Gaba ɗaya jikinsa yayi nauyi ji yake kamar idan ya motsa jikinsa zai rabu biyu, idonsa kawai yake iya zagaye ɗakin da su. Hakan ya bashi damar ganin mutanen da ke ciki a ɗakin ciki har da Abbah.
“Sannu Uzair, Sannu Allah ya baka lafiya”
Shine abunda kowa yake faɗa, sai dai shi abunda be gane ba, miya ke damunsa! Abunda zai iya tunawa kawai yaji abu ya tsikare shi sai ya faɗi, daga nan be iya tuna abunda ya faru.
Be iya amsa musu da komai ba in banda ido da yake binsu da su da kallo, har suka masa sannu suka fice cike da tausayawa. Abbah ne ya zauna kusa da shi sannan Mahaifiyarsa.
“Uzair ka ɗauki abunda ya faru da kai matsayin ƙaddara komai yana zuwa ne daga abunda Allah ya rubuta maka, kuma haƙuri shi ne zai kai ka ga har kaga ka ci riba ka samu a nan ka samu a acan”
“Wai mi yake faruwa da ni ne?”
Sai a lokacin ya samu damar tambaya.
“Uzair ka haɗu da matsala ne a ƙashinka na baya da kuma ƙashinka na ƙafarka, you wouldn't be able to walk again”
“Taya taya za a ce mun haka bayan ba haɗri na yi ba, ba wani ciwo na ji ba haka nan kawai za a ce mun na samu matsala”
“Nima abunda ya ba ni mamaki kenan, za a fitar da kai waje a duba lafiyarka”
“Abbah mi yake faruwa da ni ne?”
“Muma ba mu sani ba, likitan da ya duba ka ya tambaye ni wai ko ka taɓa haɗarin mota nace masa aa, ko ka taɓa yi baka faɗa ba?”
Hawaye suka fara masa zuba.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Wannan wane irin bala'i ne? Miya faru da ni ne haka, Hajiya ko dai mafarki na ke yi? Allah kasa na farka Allah wayyo ni Allah na”
Haka ƴa ɗinga maganganu Abbah sai kallonsa yake cike da tausayawa, suna haka sai ga wasu friends nasa sun shigo duba shi ciki har da Dr Tahir, da wasu abokanin sha-shancinsu na Abuja. Abbah suka fara tambaya ya mai jiki ya amsa musu da sauƙi sannan suka gaishe da Hajiya dake ta sharar hawaye, suka matsa kusa da Uzair suka tsaya suna masa ya jiki.
Amsa musu kawai yake amman kana ganinsa kasan ya rikice, ba fita hanyyacinsa yayi ba, amman wannan ƙaddarar da ta faɗo masa ya gaza yarda da ita, ta ya zai zama haka mutumen da ke tafiya lafiyarsa ƙalau shi ba faɗowa yayi ba shi ba haɗari ba ace ya haɗu da wannan matsalar, ta ya haka zai faru?
Sun aje masa kuɗi mai yawa ban cin siyayyar da suka masa, Abbah na yayi musu godiya, suka kama hanya suna Allah ya sauwaƙe, sai kawai Uzair ya ƙwalawa Tahir kira, cikin sauri ya juyo ya nufo inda yake su kuma sauran abokan suka fice.
“Ina son mu yi magana da kai Abbah dan Allah ku ɗan ba mu guri”
Daga Hajiya har Abbah tashi suka yi suka fita, sai Tahir ya zauna a kujerar da Abbah ya tashi yana fuskantar Uzair ya ce.
“Na je gida na samu baka nan, matar ka ce kawai, naje na saboda na ta buga wayarka ban samu ba, kuma naje guest house ɗin ka baka nan, babu abunda matarka bata faɗa min ba, har ɗan wuta ta kira ni, daman ta san kana wannan harkar ne?”
“Shekaran jiya ta gano, lokacin da na Amira ta aiko min da saƙo, ni zargin nake ma ko ita ce ta yi min wannan asirin na koma haka ne? Da wannan daga gani lamarin iska ne aljanu ne”
“Ko kuma Amira ba saboda ta dawo na samu labarin gurin Yayanta”
“Lallai zata iya min asiri, yarinyar nan muguwace”
“Zata maka ko kuma zai dawo kan ka idan na jikinta ya kare? Kasan fa bokan nan yace maka idan be kama Namra ba, zai dawo gun ka ne, sai gashi ya kama Amira yanzu kuma Amira ta dawo ina tunanin kai zai dawoma”
“Dan Allah Tahir kaje gurin bokan nan ka faɗa nasa halin da muke ciki, idan ma wani ne yayi min ya san yadda zai yi ya kare shi, idan kuma wannan aikin ne ya kare shi dan Allah Tahir”
Tahir ya dafa shi.
“Zanje karka samu damuwa zan je har can na masa magana duk yadda aka yi zuwa yamma zan dawo na faɗa maka”
“Tahir ba sai yamma ba, kaje yanzu baka ganin halin da nake ciki...?”
Ya ƙarasa cikin kuka mai ban tausayi.
“Okay zanje yanzu Allah ya baka lafiya”
“Na gode”
Ya faɗa hawaye na zuba a idonsa. Jikin sanyin jiki Tahir ya fice yana mamakin lamarin Uzair.
ASIM POV.
Yayi rama sosai a ƴan kwanakin nan da aka yi na amsar gaisuwa, Ranar da aka kwana ɗaya da rasuwar Ƴan gidansu Mardiya suka zo har da Mardiyar gurin gaisuwa, a nan ne yake nunawa wasu ita yana cewar ita ce matar da yake son aure.
Bayan an yi addu'ah uku ya ɗaure ya ƙara kwana biyu saboda masu zuwa ƙara masa gaisuwa. A ranar ne Mama Inno ta raba yaran ta ɗauki Hajara da ƙanenta biyu wasu daga ɓangaren mahaifinsu suka raba sauran ƴaƴan, abun gwanin tausayi, ranar Asim ya ci kuka kamar zai haɗiye zuciya ya mutu dan baƙin ciki, ashe Mama bata da rabon ta shiga gidan da yake da niyar sai mata, be taɓa baƙin cikin haɗuwa da Hajiya Sadiya ba sai yau, ji yayi kamar ace tana kusa da shi ya kamata yayi mata gunduwa-gunduwa, gashi ita kuma sai damunsa take da kira, yana ce mata bashi da lafiya.
Be yarda ya labartawa Nably abunda ya faru ba, amman yana faɗa mata bashi da lafiya kuma tace zata zo ganinsa ya hana, ita kuma duk hankalinta ya tashi hakan ya hanata komawa Abuja, dan ya faɗa mata ranar da zai dawo.
Ranar da bar sokoto sai da yayi kamar zai kashe kansa, gudu ya riƙayi da motar yana kuka kamar zai tashi sama. Da wuri ya isa Katsina saboda ya tashi tun asuba ne, ɗan kawai kar Hajiya ta gane halin da yake ciki ne yasa ya sauka nasarawa, dan yin wanka ya shirya ya canja tufafi. Daga wankan har shirin be ɗauke shi minti talatin ba, yana gamawa ya fito ya nufi gurin da motarsa take. Juyowa ya yi yana kallon gidan.
Be taɓa jin yayi missing ɗin Namra ba sai yau, haka kawai yau da ya tuna ta sai ya ji babu daɗi, daya tuna mamarsa sai Namra ta faɗo masa a rai, jikin rashin daɗin rai ya nufi gidan Hajiya Sadiya.
Sai da ya kama hanyar gidan sannan ya kira ya faɗa mata gashi nan ya shigo katsina har ma ya iso gidan.
“Okay okay galni nan zuwa”
Ko minti goma sha biyar ba'ayi ba, sai gata ta iso. Yayita ƙoƙarin danne damuwarsa ya nuna mata mara rashin lafiya ne kawai matsalarsa, bayan sun zauna a falo yake labarta masa yadda rashin lafiyar ta fara da fever kwanansa biyu asibiti.
“Gaskiya ka ji jiki sosai, ka rame Allah ya ƙara lafiya”
Da Amin ya amsa yana mata wani irin kallo wanda shi kaɗai yasan Manufarsa da kuma abinda yake ji a ransa a tare da shi. Ta shi tayi ta shiga ɗaki dan ɗauko masa apple ɗin, shi kuma ya fidɗo wayarsa ya aikawa Nably saƙo.
_Ki same ni a Dahir Exclusive Restaurant, yanzu ina gurin_
In few minutes ta masa reply.
_Okay on my way_
Ya aika mata da saƙon ne a yanzu dan ya samu ta fita gidan kamin Hajiya ta san wani abu kai, dan yasan ba zata bari ta fita ba.
Ta daɗe a ɗakin sannan ta fito riƙe da farin ƙyale da kuma jika ƙarama mai kamar hand bag, jakar ta fara jefa masa.
“Miliyan biyar ne a ciki, dan Allah Asim ka tabbatar ba a samu matsala irin waccan karon ba, ka ɗauki abun nan da muhimmanci sosai”
“Ba za a samu matsala ba wannan karon na miki alƙawari”
Ya faɗa kamar da gaske. Sannan ya miƙa mata hannu, ta bashi apple ɗin ya ɗauki jakar ya fice zuciyarsa har mazari take ya isa gurin da yake zaton Nably ta isa. Yana shiga mota tana kiransa tace masa gata nan gakin gate.
“Gani nan zuwa yanzu”
Ya kashe wayar, a hanya ya tsaya ya siye wani Apple green, sannan ya ƙarasa restaurant ɗin, yana fakin motarsa ya hangota tsaye jikin wata mota da yake zaton ta tace. Tana hangoshi ta ƙaraso kusa da shi idonta tab da ƙwalla, ji tayi kamar ta rumgume shi dan har ga Allah ta yi missing ɗinsa kuma tana son Asim sosai.
“Ya jikinka?”
“Alhamdullah”
Tare suka shiga ciki suka kama tebur, sai yasa aka kawo musu plate da ƴar ƙaramar wuƙa sai fork. Apple ɗin ya fiɗo ya za a mata ɗaya ya ɗauki ɗayan mai green.
“Wannan ita ce tsaraba ta zuciyata na baki ita har abada, wannan kuma ki ɗauke ta a matsayin zuciyarki ce Asim zai cinye”
Dariya ta yi mai cike da shauƙi da kuma so da ƙauna.
“Ai ka daɗe da cinye zuciyata, har ma da ganganjikina gaba ɗaya”
Ya kalli wayarta yana murmushi.
“Ki kashe wayarki kar wani ya dame mu da kira”
Ba musu ta kashe wayar, shi kuma tsoron yake kar Hajiya ta kirata.
“Bana son ki raga komai daga zuciyata. I love you”
“I love you too”
Ta faɗa sannan ta fara hanya apple ɗin ta tasoma ci kamar yadda shi ma ya fara cin nasa, sai fira yake mata kamar gaske ita kuma sai faman murmushi tana faɗa masa irin yadda ta yi missing ɗinsa.
Sai da suka gama cin apple ɗin sannan ya haɗa ma wayarsa alarm ɗin ƙarya ta yadda zai yi kamar an kira shi.
“Ko na miki oder abinci...?”
“A'a na ƙoshi wannan zuciyar taka ba zata bar ni na ci komai ba”
Ya fiddo wayarsa dake saman cinyarsa, yana faɗin.
“Kai Ogaba na kirana”
Yayi picking cikin ladabi kamar gaske.
“Okay to gani zuwa”
Ya sauke wayar tare da miƙewa tsaye.
“Am so sorry Dear Wallahi ana nema Urgent, amman idan kin min izinin tafiya”
“Ba komai daman ni dai burina na ganka, kuma na ganka, take care of yourself”
“I will my love, ke ma ki kula min da kan ki, bari ma saukeki gida ko?”
“No da mota na na zo”
Sai da yaje ya biya kuɗi sannan suka jero suka fito tare, har gurin motarta ya rakata ta kama hannunta ya riƙa ya ɗan murza, yana mai jin tausayinta a ransa, sai dai kuma idan ta tuna Mama sai yaji babu wani tausayi a zuciyarsa. Sai da ta kama hanya sannan ya nufi motarsa ya shiga.
SORRY MY FAN'S🙏
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *84*
*Shafin na ku ne ƴan ZAGON ƘASA CONVERSATION I HEART YOU ALL*
Wani irin taku Abdallah yake mai ɗaukar hankali da burge duk wata mace mai kallonsa. Ko da wasa be kalli gurin da Lamido yake ba, yayi kamar ma be san da shi a gurin ba.
“Surprise...”
Namra ta faɗa tana tare hawayen da ke ƙoƙarin zubo mata. Ɗaya daga cikin murmushinsa mai tsadar nan ya ɗauka ya miƙa mata, yana kallonta cike da shauƙi dan ta masa kyau sosai.
“Surprise is better than disappointed, haka naji turawa na faɗa, faɗa min wanda ya saka idon nan nawa kumbura, na hukuntasa”
Ya faɗa dai-dai lokacin da ya ɗoro ƙafarsa saman matattakar balcony ɗin da suke tsaye. Kallon mamaki na musamman Namra ta yi masa.
“Idon ka ko nawa?”
“Idon ki ai nawa ne”
Ya bata amsa kai tsaye, and yana acting like akwai wani abu a tsakaninsu. Saurin kawar da maganar tare da cewa.
“Meet my Brother. Lamido meet Abdallah”
Lamido ya danne abunda ke zuciyarsa, na kalaman da ya ji Abdallah yayi a yanzu, ya miƙa masa hannu.
“Am Aliyu Adam Lamido”
Wani kallo Abdallah ya watsa masa irin like sai a yanzu ma ya lura da shi, sai kuma ya tsaya kallon hannun kamar mai karantar abu a jikin hannun. Sai kawai ya zuba hannayensa duka biyu a aljihunsa yana ɗaga masa.
“Nice to meet you Lamido”
Ɗan murmushin ƙarfin hali Lamido yayi ya janye hannunsa, abunda be yi ma Namra daɗi ba.
“Baka ga ne shi ba ne? Lamido ne fa wanda...”
“Na gane shi *ABNAM* let talk something important”
New name ɗin da Abdool ya bata ya bata mamaki yana abu kamar su ɗin daman can masoyana, a ɗayan ɓangaren kuma bata jidaɗin kalmarsa ta ƙarshe da ya furta akan Lamido ba. Sai kawai ta kalli Lamido ta ce
“Zan kawo maka keys ɗin kaje ka duba”
Kai kawai ya iya ɗaga mata, fuskarsa na nuna rashin jindaɗin da ke zuciyarsa. Saukowa ta yi saman balcony ɗin ita da Abdool suka nufi ɓangare Abbah gurin da yake sauke baƙinsa.
“Faɗa abunda yasa ki kuka mana Abnan”
“Abun farinciki ne da tsoro da mamaki a lokaci ɗaya”
“Kamar...”
Ajiyar zuciyarta ta sauke ta kai hannu ta tura ƙofar falon.
“Bismillah”
“Thank you”
Ya faɗa sannan ya saka ƙafafunsa cikin falon, sai da ya shiga sannan ita ta shiga ta maida ƙofar ta rufe, sai ta nufi wata ƙofar da zata sadata da part Anty Amarya.
Bata samu kowa a falon Anty ba, sai kawai ta nufi ɗakinta dan labarta mata zuwan Abdallah nan ma sai ta samu bata nan, ɗakin Aisha ta shiga.
“Ke Anty ta shigo nan?”
Ko kallonta Aisha bata yi hankalinta yana kan computer ta, ta kaɗa mata biro alamar no. Namra ta janyo ƙofar ɗakin, ta nufi freezer tana ta tunanin abunda zata haɗa masa, ya zo mata a bazata, bata shirya masa komai ba, Lamido ma bata masa komai ba, su biyu ɗin sun zame mata ƴan uwa babu na wulaƙantawa a cikinsu. Hannu tasa ta dafe kanta kamin ta kai hannu ta buɗe firiza ta ɗauko fruits ta haɗa masa fruit salad, sannan ta haɗa tea da coffee ko wane one cup sai kuma ta ɗauki ƙaton ture ta ɗora kayan sama. Wani tunani ya zo mata na ta canja tufafin da ke jikinta, kar kuma ya ɗauka dan ta ganshi ta canja kaya he may think otherwise. Kai ta girgiza sai kawai ta ɗauki turen ta nufi part ɗin Abbah.
Zaune ta same shi ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana kallon tv, sam ta manta ma bata kunna masa tv ba. Ta dire turen gabansa tana faɗin.
“Na manta ban kunna maka kallon ba”
“Ai na kunna ni ba baƙo ba ne”
Yayi maganar cikin wata kalar murya.
“Ka zo unexpected, ba a shirya maka komai ba”
Ta faɗa tana ɗora fruit salad ɗin da Drink a saman wani ƙaramin tebur da ta janyo ta aje gabansa.
“Tea or coffee?”
Ya daɗe yana kallon gashin kanta da ya buɗe kamar ba zai ce komai ba.
“Da rana”
“Ban san abunda zan kawo maka ba ne... Wai ka ɗan ci kamin na girka maka abinci”
Ta faɗa kamar wacce ta ji kunya.
“Ban zo dan ki girka min komai ba, i just come to see you, kuma na gan ki hankalina ya kwanta”
Ya koma saman kujera ta zauna tana murmushi. Ya sauko da ƙafafunsa ya ɗauki fruit salad ɗin ya fara sha, still idonsa na kan ta yace.
“Ba ni labari”
“Kamar na me...?”
“Komai da komai”
“Nothing new”
“Seriously! What bought Lamido here?”
“Oh... He's my new driver”
“Driver...?”
“Yep Abbah ya kawo min shi ɗazu, zan fara zuwa scul Monday shine Abbah ya samo min sabon direba”
“Nice”
Ya faɗa kamar ba komai. Wayarsa ya fiddo ya kashe flash camera sannan ya shiga ɗaukarta hoto ba tare da ta sani ba, dan yasan idan har yace zai ɗauke hoto ba zata bari ba, kuma sisters nasa da Ummi sun dame shi akan suna son ganinta.
Haka suka ɗauki dogon lokaci a falon ita da shi babu wanda ya iya sake cewa ɗan'uwansa wani abu, kowa da abunda yake tunani, Namra gaba ɗaya hankalinta ya tafi akan halin da Uzair yake ciki, shi kuma hankalinsa ya tafi gurin Lamido dan yana ganin kamar zai masa zagon ƙasa ne, taya zai zauna ya zuba mata ido shi ya riƙa driving ɗinta scul ya sace zuciyarsa shi ya bar shi a nan.
“Zamu iya gaisawa da Abbah?”
“Yeah Yeah yes, bari na kira shi”
Ya miƙe tsaye tana taɓa kanta dan gaba ɗaya hankalinta ya tafi gurin wacan tunanin nata.
Ƙofar da zata sadata da ɗayan falon Abbah ta nufa, tana tura ƙofar falon ta jiyo muryar Abbah sai ruwan bala'i yake, shesshekar kuka na tashi, cike da faɗuwa gaba ta shiga ɗakin Abbah, sai ta samu Anty Amarya da Hajiya Barau zaune ƙasan carpet ko wannensu na kuka. Hajiya Barau ta rashi tana kuka ta fice daga falon, Anty Amarya ta kama ƙafafun Abbah ta riƙe tana kuka.
“Dan Allah karka aikata abunda zaka dawo kana nadama a lokacin da bata da amfani, dukanninmu ƴan'adam ne kuma ajizai masu yawan laifi da kuskure”
“Idan baki daina saka min baki a lamarin gidana ba, ke ma zaki haɗu da ɓacin rai na...”
Juyawa Namra ta yi ta koma jikinta a sanyaye, ba tare da ta kalleshi ba tace.
“Maybe idan ka sake dawowa zaku gaisa”
“Why...?”
“Abbah is not in the mood now”
Hawayen dake idonsa ya zubo muryarta kuma ya soma rawa alamar kuka yana tare da ita. Da sauri Abdool ya taso ya nufo inda take tsaye.
“Faɗa min Abnam, minene? You can't hide the truth”
“Mutumen da na taɓa baka labarin yace ƴana so na kuma ɗan luwaɗi ne, yanzu haka yana asibiti cikin mawuyancin hali, kuma ɗazu ya tara mu ya faɗi gaskiyar duk abunda yayi, ciki har da asirin da ya haɗa kai da Aminiyata Amira yayi min akan na gudu na bar gida, sai gashi asirin be kama ni sai ya kama Amirar Amiyar tawa ita ta gudu ta bar gidansu bata dawo ba sai ranar da na dawo garin nan...”
Ta ƙarasa cikin kuka.
‘Amira...’
Ya maimaita sunan a zuciyarsa, yana kallon zubar hawayen gimbiyarsa.
“Wannan ba abun kuka ba ne abun dariya ne da murna, amman komai daren daɗewa sai gaskiya ta bayyana kuma mai haƙuri mawadaci”
“Aminiyata ce fa, ace ta min irin wannan aikin ai dole na yi kuka, babu yadda ƴan'uwana ba su yi ba akan na rabu da ita amman na ƙi”
“Kin share hawayen ki, shiga ciki ki canja kamin na dawo, zan nuna miki wani abu”
“A'a Abbah ba zai bari ba”
“Zai bari just go”
Be jira amsarta ba, ya juya ya fice yana danna wayarsa.
MANAGE IT PLEASE 🙏
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *83*
Cikin nishaɗi da walwalah ta isa gida, tana faka Motarta Hajiya Sadiya ta fito hankalinta a tashe ta nufi inda take tsaye ta riƙa ta.
“Daga ina kike Nabila?”
“Mun ɗan fita ne da Asim, Lafiya”
“Na kira wayarki a kashe, ina kika je ne?”
“Munje cin abinci ne”
“Me kuka ci? Talk to me”
Ta riƙa fuskarta tana girgizawa. Itakam mamaki duk ya cika ta tashin hankalin da ta gani a fuskar Mahaifiyarta ta ruɗa ta.
“Miyasa kika tambaya?”
Hannunta ta riƙa ta jata suka nufi cikin falon sannan ta zaunar da ita saman kujera itama ta zauna fuskarta da damuwa ta ce.
“Ina tsoron kar ya baki wani abun ne, kin san mutane ba abun yarda ba ne”
“Hmmm Momi Asim ba irin mutanen da kike tunani ba ne, yana da kirki sosai”
“Ba daga nan take ba, Nabila ina fatar be baki Apple kin ci ba?”
“Ya bani apple kam kuma shi ma ya ci”
Ta dafa kanta ta sauko ƙasa ta riƙa hannayen Nably tana kuka.
“Wane irin apple ya ba ki? Na shiga uku na lalace, ya kai ki ya baro Nabila shi kenan, tawa ta ƙare”
“Momi me ke damunki ne?”
Kuka ta yi sosai har hankalin Nably ta tashi sannan ta labarta mata abunda ta shekara da shekaru tana aikatawa. Kuka Nabila ta saka zuciyarta ta cika da baƙinciki.
“Asim yayi daidai idan har da gaske ya bani apple ɗin na ci, na cancanci mutuwa a yanzu, ke ba uwa ba ce Momi, kin shirya kashe wata saboda tsiratar da ƴarki, kin shirya aikata komai saboda duniyarki”
Ta tashi da gudu ta nufi ɗaki tana kuka, saman gado ta zauna tana kunna wayarta, saƙon da ya shigo mata be bata mamaki ba saboda momi ta faɗa mata komai tun kamin Asim yayi mata wannan saƙon.
_Apple ɗin da kika ci Mahaifiyarki ce ta ba ni tace na kaiwa tsohuwar mamata, bayan kuma ta san na mutuwa ne, mahaifiyata ta ci ta mutu dan haka na yi ɗaukar fansa da ke_
_Ba ka yi kuskure ba Asim, Mahaifiyarta ta cancanci fiye da abunda ka yi mata, ni kuma na yi kuskuren yarda da kai, amman har gobe ina son ka_
Shine amsar da ta mayar masa, ta share hawayenta ta kwanta saman gado tana kallon window. Yayinda Hajiya Sadiya take tsaye a falo tana ta buge-bugen waya akan a taimaka mata kar ƴarta ta mutu, idan ta kira wannan tana kuka ta kira wannan duk ta bi ta haukace sai kuka take kamar zata tashi gidan. jin kamar ƴarta na tari yasa ta bar falon a guje ta nufi ɗakin tana kiran sunanta, amman ina Nably ta yi nisa har bata iya magana, duk ta ɓata gadon da aman jini kamar wacce ta amaye hanjin cikinta. Hannayenta biyu tasa tallafo kanta tana shafata.
“Nabila karki ta fi ki bar ni ke kaɗai kika rage min, na shiga uku na saka kai na a halaka, wannan baƙar ƙungiya bata min rana ba”
Kallonta kawai Nabila ke yi a wahalce tana numfashi da ker, hawaye na bin fuskarta har ta amsa kiran mahallicinta.
Wani uban ihu Hajiya Sadiya ta saki ta fita a ɗakin a guje, tana kaiwa harabar gidan ta zame ta faɗi ƙasa ba sumammiya.
UZAIR POV.
Wasa-wasa yau kusan talatin da ɗaya ana abu ɗaya babu sauƙi, sau biyu ana fita da shu waje amman babu abunda yake canjawa kuma ko ina aka je abu ɗaya ake faɗa cewar ba zai sake tafiya ba.
Tun ranar da ya aika Tahir be gane kan maganarshi ba, sai yawo yake ta masa da hankali, kullum da kalar abinda zai faɗa masa, kuma duk tsowon lokaci Yasmin bata taɓa taka asibitin da sunan ta zo ganin Uzair ba, abunda ya bawa kowa mamaki ciki har da Abbah. Ranar wata Lahadi duka ƴan'uwa suka saka ta gaba ana mata faɗa da tambayar dalilin ƙin zuwa ganin mijinta, amman ta kasa furta musu komai sai kuka take, a dole tasa suka ƙyaleta suka saka mata ido.
Ana sauran kwana biyu Abbah ya sake fitar da shi india, Tahir ya zo dubasa daman duk bayan kwana biyu yake zuwa ya gansa.
Yau ya fi bashi tausayi fiye da ko yaushe, ya rame sosai kamar ba abokinsa ba, wai yau Uzair ne kwance a nan baya iya komai, lallai duniya abun tsoro ce. Hawayen da ya gani a idon Uzair ya tashi hankalinsa sosai hakan yasa yau ya yanke shawara faɗa masa gaskiya, da kuma ba shi shawarar abunda yake tunanin zai zame masa mafita.
Ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana kallon Uzair ya ce.
“Na yi ta maka wasa da hankali akan maganar Malamin nan, magana ta gaskiya Uzair mutumen baya raye, lokacin da naje gidansa na samu ranar ake sadakan bakwai nasa, na ɓoye maka ne saboda karka tashi hankalinka”
Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa Uzair, ya haɗe yawun bakinsa cike da tausayin kansa ya ce.
“Tawa ta ƙare kenan! Haka ƙarshe na zai zo ni kuma? Ina ma ace mutuwa na yi na huta...”
Tahir ya dafa ƙafaɗarsa ya matsa kaɗan.
“ina tunanin abunda ya fi, ka samu Namra da iyayenta ka yi musu bayanin komai, kuma na nemu yafiyarsu, wata ƙila abunda ka aikata ne haƙƙi yake biye da kai, idan kuma har ba haka bane, to Amira ce ta yi maka asiri, idan zaka fallasa komai ka fallasa tare da Amira idan tana gurin, hakan zaisa guiwarta ta yi sanyi ta je ta kare abunda ta yi maka”
“Zan aikata Tahir indai har wannan zai sa na samu lafiyata, amman ya za'ayi Amira ta zo nan? Da wane ido zan kalli Abbah na ce ina son magana da Namra?”
“Zan kawo maka Amira, Namra kuma ka faɗawa Abbah kana son ganinta tare da Abbah”
Ya jinjina kai, shi dai ya shirya yin komai akan lafiyarsa, dan bai jin zai jure zama a irin wannan rayuwar. Bayan Tahir ya fita Mahaifiyarsa ta dawo ɗakin daman yanzu ita ce take jinyarsa ita da wani ƙanensa da kuma ƙanwarsa.
“Umma ina son ganin Abbah da Namra”
Ta kalleshi cike da mamaki.
“Ta maka me? Yarinyar da tun da ka kamu da rashin lafiyarnan bata taɓa cewa tana gaisheka ba balle ta zo duba ka ita zaka nemi gani yanzu?”
“Zan yi wata magana da ita mai muhimmanci, dan Allah ki taimaka min itace kawai mafitar wannan ciwon da nake yi, da ta zo zan samu sauƙi”
“Ban gane ba? Kamar ya itace mafitar ciwonka? Kana magana kamar wanda baya cikin hayyacinsa, Uzairu cuta fa ba mutuwa ba ce”
“Ki taimaka min ki kawo min ita mu yi magana zan faɗa muku komai,ciki har da dalilin daya sa Yasmin ta ƙi ta tako asibitin nan”
Da farko Umma ta ɗauka zafi ciwo ne yasa shi wannan maganar, daga baya kuma sai ta fahimci yana cikin hankalin kansa, sai dai maganganun da yake sun ɗaure mata kai.
Tahir na barin gidan ya nufi gidansu Amira, kamin ya isa sai da ya kira yayanta ya faɗa masa shi baya gida amman Amira tana gida. Harabar gidan ya shiga da motarsa, sannan mai gadin ya shiga ciki yace ana sallama da Amira, bayan ƴan mintuna ya dawo yace wai ance wanene?
“Kace Tahir ne abokin Big Bro”
Sai mai gadin ya koma, ya dawo ya ce wai ance ya shigo ciki. Ba musu ya doshi babbar ƙofar Falon. Da sallama ya shiga Ammy ta amsa masa tare da Amira sannan ya zauna, suka gaisa ya faɗa musu abunda yake tafe da shi. Ba Amira ba har Ammy ta yi mamakin jin Uzair na son ganinta to me zai ce mata? Bayan duk abunda yayi mata, daman tun da suka samu labarin bashi da lafiya Ammy da Abban Amira suke cewa wai amanar Amira ce ta kama shi.
“Yana nemana kamar ya ? Me zai ce mun?”
“Nima ban sani ba, amman yace maganar tana da muhimmanci, sosai”
Ammy ta ce
“To ba zata ita kaɗai ba, tare zamu je, kuma sai Abbah ta ya dawo duk abunda ya ce shi zamu yi”
Tahir ya miƙe tsaye yana faɗin
“Kamin na zo nan sai da na yi magana da Big bro, idan har wani abu ne mai cutar da ke ba zai bari na shigo nan na faɗa miki ba”
“Koma dai minene sai mahaifinta ya dawo”
“To hakan yayi, ni zan wuce”
“A gaida gida”
Ammy ta faɗa sannan ta bishi da kallo har ya fice. Gaɓa ɗaya jikin Amira yayi sanyi, zuciyarta sai yaye-yaye take mata, ta rasa dalilin da zai sa Uzair ya so ganinta, to ko yana zargin tana da hannu a ciwonsa ne? Ko kuma wani abun ne kuma ya faru? Maganar Abbah ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi.
“Bari na kira Abbah ki na faɗa masa”
Kai kawai ta iya ɗagawa ta cigaba da tunanin da take.
NAMRA POV.
Bayan an gama bikin Maryam da Hindatu, Abbah ya shiga fafutukar nemawa Namra Admissions a wata makarantar koyarda ilmin computer. Kasancewar duka jami'o'i a yanzu sun gama ɗaukar ɗalibai, gashi kuma bata da komai a yanzu saboda ƙonewar da takardunta suka yi a motarta lokacin da Asim ya taɓa haɗari, ba ƙaramin kuɗi Abbah ya kashe ba wajen fito mata da tsofin takardun da suke makarantar primary da kuma Secondary school. Jami'ah kuma sai next year zata fara, tun da ta riga ta lalata karatunta tun a wacan lokacin.
Sai dai wannan karon kan Alhamdulillah komai ya zo da sauƙi, kasancewar Abbah ya saki ƙuɗi cikin ƙanƙanen lokaci aka yi komai. Aiko murna gurin Anty Amaeya da Namra ba a magana kamar su haɗe Abbah, dan jindaɗi.
Monday mai zuwa Namra zata fara zuwa makaranta, ranar Assabar da Safe Abbah ya kawo mata sabon direba da zai riƙa kai ta makaranta, Namra ta yi murna sosai dan bata tsammaci haka daga gurin Abbah ba.
“Abbah ka yi min abubuwan da ban yi tsammani ba, ka nuna min sosai, Allah ya ba ni ikon saka maka”
Duk suka amsa da Amin har Anty Amarya dake ƙara jin son Abbah har cikin ɓargon ranta. Namra ta ɗauki ɗankwalin abayarta ta yafa ta fita dan ganin sabon direban nata. Tsaye tayi cak a baki ƙofa tana furta
“Lamido”
“Yes Ma'am”
Ya amsa a natse, yayi fari yayi kyau sosai ƙananna kayan da ke jikinsa sun ƙarɓe sa sosai. Ta nunashi da yatsa sai ta kasa magana. Murmushi yayi ya gabatar da kansa.
“My Name is Aliyu Adamu Lamido your new driver”
“How.... How....”
Maganar ta laƙe ta ƙi fitowa sai ta sake nuna shi da yatsa.
“You...”
Murmushi ya sake yi yana kallon yadda ta canja ta yi kyau kamar ba ita ba, baƙin nan nata sai sheƙi yake ga dogon hancin nan da farraren idonta da suka ƙara fitowa.
‘Black beauty akwai kyau’
A zuciyarsa yayi maganar a fili kuma murmushi yake mata mai ɗaukar hankali. Juyawa ta yi ta koma cikin falon, cike da ruɗani ta kalli Abbah ta ce.
“Abbah da gaske shine sabon direba na?”
“Eh ko be miki ba ne?”
“Me direban yayi”
Anty Amarya ta tambaya. Zaunawa Namra ta yi tana faɗin.
“Anty Lamido ne fa”
“Wane Lamido kin san shi ne?”
“A gidansu na sauka Kaduna, shi ya ɗinga ɗawainiya da ni har kuka zo kuka ɗauke ni, Lamido na gidansu Neina fa”
“Au shine? Ya akayi ya zo nan ne?”
“Nima ban sani ba, abun ya ɗaure min kai ne, Abbah ina ka haɗu da shi?”
“A can ƙamfani ya same ni, wai yana son a ɗauke shi direba idan zai samu, kuma baya son na kamfani na gida yake so, kin san daman ni kuma ina neman direban da zai riƙa kai ki scul yana maido ki, shiyasa na ɗauke shi”
Namra ta girgiza kai.
“Abbah why not ka ɗauke shi aiki a kamfanin ka, yayi degree fa, aikin ne be samu ba”
“Ko zan ɗauke shi ba yanzu ba, sai naga gudun ruwansa, idan dai be miki ba za a iya canja miki wani”
“Oh no yayi min, ba matsala Allah ya saka maka da alheri”
“Amin, yanzu sai ki tashi muje Asibiti, Uzair ya ce min yana son ganinki”
“Ni?”
Ta nuna kanta, ba ita kaɗai ba, har Anty Amarya mamaki ta yi.
“Ya za'ayi Uzair ya cw yana son ganin Namra? Kin yi wata magana da shi ne?”
“Anty ya za'ayi na yi magana da shi, tun da na bar garin nan har na dawo wata kalma bata taɓa shiga tsakani na da shi ba”
“Ɗazu dai Mahaifiyarsa ta kira ni tace min dan Allah na zo da ke, Uzair yace zai yi wata magana da ke mai muhimmanci”
“Ni gaskiya ba zani ba”
“Sai fa kin je, indai har zan baki umarni ki bi, bawan Allah nan ban san abunda ya tare miki ba, daga kawai yace yana son ki, kuma na ga yanzu ko lafiyar jikinsa bata ishe shi ba, ya aikamata ki je ki masa sannu”
“Zan je kawai bisa Umarnin ka”
“To tashi ki saka Hijabin ki”
Ba musu ta tashi ta nufi ɗakinta dan ɗauko Hijabin.
“Wai ko na taso muje har da ni ne?”
Anty Amarya ta faɗa tana kallon Abbah, dan taji me zaice, dan tana cike da son sanin dalilin kiran Namra da Uzair yayi bata son a bata labari.
“Tashi muje komai dai son gulmarki sai kin ba su ɗaki sun yi magana”
Abbah ya faɗa da fuskar zolaya. Anty Amarya ta tashi tana dariya ta nufi ɗakinta.
Cikin ƙanƙanen lokaci suka isa asibitin, gaban Namra sai fat fat fat yake, duk da bata san ta yi wani laifi ba, tana jin tsoron kiran da Uzair yake mata. Bama kamar lokacin da suka shiga ɗakin ta yi ido huɗu da Amira, kallon kallon Akuya kallon Kura suka riƙa yi ita da Amira, ko wannen kuma.ya kasa cewa ɗan'uwansa uffan. Daga su har Ammy da Anty Amarya, Ammy sai faman hararar Anty Amarya take da Namra, Abbah ne kawai ya gaisa da Abban Amira, sannan Big Bro ya gaishe shi, ya kuma gaishe da Anty Amarya sai kuma ya kalli Namra fuskarsa da murmushi ya ce.
“Namra ba gaisuwa, kin san ni fa yayanki ne”
“Ina wuni”
Ta gaisheshi ba tare da tayi murmushi ba, ita hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma kan Uzair yanayin yadda ta ganshi ya bata mamaki, daman hausawa suka ce abunda duk ya baka tsoro wata rana sai ya baka tausayi, gaba ɗaya ya tafi da imaninta, ya rame sosai, ga ledar fitsari an saka masa ta ƙasanshi, saboda rashin tashin da yake. A ɗayan ɓangaren kuma tana mamakin ganin Amira a ɗaki tare da iyayenta da kuma abokinsa Tahir.
“Ka tara mutane a nan kuma baka ce komai ba”
Umma ta faɗa cikin rashin daɗin rai, dan bata so ya kira Amira ba, duk da bata san dalilinsa na kiranta ba.
Ya ɗauki dogon lokaci kamin hawayen da suke masa zuba su tsagaita masa har yaja dogon numfashi ya sauke, sannan ya soma magana.
“Abbah zaka iya tuna wani lokaci a baya da aka ce Namra ta gudu taje gurin Asim? Ni na ɗana mata tarko tare da aminiyarta Amira, na bata sabon number da sunan zata zo ta ga Asim a bayan gidansu su gaisa, alhalin ni ne ba Asim ba, bayan na ɗauke ta sai abokaina suka canja min shawara da sunan kar na mata komai, na maidata a can, abokina ne ya faɗawa mai gadin gidana abunda zai faɗa akan ya tsince ta a bayan gidan ana ƙoƙarin yaga mata mutunci, kuma ana kiran sunan Asim... Kasan dalilin da yasa na yi mata wannan sheri? Saboda ta tona min asiri akan abunda na ke aikatawa, wato na neman maza ƴan'uwana, ba ƙarya ta faɗa ba, ta gan ni da gaske ina aikata wannan abun, amman na ƙaryata ta ne saboda ina ganin kamar asirina zai tonu ne, a lokacin, shine dalilin da yasa na ɓullo da maganar neman aurenta, sai ita kuma ta ƙi yarda, sanadin hakan da kuma gudun karta tona min asiri abokina Najib ya kai ni gurin wani boka muka mata asiri, yace sai an kawo rigarta da ita za ayi wannan asirin, sai na samu Amira na biyata na faɗa mata haka kuma ta yarda ita taje ta aro min rigarta da sunan ita zata saka muka kai akayi mata asiri da wannan rigar, daman can bokan ya faɗa mana duk lokacin da ta saka rigar idan har asirin be kamata ba to zai dawo kan mu ne, saboda Namra tana da ƙarfin addu'ah. Da asirin be kama Namra ba sai ya kama Amira, sanadin hakan ta gudu ta bar gida, ban sake jin ɗuriyarta ba, sai a lokacin da ta aiko min da wasiƙar cewar idan har ban je na kare wannan aikin ba zata iya aikata min komai. A lokacin ne Yasmin ta gani, kuma ta gano abunda ya shiga tsakanina da Adnan, wata rana ne da rana na shigo sai na tarar bata cikin gidan, sai kawai na afkawa ɗa na, daman can nafi son yi namiji, tun daga lokacin na keɓe Adnan ina jiyarsa bata gane ba, sai daga baya, sanadin hakan tace zata kai ni kotu, ni kuma na ƙaryata gaskiyarta, Washe garin ranar ne Hajiya barau ta kira ni ta faɗa min Namra ta dawo, daman ita take labarta min halin da Namra take ciki, da kuma duk wani abu dake gudana a gidan...”
Tun da ya fara maganar be tsaya ba sai da ya kai aya. Idon Abbah sun rine sun yi ja sosai, Abbah Amira ma kansa ya ɗaga sama ya maida hannayensa baya yana jinjina lamarin. Anty Amarya da Ammy kuma suna hawaye, Amira kan kasa kuka ta yi duk ta rikice jikinta sai rawa yake gumi na keto mata ta ko'ina.
“Miye dalilinka na faɗar gaskiya Uzair miyasa ba ka yi shiru da bakin ka ba? Miyasa baka ɓoye sirrinka ba kamar yadda nima na ɓoye nawa? Ban yi niyar faɗawa kowa abunda ka aikata ba Uzair, duk da rayuwar da na shiga ta fi wacce kake ciki a yanzu, dan ni nafi ƙaunar irin ciwon nan naka na san zai sadani da lahira a nan kusa, sama da jiran gawon shanu, jiran abunda babu ranar zuwansa. Ban taɓa tunanin haka ba, na yi tunanin ka haɗa kai da Namra ne ka cutar da ni ashe ni na cutar da kai na! Yanzu na fahimci dalilin da ya sa na gudu na bar gidan mu, kuma bayan na gudu ban faɗa hannun ƙwarai ba, sai na faɗa hannun ɗan fashi, ya mayarda da ni kamar matarsa, ta sanadinsa na ceci wani mutun wanda nake wa jiran gawon shanu, a familynsu na zauna, ina ganin kamar wata sabuwar rayuwa zan shimfiɗa ashe a saman wuta na yi shinfiɗar....”
Amira ta ƙarasa tana durƙushewa a gurin cikin wani irin kuka da yake jin kamar ta haɗiye zuciya ta mutu ta huta. Lokuta da dama ta kan ji hakan idan ta tuna yadda Abdool ya juya mata baya, mutumen da ta fi ƙauna fiye da komai a rayuwarta, a yanzu haka bata da buri sai na shi, shiyasa ta kasa maida jikinta duk da tana tare da iyayenta.
Gaba ɗaya Namra ta ruɗe ta kasa gane komai, daga Uzair ɗin har Amira kallonsu take tana hawaye.
“Yasmin ta kasa samun fili a zuciyarta ta yafe min, saboda na yi mata sara ne a baƙin wuya, amman ke na san zaki iya yafe min, duk da kema na miki illah, amman ki dubi girman Allah ki yafe min ko Allah zai tashi ƙafaɗuna. Idan kuma har wani aikin ne Amira ta yi min dan Allah ki je ki warware shi, saboda na tsorata da kalamin da kika rubuta min cewar zaki ɗauki mataki. Ba zan iya jure zama cikin wannan rayuwar ba, ki taimaka min ki yafe min Namra...”
“Ba zata yafe maka ba, ashe kai ne silar komai, Namra ba zata yafe maka ba...!”
Abbah ya faɗa a tsawace, har sai da Namra ta kalleshi. Ya nufi ƙofa a hasale ya buɗe.
“Mamana wuce mu je”
Abban Amira yayi saurin riƙe Abbah.
“Haba ai babba baya haka, babba baya taɓa zama ƙarami, kuma tun da har yayi nadama ya kamata ka yafe masa”
Abbah ya girgiza masa kai yana ɓanɓare hannunsa daga riƙon da yayi masa.
“Sake ni Alhaji, yaron nan be kyauta min ba, babu abunda ban masa ba a rayuwa, acw ya rasa wanda zai yi ma zagon ƙasa sai ni da iyalina, wannan wane irin abu ne? Yanzu da be shiga wannan halin ba babu wanda zai san gaskiya, sai dai ayi ta zargin Namra, babu abunda ban ma yarinyar nan ba saboda shi, ashe tana kan gaskiyarta...”
Tuni Anty Amarya ta kama hannun Namra suka bar ɗakin, sannan Abbah ya rufa musu baya. Bayan fitarsu Big Bro ya kalli Amira dake taugune a gurin tana kuka ya ce
“Kinji kunya wallahi kin ci amanar ƙawarki”
Ya ƙarasa tare da jan tsaki ya juya a fusace ya bar ɗakin. Baka jin kukan kowa a ɗakin sai na Umma da Amira, dan Ammy hawaye kawai take, kamar yadda Tahir ke yi..
***
Kuka sosai Namra ta dinga yi a a motar har suka iso gida daga Anty Amarya har Abbah babu wanda ya iya buɗe baki ya furta wata kalmar balle kuma ya bata haƙuri.
Inda suka bar Lamido a gurin suka same shi zaune, Abbah be bi ta kansa ba ya wuce Anty Amarya ma haka, Namra ce ta tsaya dai-daice tana share hawayenta da Hijab ɗinta ta nuna masa wasu ɗakuna da suke can gefen gardem.
“Kaje ka zaɓi ɗaya daga cikin ɗakunan can, zan kawo maka keys ɗin ɗakin anjima...”
Gaba ɗaya hankalinsa na kanta, ya tsorata da yanayin da ya ganta saboda ya tsani zubar hawayenta.
“Allah yasa ba nine dalilin zubar wannan hawayen ba!”
“Ba kai ba ne, gaskiya ce ta yi halinta...”
Ta faɗa tana kallon sabuwar motar da aka buɗewa gate ta kunna kai a harabar gidan. A gurin da aka tanada dan faka motoci, aka nufa da motar kasancewarta mai baƙin gilashi baka iya hango wanda yake cikin motar. Ya ɗauki daƙiƙa goma sha biyar zuwa ashirin kamin ya fito daga cikin motar. Gaban Namra yayi mugun faɗuwa hango Abdool daya fito daga cikin motar sanye da farin yadi fuskarsa sai sheƙi take..
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *85*
Bayan Abdool ya fita Namra ta koma cikin falon Abbah, har lokacin tana jiyo shessehakar kukan Anty. Hannu ta kai ta tura ƙofar ɗakin Abbah ta tsaya daga bakin ƙofa tana hawaye. Bata san abunda Abbah yayi ba ko yace, sai dai tasan yadda ransa ya ɓace hakan nan dole sai wani abu ya faru.
Kallo ɗaya Abbah yayi mata ya ɗauke kai, ya zauna saman kujera yana kallon Anty Amarya.
“Dan Allah ki tashi ki ba ni guri ni bana son hayani”
Unƙurawa Anty ta yi ta tashi tana cigaba da kuka ta fito sai Namra ta riƙa ta suka nufi part ɗinta.
Saman kujera ta zauna tana kuka, Namra ta zauna kusa da ita ta kama hannunta ta riƙe.
“Anty mi Abbah yayi? Miyasa kuke kuka?”
“Yace Hajiya ta tafi ta bar masa gidansa, nayi nayi da shi amman ya ƙi, taya zai tura mace mai ƴaƴa da ƴawa kuma uwargidansa ya ce ta bar masa gida? Wannan sam be dace ba, komai ta aikata aiko ƙyaleta yayi ya barta da kunyarta, gaskiya dai ta riga ta bayyana babu abunda zata koma yi, amman yanzu ai ƴaƴanta ba za su ji daɗi ba”
“Ya sake ta ne?”
“Be sake ta amman ya ce da tafi duk inda zata je sai ya nemeta”
“Idan ya huce zai maida ta Anty, kowa dole ne yaji baƙinciki ace da matarsa za a haɗa kai a cuci iyalansa”
“Nasan abunda ta yi bata kyauta ba, amman ki duba ki ga halin da yaron nan yake wannan kawai ya isaahe ta ishara, ita sai ya zuba mata ido ko dan ƴaƴanta, wani lokacin mahaifinki yana rufe ido ya aikata abu kamar bai san kowa ba sai kansa”
“Zai dawo da ita, kawai ki bashi lokaci”
“Allah yasa”
“Amin. Abdallah ya zo”
Anty ta share hawayenta tana faɗin.
“Yaushe?”
“Yanzu ya tafi amman yace zai dawo”
“Na manta kin kaiwa Lamido abinci?”
Namra ta miƙe tsaye da sauri dan ita ta manta da shi gaba ɗaya.
Kitchen ta shiga ta haɗa masa fruits da drinks, ta dauƙa nufi waje. Zaune ta same shi cikin ɗakin hannunshi a bakinsa kamar mai nazari.
“Sorry mun cinye abincin rana amman yanzu xan girka maku wani”
Janye hannunsa yayi yana murmushi ya karɓi turen ya aje yana faɗin.
“Kin manta da direban ki saboda sahibin ki ya zo”
Wani kallo tayi masa mai cike da mamaki.
“Kai da Abdallah duk matsayin ku ɗaya a gare ni”
“Ba ɗaya ba ne, Shi ɗan masu kuɗi ne”
“Kai kuma ɗan talakawa”
“Shi ɗan sarauta ne”
“Kai kuma ɗan bayi”
“Yana da matsayi a zuciyarki”
“Kai kuma baka da shi. Na gode”
Tana miƙewa tsaye shi ma ta miƙe yana ƙokarin shan gabanta.
“Am sorry ban yi dan na ɓata ran ki ba, kawai ina ganin ba zan taɓa taka matsayin da Abdallah ya taka a zuciyarki ba ne, daga yau zan sauka a matsayin masoyinki, daga yau ni yayanki ne”
Ya faɗa cikin muryarsa marar daɗi, kallonsa kawai ta yi ta ɗauke kai, ta fice. Tana fitowa ta hango Abdool tsaye tare da Abbah suna magana, yadda Abbah yake watsar haƙora zaka rantse da Allah ba shi ya gama yi ma Hajiya Barau faɗa ba. Har zata wuce Abbah ya kira ta
“Mamana”
Sai ta ƙarasa gurin cikin ladabi.
“Ba ki ga ɗa na bane? Ko baki iya gaisuwa ba”
Ɗan risina tayi ta gaishe da Abdool suna haɗa ido ya kanne mata ido ɗaya ƴana murmushin gefen baki.
“Mun samu ku lafiya”
“Lafiya ƙalau”
“Je ki shirya zaki zaka shi wani guri”
Abbah ya faɗa, har ta buɗe baki ta yi magana sai kuma ta yi shiru ta amsa da to kawai ta nufi part ɗin Anty.
Ya kusan awa ɗaya yana jiranta sannan ta fito cikin ƙaton hijab, a lokacin Lamido na jikin window yana kallonsu, a front seat ta shiga sannan yayi ma motar key suka fita.
AMIRA POV.
Tun tana kuka hawaye na mata zuba har hawaye suka daina kukan kawai take ba hawaye. Gashi tun da suka dawo gida Mahaifinta be ce da ita uffan ba, Ammy xw kawai take bata magana.
Tashi ta yi ta nufi ɗakinta, tana shiga ta maida ƙofa ta rufe. Haƙiƙa ta yi rashin abubuwa da yawa, ta rasa mutuncinta ta rasa martabarta ta rasa wanda take so yanzu me ya rage mata?
Ta ci amanar ƙawarta dole ita taga ba daidai ba, tabbas hassada bata haifar mata da komai ba sai nadama da dana sani. Da ace tun farko bata hassadar Namra da bata yarda ta aikata abunda ya kai ta ga halaka ba, da ace ta zauna da ita da zuciya ɗaya da duk wannan be faru da ita ba.
Yanzu gashi daga ita har Uzair babu wanda yake cikin rayuwar jindaɗi, Allah ya jarrabeta da son Abdool idan ta tuna shi har ji take kamar zuciyarta zata rabe biyu.
Bugar ƙofar ɗakinta Ammy tayi dan tana tsoron kar ƴarta ta saje shiga cikin halin da ta shiga a baya, musamman yanzu da take ganin duniya ta juya mata baya.
“Amira an kira wayarki”
Miƙewa tayi tsaye taje ta buɗe ƙofar da idonta da suka kumbura sosai suka ƴi ja kamar an zuba mata barkono a ciki. Hannu Ammy ta kai ta shafa fuskarta.
“Amira karki sa ranki a damuwa, dan adam be isa ya wuce ƙaddararsa ba, Allah ya rubuto haka zai faru da ke babu yadda zaki yi, dan Allah kar zuciyarki ta sake tunanin guduwa ki bar mu”
“Idan ma na gudu ina zanje? Ko wace mace bata da daraja sai a gurare biyu, gidan iyayenta ko gidan mijinta, guduwa da na yi a wacan karon yasa na gane iyaye suna da muhimmanci sosai a rayuwa, rashin zaman mace a gaban iyayenta yana karyarda darajarta, wannan ne ya hana Abdool da family sa su kalle ni da daraja da ace ina a gidan iyayena xauna wata ƙila da zai iya aurena”
“Wanene Abdool kuma?”
“Shine mutumen da ya hana zuciya sukuni, Allah yayi min jarawata ta nan ne, ina son shi, shi kuma yana son wata”
Komawa ta yi ta zauna, Ammy ta zauna kusa da ita tana kallon ƴarta cike da damuwa. A nan Amira ta faɗawa Ammy komai a zaman da tayi da Abdool da kuma wanda ta yi kamin da haɗu da shi da yadda ta sadaukarda kanta gareshi.
“Kin sadaukarka da kanki gurin da bashi da amfani, kin salwantar da rayuwarki gurin da ba a san darajar rai ba, kin yi sadaukarwar da ba zaki taɓa cin ribarta ba, kin yi kuskuren da ba zaki iya gyarawa ba, kuma ina tsoron kar ɗaya daga cikin ƴaran mutumen nan ya farauci rayuwarki, kin yi kuakuren ba rin zuciyarki ta kamu da son mutum kamar wannan”
“Na sani, amman zuciya bata da laifi babu yadda ta iya, ina son sa Ammy amman shi baya so na, be san hallaci ba”
NAMRA POV..
Ta share hawayen da suka zubo mata cike da tausayin labarin da Abdool ya bata.
“Amman wannan yarinyar ta cancanci komai daga gareka, ya kamata kai ma ka yi mata hallaci, duk wanda ya sadaukarka da ranshi a gareka ya cancanci ko wane irin sakamako daga gareka, da yanzu ta mutu kai ka rayu”
Murmushi yayi yana cigaba da tuƙinsa hankalinsa kwance.
“Ashe ko na cancanci ko wane irin sakamako a daga gareki, dan na daɗe da salwantar da rai na akan ki”
“Kar zuciyarka ta raya maka abunda ba shi bane a Abdallah karka cuci kan ka ka cutar da yarinyar nan”
“Namra baki taɓa tambayar kan ki miyasa Abdool yake son ki ba? Baki taɓa wannan tunanin ba? Ko dan ban taɓa furta miki ina son ki ba?”
“Babu so agaban Namra a yanzu balle har ta yi tunanin dalilin na ka son, kar zuciyarka ta yaudareka a yanzu Abdool ban shiryawa irin wacan rayuwar ba”
“Ashe ke ba mumuna bace Namra, har yanzu kina da sauran cikon imani a zuciyarki tun da baki yarda da ƙaddara ba. Miyasa zuciyarki take ta nuna miki Asim kamar Abdool yake, dan me kike tunanin irin rayuwar da kikayi a gidan Asim irinta zaki yi a gidan Abdool? Mahaifiyata bata da buri a yanzu wanda ya wuce na maganar aurena da ke, ina da ayukan yi da yawa Namra amman na danne su na tako garin nan saboda ke kawai”
Hannu ya kai ya canja fm zuwa wata sannan ya ce
“Wata kila zuciyarki wani take so ba ni ba, na lura Lamido na da matsayi a zuciyarki sama da ni”
Kalamansa da fakin ɗinsa sun rikita ta a lokaci ɗaya, ya faɗa mata abunda yau ma Lamido ya faɗa mata, dan me suke ƙoƙarin saka ta cikin matsalar da bata daɗe da fita ba?
“Miya kawo mu nan?”
A fili ta tambaya tana kallonsa, ba tare daya kalleta ba ya sauke wayar kunnensa yace
“Zaku gaisa da yarinyar ne”
“Nan gidan su Amira ne”
“Ita ma yarinyar sunanta Amira”
Kamin ta ƙara wata magana sai ga Amira ta fito da gudu daga cikin gidan ta nufo motarsu. Buɗe motar Abdool yayi ya fita sai tazo gabansa ta durƙusa ta riƙe ƙafafunsa ta tada kanta sama ta kalleshi. Shi ma kallonta yake kamin ya janye ƙafafunsa ya nuna mata front seat. Bata fahimci mi yake nufi ba, ta shiga ko kuma ta buɗe ta gani, sai dai bata tambayeshi ba ta tashi tsaye ta nufi motar ta buɗe. Ganin Namra yasa ta murmushi da hawaye a lokaci ɗaya.
“Itace?”
“Itace”
Ya amsa mata kai tsaye. Sai ta ƙara faɗaɗa murmiahinta.
“Kayi dacen mata, itama kuma ta yi dacen miji, congratulations Namra Allah ya baki abubuwa da dama, ciki har da wanda na fi so sama da komai, Allah ya haɗa kan ku ya baku zama lafiya”
Uffan Namra bata ce mata ba, har tayi surutunta ta gama ta koma gurin Abdool.
“Haƙiƙa kun dace da junanku, namiji irinka be dace da ko wace irin mace ba sai Namra kamar yadda ita ma bata dace da ko wane miJi ba sai kai, na yarda da ƙaddara haka Allah ya so ta kasance a gareni...”
“Amir...”
Ta ɗaga mishi hannu.
“Na fahimta, na gane ƙaddaratace a haka”
Bata jira abunda zai faɗa ba ta juya ta koma cikin gidansu, hawaye na mata zuba kamar ruwa. Buɗe motar Abdool yayi ya koma ciki ya zauna yana kallon fuskar Namra.
“Itace yarinyar da ta cutar da ke ko?”
“Abunda ta yi min tsakanina da ita ne, kai kuma sadaukarwar da ta maka tsakanin ka da ita ne, ka maida ni gidanmu ban yi tunanin ka ɗauko ni dan ka ɓata min rai ba, na tsani yarinyar nan na tsane ta, idan ma kana son ta ni ina ruwana karka sake kawo ni gurin, idan ma zaka so ka kaje can ka so ta ni karka sake sako ni a matsalar ku”
Shiru yayi yana saurarenta har ta yi masa faɗan ta gama sannan ya tashi motar yana murmushi ya suka nufi hanyar gida. Sarai kalamata suka wanke masa zuciya ɗan ya fahimci inda ta dosa. Yana yin fakin ya buɗe motar ta fita a hasale ta shiga cikin gida.
Wayarsa ya ɗauka ya kira Abbah suka yi magana sannan ya faka motarsa ya fita ya shiga part ɗinsa.
Yayi awa ɗaya a part ɗin Abbah sannan ya fito tare da Abbah ya shiga motarsa ya kama hanya.
KALSOOM POV.
FIVE MONTHS LATER...
Daga ita har su Izza basa da wata matsala a yanzu, tana zaune da yaran lafiya ƙalau ga Hajiya sai nuna musu kulawa take. duk wani rashin kunya na Izza ta watsar, ulfah kan ba a magana daman tun da warke daga jinyar ruwana zafi sai ta ƙara ladabi, dan sosai yanzu suka gane muhimmanci Kalsoom, gashi lokaci-zuwa lokaci takan kira musu mahaifiyarsu su gaisa, ranar weekend kuma Hilal ya kaisu gidan Hajiya. Idan zai dawo Hajiya ta bashi rubutu ya kawo mata na neman ta sauka lafiya. Babu yadda Teema ba tayi ba akan ta dawo gidan amman Hilal da Hajiya suka ƙi, su Izzah kan ko zancenta basa so.
***
Bayan ta ƙare waya da Salma ne ta kalli Hilal dake kwance gefenta yana wasa da wayarsa tace.
“Salma na gaishe ka”
“Ina amsawa, bari naje na ɗauko su izza scul”
Ya faɗa yana unƙurin tashi, kai kawai ta ɗaga masa dan maganar ma wahala take mata ko wayar da take da Salma na ƙarfin hali ne, tun jiya take jin abu amman ta kasa faɗa, duk da ta kan ji irin haka lokaci lokaci amman wannan ya tsananta mata da yawa. Aiko kamar karya tashi daga gurim ta soma jin ana tsikararta, har zaman ya gagareta sai da ta kwanta.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Shi take ta maimaitawa tana rumtse rumtsen ido. waƴarta na kusa da ita amman ta kasa miƙa hannu ta ɗauka, wani irin juyi take jin duniya na mata, tun tana faɗar Innalillahi a hankali har ta fara yi da ƙarfi tana ta rumtsar ido da buɗewa kamar wacce ta ci bashi. Ko da Hilal ya ɗauko su Ulfah daga makaranta Kalsoom ta jigata, jini har ya fara mata zuba, daman tun safe ya kula da yadda cikin yayi mata ƙasa sosai. Ɗakinsa ya shiga ya ɗauko kayan karɓar haihuwa ya dawo ɗakinta ya shiga ya rufe ƙofar ya shiga bata taimako, because ya san it too late yace zai ɗauke ta suke asibiti a yanzu bayan ga har kan yaro ya fara fitowa😷
ASIM POV.
Tun bayan rasuwar Mama ya daina ganin kam kowa da gashi, gani yake tun da yayi losing mahaifiyarsa a yanzu baya gudun komai, haka zai shigo cikin sokoto ya kwana gurin ogansa, ba zai leƙa ƙanensa ba sai zai tafi sannan ya basu kuɗi mai yawa, babban gida ya siya musu, dan yana ganin kamar su ne family da suka rage masa yanzu. Sai duk lokacin da ya shiga sokoto sai ya binka labarin Namra ace masa tana nan lafiya, har wani ya ɗauka mai aikin bincika masa labarinta, dan a tunaninsa tana nan ɗauke da cikinsa, burinsa kawai ta haifa masa ɗan ko ya ya ɗauke ta dan kawai ya ɗasa mata baƙin ciki. Sati ɗaya da rasuwar Mama aka saka ranar aurensa da Mardiya, yadda yake kashe mata kuɗi sai ka rantse da Allah shi ne yake buga kuɗi, dan yana samun kuɗi sosai a yanzu manyan mutane yake tare da su. Ya faɗa musu baya buƙatar komai dan tun kamin a kai lefe ya saka komai a gidan da zata zauna, kama daga kayan kitchen har zuwa na kwalliya da sutura kai kace ma be mata lefen gaba ɗaya ba sai taje can, har kayan abinci babu abunda be zuba ba, freezer goma ya saka a gidan jo wace cike take da kayan daɗi.
Ranar talata aka fara event an zubar da naira a kamu sosai kasancewar Asim ya bawa kawaye amarya kuɗi sosai, gashi shi ma yaje shi da abokaninsa dan yanzu yayi sabin abokai yayan manya sai kuma masu irin aikinsa, duk wani gaye mai kuɗi da kasani a cikin garin katsina mai ji da kansa sai Asim yayi abota da shi, dan gani yake sune sa'o'insa.
Friday aka yi walima, a instagram Namra take ganin bikin kamun su, tayi mamakin da ya auri Mardiya dan bata manta lokacin da yake yawan maimaita mata cewar shi sai ƴar da ubanta ya fi nata kuɗi zai aure, wata ƙila farin jikinta ne ya jashi hankalinsa ko kuma bayan ya aureta zai ƙara wata.
Tun ranar da aka gyara ɗakin aka saka komai Asim yake kwana a gidan. Wasu abokansa da suka zo daga sokoto da Abuja sai ya kama musu hotel wasu kuma ya sauke su a ɗayan gidansa dake GRA, shi kuma ya koma Light up road inda gidan amaryarsa yake dan kwana. Light up unguwace ta masu kuɗi ko wanne gida ka gani sai ya burge ka, amman duk da haka a layin da Asim yake gidansa ya fi ko wanne gida kyau da tsari, kana ganinsa kasan ba ƙananan kuɗi aka kashe ba gurin gina shi.
Ƙarfe ɗaya da rabi na dare ya shigo gidan, cikin wani irin yanayi marar misaltuwa, yana jinsa a wani matsayi na daban kwatankwacin matsayin da ya riƙa jin kamsa a lokacin da zai auri Namra, freezer da ke kitchen ya nufa ya buɗe ya ɗauko power horse ya fito falo yana sha. Kansa ya ɗaga sama yana kallon pop zuwa labulayen da aka saka falon, hantin kawai idan ka kalla sai ya burge ka, balle kuma kujera da plasma da flowers, daga kujera har center carpet da labulayen da da fantin ɗakin milk and red ne, dinning area kuma aka ƙawata gurin da red color. Relaxing yayi sama cushion yana furta sunan Namra, a zuciyarsa, haka kawai ta faɗo masa a rai, duk wacan dukiyar da aka narka masa a wacan gidan da Namra ta kama musu haya ubanta ne ya narka masa ita yayinda wannan kuma shi ne ya narka ma Mardiya. Haƙiƙa Namra ta yi masa hallacin da ba duk mace ce take yi ma namiji irin wannan hallacin ba.
“Dole wata rana zaki dawo gare ni Namra, dole idan kika haifa min ɗa ki dawo kina so na idan na karɓe abu na, zaki dawo ki ga yadda Asim yake amsa sunansa a cikin garin Katsina, daga lokacin zan nunawa Ubanki iko na da kuma karfin kuɗi na”
Ya furta yana jefar da kwankwanin power horse ɗin sannan ya ciro wayarsa daga aljihu ya nemo number Sufiyan ya aika masa kira, be damu da ganin dare yayi ba ganin yake tun da yana biyansa kuɗi dole ne ko a wane lokaci ya yi masa abunda yake so.
“Hello oga Allah yasa lafiya ka kira ni a wannan lokacin”
Ya faɗa cikin muryar bachi.
“Lafiya ƙalau, kana da labarin Namra? ”
“Akwai labari oga amman da ka hakƙura har da safe”
“Ba zan haƙura ba, faɗa min kawai”
“Oga wannan monday da ta wuce ta fara zuwa makaranta, na bita har makarantar na ganta Mahaifinta ya ɗaukar mata sabon direba, amman oga sam babu alamun ciki a tare da ita, dole ne idan har akwai cikin da zai tsawon wannan watannin ya nuna ko da kaɗan nan, sam ban ga alamun tana da ciki ba, kuma kaga da tana da ciki da ba zata koma karanta ba yanzu”
“Ka tabbata?”
“Na tabbata oga”
Ya katse kiran yana lasa lips ɗinsa.
“Idan ko har kika yi kuskuren zubar da cikin nan sai kin yi nadama Namra, ke da ubanki sai na kaskantaku”
Yayi ƙwafa tare da busar da iskar bakinsa. Ɗan kishingiɗawa yayi kaɗan sai bachi yayi gaba da shi daman a kwai gajiya sosai a tare da shi. Be yi bachin awa biyu ba ya soma jin hancins ana mugun yaji numfashinsa na sama-sama sai sarƙewa yake, ba shiri ya farka a firgice sai hayaki ya turniƙe masa ido, duhu ya soma gani sai tari yake kamin ya waiga ɗayan gefensa ya hango bedrooms ɗin suna ci da wuta. Wani irin tsalle ya daka ya sai gashi gaban ƙofar falo yana ƙoƙarin ɓanɓanreta amman ina hayaƙi da tsage ƙofar. Mai gadinsa ne ya farko yaga halin da ake ciki ya fita neman jama'a abunka da unguwar masu kuɗi sai kowa yayi maaa banza sai gaba ɗaya mutane suka fiffito, daker aka samu aka ɓalle ƙofar falon, suka fito da Asim, domin hayaƙi ya turniƙe shi tuni ya faɗi a gurin yana haƙi.
Kan kace kwabo sai ga ƴan fire service mota kusan uku aka shiga kashe wutar, amman kamar ana ƙarawa, haka wutar ta riƙa ci har asuba, bata mutu ba sai da ta ƙone komai na gidan.
Ta ɓangaren Mardiya ma ƴan kashe wutar gobara ne suke ta kai da koma amman wutar da ƙi mutuwa, babu abunda yaba jama'ah tsoro kamar yadda wutar take ta sama kamar abar da ake sawa fetur, ba ɗakinsu wutar da tashi ba, amman bata rage komai da yake ɗakinsu Mardiya ba, har da kayan baƙi ƴan zuwa biki sai da wutar da cinye, sannan ka bi sauran ɗakunan gidan duk ta cinye.
Mardiya na maƙota aka faɗa mata, daman tun da aka fara bikin maƙota take kwana ita da ƙawayenta, ko da ta zo wutar ta ci har ta cinye babu abunda ya rage a cikin gidan, a take ta saka kuka ganin komai ya ƙone babu abunda take ji kamar kayan mutane da suka ƙone, babu daɗi ace kaje biki wani abu ya faru. Bata ƙara firgicewa ba har sai da wani abokin Asim ya zoɓya labarta mata halin da suke cikin ma ƙonewar da wacan gidan yayi wanda za a kaita.
Hannu ta ɗora saman kai ta fashe da kuka tana kiran ta shiga uku.
“Allah yasa ba wutar da nake mafarki bace take bi na ba, na shiga na lalace”
Kuka ta riƙa yi kamar mahaukaci sai da ka riƙeta ana bata haƙuri.
RASHIDA POV.
Bayan ta gama sallah azahar ta tashi tayi nafila sannan ta ɗauki carbi tana lazimi, haka take kullum cikin ibada take fatanta kawai Allah ya yafe mata kamar yadda mijinta da Kalsoom suka yafe mata, a iya yanzu ta yarda da ƙaddarar da Allah ya aiko mata kuma ta aminta babu mai iya yaye mata ita sai Allah, tabbas tasan Allah yana son ta tun da har ya ganar da ita tun gabanin ya karɓi rayuwarta.
Ta miƙa lamurranta ga Allah, kwata-kwata ta cire rayuwar daga yin aure dan tasan ba zata samu mijin da zai aureta ba, da ma kuma ta samu bata tunanin zata iya zama aure da namijin wanin Hilal. Daman ta daɗe da aje aikinta, duk wani abunda da take da buƙata Mahaifinta yana yi ma, abokanta kuma suna kawo mata ziyara a gidan, waɗanda suka wayanci miye hiv wasu kuma tuni sun ƙaurace mata gudun kar suma su ɗauka.
Ta ɗauki darasi a rayuwarta sosai, tun daga cin amanar aure da tayi, da kuma neman taimakon wanin Allah wato bokaye da ƴan duba, a iya kallon rayuwar Kalsoom da tayi ta fahimci darasin da yake tattare da itazm, tabbas wanda duk ya miƙa lamurransa ga Allah, lallai Allah yayi alƙawarin jiɓantar al'amarinsa, babu irin shige-shige da bata yi ba wajen ganin da raba Kalsoom da Hilal ko ta raba ta da lafiyarta amman addu'o'in da take suka mata kariya da katangar tsari daga duk wani sherinta. Hakan yasa itama ta tattara lamurranta ta miƙa wajen Ubangiji, ta samu natsuwa da kwanciyar hankali sosai, duk da tasan ciwon dake jikinta ba zai taɓa rabuwa da ita ba, amman tana Allah ya sanyaya mata zuciyarta har ta samu ƙarfin halin sakewa tana fita cikin mutane.
Bayan ta gama istigifari ta ɗauke carpet ɗin ta naɗe ta maida mazauninta, sannan ta nufi kitchen dan ɗora abunda zata ci. Vegetables soup ta girka da white rice daman likita yana yawan faɗa mata ta riƙa cin su. Falo ta fito ta zauna tana cin abincinta hankali kwance tana kallon tv, wayarta ce ta yi ringing sai ta miƙe tsaye ta ɗauko, murmushi ta yi ganin number Hilal a zatonsa zai sadata da su Ulfah su gaisa ne sai kawai ya miƙawa Izzah ta yi masa albishir ɗin Anty su ta haihu.
“Mashallah me aka samu?”
“An samu Baby boy, Momi Mai kyau sosai”
Wannan karon Ulfah ce take magana.
“Allah ya raya ashe kun samu ƙane ko? Ina dady ku?”
“Yana can gurin Anty be san mun kira ba, Momi Boy ɗin kato ne sosai kuma fari”
Ezzah ta faɗa with so much joy and excitement. Idon Rashida ya cika da ƙwalla dan har gobe har jibi tana son mijinta sai dai tasan yayi mata nisa.
“Zan zo gobe na ga Baby kun ji”
“Toh Momi”
Suka kashe wayar, ita kuma ta share hawayen idonta tana tuna lokacin da ta haifi Rafiq yadda Hilal ya dinga ɗauki kamar zai haɗeta ita da yaron.
‘Allah sarki duniya’
Ta yi furucin a zuciyarta, a fili kuma sai ta amsa salamar da Alhaji Bashir yake yayinda yake turo ƙofar falon ya shigo.
[7/21, 10:29 AM] Khadeeja Candy♥: *86*
“Miya kawo ka gidana?”
Murmushi yayi ya zauna saman kujera yana kallonta fuskarsa da annuri.
“Haba Hajiya ai ko baki san inda na fito ba kya saurara min ko?”
“Na fi ƙaunar ganin baƙin maciji da kai, bana son abunda zai sake kusantar da ni a gareka Alhaji bashir dan Allah dan Annabi ka tashi ka fitar min daga gida”
“Ban zo gidanki da wata manufa ba Rashida sai ta alheri”
“Babu alheri a tare da kai, dan Allah ka tashi ka bar min gidana”
“Miyasa kike alaƙanta rayuwar da kika shiga da laifina? Bayan kuma idan baki amince ba ba zan iya miki da ƙarfi ba?”
“Nasan nayi kuskure ai a lokacin shiyasa yanzu na tuba na koma gurin Ubangijina, kuma Alhamdulillah rayuwata da dai-daita”
“Nama ai tuban na yi shiyasa nake son dai-daita rayuwa da taki, har ga Allah Rashida ina son ki ba wai so na zina kawai ba, so na haƙiƙa kawai saboda babu yadda zan yi ne, ni da ke kukan mu munyi kuskuren faɗawa a halaka, ke saboda baki da lokacin da zaki tsaya ki bawa mijinki kulawa shi ma kuma ya baki, ni kuma na kasa ƙara aure duk da ina ganin sha'awar wasu matan saboda sherin da matata ta yi min, yanzu kuma Alhamdullillah na gane kuskurena kuma am ready to marry you idan kin aminta, saboda kin rufa min asiri a lokacin da ya kamata ki tona min, kin rufe bakin ki kin haƙura kin bar ni akan aikina, bayan kuma kina da damar da zaki tona min asiri, ki faɗawa duniya abunda muka aikata”
“Ban shirya aure yanzu ba Alhaji Bashir idan ma shi ya kawo ka ka tashi ka bar min gidana”
“Kin fi son ki yi ta zama a haka? Indai akan Asmee ne karki damu bata isa ta hanani ƙara aure ba yanzu”
“Baka tsoron ace ka auri mai cutar ƙanjamau?”
“Daga lokacin da kace zaka damu da matsalar mutane zaka saka kan ka ne kawai cikin matsala, ni da ke da Asmee duka muna ɗauke da abu ɗaya, miye amfanin ke na ƙyale ki akan gudun abunda duniya zata ce min? Zan yi ritaya gudun kyamar da za a nuna min gurin aiki, amman karki manta ina da hannu jari kuma ina da kasuwancin da zai iya riƙe jikokina ma ba ƴayana da matana kawai ba, ki yi tunani Rashida karki yaudari kanki akan abunda zuciyarki take muradi”
Yana kaiwa nan ya miƙe tsaye ya fice. Da kallo ta bishi tana sauke ajiyar zuciya, sam bata shirya irin wannan rayuwar ba, aure yanzu? Ita da yanzun tana jin ta samu sukuni a rayuwarta, taya zata yi aure ta sake jefa rayuwarta cikin wani halin kuma? Ita kan bata shirya kishi da Asmee ba.
KALSOOM POV.
Hilal kamar ya haɗe yaron dan murna, duk wanda ya ga Baby boy ɗin sai yayi mamaki ace da kanta ta haihu musamman da suka ji gida ta haihu, wasu daga cikin abokansa suka riƙa zolayarta wai ai matar doc ce dole ya karɓi haihuwarta. Hajiya ta nuna farincikinta sosai duk bayan kwana biyu sai ta zo gidan duba jikanta, Salman kam kullum tana biye da hanya, sai da aka kwana uku sannan Rashida ta zo ganin Baby shi ma kuma da dare, ta yi siyayya mai yawa ta kawo, sai dai bata yarda ta karɓi yaron ba duk da Kalsoom ta yi kawaicin miƙa mata shi, bata yi minti ashirin a gidan ba ta fito su Ulfah suka rakota har bakin mota ta basu kuɗi da chocolate.
Ranar suna Baby ya ci sunan mahaifin Hilal wato Abubakar aka yi masa laƙani da Rafiq. Fuskarsa sak ta Hilal yaro ya sha stickers har ya gaji, an raba abubuwa da yawa ranar sunan, da yamma aka yi walima ta gani ta faɗa, kuloli da manyan kofuna da agogo sai har ma da handbags masu kyau, wasu kuma su samu shoes.
An kashe kuɗi da yawa gurin walimar nan kai kace ma yanzu ne Hilal yake samun haihuwar fari, yadda ya zuba mata kayan barka ma a abun kallo ne, ga kuma waɗanda ta samu daga ɗai-ɗaikun mutane ƴan uwa da kuma abokan arxiki.
ABDOOL POV.
Tafiya yake shaddar dake jikinsa tana amsa amo saboda maiƙon da ke jikin shaddar da kuma sabuntakarta.
Ko da ya shigo part ɗin Ummi yana waya da Mai Martaba dake faɗa masa yana nemansa, a falon ya zauna sai da suka gama tattaunawa sannan ya kalli Ummi da ke cikin shirin ta na fita ya ce
“Ummi fita zaki yi?”
“Eh Asibiti zan je na duba Hajiya Sadiya kasan ciwon nata ya zama abunda ya zama, kuma kaima ya kamata ace ka duba ta, tuɓ da ta kwanta asibitin nan baka taɓa zuwa duba ta ko sau ɗaya, wai anya ma ka mata gaisuwar yarinyar ta da rasu?”
Ya shafa kansa yana murmushin rashin gaskiya.
“Kin san ko da ta rasu ina Abuja, amman dai na kirata a waya”
“Abdallah baka da kirki sam, kai kullum aiki ƴan uwanka ma baka da lokacin ziyartarsu? Sai yaushe zaka huta ne?”
“Ai yanzu zani iya zuwa na mata gaisuwar daga nan na duba jikin nata”
“Allah ya sauwaƙe maka wannan rayuwa, wai ya maganar yarinyar nan ne?”
“Muna nan muna ta sutsa kai, yanzu haka maganar da Mai Martaba yake min kenan, yace min yayi magana da Abbah”
“Ban gane ba, ita bata son ka ne?”
“To gani dai wani ne yake min zagon ƙasa, ita kuma tana min jan aji, yanzu haka anjima kaɗan gurinta zanje, domin hankali yaƙi kwanciya tun lokacin da yaron nan na zo gidansu, last week ma da naje gidan kamar...”
Sai kuma ya fasa maganar ya miƙe tsaye.
“Muje na dubata Ummi, sai na wuce airport flight zan hau”
“Ka fara bani labari baka ƙarasa ba, zan ƙarasa”
“Zan ƙarasa miki idan na dawo”
“Ƙanenka dai ga su nan sai himmar fitar da maza suke kai kana nan”
“Nima ina kan hanya”
Dariya ta yi ta miƙe tsaye suka fita tare. Kai tsaye asibiti suka nufa, ko da suka shoga ɗakin tana kwance wata ƴar'uwarta tana jinyarta, ta rane sosai bakinta duk ya bushe, Abdool ya ji tausayinta sosai da sosai, duba da yadda take damawa kuma gata mai jiki amman yanzu ta dawo haka. Tana ganin Ummi ta fara hawaye.
“Nikan tawa ta ƙare, Nabila ta tafi ta bar ni”
“Kiyi haƙuri Hajiya Sadiya duk mai rai mamaci ne, duk haka ƴaƴanki suke mutuwa kuma ki haƙura, na san Nabila ita kaɗai ta rage miki amman Allah baya barin wani dan wani, dan Allah ki sawa zuciyarki sassauci”
Shiru bata ce komai ba, sai hawaye take ita kaɗai ta san dalilin mutuwar Nably kuma ita kaɗai ta san dalilin wannan ciwon nata.
“Sai Yaushe zasu sallame ki ne?”
Ummi ta sake tambaya. Wacce ke jinyarta ta kada baki tace
“Ba yanzu ba, wai sai sun mata aiki”
“Aiki kuma?”
.
“Eh wai wasu abubuwa ne a cikinta masu kamar ƙanƙara sun ce dole ne sai anyi aiki za a cire”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. To Allah ya sauwaƙe, amman da waje aka je naga sun fi ƙwarewa a irin aikin nan”
“Nima haka na ce mata, amman ta ƙi”
“Allah ya bata lafiya ai da nan da can duk ɗaya a gurin Allah”
Wannan karon Abdool ne ya faɗa yana kallon agogon hannunshi. Dubu talatin da ƴar siyayya Ummi ta aje mata sannan suka taso muna mata Allah ya sauwaƙe ya bata lafiya.
A mota Ummi take ta labartawa Abdool irin rayuwar da suka yi ta ƙurciya, yadda aka riƙa ta a gidansu da kuma irin nasarorin da tada samu a rayuwarta.
“Kai Mai rai ba komai ba ne”
Abdool ya faɗa yayinda yayi parking a harabar gidansu. Cikin yanayin damuwa da jimami Ummi ta fita daga motarsa, shima ya fito yana faɗa mata yanzu zai kama hanya.
“Allah ya tsare ya kiyaye ya kuma kai ka lafiya”
“Amin Ummi”
Sai da ya shiga part ɗinsa ya fito, sannan ya shiga wata motar direbansa yayi driving ɗinsa zuwa airport.
***
An sake fitar da shi waje kamar yadda Abbah yayi alƙawari, sai dai tun daga lokacin Abbah be sake leƙa asibitin da sunan yazo ganinshi ba, wani kuma daga gidan be sake zuwa ba, duk da ƴan'uwa sunta ƙoƙarin shiga tsakani na ganin an sasantashi da Abbah, amman Abbah be saurara ba dan ya riga ya bashi baya a yanzu, kuma duk wanda ya ji dalilinsa dole yayi masa uzuri, dan kaf a ƴaƴan ƴan'uwa Abbah ya fi son Uzair da kowa. Babu wanda be yi mamakin jin abunda Uzair ya aikata ba na neman maza ƴan'uwansa, a lokacin ne wasu ke cewa ashe Namra tana da gaskiya, wasu kuma su labarta tsegumi da zargin da suka ji ana masa, daman abun duniya baya ɓoyuwa. Har kuma tsawon lokacin Yasmin bata taɓa zuwa ta duba shi ba ko da sau ɗaya. Shi kam duk ya biya rame ya lalace, sauƙi ɗaya ya samu yanzu yana iya tashi zaune,ko ya kwantar da kansa, kuma ya kam miƙa hannunsa ya ɗauki abu ko ya karɓo, sai dai bayan haka babu wani abu da yake iyayi ma kanshi.
Bayan ya gama cin abinci likita ya shigo ya duba shi, ya bashi magani sai kuma yayi masa allura, sannan ya rubuta wasu ya bawa Umma yace a siyo masa su. Sai da ya fita Umma ta rafka uban tagumi tana kallon ɗanta, tabbas be kyautawa kansa ba da ya saka kansa a wannan rayuwar, gashi yanzu kowa ƙyamarsa yake ana masa kallon kamar ba mutum ba, shi kansa a yanzu ya gane ba kowa ba ne, duk abokaninsa sun guje shi cikin ƴan watan ni sun manta da shafin rayuwarsa ga matarsa ta nuna masa tsantsar ƙiyayya, yanzu da Mahaifiyarsa bata raye haka rayuwarsa zata ƙare kenan a wulaƙance?
Turo ƙofar da akayi ne yasa duk suka ɗago suka kalli ƙofar daga shi har Umma, Yasmin ce sanye cikin suit da alamu daga gurin aikinta ta biyo asibitin. Ba Umma kaɗai ba shi kansa da yake mijinta sai da yaji tsoron zuwan nata.
“Miya kawo ki mi kika zo ki yi? Ai na ɗauka kina da zuciyar da ba zaki iya taka ƙafarki ba ma a asibitin sai idan ya mutu a akai miki gawa, wai ke nan har kin isa ki wulaƙanta mijinki akan wannan abun daya aiakata, kowa fa be wuce ƙaddaraba, mutane nawa ne suke zama da mijinsu bayan kuma sun san mijin yana aikata irin wannan abun, amman su rufa masa asiri su zauna da shi”
“Matan da suke rufawa mazansu asiri akan wannan aikin suna yi ne akan kwaɗayin kuɗin mijin, ni ko na dan dukiya na auri Uzair ba, wasu kuma suna yi saboda ƴaƴansu, ni ko ya keta haddin ɗa na, ko be faɗa miki yayi raped ɗa na ba? Idan be faɗa miki ba to yau ki sani, kuma dalilin zuwa na a nan saboda ina son na karɓi takardata ne, idan kuma be shirya sakina ba ni na shirƴa kai shi kotu”
Yasmin na maganar hawaye na zuba a idonta, hannu Umma tasa ta rufe baki tana kallon Uzair, furucin da Yasmin ta yi a yanzu yayi nauyi, sai dai ta fahimci gaskiya Yasmin ta faɗa tun da ya kasa ƙaryatata har ma ya sadda kansa ƙasa yana hawaye.
Yasmin ta kalleshi tana share hawayenta
“Ka daina yaudarar kanka da sunan wani yayi maka asiri, mugun abunda kake aikatawa ne ya kama ka, kuma Allah ya yanke maka wahala komai ya zo maka da sauƙi, da ace kana da lafiyarka wallahi da ko wace jarida sai ta buga hoto na da naka, dan sai na bawa duniya mamaki da kai mijina kuma uban ƴaƴana kotu, kuma ko yanzu ka taki sa'ah ne mahaifiyata ta hana ni, amman idan har shiga kotu kake so ka yi ƙoƙarin yin jayayya da ni akan aurena...!”
Juyawa ta yi ta fice tana kuka. Ajiyar Zuciya Umma ta sauke cikin muryar kuka ta ce
“Abun naka har ya ɓace Uzairu, wannan ba halina ba ne kuma ba halin Baban ka ba ne, ban san inda ka ɗauko wannan rayuwarba, yanzu a ce har ɗan cikin ka zaka aikatawa wannan abu? Ko a masu yi ƙoƙarin kare iyalinsu suke kada su faɗa wannan halaka balle kuma har su saka su da kansu, abun da naki ji a redio yau a gidana zai faru? Na yi tunanin ko zafi ciwo ne yasa ka faɗar haka a baya ashe dai da gaske ne, Uzairu baka kyautawa kan ka ba”
Ta rufe fuska tana kuka. Shi kan hawaye yake sai a yanzu yake ayyana zancen Allah na cewar cikin matan ku maƙiyanku, a cikin ƴaƴanku akwai maƙiyanku, ji yake kamar ma shi aka saukarwa ayar dan tsanar da Yasmin ke nuna masa ta yi yawa.
Wasa-wasa abu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa magani yake amman babu sauƙi, haka ya kwashe wata shida a asibitin sannan aka sallamoshi ya dawo gida gurin Umma. Daman tun a asibiti aka siya masa keken guragu yana tura kansa a ciki duk lokacin da wani abun uzuri ya same shi ko kuma yayi sha'awar fita waje.
Ranar da Yasmin ta samu labarin ya dawo gida, ta samu Mahaifiyarta a falo akan maganar shigar da shi kotu tun da har yanzi ya kasa aiko mata da takardarta.
“Wai ke Yasmin wace irin zuciya ce da ke haka? Ke bakya ganin tausayinsa ne? Ki duba halin da yaron nan yake ciki wannan kawai be isa ya saka ki barshi da Allah ba, ai da Allah ya tashi kama shi sai ya kama shi ta wannan hanyar da babu wanda ya isa yai masa magani sai shi, ko ba komai fa Uzair ɗan'uwanki ne Yasmin ya kamata ki riƙa tausayinsa, sannan uban ƴaƴanki ne, ko ƙin ki ko kin so kin riga kin haihu da shi, nan gaba kina tunanin yaransa zasu ji daɗi idan suka samu labarin abunda kika yi ma Ubansu?”
Fashewa ta yi da kuka
“Idan na fita wani lokacin har nuna ni ake, na rikice gaba ɗaya yanzu ko gurin aiki ba komai nake ganewa ba, so nake ya sake ni ko na samu sukuni na natsu”
“Damuwace kika sawa ranki, bayan kuma be kamata ya dame ki, tun da ba ke kika ƙaddarawa kanki wannan rayuwar ba, focus on your journey ki cire komai a rankiz ina nan ina miki addu'a da sannu komai zai wuce”
Tashi tayi ta shige ɗaki tana kuka.
NAMRA POV.
Satin Hajiya Barau biyu ta Abbah ya dawo da ita saboda haƙuri da ake bata da kuma ganin idon ƴaƴanta, ita kanta yanzu ta saduda dan satan bata kyauta ba, duk abunda take tana yi ne dan kishin Anty Amarya tana ganin kamar Abbah yafi sonta da ita.
Ga kuma ƴaƴanta da suka sata gaba suka nuna mata rashin jindaɗinsu, ko ba komai dai ya ga ishara a zmfitowar da ƴarta tayi wato Zinatu, yanzu ba Namra ba ce kawai take zawarci a gidan har da ƴarta da uwar miji ta hanawa zama.
***
Anty Amarya na kallonta ta yi murmushi.
“Wannan shaddar duk tsadarta Lamido zaki bawa?”
Ta gyaɗa kai tana murmushi.
“Lallai ana jin Lamido nan, kar fa ya karɓe min faɗar ɗa”
Dariya ta yi wannan yaron tana shafa shaddar.
“Anty kina jin ɗan nan na ki”
“Ai bana da kamar sa ne Namra, kema kuma idan ba kin yi butulci ba baki da kamarsa, abubuwan da kike masa basa min daɗi, yaron nan yana son ki wallahi, kin san yafi ƙarfin wulaƙanci idan ba ke ba babu wacce ta isa ta wulaƙanta namiji kamar Abdallah”
“Ba wulaƙanci ba ne Anty, ni rayuwarsa ce bana so, ya cika zafin kishi, kuma bana jindaɗin abunda yake ma Lamido”
“Ai naji mahaifinki yana zancen sama masa aiki dan yace ya kusa barin driving ɗin ki”
“Saboda me?”
“Nima be faɗa min ba”
Ta faɗa fuskarta da Murmushi. Namra ta baro gurin da take zaune ta zauna kusa da Anty.
“Dan Allah Anty ki faɗa min”
“To aure zai miki”
“Anty Aure yanzu? Ni gaskiya ban shirya ba, halin mazan zamanin nan duk yaushe na fita daga wannan rayuwar kuma za a ce na sake wani”
“Toh sai ki tashi ki faɗawa Mahaifinki ai yana part ɗinsa”
Ta yi saurin rufe baki tana dariya, sai ta tashi ta ɗauki shaddar ta fice. Murmushi Anty Amarya ta yi tana unƙurin tashi ta nufi part ɗin Abbah.
Yau weekend ce daman babu aiki kuma babu wani taro ko wani abun da zai fitar da Abbah, dan haka yana part ɗinsa yana hutawa. Da sallama ta shiga, ya amsa mata yana kallon labaran bbc. Plate ɗin dake kusa da shi da ɗauke ta aje ƙasa ta zauna bakinta ƙumshe da murmushi.
“Yanzu na ke shirin kiranki”
“To Allah yasa samu ne”
“Samu ne kan, ɗana nake nemawa auren ƴarki idan kun aminci”
“Ai Abdool ɗana ne ba ɗan ka ba, ni ya kamata na nema masa aure”
Dariya Abbah yayi yace
“Amman miya hana ya biyo ta gefen ki? Ko dai ƴarki bata son sa ne? Bana son na sake mata wani zaɓin ne wanda ba shi ranta yake so ba, kar a sake samun matsala”
“Ba wata matsala, yanzu haka maganar da na gama da ita kenan”
“Toh Allah ya shige mana gaba, amman zan so jin ta bakin Namra”
“Ai gaka gata, waya isa ya shiga tsakanin uba da ƴa?”
Anty Amarya ta faɗa tana dariya.
*** *** ***
Kai ya girgiza mata alamar ba zai karɓa ba.
“Ba dan ki bani abu na zo gidanku ba”
“Ni ma na sani shiyasa na siya maka wannan shaddar, da wata manufa na yi ba”
“Na sani na gode?”
“Ba zaka karɓa ba kenan?”
“Gaskiya bana so”
Miƙewa ta yi tsaye ciki da jin haushin ƙin karɓar da yayi ta baro garden ɗin. Ko da ta shigo falo wayarta dake kan kujera tana ringing cikin sauri ta kai hannu ta ɗauka, Abdool ne rubuce a screen ɗin wayar. Tsayawa tayi kallon wayar sannan ta danna picking ta kara a kunne.
“Abnam gani kan hanya?”
“Ba zaka daina yi min zuwan ba zata ba ko?”
“Zan daina daga ranar da kika zama mallakina”
“Allah ya kawo ka lafiya”
“Amin Sweet Abnam thank you”
Shi kanshi baya son zuwan ba zata da yake mata, sai dai yana yin hakan ne dan ya riski Lamido gani yake kamar ya tare masa komai ƙara dai ya riƙa masa ba zata yadda zai riƙa fahimtar alaƙar dake tsakaninsu.
Kitchen ta shiga ta sarrafa masa abu mai sauƙi sannan ta haɗa masa fruit salad dan ta fahimci yana son sa sosai. Sai kuma ta shiga ta yi wanka ta saka abaya da jan mayafi. Tana jin lokacin da mota ta shigo harabar gidan kuma zuciyarta ta ayyana mata shi ne, amman saboda ƙarfin hali ta ƙi ta fita ta tarbe shi, har sai da ya buga ƙofar falon.
Turare ta ɗauka ta feshe jikinta sannan ta fito falo taje ta buɗe masa ƙofar, jinginawa yayi yana kallonta fuskarsa sa annuri, sai dai hakan be ma murmushinsa damar fitowa ba.
Yadda ƴake kallonta ta yi zaton zai ce mata tayi kyaune kamar yadda ya saba sai kawai taji ya ce.
“Ina Anty?”
“Tana ciki, ka shigo mana”
“No ba sai na shigo ba, ai baki bukatar ganina”
“Nace maka? Abdool miyasa kake irin wannan maganar ne? Sai kace wata maƙiyiyarka kace bana son ganinka”
Ya wara ido.
“Wasa nake miki fa, ai nasan ni kika yi wa wannan kwaliyar”
Sai kuma ta ji kunya.
“Zaka shigo ko part ɗin Abbah zaka je”
“Cikin wata tara kin zama wata babbar mace”
Ya salam. Ta juya ya bar masa jikin ƙofar, sai kawai yayi murmushi ya shigo. Daman gidan ba baƙonsa bane sai dai duk lokacin da zai zo Abbah ne kawai yake sanin shigowarsa garin. Kasa sakewa Namra ta yi haka take duk lokacin da ya shigo part ɗin shi kuma sai ya bi ya tsare ta da ido duk wani motsi nata yana idonsa.
Fruit salad ta fara kawo masa da ruwa sai kuma pineapple juice da ta haɗa masa. Gabanta sai faɗuwa yake kar Anty ta tararda su, tana jin kunyar Anty ta ganta da Abdool sosai.
“Gaskiya na yi sa'a, Matata ga iya abinci ga iya kwalliya ga haƙuri da kawaici”
Ƙasa ta yi da kanta tana murmushi, this is not the first time da yake yaba girkinta a duk lokacin da ta girka masa wani abu.
Kamar munafuka haka take satar kallonsa, yana mata kyau yau fiye da ko yaushe, ga wani ƙyalli da fuskarsa take.
Ƙarar da wayarta ta yi ne ya dukan su suka kalli wayar, ita sam ta ma manta da wayarta tana saman kujera dan tun da tayi waya da shi ta aje ta a gurin. Hannu ya kai ya ɗauka.
“Waye Dr Faruk?”
“Likita na ne”
Ido ya sakar mata kamar be yarda da maganarta ba, kuma yaƙi ta bata wayar sai ringing take.
“Me zai sa ya kira ki yanzu? Baki da lafiya ne?”
Kasa amsa mashi ta yi. A take yanyinsa ya canja sai kawai ya miƙe tsaye ya aje mata wayar ya fice, zuciyarsa na masa mugun zafi.
AMIRA POV.
Kullum cikin ɗaki ta wuni duk tabi ta takura kanta, akan abunda ta san har a bada ba zai taɓa zama nata ba, babu yadda Ammy bata yi akan ta riƙa fita tana shan iska amman ina, har ta gaji yanzu ta saka mata ido sai kuma addu'ah da take mata.
Cikin rashin ƙwarin jiki ta fito ta daga ɗakinta ta haɗawa kanta tea, bayan ta haɗa tea ta zauna a falo, saboda ta samu falon babu kowa a ciki sai tv dake ta aikinsa.
Ƙofar falon aka turo aka shigo, mai gadinsu ne, hannunshi riƙe da wasiƙa, sai da kai ƙasa sannan ya miƙa mata takardar.
“Gashi inji wasu mutane suka ce a baki”
“Su waye?”
“Wlh nima ban sani ba, cikin mota suke kuma sun tafi”
Hannu ta kai ta karɓa, shi kuma ya tashi ya fice, sai da ya fita sannan ta warware takardar ta fara karantawa...
ASIM POV.
Yanzu tsawon wata tara kenan ana abu ɗaya, a duk lokacin da ya gina gida da sunan Mardiya sai gidan ya ƙone, idan ya kama haya ma abu ɗaya ne, tun lokacin da aka ɗaura auren ta gagara tarewa sai dai su kwana a hotel ko kuma gidan abokai, dan ko lokacin da aka ɗaura auren hotel ya kama mata, baya jin zafi cire kuɗi ya gina mata gida ko ya zuba mata dukiya amman ta kasa mararta saboda yawan gobara da take. Ita kanta yanzu abun yana damunta sosai, musamman da ta samu labarin Asim yana neman auren ƴar masu kuɗi, tasan babu namijin da zai juri zama da ita tana gora dole ko wanene ya nemin ƙarin aure, ga mafarkin wutar da take har yanzu bata daina ba, lallai haƙoƙan mutane da yasa yana kanta, domim ba Namra ce kawai ta taɓa cuta ba, mutane da tayi ma cuta suna da yawa ga satar da tayi ta yi, ga kuma yawan banza data ɗaukarwa kanta. Shi kansa Asim sai yanzi ƴake gane yayi zaɓen tumun dare, dan duk ƙyalƙyalin da yake hangowa sai ya tarar na ɗan maciji ne, be same ta a budurwa ba, kuma daman be aureta dan Allah ba, auren sha'awa yayi mata daga lokacin da ya kai ga jikinta sai duk da fita ranshi daman yanzu ba maxe ba burgeshi take ba, wannan ma da zai aureta dan kawai kariyar kai ne, kuma yana son ganin shi wutar take bi ko Mardiya.
Babu irin neman taimakon da ba ayi ba akan wannan matsalar, wani gurin ace aiki ne aka mata wasu kuma su ce iska ne yake mata, tana zuba kuɗi da yawa dan ganin ko za a dace amman babu wani sauƙi sai abunda ya cigaba.
A unguwa kuma sai gulma ake mata kowa da irin abunda yake faɗa, waɗanda suka san halinta suce amanace ciki har da masu cewa ai taci amanar Namra tun da ta aure mata miji....
[7/22, 10:00 PM] Khadeeja Candy♥: *87*
NAMRA POV.
Shiru-shiru bata ga Abdool ya dawo ba, hakan ya tabbatar mata da fushi yayi. Miƙewa tayi tsaye ta fita sai ta hangoshi jikin motarsa yana kallon ƙofar falon. Ƙarasa tayi cikin wani taku mai jan hankali da ƙasaita, ta rumgume hannayenta tana kallonshi.
“Ina da matsalar mahaifa ne Abdallah, ciki baya iya tsayawa tun ina gidan Asim, wannan matsalar ce tasa Dr Faruk ke kula da lafiyata”
Uffan be ce mata ba, sai kawai ya kawardar fuskarsa yana kallon part ɗin Abbah.
“Abdallah...”
“Abnam...”
Ya kira sunanta kamar yadda ta kira nashi, still be kalleta ba.
“Baka yarda da ni ba ko?”
“Babu rashin yarda a tsakani na da ke, sai dai zai fi idan muka bar maganar nan”
Murmushi tayi ta juya koma ciki. Haka ya tsaya a gurin har sai da yaji ya samu sassauci a zuciyarsa sannan ya nufi part ɗin Abbah. A falo ya samu Abbah daman yasan da zuwansa sun samu awa ɗaya suna tattauna akan rayuwa da abubuwan duniya sam ba zaka ce Abdallah ne yake neman auren ƴar Abbah ba, sam ba zaka ce surukinsa ba ne.
*ONE MONTHS LATER...*
Har yanzu jikinsa na nan a yadda yake, Umma yanzu na hausa take nema masa wai ko Allah zaisa a dace.
Bayan ya gama shan magani ya turo kekensa ya fito harabar gidan. Wayarsa dake cikin aljihun wandonsa ya ciro ya kira Tahir.
“Bros ya ne, ya jikin naka ne?”
“Alhamdullah, ya aiki?”
“Mun gode Allah”
“Tahir tun ranar baka sake ce mun komai, ko baka kai mata ba ne?”
“Wallahi na kai mata, sai dai ban ji wata magana daga gareta ba, Uzair ina son na.baka shawara akan rayuwa, ka yi haƙuri ka rumgumi ƙaddara, wannan abun da ka gani na ishi kowa ishara ni kaina wannan ciwon naka yasa na zubar da duk wata muguwar da nake da ita, ba kai kaɗai ba, yawancin duk mai aikata irin wannan matsalar ce take faɗa musu, ka duba lamarinka Uzair ba haɗarin mota ka yi ba, ba kuma faɗowa kayi daga wani guri ba, haka kawai rana tsaka ance ka kamu da irin wannan ciwon, ita kanta Amira yanzu ta kanta take balle ka zargeta da aikata maka wani mummunan abu”
Tun da Tahir ya fara masa maganar jikinsa yayi sanyi, be san lokacin da hawaye suka zubo masa ba, lallai maso rai wawa, haƙiƙa yanzu Tahir ya lurar da shi abunda be kasa ganewa.
“Na gode”
Shine kawai abunda ya faɗa ya katse kiran. Hawaye na cigaba da masa zuba, tabbas wannan kawai ya isheshi ishara, a yanzu idan ba Mahaifiyarsa babu kowa a tare da shi, zai barwa ɗansa mumman tahirin da ba zai taɓa goguwa ba har a bada.
Kekenshi ya tura ya koma cikin falon, ƙanensa na zaune sai sha'aninsu suke ko kula da shi basu yi haka ya tura kansa ya shiga ɗakin da aka ware masa ya zamo kamar nasa. Farar takadarda da ya gani a saman gadonshi ya kai hannu ya ɗauka.
Sammaci ne daga kotun high court, ganin sunan Yasmin yasa shi murmushin da ya fi kuka ciwo, sannan ya sake tura kekena ya fito falon yana tambayar wanda ya kai masa wasiƙar.
“Ɗazu ne kana shan magani aka kawo, na shiga ban ganka ba shine na aje saman gadonka”
Ƙaramar ƙanwarsa ta faɗa. Sai kawai ya kaɗa keken ya nufi ɗakin Umma.
***
Hankalin Mai Martaba ya kwanta yanzu, har ma da na Ummi. Ganin an tsayarda magana, ranar da Mai Martaba ya aika aka yi maganar aure har da sadaka sai da yayi. Sai dai tun daga lokacin magana ta riƙa zuwa tana dawowa akan Abdallah zai auri bazawara, abun mamaki ne mutun kamar Abdallah ace zai auri bazawara kuma ɗan Sarkin Ƙatsina, wanda hakan sam be yi ma Mai Martaba daɗi ba, sai dai ya kan zuciyarsa nesa domin kawai ya farantawa ɗansa, domin yasan Annabi ma ya auri bazawara kuma yana sauranyinsa.
Ita kanta Ummi tana shan magana akan aure wasu su ce kar ta barshi wasu kuma su ce kamata yayi ya haɗa biyu. Sai dai duk wannan maganganun da ake be taɓa zuwa kunnen Abdool ba, ko da wasa ƴan'uwa da abokai basu taɓa masa wannan maganar ba, saboda sun san waye Abdool idan yana yin abu yana yi ne no matter what, ao faɗa mishi irin wannan maganar zai sa ya ɓata da kai ne kawai, ko kuma kai ma ya faɗa maka marar daɗi, sai dai abokai sun ka zolayeshi cikin wasa. Babu abunda yayi masa daɗi kamar auren da Abbah be yarda aka saka nesa ba, shi kansa da ansaka auren nesa zai roƙa a rage ne, domin ya matsu ya ɗauke Namra daga gidan. Ta ɓamgare ɗaya me yake jin zai iya zame masa matsala karatunta da take yanzu.
NAMRA POV...
Babu inda zance baikon Namra be kai ba cikin garin Sokoto da kewaye, a social media kan ba zaka iya lissafawa ba, babu abunda zai baka mamaki kamar ace bazawara ce aka yi ma wannan kayan, kuma duk da sunan an gani ana so abunda aka san budurwa ake yiwa. Kayan ƙwalah da maƙulashe ba zaka iya ƙigarsu ba, ga akwati goma da aka sako na tufafi har da zinari duk a cikin an gani ana so, kowa abunda yake faɗa to lefen me za'ayi?
Ba a gidan aka kawo kayan ba, daman haka Abbah yake duk lokacin da za a yanka ma ƴaƴansa sadaki ko a kai lefensu, gidan ƴaƴanshi yake turawa.
Ko da ake hidimar kai kayan Namra tana makaranta a lokacin duk da yake asabarce amman a ranar tana da darasin (lecture) da zata ɗauka a makaranta, bayan sun gama tayi sallama ta abokanta ta nufo gurin da tasan Lamido ya saba tsayawa ya jirata.
Ko da ta isa yana zaune cikin motar buɗewa kawai ta yi ta shiga ta zauna sai kawai taji ya ce
“Congratulations”
Tasan abunda yake nufi, yanayin muryarsa ya karantar da ita baya cikin daɗin rai.
“Na amince da auren Abdallah ne saboda mahaifina, kuma na san kai ma baka ƙi goya min baya ba wajen amincewa da hakan”
“Abdallah ya kasa ni, daman ya faɗa min zai kasa ni, ta tabba yanzu shi ne a zuciyarki ba kowa ba”
“Ya faɗa maka? Alfahari yayi, fariya yayi da zai kasa ka? Yaushe bakin ka ɗa nashi ya taɓa haɗuwa?”
Yayi ma motar key yana cigaba da magana a hankali.
“Bayan tafiyarki, abubuwa da tawa sun faru, ciki har da dalilin zuwa neman aurenki, da kuma neman zama direba a gidanku...”
Ta gyara zamanta a gidan bayan da take.
“Ban gane ba dan Allah ka ƙara min bayani, karka ɓoye min komai”
“Bayan kin bar Kaduna da kwana biyu, Yarima yasa aka ɗauko ni daga Kaduna aka kawo ni Katsina, mahaifata garin da ƙabarin ubana yake, kuma garin da nayi alƙawarin ba zan sake takawa ba.....”
Kamar wanda ya tuna abu sai kawai yayi shiru ya cigaba da driving ɗin da yake. Ita kuma gaba ɗaya natsuwarta ta bar jikinta hankalinta ya karkata kan labarin da Lamido ya fara bata...
IS BETTER THAN NONE... 😎 YI HAKURI DA SHORT CHAPTER 🙏
[7/23, 9:21 PM] Khadeeja Candy♥: *88*
“Ka tsayarda motar nan Lamido”
Ta faɗa a tsawace, umarninta yake bi tunda danta yake wannan aikin, a dole ya faka mota a gefen ti-ti, sai dai be juyo ya kelleta ba balle yace mata wani abu.
“Miyasa Abdallah ya sa aka kai Katsina? Miya ce maka? Miya faru bayan na baro Kaduna?”
“Faɗa miki abunda ya faru ba zai yi maganin komai ba”
“Wata ƙila zai yi wata ƙila kuma ba zai yi ba, amman faɗin shine mafi a'ala”
“Ni da Mahaifina asalin mu fulanin Katsina ne, mahaifiyata kuma ƴar asalin jihar kano ce, mahaifina ɗan kasuwa ne ya kan ɗauki kaya daga Katsina ya kai Kaduna idan ya siyar sai ya siyo na Kaduna ya kawo Katsina da hakan abun nasa ya girma, har ta kai ya kan ɗauka daga Katsina ya kai Nijar, a lokacin muna ƙanana, iya gata mahaifinmu ya nuna da kulawa mun taso cikin jindaɗi, arkizin mahaifinmu ya bunƙasa cikin ƙanƙanen lokaci, sai dai mahaifin mu be da amini irin Alhaji Mu'azu, ita kanta mahaifiya bata da ƙawa irin Hajiya Zuwaira, ba unguwar mu ɗaya ba, amman duk ranar weekend sai an kawo yaranta gidanmu su yi weekend, bana da wayo sosai a lokacin, amman ina jin yadda Mahaifina yake faɗin idan har ya haɗa wannan kuɗin ya tura aka turo masa kaya zai samu kuɗi sosai, haka ya tattara komai na shi ya haɗa kai da Aminsa ya tura kudaɗensa masu yawa sosai. Shiru-shiru babu kaya babu labarinsu, har ta kai mun fara shiga wani hali na ha'ila i, Alhaji Mu'azu ne yake aiko mana da cefane wani lokacin kuma har da ɗinkuna da wasu abubuwan na more rayuwa, ashe duk wannan yana masa ne a cikin kuɗin da yake binsa, wata ranar Assabar mahaifina yake labarta masa kayansa suna nan zuwa, har an kamo hanyar nigeria da su ta jirgin ruwa, haka muka ɗauki tsawon wata ɗaya muna jiran isowar jirgin, sai kawai dirar ƴan sanda muka gani a gidanmu, wai ana zarginsa da safarar muyagun ƙwayoyi, haka suka tisa ƙeyarsa a gaba suka tafi da shi, sau ɗaya suka bar mu muka ganshi tun daga lokacin ba mu sake ganinsa ba, sai dai abokinsa ya zo ya faɗa mana cewar ana nan za a sako shi, amman shiru har Allah ya karɓi ransa. Bayan rasuwarsa Alhaji Mu'azu yake faɗa mana cewar babu dukiyar Mahaifinmu ko taro a hannunsa, sanadin haka muka bar garin Katsina ni da Mahaifiyata, sai muka koma garin Kaduna da zama wato mahaifarta, a gidan data gada gurin mahaifinta, tun daga lokacin garin Katsina ya fita daga raina duk da kasancewar a nan mahaifar ubana take, sai sai bayan rasuwar mahaifina babu wanda ya sake waiwayar mu a cikinsu”
Namra ta share hawaye idonta cike da tausayawa ta ce
“Ba shi na tambayeka, abunda Abdallah yayi maka na tambaye ka”
“Abdallah yasa an ɗauko ni daga garin Kaduna aka kawo ni Katsina saboda kawai yana ɗan sarauta kuma ɗan mai kuɗi yafi ƙarfin ya bar garinsa ya zo kaduna saboda ni”
“Har yanzu baka faɗa min dalilin ɗaukoa da yasa aka yi ba”
Shiru be sake ce mata komai ba, hara aka kira sallah la'asar, tasan ba zai faɗa mata ko minene a yanzu ba. Zata sake magana wayarta ta yi ƙara number Abbah ta gani cikin sauri ta yi picking.
“Gamu nan kan hanya”
Shine kawai abunda ta faɗa ta sauke wayar. Shi kuma ya tashi motar suka hau ti-ti. Ta madubin gaban mota take kallon yadda hawaye suke zuba daga idon Lamido.
Sai da suka kusa isa gida sannan ya ciro handkerchef ɗinsa ya share hawayensa. Yana faka motar ta buɗe ta fito sai shi ma ya buɗe ya fito ya miƙa mata keys ɗin motar.
“Aikina ya ƙare daga yau! Gobe zan kama hanyar garin mu”
“Ba a gurina ka karɓi keys ɗin motar ba, ba ni na ɗauke ka driving ba”
Tana bashi amsa ya gyara tsayuwar littafan da ke hannunta ta nufi hanyar falo.
Tana shiga Maryam da Wasu old friends ɗinta suka jo kanta suna mata murna da zolaya. A abubuwa biyu ta samu kanta, farincikin da akasinsa, ba data dalilin yin duka biyu ɗin, dan har ga Allah bata shirya aure a yanzu ba, sai dai babu yadda ta iya tun da Abbah ya nuna yana son ta yi, a ɗayan ɓangaren kuma idan ta tuna halin da Lamido yake ciki sai ta ji Abdool ya fita a ranta. Cikin ƙarfin hali take musu dariya tana nuna musu farincikinta sannan ta wuce ɗakinta. Littafanta ta jefar saman gado ta shiga banɗaki ta yi alwala, ko da ta fito wayarta na ringing, wasu kawayenta ne na makaranta hakan yasa bata ɗauka ba, tasan ba zai wuce su taya ta murna ba, ko kuma su faɗa mata yadda zancen engaged ɗin ta ya cika social media. Har ta saka Hijab ɗinta sai wayar ta sake ringing wannan karon Abdool ne, tana son magana da shi sosai hakan yasa tayi picking tana aika masa sallama.
Ya amsa mata yana ƙarantar saƙon dake cikin muryarta na ranshin daɗin rai.
“Tell me i'm wrong, amman kamin ki yanke hukunci ya kamata kisan duk abunda aka yi Mai Martaba ne yayi ba ni ba”
A tunaninsa ko akan kayan ta ya tura ne wani abun be mata daɗi ba, sai kawai yaji ta ɗauko masa wata magana ta daban.
“Miyasa kasa aka ɗauko Lamido daga Kaduna ka kawo shi Katsina? Mi kace masa?”
Yannu ya kai yana shafa dogon hancinsa, tare da maimaita sunan Lamido a zuciyarsa.
“Be faɗa miki abunda Yarima Abdallah yayi masa ba? Be faɗa miki gaskiyar abunda ya faru ba?”
“Be faɗa min ba, amman ga dukan alamu abunda ka yi masa babba ne, domin har hawaye na gani a idonshi”
Ƙafarsa ya ɗora ɗaya saman ɗaya yana imaging fuskar Namra a wannan lokacin duk da kuwa bata kusa da shi.
“You're crying...”
Sai kawai ta katse kiran ta share hawayen idonta ta miƙe tsaye ta kabbatar sallah. Har ga Allah tana jin son Abdool a zuciyarta sai dai bata fatar ta yi amfani da wannan damar ta cutar da Lamido, dan tana jin rashin kyautawa a abunda ta yi masa, sai dai bata da zaɓi bayan na Allah daman can shi ta miƙawa lamurarranta, har gobe roƙon Allah take idan har babu alheri a aurenta da Abdool Allah ya musanya mata.
Haka ta kwashe kwana biyu, babu wata magana mai daɗi dake shiga tsakaninta da Abdool, saboda tana ganin kamar yana amfani da saurautarsa da kuma kuɗinsa ne wajen nuna mata ƙarfin iko ya ita da Lamido, ga kuma farin jikin daya samu a tsakanin iyayenta wanda hakan ya hanata ko da wasa ta cewa Anty wani abu ya shiga tsakaninta da Abdool ba.
Har yanzu Lamido ne yake kaita makaranta, bata tambaye shi yadda yayi da Abbah ba, shi kuma be ce mata komai ba. Sai dai ta kan tsargu da abu ɗaya a yanzu, ya kan tsura mata ido ta madubi mota ko kuma idan tana waje kamar madubinshi.
Ita kuma a yanzu bata magana da shi saboda ya ƙi ya faɗa mata.
ABDOOL POV.
Tun da ya karanci halin da Namra ta sashi, sai ya ke ganin kamar Lamido ne yake masa zagon ƙasa, daman shi zuciyarsa bata natsu da zaman lamido a gidan ba, a duk lokacin da ya tuna sai yaji kamar zuciyarsa zata rabe biyu, musamman da yasan shi yake kaita makaranta ya ɗauko ta, tabbas yayi sake da yaba har tsawon wata takwas tana keɓancewa da Lamido, aiko dole ta so shi fiye da shi.
Kamar an masa allurar ƙarfi haka ya zabura ya miƙe tsaye be damu da saka hula ba duk da shaddace a jikinsa ya fito ya nufo part ɗin Ummi.
Be same ta a falon ba, sai Amal ya samu tana ta faman solved Maths.
“Dude Ina Ummi?”
“Tana Garden lalle ake musu, Dude na taso mu yi wannan assignment ɗin?”
“No bari sai na dawo fita zan yi”
Ya juya ya fice. A garden ya sameta zaune saman carpet ta jera ƙafafunta ana zizira mata lalle irin wannan na zamani.
Tsaye yiyi ya jingina da icen guava yana wasa da keys ɗin hannunsa.
“Ummi na canja shawara, zanje na ga Mai Martaba”
“Shawarar me?”
“Nan da One Months nake son a yi auren nan?”
Da mamaki Ummi ta kalleshi.
“saboda me?”
“Kawai ni nafi son haka ne”
“To su ƙanenka da aka saka date ɗin aurenku a tare fa?”
“Su a barsu sai lokacin ni kan gaskiya i can't wait, zan samu Mai Martaba mu yi magana”
“Amman zai zama kun yi magana biyu Abdallah, da ka yi haƙuri har lokacin nan da wata biyar a ba wani abu ba ne”
“Haƙuri ba zan iya ba Ummi, kawai ki min addu'a”
“Toh Allah yasa alheri, amman nasan Mai Martaba ba zai amince ba”
“Zai amince ki daina ƙwanƙwanton mahaifina akai na”
Hannu ta ɗaga masa.
“Tafi kai da kan ka zaka dawo ka ba ni labari”
Murmushi yayi ya juya ya bar Garden ɗin tana ta saƙe-saƙe a ranshi har ya isa faɗar Mai Martaba.
Be same shi a gida ba, saboda wani taro da taje, haka ya zauna a gidan har aka yi sallah magariba, bayan ya fito daga masallaci ne Mar Martaba ya dawo, dan shima sai da ya tsaya a can suka yi sallah sannan ya kamo hanyar gida.
Mai Martaba na gaba Yarima Abdool na biye faɗawa sai zuba masa kirari suke har aka shiga fada. Kai tsaye Mai Martaba ya wuce turakarsa Abdool ya rufa masa baya yana masa bangajiya. A saman fafaffaɗa kuma ƙasaitacciyar kujera Mai Martaba ya zauna ya cire rawaninsa ya miƙawa Abdool. Bayan ya aje rawanin ya dawo kusa da ƙafafun Mai Martaba ya zauna yana mai natsar da kai kasa kamar yana gaban sukurinsa, ya kan yi hakan a duk lokacin da da yake neman wata alfarma a gurin mai Martaba saboda kawai Mai Martaba yaji tausayinsa ya amince.
“Buɗe baki ka yi magana, Babana ni mahaifinka ne idan ban maka uzuri ba waye zai maka?”
“Allah ya taimaki Mai Martaba ya ƙara maka lafiya, daman magana ce na zo da ita akan auren mu, sai dai ban san ta fuskar da zaka kalli abun ba”
Mai Martaba ya jingina da kujera yana cigaba da kallon ɗansa. Abdool ya cigaba ba tare da ya ɗago ya kalli Mai Martaba ba.
“Idan har ka amince min, ina son ka roƙa mahaifin Namra akan ya rage lokacin da ya saka na aurenmu saboda yayi tsawo...”
Sai da aka ɗauki tsawon ɗakika talatin da huɗu wata kalma bata fito daga bakin Mai Martaba, sannan ya nunfasa kana ya ce
“Ni kaina na yi tunanin hakan, saboda maganganun da suke ta zuwa suna dawowa, ba a son magana ta yi yawa akan aure, kuma idan har aka ja abu nesa wannan kan iya haifarda da wata matsala wace ba a tsammanin zata zo, sai dai ganin lokacin auren yayi dai-dai da lokacin auren ƴan'uwaka yasa ban ce komai a kai ba”
Abdool ya jidaɗin wannan maganar, daman yana neman da inda zai fake yayi hujja da shi akan maganar auren. Sai gashi Mai Martaba ya taɓo masa inda yake masa ƙai-ƙaiyi.
“Nima hakan na gani, kada sheɗan ya shiga ciki, ko kuma baki yayi mana yawa”
“Gaskiya ne, amman kai zuwa yaushe kake ganin ya dace a saka auren?”
“Allah ya taimake ka ina son ace nan da wata ɗaya”
Mai Martaba yayi masa wani kallo.
“Nan da Wata ɗaya sai kace wanda zai auri ƴar tsana? Wata ɗaya yayi mana kaɗan da shirya lamarin auren ka”
“Allah ya taimake ka duk yadda ka yanke dai'dai ne, amman be yi kaɗan ba, indai matsalar lefe ne ciki sati ɗaya za a iya haɗawa, kuma na san bama buƙatar komai daga gareta”
Ɗan Murmushin gefen baki Mai Martaba yayi, lallai ya tabbatar da ɗansa ya matsu, hakan ma yasa shi gane Abdool yama neman girma a yanzu, bayan kuma a da neman masa ake yana gudu.
“Za mu yi tunani akai, kar ya zama mun matsa musu, zan yi shawara da Umminka, nan kuma cikin gida zamu shawara”
Mai Martaba na gama faɗar hakan ya miƙe tsaye...
__________________________________
I think we should create a team for LAMIDO ko 🤔 i pity him bawan Allah 😢
[7/24, 9:38 PM] Khadeeja Candy♥: *89*
Yau day ta leƙa whatsapp domin ta kwana biyu bata hau ba, daman bata hawa sai idan tana da time saboda karatun da ta sawa gaba.
“Abbah na kiran ki”
Aysha ta faɗa tana tsare jikin ƙofar ɗakin Namra.
“Okay ga ni zuwa”
Ta kashe data ta sauka saman gado. Ko da t fito Zinatu na zaune falo ita da Anty Amarya suna cin ɗatun zogale (kwaɗo). Wara ido tayi ta sha mur
“Lallai Anty shi ne cika zauna da ƴarki kika ci ɗatu ni aka ƙyale ni”
“To idan ban ci da ƴata ba da wa zan ci? Kaji min yarinya”
Anty Amarya ta faɗa fuskarta da annuri tana murmushi. Zinatu tasa dariya.
“Na gan ki online fa kuma na miki magana kika share ni”
“Allah ban duba ba, hankalina yana can ina duba chat ɗin grp”
“Gashi ai sai ki zo ki ci”
“Abbah ya kira ni, aje min na dawo”
Ya aje wayarta saman kujera ta nufi part ɗin Abbah. Zaune ta same shi sanye da jallabiya, idonsa sanye da farin gilashi hannunsa da jaridar daily trust. Ƙasa ta zauna bayan ya amsa mata sallamar da tayi idonta kan Arewa24 da suke maimaita shirin Daɗin kowa.
Remote Abbah ya ɗauka ya kashe tv, ya aje jaridar da ke hannunshi sannan ya fuskanci Namra ya ce.
“Magana na ke son mu yi a tsakanin ni da ke, kuma bana son ki takura kan ki, na fi son ki faɗi ra'ayinki”
Ta ɗan kalleshi kaɗan.
“Abbah maganar me ce?”
“Akan date ɗin da aka saka ne na aurenki, Mai Martaba ya kira ni yace a rage musu ranar da aka saka ta yi musu tsawo, amman yace baya son a cilasta miki yafi son sai anji ta bakinki”
“Abbah ban da wani zaɓi sai naka, abunda duk zai fito daga bakinka shi xai fito baki na, kai da Mai Martaba duka iyayene a gurina, duk yadda kuka yanke yayi, idan ma a yanzu kuke son a ɗaura auren babu matsala ni dai a guna, sai idan gurin Abdool”
Abbah ya jidaɗin maganarta sosai, daman haka yake son ta kasance gareshi mai biyar dukan umarninsa da yarda da abunda ya zaɓa mata, babu ruwanshi da duba zamani ya canja a ƙyale yara su yi ra'ayin kansu, yafi son duk yadda ya zaɓa maka kawai ka bi.
“Na jidaɗi da wannan kalami na ki Namra, kuma tun da har kin amince zan faɗawa Mai Martaba kuma na san shi ma zai jidaɗin wannan maganar, daman shi yana son a saka me nan da wata ɗaya”
Dam! Gaban Namra ya yanke ya faɗi sai ɗai bata nuna komai a fuskartaba.
“Babu matsala a gurina Abbah, amman ya maganar Lamido?”
Abbah ya sauke ajiyar zuciya.
“Yadda kike so Namra ba zai yiyu ba, ba zan ɗauki mutun haka kawai na bashi MD, mutanen duniya a yanzu ba abun yarda ba ne, abunda Uxair yayi min kawai ya isa ya lurar da ni duniya, zan iya bashi aiki dai a ƙarƙashina, kuma daman ina da niyar gyara musu gidansu kuma na ƙullawa mahaifiyarsu jari, ko da be yi komai ba zan iya masa haka balle kuma ya taimake ki sun riƙa ki tsakani da Allah, na san yana son ki Namra kuma kema kin san da haka, sai dai hakan ba zai sa na ɗauke shi haka kawai na bashi mb ba”
“Amman Abbah idan ya fara aikin nan ka aminta da shi zaka iya bashi md, wallahi mutumen kirki ne”
Abbah yayi murmushi.
“Har yanzu akwai ƙurciya cikinki, ai ba a gane mutum mai amana a fuska sai a aiki, sai dai na yarda da abu ɗaya, duk yadda duniya ta lalace za a samu na ƙwarai, zan jarrabashi na gani”
“Na gode Abbah”
“Allah ya miki albarka”
“Amin Thank you”
Haka ta tashi jiki babu gwari ta fice. Tun daga lokacin aka fara shirye-shirye, a dukan ɓangarorin guda biyu. Kullum sai Abdool ya kirata safe, rana da dare domin jin muryarta da kuma son sanin ko akwai abunda take shiryawa, sai dai duk lokacin da ya tambaye cewa take bata shirin komai.
Hakan yasa ya baro Abuja a daren ranar ya sauka sokoto, dan kwata-kwata ya rasa gane kan matarshi (His wife to be). Haƙuri yayi har sai da yayi sallah isha'i sannan ya doshi gidansu Namra. Wannan zuwan na musamman ne baya son kowa yasan da zuwanshi sai ita, a harabar gidan ya faka motarshi ya kira a waya yace mata yana gefen gate. Bata yarda ba har sai da ta saka Hijab ɗinta ta leƙo ta hango mota a gurin sannan ta yarda da gaske yake.
Ƙarasa ta yi kusa da motar ta buga ƙofar motar sai ya fito ya buɗe mata motar ta shiga sannan ya koma mazaunin direba ya zauna. Wasa take da ƴatsun hannunta ta kasa buɗe baki ta gaisheshi ma balle ta yi masa wata maganar, ta dai yi shiru tana shaƙar turarensa da ke kaiwa hancinta ziyara. Wani dogon numfashi yaja ya sauke kana ya kalleta ya ce.
“Na miki zuwan bazata, saboda na lura kamar baki cikin yanayin da ya kama ki kasance, idan har bakya ra'ayin aurena Namra, wallahi ba zan cilasta miki ba, duk yadda nake son ki zan iya bawa zuciyata haƙuri matuƙar ke hakan shine farincikinki, ba jindaɗina ba ne muyi aure kuma mu koma muna zaman da be kamata ba ni da ke, ba zan aureki dan wani abu ya shiga tsakanin mu har na sake ki ba, burina idan mun yi aure ni da ke mutuwace kawai zata raba, ba zan aureki dan wani abu na ki ba sai dan so da tausayi waɗanda abubuwa ne guda biyu da ba zasu taɓa saka ka ganin laifin mutum ba, shiyasa bana ganin laifin abunda kike min, sai dai ina kallon hakan da rashin so, ina ganin kamar na cilasta miki ne akan abunda baki da niya...”
Ɗagowa ta yi ta kalleshi idonta tab da hawaye, cikin rawar muryar ta fara magana.
“Tun bayan abunda Asim yayi min, ban taɓa tunanin zan so wani ɗa namiji ba, haka na saka a zuciyata kuma haka na ayyana. Amman daga lokacin da na saka ka a idona gidansu Lamido, sai wani irin kwarjini da ƙimarka suka kama ni, sai kuma gashi ka zama sanadiyar haɗa ni da iyayena, wannan ne yasa son ka ya ɗasu a zuciyata, ko da ban aureka ba, zan son ka Abdallah, irin son nan da ƴan matan hausawa suke yi ma mazan hausa novels da larabawa, kasan irin wannan son yafi ko wanne haɗari da saka rayuwa cikin ƙunci da nadama, da kuma ganin munin kowa, sai gashi Allah ya ƙaddara zan zama matarka, amman son da na ke maka doesn't give you the chance to hurt innocent people”
Sanyayiyar ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta irin kallon nan mai cike da shauƙin so da ƙauna.
“Wana cutar?”
“Lamido, ya ƙi ya faɗa min abunda ka yi masa amman nasan abunda ka yi masa ba ƙarami ba ne”
“Dukan abunda na yi masa saboda ke ne Namra, saboda ina son ki ne, nasa an kawo min shi daga kaduna zuwa katsina ne saboda na masa magana a akan ki, nace zan biyashi ko nawa ne, ya ƙyale ki saboda bana son mu tarayya ni da shi a lokaci ɗaya mu raba miki hankali, saboda na lura yana son ki, kuma zuciyata tana nuna min zai bibiyeki, amman shi be ƙarbi tayin da na masa ba, har ma yayi min iƙirarin shi ne zai mallake zuciyarki, kuma yayi nasarar aurenki, amman duka be faɗa miki wannan ba sai a yanzu da yaga komai ya kankama kuma ya ɓoye miki saboda yana son shiga tsakanin mu, wannan yasa na roƙi Mai Martaba akan ya nemi a rage tsawon lokacin auren da aka saka, saboda magangu sun yi yawa akan zan auri bazawara, kuma gashi Lamido yana ƙoƙarin yi min zagon ƙasa, ina gudun kar shedan ya shiga ciki ya lalata lamarin aurenmu, saboda duk lokacin da aka shirya abun alheri za'ayi sai ka ga shedan na neman ɓata abun”
“Amman abunda ka masa baka kyauta ba”
Ta faɗa da muryarta mai kamar zata yi kuka. Shi kuma ya kwantar da kansa jikin kujera yana kallonta, dan har cikin jininshi maganarta ta shiga ta zauna, a take kasala ta sauƙo masa.
“Naji Gimbiyata ayi haƙuri a gafarta min”
Yanayin yadda yayi mata maganar yasa ta jin kunya har murmushi ya suɓuce mata bata shirya ba.
“I love you, i can't wait to see us on one bed...”
Ya faɗa muryarsa ƙasa sosai kamar mai raɗa. Buɗe motar ta yi zata fita sai yayi saurin riƙo hannunta, ta zaro ido tana faɗin.
“A'uzubillahi...”
Sai ya saki hannunta da sauri.
“I cross the limit... But sorry wai ba mu gama maganar ba”
“Mun gama mana”
“Dan Allah ki yi magana da kyau Abnam ki daina kashe min jiki”
Ƙyalƙyale ta yi da dariya, saboda har ga Allah ya bata dariya ita bata yi dan ta kashe masa jiki amman shi yana ƙoƙarin juyarda abun. Shima dariya ya samu kansa da yi saboda be taɓa ganin ta yi irin wannan dariyar a gabanshi, ta tafi da imaninshi sosai.
“You're so cute Abnam na fi kowa sa'ar mata”
Ƙoƙarin kawarda maganar ta yi.
“Na san maganar akan events ne, so bazawara zaka aura bana buƙara events bayan walima”
“Amman ni saurayi ne ai, ina buƙatar ayi mana wani ɗan event haka ko da biyu ne ko ɗaya”
“Ni dai idan ta ɓangarena ne bana so”
Ya ɗaga kafaɗunshi.
“As you wish your royal highness”
Dariya ta yi ta rufe masa motarta ta tafi. Shima murmushi yayi yana mai jindaɗi.
Namra ta kusan minti talatin tsaye a jikin windo tana kallon motar Abdool, sai ya kunna motarsa ya bar gidan sannan ta fito ta nufi sashen BQ.
Tun daga nesa ta hango Lamido zaune yana danna wayarsa. Ta ƙarasa kusa da shi tana masa sallama.
“Wa'alaikissalam, Hajiya”
“Na'am hutawa kake yi”
“Ina ɗan duba duniyar facebook ne”
“Hakan na da kyau, amman miyasa bakinka yayi nauyi har ka kasa faɗa min Abdool ya nemi ka siyar masa da soyayyata ne?”
Murmushi yayi ya cire hular taɓani ka ji hadisi da ke kansa ya ce
“Saboda soyayyarki tana da girma a gareni, amman ina fatar ya faɗa miki mahaifinshi ne dalilin talaucewar mu”
“Abunda ke tsakanin Mahaifinka da mahaifinshi be kamata ya shiga tsakanin ku ba, balle kuma ni har na shigo ciki, be nuna min ya san kamin lokacin ba kuma kai ma baka nuna min ka san shi, dan haka babu ruwana da abunda ke tsakaninku”
“Na gode Namra na gode sosai”
Yana kaiwa nan ya miƙe tsaye ya shige ɗakinshi. Ita kuma ta juyo ta dawo part ɗin Anty Amarya, a bakin ƙofa ta samu anty amarya a tsaye tana mata wani mugun kallon.
“Me kika je yi can?”
“Magana na yi da shi”
“Wace magana bata da suna ne? Ban miki maganar tun ranar akan ki daina keɓewa da shi ba?”
“Wallahi ba abunda kike tunani ba ne, yana ta ƙoƙarin shiga tsakani da Abdool ne ni kuma ban ga ne ba sai yanzu, shi ne na masa magana”
“ko ma minene karna sake ganin ki part ɗin nan, ai ba zarginki nake ba, kawai ina gudun shaedan ne, kuma tun da yana son ki zai iya aikata miki komai, ki yi taka tsantsan”
Ta gyaɗa kai.
“Ba zan sake ba daga yau”
“Good”
Anty ta bata hanya sannan itama ta shiga.
Ko da Namra ta shiga ɗakinta ta tararda missed calls na Abdool. Dan haka tana cire Hujabinta ta kirashi.
“Hi Babe-Abnam”
“Abdallah”
“Faɗa min wani abu mai daɗi...”
“Ni ko tambayar ka zan yi, miye tsakanin mahaifinka da Mahaifin Lamido”
“Me kuma ya sake ce miki?”
“Yace wai mahaifinka ne silar talaucinsu”
“Ya ɓoye miki ne kawai ko kuma be san gaskiyar zancen ba, a da mahaifinshi abokin Mai Martaba ne kamin a bashi sarauta, sai dai mahaifinshi yana safarar ƙwayoyi ne daga wata ƙasar ana sakawa cikin kayanshi da yake oder, sai yace musu zai kai kaya kaduna alhalin ƙoyoyine yake safara, babu irin jan kunne da mahaifina be masa ba amman yaƙi ji, ranar da ya shirya dainawa sai ya aika duka kuɗinsa waje ya siyo kayan fasa ƙwairi,wanda sanadin hakan customs suka kama kayan, kuma aka bincika aka gano yana safarar ƙwayoyi sanadin hakan aka maka shi, amman sai yake ganin kamar mahaifina ne ya saka shi a matsalar”
“Amman daman ka san Lamido baka taɓa faɗa min ba?”
“Ban san shi ba Wallahi shi ma kuma be san ni ba, sai a lokacin da nasa aka kawo min shi daga Katsina, a lokacin ina gida ne gurin Ummi, Ummi ce ta ganshi ta gane shi, shi ma kuma ya ganeta bayan ya tafi take bani labari, dan ni ban san anyi abun ba ma, lokacin da aka yi abun ina waje gurin karatu, so duk wasu abokai na Mai Martaba ni ban sansu ba domin ban dawo naija ba sai da na yi digiri na biyu”
Namra ta jinjina lamarin sosai, daga nan zance ya cigaba, har ya ɗauko mata labarin labarin zamansa a England.
*** *** ****
A GURGUJE...
Gyara na musmman Anty tasa ake mata irin wanda ake ma amare, tun daga kan dilka da kuma kayan mata.
Daga Dubai Abbah yayi mata odar furniture aka kawo su ta jirgin sama, saboda jirgin ruwa za a iya ɗaukar watanin basu iso ba, gashi kuma aure ya maso kusa, duk da Mai Martaba yace kar su kashe kuɗinsu hakan be hana Abbah siya mata kaya mai shegen tsada ba dan nemawa ƴarshi mutumci da ƙima a idon manyan mutane.
Ranar da aka kayo lefen Namra ana sauran sati ɗaya, bikin ranar kowa ya sha mamaki, sai dai duk wanɗa ya ji labarin ɗan sarkin Katsina zata aura sai su daina mamakin dan sun sa waye mahaifinsa balle kuma shi ɗan da kansa, an kashe neira a ɓangaren Abbah saboda tarbar lefe yayi duk abunda ya kamata wajen ganin ya kashe kunya.
Bayan kowa ya watse Hajiya Barau da Anty suka zo suna ƙara duba kayan, daga ɗan kunne har ribbon babu wanda aka siya a naija duk daga waje Ummi taje ta ɗawa ɗan lelenta lefe. Akwati ashirin da bakwai ɗan ƙaramin akwatin zinari ma daban ne, motar da aka kawo lefen da ita ba a koma da ita ba wai ita tana cikin lefen, ga kuɗin tsintuwa da ake sakawa a gefen akwati su daloli suka saka. Ko kaɗan wannan be yi ma Anty Amarya daɗi ba, domin ta tsani bidi'a a rayuwarta, dukan wani abun da za'ayi almubazzaranci da kuɗi Anty bata son shi.
“Ai ƙara ma da ba za ayi wani Event ba, da Allah kaɗai yasan iya bidi'ar da za'ayi, shi kesa aure yaƙi yin ƙarƙo, ni wannan abun ba burgeni yake ba”
Hajiya Barau ta yi murmushi tana danne abunda ke zuciyarta.
“Ai ke baki ga komai ba ma, mu da muka je jere mu muka ga abu, kin ga gidan da ya ƙera mata kuwa? Kamar ba Katsina ba, wallahi an kashe kuɗi sosai”
“Uhm Allah ya kyauta”
“Amin ai kinsan su masu abun idan ba sun fitar da kuɗin ba ne sun kashe basa jin sun yi, kuma tun da har Allah ya hore ai ƙara ayi, abunda kawai ba a so a zubar da kuɗin kamar kari haka”
“Ke dai Allah ya kyauta kawai, amman bidi'ah bidi'ah ce”
Haka suka yi ta firarsu suna duba kayan da tsayawa ƙirga ko kala nawa ne ɓata lokaci ne. A daren ranar Abbah ya kira Lamido ya bashi offer kuma ya sanar masa aikinsa ya ƙare a gidan da sunan driving. Ba laifi yayi farinciki duk da ɗayan ɓangaren yana baƙinciki an kasashi. Sai dai matsalar rashin aikin yi ita ta fi damunshi fiye da kowace irin matsala.
RANAR JUMMA'AH...
Da misalin ƙarfe biyu na rana aka ɗaura auren Abdallah Ahmad Mai-doki da Khadija Usman Zamau, a masallacin Muhammadu Maccido da ke Amir Yahaya. Duk wanda ya wuce a gurin sai ya tambaya ɗaurin auren wa ake saboda yadda aka taru sosai, ga manya mutane minister da sarakuna da ɓangaren Mai Martaba, da kuma gwannan Katsina, da na kano wasu kuma basu samu damar zuwa ba suka tura akillansu. Mr Presiden ma Wakiltarsa aka yi, saboda baya ƙasar.
Bayan an ɗaura aure aka yi ƙiyafar cin abinci a Shukura Hotel. a ranar Mai Martaba da muƙarrabansa suka koma Katsina, da dare Mai Martaba yayi nasa liyafar shi da manyan baƙinsa, a faɗarsa da aka sauyawa hallita kamar ba a naija kake ba.
Ta Ɓangaren Namra bayan an ɗaura aure da rana. Da dare suka yi walima, saboda an sauya salo yanzu walimar dare ake, an raba kayanyaki masu ɗubin yawa da burgewa. Sai dai ƴan ɓangaren ango basu halarta ba saboda Ummi ta ce zata yi nata walimar idan an kawo Amarya, saboda wasu haka suke sai idan an kai amarya sannan suke nasu walimar...