Satinsa biyu a kaduna, kusan kullum sai Amira ta tura masa saƙon barka da safiya da dare ma haka, sai dai har yanzu be taɓa mata reply ba, shi kan ba ma ita ce gabansa ba. Kusan kullum sai yayi waya da Ummi kamar yadda ya saba, ya maida hankali akn aikinsa sosai dan aiki ne mai muhimmanci.
Yau kam be kira Ummi da safe ba har sai da ya shiga office, yana shirin kiranta sai gata ta kira shi. Da sauri ya ɗauka Cikin jindaɗin kiran na mahaifiyarsa
“Ummi na ta kai na good morning”
“How are you?”
“Im fine i miss you, na ga nawa satin nan ya zo na zo gida na ganki”
“Nima ai ina son ka zo akwai maganar da zamu yi da kai”
“Wace magana ce?”
“Idan ka zo zaka ji, akwai kayan da nayi oda daga paris za su iso Lagos jibi, zan tura maka address ɗin sai ka aika a karɓo min”
“Yes Ma'am”
Dariya tayi ta kashe wayar shima ya sauke yana murmushi cike da ƙaunar mahaifiyarsa.
Ɗayan ɓangaren kuma yana jin rashin daɗin maganar da tayi ma mai martaba na cewar yace a nema masa mata, sai dai babu yadda ya iya tun da shi kansa ya san yana buƙatar auren a yanzu, idan be yi ba a yanzu sai yaushe, lokaci tafiya yake baya jiran kowa, kuma shi har yanzu be da wacce zai iya fitarwa a matsayin matar aurensa.
Sai dai shi kuma ya sha alwashin aurar da duka ƙanensa dan ba zai yarda Ummi ta riƙa matsa masa ba bayan ga ƙanensa mata nan duk sun isa aure.
*Ummi*
Tana gama waya da shi, sai ga Amira ta shigo da sallama cikin ladabi, already ta gaishe da Ummi da safe so bata buƙatar repetitive, sai kawai tace
“Ummi me za a girka na rana?”
“Ayi mana mana miyar kuɓewa sai Shukura tayi tuwon semo”
“Tau”
Ta miƙe tsaye ta fice cikin tsantsar ladabin nan. Bata kira Shukura ba da kanta tayi tuwon semo miyar kuɓuwa sannan kuma tayi miyar agusi dan kawai ta burge su. Ko da azahar tayi har ta gama komai ta jera a dinning sannan ta shiga tayi wanka.
A lokacin ne su Amal suka dawo makaranta tare da Haleema, daman yau Meesha bata je ba, dan su da lacca. Fauza ce kawai ta tafi sai Haleema.
A ɗaki suka samu Ummi da Meesha suna duba wasu atamfofi da aka turo ta whatsapp. Jikin Ummi Amal ta faɗa tana zuba shagwaɓa wai ita ala dole ga auta.
“Ummi yunwa”
“Ai ga abinci can ana gama”
“Me aka girka”
Haleema ta tambaya tana zaunawa kusa da Meesha.
“Tuwon semu miyar kuɓewa”
“Ɓi bana so, sai dai ki girka min makaroni”
“Kai Amal kin cika son rigima wallahi, miyar tayi daɗi fa”
“Wa yayi? Wannan Amira ko”
“Eh miya har kala biyu tayi”
.“Ni bana so bata iya komai ba sai ƙazanta”
Haleema ta buge mata baki
“Data saba girkawa kina ci fa? Wai Amal miyasa baki da kunya, ke uban kowa kin raina, Amirar nan aiki da take ko da muke cikin gida albarka, tana ƙoƙari sosai wallahi”
“Ta riga ta saba wahalar ne tun gidansu, maybe talakawa ne”
Cewar Meesha, tana taba eyebrows.
“Ba wani sabo wallahi kawai dai tana da mutunci ne, kuma gani nake kamar Big bros take so, dama an haɗa su wlh dan zata kula da shi”
Meesha ta tofarda yawu
“Tuuu Allah kiyaye big Bros da wannan yarinyar amman wallahi Haleema baki da hankali zuwa makaranta be amfane ki ba, daga ganin yarinya an taimaka mata ki ce wai ta auri yayanki, ke anya kina son yaya kuwa? Ke nifa ban ma yarda da yarinyar nan ba, tsantsan ɗinta yayi ta cika shige mana jiki, waya sani ko cutar mu ta zo tayi”
Amal ta haye saman gadon Ummi tana hararar Haleema.
“Sai na gayawa Dude, mu mana son ta”
Ummi ta kama kunne Amal.
“Bana raba ki da yi ma manya rashin kunya ba?”
“Ooo Ummi it hurt”
Ta riƙe kunne, tana son kuka. Haleema yaja wani dogon tsaki
“Ke kin wuce shiga halin da ta shiga ne hala? Idan Allah ya tubuta shine mijinta ya zaki yi?”
Ummi ta kalle ta kallo da babu wasa a fuskarta.
“Ke Haleema ki daina wannan maganar, yarinya daga taimako sai kuma neman wuce gurin tana da tarbiya zata bar gaban iyayenta ana neman ta koma bata so sannan ki ce ta auri ɗan'uwanki dan baki da tunani? Kin san iya zaman da ta yi taraiya da su? Wanda yayi maka hallaci ya cancanci hallaci shiyasa take zaune tare da mu, amman nan gaba kan gurin iyayenta zan maida ta, Allah ya bata miji na gari”
“Amman Ummi ta mana hallaci wallahi, kuma idan ba a barta ta auri Yaya kamar ba a mata hallaci ba”
Meesha ta zungureta
“Ai ke sai ki mata hallaci ko? Yayan manya ma Big Bros be so ba sai ita yarinyar data ƴan fashi, ashe za'a iya haɗa kai da ke ayi ma masa wani mugun abu, haka kawai daga ganin yarinya ki ce a haɗa su amman baki da hankali Haleema”
“Ke da kika da shi ai sai ki ara min na saka, ko ita ba mutum bace? Ke idan kina so wani ya zaki ji”
“Ba zan so wanda ya fi ƙarfina ba balle har na damu, ke daga ganin ajin Yaya kin san yafi ƙarfin Amira wallahi, yarinyar data gama bada kanta ga mazan banza sai kuma ta dawo yaya ya aureta, ai abun kunya ma ne wallahi”
Cikin faɗa Meesha ta ƙarasa tana jin kamar ta kama Haleema tayi mata shegen duka. Ita Haleema ji take kamar ta daki yar'uwarta. Har sai da Ummi ta katsa musu tsawa.
“Haleema kar na sake jin irin wannan kalamin a bakin ki, Aisha ke kuma ya isa tun da ba cewa aka yi za a aura masa ita ba, ku Shafa min lafiya dan Allah ku tashi ku bani guri”
Duk miƙewa suka yi suka fita, ban da Amal data laƙe jikin Ummi ita ala dole sai an dafa maya makaroni.
“Ai kema kin iya dafawa, Amal har mota kike tuƙi fa amman ki zo kina min abu kamar jaririya, idan yanzu aka miki aure ai sai zama dan kin girma, ba kece auta ba autana tana nan zuwa”
Ummi ta faɗa da raha a fuskarta. Amal ɗin tasa dariya dan tasan abu ne mai wahala a yanzu.
“Za a ce tsohuwa ta haihu”
Ummi ta tiƙi bayanta tana dariya
“Yes Tsohuwa maman Amal, tashi ki cire uniform”
Tashi ta yi ta fice tana dariya.
*NAMRA POV*
Kamar yadda suka saba yi duk mai ciwo, bayan ta faɗa masu matsalarta sai suka bata gwajin jini da fitsari, suka sa kuma taje ta yanki sabon kati dan duba wacan matsalar nata na robar dake hannunta dan a bayanin da ta yi ma likita ya fahimci ciki ne a jikinta. Sai dai bashi da tabbacin haka tun da ta faɗa masa tana saye da roba, duk da yasan ana samun irin wannan matsalar a wani lokaci.
Awan fitsari kawai ta samu yi, a take, na jini cewa suka yi sai da yamma ta zo ta karɓa, su kuma waɗanda zasu dubata a ɓangaren robar sun tashi aiki.
Tun da karɓo results ɗin ta kasa ta buɗe dan bata son ta ga abinda yake ciki, tasan idan har ciki ne tana cikin matsala dan bata gama warkewar ciwon mahaifarta, kuma ga roba jikinta ace tayi ciki tasan duka ƙarin matsalar ne. Ko da ta koma gurin likitan yana shirin tashi, har ya haɗa kayansa, a tsai-tsaye ya duba takardar tana fuskarsa da mamaki ya ce
“Kina ɗauke da juna biyu”
Ras ras ras gabanta ya faɗi, sai ta faɗi saman kujera tana hawaye. Da sauri likitan ya aje kayan hannunsa.
“Hey wannan ba wata matsala bace ana samun irin haka daman, amman abunda yafi zan rubuta miki hoto sai kije ayi hoto a bincika lafiyar cikin, kuma ki tabbar kin je an cire miki wannan robar”
“Doc mahaifa tana da matsala shiyasa aka samun robar”
“Ba lallai ne har yanzu matsalar ki tana nan ba, shiyasa nake son ki yi hoton”
Ya ɗauki wata takardar yayi rubutu ya miƙa mata.
“Kije ayi miki hoto, zuwa gobe sai ki kawo na duba ki, ko kuma ki dawo wani likitan ya duba ki, ki kwantar da hankalin ki ba wani abu nima mai ɗaki na ta taɓa haka”
Jakarsa ya ɗauka ya rataya ya face. Sannan ita ta tashi ta fito tana hawaye, maimakon taje gurin hoton sai kawai ta yanke shawarar komawa gida dan ita har yanxu jikinta na bata ba ƙalau take ba, balle bata da kuɗin da zasu isheta hoto tun katin ganin likita na asibitin ma kusan ɗari bakwai ne.
Tun cikin Napep take ta kiran Asim amman ya ƙi ya ɗaga saboda yana gaban Hajiya, wacce ta zame masa kamar uwa a yanzu, yadda yake jinta ko Mama data haife sa baya jinta haka nan.
Hakan yasa ta yanke shawarar tura masa saƙon karta kwana.
Ƙin ɗaga wayar yayi dan akwai yana gaban Hajiya, ita ta jidaɗin hakan da yayi ko ba komai tasan ya girmamata, gashi tun da yazo gidan be taɓa fita da sunan yaje gida gurin matarsa ba.
Sai da ta gama lissafa masa abunda zai siyo mata sannan ta bashi kuɗin tana murmushi ciki ladabi ya karɓa ya tashi ya fice.
Sannan Hajiya tayi murmushi ta maida dubanta ga ƙawarta, Hajiya Ubaida.
“Gaskiya yaron nan yana da ladabi ina kika damo shi?”
“Uhmm tsuntsune daga sama gasasshe Allah ya bani daga gyaran gate”
A nan ta kwashe labarin komai ta bawa Aminiyarta yadda suka haɗu da sharaɗin data gundaya masa da kuma zaman gidan da yake, da kuma ƙudirinta a kansa.
Hannu Hajiya Ubaida ta bata suka taɓa
“Shegiya Sadiya duk abunda kika sawa gaba sai kin ga bayansa, hala yarinyar mai kyau ce?”
“Tana da kyau wallahi ta haɗu ba ƙarya, sannan kin ga na samu dama biyu, daman Alhaji Usaini ya dame ni na samo masa sabin shiga, wai duk wanda nake kai masa basa da ladabi kuma an taɓa amfani da su, kwana biyu sai su fara masa tsageranci”
“Ai kin san manyan mutanen nan sun fi son tsaida mutum ɗaya, wanda zasu riƙa amfani da shi kullum”
“Eh shi ma haka yace, wai idan yana bin irin guys ɗin nan za'a iya gane shi, yafi son tsaida mutum ɗaya, kuma kin ga irin wannan zai fi jindaɗinsa dan ga alama zai yi ladabi, sannan garin su ɗaya, idan ta kama ya koma can ma, ni sai ya barmin matar a nan, dan ba zan taɓa nuna masa ina don matarsa ba, shi wata rana zan iya buƙatarsa”
Hajiya Ubaida ta ƙalƙyale da dariya.
“Ke Allah dai ya yafe mana, ya shirya mu”
“Amin kedai ai ina son tuba amman sai nan gaba, dan bana son Zeenat ta san halin da nake ciki”
“Gaskiya kam, ai ƙara ai daina da wuri kar azo aji kunya”
Hajiya Sadiya tayi fuskar tausayi kamar mai tsoron Allah da gaske, tana kallon Hajiya Ubaida wacce sana'arsu ta zama ɗaya.
*ASIM*
Be wuce kasuwar ba, sai da ya bi ta gida dan jin abinda Namra zata faɗa masa, badan saƙonta da yaga ni babu ma abunda zai sashi bi ta gidan. Kamar baƙin haɗari haka ya doshi gidan bakinsa ƙumshe da maganganu kala-kala, dan gani yake a yanzu shi ma ya kai matsayin da zai iya faɗawa magana son ransa, balle Namra da yake gani kamar banza.
A ɗaki ya tararar da ita kwance sai hawaye take. Daker ta ɗago ta kalleshi, duk da tana cikin yanayin damuwa hakan be hanata, kallon irin shigar dake jikinsa ba. Takalmin dake ƙafarsa kaɗai zasu iya kaiwa dubu 10+ balle wando da T-shirt.
Be ji zai iya zama a ɗakinba, sai kawai ya tsaya jikin ƙofa yana mata wani kallo, azuciyaraa yake hantararta ganin yadda ta ƙara lalacewa.
“Ya aka kika samu ciki?”
Wani kallo tayi masa zafin furucinsa yana zuciyarta.
“Kamar ya? Ina da wani mijin ne bayan kai”
“Ni ya za'ayi na sani, yanzu ai ba a shedun mutum”
“Shigowarka Asim irin wannan furucin zaka min? Tun da kasa ƙafa ka bar gidan nan babu ruwanka da ni kamar ba matar ka”
“Ya kike so nayi Namra aikin zan bari na zo na tisaki gaba nayi ta kallo ko me? Yanzu ma a hanya nake saƙon da kika min ne yasa na biyo”
Kawarda kai tayi ta haɗe hawayen da take da tabbacin idan har suka fara zubar mata bata san lokacin tsayawarsu ba.
“Daga Asibiti na ke likita ya ce ina da ciki, kuma akwai roba a jikina”
“To ya aka yi haka?”
“Nima ban sani ba, amman yace min daman akan samu hakan wani lokaci, yace naje nayi hoto aga lafiyar cikin, Asim ina tsoron ko mahaifata bata gama warkewa ba”
“To a zubar da cikin mana”
Miƙewa tayi tsaye tana kallonsa.
“A zubar fa kasa kasan abunda kake faɗa?”
“Na sani mana, Namra wannan ba lokacin samun yara bane, muna planning na neman kuɗi kuma yara zasu shigo, ki duba irin wahalar da muka sha a baya yanxu kuma hanya ta fara buɗe mana sai kuma haihuwa ta zo, gaskiya ni ban shirya ba”
“Ni kuma na shriya Asim, ni nake da matsalar da nake da a mahaifata kuma im ready to give birth saboda nima haihuwata aka yi, Allah ba xai bani kyauta na jefar ba”
Cikin wata murya tayi furucin muryar da bata san tana da ita ba sai a yau. Shi kuma ya gyara tsayusarsa yana mamakin ta
“Wallahi Namra sai yanxu na gane lallai ke ba masoyiyata bace. Kin manta lokacin da nake cewa kije ki cire robar nan amman ki ƙi, ko wannan zubar da ciki da kika sha ban san lokacin da kika sha ba, wata ƙila kin yi zubar da cikin ne shiyasa har mahaifarki ta samu matsala, sai yanxu da kika ga zan yi kuɗi ko shine zaki nuna min baƙin hali ki ɓullo min ta haihuwa, to ni ban shirya haihuwa yanzu ba dan haka dole a zubar da cikin nan”
“Wallahi tallahi ba zan zubar da wannan cikin ba, ko da kuwa wannan cikin yana nufi ya rayu, ni na mutu”
“Haka kika ce?”
“Haka na ce kuma haka xaka gani”
“To sai dai ki zaɓa ko ni ko cikin nan...!”
Wani kallo tayi masa na ƙara tantance zancen daya fito daga bakinsa. Shi kuma sai ya ɗaga mata kai dan ya tabbatar mata da maganarsa.
“Yes Idan har baki xubar ba sai dai kije can gidan ku ki haife ɗan, ke kan ki ba samun lafiyarki bane ace kin haihu cikin kuɗi kuma a lokacin mahaifarki tana lafiya ƙalau, na baki lokaci ki yi tunani akai”
Juyawa yayi ya fice, zuciyarsa cikr da tabbacin abinda yayi be yi kuskure ba.
*ANTY AMARYA POV*
Sai da dare Abbah da Hajiya Barau da Anty suka samo ganin lefen da ka kawo, Abbah ya yaba sosai, Hajiya Barau ma ta yaba amman yabon baka yabon daya zame mata cilas dan sam bata jidaɗin ganin yadda aka zubawa ƴaƴan Anty wannan uban lefen ba. Hindatu kala 54 Maryam kuma 79 cikin su kuma babu shege balle ɗan iska.
“Allah yasa alheri ya nuna mana lokacin, amman na ɗauka Namra zata xo tarbon lefen nan”
Anty Amarya taji babu daɗi, sai dai bata nuna ba, sai kawai ta ce.
“Ta so tazo mijin nr ya hana ta yace wai ta bari dai nan gaba sai su zo tare”
“Allah ya taimaka, lefe yayi mashallah”
Haka ta taso ta fito daga falon da ƙahon baƙinciki daya tsaya mata a zuciya. Part ɗinta ta shigo tana shiga ta shige ɗakinta ta zauna, babu abunda take tunanu sai duniyar da Abbah xai kashe masu gurin auren, kamar ita ba a ma ƴaƴanta.
Ummi ce ta shigo ƴar gurin Hajiya Barau mai sunan mahaifiyarta hakan yasa take kiranta da Ummi.
Duk cikin ƴaƴanta mata ita kaɗaice tazo tarbon lefen. Kusa da mahaifiyarta ta xauna tana kallon yanayinta kallonta Hajiya Barau tayi
“Kin gani ke kina son kashe na ki aure su kuma suna yi, idan so kike ki dawo gida mu zauna sai ki dawo”
“Haba Hajiya wallahi ni na gaji da irin wannan rayuwar da yake nuna min, kwata kwata bana gabansa, baya da aiki sai neman mata, tun abu na ɓoye har magana ta fara fita, ko fita nayi sai ya kawo wata a gida”
“Ina ruwanki da neman matansa? Ai kedai yana baki ci da sha ko yana baki na kashewa ina ruwan ki da lamarin, yanzu neman maza ma ake balle mata, abun ai yyi ne wanda be yi ba to bashi da kuɗin yin ne, ko ni ya nema kya ce ki kashe auren ki ki dawo gida balle kuma wata can daban”
Miƙewa tayi tsaye cikin ɓacin rai ta fice, dan tasan duk yadda take son mahaifiyarta ta fahimci matsalarta ba fahimta zata yi ba.
Ƙwafa Hajiya Barau tayi taja wayarta tana soma labartawa abokin gulmarta rashin zuwan Namra tarbar lefen ƙannenta.
Duk hirar da suke be nuna mata jindaɗin hakan ko rashin jindaɗin saboda yana gaban Yasmin ne, yawancin maganar bata wuce uhn a'a ato, Har suka gama wayar.
Ƙaton cikin Yasmin ya kalla yana murmushi.
“Allah yasa karki haifa minɓɗa mai kahuwa”
Ta tsuke baki
“Mai hali dai baya fasa halinsa, ni wallahi haushi kake bani sosai”
“Daman duk kina da ciki ai baki ƙaunata kamar na kashe miki wani”
Ya faɗa yana jawo wayarsa da tayi ringing, number abokinsa Tahir ya gani.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ”
Shine abunda ya furta bayan ƴan daƙiƙu da karɓa wayar.
“Okay gani nan zuwa”
Ya tashi tsaye da sauri, har Yasmin ta kalleshi
“Lafiya?”
“Wai Najeeb yayi hatsari, nan cikin gari”
“Subhanallahi, ina fatar be ji ciwo ba”
“Ban sani ba, sai naje tukunan”
Da sauri ya ɗauke Adnan da ke saman jikinsa ya ɗauki wayoyinsa ya zuba aljihu tare da keys ya fice hankali tashe.
*HILAL POV*
Lallaɓata yayi har sai da tayi shiru sannan yaja ta zuwa saman gadonsa ya zaunar da ita ya kama hannayenta ya riƙa.
“Na yarda ba ki aikata ba shikenan?”
“Har zuciyarka ka yarda da ni?”
“Na yarda da ke?”
“Zaka daina fushi da ni?”
“Zan daina”
“Zaka dawo da su Ezzah”
“Idan Hajiya ta yarda”
Haka yake ta amsa mata kamar tambayar babba da yaro, sai ya hau saman gadon yaja ta ƙirjinsa ya rumgume.
“I Love You”
Ƙamkamshi tayi
“I love you too”
Sun daɗe a haka kamin ya sake ta ya shiga yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin sai ta ɗauko masa abinci. Ba dan yana so ba ya zauna yayi ƴan lomomi kaɗan ya tashi ya nufi gidan Hajiyarsa.
Da shigarsa Ezzah da Ulfah da sauran yaran gidan suka rugo da gudu suka tarbeshi. Ulfah ce kawai ta tambayi Kalsoom Ezzah kan ko a jikinta. Bayan ya gama ganinsu ya miƙa musu chocolates ɗin ya shigo da shi sannan ya wuce gurin Hajiyarsa.
Tun daga yanayin yadda ta amsa masa sallamarsa yasan akwai abunda ya faru. Guri ya samu ya zauna yana kallon tv dake ɗakinta, kamin daga bisani ya gaishe ta. A maimakon ta amsa sai kawai ta hau shi da faɗa
“Yanzu fisabilliahi abunda kake ƙoƙarin yi kyautawa ne? Kace xaka kare ta idan kun je kutu bayan ga abunda tayi ma ɗan ka, irin waɗannan matan fa zama da du matsala ne dan kai ma xata iya maka haka”
Daga yanayin maganar ta ya gane Amina ce ta kawo mata zancen, dan ita kaɗai yasan yayi zancen a gabanta sai kuma Alh Bashir.
“Amman Amina munafukace wallahi, zuwa tayi ta faɗa miki ko?”
“Ai dole ta faɗa min mana tun da abun yayi mata zafi, ni kama rabu da wannan matar ka nemi wata ka aura”
“Gaskiya ba zan iya rabuwa da ita ba”
“To ko zaka auro wacce zata riƙa maka ƴaƴanka, dole ne ka ƙara aure ko kuma ka rabu da ita idan baka shirya zama da mata biyu ba”
“Haba Hajiya, kuskure ne nima a yanzu na gane ba ita ce ta aikata ba”
“To waya aikata? Ga abu ƙiri da muzu ka nemi takewa dan kana son ta, ah lallai ba banza ta barka ba, Ezzah ma tana ta faɗar irin abunda take musu a gidan, cin amana zalla”
Dariya abun ya bashi yau kuma Hajiya da kanta take irin wannan furucin.
“Babu maganin komai Hajiya, amman wannan matsalar nima ban san kan ta ba”
“To ni dai na faɗa maka ko ka ƙara aure ko ka rabu da ita, tashi ka bani guri”
Kansa ya dafe yana sauke ajiyar zuciya
“Hajiya ki fahimta...”
“Ba zan fahimta ba, ka tafiyarka kawai”
Yasan duk yadda zai yi ba zata fahimta sai kawai ya tashi ya fice da jimmar idan ta huce zai dawo ya fahimtar da ita.
-----------------------------------------------------------------
*Jiya naje biki ban samu na yi typing ba, so wannan zai zama na jiya, na yau kuma sai dare zan kawo. Thank you 🖤*
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *60 - NOT EDITED ⚠️*
*RASHIDA POV.*
“Teema ya faɗa min abinda ya fi ƙarfin zuciyata da tunani, ya bani labarin yau da kuma gobe na, ƙoƙari raba ni yake da Ubangijina”
Ta faɗa cikin kuka, tana mai jin tsantsar ƙyama da kuma tsanar bokan a ranta, ta kuɗiri aniyar zata iya aikata komai akan duniyarta amman ba zata iya aikata abunda ya faɗa mata ta aikata ba.
Teema ta tsire baki, tana mamakin ƙawar ta'ta.
“Ai kin daɗe da rabuwa da raba hanya da Ubangijinki, tun da kika soma neman taimakon wani daga cikin bayinsa, Abunda zaki yi kawai ki aikata wannan in yaso daga baya sai ki nemi yafiyar”
“Ya ce min baƙin hudu yana bibiyata, kuma wannan baƙin duhun baƙar rana ce, what if ranar mutuwa na ne? Ba shine na farko daya faɗa min haka ba, Teema ina tsoro”
Kyalƙyalwa Teema tayi da dariya har da taɓawa tana kallon Rashida.
“Amman Wallahi kina da abun dariya, miye abun tsoro kuma? Ashe ke sabowar shiga ce wannan harka, ba lallai baƙar rana ta zama ranar mutuwa ba, yana nufin akwai abunda zai same ki marar daɗi wanda ke da kan ki zaki kira abun da baƙar rana”
Ta ɗan ji sassauci a zuciyarta, har ta samu damar haɗe yawun da ya tsaya mata a maƙoshi.
“Ni dai ina ganin haƙura zan yi, kar naje na sake mata kuma ya dawo kaina dan yace zan yi nasara amman akwai yiyuwar ya dawo kai na”
“Amman wallahi Rash kin ban mamaki, ke da na ke ganin, kamar zaki iya aikata komai akan Hilal, ashe son da kike masa na ƙarya ne, tun da har zaki iya bar wa wata shi, yanzu duk soyayyar da kuka yi ta tashi a banza kenan? Ƴaƴanki sun zama nata mijinki ya zama nata? Ko akwai wani wanda kike so bayan Hilal?”
“Babu shi, Hilal ne kawai, wallahi ina sonsa sosai”
“Kuma kin yarda ki barwa wata shi ko?”
“Na samu matsala akan jifar da nayi mata Teema, na jefeta ya faɗa kan ɗa na, kin ji ai yanzu yana faɗa min, yanzu haka Rafiq yana can kwance asibiti babu lafiya, ya damu matsalar ƙwaƙwalwa”
“Lallai wannan mata ita bata tsaya akan ta, irin wannan matar maganinta ki samu fitsari ki zuba mata a ruwa ya jiƙa ta sha, wallahi duk wani magani na tsari jikin data sha sai ya karye, amman kin ce tana shiga malamai ita ma?”
“Haka nake gani, saboda gaba ɗaya Hilal ya haukace ba shi da magana ta kowa sai na ta, baya kula ni a yanzu, kuma kin ga da dane ba zai iya sakina ba amman yanzu duba ki ga ya sake ni”
“To ina ganin ba tsari bane itama ta iya shige-shigen ne, sai aka bata aljana ta tsare ta, kin san wasu suna haka fa dan akwai su cimma burin su”
“Da gaske? Ballatana ta daɗe ba tayi aure ba zata iya haka”
“Dan haka ki kwantar da hankalin ki, ki share hawayen ki matuƙar ina raye sai kin koma cikin ƴaƴanki, yanzu kin ga mun fito cikin tashin hankali baki masa sallama ba, amman yanzu idan hankalinki ya kwanta natsuwarki ta dawo jikin ki, sai mu koma yayi mana aikin kawai”
“Amman ya ce sai nayi fashin salla fa?”
“To miye a ciki? Wasu ma baki ga rai suke kashewa ba? Ai daga baya sai ki ranka ki nemi yafiyar ubangijinki Allah fa gafurun rahimun ne, kin ga sai ma ki daina kwata kwata”
Shiru tayi tana nazari, tasan idan har ta aikata wannan abun ta yi, babban saɓo, ta yi fashin salla saboda biyan buƙatar da bata da tabbacin zata biya? Ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da tuƙin.
“Zan yi tunani akai Teema, amman ina jin tsoro sosai”
“Ai da tsoro zaki cuci kan ki, kawai ki cire wannan tsoron ki yaƙi zuciyarki”
“Zan yi ƙoƙarin yin hakan”
Daga nan Teema ta ɗauko mata firar ƙawarsu, ita mai bin bokaye marar tsoro, wance ta mallake miji da uwarsa.
Duk tana yi ne dan kawai ta ƙara tunzira Rashida ta aikata, so that ita ma ta samu abokin shiga wuta, dan mugu be son ace shi kaɗai yake aikata abu.
Sai da ta fara biyawa ta sauke Teema a gidansu, sannan ta wuce na su gidan dan ta yi shirin zuwa gurin aiki, ganin karfe ɗaya ma bata yi ba.
Tun da tayi parking a harabar gidansu ta fara saƙe-saƙen abunda zata faɗa gurin aikin, dan gaba ɗaya kashe wayarta tayi. Tana shiga falo sai ga Momy ta fito daga ɗakinta jiki na rawa, Rashida na ganinta ta gane hankalinta a tashe yake.
“Momy lafiya?”
“Lafiya ba lau ba, tun ɗazu nake cikin zullumi Rashida”
“Me ya faru?”
Momy ta tsaya tunanin ta inda zata soma, dan tana jin faɗin kalamar kai tsaye.
“Safiya tace min ta ga ƙawarki Asma'u a... Hiv unit....”
Yadda kasan cida haka gaban Rashida ya riƙa faɗuwa, zuciyarta na zillo kamar ta fito, a take yawun bakinta ya tsarƙe ta har sai da ta soma tari. Tasan Momy ba Asmee take nufi ba, idan kuma har da gaske Asmee take nufi to Safiya ce ta faɗa, kuma taya Safiya zata ga Asmee ita ce ta gani.
“Safiya ce ta faɗa?”
Momy ta ɗaga mata kai tana hawaye.
“Ni ta ce ta gani ko?”
Nan ma kai Momy ta ɗaga mata.
“I tell not once not twice several times, naje nemanta ne a asibitin amman ta ƙi ta yarda gani take kamar ni ce naje a karan kai na...”
Maganar take tana nuna da gaske take, amman bata son kallon Momy. Kai Momy ta girgiza na tausayin ƴarta da kuma ganin wautarta akan abunda take ta ƙoƙarin ɓoyewa.
“What about the results?”
Da sauri ta kalli Momy, tana mamakin kalamanta. Kenan bincike suka mata lokacin da bata nan! Ita da tayi ma results ɗin mugun ɓoyo taya aka yi suka gani?
Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da kuka mai ƙarfin gaske. Momy bata san lokacin data ƙarasa gaban ƴarta ta rumgume suka soma kukan tare.
“Taya haka ya faru Rashida ta ya? Miyasa kika yi ƙoƙarin ɓoyewa?”
Cikin kuka Momy take tambayarta, tana jinjigata. Da sauri Rashida ta zame jikinta daga na Momy ta tashi da sauri ta shige ɗakinta ta kulle da maƙulli. Jinginawa tayi jikin ƙofar tana kuka, irin kuka mai sa kaji kamar ka cire ranka ka huta.
Momy ma kuka take sosai, dan yanzu ne ta ƙara tabbatar da zancen Safiya. Daman tun Safe Safiya ta shiga ɗakin Rashida tana mata bincike har Momy ta same ta a ciki, anan takr faɗawa Momy haɗuwarsu da Rashida a asibiti. Da kuma maganin da abokan aikinta suke bawa ƙawarta Asmee, a wacan Asibitin ta su.
Babu irin bugun ƙofar da Momy bata yi ba, amman Rashida ta ƙi ta buɗe, kuma ta ƙi tayi magana, sai kuka take. Waya Momy ta ɗauka ta kira Dady ta faɗa masa, cikin ƴan'mintuna sai gashi ya dawo gida hankali a tashe, ɗan har gumi ke keto masa ta ko'ina.
Kai tsaye ɗakin Momy ya nufo, sai ya same ta itama tana kuka.
“Ya aka yi haka ta faru? Amman an tabbatar?”
Kallonsa Momy tayi idonta na zubar da ƙwalla.
“Safiya ce ta faɗa, nima ban yarda ba har dai yanzu dana nuna mata na ga takardun, bayan kuma ban gansu ba nace ne kawai dan na gano gaskiyarta, kuma the way she act ya nuna tana da shi”
Jiki a sanyaye Dady ya zauna idonsa sun rine sun yi wani ja sosai, irin na ɓacin rai da damuwa sun sauka ga mutum. Can kuma ya sauke ajiyar zuciya yana ta nazarin inda Rashida zata samo hiv da tsakar rana.
“Amman ƙara dai a bincika, ba lallai ba ne tana ɗauke da ciwon to ina ma zata kwaso wannan ciwon?”
“Hilal mana, ai shi kaɗai ne mutunen da take taraiya da shi”
Cewar Momy tana kuka, zuciyarta na ayyana mata shi ɗin ne tun da shine kaɗai mijin Rashida. Da sauri Dady ya kalleta
“Wallahi idan kuwa shi ne ya saka mata shi, sai na ɗaure shi gidan yari har ƙarshen rayuwarsa, marar mutumci marar taddako wanda be san halin girma ba, Allah ya usar mana, wallahi ya cuce mu, shiyasa ya sako ta. Ina Rashida take ne?”
“Tsna ɗakinta, ta ƙi ts buɗe tun ɗazu sai kuka take, ta ƙi tayi magana ma”
Tashi yayi yana cire ƴar saman suit ɗinsa, yana sassauta necktie ɗinsa, ya nufi ɗakinta jikinsa har rawa yake kamar mazari.
Sai da ya soma kiran sunanta, jin bata amsa ba yasa ya soma ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin.
“Rashida ni ne buɗe mana... Ba wani abun za mu miki ba kawai magana za mu yi, kuma ba zamu faɗawa kowa ba”
Tana jinsa amman ta kasa amsa masa dan bata da abinda zata faɗa masa, tasani matuƙar suka gano gaskiyar dalilin cutar nata ba zasu zauna da ita ba, who else kuma zai zauna da ita bayan iyayenta, lallai ko a haka rayuwa ta tsaya mata ta san ta kai karshenta.
Babu irin maganar da Dady be mata na rarrashi da tausasa zuciya ba, amman ta ƙi ta amsa masa balle ma har ta buɗe ƙofar.
Dawowa yayi ɗakin Momy ya tsaya daga jikin ƙofa fuskarsa da damuwa ya ce
“Ko dai za mu kira shi ne mu tambaye shi?”
“Idan shine taya zai amsa cewar shi ne? Zai yi ƙoƙarin kare kansa ne, kuma kasan babu wanda Rashida take mu'amala da shi sai Hilal dan shin mijinta kuma ni ƴata ba ƴar iska ba ce, ta bakinta ya kamata aji komai”
“Ta ƙi tayi magana, ɗakin ma ta ƙi ta buɗe”
“Zata yi magana, dole zata buɗe kabarta hankalinta ya kwanta kawai, ka koma gurin aikin ka”
“Ba zan iya wani aiki ba ko naje, jikina ya riga da ya mutu, Wallahi Hilal ya cuce mu, amman miyasa Rashida ta yi ƙoƙarin ɓoye irin wannan babban al'amari?”
“Allah kaɗai ya sani, amman rufawa irin wannan mutumen asiri ai ba abun yi ba ne, wallahi sai na sashi yayi nadama sai ya ƙwammace kiɗa da karatu”
A bakin ƙofar Dady ya zauna irin zaman nan na baka san ka yi ba, hankalinsa baya jikinsa, natsuwarta ta gudu ta barsa.
*NAMRA POV.*
Maganganun Asim sun tsaya mata a zuciya, duk bayan dogon numfashinta sai kalmar rabuwa da yayi mata ya maimata kanta a kunnenta. Da zancen ta kwana a ranta, tana mamakin Asim, yadda yayi tsaye yana faɗa mata magangu kamar wani ɗan shaye-shaye. Bw ɗauke a matarsa ta sunna ba be riƙe ta da muhimmaci ba, shiyasa har ya zaɓi aikin da yake sama da ita, yanzu kuma yake neman rayuwa da ita saboda tana da ciki. Sai yanzu take nadamar rashin bin Anty, dan tasan babu makawa Asim rabuwa zai yi da ita, matuƙar bata zubar da cikin ba, dan ta ga gaskiyar maganarsa a idonsa, sai dai ita kuma bata jin zata iya zubar da cikin ko da kuwa shege ne balle na Sunna.
Sai dai idan Asim ya sake ta ina zata je? Ta koma gida da ciki ta faɗawa Abbah Asim ya sake ta? Ta bi sawon Anty bayan ta nemi taje gidan ta ƙi yarda sai yanzu da Asim ya sake ta kuma take ɗauke da cikinsa.?
Tashi ta yi zaune, sai ta nemi kuka da take ta rasa, washe ƙaramin abun ake yi ma kuka, tashin hankalin dake tare da ita baya barin hawayenta zuba.
“Kaico na ni Namra, Ina zan sa kai na sanyi? Ina zan sa rayuwar na samu sassauci? Haƙiƙa wanda duk ya so abinda iyaye suka ƙi yayi hasara, da nasan haka aurena da Asim zai kasance da ban aure shi ba, Allah ka yi min gata Allah”
Hannayenta ta ɗaga sama, tana roƙon Ubanjiginta, zuciyarta cike da yaƙinin lallai Allah zai ƙarɓa mata.
“Ya Allah ka tsare min mutunci na, ka tsare min lafiyata,
Allah ka yi min gata ka tsare min imani na da hankalina,
Allah ka yi min sutura ka kwantar min da hankali
Allah ka kyautata min rayuwa ta, Allah idan aure da Asim Alheri ne Allah ka tabbatar da shi, idan rabuwa da shi ne samuwar jindaɗina Allah ka zaɓa min abunda yafi zama Alheri a gare ni,
Allah ka shirya tsakani na da iyaye na, Allag ka gafarta min kurakurai na
Allah ka tabbarda duga duga-dugaina akan addinin ka”
Bayan ta shafa ta koma ta kwanta, ta kai hannu ta shafa cikinta, tana mai jin tsantsan ƙaunar abinda yake kwance a mararta.
*ABDOOL POV.*
Misalin ƙarfe biyu da rabi na rana jirginsa max air ya sauka a tashar sauka da kuma tashin jirage da ke katsina.
Be sanar da Ummi zuwansa ba, dan haka be tsamaci ta tarbe shi ba, ko ta aiko da motar da zata ɗauke shi. Sai dai hakan be a aiko masa da motar da zata ɗauki daga headquarter ba dan sun san da zuwansa.
A yadda suka tarbi shi ya burge kowa a gurin, mota uku suka faka. Already sun buɗe motar suna hangosa tafe sai suka duk suka fito wajen motar suka tsaya, a jikin kayan gida yake amman hakan be hana dukansu su tsara masa ba, babu wanda yayi motsi a cikin su har sai da ya shiga motar sannan suka rufe masa suka shiga.
“Gurin Mai Martaba zamu je”
Yanda yayi maganar ba ka ce shi ne ba, dan hankalinsa gaba ɗaya yana kan wayarsa sai faman duba shafukan yana gizo yake dan sanin abinda ƙasa take ciki.
Har aka isa Ahmad Mai-doki road, Abdool be ɗago ya kalli mai driving ɗinsa ba, balle ti-ti. Yana jin motar ta tsaya ya buɗe ya fito ƙamshin gidan ne yasa shi murmushi, dan ƙanshim gidansu daban yake, ko'ina ya ke zai iya gane ƙanshin gidan Mai-martaba.
Sai da ya shiga cikin gidan ya gaishe da mahaifansa, matan sarki sannan ya wuce faɗar mai-martaba. Be same shi a faɗar ba, hakan ya tabbatar masa da yana can turakarsa yana hutawa, tun da yaga motocinsa a waje balle yayi tunanin ko ya fita. Ta faɗar ya bi ya shiga turakar Mai-Martaba, a falon farko ya same shi zaune yana duba air conditioner da ake kan saka masa. Faɗawan na ganin Abdool duk suka faɗi suna ɗiban gaisuwa, shi dai hannu kawai ya ɗaga musu dan baya son irin gaisuwar nan da suke masa, ya fi gane a tsara masa ko a maƙe idan an ganshi. Da murmushi ya zube gaban mahaifinsa yana ɗiban gaisuwa.
Kallonsa Mai-Martaba yake da mamakin zuwan ba zata ta, sai kuma ya kai mafeshin Peacock dake hannunsa ya shafi ka ɗansa da shi. He didn't say a word dan baya son magana da Abdool a gaban faɗawansa ko baboro, yafi son sai ya keɓance yadda zai dake da shi kamar ba ɗansa ba.
Ko ba komai nuna tsantsar ƙaunar da kake wani daga cikin ƴaƴansa babban laifi ne kuma ya kan haddasa ƙiyayah, sai dai hakan be hana familynsa depending ya fi son Abdool da kowa ba, dan abu ne da ko ya ɓoye sai dai ya ɓoye mai yawan ka buɗe kaɗan.
Yana unƙurawa zai miƙe tsaye sai faɗawansa suka zo da sauri suka tara rigunansu, suna masa kirari har ya miƙe tsaye sannan suka rufa masa baya suna masa fita.
Hannu kawai ya ɗaga musu suka fahimci baya buƙatar su raka shi har can, sai kawai suka juyo gurin Abdool suna masa nasa kirarin. Be tsaya jinsun ba ma balle ya nuna masu jindaɗin abunda suke masa sai kawai ya bi bayan Mai-Martaba hannayensa laƙƙame a baya yana tafi guda-guda kamar mai takewa President baya.
Sai da suka wuce falon biyu da na uku, suka wuce garden ɗin Mai-martaba sannan Mai Martaba ya ƙarasa a wata ƴar ƙaramar rumfa mai kyau da ɗaukar hankali ya zauna, shi kuma Abdool ya zauna ƙasa complain ɗin kiraren da suke masa.
Ɗan murmushi Mai-Martaba yayi irin na na manyan sarakuna, yana kallon ɗan nasa cikin farinciki da jindaɗi.
“Wata rana kai Sarki Abdool, irin wannan kalaman be kamata yana fita daga bakin ka ba”
“Haba Mai -Martaba ta ya zan zama sarki bayan Ina da yaya? Kuma ni wannan sarautar sam ba burgeni take ba”
Mai-martaba ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora akan ɗayar yana murmushin ƙasaita.
“Har gobe Babana baka san Sarauta ba, saboda ka guje mu a lokacin daya kamata acr ka zauna ka karanci komai na gidan nan, baka san jidaɗin sarauta ba, shiyasa kake wannan furuci, na kan lura da yanayin ka sam baka sakin jiki a harkokin sarautar gidan nan, balle na wani gurin, abu kake kamar ba ɗan sarki ba, ai yanzu kuɗi da milki su ake ɗubi abawa mutum sarauta balle kuma kai da ka cancanta dan kana da natsuwa da hankali ga tarbiya”
“Mai martaba wannan sarautar fa dai ku. Ina fatar na samu sarki cikin ƙoshin lafiya”
“Yareema ya samu Mai Martaba cikin ƙoshin lafiya da walwala, ya aka yi ka yi mana zuwan ba zata? Gashi ba ko wane abinci kake so ba balle na ce a ɗibo maka”
“Na samu hutu ne jiya, shiyasa na dawo gida as surprise kasan turawa sun ce surprise is better than disappointed”
“Aiko kayi tsara kan gaɓa, daman akwai ɗaurin auren Abubakar Saturday, daman kai na ke son ka walkice ni, kuma daman can Abubakar ɗin nan abokin ka ne”
Abdool ya shafa kai
“Wai har auren ya tashi ne ? Kwanaki wani friend na mu yake ce min an kai masa kaya”
“Kai ma ai naka yana kusa, mun soma duba maka na dangi kamin mu fita waje, tun ka bamu zaɓi”
Ko be tambaya ba yasan Ummi ce tayi wannan maganar, on behalf of him. Ɗan murmushi yayi ya ce
“Ina za'ayi ɗaurin auren?”
“Zariya, ƴar sakin Zazzauce zai aura, Saturday nan”
“Okay zan je inshallah”
“Ba wai zaka je ɗin ba, ka tabbatar an ganka, zan haɗa tawagar da za kuje daga nan, kuma zaka je ne cikin shigar sarauta, sadauki zai naɗa maka rawani idan kunje can”
Ƙure yayi ma Mai martaba da ido yana kallonsa. Mai martaba yasan waye ɗansa kuma ya san kallon da yake masa.
“Kar ma ka soma, kai shikenan baka son shiga mutane? Ƴaƴan saraku irinka amman baka son shiga cikin su? Rabon ka da rawani tun a hawan salla, ni wannan rayuwar ta ka bata min Yareema, wasu ma basu kao darajarka ba basu kai muƙamin ka ba, sannan sarautar ta su ƙarama ce amman su yi ta tinƙaho suna nuna isa balle ka!”
Yayi tsuntsun da kai, yana murmushi, dan yasan Mai Martaba ya kamo tasharsa.
“Ai ban ce komai ba Mai martaba”
“Na san zaka ce ɗin ne. Tashi ga ruwa can ɗauko ka sha, kar kaje ka ce wa uwarka baka ci komai gidan Mai Martaba ba”
Ya tashi yana murmushi ya nufi wani ɓangare na gurin da aka jera freezer biyar a gurin dan shan ruwa kawai da lemu.
Be bar gidan ba sai da Mai- Martaba yasa aka daba masa wani abu ya ci. Bayan yayi la'asar, yayi ma Mai Martaba sallama sannan ya nufo gida gurin Umminsa.
Gaisuwar ban girma da tadabi sojojin gida suka masa suna masa maraba da zuwa.
Har zai wuce part ɗinsa sai kuma yaji ba zai iya ba har sai ya saka mahaifiyarsa a ido. Da far'ah da zumuɗi ya nufi part ɗinta.
Tun daga yanayin yadda yaga falon zuciyarsa ta raya masa Ummi bata cikin gidan. Sai ya ɗauki remote ya kashe plasma ɗake falon sannan ya nufi ɗakin Ummi dan tabbatarwa. Haleema ya gani kwance saman gado Amira kuma na gurin tufafinta tana gyarawa.
“What nonsense is this?”
Ya faɗa a tsawaci. Daga Haleema har Amira zuyowa suka yi suka kalleshi dan babu wanda yasan da shigowarsa. Da sauri Amira ta zube ƙasa tana miƙa masa gaisuwa zuciya na bugawa da ƙarfi, haka kawai ta samu kanta tana mai tsantsar kunyarsa.
Be amsa gaisuwar ba sai kawai ya watsawa Haleema harara, ita kaɗai tasan abunda Hararar tasa take nufi sai ta sauka saman gadon da sauri ta kama hannu Amira suka fice.
Sai ya ƙofar ɗakin ya rufe da key, ya cire keys ɗin ya nufi part ɗinsa da shi. Yana shiga ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul ya shiga Bathroom.
Ya ɗauki kusan mintuna arba'in a banɗakin yana cuɗa jikinsa kamar wanda zai canja fatarsa. Bayan ya gama wanka ya ƙarasa gaban madubi yana ƙara gyara gemensa da babu komai a gurin.
Sallamar da yaji ana ta dokawa ne yasa ya wanke fuskarsa ya fito. Ya nufo falonsa. Amira ya samu tsaye a gurin hannunta riƙe da cup ɗayan hannun kuma riƙe da wasu dinner set an rufe su da ɗayansu.
Tana kallonsa gabanta yayi mummunan faɗuwa, bodybuilding ɗinsa ne ya tashi hankalinta, yadda aka tsara jikinsa da faffanɗan ƙirjinsa, ga fararen idon nan kamar an watsa masa madara tabbas shine irin mijin da take so.
“How may i help you?”
Ya tambaya ganin yadda take kallonsa kamar bata san da shi a gurin ba. Sai da ta gyara tsayuwarta gudun faɗuwa sannan ta miƙa masa duka abunda yake hannunsa.
“Coffee and fruits, tuwo ne aka yi kuma Haleema tace ba ka son tuwo, shine na haɗa maka wannan”
“Thanks i'm not a coffee drinker”
Fruits ɗin kawai ya karɓa ya aje saman kujera ya bar mata coffee. Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalleta
“By the way bana son texts ɗin nan da kike tura min, ki daina please”
Kai ta ɗaga masa idonta na son cika da hawaye.
“Note”
“You may go”
“Thank you”
Jikin sanyi jiki ta juya ta fice, hawaye na bin fuskarta. A yadda ta fahimta kamar bata burge Abdool kwata-kwata irin ɗan sakewar nan ma baya mata shi.
Haleema na gani hawayenta tasan ba lafiya ba, daman kuma tasan za'a rina indai Abdool ne.
“Wani abun ya ce miki ne?”
“A'a kawai ina ganin kamar bana gabansa, kwata-kwata bana burgeshi”
“Daman ai shi namiji ba zai so ki lokaci ɗaya ba, komai a sannu yake zuwa, ni yanzu abinda nake so ki yi ta yin abinda zai ja hankalinsa gareki, har shi da kansa ya furta yana son ki, dan naji Ummi na maganar wai Mahaifinsa yayi masa mata”
Amira ta kalleta da sauri.
“Da gaske?”
“Wallahi amman kin ga idan shi da kansa ya ce ke yake so kin ga dole ki a ƙyale”
“Amman me kike ganin zai sa ya so ni?”
“Irin wannan ladabin da kike cigaba, kuma ki riƙa shige masa ki riƙa haɗa masa abu ko da be buƙata ba, sannan idan da hali ki koma gidanku, saboda zama a gaban iyaye yana da muhimmanci, sosai Ummi ma da kanta zata fi ganin darajarki idan kina zaune a gidan ku”
Shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya, har ga Allah ita kanta tana son komawa a gurin iyayenta amman ba hali bata iyawa, bata san yadda zata yi ba.
“Zan yi ƙoƙarin yin hakan inshallah”
“Allah ya taimaka nima ina son ki auri Yaya Wallahi”
Amira tayi shiru yana cigaba da tunanin rayuwarta.
*ASIM POV.*
Tun ranar daya bar gidan Namra be sake leƙawa ba, duk jin yake ya tsane ta ma, daman can baya akan cilas ne yake zaune da ita yanzu kuma yaji zai iya auren wata. Sannan yana ganin haihuwa a yanzu zata iya kawo masa matsala, dan haka shi be shirya haihuwa a yanzu ba.
Yau ma kamar kullum da tea da kwai yayi breakfast, sai da ys ci yayi nas sannan ya tashi yayi wanka, bayan ya fito ya shirya cikin wasu tufafin masu kyau da tsada ya shiga sashen uwar ɗakinsa dan gaisheta.
Be same ta a falo ba, sai kawai ya wuce har ƙurƴar ɗakinta dan ta daɗe da bashi damar hakan matuƙar ba mutanr ya tarar a gidan ba. Bedsheet ya tarar tana gyara jikinta sanye da kayan bachi.
Yana ganinsa ta zauna saman gadon tana murnushi.
“Asim an tashi?”
“Eh Hajiya ina kwana?”
“Lafiya ƙalau Alhamdullah, ka yi kyau mashallah”
Ya ɗan sunkuyar da kai.
“Hajiya na ce ko akwai abunda za'ayi miki?”
“A'a gaskiya yanzu kam babu sai dai zuwa anjima. Amman karka manta fa na faɗa maka za mu yi baƙo gobe zai zo daga garin ku, kuma dan kai kawai zai zo garin nan, ina fatar zaka ba shi haɗin kai, yana gida a nan idan ya zo a gidansa zaka je, zan baka maganin da zaka sha, kums ka tabbatar kana kallon videos dana tura maka ɗin dan kasan yadda zaka sarrafashi”
“Karki da mu inshallah ba za'a samu matsala ba”
“To yayi kyau haka na ke so, sai kuma a samu wata ƴar sana'a a riƙe gudun zargin mutane, ina ganin ma nan gaba kadan garin ku zai maida kai dan can yake”
“Nima ai zan fi jindaɗi dan akwai waɗanda na ke son su san nayi kuɗi dan sai na rama wulaƙancin da duk aka min”
“Allah dai ya taimaka, idan ka saki jiki ina faɗ Maka nan gaba kaɗan sai an saka ka a cikin matasan da suka fi kowa kuɗi a nigeria”
Wani kalar daɗi ne yaji marar misaltuwa. Kaɗan ya labarta mata irin gwargwarmayar da yayi da iyayen Namra sannan ya taso ya fito yana auna kansa a mizanin arziki.
Falonta ya dawo ya zauna, yana duba shafin facebook da sabuwar wayarsa. Yau ma ya tararda friend requests kamar wacan lokacin. Da kuma da kuma saƙon wata kyakkyawar yarinya ta tura masa dan katun ɗin nan na facebook mai cewa mutane Hi.
Reply yayi mata.
_“Hey How you darling”_
Sannan ya shiga profile ɗinta yana duba hotunanta.
“Wow wannan kan ba dai fari ba da kyau, irin wannan idan ka samu irinta ai ka huta”
Nan da nan yayi saving hotunanta, sai ya dawo inda taƴi masa reply yana ƙara amsa mata.
_i'm fine. By the way am Nabila Lawal Alƙali aka Pretty Nably. from Katsina living in Abuja_
_Nice to meet you dear, i'm Asim Ibrahim Sanusi aka Asim From Sokoto living in Katsina_
Bayan kamar minti ɗaya sai ta sake aiko masa wani.
_Wow which area in Katsina? I know Katsina in and out_
_Nasarawa road. Send me your number let's chat on whatsapp_
Cikin ƴan mintuna ta turo masa number. Sai da yayi saving sannan ya sauka daga kan facebook ɗin ya tashi ta fito ransa fari fes.
Motar daya saba shiga ya shiga, wacce ta zame masa kamar tasa.
Tun da ya doshi hanyar Nasarawa rayuwarsa ta soma baci, sai faman jan tsaki yake yana nasalta yadda zai tararda Namra.
“That's why i hate baƙar mace, da sun kwana biyu zaka ga sun lalace babu ko kyau kallo, ji jikinta dan Allah duk ta bi ta zube sai ƙassa me zaka kallo a jikinta ma ka yi sha'awa, mtsssss”
Be ji zai shiga da motar cikin gida ɗan haka ya faka ta a ƙofar gidan ya shiga yana wani yatsinar fuska, kamar bada aka yi rayuwa a gidan ba.
Zaune ya hango ta tana ta faman wanki tufafinta. Tana jin sawon tafiyarsa amman ta ƙi ta ɗaga kai ta kalleshi dan be yi sallama ba, kuma tasan abunda ya kawo shi a gidan be wuce abunda take zargi ba.
Zaunawa kawai yayi kusa da ita yana mata wani kallo kamar ba matarsa ba.
‘Ai dole na yi aure a ina zaka nuna wannan ka ce matar ka ce? Abu busasai haka’
Furucin da yayi a zuciyarsa kenan, a fili kuma sai ya ce.
“Sannu da aiki”
“Yauwa”
Ta amsa ba tare data kalleshi.
“Kin koma asibitin ne?”
“Bana da kuɗin hoto”
“To ma ba wannan ba, wace shawara kika yanke ne?”
Kallonsa tayi sai hawayen dake maƙale a idonta suka zubo
“Yanzu abunda kake min ka min adalci kenan? Shikenan kai babu ruwanka da danuwata kullum ni kaɗai nake kwana a cikin gidan nan idan ma wani zai shigo yayi min fyaɗe ko ya kashe ni sai dai ya zo? Asim miyasa kake min haka ne? Ka mayarda ni kamar karya marar amfani”
Hannu ya kai yana shafa ta, dan har ga Allah yayi missing ɗin jikinta.
“Ba haka bane Namra, sai da muka xauna da ke muka yi magana kan aikin nan kika ce kin yarda sai kuma yanzu ki fara complain ko dai ki shi kike ne?”
“Kishin me?”
“Kin ga zan yi kuɗi mana”
Ya faɗa da ƴar dariya, ita kuma sai tayi masa wani kallo.
“Ka min ka yi kuɗi Asim, dubun ka sun yi, wasu sun mutu sun bar kuɗin, wasu kuma kuɗin sun guɗu sun bar su. Kamin ka sanya rigar dubu goma, sai da nasa ɗan kunnen biliyan biyu da rabi na zinari, dan haka kuɗin da zaka yi basa burge ni balle na yi ƙyashinka”
Wata dariyar rainin wayo yayi.
“Amman ai kyau abu akan gashi a ƙasa, da muka yi aure mi Babanki ya kawo mana?”
“Me zai kawo maka, bayan yasan ka auri ƴarsa saboda abun hannunsa ne? Ai shi ba lurasari ba ne, irin Mama mai nuna sun abun duniyarta a fili”
Ya nunata da yatsa.
“Karki sake uwata a maganar ki wallahi”
“Nima karka sake saka ubana, dan cin mutunci ba gado bane kowa ya iya”
“Dube ki dan Allah ni in ban da kaɗɗara ma mi zan yi da irin ki?”
“Lallai kam kaɗɗara ce Asim da nima babu abunda zan yi da irin ka, dacan baka san da haka ba, sai yanzu? Dan kana jin nera ta fara keta wuyanka? Ko da yake hausawa sun ce ɗan talaka be iya samun guri ba”
Tasssss ya wanke mata fuska da mari. Ita kuma ta ɗauki bokitin da take wanki da shi ta juye masa ruwan wanki ta jeɗa masa bokinta. Zuciyarta ta kawo sosai ita kanta a yanzu ta san ba kuka take da buƙata ba, dan ta fahimcin idai har ta ƙyale Asim zai iya hallakata.
“Karka sake kuskuren taɓa min jiki dan ni ba baiwa ba ce kuma ba jaka ta siyo ba”
“Ni kika jiƙe da wannan ruwan? Wallahi sai kin raina kan ki dan sai jikinki ya gaya miki, ba ke fa wallahi yanzu ko ubanki nafi ƙarfinsa balle ke, banza a banza, kuma wallahi kije a zubar da cikin nan ko yanzu ki yi gidan ubanki wallahi, dole ki zaɓa”
“Wallahi ba zan zubar ba. Sai dai ka sake ni amman ba zan zubar da wannan cikin ba”
“Haka kika ce?”
“Haka nace kuma haka na zaɓa”
“To kije gidan ku na sakeki sa..ki ...ɗaya.... Idan kin zubar ki dawo zan maiyar da ke”
Kamar an sako duwatsu haka Namra taji saukar furucin Asim da bata tsammaci zai mata shi da gaske ba. Zubewa ta yi ƙasan guiwowinta tana masa kallon mafarki.
“Da gaske Asim ka sake ni?”
“Na sake ki mana, ba kin zaɓi abunda be isa aka masa numfashi ba balle ma har ya zo duniya ba, sama da ni”
Kai ta ɗaga masa wasu hawaye masu zafi suna bin kumatunta tace
“Na zaɓe shi sama kai, kamar yadda na zaɓe ka sama da iyaye na acan baya, na zaɓi ka sama da karatu na, na zaɓe ka sama da jindaɗi da arzikin da yake gidan mu, na zaɓe ka sama da samarin da suka yi so na, na biyo ka garin da ban san kowa ba sabida kai. Amman yau ni ka yi watsawa ƙasa a ido, lallai kai butulu ne Asim, ka tabbata ɗan bushiya. Duniya ce Asim wanda be zo ba ma ta shiriya masa balle wanda yake cikinta, ka taka a sannu dan duniya ƴar ɗauka da ajewa ce...”
Tsaki kawai yaja ya ɗauki keys motarsa da suke gurin ya juya ya fice cikin fushi. Da kallo Namra ta bishi wani irin abu ya soma zillo yana neman numfashinta.
*Best regards 🌺*
*Khadeeja Candy ♥*
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: Akwai inda na yi mistake jiya nasa ɗan kunnen biliyan biyu da rabi, miliyan biyu da rabi na ke nufi typing errors ne kuma ban yi editing ba.
*61*
NAMRA POV
Kwance tayi a gurin tana ɗaukar numfashi, sai lumshe ido take tana buɗewa, abu ya zo ya tsaya mata a zuciya kamar ƙashi kamar dutse.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Allahumma ajirna fi musibati wa'kalif ni khairan min ha”
Shine abunda take ta maimatawa tana yaƙi da zuciyarta, tana ji tana gani idonnuwanta suka fara nuna mata ba haka, sai dinshi-dishi take gani, kalmar sakin da Asim ya furta mata ne yake ta mata yawo a ƙwaƙwalwa. She just can't believe Asim ya sake ta, ina zata je? Minene a fita a gareta yanzu bata sani ba.
Hango kanta take a cikin gidansu Abbah yana korarsu ita da Anty. A ɗayan ɓangaren tana tunanin abubuwan da mutane zasu faɗa idan har aka ji aurenta ya mutu, duk wanda be son aurenta da Asim zai mata dariya idan ya ji aurensu ya mutu. Duka yaushe aka yi auren da har za'ace auren ya mutu, gashi duk ta lalace ta koma wata iri? Ciwon da yake jikinta za a ce sai da ta kwashi ciki da ciwon mahaifa sannan ta dawo gida.
“Azzalumi ma cuci Allah ya isa tsakani na da kai, Allah ya bi min haƙƙina”
Daga kwance da take tayi furucin tana kuka mai taɓa zuciya. Bata san inda zata je, tun da taƙi ta bi Anty Amarya tun da farko, yanzu kuma tace mata me?
Haka ta kwanta a gurin jikinta ya ɗige gaba ɗaya, kamar an zuba kayan wanki.
Sai ta taji an kira sallah azahar sannan ta samu kuzarin unƙurawa ta miƙe tsaye. Har taje tayi wanka tayi alwala abu ɗaya ne yake mata yawo.
Idan har Asim ya dawo ya tararda ita a gidan zai zaci ko dan tana son ya mayar da ita ne. Ita kuma yanzu ta yanke ƙauna da shi, idan akwai wanda ta tsana a duniya Asim ne, kuma har gobe bata nadamar zaɓar abunda yake cikinta saman da Asim.
Bayan ta yi sallah azahar ta ɗora da nafili sannan ta rokowa Allah buƙatarta, ta kai masa kukanta ta miƙa masa lamurranta.
Jingina ta yi da ginin gurin tana kuka, da hawaye masu zafi. Irin mutanen da suka yi nemanta aure take tuna amman kowa ya zo tace sai Asim, ayau Asim ɗin ne ya zaɓi rabuwa da ita saboda cikin shi, jininshi.
Tashi tayi ta koma saman katifa ta kwanta, tana kukan zuci wanda ya fili illa da baƙinciki. Wayarta tayi ƙarar saƙo duk da taji daɗin kwanciyar hakan be hanata unƙurawa ta ɗauƙi wayar ta duba ba.
_Karki kuskura cewa za ki siyar da gidan nan, amman na miki lamani ki zauna har ki canja shawara, idan kin yi tunani mai kyau na shirya maida ki a matsayin mata ta!_
“Kaico...”
Shine kawai abunda ta furta bayan ta gama karanta text ɗin ta share hawayenta. Kanta ta ɗaga sama tana kallon ɗakin, kwata-kwata jin tayi gidan ya fita a ranta. Sai dai kuma bata da gurin zuwa, duk inda zata je be yi kamar gidan mahaifinta ba, da ace Abbah ba xai wuƙantata ba, da ba zata damu da maganar mutane ba matuƙar tana gidansu, a ƙarƙashin iyayenta.
Hijabinta ta ɗauka ta saka, ta ɗauki jakarta da wasu ƙaƙanan abubuwa nata ta saka a jakar sannan ta fito, tun da ta baya bq ɗin baya ta sake kallon ta ba har ta fice daga gidan.
Fuskarta ta kumbura sosai haka ma idanunta, duk wanda ya ganta zai san tayi kuka, hakan yasa ta sanda kai ƙasa har ta isa titi. Napep ta tara sai da ta shiga sannan ta soma tunanin inda zai kai ta. Bata da wadataccen kuɗin da zata kama wani gidan ta zauna, kuma ta san ba mutuncin ta ba ne ta kama gida a wani gurin. Kuma bata jin zama a gidan dan zata iya aikata komai saboda baƙinciki.
“Hajiya ina za a kai ki?”
Tsayawa tayi tunani, har tashi Napep ɗin.
“Kai ni tashar mota, inda ake hawa motar sokoto”
“To amman yanzu tashar gov sun tashi sai dai babbar tasha”
Ya hau kan titi yana ƙara ƙure volume ɗin napep ɗin dake tashin wakar Umar m shariff. Ita dai saurare kawai take tana hawaye har suka isa, ɗari biyu ta ciro ta bashi ya miƙa mata canjin naira hansi sannan ta fita shi kuma ya juya.
“Sokoto, Kano, Kaduna, Abuja, jigawa, Kebbi, Zamfara”
Haka ƴan union ɗin suke ta faɗi suna neman passengers. Wasu suka yo kan Namra da gudu suna tambayar ta inda zata ta, tsaye kawai tayi tana tunanin inda zata ce duk da ta zo da niyar zuwa sokoto ne sai kuma ta ji ba zata iya, har tana jin ma kamar ta koma gida...
“Hajiya Kaduna zaki je?”
Wani daga cikin su ya tambaya, sai ta ɗaga masa kai.
“Eh Kaduna zan je”
“Ga mota can daman mutum biyu ake jira, ina kayan ki suke?”
“Bana da kaya”
“Okay muje ga mota can”
Shine yayi mata ja gaba har gurin motar, sannan ya faɗa mata kuɗin motar. Cikin rashin kuzari ta cire ta biya, sannan ta shiga motar tana ta doubting akan taje can ɗin ko kuma a'a. Idan taje kaduna gurin wa zata je? Tun da bata taɓa zuwa ba duk da akwai taubashiyar Anty Amarya a can amman bata tunanin zata gane inda take tun da zuwan da duka yi tun da daɗewa ne kuma da motar gida, sunan unguwar ma bata riƙe sosai ba.
ASIM POV
A sale ya fito daga gidan, bama abunda ya fi baƙanta masa rai kamar jiƙa masa tufafi da Namra tayi, Yana ƙoƙari buɗe motarsa ya hango Mardiya tafe, ɗan tsayawa yayi yana kallon takunta, cikin yanga izza take tafiyar dan kuma kawai ta ɗauki hankalinsa ne. Shi kam yasakar mata ido sosai yana kallonta duk da jiƙaƙin tufafin ne a jikinsa, amman hakan be hana shi tsayawa gurun motar ba har ta iso, dan kawai ta ga shine yake tuƙa motar, yasan ko ba komai zai burge ta tun da yasan mata sun fi son mai mota.
Sai da ta kusa ƙarasowa sannan ya buɗe motar ya ciro ƙyale yana goge jikinsa.
“Asim ina kwana?”
Ta gaishe shi cikin kashe murya da ƙarawa muryar zaƙi. Da sauri ya kalleta yana murmushi kamar ba shine ya fito rai a ɓace ba.
“Ah lafiya ƙalau Mardiya ya gidan?”
“Gida ƙalau wallahi miya jiƙa mata kaya haka?”
“To sha'anin ne kin san halin na ku sai a hankali. Gari za a ne?”
“Eh wallahi zan ɗan shiga gra ne”
“Okay shige na aje ki”
“Mashallah ka siye sabon mota ne?”
Ta faɗa tana kallon motar cike da burgewa.
“Eh ai tama kwana biyu, sabuwa dai muke jira”
Buɗewa tayi ta shiga, sai shima ya shiga yana ƙoƙarin tashin motar ta kalli gate ɗin gidansa ta ce
“Kar fa Namra ta hango mu ko a kai mata rahoto”
“Mtsssss amman Mardiya ma kin mai yarda ni wani wawa, ni kam ai nafi ƙarfin matata ba irin mazan nan bane na banza, ashe ke matsoraciyace ba zaki iya kishi da ita ba”
“Ai kishi dabam, da ace yanzu aurna na ne zaka yi to bana shakar taji komai, amman kaga yanzu babu wata magana ta aure dole na ji tsoron irin maganar da zata je mata a kunne”
“To kisa a ranki auren ki zan yi”
Ya faɗa yana ƴar dariya. Itama dariyar tayi mai cike da jindaɗi. Har ya kai ta inda zata je fira suke kamar masu masoya ita kuma sai wani lanƙwashewa take tana karairaya. Daman shi tuni da kasheshi da kalamanta ma.
Daga gra ya wuce gidan Hajiya Sadiya, be same ta a gidan ba hakan ya tabbatar masa da akwai inda taje kenan. Ɗakinsa ya shiga ya canja tufafin jikinsa ya saka waƴan can a washing machine sannan ya dawo ya zauna. Yarinyar ɗazu ce ta faɗo masa a rai a ƙoƙarinsa na kawarda tunanin Namra a ransa dan ganin yake ita babbar maƙiyiyarsa ce, ko kaɗan baya nadamar sakinta da yayi kuma he's ever ready ya mai data idan ta yarda ta zubar da cikin.
Number yarinya ya nemo ya danna mata kira, ringing biyu ta ɗauka ciki muryarta mai sanyi. Cikin turanci ta soma watsa masa tambayar wake kiran shima ya maida mata da yaren da tafi ganewa. Nan da nan ta sake da shi suka gaisa duk kalmar da tayi masa sai ya maida mata, ya ɗan tambaye kaɗan daga rayuwarta, sai da amsa masa a inda abunda take tunanin ya sani. Ya jidaɗin da tace masa ita ƴar Katsina ce, daman ta faɗa masa tun a chat amman a yanzu ne take faɗa masa sunan unguwarsu a Katsina.
Sun daɗe suna waya sannan yayi mata sallama ya kashe wayar. Ko da ya kalli ogagon ɗakinsa ƙarfe biyu saura ya gani, sai ya tashi yaje yayi alwalah yayi salla a cikin gida. Bayan ya sallame zancen gidan ya faɗo masa rai, wai kar dai Namra tace zata sai da gidan ta gudu da kuɗin. Wayarsa ya ɗauka ya aika mata text sannan ya kunna data shi.
HILAL POV
Yana cikin aiki wayarsa tayi ringing. Sai dai be duba mai kiransa ba har sai da ya kai ƙarshen duba marasa lafiyar da yake.
Sai da ya gama da duka katinan da suke gabansa, sannan ya tashi ya nufi office ɗinsa yana duba wayar. Number Dady ya gani Abbah Rashida, yayi mamakin ganin kiran, sai dai be kawo komai a ransa ba dan a tunaninsa, akan maganar shiga kotu ne zai sa ya kira shi tun da monday nan mai zuwa za a shiga.
Sai dai ganin text ɗinsa ya sa gabansa faɗuwa, miyasa yake son ya zo gidansa ya gansa? Duk akan maganar ne ko kuma wani abun daban. Ba tare da shakar komai ba ya shiga office ɗinsa ya cire ƴar samansa ya ɗauki keys ɗinsa ya fice.
Cikin ƴan mintuna ya isa gidan su Rashiida yayi gudu ne a hanya sosai, dan baya son Rafiq ya farka baya kusa. Yana ganin Motar Rashida da ta Dadynta yasan tana cikin gidan.
Be fita cikin motarsa ba har sai da ya kira Dady yace masa gashi ya iso.
“Ka shigo ciki”
Shine reply ɗin da ya masa a wayar cikin tsawa, ko kaɗan Hilal be ɗauki haka a wani abuba dan har gobe yana girmama iyayen Rashida tun da akwai ƴaƴa a tsakaninsu, kuma duk mutumen daya aura maka ƴarsa ya fi gaban ka raina shi ko da kuwa kun rabu da ƴar ne.
Buɗe motar yayi ya fito, yana tuna when last ya shigo gidan nan. Babban falon Dady ya nufa daman ko lokacin da yana surukinsu a can Rashida take sauke shi idan sun zo gidan.
Yana shiga ya samu Dady zaune yana jiran ƙarasowarsa. Momy ma tana zaune daga gefe tana watsa masa harara. Cikin ladabi ya ƙarasa ya zauna saman kujera yana gaishe shi. Dady be amsa ba dan ba gaisuwar ce a gabansa sai kawai ya hau shi da kalamai masu zafi.
“Ma cuce mayaudari, yanzu da kaga ka laƙa mata ciwo shine ka sake ta ko? Ai ni daman nasan sakin da ka yi mata bana Allah ba ne, kaje can kayi yawon ka ka samu cuta kaxo ka laƙa mata”
Ɗaga kai yayi yana kallon Dady maganar ta xo masa a baibai kuma da halshe biyu. Radhida ce ta faɗa musu ko kuma su suka gano haka? Har da shi tace yana ɗauke da cutar ko kuma ita kaɗai?
“Dady zan so Rashida tana nan kamin na yi magana”
“Ta zo ka kunsa mata baƙinciki ko? Ka zo ka ƙaryata ta ka ƙara mata baƙinciki ko? Ɗan iska marar mutumci, wallahi Allah sai ya isar mata”
Wannan karon Momy ce take magana tana wani ɗagowa kamar ta kama Hilal ta dake shi.
“Kuna magana ne a jahilce baku san gaskiyar lamari ba, ya kamata a kira Rashida ayi komai gani ga ta sai a fitar da wanda be da gaskiya”
Dady ya kalli Momy.
“Jeki ki kirata. Wallahi na rantse maka Hilal sai duk abunda na tara ya ƙare amman tun da kayi ma ƴata haka sai na wulaƙanta ka”
Ya ƙarasa yana kallon Hilal, jijiyar kansa har wani tashi take irin na ɓacin rai ɗin nan ya kai maƙura.
Momy ta tashi a hasale ta nufi sashenta. Kai tsaye ɗakin Rashida ta nufa sai da ta soma da buga mata ƙofa amman ta ƙi ta Buɗe har yanzu, sai kawai Momy ta zauna a gurin ta soma mata kuka.
RASHIDA POV
Babu yadda Momy batayi amman Rashida ta ƙi ta buɗe ƙofar har duka ƙanenta suka dawo daga makaranta.
Sai da aka yu salla la'asar sannan ta buɗe shima dan Momy ta zo ta zauna a gurin tana kuka ne. Da sauri Momy ta shiga cikin ɗakin cike da tausayin ƴarta.
Bata yarda ta zauna kusa da ita ba, sai dai space ɗin dake tsakaninsu ba wani mai tsawo bane sosai.
“Hilal ne ko? Shine ya saka min wannan cutar shiyasa ya zaɓi rabuwa da ke”
“Miye amfanin sanin wanda ya sa min wannan cutar, bayan cutar ta riga da ta kamani, babu amfanin ayi ta jayayar abu har a tona asirinsa, duk abunda ya faru da ni, Dady ne ya ja min”
Momy ta kalleta
“Ga Hilal can mum kira a falon Dady ki amman ya ce ba zai yi magana ba sai kina nan”
Gabanta yayi dakan huɗu-huɗu har bata san lokacin data kalli Momy baki sake ba.
“Miyasa kuka kira shi? Me zai muku?”
“Shine silar wannan ciwon na ki Rashida dole na zauna da ke, dan me zai sake ki”
Fashewa tayi da sabon kuka.
“Ni bana son ganinsa dan Allah yayi tafiyarsa”
“Ba zai je ko'ina ba har sai an tabbatar da wannan maganar yau”
Momy ta riƙa hannunta suka fito tare. Ba dan Rashida ɗin ta so ba, sai jan Momy dake janye da hannunta har suka isa falon. A jikin ƙofar Rashida ta tsaya ta risina kanta na ƙasa dan bata son kallon Hilal.
Shi kuma ya tsare ta da ido tausayinta duk ya kama shi.
“Dawo nan ki zauna, babu abunda ya isa yayi miki”
Cewar Dady yana nuna mata kusa da shi. Tasowa tayi ta dawo nan tana shirin zama kukan da take ɓoyewa ya fito fili.
“Yi shiru yanzu ba lokacin kuka ba ne, faɗi maganar ki”
Kasa magana Rashida tayi har sai da Hilal ɗin da kansa ya soma bada labarin abunda ya faru from a to z. Sun gamsu sun kuma samu tabbaci ganin yadda Rashida take ta kuka ta kasa ta kare kanta.
Dady ne ya miƙe tsaye ya soma safa da marwa. Ajiyar xuciya kawai yake saukewa yana maimaita
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Momy kan saka kanta yai cikin hijabi tana kuka. Rashida ma kukan take kamar ta mutu. Dady ya kalli Hilal cikin idonsa na marasa kunyar iyaye ya ce
“Zaka iya tafiya”
“Na gode”
Hilal ya furta sannan ya miƙe tsaye ya fice, jiki a sanyaye.
“Kin cuci kan ki Rashida kin kuma watsar da tarbiyar dana baki yanzu ai kin ci ribar zina sai kije ki auri wanda kuke aikata saɓon tare, uban waye ne ma wannan mutumen?”
Dady ya tambaya a tsawace. A nan Momy ta ɗago kai ta kalleshi cikin ɓacin rai ta ce.
“Duk waya ja mata wannan abun ba kai ba? Tana zamanta lafiya ƙalau da mijinta kace dole sai ta yi aiki, babu irin lallaɓar da yarinyar da mijinta ba su maka ba, amman ka dage akan dole sai tayi aiki, ai ga ribar aikin nan ta kwaso ta kawo maka, shine yanzu zaka taso ka rufe ta masifa ka barta ta ji da abunda yake cikinta ko so kake ta kashe kan ta”
Tashi Rashida tayi ta bar musu falon tana wani irin kuka kamar ta mutu. Momy ma miƙewa tayi tsaye ta fice a hasale tana kuka da bata san ranar tsayawar haweyen ba.
Komawa Dady yayi ya zauna har yanzu xuciyarsa bata gama gamsuwa Rashida ƴarsa tana ɗauke da cutar ba, shi dai ya fi son ayi wani gwajin.
Ajiyar zuciya ya sauke, wani yana tuna wani kalami da wata tayi masa a 1952.
KALSOOM POV
Har yanzu hankalinta ba a kwance yake ba, amman ba kamar da ba, dan yanzu tana da tabbacin Hilal ya yarda da ita, ta kan samu sassaucin hakan idan ta tuna.
Sai dai har yanzu bata cin abincin kirki, sai dai abu mai ruwa ko kuma ruwan kawai.
Tana cikin kitchen ta ji ƙarar tsayawar motarsa, nan da nan ta je aikin da take ta nufi ƙofar falo ta tarboshi.
Yanayinsa ya kararta da ita damuwar mijinta, dan haka bataa buƙatar tambayarsa akwai damuwa ko babu mafi ala kawai ta kwantar masa da hankali sannan ta nemi sanin dalilin damuwar tasa.
Da kanta ta zaunar da mijinta ta ɗauko ruwan sanyi ta siyaya masa a kofi ta kai masa a baki, kaɗan ya sha, ya ɗauke baki, sai ta cire ɗankwalinta ta soma shafe masa gefen fuska.
Hannunta ya riƙe ya jata zuwa ƙirjinsa ya rumgume ta, zuciyarsa cike da tsantsar ƙaunarta.
“Hajiya ta har yanzu bata yarda da ke ba”
Ya faɗa dan ya canja tunaninta izuwa wacan damuwar ta gurin Hajiya.
“Ba lallai ne tayi saurin yarda da ni ba, kuma tana da damar ta zarge ni yadda ranta yake so, zan ɗauki ko wani irin hukumci Hajiya ta yanke matuƙar hakan xai sa ta aminta da ni”
Tana kwance a ƙirjinsa take maganar hawaye na bin fuskarta.
“Hukuncinta ɗaya ne, wai sai na ƙara aure”
Ɗagowa tayi ta kalleshi ta girgiza kai ta fashe da kuka. Ɗan murmushi yayi dan kukanta ya sashi nishaɗi, yana shafa gefen fuskarta ya ce
“Ba zaki yarda mijin ki ya ƙara wata ba ko?”
Kai ta ɗaga masa. Sai ya ce
“To ya zaki yi da Hajiya?”
“Wallahi ban aikata ba Hilal Allah shine shaida na”
“Ai ba nine ban yarda ba, Hajiya ce bata yarda dake ba”
“To a tambaye Rafiq ɗin ai yana magana idan na bashi wani abun zai faɗa”
“Rafiq baya magana yanzu, ya koma wani iri kamar ba shi ba”
Cikin rashin jindaɗi yayi magana, yana ciro wayarsa dake aljihu tana ringing. Saurin picking yayi ganin number Nurse ɗin dake kula da Rafiq.
“Subhanallah okay gani nan zuwa”
Yayi saurin ɗaga Rashida daga jikinsa, ya tashi ya nufi ƙofa hankali tashe. Rashida sai tambayar lafiya take be kula ta ba.
ABDOOL POV.
Sai da dare ya dawo Part ɗin Ummi ɗan ya tabbatar ta dawo a lokacin. Duka falo ya same su zaune suna ta fira. Ummi na ganinsa ta aje lemun fata dake hannunta tana masa kallon mamaki.
“Ni nace fa naga Motar ka Haleema tace min wai ba kai ba ne”
Ya ɗan wara ido yana kallon Haleema, kamin ya zauna a kujarar da Amira take zaune dan three seater ce.
“Ai ba zata faɗa ba, a ɗakin ki na same su suna ta miki taɓe taɓe ita da wannan yarinya”
Ya nuna Amira data tsare shi da ido.
“Wallahi gyara ne Amira take miki, ba wai komai muke miki ba, hba sai ka ce yara”
Ummi bata bi ta kan Haleema ba ta kalli Abdool.
“Ya hanya? Ka ci abinci?”
“Na ci gidan Babana, ku da ban ma tarar da ku ba”
“To ai baka faɗa ka ce za ka zo ba, gashi ma miyar kifi aka yi kuma baka son kifi”
“Ni wallahi wannan zuwan ma be min daɗi ba, ɗan hutu ne na samu ina da zumuɗi zan zo gida shine wai kuma Mai Martaba sai naje zaria ɗaurin aure”
“Ai shine dai-dai kai kenan baka son shiga mutane kamar wani aljani. Me za'a girka maka?”
“Wa zai girka min?”
“Ni”
“Okay to a min wani abu new. Ba wanda aka saba ba”
Tashi Ummi tayi ta nufi ɗakinta tana dariya.
“Kai kam matarka ta shiga uku kullum.ba maimata abinci sai anyi wani abu new”
Shima.dariyar yayi ya tashi ya rufa mata baya yana faɗin
“Lallai kam, idan kam mace bata iya abincin ba zamu samu matsala da ita”
“Ko da kana son ta?”
“Aifa...”
Amira ta bishi da ido, daɗi har cikin rai. Dan tasan indai ɓangaren abincine ba daga baya ba, tun daga kan waɗanda ake yayi har na gargajiya gwargwado ta iya. Ga kuma xama da yayi a kujerar da take zaune abun yayi mata daɗi.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *62*
*1952*
```Cikin rawar jiki ta shigo gidan sai rabon ido take idonta tab da ƙwalla, kana ganinta kasan tana cikin halin damuwa. Bata san inda zata dosa ba tun ba data samu masu gadin suka barta ta shigo cikin gidan, gaba ɗaya a rikice take har bata iya kwantar da hankalinta ta banbanta parts ɗin
“Ke me kike a nan?”
Da sauri ta juyo ta kalle tana ganinsa sak tasan ɗan mai gidan ne, hakan yasa ta risina har ƙasa ta gaisheshi muryarta na rawa. A maimakon ya amsa mata sai kawai ya ƙara haɗe fuska dan ya fahimci irin mutanen ne masu zuwa gurin mahaifinsa a taimaka musu
“Gurin Mai gidan nan na zo, taimako za a min, mahaufiyarmu ce bata da lafiya shine aka rubuto mata magani a asibiti kuma sun ce za a mata aiki, shine aka ce na zo nan za a taimaka mana”
Da kuka ta ƙarasa maganar tana nuna masa takardun asibiti dake hannunta. Karɓar takadardun yayi yana kallon fuskarta da kuma yanayinta, taga komai a rubuce amman saboda mugun nufinsa ya kasa gasgata ta.
“Wata ƙila ma ƙarya kike, haka kuke dan kawai kun ga mahaifina yana taimakawa mutane, kowa sai ya kwaso ƙaryarsa ya kawo ”
“Wallahi ba ƙarya na ke ba, idan baka yarda da ni ba zamu iya zuwa ka duba ta tana nan babbar asibibiti, layin masu ciwon ulcer”
Kallonta yake da kyau, irin kallon da idonsa zata siffanta masa sigar jikinta, yarinya sai dai ba sosai ba, fara ce kyakkyawa mai ruwan fulani, ko kuma na ce buzayen jajaye. Hawunta ya haɗe a bakinsa kana ya ce
“Nawa ne ake buƙata?”
“Dubu ɗari biyu da sittin”
“Tam yanzu kin ga mahaifina baya nan, ya za'ayi”
“Ina zan same shi?”
“Baya nan ta tafi Lagos ganin shugaban ƙasa” (A lokacin Lagos ce fct ba Abuja ba)
“Yaushe zai dawo?”
“Wallahi ban sani ba, amman idan kina so ni zan iya taimaka miki”
“Ina so dan Allah”
“Amman fa sai idan nima za ki taimaka min”
Kallon rashin fahimta tayi masa dan a iya ganinta da tunaninta baya buƙatar wani taimako daga gareta.
“Me zan taimaka maka?”
“Idan har kina son na baki kuɗi to ki iskoni a ɗayan gidan baban mu da yake nan kwalkwaɗa, zan ninka miki fiye da abunda kike so ba”
Sak tasan abunda yake nufi, kuma ta fahimci inda kalamansa suka dosa, ita kuma bata koyi wannan tarbiyar ba, kuma bata ji zata iya sadaukarda mutuncinta ba. Sai kawai ta kaɗe jikinta ta tashi tsaye.
“Ni ba ƴar iska ba ce, dan kawai na zo neman abu gurin mahaifiya ba shi yake nuna ni ƴar iska bace, rashi mahaifi ne, kuma duka dangi babu mai shi, idan har zaka taimaka min dan Allah ka taimaka min”
“Daman ƙarya kike ciwon mahaufiyarki be da me ki, da kin aikata komai akan ta. Wuce ki ba mu guri”
Da kuka yarinyar ta bar gidan. Shi kuma ya juya ya shiga ƴar marsandin mahaifinsa ya fita daga gidan. Kai tsaye ɗayan gidan mahaifinsa ya nufa, dake can bayan babban gidansu, daman ya saba a duk lokacin da mahaifinsa baya nan a can yake tarewa yana sharholiyarsa da abokansa wani lokacin har da mata, abu ɗaya ne baya yi shine shaye-shaye.
Bayan kamar sa'a ɗaya da isarsa gidan sai ga yarinyar ɗa zu ta dawo, a nan ma sai da ta nemi iso suka zo suka faɗa masa sannan suka bata dama sannan ta shiga.
Har cikin faɗar da yake zaune ta isa ta zube masa a ƙasa tana kuka.
“Na roƙe ka, na haɗa ka da girman Allah ka taimaka min mahaifiyata zata iya rasa rayuwarta daga yanzu har zuwa wani lokaci inji likita, saboda ulcer ta taɓa hanjinta har ya lalace”
“Idan kina son ran mahaifiyarki ai sai ki bada na ki rai, ni bana da wani taimako da zan miki wanda ya wuce wannan, idan kin san riƙona ne kawai ya kawo ki to ƙara ma ki tashi ki koma kar dare yayi miki”
Ɗaga kai tayi tana kallon idonsa, rashin imanin dake zuciyarsa take hangowa. Ta karanci tantiranci da ke cikin idonsa lallai idan har bata shirya siyar da mutuncinta to ko mahaifiyarta zata iya rasa ranta bayan kuma ita kaɗai ce ta rage mata a duniya. Hkan yasa ta yarda ta amince tana ji tana gani ya keta mata haddi, abunda bata taɓa kawo ma zuciyarta ba, cewar zata bada budurcinta ga wani wanda ba halalinta ba.
Wani tsabar zalumcin kuma sai da ya gama amfani da ita sannan ya ƙirga rabin kuɗin ya bata wai shi kawai suka rage masa, da tayi maganar har da zaginta yana faɗin daman ai buzaye kowa yasan ƴan iska ne. Da kuka ta bar gida tana mai jin zafin keta mata haɗi da yayi. Shi kuma ya kwanta a ɗakin zuciyarsa cike da nishaɗi, yana jindaɗin abunda ya aikata wanda a gareshu ba sabon abu ba ne.
bachinsa ya kwasa a gurin har sai da ya hantse, sannan ya tashi, yayi salla, sai ya aika mai musu aiki ya siyo musu abincin. yana cikin cin abincin sai ga yarinyar ta dawo idanuwanta a kumbure, wannan karon bata sha wahala a gurin shiga gidan ba ganin ɗazu yace a bar ta ta shiga. A falon ta same shi yana cin abincin hankali kwance. Kuɗinsa ta aje masa tana kuka.
“Ba ayi mata aikin ba saboda rai yayi halinsa, ga kuɗinka bana buƙatar ganin su ko amfani da su, dan amfaninsu a gare ni ya ƙare. Ka kita min haddi akan abinda be wuce ka bani sadaka ba, saboda kawai na zo nema gun ka, to ka rubuta ka aje ko ba daɗe ko ba jima, sai an yima ƴarka abunda ka yi min, sai ka ɗanɗana idan da daɗi, sai Allah ya ninka maka baƙincikin raina sau biyu, wata rana sai ka wayi gari kana nadamar abinda ka aikata min, na roƙi Allah ya isar min ya nuna maka a kan ƴar cikin ka...”
Bata gama kalamin ba ya ɗauki abinci ya jefeta da shi, ya hau ta ta shuri yana zaginta. Shi kansa ya ji babu daɗi a kalaman da tayi masa, duk da ya ba, amman duk waɗanda yake da su, sune suke kawo kansu ko ya neme su kusan dai za'ace karuwai ne, wannan ce kawai ya keta ma haddi da gangan...```
Ajiyar zuciya Dady ya sauke, hawaye suka silalo daga idonsa, sai jan majiya yake. Yanzu kan ya tabbatar da alƙawarin Allah gaskiya ne, kuma kowa yayi da ƴar wani sai an yi da tashi, sai dai nashi sakamakon mai zafi ne, tun da na ƴarsa har da cutar kanjamau, kuma ta keta mutuncin aurenta, wannan babban abun baƙinciki ma ita ta ba da kanta ba wai keta mata haddi aka yi ba, dan baya tunanin hakan da keta haddin ne da tuni ta faɗa.
Miƙewa yayi tsaye zuciyarsa na masa wani irin mugun zafi ya shiga ɗakinsa hawaye na cigaba da masa zuba. Nadama ce tsantsarta a zuciyarsa sai yanzu yake baƙincikin abunda ya aikatawa ƴar mutane, lallai zina bashi ce! Dole wata rana ka biya ko a biya maka....
RASHIDA POV.
Ɗakinta ta koma ta zauna tana rare kukan baƙinciki daya cika mata zuciya. Ji take kamar ta rataye kanta ta huta, ta san duk wanda yaji tana ɗauke da wannan cutar ba zai zauna da ita ba, ga kuma Hilal da yanzu take da tabbacin ta rasa shi kenan har a bada. Iyayenta ma a yanzu ta san ta rasa su dan ta san zamanta da nasu dole zai banbanta, dole a yanzu duniya ta san abunda ta aikata, rayuwar da take gudun shiga ta san a yanzu dole ita zata yi.
Duk kukan da take Momy na tsaye jikin ƙofar ɗakin tana kallonta tare da rera nata kukan. Haƙiƙa tana tausayin ƴarta sai dai babu yadda ta iya tun da ita ta jawa kanta.
“Za muje mu ƙara gwaji, so that mu tabbatar idan har da gaske kina ɗauke da cutar”
Ɗagowa kawai ta yi ta kalli Momy da idanuwanta da suke ta zubar da ƙwalla har ɓata gani sosai da su. Sai kuma ta maida dubanta gurin hannayenta tana duba jikinta kanta take kaɗawa tana jinjina lamarin ubangijinta dan shi kaɗai ya isa yayi mata haka, sauyin rayuwa a take....
HILAL POV.
A firgice ya isa asibitin dan tun bayan abunda Nurse ɗin ta faɗa masa sai hankalinsa ya tashi sosai.
Ko parking ɗin kirki be yi ba ya buɗe motar ya fito hankali tashe har yana gudu. Likitan yara uku ya tararar akan Rafiq suna ƙoƙarin ceto numfashinsa, amman ina rai yayi halinsa. Ƙasarawa yayi a rikice yana girgiza Rafiq, tare da kiran sunansa. Da sauri ɗayan likitan ya riƙe shi yayi baya da shi yana masa magana.
“Haba Doc ya kake abu kamaɗ ba likita ba, mutuwa wace iri ce ba mu gani ba? Ka yi imani da kaddara mana, komai ka yi ba zai sai Allah ya fasa abunda yayi niya ba, dan kasan ba'ayi Rafiq dan kai ba, kamar yadda ba'ayi Rafiq dan ka ba”
Lumshe ido Doc yayi ya dantse bakinsa, yana ta ganin Rafiq yana masa yawo a ƙwaƙwalwa, ƴana buɗe idon sai hawaye. A hankali ya furta Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Sannan ya juya ya fita daga ɗakin. Rufa masa baya likitoci suka yi suna tausasa masa zuciyarsa.
Ba laifi ya samu gwarin gwuiwa daga ƴan'uwnsa likito wanda hakan ya hana shi bayyana damuwar mutuwar ɗansa a fili, duk da yasan abunda da zai daɗe a zuciyarsa yana masa yawo kasancewar ƙananan yara suna da shiga rai.
Da kansa ya kira Hajiyarsa ya faɗa mata, kamin ya kira wasu daga cikin ƴan'uwansa da kuma ɓangaren Rashida.
Sannan abokansa suka saka shi a motarsu , shi kuma ya shiga a ɗayar motar abokinsa suka nufo gida dashi. Tun da Kalsoom taji ƙarar buɗe gate ɗin gabanta yayi mummunan faɗuwa, tana jin tsayawar mota ba ɗaya bugun zuciyarta ya ƙaru. Balle kuma da taga Hilal ya shigo idonsa a rine.
“Ya rasu ko?”
Kai kawai ya ɗaga mata ya zauna saman kujera. Ita kuma ta ɗora hannu saman kai ta fashe da kuka ta durƙushe a gurin. Yana unƙurawa zai tashi Hajiya ta turo ƙofar falon ta shigo tana kuka, tare da wasu sisters na shi.
Da sauri Hilal ya tare ta yana faɗin ta daina kuka.
“Hajiya be kamata ki masa kuka ba, haka Allah ya kaddara babu yadda muka iya”
Hajiya bata daina kukan ba ta nuna Kalsoom ta ce
“Idan baka saki wannan yarinyar ba ban yafe maka ba Hilal, kuma sai dai ka nemi wata uwar ba ni ba...!”
A gigice ya kalli Kalsoom sai kuma ya kallon bakin Hajiya da yayi wannan furucin. Kalsoom ma kallon Hajiya take hawaye na bin fuskarta. Rashida ta turo ƙofar ɗakin ta shigo tana kuka.
“Ina ɗa na? Ka hana ni ganinsa lokacin da yake da rai yanzu na zo na ga gawarsa ina ɗa na yake?”
Rumtse ido Hilal yayi ya zauna saman kujera ya dafe kansa ya dantse bakinsa gam.
NAMRA POV.
Ana kiran salla magariba suka sauka babbar tashar kaduna, da sauri passengers suke fita wasu saboda suna nesa ganin dare ya soma yi wasu kuma dan su samu bin jam'in salla magariba. Ita ce kawai ta fito daga motar kamar marar kuzari tana tafiya tana kallon tashar da bata taɓa mafarkin zuwa ba. Tana fita daga gurin da motoci suke sai masu Nepep irin wadanɗa suke tsayawa a gefen tashar suna neman masu shiga gari.
“Malama ina za kije?”
Ɗaya daga cikin matasan dake tsaye a gurin masu Napep ya tambaya yana shafe ruwan dake alwala dake fuskarsa. Matashin saurayi ne mai jini a jika fari kyakkyawa da shi, a zahiri akwai natsuwa da sanin ya kamata a shimfiɗe a fuskarsa. Ga sajensa gwanin sha'awa.
“Cikin gari...”
Ta faɗa da muryarta mai kamar zata yi kuka.
“Okay, shiga muje amman zan tsaya a hanya na samu jam'i”
“Ba matsala”
Ya jefar ledar pure water dake hannunsa ya shiga napep ɗin tasa mai kamar sabuwa ya kunna, ita kuma sai ta shiga gidan baya ta zauna tana ta tunanin inda zata ce ya kai ta. Har ya kunna Napep ɗin ya fara tuƙi be tambaye a ina za'a kai ta cikin garin ba, dan shi dai danuwarasa a yanzu ya samu jam'i.
Ba suyi tafiya mai nisa ba ya faka a gafen titi, ya fita yana faɗin
“Bari na yi salla a masalacin”
Kai ta ɗaga masa tana kallon mutane dake ta haɗa haɗa a kan babban titin. Tunanin unguwar da zata ce masa ya kai ta take, amman har yayi salla ya dawo bata samu unguwa ɗaya da zata ce ya kai ta, dan bata san garin kaduna balle yace ga inda zai kaita.
Sai da yayi mata sallama sannan ya shiga Napep ɗin ya tasheta ya hau titi. Can ya ciro wani ƙyale ya kare ƙasar salla dake goshinsa ya juyo kaɗan ya kalli Namra.
“Wace Unguwa za muje?”
“Uh...m ca..an can..gur.in gra”
Ta faɗin hakan ne dan bata san inda zata ce masa ba, amman ta san ko wane gari akwai gra.
“Okay GRA ta gurin ina?”
“Ta gurin manyan gidajen nan”
Daga nan wata kalma bata sake shiga tsakaninsu ba, shi dai ya mai da hankalinsa gurin tuƙinsa, ita kuma hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma gida da tunanin inda zata kwana yau a garin kaduna. Ganin sun shiga GRA har suna ƙoƙarin wucewa bata ce ga inda za a sauke ta ba yasa yayi mata magana.
“Malama mun shiga GRA ɗin fa”
Sai kawai tayi shiru ba dan kuma bata ji shi ba, sai dai bata san abunda zata ce masa ba. Hakan yasa ya ƙara maimatawa yana mai rage gudun da yake.
“Gaskiya ni ban san inda zanje ba”
Juyowa yayi ya kalleta.
“Baki san sunan mai gidan ba ne? Kuma baki da number waya?”
“Ban sani ba, kuma bana da number, sau ɗaya na taɓa zuwa”
“Amman irin wannan tafiya ai it risk, ace baka da number wanda zaka sauka gunsa kuma ba kan guri ba?”
Tayi shiru bata ce komai ba. Sai a yazu take nadamar zuwan da tayi a kaduna ita kanta ta san tayi wauta.
Jin bata ce komai ba yasa ya ce
“Ina zan sauke ki dan ni akan aiki na ke”
“Wallahi idan ka sauke ni ban san inda zanje ba, dan bana da kowa a kadunar nan sai Allah, tun da ban san gurin wanda zan sauka ba”
Cikin muryar kuka tayi maganar, juyowar da zai ya kalleta sai kawai yaji shesshekar kukanta. Baya iya ganin hawayen idonta dan Napep ɗinsa bata da wutar ciki wance wasu suke sakawa, hasken dake gefen titin be iya ya haska fuskarta har yaga hawayenta ba,amman a yadda ya karanta kamar tana cikin wani hali ne.
“Bawai Allah ke mutum ce?”
“Ni mutum ce wallahi kuma ba cutar da kai zan yi ba”
A nan ta saka ƙafarta ta sauka daga cikin Napep ɗin ta saka hannunta a jaka ta ciro ɗari biyu ta miƙa masa.
“Ba ni canji”
Ta faɗa tana ta ƙoƙarin tare kukanta dake son fitowa. Kasa karɓar kuɗin yayi kuma ya kasa tafiya, kallon fuskarta yake dan yanxu hasken gurin ya haska fuskarta, bata yi masa kama da mugayen mutane ba, jikinsa be bashi zata cutar da shi ba, hakan yasa shi idan har ya barta a nan gurin be kyauta masa ta, kuma besan abunda zai same ta ba tun da tace masa bata da kowa sai Allah.
“Shiga mu je”
“Na gode”
Ta faɗa tana share hawayenta, sai ta shiga Napep ɗin da sauri. Tun da ya soma tuƙin be tsaya ko ina ba sai malali, a mararraba ya tsaya ya miƙa ɗari da hansi aka bashi canji sannan ya ƙarasa ƙofar gidan na su mai cike da rufin asibiti, dan a kira su da talakawa ba kasancewar suna da rufin asiri da wadatar zuci. Sai dai a zahiri kan talakawa ne sosai masu ginin bulu wanda ba ayi ma filistaba.
“Fito muje”
Ya faɗa bayan ya kashe Napep ɗin. Cikin sanyin jiki ta fito tana dansar bakumi saboda mugun murɗa da mararta take mata. Yana gaba tana biye har suka shiga cikin gidan mai ɗauke da ɗakuna uku, duk da dare ne hakan be hanata ganin yalwantaccen tsakar gidansu ba mai ɗauke da bishiyar mangoro guda biyu ɗaya a jikin ɗaki ɗaya kuma a tsakiyar gidan.
“Neine (Inna da yaren fulatancin) ga baƙuwa”
Wacce saurayin ya kira da neiner ta miƙe daga saman tabarmar da take ta nufo Namra tana murmushi.
“Maraba maraba laƙe marhabun baƙonƙa annabin ka, siter ƴata sita (Zauna zauna)”
Ya faɗa lokacin da take ƙoƙarin zaunar da Namra saman tabarmar da take zaune. Namra ta zauna tana kallon yaran gidan da suka kewaye waya suna kallon india hausa a wata ƙaramar wayar hannu. Gaba ɗaya hankalinsu ya tattara ya tafi can sam basu ma san da zuwanta ba.
Neine da kanta ta shiga ɗaki ta ɗauki ma Namra tuwon masara ta aje mata gabanta, sai ta nufi wani ɗan madaidaicin tulu ya bulbulo mata ruwa a kofi ta kawo mata tana mai sakar mata fuska kamar ta santa.
Shi dai yana daga can gefe yana bawa cat ɗinsa kifi, amman hankalinsa yana gurin Namra yana kallon yanayinta.
-----------------------------------------------------------------
I PITY RASHIDA 😢
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *64*
Suna ta gaba-gaba suna tare Abdool kamar wanda wani abu zai same shi, sai kirari suke masa wasu na ture mutane dake gefen gurin dan Abdool ya samu hanya. Mutane sai kallo a ke wasu ma har sun wuce sai suka dawo ganin duka numbobin motar an saka YARIMA ABDOOL, duk wanda kuma yaga jajaye kaya yasan sarki ne ko kuma ɗan sarki.
Abdool be nuna tausayi a fuskarsa ba, na ganin irin raunin da aka yi ma Lamido, sai dai a can zuciyarsa ne yake tausayinsa ganin yadda jini yake masa zuba a kai kuma ya riƙe ƙafarsa sai cizar baki yake alamar yana jin zafi sosai, kowa yaga yadda Napep ɗin tasa ta yi sai ya tausaya masa duk ta lalace kai baka ce ma wanda yake ciki zai yi rai ba, saboda buguwa da tayi da transformer garin ya kauce musu har ya transformer ta faɗo kan Napep ɗin tasa, shi da be yi hanzarin fita ba da Allah kaɗai yasan irin ciwon da zai ji.
Lamido ya kalli Sadauki ya soma magana da shi kaɗan-kaɗan, yana gama maganar ya juya da sauri suka soma take masa baya, suka buɗe masa motar ya koma. Sannan Sadauki ya kalli sauran dogara ya ce
“Yarima ya yi umarnin a kai shi asibiti”
Da sauri Dogaran suka nufi gurin Lamido suka riƙa shi suka saka shi motar su. Sai suka sauya hanya daga masaukin Abdool zuwa Asibiti mafi kusa da su.
Anyi masa kyakkyawar karɓa, a asibitin, duk da kasancewar basu san Yarima Abdool ba amman suna ganin motoci ya dogarai sun san babban mutum ne.
Duk abinda aka yi aka maga Abdool na ciki mota zaunensa har aka gama dubasa aka saka masa baldeji a kai suka rubuta masa magani, a cikin asibitin dogaren yaje ya siya masa magani sannan suka dawo da shi gurin motar. Da gudu Sadauki ya nufi Motar Yarima Abdool ya ƙwanƙwasa gilashin motar sai ɗayan dogaren dake ciki ya sauke gilashin motar.
“Ran Yarima ya daɗe, an kammala masa komai, sun ce yaji ciwo kai sai kafarsa da ɗan targaɗe kaɗan”
Da Abdool yake magana amman yayi kamar be jisa ba, idonsa na kan Lamido dake tsaye jikin wacan motar yana kallon titi. Kallonsa sosai Abdool yake a zahiri yana da kyaun natsuwa da kuma kyaun fuska, gashi dogo ga fari ga dogon hanci gashin kansa kawai idan ka kalla zaka gane bafulatani, sai dai hakan be hana Yarima Abdool jin wani iri akansa ba, wata ƙila akwai wani giɓi a tare da shi, ko kuma akwai wani abu a tare da shi wanda Yarima Abdool baya so, dan ya tsanar mutum haka nan kawai.
Haka Abdool ya kwashe daƙiƙu talatin da wani abu be ce da Sadauki komai ba, wata ƙila yau jinin sarautar ni ya motsa har yayi abunda be saba ba, kuma abunda yake ganin kamar be dace ace mutum yana yi ba.
“Za mu bi ta gidan su mu aje shi sai mu wuce”
Ba dan sun saba ba, da ba zaka zaci da su Yarima yake ba, yanayin yadda yayi maganar muryarsa na ƙasa sosai, ko kaɗan idonsa ba su kalli Sadauki ba, har yanzu idonsa suka kan Lamido yana masa kallon rashin dalili.
“Allah yaja zamanin Yarima, an gama”
Ya bar jikin motar da sauri ya nufi gurin wacan motar da Lamido yake tsaye.
“Kai ɗan talakawa shiga mota muje, Yarima mai jiran gado ya ce aje a kai ka gida”
Maganar ta daki zuciyar Lamido har sai da ya kalli Sadauki sai kuma ya kalli Motar yarima duk da baka iya hango wanda yake ciki sai dai na ciki ya ganga. Har zai yi magana sai kuma wata zuciyar ta hana shi, sai kaeai ya rage tsawonsa ya shiga motar, still ransa ya sosu da furucin da Sadauki ya yi masa. Sai da ya shiga motar sannan Sadauki ya dawo a motar ya Yarima ya shiga suka kama hanyar Tudun wada.
Lamido ne yake ta nuna hanyar da za abi har aka isa gidansu. Ganin masu jajayen kaya sun fito tare da Lamido yasa mutane suka fara taruwa ana kallonsu, dan kowa yasan daga gidan sarki ne. Masu boko suka karantar number motar, yara kuma suka shiga cikin gidan da sauri suka sanar da Neine cewar ga wasu nan sun zo da Lamido ciki motar sarki an ji masa ciwo. Ba shiri suka fito daga gidan gaba ɗayasu suka nufo Lamido. Bugun gabansa ne ya ƙaru ganin Namra a cikin mutanen dake fitowa daga cikin gidan, ita ma hankalinta a tashe yake kamar wani nata ne aka jima ciwon. Sai da suka saka shi cikin gidan, sannan ɗaya daga cikin dogaran ya zo ya buɗewa Yarima mota ya fito.
Ƙarƙashin itacen mangoro suka shimfiɗe Lamido, uwani ta ɗauko matashin kai a ka aza masa. Kusa da shi Namra ta zauna tana ta kallon kansa tare da yi masa sannu, idonta cike da ƙwalla, har cikin jikinta take jin ciwon Lamido.
Shigowar Yarima Abdool yasa Namra ta ɗago kai ta kalli ƙofa, karam idonta ciki cikin nasa, sai yayi saurin kawar da nasa idon, ya cigaba da takawa kamar wani ɗawuisu, ya tunkaro tsakar gidan, dogarai na take masa baya. Ita kam kallonsa take da kyau dan tantance wanda ta gani ɗin, da gaske shi ɗin ne ko kuma waninsa mai kama da shi? Daman Ɗan sarki ne? Anya shi ke wacan kuwa na Katsina wanda yayi mata kyautar gida ko dai twins ne?
Har ya ƙaraso gurin idonta na kansa, shi kuma ya ƙi ya kalleta sai kallon ƙyakkyami yake ma gidan abunda ba halinsa ba. Da sauri Uwani ta ɗauko wani Babban tabarma ta shimfiɗa masa, jikinta har rawa yake. Baya cikin kayan sarauta hasalima farar shaddace jikinsa, wanda ta haska kyaunsa. amman hakan be hana ƙwarjinsa fita ba, dan du Ƴaƴan sarakuna da ban suke a duk inda suke.
Be zauna ba, kuma be cewa kowa ko ƙala ba har sai da Neina da sauran matan unguwar suka miƙa masa gaisuwa, nan ma hannu ya ɗaga musu sai dogaran suke amsa musu da sunan Yarima ya amsa, kuma ya gaishe ku.
“Allah ya sauwaƙe”
Shine kawai abunda ya furta, shi kuma iyakar laɓɓansa Sadauki ne ya maimaita dan suji. Sannan ya ciro cak ya miƙawa Sadauki shi kuma ya karɓa ya miƙa wa Neina dan ita yake zaton ma mahaifiyarsa ce.
“Godiya take Yarima”
Hannu biyu tasa ta karɓa jikinta na rawa, badan tasan ko takardar me ne ba. Kuma tsoro ya hana ta tambayar ko minenen.
Juyawa yayi ya sai dogoran suka take masa baya. Tunani biyu ne a zuciyarsa miya kawo Namra gidan ita da take Katsina? Mine alaƙarta da ƴan gidan? Ko kuma ƴar'uwarta ce? Mijin ta ne wacan to wannan fa? Ko dai yayanta ne? To ai ba suyi kama ba. Shine abunda yake ta tunani har ya doshi motar.
_Miyasa ba zaka iya yaƙin zuciyarka ba? Dan me zaka nace abunda ba halalinka ba? Idan ita ce sai me miye ruwanka da ita?_
Iskar bakinsa ya furzar yana sauraren bugun zuciyarsa, da kuma tunanin yadda ƙaddara take kawo masa mai kamaninta.
“Ya Rahman”
Ya furta yayinda yake ƙoƙarin zama cikin motar. Wannan karon hankalinsa ba akan jarida yake ba, gaba ɗaya ya tattara ya koma can gurin Namra daya gani, idanuwansa suna kan titi ruhinsa kuma yana can gurin motar da ba tasa ba.
Daga nan basu tsaya ko ina ba sai masaukinsa, kamin ya fita motar sai da ya duba agogon hannunsa ɗaya saura ya gani, hakan ya sashi ɗan hanzarin fita yana magana da sadauki.
“A kira Mai Martaba a sanar masa mun iso, wayana a kashe yake zan ɗan kwanta na huta”
“Allah ya taimaki Yarima yadda ka ce haka za'ayi”
Gaba ya wuce suka buɗe masa ƙofa, duk jin yake rayuwarsa babu daɗi, kuma be san dalili ba.
HILAL POV.
Jikin ƙofar ɗakin ya jingina yana kallonta da sauraren kukan da take rerawa. Rumgume hannayensa yayi yana tunanin ta ina zai fara. Ita kam bata ma san da shigowarsa ba, ta maida gaba gabas sai rusar kuka take.
Sauke hannayensa yayi ya nufi inta take zaune ya zauna gabanta yana kallon idonta.
“Yanzu abinda kike min adalci ne? Ki zauna kina kuka kin san yadda nake ji kuwa? Na rasa ɗa na ke kuma kin zauna a nan ki na kuka”
Ɗagowa tayi ta kalleshi
“Kai ɗa ka rasa, kuma kana da wasu, ni kuma miji na rasa”
“Ba ki rasa ni, kin san abinda na ke so da ke?”
Ta girgiza nasa kai.
“Zaki zauna nan for a while as zaman idda kamar yadda addini ya ce, ni zan je gida na faɗawa su Momi komai, wannan fushi na Hajiya na kwana biyu ne na nasan nan gaba kaɗan zata sauka, dole ne Hajiya tayi fushi Kalsoom saboda bata fahimce kamar yadda ni na fahimta ba”
“Ta yarda na zauna ne?”
“Bana jin zata hana, abunda na ke so dake ki yi mata uzuri kuma ki bata lokaci. Zan ɗauke ki muje gida anjima a can zan maida aure na”
Kai kawai ta ɗaga masa ta share hawayenta. Har ya mike tsaye sai kuma ya juyo ya kalleta ya ce
“Hajiya ta ce za a maida zaman makoki a can”
Nan ma kai ta ɗaga masa. Sai ya juya ya fice zuciyarsa babu daɗi. Zaune ya hango Hajiya a falon tana kallon ƙofar ɗakin Kalsoom daya fito fuskarta babu annuri. Kai ya girgiza cikin yanayin damuwa ya ƙaraso kusa da ita ya dafa kujera yana kallonta.
“Hajiya karki zama cikin iri surukan nan”
“Ba ƙoƙarin zama nake ba Hilal amman duk abunda yake gaskiya dole a faɗe shi, idan kai ta maka magani ni bata min ba, kuma Wallahi tallahi sai ka ƙara aure ko da kuwa bana numfashi, dole ka auri wacce zata riƙa maka ƴaƴanka mace ƙwarai ba mai ƙoƙarin kashesu ba, ni zan nema maka mata da kai na”
Tana kaiwa nan ta miƙe tsaye ta nufi ƙofar fita ranta na ƙololuwa a ɓaci. Shi dai da kallo ya bita har ta fice sannan ya saka hannyensa aljihu ya nufi ƙofar ransa a jagule.
RASHIDA POV.
A nasu gidan suke nasu amsar gaisuwar daban, duk da kasancewar waɗanda badu san aurenta ya mutu ba suka je can gidan gidan har sai idan sun tambaya ne sai ace musu gata nan. A harabar gidan suka shimfiɗa tabarma duk da kasancewar yaro ne hakan be hana ayi masu taro ba, sai dai ba irin zuwan nan ake na wuni ɗaya ba sai dai su zo su zauna na ƴan mintu su yi mata gaisuwar su wuce.
Tabarmarta daban tana zaune gefe ɗaya, ƴan gidan suna zaune gefe ɗaya. Idonta kumbura sosai duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata wasu har da Allah ya isa suke mata duk a tunaninsu tana kuka ne saboda rashin ɗanta, sai dai a gurin Rashida abun ba haka yake ba, ita tana kuka ne saboda tunanin makomarta ganin asirinta ya tonu tun yanzu, tasan dole zamantakewar ta da ƴan gidan dole zai canja dan taga alamun hakan tun yanzu.
Misalin biyu da rabi Teema ta zo gidan gurin gaisuwa, sosai take son magana da Rashida amman babu dama saboda mutanen dake ta kai da kawo. Tana gurin kuma sai ga Asmee bayan ta fito gidan Hilal ta nufo nan.
Duk abunda ya faru a gidan sai da ta bawa Rashida labari. A nan Rashida take labarta musu maganar sakin da Hajiya tasa aka yi ma Kalsoom, dan su ba susan da maganar ba. Duk daɗi suka ji har mutenan dake gurin da kuma Asmee da basu san kan abun ba, amman ban da Teema da ita kan tasan komai.
“Amman Hajiya ta kyauta, daman ai ni za ci tuni zata sata shi aikata sakin, duk wanda yayi maka haka ga jika kan ai be cancanci zama da ɗan ka dan wata shi zata hara”
Gaskiya kam. Abunda suka mutanen suka masa da shi, sannan ƙananan maganganu suka biyo baya. Teema ta kada baki ta ce
“Gaskiya Hajiyar ta kyauta daman tun tun tun Hajiyarmu take cewa ya kamata ace Hajiya ta saka Hilal ya rabu da matar nan”
Rashid ta kalleta tana murza idonta.
“Hajiyar ku ta san ta ne?”
“Eh sukan haɗu a harkar siyasa wani lokacin, suna gaisawa sosai”
“Allah sarki”
Cewar Rashida. Sai kuma ta kawar da fuskarta tana kallon Asmee irin kallon nan da ita kaɗai ta san dalilinsa.
Teema kuma wani gurin take kallo tana wani tunanin na daban. Sai da aka kira la'asar sannan Teema ta wuce gida, Asmee kam a gidan tayi sallah sannan ta fice bakinta cike da magangu amman bat samu damar yi ma Rashida ba, ganin Safiya duk yasa ta tsargu, hakan yasa ta yi a zamar barin gidan.
Tashi Rashida tayi ta nufi cikin gidan rayuwarta duk babu daɗi saboda abunda take tunanin su momi sun fara nuna mta na ƙyama tsakanin jiya zuwa yau. Babu abunda ke ranta kamar ta bar musu gidan ta kama wani, tasan hakan zai fi mata kawanciyar hankali.
ASIM POV.
Yana ji a jikinsa akwai rashin dacewa a abinda suka aikata. Musamman yanzu da yake jin abu kamar ƙashi ya tsaya masa a takashinsa, ga wani zafi zafi da yake ji kamar an zuba masa barkono. Wasu ƙwayoyi dattijin Alhajin ya miƙa masa kusan kala huɗu ya ce ya sha, daman kamin su aikata sai da ya bashi wasu, tun jiya da dare suke abu ɗaya har yau da safe, sai yanzu nan ne Asim ya samu kansa. Sai a yanzu yake ƙarema Alhajin kallo, tabbasa ya sanshi a cikin manyan mutane. Amman duk misalin da yake masa jiya be gane shi ba sai yau. Daman tun lokacin daya ji sunansa ta ayyana a ransa ko shi ɗin ne, sai gashi mitumen ya fere ma tun daga biri har wutsiya.
“Na bawa Hajiya miliyan biyu ta baka, na siya maka mota ta miliyan uku. Idan ka riƙe min sirrina nan da ƴan wasu watan ni za'a far ƙirgaka a cikin manyan Alhazai. Zan wuce Abuja yau, idan na dawo zan samr ka a nan ko kuma nas Hajiya ta aika min kai a can sokoto”
Alhajin ya faɗa yana shafa fuskarsa. Asim kan daɗi har cikin kai, hankalinsa da zumuɗi gaba ɗaya sun tattara sun koma gida, babu abunda yake ransa kamar motar nan, a take ya ji duk jikinsa ya warysakr kamar babu wani ciwo jikinsa.
Be bar gidan ba sai da ya ci ya ƙoshi, sannan Alhajin yasa direba ya mai da shi gida.
Yana fita cikin motar sai ga Nably ta kira shi kamar ba zai ɗauka ba dan ya matsu ya ga motar da Alhajin yake ce masa. Sai dai farincikin dake ransa ba zai hana shi ɗaukar wayar Nabila ba.
“Hello my girly”
Ya faɗa cikin wani irin yanayi na shauƙi da annashuwa. Ita kaɗan ta karanci hakan a muryarsa.
“Da alama yau akwai labari mai daɗi a tare da kai..”
Ƙyalƙyalewa ya yi da dariya.
“Labari mai daɗi, na kusa zuwa Abuja na gan ki”
“Nikam ba zan iya jura har jibi ba, akwai birthday friend ɗita da za'ayi yanzu take faɗa min ni kuma na ce dole zan zo ko dan kai”
“Wow Amman gaskiya kin kyauta min, i can't wait to see you”
“I can't wait to see you too, sorry zan katse kiran, Momy na kira na zan kira ka idan mun gama”
Hajiya Sadiya ce ta fito waya a hannunta tana faman kiran waya, fuskarta ɗauke da murmushi, ganin Asim.
Shima Murmushin ya mayar mata ya doshi inda take cike da zumuɗi, sai kawai ta jefa mishi keys ɗin mota ta nuna masa motar tana cigaba da murmushi sai ta nufi wani ɓangaren na gidan tana amsa wayar da aka yi picking yanzu.
Wani irin tsalle Asim ya daga tsinkawo motar da yayi, da gudu ya doshi gurin yana wani irin gurnani kamar mahaukaci.
NAMRA POV.
Abdool na fita Uwani ta karɓi takardar hannun Neine ta duba, tana gani tasan cak ne sai dai bata iya gane ko nawa aka rubuta ba, kasancewar ilminta be kai har can ba, zero da ta ga a rubuce sun mata yawan karantawa.
“Minene?”
Neine ta tambaya, cike da son sanin abunda yake ciki.
“Ni wallahi ban gane kan abun ba, amman dai takardar kuɗi ne”
Uwani ta faɗa, dai Namra ta kai hannu ta karɓa tana dubawa.
“Miliyan ɗaya ne cif”
Uwani da Neina sun daki ƙirji tare da zaro ido.
“Miliyan ɗaya?”
Duk mutane da suka shigo cikin gidan duk ko wanne sai da ya riƙe baki, har ga Allah yawan kuɗin suke gani, Namra kam bat ɗauke su a bakin komai ba, abun ka da wanda yasan kan abu. Wani dogon tsaki Lamido yaja ya kawardar da kansa.
“Sam sam sam mutumen be san darajar mutane ba Wallahi”
Aiko yayi ƙoƙori irin wannan kuɗin haka! Ƴaƴan manyan mutane da da zasu taka rai su bar mutum balle har ya baka wannan kuɗin. Shine abunda mafi yawan matan maƙotan gidan suke ta faɗa.
“Ai dole yayi min mana, tun da ya lalata min Napep dole ya bada kuɗin jinya dan siyen wata”
Neine ce ta saka bakinta wannan karon tana nuna Abdool ya kyauta iya kyautawa.
“Wallahi da wani can ba zai kula ka ba Abdool ba gasu nan muna gani ba, wannan kuɗin ka siye sabon Napep har ka rage. A dole ya nuna wannan halin kasan a jinin su yake, babban mutum kamar wannan”
“Da Sarauta kawai zai fi ni, amman ina tabbacin be fini ilmi zamani ba, balle ma na addini, ji yadda yake kallon mutane warwatse”
Har cikin ransa yake maganar yana mai jin tsanar Abdool sosai. Namra kam bata ce komai ba hankalinta ma gaba ɗaya yana wani gurin, sam bata lura da kallon baƙuwar fuskar da mutanen dake shigowa cikin gidan suke mata ba. Murɗawar da taji mararta na mata ne yasa ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu. Ƙasa ta zauna tana riƙe tsararta tana dannar baki alamar tana jin zogi sosai. Tun tana juriya a zaune har ta kasa ta kai kwance tana rumtse ido.
SAI MUN HAƊU BAYAN SALLAH 😍
INA NEMAN YAFIYAR DUK WANDA NA ƁATAWA, ƊAN A'ADAM AJIZINE. WATA ƘILA ZAN KAI BAYAN SALLAH, WATA ƘILA BA ZAN KAI BA. KU MIN ADDU'A IDAN LABARIN MUTUWA NA YA SAME KU KUMA KU YAFE MIN ALFARMAR ANNABIN RAHAMA S.A.W 🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *63*
Kasa cin tuwon masarar Namra ta yi sai kawai ta sha ruwan tulun mai jiƙa maƙoshi kamar ruwan freezer.
Da fulatanci matar da ba zata wuce mai shekaru hansin da huɗu ba ta yi ma yaran magana akan ba su gaishe da Namra ba. Sai duk suka taso cikin ladabi suka gaisheta cikin su har da manyan ƴan'mata da kuma ƙanana. Da murmushi Namra ta amsa su sannan ta maida kanta ƙasa tana murza yatsun hannunta.
“Ban wayence ta ba”
Neina ta faɗa da yaren fulatanci tana kallon Saurayin. Shima da yaren ya maida mata da amsa.
“Ni ban san ta ba, kawai na ɗauko daga tasha ne, sai tace bata da gurin zuwa na taimaka mata shine na kawo ta nan”
“Amman Lamido taya zaka ɗauko yarinya baka santa, baka san inda ta fito ba? Kasan ko wace iri ce?”
“To Inna idan na bar ta can ban san halin da zata faɗa ba, kuma kin ga tace bata da kowa nan”
“Bata da kowa a nan zata zo? Lamido karka mana jaye-jaye muna neman abinda mu ka ci”
Da yaren fulatanci suke maganar, a zahirin gaskiya Namra bata jin yaren duk kuwa da kansacewar kakaninta fulani ne. Amman hakan be hanata fahimtar zancen ne suke ba.
“Ni ba macuciya ba ce lalura ce ta kawo ni nan, mijina ne ya sake ni kuma mahaifina ya riga daya gargaɗe ni akan karna kuskura na je gidansa, shiyasa na zo garin kaduna, amman idan ba ku yarda da ni ba ba zan zauna a nan ba, dan ba zan takura ku ba”
Wannan karon cikin halshen hausa Neinah ta ce
“Duniya ce a yanzu ake tsoron mutane, ba kowa ake yarda da shi ba, amman me kika aikatawa mahaifinki ya yi miki haka kuma a ina mahaifinki ya ke?”
“Mahaifina yana garin sokoto da zama, ni kuma a Katsina nake aure, sai dai ba zan iya labarta muku labarin aure na a yanzu ba, ina neman ku min lamani har zuwa gobe zan faɗa muku ba zan ɓoye ba”
Daga Neinah har Lamido shiru suka yi babu wanda ya iya cewa uffan, shi baya son yayi magana mahaifiyarsa ta ga kamar yayi mata katsa ladan ita kuma har yanzu bata gama gamsuwa da ita ba saboda halin da duniyar yau take ciki. Ɗaya daga cikin ƴan matan da suke zaune gurin ne ta taso ta dafa Namra tana murmushi ta ce
“Ba komai mun yarda da ke, ba ki yi kama da mugayen mutane ba, kuma na san ba zaki cutar da mu ba”
“Na gode”
Namra ta faɗa cikin muryar kuka.
“Uwani zuba mata ruwa ta yi salla”
Lamido ya faɗa cikin halshen fulatancin yayinda yake ƙoƙarin miƙewa tsaye ya jefar da ledar kifin dake hannunsa. Cikin ladabi ta tashi ya ɗauko mata buta ta miƙe mata sannan ta nuna mata banɗaki. Kamin namra ta yi alwala har ta shinfiɗa mata tabarma ta ɗosa mata sallaya sama ta aje mata carbi. Sannan ya ɗauko ɗayar tabarmar ta shimfiɗa mata gefe ɗaya ta ɗauko zanen gado ta shimfiɗa mata ta aje mata matashin kai. Sai ta dawo ta ɗauki abincin taje can kusa da tabarma ta aje mata.
Namra bata tashi daga saman sallayar ba sai da tayi salla insha'i sannan ta ƙara faɗawa Allah buƙatarta ta sai ta tashi ta koma inda Uwani tayi mata shimfiɗa ta kwanta. Babu abunda ya zo mata a rai sai gidan su, a ɗayan ɓangaren kuma idan ta tuna irin abunda Asim yayi mata sai ta ji kamar zuciyarta zata rabe biyu tsabar baƙinciki.
Kusa da ita Uwanin ta zo tayi shimfiɗa, ta kwanta, sauran yaran gidan kam sai da dare ƴa raba sannan suka nemi guri suka kwanta. Juyi Namra ta yi ta yi har safe ba yi bachi ba, abun nan da take jin ya tsaya mata a ƙahon zuciya yaƙi saukar mata har yanzu numfashinta ma daker take yinsa.
Bata san kan gidan ba amman haka be hanata tashi da wuri ba dan gabatar da salla azuba, sai duk sakkon tashin da tayi sai ta hango Lamido a ƙofar ɗayan ɗakin 6ana salla nafila, kallo ɗaƴa tayi masa ta ɗauke kai. Sai da tayi alwala tana daf da gamawa sai ga Neina ta tashi sai ta tashi dukan sauran yaran gidan har da waɗanda ba su wuce shekara bakwai ba zuwa takwas.
Bayan sun yi alwala dukan mazan sai suka tafi masallaci su kuma suka yi nasu salla a gida. Tun da Neina ta maida gabanta gaban bata juyo ba sai ta ta gama lazumin da take. Uwani ma ta maida gabanta gabas tana nata karatun ƙur'ane, ɗayar ma da tsawon su zai iya zuwa ɗaya da uwani ita karatun take, duk yaran masu ɗan tsawo da wayo kowa ya kama surar da yake yana karantawa. Ƙananen kawai suka koma bachi, sai ita kuma ta jingina jikin icecen dake tsakar gidan tana tasbihi da hannu. A hankali ta karkata kanta tana kallon Lamido take can ƙofar wani ɗaki yana nashi karatun cikin natsuwa da ƙira'ah mai daɗin saurara.
Hakan ya karantar ita irin tsantsar natsuwa da kuma ilmin da ƴaƴan gidan suke da shi, tun daga yaran su har ƙanana, ta samu kanta da ɗan sakewar zuciya tun bayan daga irin karatun ƙur'anen ta suke, daman sauraren karatun ƙur'ane yana saukar da natsuwa karanta shi kuma yana sa kwanciyar hankali da walwalah.
Bayan duk sun gama sai suka duk suka zo suka gaishe ta, ta amsa musu da far'ah sannan ta gaishe da Neina, kamin ta kalli Uwani dake mata murmushi ta ce.
“Ina kwana?”
“Lafiya ƙalau ai daman na ce sai dai ki gaishe ni, ba dai ni na gaishe ki ba, dan nayi ƙanwa da ke”
“Ni...?”
“Eh mana Lamido da kike gani ni nake binsa kin ga kuwa ni yayarki ce”
“Gaskiya ban yarda ba”
“Ta girme ki ƴar nan, jikin ne haka ba'a gane girman ta, yaran nan da kika gani duka ƴaƴanta ne”
Neina ta saka baki a maganar su da Namra tana murmushi. Namra tayi mata kallon mamaki.
“Amman ba za a ce ke ce kika haifesu ba, dube ki fa”
“Kowa haka yake cewa sai wanda ya sani, kin san jikin fulani”
“Allah sarki Allah ya shirya miki su”
“Amin. Maryam tashi ki ɗumama mana tuwon can”
Da sauri Namra ta kalli wacce uwani ta kira da Maryam ɗin tana murmushi.
“Marƴam sunan ƙanwata kenan, amman ita kam uwar masifa ce”
“Hmm wannan ma ai ba baya ba, ga shegen rashin kunya da kauɗi ɗuk ta tara kamar ya kashe ta”
Neina tayi dariya tana ƙoƙarin tashin tana faɗin.
“Maryam bar ni na gyara abu na da kai na, karki je ki min ƙire-ƙire da shi”
Uwani ta kalli Namra.
“Ke kan sai dai asiyo miki koko ko shayi ko? Naga ko jiya ba ki ci komai ba”
“A'a kawai bana jin cin abincin ne”
“Saboda me?”
“Damuwar da ke raina ba zata bar ni na ci abinci ba”
“Hmm idan kika ce zaki saka damuwa a ranki zaki samu matsala, kin gan ni nan damuwar da take rai na mai yawa ce, amman a haka na ke sakewa ina walwalah kamar komai”
“Wata ƙila damuwar ki bata kai tawa ba”
“Ko kuma ke na ce damuwarki bata kai tawa ba, kin ki yaran can? Ubansu yana nan da ransa amman babu ruwansa da mu, saboda mahaifiyarsa bata so na tun ina auren fari, sai take ganin kamar na mallake mata ɗa, kullum kalar masiba daban har na haifi yara biyar ina da cikin na shida can ne tasa ya sake ni, kuma tun daga lokacin babu ruwansa da cin mu da sham mu, balle sutura yau tsawon shekara biyu kenan, Lamido ne da Neina kawai suke hidima da mu, sai kuma ƴar sana'ar da na ke. Kin ga kuwa damuwarki bata kai tawa ba”
“Kowa dai irin ƙaddararsa, amman miyasa ba ku sashi kotu ba? Ai kamata yayi ace an karɓa muku haƙƙin ku”
Daga can gaban murhu da Neine take ta amsa ma Namra tambayar da tayi ma uwani
“Muna kotu yanzu haka, amman shari'ar ta zama wani iri saboda mu talakawa ne, shi kuma yana da rufin asirin da zai tsaya masa a ko'ina, duk da yakr matsalar daga gurin muguwar uwarsa ne”
Namra ta sauke ajiyar zuciya tana jinjina lamarin.
“Rayuwa kenan! Kows da kalar ƙaddararsa, kowa da yadda aka rubuta masa tasa, wani matsalar daga gurin mijin ne, wani uwar miji wa su ƴan'uwan miji wasu kuma ahaɗa musu duka”
“Haka ne kowa ai baya wuce ƙaddararsa, shiyasa idan kaga ta wani sai ka gode Allah da ta ka”
Cewar Neina tana ƙalla itace yana sakawa cikin murhu. Lamido dai yana daga jikin ƙofar ɗakin yana dannar shakiɗin ka baƙauyensa kamar baya jin firar da suke.
“Kin ga tawa ƙaddarar ta so tayi yanayi da taki, nima saboda ciki dake jikina mijina ya sake ni, kuma saboda ya san babu inda zanje tun da na riga da na ɓata da mahaifina”
Dukasu kallonta suka yi, except Lamido, kowane cike da mamaki da kuma shauƙin son jin labarin nata. Sai dai duk da haka Lamido be ɗago ba balle ya nuna hankalinsa yana kan labarinta sai dannar wayarsa yake alhalin kuma dukan hankalinsa da jinsa ya tattara ya koma gindin iccen mangoro da Namra take zaune.
Babu abunda Namra ta ɓoye su, tun daga neman aurenta da Asim da irin gwagwarmayar da suka sha, kamin auren da kuma irin abubuwan da suka biyo bayan auren da irin wulaƙancin da Asim yayi mata har i zuwa jiya da ya sake ta.
Sun tausaya mata. iya tausayawa ganin yadda tayi sadaukarwa amman ace ya ci amanarta, duk da basu sanshi ba hakan be hana su tsine masa ba tare da roƙon Allah ya isar mata.
Kuka take sosai duk da irin haƙurin da suke bata be hana ta zubar da hawayen baƙinciki ba. Wannan karon idon Lamido yana kan Namra, be ce uffan akam labarinta amman yana jinjina irin cin amanar da Asim yayi mata, a ransa yake ƙyama da kuma mamakin irin mazan nan da suke auren ƴaƴan masu kuɗi dan su gina nasu rayuwa, ya daɗe yana jin irin wannan labarin na auren jari yau kuma sai Allah ya haɗa shi da wace aka yi ma.
Haƙiƙa rayuwar Namra abar tausayince,duba da irin rayuwar da zatayi da kuma wacce tayi, ga kuma tunanin makomar abunda tafi nanata musu a labarin na ɓatawar da mahaifinta yayi da ita. Saukowa yayi daga saman banrandar da yake ya saka takalminsa ya nufo gindin bushiyar ya ciro ɗari biyu ya miƙawa Maryam
“Karɓi ki amso mata tea da bire a waje”
Sai da Maryam ta karɓa ta fita sannan ya kallin saman kan Namra yace
“Kuka baya magani abunda Allah ya rubutawa ma bawa, haƙuri ya kamata ki yi, Allah zai bi miki haƙƙin ki, abunda ya fi akwai kiyi ƙoƙarin shiryawa da iyayen ki babu kamar iyaye duniya komai kika zama a duniya idan babu albarka iyaye sai kin lalace kuma komai kika lalace idan akwai albarkar iyaye sai kin kai inda baki zato”
Ɗagowa tayi ta kalleshi ido cikin ido.
“Ta ya zan shirya da su? Na je gida da cikin wanda suka hana na aura? Bayan mahaifina ya yi min gargadi? Naje na faɗa mu su Asim ya sake ni? Ya kake ganin za su karɓe ni?”
Ɗauke kai yayi daga kallonta saboda zubar hawayen da take, ya samu kansa a tausayinta. Hannayensa ya zuba cikin aljihu ya nufi ƙofar fita gidan zuciyarsa nata raya masa abubuwa da dama.
Tea kawai ta sha, sai Neina tasa ta shiga ɗakinta ta kwanta, ganin an kawo musu wutar safe wai ko ta samu ɗan bachi. Lamido kuma ya dawo yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin yayi ma mahaifiyarsa sallama ya fita zuwa gurin a neman halalinsa.
KALSOOM POV.
“Ba zaunawa za kayi ba sakin ta nace ka yi ko baka ji ba?”
Hajiya ta faɗa a tsawace tana kallon Hilal. Gaba ɗaya sai hankalin Rashida ya tattara ya koma gurin da zancen da Hajiya tayi duk da bata san wainar da ake toyawa ba, hakan be hanata karantar akan mutuwar Rafiq ba ne, sai kawai ta ƙara narkewa ta fashe da kuka tana faɗin.
“Ina gawar ɗa na? Hilal ina ɗa na ya ke”
“Yana waje a motar Doc Noor”
Durƙushewa tayi a gurin wani kukan gasken ya zo mata. Sai ta Ummu Faisak ta shigo tare da wasu ƙanenen Rashida ciki har da Safiya.
“Da gaske ya rasu kenan? Kalsoom kin ci amana ta, kin kashe min ɗa sauran ƴaƴa ma na bar miki suma ki kashe”
Rashida na kaiwa nan ta tashi ta fice tana wani irin kuka. Ummu Faisak ya nuna Kalsoom da yatsa.
“Wallahi baki da imani Kalsoom kin kashe shi kin huta, yanzu sai ki zuba ruwa ƙasa ki sha, kin ƙori ƴar'uwarmu kin kashe ɗan ta hankalinki ya kwanta ko? Tam congratulations”
Ita ma ficewa ta yi tana kuka, tare da sauran ƴan'uwan. Kai kawai Kalsoom take girgizawa alamar a'a dan bata iya magana saboda kukan daya ci ƙarfinta.
Hilal har cikin ransa yake jin kukan Kalsoom cos shi kam he believe ba ita ta aikata ba.
“Hajiya kar mu aiakata abunda za mu zo muna nadama, wallahi ba ita bace ta rantse min”
“Iyyye nadama? Ah lallai Hilal yau kai da kan ka kake faɗin haka? Kasan hukumcin wanda ya aiakata kisan kai kuwa? Tafa kashe maka ɗa har lahira amman kake wannan maganar kamar wanda baya cikin hankalin kansa, ka sake fa nace ko kuma wallahi na tsine maka a yanzu”
Kalsoom ta matsa ta kama ƙafafun Hilal tana kuka tana girhiza shi
“Sake ni Hilal, ka sake ni a yau karka sallaaƙe maganar mahaifiyarka, ka sake ni dan girman Allah Hilal”
Kallonta yake kamin ya ɗaga kai ya kalli Hajiya idonsa da hawaye.
“Haba Hajiya da wanne zan ji? Rashin ɗa na ko kuma wannan matsalar? Ki bari komai ya laɓa za'a gano gaskiya”
“Da uwarka zaka ji, wawa kawai marar hankali, a yau fa sai ka zaɓa ni ko ita”
Ya maida dubansa akan Kalsoom da fatar fuskarta ta soma ja saboda kuka. Cike da nauyin baki ya ce
“Na sake ki saki ɗaya...”
Wani irin abu taji ya ratsata tun daga saman kanta har zuwa ƙasan ƙafafunta, wani sanyi ya ratsa gefen jikinta.
“Tashi ka yi ma ɗan ka sutura akai shi makwancinsa”
Ba musu ya tashi ya shiga ciki. Ya ɗan ɗauki lokaci kamin ya fito ya nufi waje. Da kansa yayi masa wanka daman yasan wanka gawa kamar yadda ake wankan tsarki ake yinsa, banbanci shine wannan ana saka masa magarya da kuma turare, sai kuma na mata daya ɓanɓanta dan shi akan tufke kan mace gida uku ne sannan a yarfar da shi a bayanta saboda hadisin Ummu Aɗiyya wajen siffanta wankan gawar ƴar Annabi S. A. W tace sai muka kitse gashin kanta tufka uku muka yarfa shi a bayanta _Bukhari da muslim ne suka ruwaito shi_ sai kuma inda take cewa na kasance cikim waɗanda suka yi wa Ummu Kulsum ƴar Manzo Allah s.a.w wanka lokacin data rasu farkon abinda Manzon Allah ya fara ba mu shine gyautonsa, sannan taguwa, sannan mayafin ka, sannan mayafin jiki sannan aka lulluɓe baki ɗayan jikinta da wata tufar. _Ahmad da abu Dawud suka ruwaito shi_ (Amman yanzu duk yadda aka samu yi ma mamaci ake indai ba an haɗu da masu illimi a gurin wankan gawar ba, Allah kasa mu cika da imani kasa ayi mana kamar yadda ma'aiki ya koyar)
A cikin gidan akayi masa salla, duk da yake gidan mai faɗi ne kuma ƙaramin yaro ne amman hakan be hana mutane da dama halartar zina'izar ba, wasu saboda Hilal wasu kuma saboda Hajiya wasu na ɓangaren Rashida ne wasu kuma dan gulma ne, saboda labari ya ishesu ɗan da kishiyar uwarsa tasa masa guba ya rasu, so that su samu damar bada labarin ai da su ma akayi salla yaron. Har da masu ɗaukar hoton gawar suna ɗorawa status duk da kasancewar wasu ƴan'uwane amman hakan be hana su yaɗa abunda suke ganin ya zame musu wajibi ba. Kan kace kwasi.har labarin mutuwar Rafiq ya cika social media, kowa sai faɗin albarkacin bakinsa ya ke, alhalin wasu basu sam komai akai ba.
Bayan sun tafi kai Rafiq ne maƙota mata suka shio cikin gidan, suka zazzauna tare da Rashida dake ta kuka kamar ranta zai fita suka bata haƙuri wasu kuma a ransu suke tsine mata suna faɗin wai kuna munafurci ne, daman wasu ganin fuskarta ya kawo su cikin har da Asmee Aminiyar Rashida.
Bayan sun dawo daga kai shi ne, mutane suka soma yi ma yi ma Kalsoom da Hilal gaisuwa. Tashi Kalsoom tayi ta shige ɗakinta ta bar su Hajiya falo dan duk sai ta tsargu da zaman Hajiya a falon.
Aikaws Hajiya tayi aka kira mata Hilal sai ta koma can ƙarshen falon ita da shi ta faɗa masa wai a maida zaman makokin a gidanta zai fi, shi dai to kawai ya amsa mata, dan ransa baya masa daɗi.
“To ita wannan yarinyar fa?”
“Hajiya a nan zata zauna ai kinsan Musulumcin ya yarda mace ta yi idda a gidan mijinta”
“Ikon Allah anya Hilal kana cikin hankalin kan ka? Wai wace hujja kake da ita ne na yarinyar nan ba ita ta aikata ba?”
Ajiyar zuciya ya sauke, dan har ga Allah be da abunda zai nunawa Hajiya a matsayin dalilinsa na ba ita ta aikata ba, shi dai a rantsuwar da tayi masa ya gamsu, kuma jikinsa na bashi ba ita ce ta aikata ba, wata ƙila dan yana sonta ne.
Ganin be ce komai ba yasa ta ce
“Zamu wuce can, idan ka gama lelenta sai ka kaita gidan su”
Juyawa ta yi ta koma gurin mutanen da suke zaune falon, shi kuma ya nufi ɗakin Kalsoom jiki a sanyaye.
ASIM POV.
Har yanzu bashi da damuwa akan abunda yayi ma Namra, shi yana nan yana jiran ta kira shi ko kuma ta aiko masa da saƙon ban haƙuri. Yana yawan waya da Nabila Nably da kuma Mardiya, a ɗan kwana ɗayan nan har ya saba da Nably kusan kullum sai sun yi waya sau biyar ko fiye da haka. Ya tura mata hotunsa ita ta turo masa, sai yaba kyawunta yake yana faɗin nan gaba kaɗan zai zo Abuja dan ta kawai.
Yau ya tashi da nishaɗin ɗaya kwana da shi tun jiya da dare da Hajiya Sadiya ta labarta masa zuwan baƙonsa. Yasan saɓon Allah ne zai aikata amman zuciyarsa a wanke take saboda burin samun kuɗin da Hajiya ta faɗa masa zai samu idan har ya sake jiki da mutumen. Suna breakfast ta ke ƙara nanata masa yadda zai masa da kuma irin shigar da zaiyi, already ta siya amsa turaruka masu kyau da tsada da zai saka.
A gida ya wuni duk da kasancewar ta yi nata bakin amman a ɗakinsa dan ta faɗa masa iɗan har tana da baƙi bata da buƙatar ya shigo gurinta idan ba wani babban dalili ba. A gida yyai Salla magariba bayan yayi isha'i ya shiga yayi wanka ya cuɗa jikinsa sosai kamar zai cire fatan, sannan ya fito jikinsa sai ƙamshin sabulan wankan yake kamar wanda ya saka turare, saboda tsadarsu, wasu ma ayau ya fara amfani da su.
Gaban madubi ya zo ya xauna kamar wani mace yana kallon jikinsa, tare da gyara gashin kansa. Mayuka masu kyau da saka laushin jiki ya shafa sannan ya bi jikin nasa da humra na maza sannan ya shafa wasu turarukan masu tafiya da imanin mutum ya shafe duka jikinsa. Sannan ya ɗauki wani baƙin jean ya saka da farar riga mai kyau, sannan ya ɗauki facing cap baƙa ya saka ya ɗauki wani turaren ya feshe jikinsa, da shi ya ɗauki lipstick ya shafa a bakinsa ka ɗan, sai kuma ya ɗauki baƙin madubin ido ya saka. Tsayawa yayi gaban madubi yana duba kansa da kansa, shi kansa yasan ya yi kyau mashallah, hakan yasa shi murmushi tare da ɗaukar kansa hoto.
Shigowar Hajiya Sadiya ne yasa ƴa ɗan natsu ya rage murmushin da yake.
“Wow...... Gaskiya Asim kana da kyau, kaga kan ka kuwa”
Ta taɓa masa gemu tana murmushin jindaɗin ganin yadda yayi kyau, har ya ɗauki hankalinta.
“Lallai za a je da kai Asim, wannan ƙamshi haka hhmnn ka iya business, to sai ka fito ga mota can ya aiko da dareba a ɗauke ka”
“To Hajiya”
Ya faɗa kamar a kumyace, sai kuma ya samu kansa da faɗuwar gaba. Ita kanta ta lura da yanayinsa na alamar tsoro ko kuma fargaba da ke cikinsa.
“Ka kwantar da hankalinka ka sake jiki ka ci arziki babu abunda zai faru, jeka mota na jiran ka”
“Okay”
Ya faɗa kana ya ɗauki agogon hannunsa ya saka, bayan ya ƙara fesa turare, ya nufu ƙofar fita. Ita kuma ta bishi da kallo tana murmushin jindaɗi.
ABDOOL POV.
Da wuri yyi breakfast gurin Ummi saboda tafiyar data zame masa ta dole, dan tun cikin dare Mai Martaba ya kira shi ya faɗa masa ya tura tawarga da za su je tare tun da rana, shi kuma zai bi jirgin safe ya sauka kaduna, dan da ƙarshe biyu za a ɗaura aure, so zai sauka da wuri dan ya samu ya huta ta kuma kimtsa cikin lokaci.
Duk cin abincin da yake idon Amira na kansa, irin kallon take masa na rasa yadda zan yi da kai. Sai dai bata bari ya ganta ko kuma Ummi ta ganta duk kallon da take ƙasa ƙasa take masa shi wanda ba kasafai mutum zai kula ba.
“Dude za ma zaka je da ni”
Amal ta faɗa tana ƴar dariya tare da kallon Ummi.
“Yaje dake ya aje ki ina? Shi da zai je ɗaurin aure kuma”
“To yau Assabar ba aiki”
“Ba shi na ke magana ba, yau zai je yau zai dawo”
Ummi ta amsa tana cin wainar ƙwai. Daman duk weekend sune suke rigan karyawa, sauran ƴan matan gidan duk sai dai su yi ta kwanan gajiya.
Agogon hannunsa ya kalla sai yayi saurin miƙewa tsaye yana dire kofin tea ya ce
“Ummi ayi mana addu'ah”
“To Allah ya tsare ya kiyaye hanya”
“Amin ya rabb, dude sai na dawo ko?”
“To Allah ya tsare”
Ta ɗaga masa hannu. Har ya juya sai Amira ta kira shi.
“Ya Abdool”
Yana juyowa ta miƙa masa tissue paper dan ya goge bakinsa. Hannu ya kai ya karɓa yana murmushi.
“Thank you. Sai na dawo”
“Allah ya tsare”
Ta faɗa tana murmushi kamin ta biyo sawunsa tare da Ummi suka raka shumi har gurin mota. Sai da ya bar gidan sannan suka koma ciki.
Goma da rabi na safe ya sauka kaduna, daga airport motocin Mai Martaba suka tarbosa, dukansu dagarawa ne cikin jajayen kaya sai bashi girma suke suna masa kirara, abunda ya tsana a rayuwarsa, shiyasa ya fi ƙaunar ya zo da a cikin motar Army's.
Yana shiga motar suka kama hanyar masaukin Mai Martaba da ke kaduna, dan acan zai huta sannan ya shirya su ɗauki hanyar Zaria. Jaridar dake cikin motar ya ɗauka yana duba, sababin labarai ne a cikin. Akwai labaruka kala-kala na abubuwan da suke faruwa a nigeria da kuma na ban aljabi.
Kerrrrr motar dake gabansu ta taka burki, sai direban dake jan Abdool ya tsayar da motar da suke ciki. Abdool be damu daya tambaye dalilin tsayawar motar ba, shi dai hankalinsa gaba ɗaya ya tattara ya koma kan jaridar.
Ɗaya ɗaga cikin dogaran da suke motar gaba ne ya zo ya ƙwanƙwasa ma direban dake tuƙa Abdool da kuma dogarin da ke front seat. Zuƙe gilashin motar dogarin yayi yana sauraren abunda ɗayan dogarin yake ce masa.
“Subhanallahi”
Kalmar da diriban motar yayi ne ya ɗago da hankali Abdool a izuwa gare shi.
“Ran Yareema ya daɗe, wani mai Napep ne aka kaɗe”
Dogarin dake front seat ya faɗa 6ana ɗaga ma Abdool hannu irin girmamawa nan.
“Garin yaya?”
Dogarin dake tsaye jikin motar ne ya amsawa Abdool.
“Allah ya taimaki Yarima Kutse yayi mana, yyai aron hannu ne mu kuma zo da gudu. Amman za'a wuce da kai gida ne mu sai mu ji da da shi”
Uffan Abdool be ce ba, sai kawai ya aje jaridar dake hannunsa ya buɗe motar zai fita, da saurin sauran dogaran duk suka yo kansa, na gaban yayi sauri buɗe gambun motar wa Abdool yana mai girmamashi.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *65 NOT EDITED⚠️*
*ASIM, AMIRA, MARDIYA, UZAIR, RASHIDA. Duk suna muku barka da sallah 😂*
Da ƙarfi take cije bakinta, tana mulmula saman tabarma dake ɗakin, sai faman rumtse ido take tana buɗewa, ita kaɗai tasan irin zugin da take ji.
Hawaye ne ya fara mata zuba, lokacin da ta ji abu mai ɗumi ya fara bin ƙafafunta, bata buƙatar a faɗa mata abunda yake shirin faruwa da ita, tasan abunda yake cikinta yake ƙoƙarin rabuwa da ita, sai dai ita kam har ga Allah bata shirya rabuwa da shi ba, dan tana jin kamar shi kaɗai ne mafita a gareta, ko ba komai bata son ta mutu bata bar abunda za a kalla a riƙa tuna ta ba. Babu banbanci tsakanin wacan ciwon da ta ji da kuma wannan, sai ma jin da take kamar wannan ya fi tsananta masa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi”
Shi ta samu ta furta da ƙarfi tana ƙoƙarin fita hayyacinta. Kana ganin yadda take yaƙi da numfashinta, kasan tana da buƙatar ratuwarta, wata ƙila saboda wasu dalilai na ta na karan kanta, ko kuma saboda cika wasu kuɗirinrika da suke gabanta.
Lokaci zuwa lokaci numfashinta yake barin jikinta, sai ta yi hanzarin dawowa da shi tana sauke ajiyar zuciya da ƙarfi.
Uwani ce ta shigo ɗakin da sauri tana tambayar.
“Lafiya Namra?”
A yanayin yadda ta ga Namra yasa ita ma ta furta innalillahi tana riƙa ta.
“Inna waurei”
Ta faɗa da yaren fulatanta tana mai ɗaga murƴa ta yadda Neina zata ji ta. Aiko sai ga Neina cikin ɗakin da gudunta har da ɗayar maƙociyarsu mai ganin sanin abunda yake faruwa, Maryam ma tana bayansu tare da ƙanenta maza.
Neina na ganin halin da Namra take ciki ta yi saurin kora Maryam da ƙanenta da kuma maƙociyar waje, ta sauke ƙyauren ɗakin.
cikin ƙarfin hali ta riƙa Namra, tana ƙoƙarin zame mata uwa a wannan lokacin, aiko nan Namra ta kama hannun Neina ta riƙe gam tana hawaye.
“Sannu ƴata sannu Allah kawo miki sauƙi, uwani ki je ki ɗibo mana lafiya dubu da wasu itatatuwan gidan su Mama a'i”
Neina ta faɗawa Uwani tana kallon Namra cike da tausayawa. Cikin sauri uwani ta tashi ta fita, bata ɗauki lokaci ba sai gata ta shigo da ruwa a kwano daga ta dire gaban Neina daga bisani ta miƙa mata ganyayyakin. A cikin ruwan Neina ta mirza su, ta miƙawa Namra, daker ta ɗan kurɓa kaɗan, sannan Neina ta shafa mata lafiya dubu a goshi, sai ta maida kwanon ta aje gefe da taimakon Uwani suka riƙa ta ta miƙe tsaye.
“Tashi muje banɗaki”
Tana fara takawa jiri ya ɗibeta sai ta rafke a gurin ta faɗi ƙasa. Hakan yasa Neina ta tura ƙofar ɗakin, ta rufe gudun kar wani ya shigo.
Gaba ɗaya idonsa da hankalinsa ya tattara ya koma kan ƙofar ɗakin, baya buƙatar a faɗa masa komai tun shi ba ƙaramin yaro ba ne, tun daga yanayin ihun Namra da ya ji da kuma gayyen da ga Uwani ta samo, yasan abunda yake faruwa. Wani irin tausayinta Namra ne ya lulluɓe masa zuciya, gaba ɗaya ya manta da nasa ciwon, he feel her pain, masu shigo suna masa sannu ma ba jinsu yake ba, sai dai ya amsa masu sama-sama, dan gaba ɗaya hankalinsa yana can, ga masu shigowa sai tambayar Neina suke daga shi har su Maryam babu wanda ya iya furta ga inda take, sai duk suka yi kamar bata cikin gidan. Hankalinsa ya fara tashi ganin an ɗauki lokaci, daga Neina har uwsni babu wanda ya sake leƙowa, ya san duk wani abu da Neina zata mata ba zai kai na asibiti ba.
“Maryam zaki iya zuwa bank ki ciro kuɗi?”
Ya faɗa yana kallon Maryam ɗin dake zaune kusa da shi. Kai ta girgiza masa alamar a'a.
“Okay je gidan su Mustafa ki ga idan yana nan ki ce masa ya je ya samo mota kuma ya ciro min wannan kuɗin sai a kaita asibiti”
Ya miƙa masa takardar kuɗin da Yarima ya bashi na one million. Zuwa tayi ta karɓa sannan ta sakata cikin hijabin dake jikinta ta nufi ƙofar fita. Bata ɗauki lokaci ba sai gata ta dawo sai faman sauri take.
“Baya gida”
“Aro min wayar uwani na aro wayarta na kira shi”
Miƙa masa takardar ta yi sannan ta nufi ɗakin tana buga ƙofar.
Daga can cikin ɗakin Neina ta tambayi waye, sai Maryam ta amsa da.
“Ya Lamido yace Uwani ta aro masa wayarta zai kira mustafa a kai Namra asibiti”
“Ai ba sai anje asibiti ba, Allah ya kawo mata sauƙi”
Buɗe ƙofar Neina ta yi, sai ga Namra tana takawa a hankali Uwani na riƙe da ita an ɗaura mata zane saman wani zane suka fito. Kallo ɗaya Lamido ya yi mata ya ɗauke kai be sake kallon inda take ba, har suka shige banɗaki.
Har cikin ransa yake aiyana irin zafin da Namra ta ji, a take wani irin tausayinta ya lulluɓe masa zuciya, idan kuma ya tuna irin rayuwar da ta fito ciki sai yaji kamar ya zubar mata da ƙwalla.
Uwani ce ta taimaka mata wajen gyara jikinta, sannan ta fito ta ɗauki kuɗi cikin jakar Namra ya aika Maryam ta siyo mata Pad, sai ta bi ta gidan maƙotansu ta karɓo mata bashin pant guda huɗu hannu Sadiya mai haja.
Neina ta gyara ɗakin sam kamar ba ayi komai ba, sannan taje ta ɗora mata ruwan wanka masu ɗan ɗumi ta kai mata banɗakin ki. A nan ne uwani ta bar mata banɗakin dan ta yi wanka.
Ta ɗan samu ƙarfin jikinta lokacin da ta yi wanka ta saka pad sannan ta ɗauki zanen da Uwani ta ɗora mata saman ƙofar banɗakin ta ɗaura ta saka hujabi, ta ɗan ɗauki lokaci zaune a banɗakin sannan ta unƙura ta fito. Da sauri uwani ta zo ta riƙa ta suka nufi ɗayan ɗakin da su Maryam suke kwana.
Saman katifar ta kwanta idonta tab da hawaye, tausayin kanta take ji irin ƙaddarar dake faɗa mata ɗaya bayan ɗaya, idan ta fita wannan sai kuma wannan. Bata da tabbacin cikin ya zube gaba ɗaya amman a yadda taga tsare tsaren jini bata zaton akwai abunda ya yi saura a cikinta. Bata bari Uwani taga hawayen da suka zubo mata ba, har sai da ta fita sannan tasa hannu ta shafa cikinta, tana tuna dalilin barin gidan Asim saboda cikin da yanzu babu shi, kuma bata da madafa, dan ba zai yiyu ta zo ta zauna musu a gida haka nan kawai ba, sai dai har yanzu tana tsoron komawa gurin Abbah, to tace masa me? Mutumen daya ce kar tayo fushi ma balle kuma saki ya shiga tsakaninta da Asim.
“Ba adili ba ne”
Ta furta a fili zuciyarta cike da ƙololon baƙinciki, tana tuna irin hallacin da tayi masa yayi mata wannan sakamakon.
Kai kawai take iya girgizawa tana tuna yadda ta rabu komai nata saboda shi, shi kuma a yau ya butulce mata. Dafata da Maryam tayi ne yasa ta dawo daga duniyar tunanin da take.
“Ki yi haƙuri Allah zai sake baki wani”
Kai ta ɗaga mata, tana mata kallon wacan Maryam ɗin ƙanwarta.
“Haka ne, babu abunda bata faɗa min ba, amman na ƙi na yarda na riƙa ƙaryata ta, yau gashi na ga komai daman duk wanda ya ƙi ji ba ya ƙi gani ba”
Da kuka ta ƙarasa maganar kamar wanda bata cikin hayyacinta. Maryam ta girgiza ta.
“Namra lafiya kike kuwa?”
Da sauri ta ɗaga mata kai tana ƙoƙarin share hawayanta.
“Lafiya ta ƙalau”
“Tau ga Maltina nan Ya yace ki sha da madara, mustafa zai karɓo kuɗi a kai ki asibiti”
Ta faɗa tana dire mata gwangwanin maltina guda biyu da madara.
“Ba sai an kai ni asibiti ba, na gode sosai Allah ya saka muku da alheri”
“Amin”
Maryam ɗin ta miƙe tsaye ta bar mata ɗakin. Dawowa tayi gurin da Neina take zaune da Uwani da Lamido, suke zaune ta zauna tana faɗin.
“Tace wai ba sai an kaita asibiti ba, ta gode Allah ya saka mana”
“A'a ba za'a barta haka ba kam, bari dai mustafa ya dawo”
“Ai taji sauƙi Lamido ko ba a kai ta ba, ko minene a cikinta be nina ba”
Neina ta faɗa, Lamido ya kaɗa kai.
“Ƙara dai aje asibiti nan ba zasu rasa abunda zasu mata ba”
“Kuɗin zaka ɗauka ka kashe kuma? Lamido kana ganin Napep ɗin nan taka ta lalace an baka ka siya wani ka samu na jari sai kuma ka ce zaka kashe”
“Haba ai kuɗin yayi yawan da ba zan iya kashesu duka a maganin baiwar Allah nan ba, kuma ko duka za a kashe mata wallahi zan iya badawa, kai ko Napep ɗin ce zan iya siyarwa dan nemaw yarinyar nan lafiya, wallahi mugun tausayi take ba ni”
Daga Uwani har Neina kallon juna suke da mamaki. Maryam ce ma tayi ƙoƙarin magana.
“Lallai Yaya kana tausayin yarinyar nan, Allah dai yasa labarin gaskiya ta ba mu dan kasan duniya yanzu yadda take”
“Amman ta miki kama da wacce zata baki labarin ƙarya? Haba Mairo ki duba yanayinta mana”
Har Neina zata yi magana sai ga Mustafa ya shigo, sai kawai ta sauya maganar da amsa masa sallamarsa. Kusa da abokinsa ya zauna yana bashi labarin yadda suka yi a bank.
“Wallahi akwai layi sosai, kuma naga rashin lafiya ne shiyasa sai nace bari na dawo sai ayi amfani da abunda yake aljihuna in yado idan aka ciro kuɗin sai na ɗauka, kuma kasan manyan kuɗi ne ba zan iya zuwa ni kaɗai ba, kar abiyo ni”
Duk da Lamido baya jin dariya hakan be hana shi darawa ba.
“Wallahi kai dai Mustafa kamar baka yi boko ba, ko da yake karatun naka iya diploma ya tsaya, amman miliyan ɗaya indai ƴan dubu dubu ne ai ba wasu kuɗi ba ne”
Neina ta girgiza kai.
“A a nan Alhaji Isa ba dubu ɗari ya zo dasu gida akan haka aka kashe shi balle mai miliyan ɗaya, ni tun ranar da Allah ya yi ni ban taɓa ganin dubu ɗari biyar a idona ba, balle kuma miliyan ɗaya”
Mustafa ya amsa.
“Wallahi fa ai zamani ne ya riga da ya lalace shiyasa komai sai an yi kafa kafa da shi”
“Allah dai ya shirya mana, ko bana ma son ana faɗar an fashi kuɗi har haka da yawa”
Cewar Neina tana miƙewa tsaye. Uwani ta ce
“Ai babu wanda ya sani idan ba mustafa ba, tun da ba mu faɗawa kowa ba”
“Allah dai ya tsare mu”
Duk suka amsa da Amin har Maryam dake ƙoƙarin tashi ita da Uwani su basu guri.
Bayan sun wuce Mustafa ya kalli Lamido.
“Wallahi babu wanda ya faɗa min haɗarin nan da ka yi in ba dan daka kira ni ba”
“Toh ai ba wani abun daɗi ba ne balle a riƙa yayatawa, kuma ba a daɗe da yin abun ba, Allah ma dai ya tsare”
“Allah ya ƙara tsarewa, amman dai wannan ɗan sarki ko sarki zan ce Allah be yi shi da rowa ba har miliyan ɗaya! Kamar wanda be san zafin kuɗi ba”
“Ya za'ayi ya san zafin kuɗi? Iyayensu suna kawashe kuɗin ƙasa, yanzu dai idan ka fita ka biya ka biya bilya kuɗin maltina da madara na aika am karɓo mata”
“Okay maganar asibitin fa?”
“Tace ba sai an jibe kuma naga kamar Neina bata son aje, ƙara mu ɗan saurara tukuna”
“Okay yayi Allah bata lafiya, amman ƴar'uwar ku ce ko? Naga kamar baƙuwar fuska ce”
Shiru ya ɗan yi yana tunanin faɗawa abokinsa nasa, sai dai baya jin zai iya ɓoyewa mustafa komai, kamar yadda mustafan baya ɓoye masa, kuma yasan idan ma be faɗa masa yanzu ba zai faɗa masa gaba, ko kuma ƴan gulma su tsegunta masa.
Hakan yasa be ɓoye masa komai daga haɗuwarsa da Namra da kuma labarin da Namra ta ba su nata.
Shi kansa Mustafa ya girgiza kuma ya tausayawa Namra matuƙa. Babu ma abunda yafi taɓa shi kamar rabuwa da tayi da iyayinta.
“Ai kaji matsalar mata suna da ƙaramar ƙwaƙwalwa, dan me zaka rabu da uwayen ka kan saurayi?”
Lamido ya numfasa.
“Ai mutum baya iya tsallake ƙaddararsa, sannan mu kan mu maza muna da matsala, da yawa sai ki ga dan kuɗin gidansu yarinya ake son ta, ni ina mamakin irin mazan nan wallahi, haka kawai abun wani ya tsune maka ido, ni dai Allah be sa min irin wannan rayuwar ba wallahi”
“Ai irin ka irin ka kaɗan ne Lamido, ni ma nan idan na ga arziki ba zan ƙi bi ba, masu arzikin nan suke kawai suke watayawa, ka duba kaga tun yaushe ka gama digiri ka yo bautar ƙasa, amman aiki ya gagareka, yanzu da kai ɗan wani mai kuɗi ne, da yanzu kana can Abuja kana hanawa kana aiki a wani babban kamfani”
Ajiyar zuciyar Lamido ya sauke.
“Muma Allah be manta da mu ba, kuma kaga wannan sana'ar Napep ɗin da nake? Ni ta wadarta da ni kamin Allah ya buɗo min wata hanyar kuma”
“Allah ya tabbatar mana da alheri, amman babu wanda ya ƙi kuɗi”
“Ita yanzu kallo ɗaya zata yi ma duka mazan takalawa alhalin ba haka muke ba, dan bamu taru muka zama ɗaya ba”
“Uhm, rayuwar ce sai a hankali, Allah ya bata wani na gari, ya shirya tsakaninta da iyayenta”
“Amin Amin”
*ABDOOL POV*
```Yana tsaye jikin wani upstairs, ya hango ta tana wani irin gudu kamar zata faɗi, kare na biye da ita a baya yana mata haushi, da alama karen take ma gudun, bata ankara da ƙaton ramen dake gabanta sai kawai ta faɗa cikin kamar an jefata. Daga can cikin ramen ta ɗagowa Abdool hannu tana son ya taimake ta sai kuma take, shi kuma ya yi tsaye yana kallonta kamar zai je, kamar ba zai je ba.```
Firgigit ya farka daga ɗan kajeren bachin daya kwashe shi yanzu-yanzu.
Haƙi yake sosai yana maida numfashi, jin yake kamar a zahiri ne abun ya faru. kyakkyawan askin kansa ya shafa, ya lumshe ido ya buɗe yana kallon agogon ɗakin.
“Mtsssss mi zai sa ba zan yi mafarkinta ba? Bayan na kwanta da ita a raina? Why this? Miyasa na zurfafa akan yarinyar nan ne? I'm totally mad”
Ya unƙura ya tashi ya nufi bathroom, zuciyarsa na raya masa ba zai yi mafarkinta haka nan kawai ba, shi kumasai yaƙar zuciyar tasa yake yana ƙaryata ta, dan ganin yake idan har ya yarda da ita to zata kai shi ga hallaka ne kawai.
Sai faman faɗa yake ma kansa kamar wani taɓaɓɓe. Har yayi wanka ya fito mafarkin be daina tsaya masa a rai ba. Haka ya shirya cikin tufafi na alfarma, wata musulmar shadda ya saka har wani maiƙo take tana shining daya ya motsa sai shadda ta amsa amo, shaddar ta karɓesa sosai, ta zauna a jikinsa kasancewarta sky blue, shi kansa da ya kalli kansa a madubi sai da yayi murmushi.
Wayarsa ya ɗauka ya ɗauki kansa hoto, sannan ya baro gaban madubin baya ya feshe jikinsa da turare mai mugun tsada da ƙamshi.
Already ya saka agogo hannunsa da zabban azurfa.
Yana doso sitting room mafarkinsa ya faɗo masa a rai. Wani irin faɗuwa gabansa ya yi har sai da ya rumtse ido ya murƙushe bakinsa.
“Wai miyasa yarinyar ta tsaya min arai ne? Ko dai akwai wani abun ne? Yeah na ga kare yana binta, ta faɗa rame? Me wannan yake nufi ne?”
“Allah ya taimaki Yarima, ba mu da masaniya akan abunda kake magana a kai, Allah yaja kwanan ka”
Kallon mamaki yayi musu yana juyar da kai, dan shi be san ya iso sitting room ba ma sai yanzu, ashe a fili yake maganar.
Iskar bakinsa ya furzar ya kalli tsadadden agogon hannunsa. Ƙarfe biyu saura minti goma ya gani, ya san ɗaurin auren ƙarfe biyu ne.
“Allah ya taimaki Yarima, tuni Mai martaba, ya kira kana bachi har ya bada umarnin tashin ka”
Hannayensa ya zuba cikin aljihu.
“Yanzu dole sai an naɗa min rawani?”
“Allah ya taimaki Yarima, haka Mai Martaba ya ce, har alkibar da zaka saka mun zo da ita”
Haka ya zauna suka naɗa masa rawani akai, ya fito fes Sarki, ba ma ɗan Sarki ba.
Miƙewa yayi tsaye suka saka masa baƙar alkyabar mai ratsin zaiba, sannan suka fiddo takalmin alkyabar suka aje masa ƙasa. A ƙoƙarinsa na saka takalmin ya kalli Sadauki ya ce.
“Idan ka yi mafarki kare yana bin ka me hakan yake nufi?”
“Allah ya taimaki Yarima, Maƙiyi ne.”
Ya ɗan yi shiru na wasu mintuna, kamin ya sake furta.
“Idan kuma ka faɗa a rame fa? Sai kuma ka miƙo min hannu kana son kamo ni?”
“Wannan Makaru ne, Allah yaja kwanan ka, idan kuma ina miƙa masa hannu to ina neman taimakon ka ne”
Sai da Sadauki ya gama amsa masa duka tambayoyinsa sannan ya saka takarmin, zai soma tafiya Sadauki ya ciro wani turare zai fasa masa.
“Allah yaja kwanan ka Mai Martaba ya ce afesa maka wannan”
“Na saka turare bana da buƙata”
“Allah ya taimaki Yarima, wannan na gidan sarautar ne, na Masarautar Katsina ne, ƙamshinsa ne zai sanar da isowar ka, kuma wannan turaren na gidane da ake haɗawa tun gadon gadon”
Ba dan yana so ba, ya tsaya suka fesa masa turaren sannan suka shiga gaba, wasu kuma a baya, shi kuma sai wata tafiya yake kaɗan-kaɗan, mai cike da tsantsar kasaita, da nuna isa, bayan kuma shi hankalinsa yana can wani gurin dabam.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *66 NOT EDITED ⚠️*
AMIRA POV.
Ta san yau zai dawo, amma hakan be hana ta kiwarsa ba, duk sai taji gidan ya mata girma kamar ita kaɗai ce a ciki. Tana son aika masa da saƙon tana tuna gargaɗin da yayi mata akan ta daina.
Bata san hawaye sun zubo mata ba, har sai da ta ji ɗuminsu a kumatunta, ɗan murmushi ta yi ta kai hannu ta share hawayen tana magana da kanta.
“Idan na ce zan yaƙi zuciya akan ka, zan cuce kai na, ban cancanci komai ba sai kyakkyawan sakamako, zan iya barin komai a kan ka, zan jure haƙurin rasa komai akan ka amman ba zan iya raka ka ba, ni nafi dacewa da kai Abdool, ba zan jure ganin wata ta raɓe ka ba, ba a hallinta maka wata matar aure ba, face Amira.
Wallahi ina son ka Abdool fiye da irin son da uwa take yi ma ɗan ta, kai mafarki, kuma kai kaɗai ne cikar burina, idan har na rasa ka Abdool to sai dai ko wace mace ta rasa ka”
Cige bakinta ta yi tana karɓar kukan da ya zo mata gadan-gadan. Mulmulawa ta yi ta mulmulo saman gado tana jin abu marar daɗi yana ratsa zuciyarta. Hoton da Abdool ya yi da Amal tafi tsurawa ido, tana masa wani kallo kamar wacce bata san shi ba.
“Kin yi sa'ar ɗan'uwa ni kuma zan yi sa'ar miji, ina son ka da iyalan ka Abdool”
Bata ankaro da ɗauki lokaci tana kukan ba, har sai da ta ji abu na ƙoƙarin rufe mata ido, alamar idon ya kumbura kenan.
Muryar Ummi da ta ji ne yasa ta sauri sauka saman gadon ta shiga bathroom ta wanke fuskarta, ta fito ta nufo falo.
A tsaye ta samu Ummi tana rataye da jakarta, mayafinta a hannu, Amal ma na tsaye a bayanta sai kumburi take, ita ala dole ga auta.
Tun da Amira ta soma saukowa downstairs Ummi take kalle da yanayinta, ga kuma kumburin da idonta da ƴa yi, fuskarta har ya soma ja abun ka da farar mace.
“Ba ki da lafiya ne?”
“A'a... Eh... Kai na ne yake ɗan ciwo”
Ummi ma uwace, ta fahimci Amira tana cikin damuwa ne, ko da bata fito a fili ta faɗa mata ba. Hannu ta kai ta shafa kan Amira zuwa wuyanta.
“Ki yi haƙuri kin ji, komai mai wuce wa ne, kin ji? Rayuwa bata tabbata haka amman dai ki yi tunani kin ji? Mu zamu fita, Haleema da Meesha ma sun fita Fauza ce kawai take bachi”
“Okay to sai kun dawo, me za'a girka?”
“No no kije kawai ki kwanta Shukura za ta yi komai, kije kawai ki yi ma kan ki karatun ta natsu”
Daga haka Ummi ta fice Amal na binta a baya, tana waigo Amira da harara dan ita har yanzu haushinta take ji, wai ta maida mata ɗaki kamar nata, daman can Amal ba son mutane take ba.
Maganar Ummi ta tsaya a mata a rai, me take nufi da ta yi ma kanta karatun ta natsu? Me hakan yake nufi? Juyawa ta yi ta nufi upstairs zuciyarta da tunani kala-kala.
RASHIDA POV.
Tana kewar ɗan ta sosai, wata ƙila dan kasancewarsa shi kaɗai ne ɗa namiji a gareta, ko kuma dan ita silar mutuwarsa.
“Na rasa abubuwa da dama, na rasa mijina, ɗa na, na rasa lafiya ta, yanzu kuma ina ƙoƙarin rasa iyayena, ni ka ɗai ce mai Aure da nake aikata zina? Ba suna nan da yawa ba? Miyasa ni bana da sa'a?”
Miƙewa ta yi tsaye daga saman prayer mat da take ta cire hijabinta ta nufi window.
“Idan har na bar gidan nan kowa zai tambayi dalili, kuma dole wasu za su gane abunda yake faruwa, idan kuma na zauna zan fuskancin tsagwama da takurawa, miye mafita?”
Hannu ta kai ta riƙa window, wannan karon sai ta koma zancen zuci.
‘Hakan yana nufin na rasa aure kenan har a bada? Idan kuwa gaka ne, to ba ni kaɗai zan shiga matsala ba, har Asmee tana ciki, kamar yadda nima ta jefa ni, kuma mijinta ma yana ciki, dan asirina ba zai tonu su na su ya rufu ba, bayan su ne silar komai, idan har na rasa Hilal ba zan rasa Alh Bashir ba’
Juyowa tayi ta jingina da window, yana motsa bakinta.
‘Idan kuma har na tona musu asiri na tonawa kai na, na matso da mutuwa ta kusa bayan kuma tana nesa da ni.
Amman kuma ba zai yarda ya tonawa kansa asiri ba, dan ba zai yarda ya rasa martabarsa da aikinsa ba, ni kuma ba zan rasa mijin aure ba, kuma hakan ba ƙaramin ƙona zuciyar Hilal da Asmee zai yi ba, su ma ya kamata su ɗanɗana yadda zafin baƙin ciki yake. I will never gave up, i will fight for my happiness, i deserve happiness again’
‘Idan kuma har Hilal ya rasa ni, be cancanci sake farin ciki ba, ya kamata ya ɗanɗana zafin rabuwa da ni, yasan akwai banbanci tsakanina da ita, Idan har ban more Hilal ba the love of my life be kamata wata ta more shi ba’
Komawa ta yi saman gado ta zauna ta ɗauki wayarta ta soma kiran Teema.
HILAL POV.
A gidan Hajiyarsa ya zauna har dare, sai da kowa ya watse sannan ya shiga sallama da Hajiya zai mata sai da safe.
Wani kallo uku saura kwata ta yi masa iron kallon Namijin da be san ciwon kansa ba, ƙasan carpet ya zauna kansa a ƙasa yana mai nuna mata tsantsar ladabinsa.
“Ban yarda ku kwana daki ɗaya da matar nan ba, kai dai ba jahili ba ne tun da kasan babu aure a tsakanin ku a yanzu”
Ba tare da ya ɗago kai ba ya ce
“Amman musulumci ya yarda da zaman idda, Hajiya zan bi duk wani umarni na ki, amman dan Allah karki gina katanga tsakanina da matana wallahi ina son ta”
“Kai wawaye Hilal, baka iya son mata ba, kana zurfafawa har ya zama baka iya ganin laifinta, ba zan gina katanga tsakanin ka da matar ka ba, dan ni ba irin surukar nan ba ne, amman zan nisanta ka da ita har sai ta gane kuskurenta ta yadda gaba ko ance ta aikata ba zata aikata ba, kuma ya zama dole ka ƙara aure!”
Ajiyar zuciya ya sauke still be ɗago ya kalleta ba, sai dai ransa be masa daɗi ba akan kalamanta.
“Zan yi duk yadda kika ce Hajiya, ke na fara sani kamin na san kowa a duniyar nan, ba zan zaɓi wata akan ki ba”
“Allah ya yi maka albarka, zan nema maka matar da zaka aura da kaina inshallah mai mutunci”
“Consider it done Hajiya, mu kwana lafiya”
Miƙewa ya yi tsaye idonsa sun rine sun yi ja sosai, irin ran maza ya ba ce sosai.
KALSOOM POV.
Tun da kowa ya watsa aka barta ita kaɗai sai duk ta ji babu daɗi ga kuma danuwar data saka ta gaba, tana ji a jikinta Hajiya ba zata barta ta zauna da Hilal ba. Haka ta zauna ta ci kukanta tun tafiyarsu har dare bata aikin komai sai kuka.
Tana jin tsayawar motar Hilal gabanta yayi dakan uku-uku. Ji take kamar ya zo mata da wani sabon abu, jin take kamar wata maganar zai faɗa mata wacce kunnuwanta ba zasu iya ɗauka ba.
Bata ƙarasa tsorata ba, har sai da ta ga ya ɗauki tsawon lokaci be shigo cikin gidan ba, hakan yasa ta unƙura cikin rashin kuzari ta miƙe tsaye, ta fito falo. Zaune ta same shi saman kujera ya haɗa kan sa da gwuiwa.
Ta ji babu daɗi sosai, sam bata jin damuwarta, ta sa damuwar take ji, bata san me Hajiya tace masa ba, amman a yanayin yadda taga mijinta ta karanci damuwarsa, duk abunda Hajiya zata ce mata ba zai wuce akan zamanta gidan ba, ko kuma wani abun daya shafe ta.
Juyawa ta yi zata koma ciki, sai kawai ta ji muryarsa ta daki dodon kunnenta.
“Ɗauko mayafin ki zamu je gida mu yi na su Momi bayani”
Bata juyo ba, ba kuma amsa masa ba, sai kawai ta cigaba da tafiyarta, hawayen na bin fuskarta.
Hijabinta yana kusa da gadonta, amman tsabar hankalinta baya jikinta haka ta bi tufafinta ɗaya bayan ɗaya bata ga Hijabin ba, sai kawai ta bude wardrobe ta ɗauko wani, Sannan ta ɗauki wayarta, ta handbang ɗin ta ta fito hawaye na cigaba da bin fuskarta.
Kamar mai koyan tafiya haka ta fito daga ɗakinta zuwa falo, shi kuma har lokacin yana nan zaune a yadda ta bar shi. Zuwa tayi ta tsaya bayansa tana hawaye.
Be yarda ya haɗa ido da ita ba, sai kawai ya miƙe tsaye ya nufi ƙofa ba tare da ya ce da ita komai ba.
Sai da ya yi ma motar key sannan ta fito daga falon ta shiga gidan baya, ja fisgi motar da ƙarfi, mai gadi na buɗe masa gate ya fara gudu kamar zai tashi sama. Shesshekar kukanta ne yasa ya rage gudun da yake ya faka gefen titi. Ya juyo ya kalleta.
“Try and cry so that i can tell you not to cry, Na fi ki shiga damuwa Kalsoom, ga damuwa na ga na ki ga na Hajiya ga na ƴaƴana ga na rashin yaro na duk ni kaɗai. Ba ki san waye Hilal ba shiyasa kike damuwar kan ki, yanzu haka za muje gida kina ciki damuwa da kuka? Kuka ba komai yake ƙara min sai karya min gwuiwa”
Be jira abunda zata ce ba, ya hau ttiti ya cigaba da tuƙa motar a hankali, har suka isa estate ɗin su. Gabanta ya faɗi sosai lokacin da ya danna horn a ƙofar gidansu.
An ɗan daɗe kamin a buɗe musu gate ɗin kasancewar a lokacin goma da ɗan gota, daman can a al'adar gidan da tara ta yi suke rufe gate.
Sai da mai gadin ya fara buɗe gate ɗin ya leƙo su ya ga su ne sannan ya koma ciki ya buɗe musu gate ɗin. Nesa da motocin gidan ya faka motarsa sannan ya jingina kansa jikin sitarin motar yana karanto irin bayanin da zai ma Daddy har ya fahimta.
“Ni ce zan faɗa musu komai?”
Dagowa ya yi ba tare da ya juyo ba ya ce
“Ta wace fuska?”
“Ta fuskar da za su fahimta, ka jira ni a nan”
Gefen hijabinta ta saka ta ƙara goge fuskarta sannan ta buɗe motar ta fita. Ita kanta tana fargaba yadda zata faɗa musu tun da ba magana ba ce mai daɗi, sai dai basa buƙatar a ɓoye musu komai. Ta daɗe tsaye jikin ƙofar falon tana tunani kamin ta tura ƙofar ta shiga.
Sallama tayi can ƙasan maƙoshinta, muryarta a dakishe alamar kuka ya kamata, babu kowa falon kuma kayan kallo a kashe, hakan ya tabbatar mata da sun shiga bachi ko kuma ƙannenta suna can suna karatu. Sai kawai ta juya ta fita daga falon ta nufi falon Dady.
Tun daga bakin ƙofar falon ta jiyo muryar tv, da alama yana kallon labarai ne.
“Assalamu alaikum”
Ta faɗa a daƙishe, haɗa baki suka yi gurin amsa mata. Duk da mamaki suka kalleta Momy ta aje plate ɗin abincin dake hannunta.
“Kalsoom shigo mana kika tsaya jikin ƙofa kamar baƙuwa”
Shigowa ta yi tana kuka, ta zauna kasa tana duƙunƙune fuskarka. Kallon natsuwa Dady yayi mata kana yayi gyaran murya ya ce
“Idan kin jin wani abu ne ya shiiga tsakanin ki da mijinki kuma ke ce mai laifi kar ma ki soma ba mu labari”
Cikin muryar kuka ta ɗago kai ta kalle shi
“Ba ni ce mai laifi ba, kuma Hilal ba shi da laifi, mahaifiyarsa ce ta saka ya sake ni”
Momi ta dafa ƙirjinta.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Dady kuma ya rumtse ido yana sauraren yadda maganar ta daki dodon kunnensa.
“Me kika mata?”
Momi ta sake tambaya.
“Wallahi ban mata komai ba, saboda mutuwar Rafiq ne”
A nan ta kwashe labarin duk abunda ya faru ta faɗa musu, sai da ta kai aya, sannan Dady ya kalleta ya ce
“Je ki shigo da shi”
Ba musu ta tashi tana kuka kamar ta shure ta fita. Hilal na tsaye jikin mota ta fito, yadda ya hango ta zuciyarsa ta nasalta masa bata faɗa musu gaskiyar abunda ya faru ba.
“Dady ya ce ka shigo”
Ta faɗa tun kamin ta ƙaraso kusa da shi, sai kawai ta juya, shi kuma ya rufa mata baya, zuciyarsa cike da zullumi.
Jimmm yayi lokacin da ya isa bakin ƙofar falon, sannan ya shiga da sallama yana mai sadda kansa ƙasa. Can jikin ƙofa ya zauna dan baya jin sakewar da zai ƙarasa kusa da su ya zauna.
“Kalsoom ta faɗa mana komai, kuma ba mu ga laifin ka ba, ko nine kwatankwacin abunda zan aikata kenan”
Cewar Dady. Hilal ya ɗan ɗago kaɗan ya ce
“Fushin Hajiya na ɗan wani lokaci ne, nan gaba kaɗan zata sake, shiyasa na ce za tayi zaman idda acen kamin Hajiya ta yarda na mai da ta”
Dady ya gyara zamansa, yana yi ma Hilal kallon hankali da kamala.
“Hilal ina son ka kasance mai haƙuri a duk halin rayuwar da ka tsinci kan ka. Kalsoom zata koma gidan ka amman ba yanzu ba, zata zauna a nan har sai lokacin da Hajiya ta ce ka zo ka tafi da ita, kuma ina mai baka shawara ka nemi matar da mahaifiyarka dake jin hankalinta ya kwanta da ita ka aura”
Da sauri Hilal ya kalli Dady
“Amman Dady bata hana....”
Dady ya ɗaga masa hannu.
“Ni a ɗana na ɗauke ka, kuma ba zan baka shawarar da zata cutar da kai ta cutar ƴata ba. Ka ɗauki shawarata kawai”
Maida kansa ya yi ƙasa.
“Amman Dady ita Kalsoom ta yarda?”
Dady ya kalli Kalsoom da ke kusa da Momi tana aikin kuka ya ce
“Zata yarda, ai tasan mahaifinta ba zai mata abunda zai cutar da ita, ka tashi ka je kar dare ya yi maka, ke kuma ki wuce ɗakin ƴar'uwarki”
Ita ce ta riga tashi ta nufi hanyar da zata sadata da ɗakunan tana kuka. Hilal kuma ya miƙe tsaye jikinsa a sanyaye ya bar falon, zuciyarsa na raya masa Dady yayi fushi ne shiyasa har ya yanke wannan shawarar.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *67*
Rasa ya yi inda zai sa kansa, gaba ɗaya ganin yake gabas da yamma sun haɗe masa, musamman ma daya dawo gida.
Sai tunani ya taru ya yi masa yawa, wanka daya saba yi kamin ya kwanta yau kam be yi ba, ko kayan jikinsa ma be damu ya canja ba haka ya hau gado ya kwanta, bachi ya ƙwauracewa idonsa gaba ɗaya, har safe be rumtsa ba, sai juyi yake kan gado.
Biyar da rabi na safe ya yi sallah asuba, bayan ya gama tasbihinsa ya ɗauko alƙu'ane ya buɗe ya fara karatu.
Ƴar ƙara wayarsa ta yi alamar saƙo ya shigo, sai dai be duba wayar ba, har sai ya gama karatun nasa yayi addu'ah sannan ya maida ƙur'ane mazauninsa ya aje. Kayan dake jikinsa ya cire ya ɗaura tawul ya shiga wanka, ya daɗe zaune a bathroom ɗin sai tunane yake kamin ya samu kuzarin watsa ruwa ya fito. Cikin rashin daɗin rai ya shirya, Farar shadda ya saka, be damu da duba kansa ba a madubi ba, ya saka agogon hannunsa tare da hulla, sannan ya ɗauki wayarsa yana duba ya nufi ƙofa,
Tunawa yayi da be saka turare ba hakan yasa shi ya dawo ya saka turaren sannan ya fice.
_Ka yi blocking ɗin number na, ka raba ni da ƴaƴana, Hilal ka ci amana ta, ina roƙon ka alfarma, dan Allah dan Manzon Allah ka bar ƴaƴa su dawo a gare ni su ne kawai gata na_
Yana karanta saƙon yasan daga inda ya fito duk da ba number ba ta bace. Wani godon tsaki yaja.
“Duk halin dana shiga ke ce sanadi Rashida”
Sai da ya yi deleted ɗin saƙon sannan ya buɗe motarsa ya shiga. Ya ɗauki hanyar da zata kai shi gidan Hajiyarsa.
Be iso mutane sosai a gidan ba, kasancesar Safiya ne, kuma mutum na ƙaramin yaro ɓe ba babba ba, ita kanta a lokacin da ya shiga cikin gidan tana can cikin ɗakinta tana shiryawa.
Guri ya samu a falonta ya zauna, yana kallon tv duk da hankalinsa baya gurin, ɗai da ɗai ƙannensa da mutanen gidan suka riƙa shigowa suna gaishe shi da yi masa ya haƙuri, shi kuma yana amsa musu kamar an cilasta masa.
Sai takwas saura Hajiyaraa ta fito daga ɗakinta. Ta yi mamakin ganinsa a falon kamar wani baƙo mutumen da ya saba shiga har ɗakinta idan ya shigo cikin gidan.
Ƙarara Hajiya ta ga damuwa da rashin bachi a idon ɗanta, ba ta yi mamaki ba, daman can ta tsammaci haka, sai dai ita aabunda yake duba mas ba shi yake hangowa ba.
“Hajiya ina kwana”
Ya gaishe ta ba tare da ya ɗaga ido ya kalleta ba.
“Lafiya ƙalau ya haƙurin mu?”
“Alhamdullah”
“Ka yi haƙuri Hilal haka rayuwa take zuwa wani lokacin, kai taka ƙaddarar ta rashin mata na gari ne, ta ɗayan ba daɗi wannan ma ba halin ƙwarai, amman inshallah zaka ji daɗi, zan nema maka mata mai hankali da ladabi, mun yi magana da mahaifin ka ma, da ba dan wannan gaisuwar ba da kaje ka ganta, dan bana son auren ku ya wuce wata biyu ko uku ba, yarinyar ƴar gidan mutunci ce”
“Duk yadda kika ce Hajiya haka za'ayi amman ina roƙon alfarmar zan je aiki idan da dama a yi addu'ah yau, tun da yaro ne kuma daman can sunna bata koyar da mu wannan zaman kwana ukun da ake ba....”
“Eh Mahaifinka ma yayi wannan maganar amman naga tun da kwana uku ne, kuma kaga yanzu kwana ɗaya ya rage ai ƙara ka yi haƙuri kawai,amman kai zaka iya juwa aikin ai”
Kamin yayi magana sai ga Ezzah da Ulfah sun fito cikin shirin makaranta, da gudu suka zo suka rumgume shi.
“Dady i miss you”
Ulfah ta faɗa. Ita Ezzah sai tasa kuka.
“Dady shikenan Rafiq ba zai dawo ba?”
Kansu ya shafa cike da ƙaunar ƴaƴan nasa, da kewarsu kamar ba jiya ya rabu da su ba.
“Kin taɓa ganin wanda ya rasu ya dawo? Sai dai ki yi masa addu'ah”
“Ni kam i hate Anty Kalsoom ita ta kashe mana Rafiq”
Ya buge mata baki kaɗan.
“Kar na sake ji, akwai mai kashe wani bayan Allah ne? Kar bakinki ya sake irin wannan furucin”
“Dady wallahi ita ce ta kashe shi”
Ulfah ma ta faɗa, ta fuskanta kamar za ta yi kuka.
“Kuje driver na jiran ku zaku je school”
Hannu yasa aljihu ya ciro dari biyu ya mika musu, suka karɓa da far'ah suna godiya.
Da kallo Hajiya ta bi su har suka fice sannan ta ce
“Ni wallahi tausayi suke ba ni, shiyasa nake son ka auri yarinyar nan dan ga alama tana da natsuwa zata kula da su”
miƙewa ya yi tsaye yana dai-daita hular kansa.
“Zan leƙa office, idan na gama abunda na ke zan dawo”
“Amman ka karya kuwa?”
“A a zan karya a can”
“Allah ya tsare amman da ka tsaya ka karya a nan dan na san a can ba komai za ka ci ba”
“Zan ci”
Daga haka yasa kai ya fice, ransa a jagule.
NAMRA POV.
A ɗakin ta wuni har yamma, tun tana kuka mai hawayen har hawayen suka daina zuba, sai dai tayi kukan kawai babu hawaye.
Gaba ɗaya yanzu hankalinta ya tattara ya koma gida, tana kewar ƴan'uwanta sosai, duk da tadan itace bata kyauta musu ba, sai dai tana jin son mahaifiyarta a ranta tana kewarta.
“Bana jin ina daga cikin masu daɗewa a duniya, ina ji kamar mutuwa ta tana kusa da ni, ina da bukatar ki Mama, Abbah ka yafe min na tuba”
Magana take da kanta kamar wata taɓɓabiya. Miƙewa ta yi tsaye ciki da ƙargin hali dan bata jin karfi sosai a jikinta, fitowa ta yi waje, tana sun sun da kai kamar mai jin kunyar kallon inda su Neina suke.
“Ba wuta ai ƙara ki fito nan kam ki sha iska”
Neina ta faɗa tana gyara mata gurin da zata zauna. Ita kuma har ga Allah kunyar haɗa ido takw da Lamido balle kuma ta zauna inuwa ɗaya da shi.
“Zo ki zauna mana, jiri zai iya ɗaukar ki idan kina tsaye”
Ya faɗa ganin yadda ta tsaya a bakin kofar kamar ba zata zo ɗin ba, sosai gabansa yake faɗuwa, har murƴarsa na ƙoƙarin gargadar a maganar da yake mata saboda faɗuwan gabansa da ya tsananta.
Tana fara takawa gabansa ya fara fisgarsa yana wani zillo, da zaka tsaida idonka a lokacin da kyau a ƙirjinsa zaka ga yadda zuciyarsa take bugawa. Saurin ɗauke kansa ya yi daga kallo tafiyarta da yake kamin ta ƙaraso kusa da su.
Tana ƙaraso gurin sai kawai ta ɗauki filon da Neina ta aje mata, ta kalli Uwani ta ce.
“Dan Allah dan duba cikin jaka na akwai waya sai ki ɗauko min”
Ba musu Uwani ta tashi nufi ɗakin. Bata ɗauki tsawon lokaci ba ta fito da wayar a hannu ta miƙa wa Namra.
“Na gode”
Ta faɗa sai ta juya da zimmar komawa.
“Ai da kin zauna a nan”
“A.a daman wayar kawai nake son ɗauko wa”
“Zauna a ɗakin kawai, make yourself comfortable”
Kai kawai ya iya ɗaga masa, ta juya ta koma cikin ɗakin. Zaunawa ta yi tana sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta kafe wayar da ido kamar mai shakkun kunnawa.
Can dai ta kunna wayar zuciyarta cike da fargaba, da tunani kala-kala. Gabanta ya soma faɗuwa lokacin da saƙwanni suka riƙa shigo mata bayan ta kunna wayar. Sai dai mafi yawanci su duka na Mtn ne, sai saƙo ɗaya mai ɗauke da number Yasmeen. Saƙon ta fara buɗewa, tana tunanin wane irin saƙo ne Yasmin ta aiko nata.
_Salam Namra na haihu na samu baby girl, na kira wayarki ban samu ba_
Murmushi ta yi tare da hawaye a lokaci ɗaya.
“Allah ya raya miki babyn ki, ya baki lafiyar shayarwa”
Shine furucin da tayi a fili, ta rumgume wayar ta lumshe ido.
‘Ya kamata na koma gida, ko me me zai faru ya faru a can, na yi kuskure tun farko da ban sauka gidan mu’
Tunanin da take a ranta kenan, kamin ta buɗe ido, ta fara kallon ɗakin.
“Gobe... Gobe ya kamata na je gida, an cire duk wani fargaba da yake rai na, zan cire tsoro zan gwada ƙarɓar sunana ko Alƙah zai za na dace, ba zaka taɓa winning ko losing ba matuƙar baka taɓa gwadawa ba, i hate to try”
A fili ta yi furucin zuciyarta cike da yaƙinin lallai zata iya, kuma ta shirya fuskantar ko wane irin hukunci na Abbah.
“Taya zai yafe min idan ban je ba? Taya zan shirya da Anty idan ban je ba? I have to do this, Allah ka taimake ni”
Komawa ta yi ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala.
ABDOOL POV.
“Lafiya ƙalau aka ɗaura aure”
“Mashallah Allah ya nuna mana na ka, ya maka albarka”
“Amin Mai Martaba”
“Ka yi kyau sosai, ka fito kamar wani babban sarki”
Kallon Mamaki Abdool yayi kamar ance masa Mai Martaba yana tsaye gabansa.
“Waya faɗa maka?”
“Babu ruwanka, ai har hoton ka an turo min alkyabar ta karɓe ka sosai”
Dariya yayi cike da mamaki, dan shi dai be san ya ɗora hoton daya saka alkyaba ba a media balle yace ko wani ne ya tura masa.
“Mai martaba kasan ance informer hukunsu ɗaya da da mai fashi da makami ko”
“To ayi haƙuri Major ayi haƙuri muma muna kan aikin mu ne”
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya daga shi har Mai Martaba, daga bisani Mai martaba ya ɗora da.
“Ƙarfe nawa zaka ta so?”
Shiru yayi kamar mai tunani, haka kawai ya samu kansa da rashin jindaɗin tafiyar.
“Zan turo maka dogarawan ka sai a bar min Sadauki, zamu kwana biyu kamin mu dawo”
“Why?”
“Just kawai ina son ganin kaduna ne, kasan rabo na sa kaduna since... I can't even remember”
Ya ɗan sosa kansa yana kallon titi da mutake ta kai kawo suna sha'aninsu.
“Fine as you wish, amman aikin ka fa”
“Mun samu hutu ai ko ka manta?”
“Haka ne, to ba matsala amman dai karka ɗauki lokaci i have surprise for you”
“Thank you super Dad”
Daga haka ya kashe wayar ya kalli Sadauki dake front seat ya ce.
“Mai Martaba ya ce sauran za su iya kama hanya yanzu kai kawai zaka tsaya sai jibi za mu koma”
“An gama Yarima, Allah ya ƙara maka lafiya”
Be amsa ba sai kawai ya maida hankalinsa kan titi. Can kuma ya kalli agogo hannunsa.
“Yaushe zamu isa Kaduna?”
“Allah ya taimaki Yarima, nan da minti goma sha biyar zamu isa”
Daga nan be sake cewa komai ba har suka isa masaukinsa. Su suka buɗe masa mota ya fito suka rufa masa baya suna masa kirari, iya ƙofar falon suka tsaya. Sai ya juyo ya kalli Sadauki ya ce.
“A ba ko wannensu 30k kai kuma ka shirya anjima zamu je mu duba marar lafiyar nan”
“An gama Yarima, takawarka lafiya ɗan sarki jikan sarki, an gama ɗan adalin Sarki”
Sai da ya shige sannan suka janyo ƙofar suka rufe masa. Alkyabar jikinsa ya fara cirewa sannan ya buɗe maɓallan rigarsa, ya kishingida saman kujera, ya lumshe ido.
Tun da ya shiga ciki be fito ba sai da aka yi kiran sallah magariba daman basu baro zariya ba sai da aka yi la'asar.
Tare da Sadauki suka yi sallah a masallacin da ke kusa da gidan, sannan suka nufo gida. A hanyar su ta dawowa ne Abdool yake masa jan kunne.
“Bana son abunda kake min, karka sake ɗauko min takalmi ka aje min, kuma daga yau kar na sake jin wani kirari nawa a bakin ka, ka kira ni da Abdool kawai ko Yarima amman ba sai ka min kirare ba”
“Allah ya taimake ka za a daina”
Ya faɗa cikin girmamawa.
“Zaka iya tuna inda muka je gidan mai Napep ɗin nan da muka kaɗe?”
“Allah ya taimake ka, zan gane”
“To za mu koma mu duba shi, akwai canji a hannunka ko? Zamu siya musu fruits”
“An gama Yarima”
“Zan shiga na canja sai muje”
“A canja da kyau ɗan Sarki, Allah yaja zamanin ka”
Kallo ɗaya Abdool yayi masa ya kauda ido yana girgiza kai.
******************
Bayan salla magariba Uwani ta shigo ɗakin ta kunna mata kendir, ta aje mata maltina da Madara da kuma tea mai kauri, tare da biredi.
“Kuma ɗawainiya da ni na gode sosai”
Mirmushi Uwani ta yi
“Ba komai ai yi ma kai ne. Ki ci dai ki samu karfin jiki”
“Ni kaina ina son na samu ƙarfin jikin ko zan samu damar komawa gurin iyayena”
“Tafiya za ki yi?”
“Gobe na ke so idan Allah ya yarje min”
“Amman ina laifin ko nan da sati idan kin ƙara jin sauƙi?”
“Wata ƙila idan suka ga na samu sauƙi su ƙi karɓa na, amman ganina a hakan zai sa su tausaya min”
“Amman dai da kin yi haƙuri har ki ji sauƙi”
“Ina son tafiyar ne”
“To bari na faɗawa Neina”
Ta juya cikin rashin jidaɗi dan yanzu sun ɗan fara sabawa da Namra, zancen tafiyarta be mata daɗi ba.
“Neina wai kin ji Namra zata tafi”
Abunda ta fito tana faɗa kenan, ganin Yarima yasa ta yi saurin sadda kanta ƙasa jikinta ya shiga rawa.
“Barka da dare”
“Barka...”
Ya amsa kaɗan-kaɗan yana tsaye kan Lamido, dan ya kasa zama tun da ya shigo gidan yanzu ma ya samu kansa da ƙyamar gidan. Farar shadda dake jikinsa sai ƙara haska shi take. Uwani ta yi mamakin ganin sa ba dogorai, sai dai haka be hana ta gane shi ba.
Unƙurawa Lamido yayi ya tashi zaune daga kwance da yake, dan zuwan Abdool be sashi ya ɗago ba duk da cika masa ido da yayi, da kuma kwarjinin da ya yi masa, yana jin rashin sakewa da Abdool wata ƙila saboda ba matsayin ɗaya ba, ko kuma dan kaɗewar da yayi masa ne ya hana shi ganin farinsa sai haushinsa yake ji. A ƙoƙarinsa na avoiding ɗin Yarima ya kalli Uwani da Neina ya ce.
“Wani abu aka mata ne?”
“A'a wallahi sai dai ko ta gaji da zama ne, ko tana son ta koma Katsina ne”
Cewar Neina. Sai Uwani ta amsa da
“A'a wai ta ce tana son ta koma gida ne, ko zasu tausaya mata su karɓe ta, kuma wai gobe zata je, kamar wace ake kora”
“Amman Namra bata da tunani, taya zata koma gurin iyayenta cikin wannan hali?”
“Wlh kuwa, ni ma na ce ta yi haƙuri dai har gaba...”
Tsawa Sadauki ya katsawa Uwani, wanda shi kansa Lamido sai da ya zabura balle kuma Neina da daman jikinta rawa yake, ganin ɗan sarki tsaye a gidansu.
“Ke ƴar talakawa ba a wata magana a gaban Ɗan Sarki, kama kan ki ki iya bakin ki...”
Sosai Uwani ta shiga natsuwarta tsabar tsoro ma har ji tayi kamar ta amayar da hanjin cikinta. Abdool kuma wa watsa ma Sadauki Harara, dan sosai yake jin daɗin maganar da suke, sarau zuciyarsa ta raya masa da Namra ake, duk da bashi da tabbacin hakan.
Tsawar da Sadauki yayi ma Uwani ne yasa Namra ta san da akwai baƙo a gidan dan ta ji muryar da ba ta ɗan gidan ba. Hakan yasa ta aje maltinar dake hannunta, ta gyara tsawyuwar Hijabin dake jikinta ta leƙo ƙofar ɗakin.
Bata gane ko waye ba, bata kuma ta mu da ta sani ɗin ba, sai kawai ta juya ta koma ɗakin. Shi kam Abdool sarai ya gane ta, dan ya daɗe da haddace fuskarta, duk da duhun magariba ya fara saukowa hakan be hana shi gane ta ba.
Ya daidaita tsayuwar hannayensa da ke cikin aljihu, ya juya ba tare daya ce da su komai ba, sai sadauki ne yake musu Allah ya ƙara lafiya, duk suka amsa da Ameen ban da Lamido.
Be yarda yayi ma Abdool kallon banza ba, ko wata yassar magana sai da ya juya baya ya fice.
“Wani zai nunawa isa, girman kan tsiya”
“Aa Lamido karka jawa kanka, dan Allah ka iya bakin ka”
Neina ta faɗa zuciyarta cike da tsoro. Wani wawan tsaki Lamido yaja ya wuyar da fuskarsa zuwa ɗakin da Namra take ciki.
**************
Tafiya yake guda guda yana tsotsar bakinsa kamar mai shan minti. Jinginawa yayi da motar da suka zo, yana kallon Sadauki yana tsaya gefensa cike da ladabi.
“A bincika min baƙuwar fuskar da take gidan nan, wacce ta zo daga Katsina i can't recall her name amman ai ka ji yarinyar da suke magana akai ko?”
“Za a bincika, Allah yaja zamanin ka, ya ƙara maka lafiya”
Wannan karon Abdool da kansa yayi driver zuwa suka ɗauki hanyar masaukinsa, sai tariyar maganar su Uwani yake, yana analyzing.