya tambayeta inda za a kai ta ganin bata ce masa komai ba tun da ta shiga Napep ɗin.
“Hajiya ina za mu?”
Shiru tayi kamar mai tunani, ta ɗauki tsowon lokaci bata amsa shi ba, har sai da ya ƙara tambayarta.
“Clapperto....road, gurin....gawon nama”
“Dari biyu zaki biya Hajiya”
“Ok..ay.. Allah Kai... Mu lafiya”
“Amin”
Ya kai hannu ya kunna waƙar Umar M Shariff ta duniya makaranta. Sauraren waƙar take tana hawaye, hankalinta da tunaninta gaba ɗaya ya tattara ya koma gidan su da take tunkara yanzu. Abunda zata faɗa musu take ta saƙawa amman har ta saka samun mafita.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ta furta a hankali lokacin da Mai Napep ɗin ya kunna kai cikin unguwar. Jin tayi kamar tace ya juya da ita, sai dai idan ya juya da ita ɗin ina zata ce ya kai ta?
“Ya isa...”
Ya faɗa a lokacin daya kawo bakin ƙofar gidan su. Sai da ta share hawayen idonta sannan ta ciro kuɗinsa ta miƙa amsa, sannan ta fita jikinta har rawa yake irin na tsoro da rashin gaskiya yana tare da ita.
Sai da Mai Napep ɗin ya wuce, sannan ta doshi ƙofar gidansu, cikin wani irin mugun faɗuwar gaba. Har ta kai hannu zata tura ƙofar gate ɗin sai kuma ta tsaya tana jan numfashi.
Tafi kowa sanin waye mahaifinta, ta kuma san halinsa ba zata manta furucin da yayi mata ba, bata san iya furucin da zai ƙara mata ba.
Babu wacce ta faɗo mata a rai, sai Gwaggo Kulu, ƙanwar Abbah, mahaifiyar Anty Yasmin.
Tasan ƙanwar Abbah ce amman Abbah yana jin maganar ta sosai kuma tasan yadda Gwaggo Kulu take son ta cikin ƴaƴan Abbah.
Juyawa tayi da saurin ta nufi farƙon unguwar dan ta can ne zata fi saurin samun abun hawa. Sai da ta kusa ƙarasawa babban ti-ti sai ta ga Motar Maryam ta kunno kai cikin unguwar. Da sauri Namra ta kawar da fuskarta dan kar Maryam ta ganta, ashe tayi a banza dan baya-baya Maryam tayi da mota ta fara leƙen fuskarta, hakan be gamsarda ita ba har sai da ta faka motar gefe ta fito ta fara bin Namra da ƙafa tana kiran sunan ta.
“Anty Namra ke ce?”
Juyowa Namra tayi ta kalleta idonta da hawaye ta ɗaga mata kai.
Wani irin tsalle Maryam ta daka ta rumgumeta tana ihu.
“Wallahi ban ɗauka ke bace nayi zaton wata ce mai kama da ke, Anty Namra ina za ki?”
“Gidan Gwaggo Kulu zan je”
Ta faɗa cikin kuka tana rumgume da ƙafaɗar Maryam. Maryam ta ɗago ta kalleta
“Miyasa ba gida kika zo ba?”
“Amman nasan Abbah ba zai bari na zauna ba, korata zai yi”
Maryam ta dafa kafaɗunta.
“Fushi kika yi?”
Tayi shiru bata amsa ta ba, hakan ya tabbatar ma Maryam amsar tambayar.
“Wani abun Asim yayi miki ne? Karki ɓoye komai Anty Namra ki faɗi abunda yayi miki, dan ba zai yiyu ya taɓa mana ƴar'uwa ba mu ƙyale shi”
“Be min komai ba, ni dai kawai na gaji da zaman can ne”
“To ki zo muje gida”
“A'a ni ba zan je ba, Abbah zai kore ni kuma Anty ba zata ji daɗi ba”
“To ya zaki yi? Kina da inda ya fi miki gidan uban ki ne? Ko yanka namanki zai yi yayi gunduwa-gunduwa da shi dole ne ki shiga tun da baki da inda ya fi miki nan”
“Ni dai ba zan je ba, gidan Gwaggo Kulu zan je”
“To muje na kai ki”
Maryam ta faɗa tana nuna mata motarta. Kamar ba zata shiga ba, sai kuma ta nufi motar ta buɗe ta shiga. Sannan Maryam ta shiga driver seat ta tashi motar, ribas tayi ta juya ta inda ta fito, sai da suka hau babban ti-ti sannan Maryam ta kalleta tana takaicin halinta tace
“Wani lokacin Anty Namra kina ban haushi da mamaki wallahi, kina abu kamar ba kece yayata ba, abunda kike yi ko Aisha da take ƙaramar mu ba zatayi ba. Kin san abunda yake cutar da ke? Tsoro da gudun zuciya, da ganin ke ba zaki iya ba, sune suke cutar da ke.
A duk kuma lokacin da kike ganin ke ba zaki iya ba, to ba zaki taɓa iyawa ba har a bada, lokacin da zaki hankalto kice zaki yi a lokacin ba ki da time, shiyasa yan karon magana suka ce if you say yes to others make sure you didn't say no to yourself, saboda zaki cutar da kan ki ne kawai, ba zaki taɓa burge kowa ba a duniyar duk abunda za kiyi wani sai yace kin masa ba dai-dai, ya kamata ace kin canja haka nan accept responsibility for your life, ya kamata ki san it is you who will get you where you want to go, no one else, duk wanda kika gani yana kusa da ke wallahi da zaki waiwaya wata rana zaki ga duk babu so, sai mai miki so na haƙiƙa, wasu duk dariyar fuska ne bda xaki san abunda yake zuciyarsa da ba zaki sake kallonsa ba.
A maimakon ki ƙara hankali da tunani amman kullum sai wata iri kike zama, kamar wanda ake cirewa ƙwaƙwalwa ana zubarwa, tsoron nan da yake ran ki dan Allah ki cire shi Namra, you have to your fears, kuma ya kamata ace kisan cewa kema kina da right and freedom...”
Tun da Maryam ta soma maganar in banda kuka babu abunda Namra take, ta san gaskiya ƴar'uwarta ke faɗa mata, tabbas akwai tsoro a a tare da ita, tsoron abunda mutane za su ce, tsoron ɓacin rai, tsoron ganin ita ba zata iya ba, da kuma gudun zuciyar wanda duk take tare shi. A rayuwar Namra bata iya so ba, irin son nan take yi na sadaukar da komai nata saboda wanda take so ko kuma ta yarda da shi. Indai Namra ta aminta da kai to kai je ka kwanta kawai kayi kwana, ita zata maka komai idonta ya kan makance ga duk wanda take so, bata ji bata gani.
“Mtsssssss”
Maryam taja tsaki.
“Aikin kenan sai kuka, da anyi miki abu kuka dai kuka, da kuka zai miki magani ai da tuni yayi miki, haka kika zo kika sakarwa yarinyar Amira jiki ta yi ta cin amanarki, Allah kaɗai yasan dalilin guduwarta daga gida, amman kullum uwarta ke take cewa ke ce sanadi”
Unguwar Bafarawa estates Maryam ta kai Namra, gidan Gwaggo Kulu.
A bakin gate ɗin gidan tayi farkin ta kalli Namra
“Yanzu idan kin shiga sai kice mata me?”
“Zan ce nan na fara sauka ne”
“Toh nidai ba zan shiga ciki ba, kuma idan na koma gida zan faɗawa Anty duk yadda muka yi da ita zan dawo na faɗa miki”
“Amman dan Allah karki faɗawa Abbah”
“Tau ina gaida Gwaggo”
Namra ta fita motar cikin yanayin damuwa ta shiga gidan Gwaggo. Sai da ta shige sannan Maryam ta juya da motarta tana mamakin lamarin Namra.
Cikin sanyin jiki Namra ta shiga harabar gida,har ta ƙasa falon tana jin tsoro kamar wanda za'ayi ma wani abu.
“Assalamu alaikum”
Cikin sanyin muryar tayi sallamar Yasmin da Gwaggo Kulu suka amsa mata. Tun da ta shigo cikin falon Yasmin take mata wani irin kallo kamar bata gane ta ba. Kallon gulma take mata ganin yadda tayi baƙi sosai, daman can ba fara bace amman baƙin na yanzu ya ninka sosai, ga wata rama da tayi kamar wanda ta kwanta ciwo.
Ita kuma duk taji wani yanayi na daban, musamman ganin Yasmin da tayi a gidan. Bata zace zata rarar da ita ba.
AMIRA POV.
Duk wani farinciki da Amira take yi na zuwa abuja, a yanzu na zama labari, tun jiya da Guy son ya labarta mata dalilinsa na zuwa abuja da
Sam bata son aikin da Guy son yake wani lokacin ƙara kidnapped da saffara ƙwayoyi da yake da aikin kisan kai, sai dai ta san bata isa ta hana shi wannan aikin ba, dan be haɗa aikinsa da komai ba, bata wani daɗe da shi sosai ba, amman ya sake da ita ya shigar da ita jikinsa ya nuna mata so da yarda sai dai be yarda ta hana shi aikinsa ba.
“Wa zaku je yin attacking?”
Ta tambaya tana saka kayanta a jaka.
“Wani soja ne, amman ba a Abuja za muyi attaching nasa ba, daga nan sai za mu bisa za a bamu address nasa sai idan ya koma gida za mu ƙaddamar masa”
“Kashe shi zaku yi?”
“Haka ake son mu yi”
“Waya sa ku?”
“Wata mata ce amman bata son a gane ita ce, shiyasa take son mu bishi daga nan abuja ta yadda za'ayi zaton ko abokan aikinsa ne, yanzu haka ance mana yana cikin garin abuja”
“Amman Guy miyasa kake son kashe rai?”
“Saboda ban ɗauki rai a bakin komai ba, kema wata rana zaki aikata”
“Bana fatan aikata kisan kai har a bada”
Zuwa yayi ya dafata yana murmushi.
“Karki damu idan har kin kashe mutum kin lasa jininsa babu abunda zai same ki, ki shirya muje kar mu yi latti”
Cikin sanyin jiki ta rufe akwatin. Bata san wanda zasu kashe ba amman tana jin rashin kyautawa a lamarin.
Zama tayi saman gadon kamar mai jimami har sai da ya shigo ya ɗauki akwatin nata sannan ta tashi ta fita cikin sanyin jiki.
ABDOOL POV.
Jirgin safe ya bi ko da biyu na rana tayi har ya gama meeting ɗin da zasu yi, ya koma masaukinsa.
Kwantawa yayi ya ɗan runtsa na mintuna sannan ya tashi ya shiga yayi wanka, ya ɗauro alwala sannan ya fito, ƙananan kaya ya saka yayi sallah la'asar sannan ya ɗauki wayarsa ya kunna, text ɗin Ummi ya gani, hakan ya sashi jindaɗi tare da murmushi, sai ya danna numberta ya aika mata kira. A harabar gidan yana waya da Ummi, sai shafa kansa yake yana mai jin shauƙin son mahaifiyarsa cikin ransa.
“Alright Ummi i will, Thank you love you lot”
Ya kashe wayar fuskarsa da murmushi, yana kallon wata kurciya dake sha'aninta a harabar gidan nasa.
Ido ya tsura mata sosai yana son tantance abunda ya gani rataye a wuyanta. Ɗan matsawa yayi a hankali yana kallon layar dake wuyan nata, sai ya shiga ƙoƙarin kamata, be yi nasara ba ta yi firrrrr ta tashi sama, ta haye saman ginar gidan.
Tsaye yayi yana kallonta. Sai ya ƙwalama yaransa kira.
“Hey Boys”
“Sir”
Duk suka sheƙo da gudu, sai dai kamin su ƙaraso har ta ƙara fira ta bar gurin.
1869k words. Sorry for the short chapter 🙏🙏🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺*
*© Khadeeja Candy*
*PAGE - 43*
NOT EDITED ⚠
Cikin rashin kuzari Namra ta zauna saman kujera tana kallon ƙasa kamar mai jin kunya.
“Namra...”
Ta ɗan ɗago kaɗan ta kalli Yasmin data kira sunanta, sai kuma ta kalli Gwaggo Kulu dakr tambayarta saukar yaushe.
“Yanzu na zo”
“Ya hanya ina mijin na ki?”
“Yana lafiya”
Kallon Namra Yasmin take zuciyarta na raya mata ba haka kawai Namra ta zo gidan ba, idan ma wani abun ne ai gidansu zata sauƙa. Murmushi tayi ta tashi ta nufi Namra ta riƙa hannunta.
“Tashi muje ciki kin wani zo nan kin zauna kamar baƙuwa”
Kallon Yasmin Namra tayi, murmushin data gani a fuskarta ne ya bata kwarin guiwar tashi ta bita. Ɗayan ɗakin Gwaggo Yasmin ta shiga da ita, daman can ɗakin ta fi zama a duk lokacin data zo gidan.
Yasmin ta buɗe bathroom ta duba ruwan dake ciki, sannan ta fito tana miƙawa Namra tawul.
“Shiga ki yi wanka, sai na kawo miki abinci”
Idonta a ƙasa take miƙawa Namra tawul ɗin irin bata son kallonta tana jin nauyin Namra sosai.
Hannu Namra tasa ta karɓa, sai Yasmin ta fice, ita kuma ta kwaɓe tufafinta ta ɗaura tawul ɗin ta shiga wanka, ko da ta fito Yasmin ta aje mata gown ɗin atamfa da abinci.
Ɗaukar rigar tayi ta saka, daman tayi alwala tun a toilet ɗin, sai kawai ta saka hijabinta, tayi sallah. Bata ci abincin ba dan bata jin cin komai, lemum kawai ta sha, sai ta ɗauki carbi tana tasbihi.
“Assalamu Alaikum”
Yasmin ta shigo bakinta ƙumshe da sallama, murya ƙasa-ƙasa Namra ta amsa mata, sai ta zauna kusa da ita tana wasa da hannayenta.
“Kin abincin dai ko?”
“A'a bana jin yunwa”
Kallon fuskar Namra tayi da kyau-kyau, tana ƙoƙarin karantar danuwarta
“Namra, kiyi haƙuri na ji ance mijin ki yayi haɗari, kuma duk a familyn nan babu wanda yaje ganinsa, ni ma naso naje na gansa Allah be nufa ba”
“Ba komai, ai yaji sauƙi”
“Allah ƙara lafiya, tare dashi kuka zo?”
“Ni kaɗai na zo”
“Amman ba kije gida ba ko?”
Ta ɗaga mata kai, kalar tausayi. Har Yasmin zata
tambaye ta ko dai faɗa suka yi da Asim, sai kuma taga rashin dacewar haka. Sai kawai ta tashi tana faɗin
“Ni kan zanje gida, ai nan zaki kwana ko?”
Ta ɗaga mata kai. Sai Yasmin tace
“Da safe zan aiko miki da breakfast”
“Na gode Anty Yasmin”
Namra ta faɗa idonta cike da hawaye. Rayuwar da suka yi a can baya ne ya riƙs dawo mata sabo, yadda Yasmin take treated ɗi kamar wata ƙanwarta da suka fito ciki ɗaya, amman yau duk babu wannan, tun da Uzair ya shiga tsakaninsu.
Ɗan murmushi Yasmin tayi ta juya ta fice.
Ɗakin Mahaifiyarta dan yi mata sallama. Ko da ta shiga Gwaggo Kulu na banɗaki, tana alwalar magariba. Gefen gado ta zauna har ta fito sannan ta miƙe tsaye.
“Gwaggo ni kam zan tafi, Uzair ya kira ni tun ɗazu wai yana gida”
“Ba zaki bari kiyi sallah magariba ba”
“A'a sai na je can zan yi”
“Toh Allah ya tsare, kin yi magana da Namra?”
“A'a ba mu yi mafanar komai ba, amman dai tace min bata je gida ba, ina ganin dai ta zo ne ba tare da sanin mijin ba”
“Toh Allah ya sauwaƙe, shiyasa ta ƙi sauka a can ta sauka nan”
“Haka nake tunani, kuma kin san halin Abbah da zuciya ƙila ma ta je ya hanata shiga gidan”
“Toh ai sai ta yi zamanta nan”
“Ni dai na tafi, da safe zan aiko mata da breakfast”
“To Allah kai mu lafiya”
Ta ɗauki jakarta da mayafinta ta yafa ta fito, zuciyarta cike da tausayin Namra.
Motarta ta shiga tayi mata keys kamin ta isa gida Uzair yayi mata kira biyu tana ce masa gata nan kan hanya amman duk be yarda ba gani yake kamar tana gidan zamanta ne, shi ta bar masa yaro sai fitina yake masa.
A harabar gidan ta faka motarta, sannan ɗauki takardun dake cikin motar da system ɗinta ta buɗe motar ta fito, ɗayan hannunta tasa ta lanƙamo jakarta sannan ta rufe motar, ta nufi ciki gidan.
“Assalamu Alaikum”
Tun a bakin ƙofa ta zubar da files ɗin dake hannunta da handbag, system ce kawai ta samu ƙarasa tsakiyar falon ta aje ta saman kujera, tana kallon Uzair daya kama hannun Adnan ya riƙe.
“Dan Allah zo ki raba ni da yaron nan, sam be jin magana wallahi, tun ɗazu yaƙi bari na huta”
Ƙyalƙyalewa Adnan yayi da dariya yana kallon Yasmin dake murmushi yace
“Mom wai ba zai ba ni wayarsa ba, tun da ba ke kika siya ba”
“Zo ka ɗauki nawa kayi game, amman ka kwashe takardun nan ka kai ɗaki”
Ta faɗa tana nuna masa bakin ƙofa inda ta jefar da jakarta da takardun. Da gudu yaron ya sance hannunsa daga riƙon da Uzair yayi masa ya nufi gurin ƙofar yana tsalle.
“Wallahi duk kin ɓata min yaro, sam yanzu baya jin magana”
“Kai dai ka ɓata abun ka karka ɗora min laifi”
“Kuma na faɗa miki ki daina wucewa gida idan kin san ki bar min Adnan”
“Bloody yau ina gida sai ga Namra”
“What!... ”
Ya gyara zamansa.
“Wallahi, duk ta rame tayi baƙi sosai kamar ba ita ba”
“Me ta zo yi?”
“Ina ganin tayi yaji ne, dan ƙin sauka tayi gida sai ta sauka gidan mu”
Ya taɓe baki, irin ko a jiki na can ta matse mata.
“Ai bama zata yi kuskuren sauka gidan Abbah ba kam, ko minene ai ita ta jawa kan ta”
“Ni wallahi tausayi take bani, da na sani tun farko dana barka ka aureta, ji duka yaushe akayi auren amman har ta koma haka”
Ya miƙe tsaye yana wata dariya.
“Na aure ta na kai ta ina? Kin ɗin ma kin fitineni kin hanani sukuni balle kuma na haɗa ku biyu, ai ni sai yanzu na ga hikimar rashin aurenta da nayi, na gode Allah wallahi”
“Haƙurin da nake da kai babu macen da zata iya yinsa da kai, baka da time ɗin na, baka bani haƙƙina kwata-kwata ma bana gabanka, in nayi kwalliyar duniyar nan bana burge ka, ai dole nayi magana tun da ni ba ice ba ce”
“Kyaji da kan ki, kin cika jaraba ne, akwai wanda yake shekara ma babu ruwansa da iyalinsa kuma suna zaune lafiya, sai ni kullum cikin complain kike, kuma tun da kika ga ban gyara ba ai kinsan haka Allah yayi ni, ni bana da sha'awa”
“Wallahi ba haka Allah yayi ka ba, ko minene dai daga baya ne ya same ka, ai da can ba haka kake ba, ko dai dan na haihu ne na daina burge ka?”
“A'a karki sawa ran ki wani abu, wallahi bana neman mata a waje, babu ruwana da mata, kawai dai sauyin yanayi ne”
Ya sa hannayensa aljihu ya nufi ƙofar fita. Da kallon ta kaici ta bishi, har ta fice, sannan ta sauke ajiyar zuciya ta tashi ta nufi ɗakinta dan dauke faralin da yake kanta na sallah magariba.
A masallacin unguwar ya yi,alwalah yayi sallah magariba, shi kaɗai yayi abarsa dan su tuni suka sauke jan'i. Bayan ya fito ne ya ciro wayarsa dake aljihu ya kira number Hajiya Barau dan tsegunta mata labarin Namra, duk da yana tunanin ta san da zuwan na ta.
Two missing calls yayi mata, bata ɗauka ba, har ya mai da wayar aljihu sai gata ta kira, cikin sauri ya ɗaga kiran nata yana takowa zuwa gida.
“Hajiya ina wuni?”
“Lafiya ƙalau Uzairu ka kira ni ina sallah, ya gida ya mijina da Yasmin?”
“Suna nan ƙalau, yanzu ma Yasmin take faɗa min wai Namra ta zo, tana gida da yake ita gida ta wuni daga gurin aikin ta wuce gida”
“Namra kuma? Amman bata sauka nan?”
“Au daman bata sauka nan ba? Ai na ɗauka ta kwana biyu da zuwa ma”
“A'a Wallahi ni ban ji labari ga kowa ba, amman ita taga Namra ɗin da idonta?”
“Haka tace min, yanzu haka tana gidan Gwaggo”
“To ko fushi take da Alhaji ?shiyasa bata sauka nan ba?”
“Idan ma fushi take da Abbah ai ke ba zatayi da ke ba, kuma ga Anty”
“A'a mu a su wa? Kishiryar uwa mai ƙaurin suna? Ta dai san ba zuwan lafiya bane shiyasa ba zata sauka nan ba, dan tasan halin Alhaji shiyasa aka ce in za a yi tukka a yi mata hanci don kada ta warware, irin wannan ranar ake gudu, daman ni nasan abin da ya ci doma ba ya barin awai, yadda yarinyar nan ta ci amanarka ai dole alhakin ka ya fita”
Uzair yayi wani shegen murmushi
“Ashe baki san ta zo ba, amman ina jin Anty ba zata rasa sani ba”
“Ina jin ta sani sai ta ɓoye, waya sani ma ko ita tace mata ta sauka gidan Hajiya Kulu tun da tasan tana son Namra, ba zata bari Alhaji ya wulaƙanta ba, ji fa ko gobarar nan da tayi har yau bata taɓa maganar ba, in ban da ƴan'uwana da suka ce suka faɗa min da ban ji ba, ai ni naji daɗin da Alhaji ya juya mata ƴarta baya, dan duk abunda take da sanin uwar nan take yinsa, ita ke goya mata baya, ko auren nan naku da anyi da sai uwar nan ta kashe shi dan bata son ka”
“Allah ya kyauta, ai ga ta nan ta dawo mata sai tayi yadda take so da ita, Yasmin tace min duk ta rame ta yi baƙi”
“Lallai kam, kowa ya keta riga tasa, ya san inda zare ya ke”
“Kaɗan suka fara gani”
Ya faɗa sannan yayi sallama da ita ya kashe wayar. Hajiya Barau ya aje wayar ta cire Hijabin dake jikinta ta tashi ta nufi part ɗin Abbah.
MARYAM POV.
Da takaicin Namra ta koma gida, sai dai bata labarta ma Anty Amarya komai ba, dan bata san ta yadda zata ce mata ba, sai bayan magariba, sannan ta labarta mata abunda ake ciki.
Duk rikicewa Anty Amarya tayi murna da farinciki suka zo mata a lokaci ɗaya, murnar ƴarta ta zo da kuma baƙinciki bata sauka a gidan ba, ita kan ta tasan sai anyi yaƙi da Abbah kamin ya barta ta zauna gidan.
“Amman Maryam ita kaɗai kika ganta?”
“Eh ita kaɗai, Anty duk ta lalace ta rame Allah kaɗai yasan abunda yayi mata tun da har kika ga ta baro shi ta zo nan, bayan kuma ta san halin Abbah”
Sai duk Anty Amarya ta ji babu daɗi, a take ta ji tana buƙatar ganin ƴarta.
“Zan faɗa ma Abbanku ta zo ganin gida ne, ai dole ya barta ta zauna”
Maryam zata yi magana sai ga wayarta tayi ringing, Sweet PaPa ta gani hakan ya tabbatar mata da number Abbah ce, da sallama ta ɗauki wayar dan tasan Abbah ya tsani ya kira mutum ace masa hello.
“Maryam”
“Naam Abbah”
“Ki ce Mamanki ta zo yanzu”
“To”
Ta kashe wayar gabanta na faɗuwa, duk da bata san anyi komai ba, amman ta ji kamar ba lafiya ba, ta kalli Anty Amarya dake cikin yanayin damuwa tace
“Wai Abbah ki zo”
Shiru Anty Amarya ta ɗan yi sannan ta tashi cikin rashin ƙarfin jiki ta nufi part ɗin Abbah ba. Zuciyarta da biyu, ta faɗawa Abbah Namra zata zo ganik gida, kuma ta ji kiran da yake mata. Sai dai duk hanzarinta ya katse lokacin da Abbah ya gargaɗe ta akan kar ta bar Namra ta shigo masa gidan.
“Ki faɗawa ƴar ki karta kuskura zuwa min gida, ta tsaya can inda ta sauka”
“Ƴata ce kai ba da kai ba? Ko shegiya na haifa ne?”
“Nine ubanta, amman na riga na yafe ta, kuma tun ranar da zata je gidan mijinta na faɗa mata karta kuskura dosomin gida da sunan yaji ko saki”
“Ai ganin gida zata zo”
“Ba ganin gida ta zo ba, na dai faɗa miki karta doso min gida”
“Ƴata tana da buƙata na, kuma dole ta zo nan gidan nan tun da ina ciki, ko wane munafukin ne ya zo ya faɗa maka sai na ci masa mutunci”
Abbah yayi banza da ita yana kallon agogon hannunsa.
“Yanzu zamu je karɓo kuɗin kwangila, karki kuskura ki bari ta shigo min gida indai ba mugun wulaƙanci kike so na mata ba”
“Idan bata shigo ba, ni zan koma gidan mu na zauna da ita, dan ba galihu ne bata da shi ba, abunda kake yi baka kyautawa Alhaji, musulunci be ce haka ba, shikenan dan kawai ta auri wanda take so sai abu ya zama ɗan zane”
“Ai daman duk abunda take da goyon bayanki take yinsa, ke kika goya nata baya”
“Ni nake goya mata baya, ai daman ka saba faɗar haka, komai nice, daman na san ba ƴata ce baka so ba, ni ce baka so, ita Hajiya da take ƴar'uwarka ai baka mata haka ba balle ƴaƴanta, sai ni da ka auro bare, nice abar wulaƙantawa ni da ƴaƴana, ko kuma saboda ni ban haifi ƴaƴa maza ba shiyasa kake min haka”
Cikin faɗa da kuka Anty Amarya tayi maganar. Sai Abbah yayi mata wani kallo na mamaki.
“Subhanallahi, ai ƴaƴa maza da mata duka ɗaya ne a gurin Allah”
“Amman kai a gurin ka ba ɗaya bane, tun da gashi kana nuna min banbanci, idan baka da rai a yau babu wanda zan kallah na ji sanyi sai ƴaƴaka, haka nima idan bana da rai babu wanda zaka kalla ka tuna da ni ko kaji sanyi sai ƴaƴana, to dan me zasu zama abun wulaƙantawa a gareka, ashe wata rana idan bana da rai abunda zaka ma ƴar ciki sai yafi wannan tun da kayi mata haka ina raye, kai da ƴan'uwanka kun sa Namra a gaba, kamar ta kashe muku wani, daman ni ce ba ku so ba ita ba”
Ta juya ta fita tana wani irin kuka kamar ta faɗi ƙasa. Har cikin ransa Abbah yake jin kukan Anty Amarya, kalamanta sun ɓata masa rai, sai kuma sun fi taɓa masa zuciya sosai har sun sa ya sauko daga fushin da yake.
Ɗakinsa ya koma ya ɗan kimtsa sannan ya fito ya nufi gurin da aka saba aje masa motocinsa.
Da kuka Anty Amarya ta shiga part ɗinta, duk hankalin Maryam sai ya tashi, kasancewar ita kaɗaice ke falon, ganin mahaifiyarta na kuka, yasa ita ta fashe da kuka ba tare da tasan dalilin kukan na Anty ba.
“Anty me ya faru?”
“Wallahi yai ba zan kwanan a gidan nan ba, babu abunda zai sa na kwana gidan da za a hana ƴata shigosa, yafi son ta je can ta zauna inda za a riƙa zaginta ana tseguminta”
“Be yarda ta zauna, ban san munafukin daya faɗa masa ba”
“Anty kiyi haƙuri, zai sauko yana cikin fushi ne”
Aisha ce ta fito daga ɗakinsu ita da Hindatu suka nufo gurin da Anty Amarya take, suna tambayar ba'asi, dan basu san abunda yake faruwa ba, suna can ɗaki suna karatun exam.
“Lafiya miya faru”
Aisha ta tambaya tana dafa Anty.
“Abbah ne yace wai Namra ba zata shigo masa gida ba”
Maryam ta faɗa tana kuka. Hindatu ta kalleta da mamaki tace
“Amman yanzu Abbah ya kira wayar Aisha yace ta faɗa niki kije ki zo da Namra”
Anty Amarya tayi saurin kallon Hindatu tana share hawayenta.
“Da gaske? Yanzu ya kira ki?”
“Eh Wallahi”
Anty Amarya ta tashi da sauri ta nufi part ɗin Abbah, kamin ta ƙarasa ta hangoshi jikin mota, yana jiran direbansa ya tashi motar.
Gurin ta ƙarasa ta tsaya masa a gaba.
“Kai kace azo da Namra?”
“Amman sati ɗaya na yarda ta yi”
Haka kawai ya faɗa ba tare daya kalleta ba, ya buɗe motar ya shiga. Sai ga Anty ta dawo falon da far'ah tana cewa Maryam da Aisha su je su taho da ita.
RASHIDA POV.
Kwanan ta biyu asibiti suka sallame ta bayan anyin mata wankin ciki, sai dai duk tsawon kwana biyun da tayi Hilal be liƙe inda take ba, duk kuwa da kasancewar a gurin yake aiki.
Kuma duk tsoron kwanakin be kawo yaransa ba, sai dai ma'aikaitam gurin sun yi ta zuwa ganinta, sanin cewa ita uwargidan Doc ce.
Ranar data dawo gida ta ci kuka kamar ta mutu, babu irin rarrashin da ƴan'uwanta ba su mata ba amman sam ta ƙi ji sai da tayi kukanta har ta gaji sannan ta saurarawa kanta.
Daren ranar da aka sallame ta ne Asmee ta zo gidan, ita tayi ta bata haƙuri tana ƙara mata ƙarfin guiwa akan inda zata kai ta Hilal ya mayarda ita, sun kitse magana akan zasu tafi tare gobe idan Rashida zata fita. Sun daɗe suna tattauna lamarin kasancewar su biyu ne kawai a ɗakin, tun Rashida na kuka har ta daina.
Tun dawowarta gida bata sa komai a cikinta ba, bata komai sai tunanin Hilal da kuma makomarta, gani take idan har da gaske tana da hiv ya makomar iyayenta zai kasance tun da dole ne tayi mu'amala da mutane. Wayarta ta janyo ta kira wata ƙawarta wace ta kasance likita ce. Bugu biyu ta ɗauka, bayan sun gaisa, Rashida take ce mata
“Dr Fatima, ina son na tambaye ki ne akan hiv, wata sis nace take rubuce-rubuce shine take tambaya ni kuma na ce bari na tambaye ki tun da ni ba sashena ba ne”
Dariya Dr Fatima tayi ta ce
“Amman gaskiya bayanin yana da ɗan tsowo, why not na yi miki ta whatsapp kina online yanzu haka”
“Yauwa to haka ma yafi, bari na hau”
“Daman na san ba zaki kira ni haka nan kawai ba”
Rashida tayi dariya bata daɗin rai ba, ta kashe wayar. A take ta kunna datar ta sa hau online. A contacts list ɗinta ta shiga ta nemi Dr Fatima tayi mata sallama. Sai da ta ɗauki ƴan mintuna sannan ta amsa sallamar sai ta koro mata da bayani.
“CUTAR KANJAMAU/TSIDA (HIV-AIDS)
HIV (human immune virus) ita kwayar cuta ce da take haifar da AIDS (Acquired immunodeficiency syndrome) ma`ana karyewar garkuwar jiki wadda aka fi sani da tsida ko kanjamau. Ita wannan cuta, cuta ce da take karya garkuwar jiki (immune system) wanda ke bada daman wanda, ke dauke da ita ya kamu da wasu cu tuttuka sakamakon karyewar garkuwan jiki. rashin kiyayewa ko kula da wannan cuta kan sa mutum ya halaka a takaitaccen lokaci kamar daga shekara 9 zuwa 11 ya danganta wani yanayi.
HANYOYIN DA AKE KAMUWA DA CUTAR KANJAMAWA/TSIDA
Ana kamuwa da ita wannan cuta ta hanyar shigar kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) chikin jini. San nan hanyoyin da kwayar cutar ke shiga jiki na dewa, kan iya shiga ta hanyar haduwar jinin me dauke da cutar ga mara dauke da cutar kamar ta hanyar cizon sauro, maniyi, ruwan farji (vaginal fluid) mafi yawan cin masu dauke da wanan cuta na kamuwane ta hanyar saduwa (sex) da me dauke da cutar. Ana kuma iya kamuwa ta hanyar yin anfani da allurar da me dauke da ita yayi mfani dashi. San nan jarirai na iya kamuwa da ita kwayar cutar daga uwa ta hanyar shayar wa, da lokacin da suke a ciki (pregnancy).
Ita wanan kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) bata rayuwa da keu a wajen jiki saboda haka akan iya kamuwa da ita ta hanyar sunbata (kissing) kokuma yin anfani da wani abu wanda me dauke da cutar ke anfani da shi kamar kofin shan ruwa, abun yanke farce, ma gogin baka (brush).
Idan yazama cutar ta kai marhala na karshe ma`ana AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) ba`a kamuwa da ita ta hanyar sunbata (kissing), cin abici tare da me dauke da ita, amfani da kayayyakin ko abubuwa da me dauke da ita ke anfani da su kamar kayan sawa, wayan salula, agogo, wanka a swimming pool, zama a kujera, cizon sauro, ma taci (comb), tawul, da kuma tafiya, hada hanu, zama,da yin aiki tare da me dauke da cutar”
Tun da Dr Fatima ta fara bayaninta Rashida take karanta abunda take aiko mata, sai da ta kai nan sannan Rashida ta aika mata da wata tambayar.
“Amman Dr ya alamomin cutar yake?”
Ta samu minti biyar zuwa shida kamin tayi ma Rashida reply
“Alamomin ita wan nan cuta ta banbanta daga mutun zuwa mutum. Mutane biyu kan iya kamuwa a lokaci guda amma ba lallai sun nuna alamomin iri day aba. Anan zamu raba alamomin kamar kasha uku muyi bayani akai.
(acute illness)
(asymptomatic period)
(advanced infection)
Acute illness
(acute illness) ma`ana alamomin farko na kamuwa da ita wannan cuta. Kashi tamanin cikin dari 80% dake dauke da cutar na farawa da jin kamar alamomin mura (flu-like) dake kai tsawon sati biyu zuwa hudu rukunin farko. Abubuwan dake faruwa a wannan rukuni sune:
Kuraje kana na a jiki (body rash)
Zazzabi (fever)
Boshewar makokoro (sore throat)
Jin gajiya (fatique)
Kumburi a (lymph nodes)
Fashewar baki da alaura (mouth and genital ulcers)
Chiwon nama (muscles pain)
Ciwon gabobi (join pain)
Amai da hamami (nausea and vomiting)
Zufa cikin dare (night sweat)
Wa yan nan alamomin na faruwa mutum ya gaggauta zuwa kuji don gane yana dauke da ita bai dauke da ita.
Asymptomatic period
(asymptomatic period) ma`ana lokachin bacewar alamomi. A wannan lokaci cutar bata nuna ko wace alama na rashin lafiya ko ciwo na wasu watanni ko shekara. Amma akwai kwayar cutar a jikin mutum. A wannan lokacin kwayar cutar na dada yaduwa (replicating) da kuma kashe garkuwar jiki (immune system). Sannan a wann lokaci kwayar cutar tafi karfi da kuma yadu ta hayoyin da mukayi bayani a yadda ake kamuwa da cutar.
Advanced infection
(Advanced infection) a wannan lokachi kwayar cutar ta riga tayi damejin garkuwar jiki (immune system) yana daukan lokachi amma idan ya kai wannan lokachi to cutar ta kan zama AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) mutum kan kamu da wasu cututtuka sakamakon damejin garkuwar jiki (immune system damage) zaizama garkuwar jiki bai iya yaki da kwayar cuta. Alamomin wannan bangare sune:
Hamami
Amai
Gudawa
Ma tsanachin gajiya
Raguwar nauyi /rama
Tari da numfashi sama sama
Zazzabi me tsanani akai akai (recurring fever)
Kwararraji masu ruwa a baki ko hanchi ko a fata da kuma alaura,
bushewar makokoro
kunburin lymph node na gabobi mara warkewa.
Kidimewa, tabuwar kwakwalwa daga nan kuma watakil sai mutuwa”
Hankalin Rashida ya tashi sosai wasu daga cikin abubuwan da Likitar ta faɗa duk tana jinsu, amman tayi tunanin ko cikine a lokacin. Ji take kamar ace ba da gaske bane
“Amman Dr Bayan wannan babu wata alama da mutum zai iya gano tabbacin yana ɗauke da cutar?”
Ko da ta tura mata saƙon ta riga ta sauka online, a lokacin 10:23pm ne. Kasa natsuwa tayi har sai da ta lalobu number Dr Fatima ta sake kiranta.
“Dr kina min bayan sai kika sauka”
“Eh Wallahi mai gida ne ya shigo”
“Dan Allah ki taimaka ki ƙarasa min, gobe zata rubuta abun yanzu haka duk ta dame ni”
“Okay bari ya gama cin abinci zan hau online”
Daga haka ta kashe wayar tana tunanin nata mijin. Whatsapp ta shiga tana duba last seen ɗinsa, ta ga biyar da kwata na yamman nan. Dp shi take kallo wani hoto ne ya ɗora yana sanye da kayan likitoci yana murmushi. Fashewa tayi da kuka ta rumgume wayar a ƙirjinta.
Sai da tayi kukanta ta gaji sannan ta ɗago wayar ta sake kallon hotonsa tayi masa kiss sannan ta shiga chat ɗin su da Dr Fatima, ashe ma tuni ta turo mata da bayanin bata gani ba.
“Ana gano mutum na dauke da wannan cutar ta tsida ta hayar gwajin jini, (serum), miyau, ko fitsari ta hanyar sanya musu wasu sinadarai dake sanya a gano kwayar cutar aciki wato HIV (human immunodeficiency virus) wadda ita take haddasa AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) wanda mukayi bayani a sama. Anfi gano mutum na dauke da cutar ta hanyar gwajin jini”
Ta haɗeye yawu ya fi sau biyar sannan ta sake aika mata da wata tambaya, wace ita ce dalilin tambayarta tun farko.
“Dr ya mutum zai kare kansa ko kuma wani nasa daga kamuwa da wannan cutar?”
“Yin gwaji don sanin akwi ko babu.
Rage yawan saduwa.
Anfani da roba (condom) wajen saduwa.
Kiyaye saduwa da mata/maza daban daban.
Gwaji da kuma maganche cututtukan saduwa STDs (sexual transmitted disease).
Kiyaye yin amfani da allurar da wani yayi anfani da ita.
Tabayar likita dangane shan PrEP (pre-exposure prophylaxis) shima wani hanya ne na kiyaye kamuwa da ita wannan cutar
Rashin kiyaye ita wanan cuta kan sa mutum ya halaka da wuri. Ana kiyaye cutar ta hanyar yin anfani da (antiretroviral drugs) magunguna ne da ake afani dasu wajen magance cututtukan virus, kusan ita wanna cuta bata da maganin warkewa sai kiyaye ta, ta hanyar anfani da magunguna da likitan ya dorashi mutum akai”
“Na gode sosai likita Allah ya saka da alheri”
“Ba a son mai cutar yana kusantar hayaƙi, ko cizon sauro ko wani abu makamancin wannan, saboda abu kaɗan yana iya ƙara cutar, an fi mai cutar ya ci abubuwan gina jiki like vegetables”
“Thank you”
Rashida ta rubuta daga ƙarshe, sannan ta kashe wayarta tana hawaye.
“Dole ne naje nayi gwaji dan na tabbatar, wata ƙila ma na ɗauke da cutar, ai za a iya min sheri tun da ba a son zamana da Hilal”
Ta faɗa a fili tana share hawayenta. Sai kuma zancen da Asmee ta faɗa mata ya dawo mata na zargin kanta da take tana ɗauke da cutar, ita kuma ta san tana mu'amala da mijin Asmee. Jefar da fillon dake saman gadon tayi ta wani irin matsa gashin kanta.
Haka ta kwana har safe tana kuka idonta ya kumbura sosai kamar an zuba mata wani abu a ciki, bata fita ɗakinta ba, abincin da Momy ta kawo mata bata ci ba, sai kawai ta shiga banɗaki tayi wanka ta saka abaya, ta fito falo, ba dan tana jin ƙarfin jiki ba, sai dan tafitar ta zame mata kamar dole ne.
Momy na ganinta ta cika da mamakin ganin ta fito da shirin fita.
“Ina zaki je?”
“Ina son na ɗan fita ne, zan je office na ɗauki hutu sai na je gidan Asmee”
“Haba Rashida yanzu cikin wannan yanayin zaki fita sai kace wanda bata son kanta?”
Idonta ya cika da ƙwallah
“Momy ina son fitar ne ko zan samu gwarin jiki, kuma na sha iska, ko damuwa zai rage min”
“Kuma Sisters naki duk sun tafi school balle su raka ki, zaki iya driving ma”
“Zan iya”
“Shiga ɗaki ki ɗauka keys ɗina”
Momy ta faɗa cike da tausayawa. Ɗakin Momy ta shiga ta ɗauki makullin motarta, dan ita yanzu komai nata yana can gidan Hilal babu abunda aka ɗauko.
Cikin ƙarfin hali take driving ɗin, kamin ta ƙarasa office ɗin ta tsaya gefen titi tayi parking, ta kira number Malamin nan. Bayan sun gaisa ta koro masa da bayaninta.
“Malam aiki nake son ka min akan kishiryata”
“Me kike son a mata a kashe ta ko a haukatata?”
“Bana son a mata ko ɗaya, wani daban nake son ka mata wanda mijina zai gaji da ita ya rabu da ita sai ka min wanda zai dawo gare ni, a halin yanzu mijina ya rabu da ni”
“Me kika masa? Ina labarin waɗancan mutanen dana haɗa ku da su?”
“Ba mu yi aikin ba, saboda auren ya riga ya mutu, kuma wallahi ina son miji zan iya mutuwa idan babu shi a kusa da ni”
Ta faɗa cikin wani irin kuka, kamar ance mata malamin yana gabanta ne.
“Ya isa daina kuka, ai wannan mai sauƙi ne, akwai aikin da zamu masa ya dawo gunki da gudu ma, ita kuma za mu sakar mata jini sannan mu saka mata warin jaɓa idan ya gaji da ita zai sake ta, amman zaki kashi kuɗi”
“Kuɗi ba matsala bane zan baka ko nawa kake so, amman ina son a buga min ƙasa a bincika min komai nawa”
“Zan miki haka, duk abunda ƙasa ta faɗi zan faɗa miki idan kin zo, amman idan kin shirya aikin ki zo da tulo da zanen haila wanda ita kishiyarki take amfani da shi”
“Malam ya za'ayi na same shi yanzu, bayan bana gida kuma ai kasan yanzu ba'a amfani da irin wannan abun yanzu duk pad ne ake sawa”
“Pad ɗin shima ai zai yi, ki bincika a bolar gidan, idan kuma ba zaki iya ba, kisa zo ki biya kuɗi mu zamu sa aljani ya ɗauko mana”
“Zan zo nan da kwana biyu, na gode”
Daga haka ta kashe wayar ta ɗora kanta saman sitarin motar, kamin ta ɗago ta cigaba da tuƙin.
Wata pravate hospital ta nufa dan yi gwajin jinin so that ta tabbatar da zarginta.
AMIRA POV.
Har suka sauka garin Abuja bata wani farinciki musamman data ga hoton wanda ake son su kashe ɗin, sai duk jikinta ta mutu, ta tabbatar mutumen ƙwarai ne dan in ba haka ba babu abunda zaisa wasu su nemi a kasheshi.
Mutumen data taɓa gani a tv she can't recall his name, amman dai tasan shine wanda aka taɓa tattauna da ashi akan tsaro har ta ji ya kwanta mata a rai.
“Guy please karku taɓa mutumen nan”
Hancinsa yasa yana gogawa a kumatunta.
“Ina son ki sosai Amira, amman akan aikina zan iya ɓatawa da ke, so ki daina sa baki a kan aikina”
Ya ciro wayarsa dake aljihu ya kara akunne
“Hello ....Okay”
Ya kashe wayar yana kallonta
“Wai ya fita, zo muje”
“Tun yanzu za ku kashe shi?”
“A'a zamu fara farautarsa ne, yana Sahaba Restaurant, akwai yara dana aje Sahaba Hotel, kisa da inda yake, nima kuma can zanje amman sai gobe”
Ajiyar zuciya ta sauke ta janye hannunta daga riƙon da yayi mata.
“Ba zan je ba ku tafi kawai”
Duƙawo yayi ya mata kiss, sannan ya fice.
Ji take bata da natsuwa idan bata faɗawa masa abunda yake faruwa ba, sai dai kuma taya zata faɗa masa bayan shi ɗin babban mutum ne ganinsa ba hakan ake yi ba. Kuma idan har ta aikata ta jefa rayuwarta cikin matsala.
Sai da ta ji tashin motarsu sannan ta tashi ta shiga binciken gidan, har ta samo paper da pen tayi rubutu akai sai ta sanya doguwar riga dan jikinta inner ne kawai ta fito harabar gidan tana dubi-dubi.
Har tayi tunanin ta hau Napep sai kuma ta tuna Abuja ba ko ina ake farin Napep na shiga ba, sai kawai ta koma ciki ta tashi ɗaya daga cikin yaransa ta ce ya kai ta, yaso ya musa mata amman sanin halinta da kuma yadda Guy ke ji da ita yasa dole yaja mota ta shiga suka kama hanya.
Suna isa Sahaba Restaurant, sai ta hango Sahaba Hotel kamar yadda Guy ya faɗa mata. Nesa da gurin tasa ya aje ta tace ya tafi ya barta zata je gurin Guy, ba musu yaja motar ya koma. Sai da ta daina hangosa sannan ta nufi Sahaba Restaurant zuciyarta cike da tsoro gabanta kuma kar ma zai zube ƙasa.
Guy na daga gefe ya hango Amira ta doshi Restaurant ɗin sai waje-waje take.
“What the fuck, me Amira za tayi can ? Ko ta ɗauka ina can ne?”
Ya tambaya yana kallon yaransa da suke tare da shi cikin motar, wanda ko wannensu ba shi da amsar ba shi. Da sauri ya buɗe motar ya tara hannayensa a baki yana mata fiito (shewa) irin na tsuntsaye. Amira na jin kira ta san Guy son ne, maimakon ya ga ta dawo sai kawai ta ranta cikin na kare.
ABDOOL POV.
Ganin kurciyar ta firanye sai kawai yayi musu alama da hannu akan su koma kawai. Shi kuma ya koma cikin gidan, ya kunna tv yana kallon news, lokaci zuwa lokaci yake jan tsaki saboda lamarin nijeria kullum abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, yau wannan kakeji gobe wani kala ne. Idan ma kace zaka maida hankali akan abun sai tunani yayi maka yawa.
Wuni yayi a cikin sallah ce kawai take fitar da shi gidan, sai da dare ya sauya kayan jikinsa ya fita siyen abinci dan be yarda a dafa masa a abinci duk kuwa da kasancewar akwai masu masa dafa masa, amman baya ci sai dai sauran ƴan gida su ci. Ko a gurin siyen abincin ba guri ɗaya yake tsayawa ba, saboda tsaro.
Bayan ya karɓi takeaway ɗin ya biya sai ya juyo ya nufi ƙofar fita. Yana fitowa ya hango budurwa tana gudu iya ƙarfinta ta doso inda yake, kallon mamaki yake mata yana son tantance abunda take ma gudun.
Sauran taku kaɗan ta ƙaraso inda yake, sai ƙarar bindiga ya tashi, cikin wani irin zafin nama ya riƙota dan ya gane ita aka harba, sai dai haka be hana bindigar samunta, sai ta sulale a hannunsa tana banƙarar bayanta saboda zafi da kuma dafin albarushin da taji ya soke ta abaya.
Daga shi har ita tare suka kai ƙasa, cikin hanzari ya ciro wayarsa ya kira yaransa. Sannan ya kira head quarters.
*🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺*
*© Khadeeja Candy*
Don't read if you didn't pay...!
*PAGE - 44*
NOT EDITED ⚠
_An kaiwa Major General Abdullah Ahmad Mai-doki hari_
_An yi nasarar kashe waɗanda suka kaiwa Major hari_
_Yarima Abdullahi Ahmad Mai-doki Ɗan sarkin Katsina ya tsallake rijiya da baya_
_Wata yarinya ta sadaukar da ranta saboda ɗan Sarki_
Shine abunda kowa wace jaridar Nigera ta online ta yi ado dashi a fuskarta shafinta, har ma da na ƙasashen waje, bayan mintuna 25 da faruwar lamarin.
Online rumors updated kuma kowa da abunda yake rubutawa, har da masu cewa har shi an harba da masu cewa ma ya mutu, da masu cewa yaje siyen abinci da karuwarsa, wasu kuma matarsa ko dai da irin yadda tayi masa daɗi yake ƙaƙarowa ya rubuta a social media.
Dandazo ƴan jarida suka yi a bakin asibitin da aka kai Amira, dan jin kanun labarai, ko wannen baya son a bashi labari.
Sai dai sojojin da ke zagaye da asibitin basu ba su damar shiga ciki ba, balle har su ɗauki rahoto ko kuma video abunda yake kan faruwa ba.
A bakin kofa Abdallah ya tsaya yana kai da kawo har sai aka fito da ita ɗakin tiyata, bayan an cire mata albarushin.
“Doc is she live?”
Shine abinda Abdallah ya fara tambaya ganin an fito da ita daga ɗakin galalla kamar wanda bata numfashi, a kife take saman gadon asibitin dan a bayanta ne suka mata aikin cirar albarushin.
“She survived, but she's unconscious now and she will take 28 -32 hours before she wake up”
Likitan na faɗar haka ya suka wuce da ita wani ɗakin, tare da wasu Nurses. Da kallo Abdool ya bita sai da duka shige da ita ɗakin sannan ya sauke ajiyar zuciya ya shafa kansa. Sannan ya zauna a kujerar dake gurin ya lumshe ido yana sauraren wayarsa da ke ringing.
Kira ne kan kira yake shigowa, tun wayar tana ringing da vibration ita kaɗai har cinyarsa ta gara amsawa, saboda yawan kira. Shi dai yasan ba zai iya ɗaukar kira kowa a yanzu ba, dan yasan ba zai wuce masu son jin lafiyarsa ba, abu ɗaya yaji zai iya, magana da ƴan jarida dan tabbatar musu da lafiyarsa. Hakan yasa ya miƙe tsaye ya ciro wayar ya miƙa PA ɗinsa dake tsaye kusa da shi.
Wani ɓangare na asibitin ya nufa, inda sauran sojojin suke. Yayi magana da su akan a canja ma Amira asibiti zuwa asibitin sojoji da ke Abuja. Cikin sirri suka kawo wata mota ya shiga yaje gida ya tsimtsa ya canja tufafin jikinsa dan duk sun ɓace da jini.
Army uniform ya saka ya shiga wata motar ya koma asibitin. Ko da ya isa har an canjawa Amira asibiti zuwa asibitin daya buƙata, wajen asibitin ya fito yayi magana da ƴan jarida ya tabbatar musu da abunda ya faru, sannan ya juya ya koma cikin asibiti shima aka soma duba lafiyarsa duk da sun san albarushin be same shi ba.
“Sir Hajiya ta matsa sai ta yi magana da kai, Mai Martaba ma ya kira tun ɗazu kusan sau biyar”
Ya faɗa bayan ya tsare masa ya maƙe guri ɗaya kamar irin ya sha jinin jikinsa ɗin nan.
Sai da aka cire masa abun awan jini sannan ya karɓi wayar. Number Mai maitaba ce wannan karon hakan yasa shi murmushi.
“My Royal Highness”
“Babana kana lafiya?”
“Ina nan ƙalau Mai martaba”
“Babana karka ɓoye min komai”
“Wallahi Babu abunda ya same ni, sai dai yarinya ita sun same ta”
“Ga mu nan gida duk sun rikice sai koke-koke suke, Ummin ka ma ta kirani wai nayi waya da kai? Ta kira ba kai ka ɗauka ba, tana jin dai ko sun same ka bata san halin da kake ciki ba”
“i'm fyn Mai martaba, yanzu nan ma nayi magana da ƴan jarida, da kun kalli news za ku gani ai”
“Wai ya abun ya faru? Kuma su wanene?”
“Wallahi ban san su ba, amman dukan an kashe su, ni ina fito daga restaurant ne kawai sai naga yarinya tana gudu ta doso inda nake, shine sai kawai naga wani ya fito a wata mota dake can nesa da mu, amman haka be hana bingdigar samunta da yake Allah ya rubuto, sai duk muka faɗi, sai na kira boys ɗin mu dake nan gida na faɗa musu sannan na kira head quarter na faɗa musu, kamin su bar gurin sai da suka harbi mutum biyu, kuma duk sun mutu. Sai dai dikansu basu tsira ba sai akayi musu ƙofar rago suna ganin haka sai suka fara buɗawa boys ɗin mu wuta, suma sai suka buɗa musu. Anyi nasara akan su dan an kashe su duka, sai dai suma sun kashe mana soldiers biyu”
“Subhanallah Allah ya tsare gaba, amman ita yarinya ba tare take da su ba?”
“Bana jin haka da ba zasu harbe ta ba, kuma ta zo da wata takardar hannunta an rubuta, wai nayi taka tsan-tsan akwai masu son kashe ni suna bibiyar sawuna, ba zasu min komai a garin Abuja ba har sai na isa katsina saboda sasu akayi”
“Amman ya akayi ita yarinyar ta san da wannan? Anya ba haɗin kai ba ne?”
“Tunanin hakan yasa aka bincika bullet ɗin dan a tabbatar na ƙwarai ne ko roba, an bincika bullet ɗin na ƙwarai ne irin wannan ne da ake shigo da shi ta waje, ta ɓarauniyar hanya, yanzu dai duk wasu tambayoyi sai idan ta farka zamu mata”
“Allah ya tsare gaba, a riƙa taka tsantsan Babana kana wasa da rayuwarka fa”
“Kar hakan ya dame ka Mai martaba, ɗan Adam baya wuce ƙaddararsa, kuma abunda Allah ya kawo babu mahani”
“Haka ne, amman gobe zaka dawo ko?”
Yayi dariya yana mai miƙewa tsaye ya nufi window gurin.
“Gobe kuma? Ai bamu gama meeting ba, akwai wanda za muyi gobe da jibi kamin na dawo”
“Kai ni wannan aiki naka Babana yana tsorata ni”
“To ya muka iya? Dole ne mu saiyardar rayuwarmu dan wasu su rayu”
“Toh Allah ya kyauta. Ga Mamanka zaku gaisa”
Haka Abdool ya bisu ɗaya bayan ɗaya yana gaisawa da matan uban masa da ƙannensa da ƴan'uwansa da suke gidan.
Yana katse kiran Mai martaba ya kira Ummi, ringing ɗaya ta ɗauka tana kuka.
“Son...”
“Ummi I'm fine Wallahi babu abunda ya same ni”
“Ban yarda da kai ba, ai ba zaka faɗa min gaskiya ba, naso na biyo mota saboda babu jirgi yanzu amman gobe da safe zan zo”
“Ummi you don't have to, Wallahi babu abunda ya same ni, yarinyar data tare min bullet ɗin ita aka samu, kuma an yi nasarar kashe su duka”
“I don't trust you”
“If you don't trust me, you should trust yourself, believe yourself remember how you treated your Son he will never ever lied to you”
“You started it”
“No I'm just show it”
“Whatever ni dai gobe zan zo”
“To Allah ya kai mu”
“Amin. Ga sisters naka za ku gaisa sun ta kiran wayarka sai wani ya ɗauka”
Ɗaya bayan ɗaya ya gaisa da su sannan Ummi ta karɓa.
“Ka kira Mai Martaba ɗazu na kira shi yace shi ma hankalinsa a tashe yake be same ka ba”
“Yanzu muka gama waya da shi”
“Okay, Son su waye ne suka maka haka?”
“Nima ban san su ba maƙiya ne kawai”
“Amman ita yarinya ta rayu? Ka santa ne? Ina ka haɗu da ita”
“Na fito ne kawai sai na ganta tana gudu ta doso inda na ke, shine suka buɗe mata wuta, tana da rai amman tana buƙatar addu'ah dan tana cikin mawuyacin hali”
“Allah ya tashi kafaɗunta, ko dan na mata godiya for what she did to our family”
“Ni kaina ina son ta tashi dan akwai tambayoyin da na ke son ta amsa min”
“Allah ya bata lafiya gobe zan zo”
“Ummi”
“Don't!”
Ya riƙe bakinsa kamar tana gabansa.
“To Allah kawo ki lafiya”
Daga haka ya kashe wayar ya juya ya fice daga ɗakin. Ba shi ya bar asibitin ba sai da ya karɓa waya ta fi a ƙirga ɗuk masu tambayar lafiyarsa ne ƴan'uwa da kuma abokan arziki.
NAMRA POV.
Tun da Yasmin ta bar gidan bata fito ko bakin ƙofa ba, balle har ta fito falo, Gwaggo Kulu bata takurata ba, dan tasan halin Namra daman can ba mai son surutu bace balle yanzu data fuskanci kamar tana cikin damuwa.
Duk wainar da ake toyawa a falon Namra bata sani ba, dan hankalinta ma kwata-kwata baya jikinta yana can wata duniyar tana tunanin lamarin rayuwa, yadda ta sauya mata a lokaci ɗaya. Turo ƙofar da Hindatu tayi ne yasa ta dawo hayyacinta har ta ɗan tsorota.
“Anty Namra”
Ta rumgune ta zumuɗi ita da Aisha. Ƴar far'ah tayi irin far'ar nan data zame maka dole tun da tasan ba zuwan daɗi ne ta yi ba.
Sai daga baya Maryam ta shigo dan tun shigowarta tana can gurin Gwaggo tanan mata faɗa akan rashin son zumunci, wai rabonta da gidan har ta manta.
A bakin ƙofa ta tsaya tana murmushi.
“Ta so muje ƴar Anty Abbah yace mu zo muje da ke”
“Da gaske?”
Namra ta tambaya tana zaro ido, irin mamakin ɗin nan da rashin yarda da zancen Maryam. Sai Aisha ta karɓa mata.
“Wallahi kuwa, da gaske shine ma ya kira ki a waya yace muje mu ɗauko ki”
“Ko dai wani abun ai min?”
Ta faɗa da muryar tausayi tana kallonsu, dan bata gamsu Abbah zai ce aje a zo da ita hakan nan kawai ba.
“Babu abunda zai miki baya ma gidan yanzu na fita, Anty ce ta buɗe masa wuta shiyasa ya yarda”
Shiru ta ɗan yi tana tunani, kamin ta miƙe tsaye ta ɗauki jakarta ta rayata, ta kalli Maryam.
“Dan Allah Abbah ne yace na zo?”
Maryam ta dafe kanta.
“Kai ni Allah na, Namra nawa zaki biya ni ne da zan miki ƙarya”
“Ina jin tsoro ne”
“Daman ai kullum cikin tsoro kike”
Ta juya ta fice tana mai jin haushin lamarin Namra. Cikin rashin kuzari ta fito ɗakin tana riƙe da hannun Aisha ta zo ta risina gaban Gwaggo dake zaune falon tana mata sallama kamar wanda bata son zuwa.
Gwaggo na kallon idonta ta kalli Maryam tace
“Duk aka haɗa baki da ke aka yi ma Namra wani abu ko? Heeeee Wallahi sai kin raina kan ki”
Maryam ta ɗora hannu saman kai tana dariya
“Oh Ni na shiga uku, wai fuskata tayi kama da mugaye ne hala?”
“Na dai san halin ki, shegen karanbani da iyayi, kuma na faɗa miki, wallahi ran ki sai ya fi na kowa ɓaci duk aka haɗa baki da ke”
Da dariya ta fita falon. Har gurin Mota Gwaggo ta raka su, tana yi Maryam jan kunne ta daina tuƙin dare kuma ta kula da hanya ban da gudu.
Har suka isa gida gaban Namra be daina dakan uku-uku ba, saboda tsoro da tunanin abunda Abbah zai mata. Lokacin da Namra ta fito motar sai ta ɗaga kanta sama ta kalli gid, idonta ya cika da hawaye, tuna rayuwar da tayi a ciki, da hawaye shaɓe-shaɓe Hindatu taja hannunta suka shiga falo.
Tsaye suka same Anty Amarya tana tsumayinsu, duk wani kunya da take na Namra yau cireshi tayi sai ta zo da sauri gurin ƙofa ta rumgume ƴarta idonta cike da hawaye, haƙiƙa tayi farincikin ganin Namra, sai dai kuma bata jidaɗin ganin yadda ta lalace ba, kamar wance ta shekara tana ciwo.
Maryam ne da Aisha suka ɗauko mata abinci da sha suka jera saman center table. Namra ta kallesu da murmushi.
“Thank you Sisters amman ni ba na cin komai”
“Saboda me? ”
Anty Amarya ta tambaya.
“Namra kamar akwai abunda yake damun ki?”
Shiru ta ɗan yi tana nazarin abunda zata cewa Anty Amarya, dan bata jin zata iya faɗa mata abunda Asim.yayi mata, ta san ba zai mata daɗi ba kuma ba zata ƙyale ba, bayan kuma koma minene itace ta jawa kanta.
“Babu abunda yake damuna, na riga na ci abinci gidan Gwaggo ne, har wanka ma nayi ina shirin bachi suka zo”
“Amman duk da haka Namra kina da damuwa be kamata ki ɓoye min ba, dan nasan wannan zuwan bana banza bane, babu yadda za ayi ki tsallake Asim ki zo nan bayan kin san yana gadon asibiti kwance”
“A...an sallame shi ai, yana gida Mamanshi take jinyarsa shine yace na zo saboda na sha kai da maganar gida ne, nima kwana biyu zan yi na koma”
Anty tayi murmushi, dan tasan ba gaskiya Namra ta faɗa mata ba.
Hajiya Barau ce ta shigo da Sallama tana faɗin maraba da baƙi.
“Yau garin mu? Ina ji maƙi baƙi”
Anty Amarya tayi dariya ta tashi ta shige ɗakinta. A ɗayan kujerar da Namra take zaune Hajiya Barau ta zauna tana satar kallonta, sai fira suke sama-sama tana tambayar labarin Katsina. Sai nanata mata rashin jindaɗin zuwa ganin Asim da Abbah be barta taje ba.
Sai da dare ya raba sannan tayi mata sallama ta tashi ta fice, zuciyarta cike da gulma.
Bayan fitarta Hajiya Barau, Aisha take labartama Namra wanda zai auri Maryam da Hindatu duk sun zo sun gaida Abbah, kuma sun turo iyayensu, dan tsayar da magana.
Namra ta kallesu tana dariya.
“Eyyyye Amare”
Hindatu ce ta ji kunya har ta rufe ido, Maryam kan dariya ta riƙayi sai ta tashi ta bar falon kasancewar tana waya da angon ne.
“Saura ke”
Namra ta faɗa tana wasa da hannun Aisha, sai Aisha tayi mata wani kallo.
“Ni Anty no da na ss2”
“Ƴar jss ma anyi ma aure balle ss”
Dariya Aisha tayi ta rufe fuskarta. Dammm gaban Namra ya yanke ya faɗi, jin ƙarar tsayawar Mota, zuciyarta na nasalta mata Abbah ne ya dawo, ji take idan ya shigo rufeta zai yi da ruwan masifa. Da sauri ta tashi ta nufi ɗakin Anty Amarya gabanta na ci gaba da faɗuwa.
Tsaye ta tararda Anty Amarya tana gyara tufafin da suke wardrobe ɗinta, kallo ɗaya tayi ma Namra ta ɗauke kai tana murmushi, kamar ta san abunda Namra ta jo ma gudu.
“Ai shine yace aje a zo da ke”
“Amman be ce komai ba?”
“Be ce ba, dan shi kansa yana san kina cikin matsala akwai abunda yake damun ki”
“Babu abunda yake damuna Anty”
Anty ta bar tufafin ta zo ta zauna kusa da Namra
“Farinciki da baƙin ciki abubuwa ne da basa iya ɓoye kan su Namra, jikin ki ma ya nuna haka, dubi kiga yadda kika lalace kika rame kamar ba ke ba, Namra karki ɓoye min damuwarki, ni Mahaifiyar ki ce babu wanda ya dace ya ji matsalar ki sai ni”
“Anty babu abunda yake damu na, kawai na zo na gan ku ne”
“Namra dubi kam ki? Kin ga yadda kika lalace?”
“Ba ni da lafiya ne”
“Me ke damun ki?”
“A nan ƙasan marana iya jin ciwo ne, sai kuma ciwon kai da nake fama da shi, ga zafin jiki”
Duk abubuwan data faɗa gaskiya ne tana jin su sai dai bata jin wata matsala ne ko kuma ciwo, yanzu kuma tayi ma Anty ƙarya ne dan ta ƙyale ta.
“To gobe za muje asibiti likita ya duba ki”
“Allah ya kai mu”
“Amin”
Ta faɗa tana janye blanket ɗin dake saman gadonta.
“Ki kwanta a nan ni part ɗin Abbah ku zan kwana, idan kuma ba zaki iya kwana nan ba ki koma ɗakin Maryam”
“A'a nan zan kwana”
Ta faɗa tana kwantawa saman gadon.
Sai da Anty ta gama gyara komai na ɗakin sannan ta ɗauki wasu abubuwa ta yi ma Namra sai da safe ta fice.
ASIM POV.
Bayan ya gama shan koko Mama ta kalleshi tace
“Yau fa kwana biyu yarinyar nan bata leƙo asibitin nan ba”
“Ai ba zata zo ba”
Ya faɗa yana goge bakinshi
“Saboda me?”
“Faɗa muka yi da ita har ma mareta kuma na faɗa mata maganganu”
“Miya haɗa ku”
“Wani na gani ya rako ta, shine wai nayi magana tace ina zarginta, har da wani wai ta ji maganar da muke ɓoyewa na kuɗin a dashe”
Mama ta riƙe baki.
“Mai kaza aljihu baya jimirin ass, daga magana sai kuma tace ana zarginta? Daman tasan abunda take kenan, ni kai na wallahi naga yarinyar da wani amman ban faɗa ba saboda kar na ɓata muku zama, daman ai na faɗa maka ba da zuciya ɗaya take zaune da kai ba”
“Ai yanzu na gane halinta, dan yi mata magana shine har ta min jawabi wai ba na da komai ta aure na lalata mata rayuwa na rabata da karatun ta”
“Amman Ibrahim ka yi wauta, ai kamata yayi ka sa mata ido ka ga iya gudun ruwanta, kuma yanzu idan ma gidan su ta tafi ai sai tace ka ci amanarta kuma ka zarge ka koreta, kuma kai yanzu ko sallamarka akayi ba itace zata yi hidima da kai ba? Ni fa gida zan koma tun da can ma akwai yara ga sana'a na baro kasan idan ba dole ba babu abunda zai zaunar da nan, tunanin hakan tasa Wallahi ban faɗa maka ba.
Yanzu zuwa kaiwai zata yi ta ɓata maka suna, sannan idan ka rabu da ita a yanzu kana da halin auren wata ne? Ai dole kayi haƙuri da ita har Allah ya nuna maka kaji sauƙi sosai ka warke kayi kuɗi, ka auro wata sannan idan ita rabuwa zaka yi da ita sai ka yi, daman sun saba yaba maka rashin mutunci, kawai ka bata haƙuri kace kayi nadama, ai Allah ma ba zai barta ba ace da aurenka kana zina haba abun ai yayi muni, daman can ba ƴar tarbiya bace shiyasa ta bi mutumen aka riƙa cewa kai ne ka ɗauke ta, har ɗan'uwanta ya fasa aurenta kai aka ƙaƙaba maka ƙaya”
Ajiyar zuciya ya sauke wani irin ɓacin rai me ke ziyartarsa.
“Amman Wallahi Yarinyar nan ta ci amanata sosai”
“Haƙuri dai za kayi, ai babu yadda ban yi ba akan karka aureta amman ka tsaya kai da fata sai ka aureta”
“Nayi tunanin aurenta zai zame min alheri ne shiyasa na yi”
“Ka kirata dai yanzu kace ta dawo, kar taje ta shafa maka kashin kaji gurin matsiyacin uban nan nata mai dukiyar likudi (Kuɗin da ba'a iya ci)”
“Bana jin tana garin nan fa”
“Shiyasa na ce ai ka kirata ba kana da number uwarta ba? Sai ka kirata ka bata haƙuri tun dai lafiya ta samu an kusa sallamar ka, idan ka kira karka nuna musu wani abun ne ya haɗa ku, idan sun ce tace kayi mata wani abu kace kai ƙarya take maka, sai idan ta gaji da auren ka ne, karka yarda ka nuna wani abun ne ya haɗa ku”
Kwantawa yayi saman gadon zuciyarsa cike da baƙinciki abunda Namra ta masa, har yana jin kamar ba zai iya kiranta ba, dan ta ci zalinsa da yawa.
“Baka da wata mafita sai wannan, idan kuma kana ganin akwai wata hanya mai fiddaka sai ka yi”
Ta faɗa tana ɗaukar ledar ƙosai da robar koko ta fice.
RASHIDA POV
Mataki uku ake bi gurin gwajin jinin dan a tabbatar da mutum yana ɗauke da cutar, idan an yi na farko ba a tsallake ba sai ayi na biyu idan shima ba a tsallake ba sai ayi na uku.
Duka an yi ma Rashida kuma results ɗaya ya bada cewar tana ɗauke da cutar, tun a cikin asibitin ta fara kuka, har ta iso gurin motarta. Nadamar taraiya da Alh. Bashir take taraiyarta da shi be haifa mata ɗa mai ido ba, be sata komai ba sai baƙinnciki da da na sani.
Tunanin yadda zata faɗawa Momy take, mutuƙar da faɗa mata gaskiya ta san ita ma gudunta za ta yi, mu'alamarta da kowa zai sauya za a fara mata wani kallo har a gurin aikinta ta san sallamarta za'ayi, duniya zata juya mata baya kowa ya tsangwame ta musamman idan aka ji silar rabuwarta da mijinta, babu kuma wanda zai sake aurenta.
Dan haka ta zaɓi zama da su a haka dan ta rufawa kanta asiri. A cikin mota ta ci kukanta ta gaji sannan ta koma gida, a lokacin yamma yayi sosai duka ƙanenta suna gida. Sai dai bata yarda sun ga fuskarta ba har ta shige ɗaki.
Ta sake ɗasa wani sabon kuka tana jin kamar ta sha wani abu ta mutu.
Sai dai wani ɓangare na zuciyarta na faɗa mata, tana da buƙatar rayuwa saboda Hilal da ƴaƴanta, idan har ta kori Kalsoom daga gidan to Hilal zai iya zama mallakinta har a bada.
A kwana biyu da tace zata yi kamin ta je gurin malamin sai ta kasa, saboda mugun ƙudirinta dan bata son ta samu wata ɗaya a gida bata koma ɗakin mijinta ba.
Hakan yasa washe gari tun da safe ya shirya ba tare da sanin kowa ba ta fita. Napep ta tara ta shiga aka kaita tasha, sai ta ɗauki shatar mota har zuwa garin da Malam yake.
Yau kan bata tsaya bin layi ba, dan tun a hanya ta kira shi ta faɗa masa gata nan zuwa, hakan yasa tana zuwa sai kawai aka mata iso cikin faɗar tasa da yake tsiface-tsifacensa.
Kamin tayi sallama wayarta tayi ringing ko da ta duba sai ta ga Hajiya Basira, wani dogon tsaki taja dan yanzu haushi Alh. Bashir take ji matuƙa.
Guri ta samu ta zauna, ta soma roko masa bayani shi kuma sai kallonta yake yana wasar haƙuransa dake cike da goro.
“Ai na faɗa miki wannan duk mai sauƙi ne, idan ma ba zaki iya ba yanzu nan zamu saka iska su ɗauko mana”
“Amman ya za'ayi su iya ɗaukowa Malam?”
“Ai ko wane ɗan 'adam yana da aljanu, sai sai sun kashi kala-kala, akwai waɗanda zaune kawai suke tare da mutum su basa magana , sune yawanci zaki ga ɗabi'unsu ɗabi'un mutum, sai idan waɗancan aljanun waɗanda ake kira iska sun shiga jikin mutum sune suke nunawa, sai kuma rauhanai su kam ƙarfinsu ma basa iya zama a jikin ɗan'adam.
Irin waɗancan da basa magana ko wane ɗan adam yana da su, duk inda mutum yayi suna tare da shi, musamman idan baya tsare addu'ah, kuma kala-kala ne akwai musulma akwai mushirikai. aljanun da zan tura zai same su ne ya tambaye su inda take aje ƙyalen haitarta ko kuma pad sai su nuna musu su kuma su ɗauko. Abu ɗaya ne zai hana su ɗaukar idan lokacin data jefar tayi bismillah to ba zasu iya ɗauka ba, ko kuma ta ƙona pad ɗin”
“To yanzun nawa zan biya?”
“Zaki bada kuɗin tulu dana jaɓa da kuma na ɗauko shi ƙyalen da za'a haɗa abun da shi”
“Dubu hansin zai isa?”
“Ba'a bori da sanyin jiki yarinya, idan kin shirya aiki kawai ki zube kuɗi ayi miki aiki, a take zaki ga aiki da cikawa”
“Zan biya dubu ɗari”
“Cikin satin nan kuwa zaki ji kyakkyawan labari, dan zamu yanka zaɓar ne mu haɗa da zagen hailarta ne, sai mu yi rubuta da wasu silkulle a saka a tulum sai a je can daji a inda babu mai zuwa a rataye tulon a ƙasan tulun za mu yi ƙaramar huduwa wanda ruwan zai riƙa fita kaɗan-kaɗan, yadda ruwan zai riƙa zuba haka jini zai mata zuba har sai ruwan ya ƙare sai mu sake yin wani. Ya sunan kishiyar taki?”
“Ummul khairi, dan Allah malam a taimaka min dan Allah na kawo kukana gareka, dan Allah a taimaka min”
“Karki samu damuwa ki komawarki gida kawai”
“Malam an bincika min ƙasar nan ? An duba lamurrana?”
“Bancika ba tukuna dan ban ƴi zaton zaki zo yau ba, kuma kin ga akwai mutane da yawa a waje, amman idan na bincika ko a waya ne zan faɗa miki”
“To na gode, dan Allah a bincika min ko zan koma gidan mijina”
“Karki samu damuwa, ƙasa zata bada bayanin komai”
Ta zube masa dubu ɗari kasa sannan ta tashi ta fito, zuciyarta cike da yaƙinin abunda Malamin zai aikata mata.
Har ta dawo gida tunanin zuwa karɓar magani take, akan shawarwarin da likitan ya bata, sai dai kuma ya faɗa mata idan har bata shan magani cutar zata bayyana kanta, kuma rayuwarta zata yanke.
NAMRA POV.
Ko da takwas da rabi tayi Maryam da Hinda har Aisha sun wuce school, da wuri Anty ta shirya ma Abbah breakfast, sannan ta zuba ma Namra nata, ita kuma ta ɗauki nata dana Abbah ta nufi part ɗinsa da shi, dan bata breakfast ita kaɗai indai har Abbah yana ɗakinta ne, sai dai tare da shi. Namra na cikin ci abinci sai ga Hajiya Barau ta shigo mata da nata breakfast, tana far'ah kamar gaske.
Wanda Anty ta zuba mata ma bata ci da yawa ba, balle na Hajiya Barau ko buɗashi ba tayi ba, sai dai tana jin ƙamshin ferfesun kayan ciki na dukan hancinta.
Tashi tayi ta wanka ta shirya cikin wasu tufafin sababin da Maryam ta ɗauko mata, tana cikin ɗaurin ɗankwali Anty Amarya ta shigo.
Ta jidaɗin ganin abincin da Hajiya Barau ta kawo ma Namra sosai, hakan ba ƙaranin faranta ranta yayi ba.
“Ai baki ma ci komai ba”
“Na riga na ƙoshi”
“Namra baki son cin abinci, wannan ma baki ci da yawa ba, gaskiya dole muje asibiti a duba lafiyarki, zan je na gyara sai kije ki gaida Abbah ki”
“Tau”
Ta amsa murya ƙasa-ƙasa tana jin kamar dai kar taje. Ɗankwalin ta aje ta ɗauki hijabin Anty ta saka ta nufi part ɗin Abbah tana wata tafiya kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki.
da Sallama ta shiga sai ta tsaya can bakin ƙofa ta risina ƙasa ta gaishe shi, kanta na ƙasa tana mai jin kunyar haɗa ido da shi.
“Abbah ina kwana? An tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau”
Sai kuma ta rasa me zata sake ce masa.
“Mahaifiyarki ta faɗa miki sati ɗaya na yarda ki yi ko? Dan kin san na gargaɗe karki kuskura dako min gida da sunan fushi ko saki”
Idonta ya cika da hawaye, a take muryarta ta soma rawa.
“Abbah ba fushi na yi ba, na zo ganin gida ne”
“Ko minene dai na faɗa miki duk kika doso min gida da sunan saki, to sai dai mahaifiyarki ta tattara kayanta ku bar min gida, tun da kin zaɓi zama da shi sama da Mahaifin ki sai kije can ku ƙarata”
Da sauri ta ɗago kai ta kalli Abbah, sam bata yi tunanin abun nasa ya kai har haka ba.
“Inshallah haka ba zai faru ba Abbah, amman dan Allah ka yafe min kuma ka fahimce ni”
Da hannu ya yi mata alama da ta tashi ta bashi guri. Da sauri ta tashi ta fice tana kuka. Kamin ta ƙarasa part ɗin Anty Amarya ta tsaya ta share hawayenta, sannan ta shiga.
Lokacin Anty Amarya ta fito daga wanka tana cikin shiryawa, falo Namra ta koma ta zauna sai da Anty Amarya ta gama shirinta ta ɗauko jakarta ta fito suka fita tare.
Driver Abbah ne ya kai su asibiti, sun yi sa'ar ganin likita dan tun kamin su isa Anty ta kaira likitan dake duba su ta faɗa masa, sai yayi ma wata likita magana dan shi be shigo asibitin ba a lokacin.
Mutum biyu aka duba kamin ita, sannan ta shiga tare da Amarya. Bata ɓoye komai ba da taji tayi ma likitar bayani, ita kuma sai ta rubuta mata text ɗin jini da na fitsari, sannan ta tura gurin hoto, dan akwai buƙatar su ga abunda yake ƙasan mararta da take ji yayi mata tsaye gefe ɗaya.
Basu bar Asibitin ba sai da suka je aka musu hoton, aka basu sai suka wuce gurin ɗibar jini aka ɗibi jininta sannan suka bata wani roba ta shiga banɗakin gurin tayi fitsari ta kawo musu, sai suka je sai gobe ta zo ta karɓi results, daga suka koma gurin likitar suka kai mata result ɗin.
“Subhanallahi”
Ta faɗa lokacin da ta kalli hotonnan guda uku da suke guri ɗaya, sannan ta kalli Namra ta ce
“Me kika sha na zubar da ciki?”
Ba Namra har Anty Amarya sai da gabanta ya faɗi.
“Ban sha komai ba”
“Kin yi ɓari amman ko?”
Ta ɗaga mata kai
“Eh na yi”
“Amman ba kije asibiti ba?”
“Na je sai dai ban tsaya ba, saboda lokacin mijina be da lafiya”
“Kin yi kuskure gaskiya, da kin tsaya an duba ki ai, yanzu kin ga rabin cikin yana cikin mahaifarki, hakan ya haddasa miki wannan ciwon da kike ji, mahaifarki ta saki sosai har wani ɓangare na jikin mahaifar ya buɗe ya hudu, jiki be yi saurin ɗauke miki ba lokacin da kika yi ɓarin? Ke duk baki lura ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Namra ta faɗa tana kallon Anty Amarya da tashin hankali ya bayyana a fuskarta.
“Yanzu likita me ye abun yi?”
“Za'ayi mata wankin mara ne, sai mu ɗorata akan magunguna, amman gaskiya akwai buƙatar tayi family planning na shekara biyu ko uku gudun karta ɗauki ciki har sai mahaifarta ta warki”
Kuka Namra ta saka tana dafe da cikin nata. Anty Amarya ta riƙa bata haƙuri, tana mamakin lamarin dan ita bata ma san lokacin da tayi ɓarin ba, kuma gani take kamar wani abu ta sha dan ta zubar da cikin.
KALSOOM POV.
Kwata-kwata yanzu bata gane lamarin Ezzah ta ɗauke ta kamar wata maƙiyiyarta, sam bata ma son zama falon idan Kalsoom na nan, abinci ma idan ba Doc ne yake gidan ba, sai ta ƙi ta koma can ɗaki ta keɓe kanta.
Bayan shi babu wata matsala da Kalsoom take fuskanta, ita kuma bata ɗauke ta matsala ba dan ba biye mata zata yi ba, zamanta da Doc lafiya ƙalau sai ƙarin so da ƙauna, ga ɗan cikinta tana raino gwanin sha'awa ɗan satin nan data samu har tayi fari sosai tayi ƙiba ta mulmule kamar ba ita ba, Doc har tsokanarta yake wai shi take tsotsewa ita tana ƙiba shi be gane ba.
Ita kuma ta san babu komai sai kwanciyar hankali da kuma kulawar mijinta da take samu a yanzu, ga Ulfah da Rafiq da suka zame mata tamkar ita ta haife su, dan ko maganar Mamansu basa yi, indai kaga wani baƙin hali to Ezzah da kicifin dan tafi kowa kishin uwarta yanzu.
500k words....
______________________________________________
Littafinan na kuɗi ne, idan kin san baki biya ba, karki karanta.
₦200 zaki turo ta wannan account ɗin 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.
Sai ki turo da shaidar biyan kudin ta wannan number 08036126660
DON'T READ IF YOU DIDN'T PAY...!
*PAGE - 45*
NOT EDITED ⚠
Sai da Yamma lis Anty da Namra suka dawo gida, bayan sun yi mata wankin mara sai da suka bata 6 hours suka ga condition ɗin ta sannan suka barta ta dawo gida.
Jikinta ya mutu sosai, ga tunanin dake zuciyarta, tana jin gajiya a tare da ita amman tunanin dake cikin zuciyarta ya hana ta tayi bachi bayan sun dawo gida.
Tana jin kamar ta labartawa wani damuwarta, sai dai kuma bata san yadda za su kalli abun ba, ace kamar Asim ya juya mata baya, sannan tana ganin idan har ta faɗa Anty ba zata barta ta cigaba da zama da shi ba, Abbah kuma ba zai yarda ta zauna a gidan ba.
Haka ta kwana ciki damuwa da tunani har garin Allah ya waye, karin safe ma sai da Anty ta tirsasa sannan ta ci.
Tana cin abinci tana kukan zuci, kukan da bata san ranar tsayawar hawayenta ba, kuka maraici amman bana rashin uwa da uba ba, kuka take kukan butulci bayan hallaci kukan nadama da bata da gani.
“Anty Namra kuka kike?”
Hindatu ta tambaya tana dafata, yanayinta duk ya canja ganim ƴar'uwarta cikin damuwa.
Hannu tasa ta taɓa fuskarta dan tabbatar da hawayen ya fito, sai kawai ta share tana murmushi.
“Ban ma san ya fito ba, baki iya sallama ba ne idan kin shigo?”
“Na yi sallama baki dai ji ba ne, me kike ma kuka?”
“Ba komai, dan Allah karki faɗawa kowa kin ji?”
“Tau, ga waya Anty tace na kawo miki Asim.ya kira”
Wayar ta sakarwa ido, kamar mai tsoron karɓa, ji take kamar ba wani abun ƙwarai bane zai faɗa mata, what if yace ya sake ta?
“Anty...”
Hindatu ta kira sunanta ganin yadda ta tsurawa wayar ido tana nazarin zuci. Sai a sannan ta kai hannu ta karɓa, ita kuma ta tashi ta bar mata ɗakin.
Wayar na fara ringing gabanta ya faɗi, ba ƙaramin ƙoƙari ta yi ba wajen picking ɗin call ɗin.
“Assalamu alaikum”
“Wa'alaikissalam Namra”
“Na'am”
“Kin je gida ba tare da kin sanar min ba, miyasa kika je? Kina son ki faɗa musu abunda ya faru ne? Na san ban kyauta miki ba, amman Wallahi sherin sheiɗan ne, ni kaina nasan ban kyauta miki ba, amman ina kishin ki ne Namra dan me zaki bar wani ya rako har cikin asibiti kin ganin hakan kyautawa?”
Hawaye ya fara bin fuskarsa.
“Kai yi min abunda wani be taɓa min ba, ko a mafarki ban za ci zaka aikata min ba, Asim ka yi taɓon da har na koma ga mahallacin na ba zai gogu ba, baka tambaye ni waye ba, baka bincike alaƙa ta da shi ba, sai kawai ka zarge ni, ka ɗaga hannunka ka mareni”
Ya fara mata kuka kamar gaske.
“Na san ban kyauta ba, kuma na cancanci ko wane irin hukumci, amman ki dubi girman Allah ki yafe min, dan Allah karki faɗawa kowa abun da ya faru tsakaninmu, Wallahi idan har ki ka bar zan iya shiga ko wane irin hali, haƙiƙa ni butulu ne kuma ajizi, Namra ki dubi girman ƙaunar dake tsakanin mu ki yafe min, ni har ganin nake kamar shiga tsakani ne”
“Ban faɗawa kowa ba, kuma ba zan faɗa ba, kuma na yafe maka”
“Na gode Allah yayi miki albarka, dan yaushe zaki dawo? Ko nasa Mama ta zo taje da ke?”
“Ba sai ta zo ba, zan dawo cikin satin nan”
“Yaushe?”
“Nan da kwana uku”
“Kwana uku yayi nisa Namra, da a'ce da hali sai ki dawo gobe ko jibi”
“Sai jibin dai”
“Na gode sosai Allah yayi miki albarka, duk suna lafiya ko?”
“Kowa ƙalau”
“Ina gaida kowa dan Allah”
“Za su ji”
“Na gode sai na ƙara kira”
Ta sauke wayar tana cigaba da hawaye.
“Na yafe maka, amman ba zan manta ba, zan zauna da kai saboda zama da kai ya zame min dole, son ka be amfana min komai ba Asim sai baƙinciki da damuwa”
Ta share hawayenta tana jin wani irin ƙuna da zuciyarta ke mata. Ɗan abincin da take ci sai ya fita ranta, ta tattara kayan abinci ta ɗauki tray ta nufi kitchen da shi, bayan ta aje ta dawo falonta zauna tana miƙawa Anty wayarta.
“Har kun gama”
“Eh wai tambaya yake yaushe zan dawo”
“Dika yaushe kika zo? Me kika ce masa”
“Nace masa sai Next week amman ya ce sai dai na dawo gobe, daker ya haƙura na kai jibi”
“Haba Anty Namra dika yaushe kika zo ma?”
Maryam ta faɗa. Anty tace
“Zan yi magana da shi ya bar ki kiyi ko wata ɗaya”
“A'a Anty kin san ba shida lafiya sosai ma, kuma bana son satin da Abbah ya bani ya cika ban koma ba”
Ɗaya bayan ɗaya Anty ta bisu da kallo, a tunaninta ko a cikinsu ne wani ya faɗa mata Abbah yace karta wuce sati ɗaya.
Maryam ce ta fara tsarguwa da kallon Anty ta yi magana.
“Wallahi ba ni na faɗa ba”
Aisha
“Ni ma dai”
Hindatu.
“Balle kuma ni”
“Waya faɗa? Ko muna da aljanu ne a gidan?”
Namra tayi murmushi, irin murmushin nan na ƙarfin hali ka danne baƙincikin ka.
“Ba suka faɗa ba, Abbah ne ya faɗa min da kan sa”
“Yaushe?”
“Jiya da naje gaishe shi, yau ma ya nanata min”
Anty tayi shiru bata sake cewa komai ba. Sai dai bata jidaɗin da Abbah ya faɗama Namra haka ba.
“Akwai abubuwan da kike buƙata ne? Dan a siya da wuri kar lokaci ya ƙure, ko kuma kuɗi zan baki kije can ki siya?”
“Kuɗin zai fi, dan ɗaukar kaya a nan ma ai aiki ne”
“Amman Namra ba zai yarda ku dawo nan ba?”
“Kwana ki ma yayi min maganar haka, amman nace ya haƙura har yaji sauƙi sosai sannan mu dawo”
“Gaskiya kam zama a nan zai fi, kim ga nan zai fi muku kuma kin ga nan ko ba komai kina kusa da mu”
Sallamar Doc Faruk ne yasa suka katse firar da suke suka amsa sallamar suna masa sannu da zuwa.
A kujerar da Namra take zaune ya zauna, kasancewar ta zaman mutum uku ce, sai ya soma gaiswa da Anty cikin far'ah, tun da shi ba baƙon gidan ba ne.
Maryam da Hindatu da Aisha sai duk suka tashi suka bashi guri, Anty ma tana gama gaisawa da shi, ta shige ɗakinta dan tasan abunda ya kawo shi, daman ita ta kira shi, ganin hakan kamar zai fi sauƙi tun da likitan gida ne.
“Daman akan maganar planning ne Anty tana tsoro kar ayi mai side effects, so ni abunda naƙe ganin ya fi shine ki yi na roba, saboda idan an saka mishi kin ga sai lokacin yayi sannan za'a cire, ba kamar allura bane da a za'a riƙa yi duk months, kuma kin ga shan ƙwayoyin zai iya ƙara miki matsala ma a mahaifa, za a iya tsuke miki bakin mahaifa”
“Amman robar idan an saka ba shi da wata illa ne?”
“Eh to kin san komai karɓa karɓa ne, amman gaskiya baya da matsaloli kamar sauran, kuma kin ga shi a duk lokacin da aka tashi cire miki za'a iya cirewa”
“Amman yanzu ina katsina da zama idan na saka ta nan za'a iya cire min a can?”
“Za'a iya cire miki mana, amman idan son samu ne inda aka saka miki a cire miki ita, saboda aikin wani ba shine aikin wani ba, kuma idan ma son samu ne likitan daya saka miki ita ya zama dik lokaci shine ya ke duba ki”
“Amman kana ganin ba zai haifar minnda matsala nan gaba ba?”
“Gaskiya bana jin zai haifar miki da matsala, indai ba abunda Allah ya kawo ba, sai dai kinsan komai yana da side effects sai dai wani ya fi wani”
“Okay, ba matsala when za'a saka?”
“Ko yaushe kika tashi, a hannun hagu ake sakawa kuma idan an saka miki ba zaki yi aikin da hannun ba tsawon 24h, amman za mu buƙaci sa hannun mijinki kamin mu saka miki”
“Mijina baya tare da ni yana Katsina, kuma idan da hali ina son a saka min gobe”
“Consider it done, zan yi replacement ɗin mijinki a gurin sa hannu ko da wannan zan yi alfahari”
Tayi kamar bata ji shi, sai ta tashi ta nufi ɗakin Anty tana faɗin
“Zan shiga ciki”
“Around nine za ku shigo”
Ya faɗa sannan shi ma.yasa kai ya fice.
“Mun yi magana da shi zai saka min roba ta hannu”
Ta faɗa tana ƙoƙarin zama kusa da Anty.
“Ta shekara nawa? Ita bata da matsala kamar sauran ko?”
“Eh haka ya ce, gobe da safe za mu shiga”
“Allah ya kai mu, ya baki lafiya”
“Amin”
Kwantawa tayi saman gado, Anty ta tashi ta fita.
Washen garin ranar da yace musu suka tafi aka saka mata, duk wani shirin a ranar Anty tayi mata shi, saboda komawar da zata yi gobe.
Hajiya Barau tayi mamakin komawarta da wuri haka, a take ta raya a zuciyarta ƙila Abbah ne yace be yarda ta daɗe masa a gida ba, ita tama yi mamakin da ya barta har ta zauna, goma na arziki ta haɗa mata, tun daga kan kayan sawa zuwa kuɗi da kayan mata.
Ranar da zata koma taje yi ma Abbah sallama, ranar ta sha kuka kamar ranar da za'a kaita ɗakinta, Anty ma tayi kuka sosai har hakan ya saka sauran ƴaƴan na ta kuka.
Direban gidan aka sa ya kaita har katsina dan Anty bata son ta shiga motar haya. Sai da ta biya gidan Gwaggo tayi mata sallama sannan suka kama hanyar katsina.
RASHIDA POV.
Washe garin ranar data dawo Malamin ya kira yana labarta mata bayanin da ƙasa ta bada akanta.
“Ba zaki taɓa komawa gidan Mijin ki ba, matuƙar wannan matar tana cikin gidan, sannan idan baki tashi tsaye ba, to har ƴaƴanki mijinki zai wulaƙanta su akan ta, kuma kin yi kuskuren ba mu suna, Ummu Kalsoom take ba Ummulkhairi ba”
“Na ɗauka ai duka ɗaya ne”
“Ba ɗaya bane, sannan mun ga wani baƙin hudu a tare da ke, kuma bayani ya nuna a halin yanzu tana sama da ke sai kin tashi tsaye”
“Malam wane irin baƙin abu ne wannan?”
Duk ta tsorta.
“Bayani be fito mana fili ba, amman lailai akwai baƙin abu yana biye da ke, kuma akwai abu a jikinki wanda kike ɓoyewa dangin ki”
“To Malam a taimaka ayi mana aiki, ta fita gidan kamin na cika idda kuma ayi min abunda zai jawo hankalin mijina gare ni”
“Dika za'ayi aikin ma nasa a aiwatar da shi yau”
“Amman ƙasa ta bada bayanin zan koma gidan Hilal?”
“Ƙasa ta bada bayani kan mijinki, matakin da muka ɗauka yanzu idan be yi ba, sai mu yi na biyu idan be yi ba, sai na uku wanda shi kam dole ne a samu nasara”
“Wane mataki ne?”
“Dika zaki jisu, amman na biyu da na uku abubuwa masu matuƙar wahala”
“To Malam na gode, amman dan Allah a taimaka a bincika min baƙin duhun nan”
“Zamu bincika”
Ya kashe wayar, ita kuma ta sauke ajiyar zuciya tana dafa kai. Baƙin abun nan ya tsaya mata a rai, sai faman tunani take wane baƙin abu ne? Ko dai Ƙalsoom ce ko kuma ciwon da take ɓoyewa ne? Bata samu amsar tambayarta ba har ta gaji da tunanin ta tashi ta shirya ta nufi makarantar su Ezzah. A hanyarta ta tafiya ne Alh Bashi ya kirata wai yana nemanta kwana biyu yayi kewarta, tsaki taja ta faka gefe tana magana da shi.
“Hala baka san aurena ya mutu ba?”
»“Na sani mana, sai dai ban san dalilin mutuwar auren na ki ba”
“Kishiyata ce ta fi ƙarfina ta mallake min miji da ƴaƴa”
Daga can cikin wayar yayi dariya ya ce
“Ke yanzu kamar ki har wata mace ta isa ta fi ƙarfin ki, anya mijin ki ya san mace kowa?”
“Hmmm ƙaddarace ta gitta irin wace zata gitta ka saki Asmee nan gaba”
“A'a aure na da Asmee ai na zobe ne, idan kin ga na rabu da ita to na mutu, indai ina raye ba zan rabu da ita ba, idan kin ga na rabu da ita to na rabu da uwata ne”
‘Hmmm saboda ta maka mugun magani ba, ai wallahi tayi ma kan ta ƙiyamul laili’
Rashida ta faɗa a ranta, a fili kuma sai ta ce
“Kasan da ita kake zama da ni”
“Wannan ai daban, ni dai ki zo ina son ganin ki”
“Ko na zo babu abunda zan maka, dan ni period na ke”
“Na sani haba, ke dai ki zo ina neman ki, amman fa anjima idan mun tashi aiki”
“Na ji”
Ta kashe wayar, ta kunna motar ta hau titi.
ABDOOL POV.
Ko da sha ɗayan safe tayi Ummi da Jidda sun sauka garin Abuja. Kai tsaye ta wuce masaukin Abdool, a lokacin baya ma gidan yana gurin meeting, haka ta zauna a gidan har ya dawo sannan hankalinta ya kwanta ganin da gaske babu abunda ya same shi.
“Ummi na faɗa miki am fine amman kika ƙi yarda da ɗan ki”
“Yanzu ai na yarda, ina ita yarinyar ta ji sauƙi?”
“Eh ance min jiya ta farka, amman ban samu na je dubata ba, amman na ce suje su ɗauƙi statement”
“Allah sarki baiwar Allah ai ta taimaka da yanzu kai ne aka harba”
“Ko bata tare ba, ba zasu harbe ni ba, dan Allah ya rubuta ba zasu same ni ba”
“Haka ne kuma”
“Ummi me kuke so a siyo muku?”
“A'a ni ba zaka ƙara siyen abincin nan ba, ai da gaskiyar Mai martaba da yake cewa ka daina yawo kai ƙaɗai, ni gaskiya ya kamata ace ma ka yi aure dan ka huta da wannan wahalar siyen abincin kullum”
Dariya yayi ya tashi ya fita. Be daɗe ba ya dawo, ya tsaya daga bakin ƙofa
“Ummi zan je asibitin idan kun huta kun ci abinci direba zai kai ku ku ganta”
“To a kula dan Allah”
“Inshallah”
Ya ciro wayarsa dake ringing ya amsa kiran ya juya yana magana ya fice. Sai da ya biya wani office nasu yayi wani meeting sannan ya wuce.
Sun masa bayanin abunda suke zargi akansa, suka nuna masa bayananta da suka ɗauka sannan ya shiga ɗakin da take.
Kife take saman gadon asibitin sanye da tufafin majiyanta, wani irin kallo take masa irin kallon nan na mutum be san yana yi ba. Har ya zauna a kujerar dake facing ɗinta bata ɗauke idonta akansa ba.
Hannunsa ya riƙa yawo da shi dan ya tabbatar tana cikin hankalinta ko akasin hakan. Sai kawai ta lumshe ido hawaye ya silalo daga idon nata. She just can't believe Abdallah take ganin da idonta, mutumen da ko a mafarki take ganin yayi mata nisa, sai dai tasan tayi betrayed wanda yayi mata mafaka a lokacin da bata da gurin zuwa, ga shi waɗanda suka mata tambaya a ɗazu sun tabbatar mata da ya mutu.
“How are you feeling”
Ta buɗe ido ta kalleashi, sai kuma ta kawarda kanta gefe kamar bata ji abunda yace ba.
“Ko ba ki jin turanci ne?”
Ya tambaya yana leƙen fuskarta.
“Ina ji”
Ta amsa ba tare data kalleshi ba.
“Me kike yi ma kuka?”
“Kukan baƙinciki nake, miyasa baka bar ni can na mutu ba? Sai ka ɗauko ni ka kawo ni asibiti?”
“Taya zan bar mace data sadaukarda ranta gare ni ta mutu?”
“Na sadaukarda raina a gare ka saboda ni na rasa nawa ran, kai kana da amfani ga alumma ni ko bana shi, kuma na san duk na sadaukarda rai na a gareka dole ne kai ka rayu ni na mutu”
“Sai gashi kuma sai dik muka rayu”
“Shiyasa ni nake baƙinciki, na yi tunanin ni tawa wahalar ta yanke daga nan ne, ashe akwai sauranta”
“Wacece ke? Miyasa kike irin wannan furucin?”
“Nice wacce ta rasa uwa da uba, wacca aka koreta daga gidan su saboda saurayi ya yaudare ta”
“Ban gane ba?”
“Ƙawata ta haɗa kai da ɗan'uwanta ta yaudare ni. Fyaɗe tasa ɗan'uwanta yayi min, sanadin hakan na samu ciki, ni kuma sai iyayena suka kore ni, na zaje garin Kaduna, ranar dana sauka a garin na haɗu da Guy son yaje tasha karɓar saƙo, sai ya ɗauko ni ya kawo ni gidansa da sunan zai kwana da ni ya biya ni, daya fahimci bana da gurin zama, sai yayi masauki a gidansa, ashe ɗan fashine kuma yana kidnapped ni ban sani ba sai bayan mun shaƙu da shi, shi ya zubar min da cikin da ke jikina ya mayarda ni karuwarsa”
“Ayyah sorry, amman me kika sani game da Guy Son?”
“Ban san komai akansa ba, baya bari na shiga lamurransa”
“Ya aka yi kika san yana attacking ɗi na?”
“Saboda ya san ina son zuwa Abuja, sai yace zai zo da ni, amman wani aiki zai zo yi, na kashe wani soja wanda wata mata tasa aka she shi, amman a nan ba su kashe ka sai ka koma Katsina”
“Ya faɗa miki wacece matar?”
“Be faɗa min ba, ban ma san kai wanene ba kawai ya faɗa min zai zo bibiyar sawon ka ne, ni kuma naga ba zan iya bari ta kashe ka ba, shiyasa na zaɓi mutuwa kai ka rayu, dan nasan dole zai nemi kashe ni, ni kuma buƙatana ya biya tun da ka rayu”
“Wane gari kike?”
“Sokoto”
“Amman miyasa kika zauna da shi bayan kin san yana aikata kisan kai?”
“Me kake tunani ga mace da iyayenta suka koreta? Idan ban zauna da shi ba da wa zan zauna? Wa zai min masauki? Ina za a karɓe ni?”
Kuka ta fara rerawa tasa hannu a baki gwanin tausayi.
Kallonta yake indai har da gaske na abunda ta faɗa, to ita abar tausayawa ce, sai dai shi yana jin be yardar da ita ba.
Jin kukan nata na son yawa yasa shi tashi ya bar ɗakin. Baga ɗaya fita yayi daga harabar asibitin ya nufi wani part na gurin. Wani ɗaki ya shiga ya kwashe waya ɗaya a ɗakin suna tattaunawa sai da aka ce masa ga Ummi nan sannan ya fito ya tare su.
“Jikin nata da sauƙi dai ko?”
“Da sauƙi sosai ma, mun yi magana da ita sosai sai dai a bayanan ta ban yarda da ita ba, dan haka nasa a bincika min komai a kanta”
“Hakan yayi mi tace maka ne?”
A nan ya fara bata labarin da Amira ta bashi, suna takawa zuwa part ɗin da Asibitin take da ƙafa.
Sosai da sosai Ummi ta ji tausayinta ya kamata, har idonta ya cika da ƙwallah, sai Allah wadai take ma iyayenta da ƙawar data cuce ta.
Amira na jin lokacin da suka shigo amman tayi pretending like she's seriously sleep. Fukarta kawai Ummi ta leƙa cike da tausayawa ta juyo ta fito tana mata addu'ar samun sauƙi.
KALSOOM POV.
Tayi mamakin ganin haila a yanzu, bayan tasan tana ɗauke da ciki, kuma rabonta da haila tun kamin ta samu ciki. Hakan yasa ta fara zargin ko dai bata da cikin ne? Sai dai kuma ita tasan tana jin alamun masu ciki kuma Doc ma ya tabbatar mata da haka. Wani tunanin ne ya zo mata, wata ƙila tana cikin matan da suke haila a lokacin da suke ɗauke da juna biyu.
Ita dai abun ya ɗaure mata kai. Tun a dare da abun ya same ta Doc ya sani sai ya ɗaga mata kafa ya saurara na tsawon kwana biyu ya gani ko jinin zai ɗauke mata, amman be ɗauke mata ba. Hakan ya bashi mamaki.
Yayi mata tambaboyi akan lafiyarta, kamin ya ɗauke ta suje suje su yi hoto dan tabbatar da lafiyarta.
Ya yi mamakin results ɗin da hoton ya bada wai bata da ciki, alamu ya nuna mahaifarta ma ciki be taɓa zama ciki ba.
A tare suka dawo gida sai dai be yarda da faɗa mata abunda result ɗin ya bada ba, dan har yanzu mamaki yake, daya sauke ta be shigo ciki ba, ya ce mata ya zai koma gurin aiki.
Ita sam bata lura ba, dan bata kawo komai a ranta ba. Tana shiga falon ranta yayi mugun ɓaci ganin yadda duk suka lalata falon kamar bata gyara shi ba kamin ta fita.
Saman kujera ta zauna tana kallon falon cike da takaici tace
“Ezzah zo ki share falon nan, Ulfah ke kuma ki kwashe plates ɗin nan shine bayan fita na kuka sake ɗiban abinci kamar ba ku ci ba? Kuma duk kuka lalata falon haba dan Allah miyasa ba ku tausayina ne?”
“Ezzah ce ta ce mu ɗibo mu ci tun da abincin Baban mu ne, wai ita bata ƙoshi ba kin sa mata kaɗan”
Ulfah ta faɗa tana shirin tattara plates ɗin. Kallon Ezzah Kalsoom tayi cike da mamaki.
“Abincin da nake sa muku ne baya isarku shine ba zaki yi magana a daɗa miki ba? Sometimes ba ke da kanki kike ɗiba ba? Ezzah me ke damun ki ne? Me yake cikin kan ki ne? Kwanakin nan kwata-kwata kin canja kina son lalata kan ki”
Wata irin harara ta bankaɗo ma Kalsoom kamar ta taso tazo ta maƙareta. Kalsoom ta nufi inda take tana nuna kan ta
“Ke ni kike harara? Warin ki ce ne?”
Ta zungureta. Sai kawai ta fashe da kuka daman jira take.
“Wayyo Ammyn mu....”
“Ooo munafuka, daman abunda kike nema kenan ko? Na dake ki so that ace na cuce ki ko? Ke ƙaramar yarinya da ke kin san munafurci? Tau Wallahi ba zan ɗauka ba, ba zai yiyu na yi kishi da uwarki ba yanzu kuma na yi da ke ba, tashi ki share falon nan ko na miki matsiyacin duka”
Cikin kuka ta tashi ta shiga kitchen ta ɗauko tsintsiya ta soma sharar. Ulfah na daga gefe tana kallon Kalsoom cikinta dik ya ɗuri ruwa ji take kamar itama zuwa zatayi ta dake ta.
Doc be dawo ba sai dare, tun a bakin ƙofa Ulfah ta same shi ta labarta masa abunda Kalsoom tayi ma Ezzah, sai dai be ɗauki abun serious ba dan yasan Kalsoom ba zata dake ta a banza ba.
Sai dai samun Ezzah a falo da yayi tana kuka ya ɗan sosa masa rai.
“Me kike yi ma kuka kuma?”
“Yunwa na ke ji, Anty tace karna sake ɗiba abinci har sai ta ga dama ta ba ni”
“Ba ki ci abinci dare ba ne?”
“Har na rana ban ci ba, wai dan nace sai na faɗa ma maka ta fita”
“Je ki ɗibi abincin zan yi magana da ita”
Ta tashi ta nufi dinning, shi kuma ya nufi ɗakin Kalsoom cike da gajiya.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: 4»»»»6»»»»»»»»»»»»»
Gaban mirror ya same ta chaɓa ado tana kallon kan ta. Dik wata gajiya da fushi dake tare da shu sai ya kushe, saboda yana son ado, mutum ne mai son ganin mace ta yi kwallaiya a ko yaushe. Murmushi ya ƙarasa kusa da ita yana ƙyaƙƙyawar fuskarta ta madubi.
Ita ma murmushin take tana lumshe ido tana buɗewa, irin na ɗaukar hankalin nan. Sun samu minti biyar a haka suna kallon junansu kamin ya risina ya rumgume ta.
“Who brought this Cute Babe here?”
Lumshe ido ta yi tana sauraren yadda yake shinshinar wuyanta.
Saukowa yayi ya duƙa gabanta ya kama duka hannayenta yayi mata kiss.
“Sweetheart, I'm sorry we lost our baby...!”
Farincikin da ke fuskarta ya gushe, idonta ya cika da ƙwalla, har sun fara zuba a fuskarta.
“How...?”
“I have no idea kawai result ɗin ya nuna ciki be taɓa zama a mahaifarki ba”
“Amman ina jin alamu na ma su ciki, kuma kai ma ka tabbatar min da ciki ne”
“Yes sai kuma yanzu ya zo akasin tunanin mu, ko kin sha wani abun ne?”
Kai ta girgiza masa tana kuka. Sai ya jata zuwa ƙirjinsa ya rumgume ta.
“Shiiiiii Allah zai ba mu wani”
Ƙamƙame shi tayi sosai tana kuka. Har ƙasan ranta take jin zafin zubewar cikin, ta yi buri akan cikin nan har mafarki take, kuma ita bata san ta sha komai na zubar da cikin ba taya za a ce ya zube?
Daker ya lallaɓa tayi shiru, amman duk kwaliyar da tayi ta dale ta ɓata mata fuska kamar yarinya ta yi kuka.
“Ya Salam, yanzu dik kin ɓata kwaliyar nan”
Bata ce masa komai ba, ta tashi ta hau saman bed ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya. Damuwar da take ciki yasa be yi mata maganar komai ba, sai kawai ya tashi ya koma ɗakinsa yayi wanka ya shirya cikin kayan bachi, sannan ya dawo falon ya kashe kayan kallo, ya tura yaransa ɗakinsu. Sannan ya ɗibi abincin mutu biyu a plate ya shiga da shi ɗakinta.
Dik yadda ya lallaɓata ta ci abincin ƙin ci ta yi, daya matsa mata ma, sai akwai ta fara masa kuka, a dole ya ƙyale ta ya aje abincin jefe dan shi ma baya jin zai iya cin abinci bayan matarsa tana cikin damuwa.
Haka ta kwana cikin damuwa tana ganin kamar dai wasa Doc yake mata, cikinta na nan tun da ita dai bata ji wani alamu na zubewar ciki ba, sai dai kuma jinin dake mata zuba ya tabbatar mata haka. Sai da ta yaƙi zuciyarta sosai, sannan ta iya godiya ga mahalaccinta, ta fawwala masa komai dan tasan shine mai yi, shi ne kuma ya bata yanzu ya karɓe dan haka sai ta gode masa.
Cikin kwana biyu ta manta abun a ranta, ta cigaba da walwalarta tana sakewa kamar yadda take a da. Ta cigaba da bawa mijinta kula sai dai har gobe matsala ɗaya take fuskanta ta ɓangaren Ezzah dan yanzu abun nata sai ƙara ta'azzara yake tana ƙara tirjewa.
Yau ma abunda ta saba mata a kullum shi tayi, ta ci abinci dik ta ɓata falon kuma haka zata tashi ta barshi haka sai dai Kalsoom ta gyara.
Da kallo Kalsoom ta bita har ta zauna saman wata kujera ta zauna ta buɗe school bag ɗinta tana fiddo littafai.
“Ezzah miyasa baki jin magana ne? Kullum idan kin ci abinci sai kin watsar kuma ki bar ni da gyara, da nace ki gyara sai ki buɗe baki ki fara yi min kuka? Wannan wane irin rayuwa ne?”
Gunguni ta fasa mata irin maganar nan ta can cikin maƙoshi ta wanda yara ke yi idan suna takarar rashin kunya. Hakan ya harzuƙa Kalsoom ta har ta ƙarasa inda take ta dangwale ta.
“Me kike faɗa? Ke marar kunya ko? Ina miki magana kina min gunguni”
Ɗan wannan abun da Kalsoom tace mata sai kawai ta ɓare baki ta fara kuka tana, ta tashi da gudu ta bar falon.
A harabar gidan ta je ta zauna tana kuka kamar wacce aka cirewa rai.
Haka ta zauna a gurin har mahaifinta ya dawo ta sanar da shi dukan da Kalsoom ta yi mata. Sam be jidaɗi ba dan babu abunda ya tsana kamar duka, komai zai iya ɗauka amman ban da a dakar masa yara, dan shi be sa musu hannu ba ba zai yarda wata ta sa musu ba, Rashida ma data haifesu baya bari ta dakesu.
“Ba ki mata komai ba zata dake ki? Kalsoom ba zata dake ki haka kawai ba”
“Wallahi ban mata komai ba, kawai tace na share falon nace ta bari na gama homework shine kawai ta mare ni”
“To ya isa yi haƙuri zan mata magana”
“Daddy yaushe Ammyn zata dawo?”
“Ba zata dawo ba”
“Miyasa?”
“Tace ta zaɓi haka”
Ya riƙa hannunta suka shiga ciki. Suna shiga falon ta fisge hannunta ta nufi ɗakinsu da gudu.
Kallo ɗaya Kalsoom tayi mata ta ɗauke ido tana masa sannu da zuwa.
“Yauwa me Ezzah tayi miki kika mareta”
Ya faɗa yana mai zama a kusa da ita.
“Mari? Ita tace maka na mareta haka tace maka?”
“Baki mare ta ba?”
“Haba Doc mi zai sa na ɗaga hannu na mareta sai kace wari na? Ni dai nasan na zungureta”
“Amman Kalsoom be kamata ace kin dake ta ba, Ezzah yarinya ce dik abunda take yi ƙurciyace, sannan rashin mahaifiyarta yana damunta dole sai kin yi haƙuri da ita, bata da uwa a yanzu sai ke”
“Amman idan ta ɗauke ni uwa mi zaisa ta min rashin kunya? Did i treated her badly ne? Miye bana mata tun mahaifiyarta na nan, sai yanzu dan daga bata nan zata fara min rashin kunya? I'm tired Hilal I'm tired ba rainon ƴaƴanka na zo yi ba, nima aure na zo, idan rainon ƴaƴanka kake so ayi maka kaje ka nemo mai raino, amman ni ba zan iya, ba kuma zan yi ba, ko da zai zamo silar mutuwar aurena ne!”
Kallonta kawai yake irin yadda take zuba masa ruwan masifa har hantanta tashi suke, gaba ɗaya ta fita hayyacinta saboda abunda be kai ya kawo ba.
But all what he thought tana cikin damuwar zubewar cikinta ne, he feel her pain, hakan yasa ya ɗaga mata ƙafa be biye mata ba, sai kaiwai ya tashi ya barta falon.
Fashewa ta yi da kuka ta cire ɗankwalinta ta jefar tana kuka.
“What is wrong with me? Miye same ni? Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ta tashi da gudu ta shige ɗakinta tana cigaba da kuka, zuciyarta cike da tsanar Hilal bayan be mata komai ba.
NAMRA POV.
Asim be yarda ta dawo ba, har sai da ya ganta asibitin, aiko ya dinga murna kamar ya ɗauke ta ya haɗiye, Mama ba laifi ta tarbe ta far'ah tana na'am-na'am kamar ba ita ba.
Namra ta jidaɗin haka, sai taga kamar saboda tayi fushi ne Asim ya tsorata yayi canja, duk sai ta ji farinciki ya baibayeta ance so hana ganin laifi, ita dai har gobe zuciyarta na son Asim, duk da da shakkun da take da shi akansa, dan ta ƙudiri aniyar naira biyar nata ba zai sake shiga hannun Asim ba, tun har ta gano nufinsa.
Ya samu sauƙi sosai, dan har likitoci suna maganar sallamarsa ganin yanzu yana taka ƙafar sai dai yayi ɗingishi, Mama ta fi kowa jindaɗin samun sauƙin nasa saboda ta matsu ta koma gida zaman asibitin dik ya isheta.
Ranar da Namra ta kwana biyu da dawo taja ƴar fulani suka je kasuwa ta siye wasu abubuwan na kitchen da na ɗaki, da kuma tufafi da hijabi, da ta dawo da yamma ne ta share ɗakin ta wanke ta zuba center carpet ɗin data siyo da taimakon yarinyar ta kira yayanta namiji ya laƙa mata labulaye sannan ta shiga da katifa, da sauran tarkace. Ta haɗa BQ ɗin ba laifi kasancewar ɗakun biyu ne sai ta mai da ɗayan kamar kitchen ɗinta, ta saka abubuwan zuba ruwa da sauran kayan aikinta ciki.
AMIRA POV.
Washe gari Ummi ta dawo ta ga Amira dan tasha alwashi ba zata bar Abuja ba sai ta yi ma Amira godiyar abunda tayi ma ɗanta.
Amira ta jidaɗin haka, ta san ko ba komai ta samu shiga zuciyar Ummi ganin yadda take tausayinta, har da zubar mata da ƙwalla, gashi jikinta ya nuna ita ɗin wata ce, tun daga kan tufafinta zuwa yadda naman jikinta ya kwanta.
Amira ta kama hannunta ta riƙe sai hawaye take tana son shige mata jiki.
“Na ji daɗi da kika zo, na ji kamar a'ce ke mahaifiyata ce”
“Ni mahaifiyarki ce mana miyasa kike magana haka, Allah ya baki lafiya”
“Amin na gode”
Ta faɗa tana kife saman gado asibitin. Abdool na tsaye hannayensa a aljihu yana kallonsu, shi dik ya gundira Ummi ta bar ɗakin, coz he don't trust Amira, kuma hankalinsa be kwanta da ita ba for no reason.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: 4»»»7»»»»»»»»»»»»»»»
“Wai Daddy yace kin ce ba zaki dawo ba”
“Yaushe yace miki haka?”
“Jiya da ina tambayarsa yaushe zaki dawo, wai yace ke kika ce ba zaki dawo ba”
“Baya son ya faɗa miki ne, saboda yanzu baya so na Kalsoom yake so, idan har kina son na dawo dole ne ki riƙa yin abunda na faɗa miki, idan kina irin haka shine sai za ya tausaya muku yace na dawo”
“Amman ita bata jin daɗin abunda nake mata”
“Ke kina jindaɗin data koreni?”
Ta girgiza kai alamar a'a.
“Idan baki yin abubuwan da nake faɗa miki ke ma wata rana sai tasa Daddy ki ya kore ki, sai ta mallake gidan daga ita sai nata ƴaƴan”
Ezzah ta.yi shiru tana tunani sai kallon ƴan makarantar su take masu kai wa da dawowa.
“Ezzah dik duniyar nan baki da kowa kamar ni, duk wacce zata so ki abaya na take, kuma ƙarya Kalsoom take tace tana son ku, tana nuna muku haka ne dan ta mallaki Daddy, yanzu kina jindaɗi zama da ita? Bata dukan ki? Lokacin da ina nan Daddy ki yana miki faɗa?”
Duk ta girgiza kai.
“Dole ne kiyi mata abunda na saki dan na samu na koma gurin Daddy ku, na yi muku alƙawari ddana koma kullum gida zan riƙa zama ba zan sake fita aiki ba”
“Da gaske?”
“Wallahi, dan haka ki cigaba da abunda kike, har abunda ban saki ba ma ki aikata indai kinsa wanda zai hassalata ne”
“Zan riƙa yi”
“I Love you”
“I Love you too”
Rashida ta rumgume ta kamar da gayya. Sannan ta ciro chocolates da Sweet Candy dake jakarta ta miƙa mata, ta kuma bata ɗari biyu na kashewa sannan ta tashi ta fita.
Daga nan Asibiti ta nufa. Yau ce rana ta farƙo da zata fara bin shawarar likita wajen ɗora kanta akan magani, dan samun tsawaita rayuwarta kamar yadda likita ya faɗa mata.
NAMRA POV.
Two months later....
A zuwa yanzu babu wata matsala da take fuskanta a gurin Asim, tun bayan da aka sallamo daga asibiti, jiki sai ƙara sauƙi yake yana mirmirjewa kamar ba shi ba.
Duk wani mugun ƙudiri dake cikin ransa, ya danne ya barwa zuciyarsa, dan yasan babu yadda zai yi da Namra a yanzu sai kallo, idan yace zai rabu da ita matsala ne a gare shi tun da baya sgi kuɗin auren wata, shi dai yanzu ba shi da wani buri sai na yayi kuɗi.
Irin yadda yake nanata maganar har tsoro abun yake ba Namra, ahi dai yayi kuɗi dai yayi kuɗi. Haka Namra zata zauna tana masa nasiha akan duniya da abunda ya ke cikinta, amman sai dai ya kalleta kawai ya nuna mata wa'azin ya ratsashi bayan a ƙasan zuciyarsa kuma mamakinta yake, wai ita zata zaunar da shi ta nuna masa illar kuɗi, bayan ga ubanta can ya tara su ita kuma da su take tinƙaho.
Sam baya ganin wahalar da take da shi, bata saba wanki ba ko a gidansu amman haka zata zauna ta wanke nata tufafin ta wanke nasa, ta kai masa ruwanka, amman kullum sai ta matsa masa yake wanke dan ganin yake kamar tana takurasa, Allah ya zuba masa ƙuiyar motsa jikinsa indai a bangaren aiki ne.
Maganganun da Namra take masa akan rayuwa da neman kuɗi da yake magana a ko yaushe sai ya ƙara riƙe ta a zuciyarsa, wai bata son sa da alheri ta fi son yayi dauwama cikin baƙin ciki da damuwa tun da ita tana da mafita.
Ga matsalar da ci masa tuwo a ƙwarya a yanzu, wacce yake ganin kamar da ganganci ne tayi masa haka dan bata son haihuwa da shi. Ita kanta tana nadamar sanar da shi da tayi robar da aka saka mata, sai dai babu yadda zatayi dole ce tasa ta faɗa masa, tun kullum sai ya tunkareta kuma jinin har yau be tsaya mata ba, daman wani lokacin haka robar yake yi mutane dan ta ji maƙonta suna firar lokacin data shiga gidan su ƴar fulani.
Ta aika tambayarta ga wani malami ya amsa mata da cewar duk jinin daya zube bana haila bane ya zama kamar jinin rashin lafiya ne dan haka ba zatayi fashin sallah ba balle azumi.
Hakan yasa robar ma sai ta fita ranta dan ita bata son abunda zai riƙa rikitar mata da addini, hakan yasa ta yanke shawawar zuwa a cire mata robar in ya so sai tasha ƴaƴan zurma, dan maƙociyarta nan ta faɗa mata indai har ta sha ƴaƴan zurma ɗaya yana matsayin shekara ɗaya ne idan kuma tasha biyu kuma yana matsayin shekara biyu ne.
Sai dai ba kowa yake yi ma aiki ba, amman ta ga wani a whatsapp wanda Khadeeja Candy take tallah shi kam idan an sha tabbas zai maka aiki, matsalar kawai ita ba a garin take ba, kuma tana buƙatar ta bincike dan ta jin yadda abun an ce mata texted and trusted ne. Ga Kuma Asim ya dame ta da maganar kullum, dan shi gani yake kamar da biyu tayi haka.
Yau wake ta dafa da shinka (rice and beans) ta saka mai da taji, daman yana cikin favorite na ta, amman Asim duk lokacin data dafa sai ya riƙa ƙin ci yana ganin kamar tana haka ne dan karta kashi kuɗi da yawa tayi musu abinci mai kyau.
Shi yanzu har ya matso jikinsa ya koma.yadda yake ya fara fita neman kuɗi, dan ya ayyana a ransa kuɗinta zai ranta ya fara sana'ar, har hango kansa yake ya zama wani Alhaji.
Kullum firar da ita kenan, yau bayan ya gama complaint ɗin baya son wake, ya ɗasa mata firar idan yayi kuɗi, ba aza a ƙara cin wake a gidansa ba.
Namra ta yi murmushi tana mamakin yadda idom Asim ya bude haka.
“Asim kenan. Idan ma zaka yi roƙon baka cewa Allah ya baka halalinka, kawai dai kai kayi kuɗi”
“Wallahi sai na yi kuɗi Namra, Wallahi Wallahi sai nayi kuɗi, kawai naji sauƙi ne”
»“Ban ce ba zaka yi kuɗi ba, Amman yana da kyau ka riƙa cewa Inshallah kuma ka riƙa roƙon halak, saboda gudun sherin zuciya, idan Allah ya rubuta zaka yi kuɗi zaka yi ko da kuwa kama kwance gida ne sai sun tararda kai, saboda an riga an rubuta zaka yi kuɗin sai dai idan kayi gajin haƙuri zaka iya samun ta hanyar da be kamata ba”
“Namra kina bani mamaki, ke yanzu da ba dan kuɗi ba iyayen ki ai ba zasu wulaƙanta ni ba”
“Wulaƙanci kamar ya?”
“Wulaƙanci ne mana, saboda an mai dani talaka wanda ba shi da amfani shiyasa aka saka miki wannan robar ba tare da sanina ba”
“Ba haka bane, kawai matsala ce ta taso kuma likitan yace dole ne nayi planning”
“To Allah ya kyauta, amman ko ma minene ai nafi kowa kusanci da ke, taya za'ayi ki yi min haka”
“Asim matsala ce fa kai yanzu kana son na samu ciki ya zo ya zube ko kuma nayi ta wahala?”
“Hmm kina dai ganin kamar ba zan iya hidama dake ba ke da abunda zaki haifa shiyasa kuka ɗauki wannan matakin”
Ta aje kofin ruwan dake hannunta
“Ba zan ɗauki halin nan naka ba Asim, babu yadda zaka riƙa cin zarafina dana iyayena, kullum mune marar mutumci a idonka, duk abunda muka maka baka gani, na sadaukar da yawa Asim, har inda be kamata na sadaukar ba na sadaukar amman baka gani”
Kamar mai jira sai kawai yayi cikinta da masifa.
“Me kika min ke da iyayenki? Me kika sadaukar min? Ran ki? Ko lafiyarki? Kullum da kin tadhi magana kin sadaukar kin sadaukar tun da na aure ki me na ƙara shi in ɓa tsiya ba? Ɗan abunda na tara dik ya ƙara na zo na kwanta a asibiti jiyan babu wani ɗan'uwanki da ya ɗauki wani abu ya ba ni, an so na mutu ban mutu ba shine yanzu zaki fara buɗe min wani babin na rayuwa, kina da kuɗi a jikin ki amman saboda baƙin ciki ba zaki fitar aci ba sai dai a mutu? To Wallahi Asim ikon Allah ne, duk wani mai son ganin bayana sai dai ni naga bayansa”
“Magana kake irin wannan zancen kamar mai magana da maƙiyansa, maitarka ta kasa ɓoyuwa har sai ta fito fili? Kuɗina sana'ah zan yi da abu na, dan ba zan zauna kullum ni ce biyar dangi a bani ba, kuma Allah be ɗora min alhakin ciyar da kai ba, ni aka ce ka ciyar ka tufatar, yanzu ka fito a siffar ka sak Asim daman dan dukiyar gidan mu ka aure ni ko, amman sai ka nuna mik baka son komai sai ni, ashe zagon ƙasa kake min ka ɗauki halin samarin zamani ka ɗorawa kan ka, masu auren jari...”
Wani irin mahaukacin mari ya kifa mata ya rufe ta da duka kamar ma dukan namiji.
Shuri yake aika mata ta ko'ina tana cigaba da dukan jikinta kamar ƴarsa.
Dukanta yayi sai da yaji ya daki iya kalaman data faɗa masa sannan ya sassauta mata ya miƙe tsaye yana ɗingishi.
“Kuma Wallahi kije aci miki wannan robar ko kuma wallahi na lahira ya fiki jindaɗi”
A fusace ya juya ya bar ɗakin. Kuka tayi har ta gode Allah sannan ta tashi zaune tana cigaba da hawaye.
Sai ynz take tabbatar da tayi kuskuren aure, ta auri mutumen da be san darajarta ba, mutumen da be san kowa ba sai kansa. Daman haka halin Asim yake abu kaɗan sai duka.
Ta share hawayenta dan itama kanta tasan ba kuka bane abunda take buƙata, sam Asim be cancanci hawayenta ba, a yanxu ta san wa take aure dole ne kuma ta shirya zama da shi. Bata da buƙatar kokawa kowa damuwarta ita ya kamata ta gyara zaman aurenta da kanta.
Ta tatsu iya tatsuwa dan haka yanzu ba zata sake bari guminta ya zuba akan Asim ba.
ASIM POV.
Ta ƙarfen dake hannunsa yana dafawa ya fito gate, sai huci yake kamar wani zaki.
Yau ji yake kamar ace ya rumtse ya bude ya gansa yayi kuɗi, ta yadda zai jidaɗin rayuwarsa. Sai yanzu yake nadamar karatunsa daya bari daman can yayi tunanin ko zai samu wani abun a gurin iyayen Namra shiyasa ya baro garin su da ita ta yadda nan zai ta cin karensa ba babbaka sai yayi ta aikata tana samu matsa kuɗi, amman yanzu ya fahimci itama maƙetaciya ce kuma bata sonsa da alheri.
Gashi yanzu ko sana'ah zai yi yasan ba zai samu kuɗi a tashi ɗaya ba, amman idan yana da karatunsa zai iya samun babban aiki.
“Mtssssss aiko karatun na yi ba aiki zan samu ba tun da nigeriyar sai da gata, su kuma waɗannan iyayen nata matsiyata ne ba aiki za su samomin ba, aiko wallahi duk wahalar da zan sha tare da ƴar su zan shata, sai na yi kuɗi tana ganin zata huta kawai na aikata gidan su.
Har ni za'ayi ma mugunta, ai ko sai na yi muku baƙin ciki dan haihuwa yanzu za a fara”
Ya ƙarasa maganar yana kallon Mardiya data doso gurin tana takawa a hankali. Tun daga kan ƙafafunta yake kallonta har zuwa fuskarta.
Shi dai kam yana son farar mace ko ba komai farar mace ko kallonta kawai kayi zata burgeka kuma zakaji kana son ta.
Tsaɓanin Namra da take black beauty, wace yake ganim a yanzu she's not his type, sai dai duk da haka ya ƙudiri aniyar sai ya kai ga jikin cos he need someone near him.
Ba zai je ya kashe kanshi da desires ba, weather blood ɗin ya tsaya mata ko be tsaya ba babu ruwansa yau zai yi yadda yake so da ita.
“Ina wuni”
Mardiya ta gaisheshi cikin ƙirsa da kisinsina. Shi kuma ya amsa mata a far'ah har kunne.
“Lafiya ƙalau Mardiya ya gida”
“Lafiya ƙalau ya jikin na ka?”
“Alhamdulillah”
“Allah ƙara sauƙi”
“Amin na gode”
Da kallo ya bita har ta ɓace masa da gani sannan ya dawo hanyyacin yana yaba kyauwon surarta a zuciyarsa.
KALSOOM POV.
Ita kanta yanzu ta rasa gane kanta balle Hilal da yanzu ya saka mata ido, dan duk ta barkace masa abu kaɗan masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba.
Da gangan zata ƙi masa girki ko kuma tasa shi gaba tayi masa kuka, bayan be mata komai ba. Tun daga lokacin ya fahimcin akwai abunda yake cikin matarsa, daman can sha'anin ɓacewar cikin nan nata ya bashi mamaki, ga kuma jinin daya ƙi tsaya mata wajen wata huɗu kenan, babu irin maganin da be bata ba amman abun be tsaya ba, tun yana ganin abun kamar wasa har ya fara tsorota da lamarin.
Ita kanta tasan yanzu wannan jinin ya wuce haila ko zubar ciki ya zama na rashin lafiya, kuma ta san hukunci mai jinin rashin lafiya.
Shi kuma jinin rashin lafiya, jini ne da yake zuba ba a lokacin al'ada ba, daga wata jijiya da ake kira da azil. Al'amarin wanda take wannan jinin yana da rikitarwa, saboda kama da jinin haila yake. Idan mace ta zanto jini yana zuba daga gareta jo yaushe, ko kuma a mafi yawan lokaci wanenen zata ɗauka jinin haila da na rashin lafiya? Domin ita mai jinin rashin lafiya hukunce mai tsarki na gareta, kuma irin wannan hukumci shine a gurin mace mai jinin planning irin wanda yake zuba idan anyi planning dan ya zama kamar jinin rashin lafiya.
*Hali na farko* Ta zanto tana da masaniyar kwanakin hailarta, kamin jinin rashin lafiya ya same ta. Misali idan tana jinin haila a kwana biyar ko takwas a farkon wata ko tsakiyarsa, watau tasan kwanakin hailarta da lokacinta. To ita wannan zata zauna gwargwadon kwanakin hailarta ta bar sallah da azumi ta bawa kanta hukunci mai haila. Idan kwanakin sun wuce sai haila sun wuce, sai tayi wanka tayi sallah ta ɗauki jinin da ya cigaba da zubar mata da zuba a matsayin jinin rashin lafiya. Dalili shine faɗin Annabi S. A. W, ga Ummu Habiba : ki zauna gwargwadon kwanakin da hailarki take tsare ki, sannan ki yi wanka ki yi sallah. Muslim ya ruwaito shi. Da kuma faɗarsa Annabi ga Fatima Bintu Abi Hubaish: Wannan jinin jijiya ne, ba haila ba ne. Idan hailarki ta zo sai ki. Bar sallah. Bukhari da Muslim suka ruwaito shi.
Idan iyakar kwanakin hailarta ya zo kamar yadda bayani ya gabata, to wajibi ne a gareta tayi wanka. Kuma wanke gabanta domin ta gusar da abinda yake zuba yayinda ta zo yin kowace salla. Kuma tayi ƙunzugu da auduga (pad) ko abu mai kama da ita wanda zai hana kwararar jinin, sannan tayi alwala daga lokacin kowace salla saboda faɗin Annabi : Ta bar salla a cikin kwanakin hailarta, sannan ta yi wanka kuma ta yi alwala ga kowace salla. Abu Dawud da Ibn Maja da tirmizi ne suka ruwaito shi.
Hakan yasa Kalsoom ta cigaba da salla da duk sauran ibadarta, sai dai har gobe halinta be canja ba a kan Hilal idan yana cikin gidan ji take babu wanda tsana a duniya sai shi. Yara kuma abu kaɗan ta dake su, tun yana haƙuri har abun ya fara isarsa dan yanzu shi da ita basa shan inuwa ɗaya, akan yaransa.
Gashi Ezzah kullum uwarta ƙara hure mata kunne take tana koya abubuwan da take ganin kamar abun ƙwarai ne, bayan ita bata san tana lalata tarbiyar ƴarta bane kawai.
Duk ranar da ba makaranta zai kwashi yaransa ya kai su gidan Hajiyarsa. Hajiya ta lura da yanayin ɗanta damuwa ta bayyana a fuskarsa ga ramar dake jikinsa, yadda ma yake yawan kawo yaran akai-akai ta san ba lau ba.
“Wai likita akwai abunda yake damun ka ne?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yana aje plate ɗin abincin da ke hannunsa.
“Wallahi Hajiya ni ban san matsalar, daga ina take ba ma, Kalsoom ce yanzu kwata-kwata na rasa ma gane kanta, indai ina gida bana da kwanciyar hankali, sai kuka zara riƙa min tana masifa”
“Me ya haɗa ku?”
“Ba abunda na haɗa mu haka kawai zata riƙa min masifa sai kuka, kin san cikinta ya ɓace”
“Ya ɓace kamar ya?”
“Jini kawai ta ga yana mata zuba, sai aka yi hoto aka ga babu cikin kwata-kwata a cikin ta, amman jinin har yau be tsaya mata ba, yau kusan wata huɗu kenan”
“Subhanallahi, me ya same ta haka ne?”
“Wallahi nima van sani ba? Na rasa gane kanta”
“Abun kamar lamarin iska shi kesa ciki ya ɓata, ko kuma sihiri”
“Sai maganar saki ta ke min, ita dai na rabu da ita na ta huta”
“Kasan me? Ka samu ƙwarya mai tsarki da za'afaran, sai a ruɓuta suratul Yasin da surar wa'ƙia da fatiha da ƙulhuwallahu ahad da ƙula'uzai da Ayatul kursiyu da kuma amanar rasulu har zuwa ƙarshe da suratul baƙara da ayar : ƙul-a-Allahu azine lakum am alallahi taftarun (10:59) to idan an rubuta sai a karya kummallo da shi idan ta sha sai ta samu dabino ajwah sai kayi mata tawada nan da Al-zaitul muraƙƙa sai ta cinye sauran kuma rubutun kuma ta shafe jikinta, da iKon Allah indai sihiri ne ko aljanu ko wane iri ne zai rabu da ita”
“Amman Hajiya irin wannan ai sai dai kisa waki ya rubuta mata a nan sai na kai mata ta sha”
“To zan nemi wanda zai rubuta mata inshallah, amman wannan ko Rashida ai zata iya ƙulle-ƙulle ganin ta ɓata zamanku”
Yayi ƴar dariya.
“Sai dai ko iska ne, amman ai Rashida bata da irin wannan halin”
“Hmmm Hilal ba a shedun mace, yanzu kasa ran tayi maka wannan abun?”
Yayi shiru yana nazarin maganar Hajiya.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: »»4»»»»»»8»»»»»»»»»
ABDOOL POV.
Ɓacin rai ne shimfiɗe a fuskarsa, idanunsa sun rine zuciyarsa har wani tafarfasa take saboda faɗan d Mai Martaba yake masa.
Har Mai Martaba yayi ya gama Abdool be ce uffan ba, dan yasan akan gaskiya yake faɗansa, kamar yadda Ummi take masa a kullum.
“Ƙanen ka Babana ƙanenka ace yayi aure har ya haihu kai ba kayi ba, kullum girma ƙara tunkararka yake amman baka ganewa, shekarun tafiya suke Babana yanzu da ace kana da mata da wannan abun zai faru da kai? Sai dai ka zauna a gida ta girka maka, ko mutuwa kayi ba mu da abunda zamu kalla mu tuna da kai sai hoton ka, ai ko mutuwa kayi ka bar mai maka addu'ah ka more, rashin auren nan naka yana damuna Babana, kuma kullum faɗa ake maka amman kamar ba'ayi”
Till now be ɗaga ido ya kalli Mai Martaba balle ta ce wani abu, shi kansa yana da buƙatar auren, sai dai matsalar bayan Namra be ga mace da ta kwanta masa ba, sannan be son ya auri mace da baya so gudun karya tauye mata wasu haƙoƙa nata, dan wanda yake so baya jin zata samu enough time nasa balle wacce baya so.
Hullar uniform ɗin dake jikinsa kawai yake taɓi yana sauke ajiyar zuciya.
“Ba na son cilasta maka auten wacce baka so, shiyasa nake ta ɗaga maka ƙafa ina baka lokaci, amman ka ƙi ka gane”
“Mai Martaba ka gafarce ni, ina nan ina ta addu'ah Allah ya bani matar da nake so”
“Allah ya baka, amman karka zarge ni da abuɓda zan maka nan gaba”
Har ya miƙe tsaye be kalli Mai Martaba ba, dan baya son Mai Martaba ya ga ɓacin ransa.
“Zan tafi, Allah ya ƙara maka lafiya”
“Yau ba za'ayi min fira ba kenan ko? Tun da nayi maka faɗa?”
Ya ɗan murmusa
“Ba haka bane, kana yawan faɗa min na kula da kai na, kuma yamma tayi i want to spend time with Ummi, dan gobe zan koma”
“Ai daman na san ita take ƙara goya maka baya kana fatali da maganar auren nan”
“Ba dan wani abu ba da sai na ce tama fika damuwa da lamarin auren nan”
“Kuma ba kayi komai a kai ba?”
“Zan yi inshallah, a ƙara min lokaci”
“Allah ya kiyaye hanya”
Ya ɗan risina kamar yadda yake masa.
“Na gode Mai Martaba”
Sannan ya juya ya nufi ƙofar fita, a bakin ƙofar ya tsaya ya saka Army shoes ɗinsa dake gurin sannan ya shiga cikin gidan sashen matan sarkin yayi musu sallama ya fito.
Kuɗin dake aljihunsa ya ciro ya miƙawa mutanen dake zageye da motarsa, sannan ya shiga motarsa boys ɗinsa suka shiga wata motar already wasu na cikin motar sake gaba sai kawai suka kama hanyar gida.
Sai da ya fara shiga part ɗinsa yayi wanka ya canja tufafi sannan ya nufo part ɗin Ummi.
Sisters ɗinsa ya samu falon tare da friends ɗin su, cikin murna suka tarbesa, sai ya gaisa da Friends ɗin su sannan ya nufi ɗakin Ummi.
Zaune ya tararda ita ƙasan carpet hannunta riƙe da qur'ane tana karatu. Kusa da ita ya zauna yana sauraren ƙira'ar nata har sai da ta kai ƙarshen suratul Maryam sannan tayi addu'ah ta shafa, ta aje qur'ane a gefe ta cire gilashin idonta ta kalli ɗanta tana murmushi.
“Soja wuta soja”
Yayi dariya yana shafa dogon hancinsa.
“Uwar soja ma soja ce”
“So ya hanya?”
“Alhamdulillah”
“Ka ci abinci”
“Eh na ci tare da Mai martaba”
“Can ka fara biyawa kenan?”
“Eh kuma na sha faɗa akan mganar aure, Mai Martaba be gajiya”
Ummi tayi murmushi irun nasu na manya tana kallon ɗan nata cike da so da ƙauna.
“Kai ma ai baka gajiya da faɗan shiyasa kaƙi kayi auren ka huta, amman Abdool bana son kana cin abincin mutanen”
“Ummi ki daina zargin komai, yanzu ba kamar da bane, suna sona sosai”
“Ba lallai bane ka iya gane haka, ai maƙiyin ɓoye baya taɓa nuna maka baya son ka, kuma dik wanda ya ƙi ni to kai ma zai iya ƙin ka you have to be very careful”
“Na kan yi bismillah idan zan ci, kin san ko minene idan ka yi bismillah ba zai taɓa samun ka ba, kuma ina addu'o'i sosai musamman da safe, kuma kin san irin addu'o'in da nake musamman laƙada ja'akum wace idan aka karanta mutum ma ba zai mutu ranar ba, saboda tsananin tsarinta, idan har zaka mutu a ranar yo Allah ba zai baka ikon karantawa ba, ga a'uzu bikkalimattillahi”
“Hakan yana da kyau, nayi tunanin ko baka samun time ɗin addu'ah ne saboda aikin ka”
“Komai nauyin aikin na na kanyi sai dai ba dika ba, amman dai bana tashi ba tare da nayi addu'o'in tsari ba”
“Allah ya ƙara tsare ka”
“Amin ya rabb”
“Ina labarin yarinyar nan an sallame ta?”
“Ni na hana su sallame ta da tuni sun sallame dan taji sauƙi sosai”
“Ni abunda na ga yafi karka bar yarinyar nan ta koma cikin ƙazamar rayuwa, ya kamata kayi wani abu a a kai”
“I try my best naga ta koma gidan su amman ta ƙi, ta tsaya kai da fata ita ba zata koma gida ba, wai ji take kamar idan ta koma mutuwa za ta yi, ni kuma ban san abunda zan mata ba”
“Why not ta zauna da mu kamin hankalinta ya kwanta sai mu mai da gida gurin iyayenta”
“Kawai yarinyar bata kwanta min bane, ta taɓa zubar da ciki, kuma kin ga ta zauna da mutane ƴan iska kala kala, kar tazo ta ɓata mata tarbiyar Sisters na”
“Ba zata ɓata ba, sai dai su su gyara mata tarbiyanta, she deserved everything Abdool dik wanda ya sadaukar da ransa dan kana ya rayu ya cancanci komai a gare ka, a yanzu bata da gurin zuwa kuma idan har muka bar ta ta koma cikin wacan rayuwar kamar ba mu mata adalci ba, :sannan ka bincika an tabbatar maka da gaske guduwa tayi daga gidansu, ai ya kamata ace kayi wani abu akai na ganin kaima ka maida mata farinciki a zuciyarta ”
“Amman Ummi har yanzu babu tabbacin abunda yasa ta gudu”
“Ai kasan ita da iyayenta ba zasu fito su faɗawa duniya dalilinta na guduwa ba, ya zaka ji idan aka ce ɗaya daga cikin ƙannen ka ne? Put yourself in my shoes zaka ji irin abunda ko wane uba ko uwa take ji”
Ya sosa kansa yana miƙewa tsaye.
“I will think about it, lemme go and pray”
Daga haka yasa kai ya fice ɗakin.
RASHIDA POV.
Kusan kullum sai ta yi waya da malamin nan ko kuma nace boka, amman labari ɗaya yake bata, cewar Hilal da Rashida basa zaman lafiya, kuma har gobe jini na nan yana mata zuba.
Sai da ita bata da tabbacin hakan tun da bata ji wani motsi daga garesu ba, dan har yanzu bata ji ya saki Kalsoom ba, kuma Ezza tana yawan faɗa mata ita bata ganin suna faɗa har sai idan ta dake ta sannan Daddy ta yayi faɗa.
Izzah bata da labarin komai da yake faruwa tun da Hilal baya faɗa da Kalsoom a gaba idonta, ko lokacin da Rashida take gidan idan zai yi mata faɗa ba yayi a gaban idon yaransa gudun abunda zai je ya dawo. Balle kuma.Kalsoom da baya biye mata dan ta fahimci bata cikin hankalin kanta duba da yadda abubuwan da take masa a.yanzu abunda be tsammaci zata masa ba, kuma baya tunanin kishi ne da sai dai ta nuna jindaɗinta akan barin gidan da Rashida tayi ta ƙara mallakarsa, sannan Hajiyarsa tana yawan tunasarda shi akan ya kawar da idonsa gareta, duk wani abun da zata yi ya riƙa sa mata ido.
Tana yawaita bibiyar shafinsa na facebook da instagram da whatsapp, wai ko zata gano idan hankalinsa ya karta kanta amman sai ta ga tsaɓanin hakan, dan har text take masa amman baya mai da mata amsa daga ƙarshe ma sai ya saka ta a blacklist.
Yau kam ta kuɗiri aniyar tura Asmee dan ta binciko mata irin zaman da suke, tun da ta san Kalsoom ta yarda da Asmee kuma zata iya bugun cikinta dan ta ji labarinta, idan ma suna zaman lafiya ko a yanayin fuskarta zata iya karantar hakan.
A gogon ɗakinta ta kalla taga 10:36Pm, ba laifi dare ya ɗan fara sai dai hakan be hana ta janyo wayarta ta kira line Asmee ba.
“Ƴar gari... Yanzu ko na ke maganar ki da Oga”
“Uhmm gulmata kuka yi kenan?”
“A'a Wallahi kawai yana yabon halin ki ne, wai duk yadda kike da haƙuri ace Hilal ya sake”
“Ke dai bari, ai sherin kishiya sai Allah, ni so ma nake kije gobe ki bincika min gidan nan, ya zamantakewar su yake”
“Zan ko miki haka, nima Wallahi ina son zuwa dan naga idon munafukar”
“Da Sassfe zaki je dan Allah lokacin da Hilal.yake gida”
“Karki samu matsala Asmee ce fa ƙawarki”
“Na gode ki gaishe da ogan na ki”
“Zai ji mu kwana lafiya”
Rashida ta kashe wayar tana kallon ƙanwarta Safiya dake tsaye jikin ƙofa riƙe da littafi.
“Shigo mana kika tsaya bakin ƙofa kina kallona”
Ta shigo tana ɗan murmushi
“Wallahi Anty ni jikina duk a mace yake”
“Saboda me mutuwa aka yi?”
“A'a, kin san mun fara zuwa asibiti yanzu...”
Ta ɗan yi shiru tana tunanin ƙarasa zancen, dan tana jin nauyin karya alƙawarin data ɗauka a asibiti na cewar ba zata faɗawa kowa wanda ta gani ba, idan ta shiga sashen masu hiv da sarin tb.
“To shine nake neman addu'ah, idan mun gama zamu fara exam”
“To Allah ya taimaka ya bada sa'ah, nima ina son ki min addu'ah Allah ya maido da hankalin mijina gare ni”
“Adda Rashida kenan, kina damuwa da abunda be kamata ki damu da shi ba, mijin daya juya miki baya meye na addu'a ya dawo gareki, bayan ya ci zalinki?”
“Ba a cikin, hayyacinsa yayi min ba, kin fi kowa sanin yadda Hilal yake so na, kawai sherin Kalsoom ne magani tayi masa, yanzu haka ma su Ezza basa jindaɗin zama da ita, so take ta kore kowa ta mallaki gidan”
“Kada Allah ya bata sa'ah, kuma wallahi indai mugun nufinta kenan sai ta ga abinta, ai karka bi mutum da sheri ka bar shi ya bika da sherin abun zai koma kansa”
“Ba zan bata damar haka ba, Safiya bata isa ta shiga gidan dana shekara ina ginawa ba a rana ɗaya ta rusa min kuma ta kore min ƴaƴa ta mallake min miji sannan na bar ta”
“Ki ƙyale ta ki bar ta da Allah, idan ma wani asirin ne tayi miki Wallahi zai karye zata dawo nadama lokacin da bata da amfani”
»“Haka ne Allah ya shige mana gaba”
“Amin dan Allah ki ma daina sa ran ki a damuwa”
“Ina nan ina addu'ah komai zai dai-daita inshallah”
“Allah yasa, sai da safe”
Safiya ta miƙe tsaye ta fice zuciyarta cike da tausayin ƴar'uwarta. Rashida kuma ta sauke ajiyar zuciya tana busar da iskar bakinta. Lallai tana ji a zuciyarta, ba a banza Hilal ya barta ba, dan tasan yadda mijinta yake son ta dan kawai ya gano tana tare da wani be isa yasa ya sake ta ba, tasan da ada ne da komai tayi ba zai rabu da ita ba.
Sai dai abunda har yau bata sani ba shine, daga lokacin da mijinki ya gano kina mu'amala da wasu a waje tun kin fita daga ransa kenan indai ya san kansa, kuma komai irin son da yake mki ba zai sake ganin darajar ki ba.
NAMRA POV.
Yau ta farka da baƙinciki da kuma tunanin mafita dan samawa kanfa ƴanci.
I zuwa yanzu ita kaɗai tasan abunda take ji a zuciyarta, idan ta soma tunani har numfashinta yake yin sama, tsabar baƙinciki da damuwa.
Dole ne taje a cire mata robar nan, dan ba zata iya da rikitarwar da jinin yake nata ba, kuma ga matsalar Asim da yanzu babu ruwansa da matsalarsa haka zai yi forcing ɗinta ya yi yadda yake so da ita.
Irin yadda yake mata Allah ya isa akan rashin cire robar da bata yi abun har mamaki yake bata, kamar ba mijinta ba, ko kuma wanda be san addini ba, abu kaɗan zai mata Allah ya isa, ga yawan kusheta da yake, shi dai kullum ya fi son ya ganta a cikin damuwa da baƙinciki.
Ba laifi yanzu dan ya ɗan fara fita, har ya koma aikinsa na ƙira da suke da Ƙanen Babansa, sai dai naira ba zai cire ya bata ba, da sunan ta siye abinci balle cefane, babu ruwanshi da matsalarta, sai dai ita tayi cefane kuma haka zai zo ya zauna ya ci dan bashi da kunya. Ita kuma har yanzu bata yi ƙarfin halin da zata iya hana shi abincinta ba.
“Idan na yi kuɗi, zan auro mace mai kyau mai tarbiya”
Sune kalamansa a kullum kuma sune kalaman da suka fi ƙona zuciyar Namra, a yanzu ne take ƙara tabbatar da son Asim be gama fita zuciyarta gaba ɗaya ba.
Ta maida hankalinta sosai gurin siye da siyarwa, na kayan aiki abinci like magi manja da sauran kayan miya, ba laifi ana siye sosai dan a unguwar ita kaɗai ce take wannan sana'ar hakan yasa ta sabo da mutane har ta buɗe islamiya tana ɗan karantar da su abubuwa game da addini da kuma ƙur'ane.
manage it please.....
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: ~4»»»»9»»»»»~
AMIRA POV.
Ta fara sabawa da Abdool cikin ƴan kwanaki ƙalilan ya shiga ranta, har matsuwa take ya zo ya ganta, dan kullum sai ya zo da safe ya duba ta, da rana ma ya kan zo idan baya da aiki, haka ma da dare sai yayi mata sallama sannan ya wuce gida.
Ta karanci abubuwa da yawa a rayuwar Abdool tun daga yanayinsa na rashin son magana da kuma shisshigi, ba kasafai yake dariya ba, ko murmushi sai idan ta kama ne yake yi.
Sai dai hakan be hana annurin fuskarsa bayyana, ya kan mata kwarjini sosai idan ta kalleshi. Sai dai har yanzu matsala ɗaya ce tayi mata tsaye a rai nasa, rashin sakewa da yake da ita, sannan idan zata shekara tana kuka ba zai iya bata haƙuri ba, sai dai ya tashi ya bata guri. Lokuta da dama ta kam ƙirƙiri kukan ne dan ya tausaya mata amman bata taɓa ganin alamun tausayinta a fuskarsa ba.
Wata ƙila baya da tausayi ne, ko kuma ba shi da kula da lamarin wasu, a yadda ta karanci rayuwarsa kamar ma yana kula ta ne by force.
Abu ɗaya zuwa biyu take ta ƙoƙarin yaƙar zuciyarta akansa, faɗuwar gaban ta take samu idan ta kalleshi, da kuma damuwar da take shiga idan ta wuni bata sashi a ido ba.
Sai dai har yanzu ta kasa, ɗan zuwan nan da yayi katsina ya kwana biyu ya dawo ji take kamar shekara biyu yayi. Tunani take idan ya rabu da ita ya zata kasance? A yanzu kam bata da gurin zuwa tun da Guy son ya mutu, kuma ta san Abdool ba zai barta ta zauna a tare da shi ba, wanda ɗaga ido ma ya kalleta yake masa wuya balle yayi mata masauki a inda yake.
Sai yanzu take nadamar abunda tayi ma Guy son, tabbas bata kyauta ba, dan me zata butulcewa wanda ya ɗauki ɗawainiyarta, dan kawai ta ceci ran wanda kallon ma mai tsada ne?
Lallai tayi kuskure kuma bata bi hanya mai ɓullewa ba. Ya kamata ta yaƙi rayuwarta dan samawa kanta yan ci, taya zata bar Abdool ya tafi haka nan ya barta ta dabon ciwo da kuma na zuciya, bayan duk akansa tayi wannan? Ashe bata cancanci fiye da haka a gareshi ba? Sam bata ga alamar karaminci a tare da shi ba, sam be san darajar ɗan'adam ba, ya kamata ace a iya zaman da tayi yayi ƙoƙarin kawar mata da damuwarta, amman sai nuna mata halin ko'in kula yake mata, sai tambayoyin banza da yake tsare ta da su wani lokacin.
Ta share hawayen idonta ta miƙe tsaye tana shafa kafaɗunta ta nufi window ɗakin tana sauraren zance da zuciyarta take mata.
‘Idan kika na bar Abdool ya kuɓuce min, lallai nayi babbar wauta kuma na yi hasara, taya zan ceci ran mutum kuma ya juya min baya? Ya kamata fa ya nemawa kai na ƴanci haka na yi ta sake har Namra ta ci galaba a kaina, tun da har na butulcewa Guy son dole ne na samu wanda zai maye min gurbinsa.
Sometimes ina abu kamar ba ni ba, zama da Guy son ya kamata ace na ko yi abubuwa da dama, amman sai kasa gazawa nake, a yanzu babu kowa a kusa da ni, ya kamata ace na zama mace. Amman sai kasawa nake, i will fight the spirit ghost of me, i will surely be my own boss, i have to answer my own name’
Ta kai hannayenta ta dafa window, dan ta ji motsin shigowar mutum kuma ta san Abdool ne dan shi kaɗai yake mata haka. Yi tayi kamar bata ji shigowarsa ba ta ƙirƙiri hawaye, ta soma magana cikin sanyin murya kalar tausayi.
“Allah ka zama gata na Allah, bana da kowa sai kai, ya Allah idan mutuwa hutu ne a gareni Allah ka karɓi rai na na huta, Allah na tuba ba zan ƙara ba”
“Ai ba haka ake tubar ma Allah ba”
Ya faɗa yana tsaye jikin ƙofa sanye da ƙananan tufafi, sai faman danna waya yake kamar ba shine yayi maganar ba.
Juyowa tayi ta sauri ta kalleshi like bata ma san yana gurin ba. Be kalleta ba, amman hakan be hana ta ganin ƙwajininsa ba saboda yadda tufafin suka karɓi jikinsa suka masa kyau sosai kamar daman can dansa kawai aka yi tufafin.
Lumshe ido ta yi tana sauraren bugun zuciyarta, hancinta na shaƙar ƙamshin turarensa daya game ɗaki, hawaye ne suka silalo mata.
Yadda zuciyarta take amsa irin kiran da Abdool yake mata ya tabbatar mata da shine mutumen da take mafarki, shine burinta a duniya bata taɓa ɗora idonta akan wani namiji taji abunda take ji akan Abdool ba, ita kwata-ƙwata a rayuwartaa bata taɓa mutumen da take so ba sai Abdool, duk wanda zata so sai dai ta soshi dan kuɗinsa ko kuma da wani abun na dabam.
Amman tana jin Abdool ko bashi da komai zata iya zama da shi, ballantana ma ya haɗa komai da ake so ga namiji, a rayuwarta bata taɓa ganin kyakkyawan mutum kamar Abdool ba, sam be yi kama da ƴan nigeria ba. Ga tarin dukiya da kowa wacce mace take so a gurin Namiji, ga shi kuma ɗan Sarki wata rana zai iya zama sarkin gaba ɗaya.
“Da ace hawaye za su miki magani da sun miki tuni, kuma tun lokacin da kika saka ƙafarki kika bar gidan ku ya kamata ace kin yi kuka kin dawo sai yanzu? Lokacin da nadamar ki bata da amfani, do you know what? I don't believe in fiction, idan har da gaske kin yi nadama ya kamata a ce yanzu kin kama hanyar gidan iyayenki”
Yayi mata maganar ne from the bottom of his heart, like he's seriously saying what is inside him, daman can shi ba mutum ne mai tausayin mace ba, indai zaki shekara kina kuka Abdool kam ko a jikinsa, wata ƙila dan ba shi da lokacin matan ne, ko kuma dan har yanzu idanuwansa basu ga zubar hawayen wacce zuciya take muradi ba. Sannan shi sam baya ganin tausayin ko kuma mutucin yarinyar da ta bar gaban iyayenta, da ma ace korarta suka yi ba ita ta gudu ba.
Babu yadda Amira za ta yi da shi duk da kalamansa sun taɓa zuciyarta, ta daɗe da karantar be iya lafazi ba, kuma babu ruwansa da tauna magana idan zai faɗa.
Sai dai hakan be sa taji haushinsa ba ko kuma ta ji ta tsane shi, sai kusanci da shi take so, dan ta koya masa yadda zai zauna da ita.
“Amman idan na koma da wane ido zan kallesu?me zan ce musu? Ya kake tunanin duniya zata kalle ni?”
“Tun kamin ki baro gidan ku ya kamata ki yi ma kan ki wannan tambayar, idan kika gudu me zaki ce musu? Da wane ido zaki kallesu? Ya kuma duniya zata kalle ki? There's no point of crying dan ke kika sai da mutunci da hannu ki”
Wani irin kallo ta watsa masa da jajayen idanuwanta, sai dai kwarjininsa be barta ta masa kallon daƙiƙa biyar ba ta kau da idon, cikin kakkausan lafazi ta ce .
“Amman mi yasa baka bar ni na mutu ba? So that na huta da rayuwar gaba ɗaya?”
Ya gyara tsayuwarsa ya ɗaga daga jikin ƙofar da yake tsaye yana sa hannayensa aljihu.
“I'm sorry I'm not harassing you I'm just telling the truth”
Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalleta.
“Park your things, Doc zai baki sallama, around 10am driver zai kai ki gida”
Be tsaya jiran abunda zata ce ba yasa kai ya fice. Rasss! Rasss! Rasss! Gabanya ya yanke ya faɗi.
“Wane gida? Gidan su ko gidan mu? Ko kuma wani gidan na dabam?”
Ta tambayi kanta, dik sanyin ɗaki be hana gumi zubo mata ba. Babu inda ya fi tsaya mata a rai a kamar gidan su. Wayyo Allah ji take kamar mutuwa za tayi idan har aka maida ita gidan su, ita kanta tana son zuwa gidan amman bata iya iyawa, bata san dalili ba.
Ta kasa sukuni sai safa da marwa take har Doc ya shigo ɗakin, bata ga alamun rahama a fuskarsa ba balle ta tambaye ko yasan inda Abdool zai kai ta, kai ba zata iya tambayarsa ba kar Abdool ya zargi wani abu.
Sai kawai taja bakinta tayi shiru, sai dai tasha alwashin indai gidansu ne ba zata taɓa zuwa ba sai dai komai zai faru ya faru.
Sai da likitan yayi mata binciken ƙwa-ƙwaf sannan ya rubuta takardar sallama ya miƙa mata, ya fice. Kamar yadda Abdool yace 10 na bugawa sai ga wani yazo cikin uniform ɗin soja yace mata ta fito suje. Nan ma sai da gabanta ya faɗi.
“Ina... za...mu....je?”
“Katsina yace a kai ki, gidan Mahaifiyarsa”
Ta lumshe ido na wasu ƴan daƙiƙu, wani irin daɗi ya ziyarci zuciyarta har ta samu maida yawun daya tsaya mata a maƙoshi.
Bata buƙatar ɗaukar komai, daman can duk kayan da tayi amfani da su shine ya kawo mata, dan ita ko waya bata da a hannunta balle wani kayan kuma. Farincikin dake zuciyarta ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a fuskarta.
Ko da ta fito Abdool na tsaye kusa da motar, da alama ita yake jira, sai dai kwata-kwata hankalinsa baya gurinta yana wani wajen dabam.
Ɗaya daga cikin boys ɗin sa ne ya buɗe mata mota ta shiga, idonta na kan Abdool.
Yayi kusan minti biyar yana magana da mutanen biyu sannan ya suka shiga motar da take sai kuma wata mota dake gabansu cike da sojoji suka kama. Shi kuma ya juya ya koma cikin.
Juyawa tayi ta cikin motar tana kallonsa. Tana ayyanawa kanta zama abokiyar rayuwarsa, dan wannan karamcin kawai da yayi mata ya isa yasa tayi sha'awar hakan. Mutum me daraja da ƙima kamar wannan? What if ta zama matarsa?
KALSOOM POV.
Tun daga lokacin data fara shan rubutun da Hajiya tasa aka mata, sai ta fara jin sauyi a jikinta, sai mafarkai take wasu ma har bata san kansu ba.
Natsuwar da take ji a yanzu, yana kan tunatar da ita rayuwar rikicin da ta yi a ƴan watanin nan, sai yanzu take mamakin kanta duk wacan abun da ta yi sai ya zama matar kamar mafarki.
Lallai a yanzu ta tabbatar da ta yi wasa da addu'ah, dan bata iya addu'ah safe balle kuma ta yamma da take gani kamar ba komai ba ce. Sai dai har yanzu bata jin ƙarfin yin addu'ah kuma jinin be ɗauke mata ba, amman dai ta dawo normal kamar yadda take, ba kamar baya ba da take jin abu na mata yawo cikin kai kamar tsutsa.
Da wuri ta tashi ta shirya musu abun karyawa, sannan ta tashi yaran duka tayi musu wanka da kanta, Izzah ce kawai bata bari anyi mata ba, sai wani cika take tana batsewa kamar wata babbar mace, ada tana yi a dole dan Rashida na sa, amman a yanzu kan na gaske take dan har cikin zuciyarta take jin tsanar Kalsoom bayan kuma bata mata komai ba, sai dai laifinta da take gani na kore musu uwa da ta yi, sannan tana ganim yadda komai ta yi musu Daddy su ba ya magana.
Sai da Kalsoom ta shirya su tsab sannan ya tura su gurin motar Daddy su ta shiga ɗan ta tashi mijinta.
A bakin ƙofar ɗakinsa ta tsaya ta buɗe maɓallin rigarta sannan ta kunna kai cikin ɗakin. Hannunta tasa cikin gashin kansa tana wasa da shi, amman be motsa ba, badan kuma be farka ba, sai dan daɗin da yake ji akan abunda take masa. Ganin be farka ba yasa ta kwantowa jikinsa ta zira halshenta cikin kunnensa. Still be motsa ba amman fuskarsa da murmushi alamar idonsa biyu kenan.
Hannu tasa ta matse masa hancin iya ƙarfinta, sai ya tashi ba shiri yana kallonta.
“K.e...”
Maganarsa ta maƙale lokacin da yayi arba da rigar bachinta dake buɗe. Rabon da ta masa irin haka har ya manta, Kullum sai dai ya haɗe mata yawu, yau ma yasan haka ne tun da jinin har yanzu be tsaya mata ba. Hannu ya kai ya laƙamo wuyanta.
“Let us enjoy ourselves...”
“No way, yara suna waje suna jiran ka”
Ya dafe kansa.
“Ya Subhanallah, gaskiya I'm tired of driving them to school”
Ta wara ido
“Then teach me how to drive!”
“No, ba zan bari ki yi driving ba, wani zai ganemin wannan kyakkyawar fuskar ba, sai dai na nemo direbe, idan kin san inda zamunsamu direba mai natsuwa ki nemo mana”
Ya yaye bedsheet ɗin dake samansa yaja kumatunta, ya sauka saman gadon ya shiga bathroom. Bakinsa ya wanke da fuskarsa sannan ya fito. Tsaye ya same ta jikin bathroom ɗin tana jiransa.
Ya ɗan risina kaɗan yayi mata kiss a baki.
“My Happiness”
Ta moɗe bakin tana hararsa irin na ma'auratan nan masu cike da shauƙin so.
“Ni kike harara?”
Ya kama kunnenta
“Ouuuch Doc it hurt”
Yana janye hannunsa ita tayi masa yadda yayi mata, ta fito falo da gudu shima ya biyota yana murmushi.
Ganin Asmee yasa dik suka tsaya cak, musamman ita dake ƙoƙarin gyara rigarta.
Be ce da ita komai ba, har sai da ita tabfara gaishe shi sannan ya amsa ya nufi ƙofar fita.
Kalsoom kuma ta koma ta ɗauki hijab tasa sannan ta fito falon cike da mamakin sammakon da Asmee ta yi musu haka kamar mai biyar bashi.
Ita kanta taji kunyar kanta, ga kuma baƙinciki ganin da tayi suna cikin walwala, dan tana taya ƙawarta kishi ne.
“Na doko muku sammako, kuna sha'aninku”
Kalsoom ta yi dariya.
“A'a nace dai Allah yasa ba bashin ki muka ci ba”
“A'a wallahi an kwana biyu ban zo ba shine nace bari na leƙo ki ban sirrin da kika bawa mijin ki ya kori Rashida”
Kalsoom ta rufe baki
“A'a sirri kuma? Ai duk wanda kika ga ta bar gidan mijinta inda akan rashin ladabi da biyayya ne to ita ce ta fitar da kan ta”
“Hmmm ba son ba mu sirrin dai ko, kin ga nima daman yara na kai scul shine nace bari na leƙo na gan ki”
“Aiko kin kyauta, an kwana biyu a a gaisa ba”
“To ai ƙara ni ke ba ko zuwa kike ba”
“Ba ya bari ne, cewa yake baya son ina yawan fita”
“Aikam baya son ki yi nisa da shi, kin ga bari na tashi na wuce sai kin zo”
Har gurin motarsa Kalsoom ta raka ta tana bata haƙurin rashin zuwa da ba ta yi ba, da kuma cewar zata zo idan Hilal ya barta.
ASIM POV.
Ba laifi yau kan yayi wanka ya shirya kansa, ko dan yana jumma'ah ne oho, da wanka ma be dame shi sai dai yayi kanta karya ya fita idan fita ta kama shi.
Bayan sun sauko daga sallah jumma'ah ya nufi gurin aikinsa yana mai jin haushin aikin nasa ace kullum sai ya yi zuga sannan ya samu ƴan kuɗin kashewa shi wannan aikin dik ya takura masa, sai jan tsaki yake yana maganganu shi kaɗai.
Tun daga nesa yake kallon wata makekiyar mota data faka gefen gurin da suke aiki, yana ayyanata a cikin jerin motocin da zai siya idan yayi kuɗi, dan kyawon motar ya ɗauki hankalinsa sosai.
Yana buɗe shagon da suke aikin, mai motar ta zoƙe gilashin motarta tana masa sallama.
“Assalamu alaikum samari”
‘Tab ashe ma mace ce’
Ya faɗa a ransa, a fili kuma sai ya amsa mata baki har kunne.
“Wa'alaikissalam Hajiya ina wuni?”
“Lafiya ƙalau, dan Allah masu aikin nan gurin nake nema za a gyara min gate ɗina ne”
Ta faɗa cikin yauƙi da rangwaɗa kamar ba babbar mace ba.
“Mu ne ai muke aikin Hajiya, ina gate ɗin na ki yake?”
“Kai ...?!”
Ta faɗa tana nunasa da hannunta, mamaki ne ya isheta, yanzu tsalelen saurayi kamar wannan ace aikin ƙira yake, dubi ko shigarsa fa.
“Okay ga kt na idan kun tashi aikin sai kuje gida ku yi min, gate ɗin be ɓalle bane duka rabi ne za'a gyara min”
Ta miƙa nasa katin. Yasa hannu biyu ya karɓa cikin girmamawa kamar wata uwarsa.
“To Hajiya da zarar abokan aikina sun iso zamu je muyi aikin, sai dai baki bamu time ba”
“Ga number waya na nan a jiki kamin ku zo sai ku kira ni”
“To Hajiya za mu zo inshallah”
Ya miƙa masa 5k
“Ga wannan asha ruwa”
Yayi taku tare da nuna kamar ba zai karɓa ba.
“A'a Hajiya ki bar shi”
“Bana mai da kuɗi idan ya fito jakana, so ka karɓa kawai idan ma watsarwa za kayi sai ka watsar”
Yasa hannu ya karɓa yana mata godiya. Ita kuma ta tashi motarta ta kama hanya. Sai da ta wuce ya kalli jikinsa.
“Ita kan ta ta ga ban yi mata kama da talaka ba, wallahi ni babban mutum ne”
Ya juya ya cigaba da buɗe shagon farinciki fal a ransa.
RASHIDA POV.
Ta kasa zaune ta kasa tsaye tun lokacin da Asmee ta labarta mata irin rayuwar jindaɗin da Kalsoom take da Hilal. Kenan ita sun manta da duniyarta? Hilal ya manta labarinta?
“Ina ba za'a shafe ni a tarihim rayuwarsa, ba zai rayu da wata ba sai ni, wata bata isa ta mallake min miji ba. Amman malamin nan ko dai yaudara yake ne? Dan me zai ce min magani yayi alhalin be yi ba”
Tayi shiru tana nazari, wata ƙila ita ma Kalsoom tana shige-shige shiyasa ta shafe ta a zuciyar Hilal gaba ɗaya. Daman idan kana yin abu gani kake kowa ma haka yake.
Wayarta ta janyo ta kira lamanin dan bata jin zuwa can inda yake a yau tun da ko aikin dake gabanta bata gama ba ma, balle ta yi tunanin fita, kuma tasan ko ta fita kamin taje ta dawo dare yayi sosai.
Kiran farko be ɗauka ba, haka na biyu zuwa na uku, amman bata sarara masa ba, har sai da ta jera masa kira kusan 10+ sai da yayi picking sannan hankalinta ya kwanta.
Sama-sama ta gaisa ta shi sai ta koro masa da bayaninsa
“Ina zuwa bari na binciki ƙasa”
Jimmm yayo shiru na ɗan lokaci sannan ya yi gyaran murya yace
“Lallai wannan matar ta sha gaban ki, ta fiki shiga bokaye, shiyasa wannan aikin be yi wani dogon tasiri a gareta ba”
“Kana nufin aikin be kamata ba?”
“Ya kamata amman yana ƙoƙarin fita jikinta”
“Amman idan har ya kamata ai dole Hilal.zai damu, dan bashi da wata mata sai ita kuma har yanzu ban ji ance sun samu saɓani ba”
“Amman ƙasa ta nuna mana an samu tsaɓani, sai dai idan kece baki sani ba”
“Yanzu malam miye abun yi?”
“Abu ɗaya ya kamata daman na faɗa miki, idan wannan be yi ba sai na biyu zuwa na uku, dole ne mu haukatata idan kuma be yi ba sai mu yi mata halbin kasko”
Ta rufe baki. Rashin imaninta be kai can ba.
“Malam babu wata hanyar ne?”
“Gaskiya wannan ce kawai mafita indai kina son mijin ki, idan ta bar gida sai ki samo sperm mu hada miki wanda Mijinki zai maida ke gidan sa dan dole”
“Zan yi tunani a kai”
“To yayi kyau”
Ta aje wayar tana busar da iskar bakinta.