YARIMA SUHAIL.π*
_STORY,WRITTEN &EDITED BY._
*SIS NERJA'AT.*
_COMPILATION BY._
*HAWWA M.U (®EAL $MASHER).*
?ππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
_Jinjina agareki my hafnan ina tayaki murnar fara new novel d'inki *HIBBATULLAH* akowane lokaci kina a ❤ππ» d'ina_
_~Sak'on gaisuwata agareki my blood sis *Aufana* sonki a cikin jinin jikina yakeππ~_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Wannan page d'in nakine Sainah Ummun Meenal uwa tagari Allah yabar mana keπ_
page 1⃣
garin gazban garine mai albarka da yawan mutane yana d'aya daga cikin garuruwan da ake alfahari da su.
sun kasance suna da babbar Masarautar da babu kamarta wajen girma da kyau sarkin garin ya kasance sarki mai adalci duk kud'in mutum bai isa yazalunci nak'asa da shi ba indai har yazalunta labari yazo ma sarki toh sai yad'auki mataki,
sarki umar yana son talakawansa sosai suma suna sonsa abun mamaki wannan sarki ya manyanta domin zai kai shekaru 76 ammah indai ba ka saniba sai kad'auka d'an shekara 50 ne, domin babu alamun tsufa a tare da shi idan dukiyarce ya tara, idan sarautarce yana d'aya daga cikin manyan sarakuna kai intabbatar muku wannan babbar Masarautar ko da me kazo anfika.
Sarki faruk matarsa d'aya dattijuwa dada, saidai abun mamakin duk mulkin nasa ammah 'ya'yansa biyu dukansu maza ne Ahmad shine babba sai k'anensa Abbas sun taso atare sun kasance suna son junansu.
saidai a tsarin mulkin garin indai sarki yahaura shekaru arba'in (40) saman karagar mulki toh d'ansa ba zai ta6a gadon mulkinba saidai babban jikan gidan, saidai idan babu jika namiji shine d'an sarkin yake hawa mulkin
lokacin da 'ya'yansa suka tasa yaza6a musu mata inda Ahmad ya auri d'iyar sarkin agadaz wato sultana Bilkisu, shi kuma Abbas sarki ya aura masa d'iyar d'an uwansa da yamutu yabari wato Sultana Sadiya.
A cikin babbar Masarautar kowa aka fitar masa da 6angarensa.
Suna zaune lafiya da matansu, inda sultana Bilkisu takasance macece mai hak'uri da tawakkali ga ta macece mai kyauta ta kasance mai son jama'a,
inda Sultana Sadiya takasance akasin haka domin bata son talakkawa suna ra6arta dan ma mijinta a tsaye yake sun d'auko hali irin na mahaifinsu, ammah duk da haka taci alwashin ita take da burin tafara haihuwar d'a namiji.
saidai kash sultana Bilkisu ita tafara samun ciki, hankalin sultana Sadiya ya tashi sosai ganin ita ko 6atan wata bata ta6a yiba,
Bayan wata goma sultana bilkisu tahaifi d'iyarta mace murna wajen iyayen ba'a magana hatta ita kanta sultana Sadiya tayi murna ganin ba namiji bane ta haifa.
ranar suna anyi shagali sosai kud'i sunyi kuka tsakanin masarautar gazban da masarautar agadaz anzuba naira sosai a inda yarinya taci sunan dada wato Asma'u ammah ana kiranta da husna.
Bayan shekara ukku Sultana bilkisu tak'ara haihuwa inda tasamu d'anta namiji kyakkyawa domin ita yabiyo kamar antsaga kara murna wajen su sarki ba'a magana hatta su kansu jama'a sun shaida wannan haihuwar domin sarki sadaka yadinga yi da dukiya sosai,
akasin sultana Sadiya da takasa 6oye bak'in cikinta turakar mijinta taje tasameshi a zaune yana ta kiran waya yana fad'a ma mutane, zama tayi gefensa tana kallonsa cike da takaici har yagama wayar sannan yakalleta fuskarsa d'auke da murmushi yace sultana akwai abinda kike buk'ata ne?
sultana sadiya d'auke fuskarta tayi daga kallonsa tace ranka yadad'e meyasa kake murna dan matar d'an uwanka ta haifi namiji kar fa kamance shine zai hau karagar mulki bayan ran sarki,
da mamaki sultan abbas yake kallonta yace sultana ba dai bak'in ciki kike ma d'an uwana ba dai ko?
d'aure fuska sultana tayi tace bak'in cikin me zanyi masa, naga kana ta murna ne mukuma kaduba kaga ko 6atan wata ban ta6a yiba bamu da d'a ko d'aya kuma kyau ace d'an kane zai gaji masarautanan.
sultan Abbas sakin baki yayi yana kallonta har takai aya sannan yace sultana inaso kisan wani abu wlh da zuciya d'aya nake son d'an uwana ban damu da sarautar da d'ansa zai hau ba domin nima d'ana ne sannan da kike magana akan rashin haihuwa inaso kisani Allah shi yake badawa ga Wanda yaso kuma yahana Wanda yaso ban cire rai ba idan da rabo nima zanga tsatsona, dan haka kar ink'ara jin kinyi wannan maganar, kibinneta daga nan da kika yi ta.
Mik'ewa sultana tayi cikin fushi tace daman nasan ba zaka ta6a fahimtaba ammah nan gaba dakanka zaka fahimci abinda nake nufi. wucewa tayi fuuu tafita tabar d'akin.
Sultan Abbas binta yayi da kallo har tafita sannan yagirgiza kai cike da takaicin abinda matarsa tayi yace Allah yashiryeki sadiya.
Ranar suna yaro yaci suna Umar sunan maimartaba ammah suna kiransa da suhail,
suhail yataso cikin gata domin yana samun kulawa sosai a wajen iyayensa da kakanninsa hatta shi kansa sultan Abbas yana ji da d'an nasu,
akasin sultana sadiya da ta tsanesa bata d'aukarsa sai idan gaban su Dada ne nan take nuna tana sonsa sosai, ammah a cikin zuciyarts ji take ina ma ace yamutu.
ahaka yataso cikin gata tun yana shekara ukku maimartaba yakesawa ad'aukosa akawo sa fada yazaunar da shi kusa da shi saisa suhail yataso ya shak'u da kakansa sosai.
Bayan shekara biyu sultana sadiya tasami ciki murna wajensu da wajebnsu sultan Ahmad ba a magana,
kulawa sultana sadiya take samu sosai daga wajensu maimartaba da mijinta hatta ita kanta sultana bilkisu tana bata kulawa sosai.
inda sultana sadiya take addu'a akan Allah yasa tahaifi d'a namiji.
inda itama sultana Bilkisu take d'auke da d'an k'aramin cikinta.
bayan wata tara sultana sadiya tahaifi d'iyarta mace ta yi bak'in ciki sosai ammah daga baya tahak'ura, murna wajen su maimartaba ba'a magana kowa ya nuna farin cikinsa,
ranar suna yarinya taci suna sumayya, anyi shagali sosai anci ansha.
inda sultana sadiya taci alwashin ta kowane hali sai d'iyarta ta auri sarki mai jiran gado .
bayan wata ukku sultana bilkisu tahaifi d'iyarta mace inda taci sunan mahaifiyarta wato Rahama,
tun daga lokacin babu wadda tak'ara ko da 6atan watane, sumayya da Rahma sun taso a tare komai nasu d'aya bacci kawai yake rabasu.
Yarima Suhail duk halin maimartaba yad'auko yatashi mutum ne mai tausayi kuma mai girmama na sama da shi saidai ya kasance bai da son hayaniya miskiline na sosai baya shiga abinda bai shafesaba baya da yawan fara'a sosai saidai ga wanda bai sansaba zai masa kallon mutum mai girman kai.
In ko kagansa a fada toh maimartabane yasa yaje ammah shi kwata-kwata baida burin yin sarauta, ko da dakagansa komai nasa irin na sarauta yakeyi.
tun da yataso abokinsa d'aya d'an waziri wato shahid tare suka taso tun suna yara sunyi makarantar arabi da boko a garinsu.
bayan sun gama secondary yarima suhail yanuna yanaso yafita waje yayo karatunsa, anyi daga sosai da maimartaba afin ya amince domin cewa yayi shi da zai gaji sarauta mezaisa yafita waje karatu, daga baya dai dakyar aka samu maimartaba ya amince inda yarima yaje india yayi karatunsa na likitanci inda yakaranci surgeon.
bayan shekara biyu akasha bikkin Gimbiya husna inda ta auri d'an chairman d'in garin anyi shagali sosai anyi bikkin da ba a ta6a irinsaba a garin, inda husna tatare a gidan mijinta
yarima suhail yaso yazo ayi bikkin da shi ammah iyayensa suka hana sukace yazauna yayi karatunsa.
Gimbiya Sumayya da Gimbiya Rahama sun shak'u da juna sosai saidai suna da banbancin halayya sumayya tana da wulak'anci sosai kuma ta tsani talaka yara6eta bata abota da kowa sai wanda yakasance jinin sarauta ko d'an wani attajiri.
akasin Gimbiya Rahama da takasance mai son jama'a kuma bata da wulak'anci kowa natane abinda yake had'ata fad'a da sumayya kenan ko a school.
Bayan shekara hud'u yarima suhail yakammala karatunsa yadawo k'asarsa ta haihu ya k'ara girma da kyau miskilancinsa ya k'aru da kagansa ka ga jinin sarauta,
murna wajen maimartaba da iyayensa ba a magana hatta kansu jama'ar gari sunyi murnar dawowarsa.
ba kamar abokinsa shahid da yayi missing d'insa sosai.
gidan sarautar hidima akayi sosai inda dukkan ma'aikatan gidan suka had'u adafa wancan asafke ad'aura wancan,
walima akayi ta azo agani hatta kansu talakawa sun ci sun sha,
Sumayya tun da tad'aura idonta akansa tace ai tayi miji ba zata auri kowaba sai shi ko da taje ma mahaifiyarta da maganar itama tayi murna sosai domin itama burin da take da shi kenan a rayuwarta inda tabata shawara akan taje tasanarwa dada.
sumayya ta d'auki shawarar da mahaifiyarta tabata dan haka tawuce tanufi 6angaren su maimartaba lokacin da tashiga d'akin dada zaune take saman kujera gefenta dama da haggu duk kuyangine suna ta mata hidima,
sumayya bisa kujerar da kaka take zaune taje tazauna tace ranki yadad'e 'yar tsohuwarmu Allah yak'ara miki tsawon kwana,
dariya dada tayi tace Ameen gimbiya ganinki da nayi haka nasan bakinki yana d'auke da magana,
sumayya murmushi tayi tace tabbas hakane ranki yadad'e akwai abinda yake tafe da ni.
kaka sallamar kuyanginta tayi duk suka fita sannan tatattara kallonta ga jikartata cike da kulawa tace ya ke sumayya inaso kifad'a min abinda yake tafe da ke nikuma indai baifi k'arfina zan taimaka miki.
sumayya duk'ar da kanta tayi cike da kunya tace dada daman akan yaya suhail ne,
murmushi kaka tayi jin an ambaci nagaban goshinta tace ina jinki me suhail d'in yayi?
sumayya tace babu abinda yayi saidai nice wlh dada tun tuni nakeson yaya suhail kuma ina tsoron intaresa da maganar dan nasan zai iya min wulak'anci saisa nace bari infara samunki da maganar wlh dada ina sonsa har cikin raina.
dada tunda sumayya tafara maganar kasa rufe baki tayi saboda jin dad'i, saida sumayya takai aya sannan dada tace masha Allah gaskiya naji dad'in labarin nan da kikazo dashi domin daman nima ina da burin hakan a raina ammah tunda har kikafurta da kanki toh ai shikenan.
sumayya kallon dada take cike da jin dad'i tace toh dada shikuma yaya suhail fa idan yace baya sona?
dada tace kikwantar da hankalinki zai ma soki domin babu yadda za'ayi nagida bai k'oshiba aba na waje ke dolene mane yasoki dan haka kikwantar da hankalinki shalele kamar kin zama matarsane kibari zamuyi maganar da shi da maimartaba.
sumayya cike da jin dad'i taduk'a takwashi gaisuwa tare da yin godia sannan tayi ma dada sallama tafito tanufi 6angarensu duk inda ta gifta tun kan ta ida isowa inda bayi da ma'aikata suke ake zubewa kwasar gaisuwa kowa tsoronsa kar tace yayi badaidaiba domin sunsan halin gimbiya sumayya da mahaifiyarta yi musu laifi abune maisauk'i, kowa yau yana mamakin yadda fuskarta take a sake sa6anin da dakullum take a d'aure.
dada ko da tasamu maimartaba da labarin shima yayi murna sosai inda yace zai gana da su gobe.
yarima suhail ne kwance saman makeken gadonsa inda shahid yake gefensa yana ta zuba masa surutu shi dai yarima daga uhm sai uhm-uhm bai cewa komai sai ma dannar wayarsa da yakeyi.
shahid ya k'ule sosai tsaki yaja yace kai fa matsalata da kai kenan sai ana yi maka magana kadinga share mutum kamar ba dakai akeba.
shuru yarima yayi yacigaba da dannar wayarsa takaici yakama shahid dan haka yafizge wayar, ganin haka yasa yarima yamaida idanunsa yalumshe.
shahid baiyi mamaki ba domin yasan halin abokin nasa tun suna yara.
knocking d'in k'ofar da akayine yasa shahid yabada izini da ashigo, wani dogarine yashigo tare da zubewa k'asa yana k'wasar gaisuwa shahid ne kawai ya amsa masa,
dogarin kansa yana k'asa yace Allah yaja da ran yarima mai jiran gado daman Maimartaba ne yake kiranka ya ce kasamesa a turaka,
yarima batare da yabud'e idonsaba yad'aga ma dogarin hannu alamun yatafi.
tashi dogarin yayi yace nabarku lafiya sannan yaficce daga d'akin.
shahid kallonsa yayi yana murmushi yace yau sarautar ta motsa kenan.....
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Sak'on gaisuwata agareku intelligent writer's Allah yabar k'aunaπ_
_My k'anwa janaf Allah yabar min keπ_
_*Wannan page d'in nakine Asma'u Yusuf Beji kiyi yadda kikeso da shi ina godia da kulawarki agareniπ*_
page 2⃣
Yarima suhail saida yayi kusan minti biyar yana a kwance sannan yabud'e idonsa ahankali yamik'e yasafka daga kan gadon, alkyabbarsa yajawo yasa batare da ya kalli shahid ba saida yataka yakusan zuwa k'ofa sannan yace kajirani bari indawo, shahid cike da tsokana yace toh ranka yadad'e
yarima baice komai ba yafita yana tafiyarsa ta k'asaita, dogarawan da suke zaune k'ofar d'akinsane suka zube suna kwasar gaisuwa sannan suka tashi domin sutake masa baya, yarima batare da ya kallesuba yad'aga musu hannu.
ganin haka yasa duk suka tsaya, yawuce yacigaba da tafiyarsa shi kad'ai duk inda yagifta kwasar gaisuwa akeyi, d'aga ma mutane hannu kawai yake idan da sabo sun saba da halin yarima ahaka har yashiga turakar mai martaba da mamakinsa yaga har da iyayensu a zaune,
waje yasamu gefen maimartaba yazauna a k'asa tare da kwasar gaisuwa wajensa da wajen iyayensu nan duk suka amsa masa,
maimartaba gyaran murya yayi yace toh Alhmdllh nasan duk zakuyi mamaki akan dalilin taraku nan da nayi ammah ba abun mamakibane alkhairine muke tafe da shi, ba akan kowaba sai akan yarima suhail,
maimartaba cigaba yayi da cewa domin na riga na yanke hukunci saboda nasan zai kar6i abinda nake tafe dashi na alkhairi, bakomai bane sai akan dubawa da cancantar da naga yayi dan haka naza6a maka matar aure bakowa bace face 'yar uwarka sumayya.
yarima gabansane yaji ya fad'i dasauri yad'ago kai yakalli maimartaba har ya bud'e baki zaiyi magana sai kuma yafasa dan haka yasunkuyar da kansa k'asa tare da runtse idonsa cike da takaicin za6in da maimartaba yayi masa, nan iyayensu sukaita murna suna tofa albarkacin bakinsu akan maganar.
shidai yarima saurarensu kawai yake,
muryar maimartaba ce yatsinkayo yana cewa toh kai uban gayyar bakace komai ba,
yarima suhail kamar ba zaiyi magana ba sai chan yace ranka yadad'e na amshi za6in da kayi min hannu bibbiyu Allah yak'ara tsawon rai.
cike da Jin dad'i maimartaba yace masha Allah, naji dad'i sosai tabbas nasan daman bazan samu matsala daga garekaba wlh ka faranta min nima Allah yakawo lokacin da zan faranta maka,
gaba d'ayansu sukace Ameen, yarima suhail nan yak'ara kwasar gaisuwa sannan yamik'e yafita
umman sumayya kamar tazuba ruwa k'asa tasha saboda murna domin ko bakomai tasan burinta ya kusan ciki ko da taje ma d'iyarta da labarin sumayya har da rawa tataka saboda murna dagudu tafita taje 6angarensu rahama tashaida mata, nan rahama tatayata murna.
yarima suhail yana komawa d'akinsa saman gadonsa yafad'a tare da lumshe idonsa cike da bak'in ciki domin an 6ata masa plan saboda shi baida burin yin aure a yanzu ko ma da zaiyi sumayya bata daga cikin irin tsarin matan da yake da burin aure saidai kawai zai amince ne saboda maimartaba domin baya iya jayayya da shi,
shahid ganin yarima acikin wannan mood d'in yasa bai tambayesa abinda yake damunsaba domin yasan ko da ma ya tambaya toh ba zai samu amsaba saidai idan shi yaso yafad'a masa toh dakansa zai basa labari dan haka yasharesa yacigaba da kallon ball d'insa.
yarima ya dad'e a kwance sannan daga baya yatashi yashige toilet.
bayan sallar isha'i yarima turakar iyayensa yaje inda yatadda mahaifiyarsa kishingid'e wata baiwarta tana mata tausa inda wasu biyu suke gefenta suna mata hira.
suhail yana shiga yatsaya bakin k'ofa ganinsa yasa duk suka zube suna kwasar gaisuwa sannan daga baya suka tashi suka fita suka basa wuri domin yagana da mahaifiyartasa,
sultana bilkisu tashi tayi daga kishingid'en da take nan suhail yataka yaje inda take yazauna sannan yagaishe da mahaifiyartasa cike da fara'a ta amsa masa.
suhail duk'ar da kansa yayi k'asa baice komai ba, ganin haka yasa mahaifiyarsa tace yarima me yake faruwane? kafad'a min damuwarka domin bakada wata uwar da tafini,
suhail d'ago fuskarsa yayi cike da damuwa yace ummi yanzu Sumayya ita zan aura?
murmurshi ummi tayi tace toh menene dan ka aureta ina ce 'yar uwarkace kuma ta cancanta da hakan,
dan haka kakwantar da hankalinka kakoya ma zuciyarka sonta insha Allahu zakuji dad'in zaman aurenku.
cike da damuwa suhail yace ammah ummi kinsan halin Sumayya ko kad'an halinmu bai zo d'ayaba,
ummi tace injiwa yace maka haka? duk abinda kaga tanayi harda yarinta, nidai burina kakwantar da hankalinka tunda ita kaga bata tada hankalintaba kakoya ma zuciyanka sonta insha Allahu zakuji dad'in zaman aurenku.
yarima suhail yace toh ummi nagode, nabarki lafiya.
ummi tace toh my son dan Allah kar katashi hankalinka tunda kaga an amince da aikinka yanzu haka mahaifinka ya sa afara maka ginin hospital d'inka.
murmurshi yarima yayi yace nagode ummi sannan yafita daga turakar yakoma tasa.
Bayan kwana biyu aka tsaida maganar aurensa da sumayya nan da wata biyu masu zuwa, yarima yaso asa lokacin dayawa ammah maimartaba yace a'a, ,sumayya farin ciki tayi sosai agaban kowa take nuna murnarta,
yarima ganin dagaske ake yasa yad'an saki jikinsa har suna d'an ta6a hira da sumayya shima d'in kafin yayi magana d'aya tayi biyar, in ko kaga sunyi waya toh itace takirasa shima daga gaisuwa yake kashe wayarsa.
Bayan wata biyu akasha bikkunsu anyi shagali sosai ak'allah saida akayi events kusan guda biyar ammah dakyar aka samu yarima suhail yaje d'aya daga ciki shima saida ummi tasa baki, ammah sauran duk k'in zuwa yayi k'arshe idan yaga za'a takurasa sai yakashe wayoyinsa yace kar abari kowa yashigo sashensa,
ranar asabar aka d'aura aure, auren da dubban mutane daga nahiya dadama suka hallara,
amarya ta sha kyau har ta gaji, inda amarya tatare a part d'in yarima da aka fitar da shi a cikin gidan sarauta, k'arshen gata an nuna mata babu abinda ba a zuba masu na amfani ba.
kowa yazo sai ya yaba tsarin gidan domin babu wanda zai ce acikin gidan sarautane saboda part d'in yarima antsarasa kamar a turai inda aka fidda ma sumayya 6angarenta sai na yarima sai wani part d'in da aka fara ginawa aka aje sai kuma part na ma'aikata da bayinsu maza da mata.
da daddare saida shahid yayi dagaske sannan yasamu yarima suhail yayi wanka yashirya suka fito suka rakasa gidansa.
suna ta tsokanarsa shidai yayi shuru yakyalesu saboda wani irin haushi da yakeji, hatta su kansu haushinsu yakeji tunda su suka matsa masa sai yaje.
saida suka rakasa har part d'in amaryarsa sannan sukayi masa sallama suka tafi.
yarima suhail 6angarensa yabud'e da mamakinsa yaga dogarawansa zaune a k'asa suna ganinsa suka zube suna kwasar gaisuwa, yarima suhail batare da ya amsaba yace kun iya tafiya ,
k'ara kwasar gaisuwa sukayi sukace toh ranka yadad'e sannan sukace atashi lafiya sai suka tashi suka fita
bedroom d'insa yashiga komai na ciki very need da mamaki yakalli yadda aka shimfid'a masa farin bedsheet mai kyau a saman gadonsa d'auke kansa yayi yawuce yashiga toilet yawatsa ruwa , bayan ya fito yayi shirin kwanciyarsa yahaye gadonsa.
A 6angaren gimbiya sumayya bayan ta gama shirinta su jakkadiya suka take mata baya zuwa turakar yarima, da sallamarsu suka shiga ganin baya parlour yasa suka kwank'wasa masa bedroom,
yarima da yake kwance yabada izinin ashigo, da mamaki yake kallonsu sumayya da suka shigo, nan su jakkadiya suka zube k'asa suna kwasan gaisuwa, ita dai sumayya zuba masa ido tayi tana kallonsa cike da son mijinta,
haydar bai damu da kallon da take masaba yace lafiya kukazo man d'aki?
jakadiya da take durk'ushe tace ranka yadad'e yarima mai jiran gado daman dada ce tace mukawo maka amarya,
yarima suhail shuru yayi baice komaina yamaida idonsa yalumshe.
ganin haka yasa su jakadiya sukace mun barku lafiya gimbiya da yarima Allah yaja da ranku atashi lfy.
Gimbiya sumayya tace idan kun fita sai kurufe mana k'ofan,
yarima suhail yana jinta mamakine yakamasa domin bai ta6a ganin amarya hakaba.
suna fita sumayya tatako ta iso bakin gadon tazauna gefen da yarima yake kwance, suhail batare da ya bud'e idonsaba yace kije kid'auro alwallah,
sumayya turo baki tayi sannan tatashi tashiga toilet d'insa tad'auro alwallah,
lokacin da tafito yarima yana shimfid'a darduma nan yajasu sallah raka'a biyu sukayi sannan yakama kanta yayi mata addu'a.
bayan ya gama yayi mata tambayoyi akan addininta baiyi mamaki ba da yaga bakomai take iya basa amsaba, wata amsarma ba daidai take basaba nan ya Ida tsurewa da lamarin sumayya ammah kuma sai yashare, mik'ewa yayi yanufi saman gadonsa yabarta nan saida yakwanta sannan yace ga nama nan idan zaki ci.
haushine yakama sumayya ganin yadda takejin labari wajen friends d'inta yadda mazajensu suka nuna musu tattalin so a daren aurensu ammah ita ba hakaba, cikin ranta tace lallai yarima halinsa sai shi.
tashi tayi itama taje saman gadon takwanta bayansa saida sukayi kusan minti goma ahaka ammah sumayya taga yarima bai da alaman nemanta dan haka tarungumesa ta baya,
yarima shareta yayi, ganin haka yasa sumayya tajuyosa tare da kwanciya saman jikinsa, yarima bud'e idanuwansa yayi da suke lumshe yawurga mata harara yace ke bakida kunya?
sumayya turo baki tayi tace yarima yau fa daren amarcinmune ammah shine kake shirin yin bacci kabarni hannu takai tana shafa jikinsa.
yarima da mamaki ya gama cikasa kasa komai yayi, jin hannunta yayi yana yawo cikin jikinsa, dasauri yarik'e hannun yace ke bakida kunya?
sumayya tace ammah ai naga ba abun kunya bane tunda munyi aure,
bakinta takai cikin nasa tana kissing d'insa cikin wani irin salo nan da nan yarima yafita hayyacinsa ya'aje sarautarsa gefe yabiye mata suka sha amarcinsu.
yayi mamaki sosai ganin yadda sumayya take zak'ewa babu alamun tsoro atare da ita,
a yadda yasameta bai kawo ma ransa komai ba gudun kar zargi yashiga tsakaninsu dan haka dayasamu nutsuwa janye jikinsa yayi yaje yayi wanka sannan yadawo yayaye bedsheet d'in yayi yakwanta tare da juya mata baya,
sumayya ma tashi tayi taje tayi wanka sannan tadawo bayansa yakwanta tare da rungumarsa ta baya,
da asuba yarima har yadawo masallaci ammah sumayya bata tashi tayi sallah ba, saida yayi dagaske sannan yasamu sumayya tatashi tayi sallah tana ta k'unk'uninta, komawa yayi yakwanta yana kallonta sallarma shaf-shaf tayita ko addu'a bata tsaya yiba tahaye gadon.
dasafe jakkadiya ce tatashesu nan tashigo takwashi gaisuwa sannan tad'auki bedsheet d'in tafita.
turakar dada taje, tun da dada tahangota take fara'a jakkadiya duk'ewa tayi takwashi gaisuwa sannan tace ranki yadad'e ga zanen gadon,
dada tace masha Allah bud'e mugani ko da jakkadiya tabud'e babu komai a jikinsa nan hankalin dada yatashi tace nashiga ukka ya akayi haka kar dai ace yarinyarnan ba budurwa bace.
jakkadiya duk'ar da kanta tayi tace ranki yadad'e ai ita mace budurwa ba dole sai anga jiniba ake gane budurwace wasu basu jinin budulci,
dogon numfashi dada taja tace hakane shikenan yanzu aje awankesa amaidasa ma'ajinsa ammah naso ace kowa ya shaida.
kowa na gidan kasa kunne yayi yaji ana gud'a ammah shuru kuma kowa tsoron tambaya yakeyi, kasancewar al'adarsuce duk amaryar da aka kowa idan budurwace da anga jinin ake ganewa nan za'a d'auki zanen gadon ayi ta yawo ana gwadawa daganan sarki zai bada shanuwa da rago ayanka ma amarya.
yarima suhail har yagama shirinsa ammah gimbiya sumayya tana kwance tana kwasar baccinta haushi ne yakamasa yaja tsaki yace mutum kamar kasa sai bacci, da mugunta yakai mata bugu, firgit tayi tafarka daga baccin
haushi ne yakamata ganin yarima tsaye, d'aure fuska tayi tace haba yarima ya za'ai katasheni bayan jiya kaine kahana ni bacci, gaskiya kadaina domin idan ina bacci ba'a tashina.
yarima da mamaki yake kallonta jin tace shi yahanata bacci bayan itace takawo kanta,
tashi tayi tad'auko alkyabbarta tasaka sannan taficce tabarmasa d'aki,
tsaki yarima yaja sannan yacigaba da abinda yake,
bayan ya gama yafito parlour yatarar da anshirya masa breakfast dogarawansa suna ganinsa suka zube suka kwashi gaisuwa sannan d'aya daga cikinsu yayi serving d'insa,
kad'an yaci sannan yatashi nan suka rufa masa baya sunacewa takawarka lafiya yarima.
tsayawa yayi batare da ya juyoba kamar ba zaiyi maganaba sai kuma yace kuje kawai zan nemeki,
su dukansa sukace angaisheka yarima umurninka muke cikawa Allah yatsare mana kai mun barka lafiya.
daganan yawuce yacigaba da tafiyarsa shi kad'ai duk inda yagifta kwasar gaisuwa ake ahaka har yazo 6angaren gimbiya ko da yashigo parlour saida ma'aikatanta sukayita kwasar gaisuwa ko inda suke bai kallaba yawuce direct bedroom d'inta,
lokacin gimbiya sumayya tana zaune bayinta suna shiryata, bud'e k'ofar da akayine yasa duk suka maida hankalinsu domin suga mai shigowa ganin yarimane yasa suka zube gaba d'ayansu suka kwashi gaisuwa sannan suka mik'e zasu fita
gimbiya sumayya ce tace ina zakuje batare da kun gama shiryaniba,
yarima kallonta yake cike da mamaki sannan yanuna musu k'ofa dasauri dukansu suka fita har suna tuntu6e.
takowa yayi cikin takunsa na k'asaita ya iso bakin gadon, gimbiya sumayya tace haba yarima ya zaka korar minsu alhali basu gama shiryaniba,
zama yarima yayi kusa da ita batare da ya kalletaba yace ke ba zaki iya shiryawaba har sai sun shiryaki?
sumayya ta6e baki tayi tace ammah ai tun ina gaban iyayena su suke min kwalliya, banza yarima yayi yakyaleta dan haka taci gaba da shirinta.
banza yarima yayi yakyaleta.
bayan ta gama kiran jakkadiya tayi tace akawo mata breakfast d'inta a nan, cikin minti biyar ancika mata gabanta da abinci da kayan marmari iri-iri
nan tazauna zata ci kallon yarima tayi tace kaifa ba zakaciba,
yarima batare da ya kalletaba yace no kici kiyi sauri kigama muje mugaishe da su maimartaba,
gimbiya sumayya tace tun yanzu?
yarima bai tanka mataba,
ganin haka yasa tacigaba da breakfast d'inta domin tasan halin mutumin nata magana tsada take masa......
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
?ππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_*Sak'on gaisuwata agareku My Haleema H.A.S nd mummy Zillππ*_
_Wannan page d'in nakune nabaku shi a kyauta my fan'sπ_
page 3⃣
bayan ta gama d'auko alkyabbarta tayi tasaka sannan suka jera ita da yarima suka fito, a k'asa suke tafiya a jere, kuyangin gimbiya suka take musu baya ahaka har suka isa fada nan mutane suka dinga kwasar gaisuwa, d'aga musu hannu kawai yarima yakeyi har suka isa gaban maimartaba dasauri dogarawa sukazo suka kare su yarima daga ganin mutane suna cewa Allah yataimaki yarima da gimbiya azauna lafiya, har saida suka tabbatar da yarima da gimbiya sun zauna sannan suka matsa nan su yarima suka kwashi gaisuwa wajen sarki nan fadawa suka d'auka, sarki ya amsa muku yarima da gimbiya, sarki yana godia yarima mai jiran gado ku ma angaisheku.
sannan yarima yatashi yaje kujerar da take kusa da sarki yazauna, ita dai gimbiya tana tsugunne a k'asa sai yatsina take tana kallon mutane a wulak'ance.
maimartaba ne yad'auko wata alkyabba maikyau da tsada yamik'a ma gimbiya sumayya hannu biyu gimbiya tasa takar6a tare da yin godia sannan tamik'a ma jakkadiya, jakkadiya tazube gaban sarki tace ranka yadad'e gimbiya tana k'ara godia Allah yaja da ran sarki mai adalci sarkin sarakai,
gyad'a kai sarki yayi nan fadawa gaba d'ayansu suka d'auka angaisheki gimbiya sarki ya ji godiar ki.
nan sarki yayi musu nasiha tare da yi musu addu'an zaman lafiya, sannan suka k'ara kwasar gaisuwa suka tashi suka fito, cikin gida suka shiga turakar dada,
nan suka gaisheta itama tayi ma gimbiya kyauta sannan suka wuce 6angaren ummi suka gaisheta itama kyauta tayi ma gimbiya sannan daganan sukaje 6angaren umman sumayya suka gaisa daga nan suka koma 6angarensu
suna shiga yarima yanufi hanyar zuwa 6angarensa ganin gimbiya tana niyar binsa yasa yadakata da tafiyar batare da ya kalletaba yace zaki iya tafiya 6angarenki domin yanzu inason inhuta bai jira jin abinda zata ce ba yawuce part d'insa.
Gimbiya sumayya tsaye tayi takaici duk ya cikata ganin yadda yarima yadizgata gaban bayinta, tsawa tadaka musu tace suwuce subata waje dasauri duk suka bar wajen,
nan gimbiya tanufi part d'inta cike da jin haushi.
haka sukayi sati d'aya suna shan amarcinsu tun yarima bai kulata daga baya sumayya saida tasan yadda tayi yarima suhail yad'an sake mata, ammah idan yana jin 'yan miskilancin ko sarautar takad'a masa toh ko kallon inda take bata yi.
bayan sati guda gimbiya sumayya ce kishingid'e a parlourn ta inda bayinta suke zagaye da ita wasu suna mata tausa wasu fifita, d'aya tana karanta mata labari, wayartace tashiga ruri baiwar da take rik'e da wayoyintane tamik'a mata, cike da Jin dad'i sumayya tayi picking d'in wayar ko sallama batayiba tace haba zinat ai ni fushi nake da ke wai har ayi aurene bakya garin,
daga chan 6angaren Zinat tace toh sarkin k'orafi yanzu dai gani a k'ofar gidanki dogarawa sun hanani shiga kituro a shigo da ni,
cike da jin dad'i sumayya tace yanzu ko zan aiko, kallon d'aya daga cikin bayinta tayi ta yamitse fuska tace ke jeki waje kishigo min da bak'uwata,
dasauri tamik'e tace angama ranki yadad'e
batafi minti biyar da fitaba sai gasu sun shigo da zinat, sumayya tashi tayi daga kishingid'en da take tace oyoyoo k'awata takaina, nan bayi suka zube suka kwashi gaisuwa wajen wadda aka kira da zinat sai yamutsa fuska take tana taunar chewing gum tazauna saman kujera, nan gimbiya sumayya takori duka bayin daga d'akin,
gimbiya sumayya kusa da ita takoma tazauna kafin kace mi ancika gaban zinat da kayan ciye-ciye da na shaye-shaye, sumayya cike da farin ciki tace k'awata kenan ai ban d'auka zan ganki a yanzu ba,
zinat kur6an ruwan inibi tayi sannan ta aje cup d'in tace wlh jiya nadawo garin shine nace ba zan fad'a mikiba surprise kawai zan baki yau.
.
murmushi Sumayya tayi tace kin ko kyauta wlh, na ma d'auka sai kin gama hutawa zaki dawo domin na sanki da son tafiya kihuta, zinat tace ai saboda ke nadawo amarya kinsha k'amshi kinga ko yadda kika koma?
murmushin jin dad'i gimbiya sumayya tayi tace ya nakoma dear?
zinat tace ai kin fito a gimbiyarki ta ainahi ke ni bani insha kifad'a min yadda kuke zaune da wannan miskilin mijin naki.
sumayya gyara zamanta tayi tace ai lafiya lou miskilanci kau saidai abinda yayi gaba, zinat tace ke ya batun first night d'inku,
dariya gimbiya sumayya tayi tace ai babu abinda yagane game da hakan kinsan nayi amfani da magungunan da kikasa aka had'a min wlh har tausayi yabani ganin bai gane komai ba.
ta6e baki zinat tayi tace ke inbanda abinki wa yace miki ana tausayin maza indai kina lalla6a miji ai sai yarainaki, shawarace zan baki daga inda miji yafara d'aga miki murya ke kinuna masa kinfi sa hauka,
sannan ba kowane lokaci zaki dinga ba mijinki kankiba saboda idan kika saba masa da haka toh sai kin gunduresa yaji ya gaji da ke daga k'arshema sai kiga kishiya
zaro ido sumayya tayi tace kishiya kuma? zinat gyad'a kai tayi tace eh man ai wlh namiji ba a basa amana ke nifa saboda tsoron halin maza yasa nakasa aure nake cin karena babu babbaka dukiya ce natara bakin gwargwado a lokacin da kuma naji ina buk'atar namiji ga mazanan birjit sai na za6a, inma macen nake buk'ata kema kin sanni.
dariya sumayya tayi tace hakane k'awata wlh kin kawo shawara mai kyau, ke nima fa sonake inga natara dukiya dan ban had'a kud'i da komai ba tunda ga mulki ga miji kinga dukiya yarage dan haka business zan fara. saidai anya zamu kwashe lafiya da yarima?
harararta zinat tayi tace kefa matsalata da ke wani lokacin baki da ganewa ammah asannu zan ganar da ke yadda zaki fahimta, ammah nagargad'eki da lallashin miji bare ma wannan mijin naki idan yashareki kema kifita harkarsa ke da nice da nasan yadda zan juyasa yakoma a tafin hannuna,
gimbiya sumayya tace hmm ba dai yarima ba anya akwai macen da zata iya juyasa?
zinat tace kefa matsalata da ke kenan bakida ganewa, kedai kigwada kigani dakanki zaki bani labari, yanzu dai taso mushiga daga ciki.
mik'ewa sumayya tayi tana dariya zinat tana binta a baya suka shige bedroom,
a ranar haka zinat tawuni gidan gimbiya sumayya tana k'imsa mata makirci iri-iri har saida taga gimbiya sumayya ta hau ta zauna sannan tabarta.
Tun daga ranar gimbiya sumayya tadaina shiga sabgar yarima shima shareta yayi yacigaba da hidimar gabansa,
yarima tun bai damuwa har abun yazo yafara damunsa yanzu tsawon wata d'aya da aurensu tun satin farko rabonsa da gimbiya domin ko d'akinsa bata zuwa.
yau da dare kasa daurewa yayi dan haka yatashi yasaka alkyabbarsa yafito yanufi 6angaren gimbiya sumayya, da key d'insa yabud'e direct bedroom d'inta yashiga chan tsakiyar gado yahangota ta baje sai baccinta take ahankali yataka yaje yahau saman gadon.
gimbiya sumayya da take bacci jin ana shafata yasa tafarka, da mamaki take kallon yarima, chan kuma sai tad'aure fuska tace lafiya?
yarima cigaba yayi da abinda yake kamar ba zaiyi magana ba sai kuma chan yace sumayya yanzu saboda Allah hakan da kike min kina ganin kin kyauta? hak'k'ina nazo kar6a,
gimbiya sumayya janye idonta tayi daga kallonsa cikin ranta tana jin dad'in shawarar da k'awarta tabata ganin yau dakansa ya aje girman kan yazo d'akinta,
ganin yarima suhail yana shirin rikitata yasa tajanye jikinta gefe tace haba dan Allah yarima wai menene haka nifa a gajiye nake.
da mamaki yarima yake kallonta yace haba sumayya saikace wadda tayi wani aiki nidai yanzu kibari inyi inyaso daga baya sai kiyita baccinki.
gimbiya sumayya komawa tayi takwanta tare da juya masa baya tace ni ba zan iyaba gaskiya, yarima binta yayi yana lallashi dakyar ta amince masa shima saida taita masa k'orafin ta gaji kan dole a k'arshe yahak'ura yabarta batare da ya ida samun nutsuwaba,
toilet d'inta yashiga yayi wanka sannan yadawo yakwanta tare da juya mata baya cike da mamakin yadda sumayya tasauya hali .
gimbiya sumayya ko murna takeyi ganin ta d'an ci nasara har Yarima suhail ya zo d'akinta yau, kuma ya aje girman kai da sarautar ya lallasheta.
Tun daga lokacin yarima shi yake biyota d'akinta ko da ace ya yi mata wulak'anci a wani wajen ita kuma sai ya nemeta take ramawa sai ya-yi dagaske yake samun hak'insa a wajenta ahaka suka haura wata shidda ammah ko 6atan wata bata ta6a yi ba,
dada ta fi kowa damuwa domin tisata gaba take a d'aki tana tambayarta ko akwai abinda take sha ita dai gimbiya a'a take cewa, dada tace a'a gimbiya indai akwai abinda kikeyi, gimbiya saidai tayi dariya tace dada inda ina yin wani abu ai da kun gane, dada saidai tace toh Allah yakawo.
ko da yarima yazo yagaishe da dada bayan sun gaisa dada tace yarima wai har yau ba wani labari?
yarima shuru yayi saida yayi kusan minti biyu sannan yace dada labarin me kuma?
dada tace hmm ciki mana.
murmurshi kawai yayi yace dada ai haihuwa lokacine, idan da darabo zamuyi.
dada tace toh Allah yakawo mai albarka yarima yace Ameen.
sannan yarima yatashi yafita dogarawansa da suke tsaye bakin k'ofa suna ganin ya fito nan suka fara masa kirari yana gaba suna biye da shi tun kan ya isa wajen jerin motocinsa da yasa aka tanadar masa dan yafita dasauri aka bud'e masa dank'areriyar motarsa da take tsakiya nan yashiga baya yahakimce sannan dogarawa suka shiga sauran motocin akasa tashi a tsaka nan aka kama hanya.
asibitoci yaje yakai ziyara yaduba marassa lfy yayi musu kyauta sannan yawuce gidan marayuwa yabada kayan abinci kowa yaji dad'in ziyarar da yakawo domin daman halinsane kyauta,
daga nan suka kama hanyar gida, ko da suka isa bai shigaba saida yatsaya yasa aka tara ma'aikatansa yaraba masu kud'i nan suka zube suna ta godia daganan yawuce part d'insa yana shiga yacire kayan jikansa yafad'a toilet yayi wanka, bayan ya shirya saman gado yafad'a yana hutawa bud'e k'ofar da akayine yasa yabud'e idonsa dayake a lumshe,
ganin gimbiya sumayya ce yasa da mamaki yakalleta domin yasan bata shigowa d'akinsa sai idan tana buk'atar wani abu, maida idanunsa yayi yalumshe,
takowa tayi tahau saman gadon tazauna gefensa ganin baida niyar bud'e ido yasa tace ashe har kadawo tun d'azun nake aikowa adubomin idan kana nan,
yarima batare da ya bud'e idanunsaba yace ya akayi kika shigo min d'aki ba'a fad'a miki nace kar wanda yashigo ba? gimbiya sumayya murmushi tayi tace yanzu dan zan shigo d'akinka har sai anbani izini a matsayina na matarka?
banza yarima yayi yakyaleta, ganin baida niyar tanka mata yasa takwanta a jikinsa ta d'auka zai gwalisheta ammah taji ya yi shuru baice komai ba, dan haka takai hannu tana shafa fuskarsa daga nan tafara kissing d'insa daman abu ga mai nema nan yarima yabiye mata,
ya yi mamaki yadda yau bata hanasa kantaba domin yasan hali da ya fara zata fara cewa ta gaji, ammah yau saida yagaji dan kansa sannan yabarta.
rungume take a jikinsa cikin shagwa6a tace my sweetheart dan Allah inaso kabani 2 million,
yarima baiyi mamakin jin hakan daga garetaba, domin daman yasan za'a rina ba zata ta6a bashi kantaba sai da dalili,
bud'e idonsa yayi yasafkesu akan fuskarta kamar ba zaiyi magana ba sai kuma chan yace mezakiyi da kud'i?
Sumayya batare da damuwaba tace business nakeso inyi kaga zaman hakanan ai baya yuwuwa zamu had'a jari da k'awata zinat zata dinga zuwa tana saro mana kaya, zamu bud'e babban boutique a chan Abuja.
yarima tunda tafara bayanin yatsareta da ido har takai aya sannan yace yanzu ke bakiji kunya ba kice zakiyi kasuwanci akwai abinda narageki da shi ne?
gimbiya Sumayya d'aure fuska tayi tace kai fa matsalata da kai kenan to shi business dole sai marar wadata yakeyinsa?
yarima janye jikinsa yayi yace idan ke bakida hankali toh ni ina da shi kuma ba zakiyi ba, yana gama fad'in haka yawuce yashige toilet domin yayi wanka.
gimbiya Sumayya binsa tayi da kallo cike da takaici tace tsiyata da kai bakasan arzik'iba saida nagama baka kaina sannan kanemi kawulak'antani toh wlh baka isa kahananiba dan haka muzuba mugani,
tana gama fad'in haka tajanyo kayanta tasaka tatashi fuuuuu tafita tabar d'akin.
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_*~Sak'on gaisuwata agareki Mummyn khalil fatana Allah yabaki lafiya, Allah yasa zakkar jikine~*_
_kuna ina Kuzo yau ranar takuce wlh ina ji daku har cikin zuciyana *My k'anwa Safiyya Aliyu, Mrs Abubakar, Ma zeenart, Hafsat Kanty, Cool Angel, Chubby, Asma'u Yusuf Beji, Husnah, Mugirat Musa, Maman Sadiq, My k'anwa Khairyy, Maman Haidar, Hadiza Abubakar, Maman Amira, Kubcy Auwal, Dr Xeey Xeey, Aisha Baba Audu, ummu walid nd Abdul, Maman khaleesat, Sadiya Abubakar, Billy....* da ma sauran wad'anda ban lissafoba, wannan page d'in nabakushi Allah yabar k'aunaπ_
page 4⃣
tana fita daga d'akin yarima part d'inta tawuce ko ta kan su jakkadiya batabiba da suke tsugunne suna ta kwasar gaisuwa wucewa tayi tashige bedroom d'inta, wayarta tad'auka takira zinat, zagaye d'akin tashiga yi tak'agara zinat tad'aga wayar ammah har tatsinke bata d'agaba, tsaki gimbiya taja tace itafa matsalata da ita ayi ta kiranta sai taga gama take d'auka,
k'ara Kiranta tayi bugu biyu tad'aga
ko gaisawa basuyiba tace zinat kinajin wancan d'an rainin hankalin wai bazai barni inyi business d'inba
zinat cikin tsawa tace what! shi har ya isa yahanaki kuma kihanu? gambiya tace hmm yoh ke kina tunanin ma zan hanu?
zinat dariya tayi daga chan 6angaren tace wlh innice yanemi yaraina min hankali tuni zan nuna masa iyakarsa ke ak'arshema zan iya kashe auren tunda dama dashi yake tak'ama,
gimbiya zaro ido tayi kamar tana gaban zinat tace kirufa min asiri ai wlh ba zan iya rabuwa da shi ba saidai nasan ta inda zan 6ullo masa kibarni da shi.
zinat tace toh shikenan nidai ina jira cikin week d'innan inga alert saboda so nake inje ingama komai dawuri indawo,
gimbiya sumayya tace toh shikenan kar kidamu, nan sukayi bankwana.
suna gama wayar gimbiya ummanta takira saida takusan tsinkewa sannan sultana sadiya tad'aga da sallamarta, sumayya ko gaisheta batayiba tace ummana wlh yarima baida mutunci
sultana sadiya a rikice tace nashiga ukku shalele miyake faruwa ne? wlh indai wani cin mutuncin yayi miki zan rufe ido inci masa mutunci shima daga shi har mahaifiyartasa a tafin hannuna suke, kifad'a min abinda yake faruwa.
Sumayya cike da jin dad'in ganin yadda mahaifiyarta take kula da ita, sannan tabata labarin business d'in da takeso tayi da yadda suka kwashe da yarima.
sultana sadiya tace ai bai isaba Indai ina raye ba zaki ta6a yin kukaba ammah kafin ind'au mataki da hannuna kije kifara samun dada kuyi maganar domin nasan ita zata fahimceki sosai inko ta yarda nasan yarima ma zai amince ko da ace baya so.
cike da jin dad'i sumayya tace hakafa za'ayi ummana wlh saisa nake k'ara sonki saboda duk abinda nake so kema kina sonsa.
'yar dariya sultana tayi tace idan ban so abinda kikeso ba toh nawa zan so? kekad'ai fa ce namallaka, ke nifa ba ma wannan ba wai har yanzu ba wani bayani?
sumayya ta fahimci inda mahaifiyarta tadosa ammah sai tanuna bata fahimtaba tace ummah wane bayani kuma?
ummanta tace ke gidanku ni zakiyi ma kwana-kwana? ke ni ban yarda da keba anya bakiyin family planning?
dariya sumayya tayi tace ni babu abinda nakeyi kuma nima insha Allahu sai na shekara biyar sannan zan haihu.
sultana sadiya tace nashiga ukku ke gidanku wa yace miki ana gudun haihuwa a gidan sarauta?
gimbiya cikin shagwa6a tace ummah kema fa saida kika dad'e sannan kika haihu.
ummah tace toh ai nima ba dan ban soba Allah ne bai baniba a lokacin, inma kinsan kina yin wani planning toh wlh kidaina,
gimbiya tace nidai yanzu dai shikenan ummah tunda nace miki babu abinda nake ai sai kibar maganar, ni nafi buk'atar business d'innan bari dai inje muyi magana da dada, ummah ba dai dan ta yardaba tace toh shikenan sai najiki,
gimbiya tana gama wayar wanka tashiga tayi bayan ta fito shiryawa tayi cikin shigarta gwanin sha'awa sannan tafito nan kuyangi da bayinta suka take mata baya har suka shiga turakar sarki,
lokacin da tashiga parlour dada tana kishingid'e ana mata tausa, nan duk ma'aikatan dada suka gaisheta tare da yi mata kirari, tana yatsina ta amsa musu, nan bayinta suma suka zube suka kwashi gaisuwa a wajen dada, gimbiya zama tayi gefen dada tagaisheta,
dada cike da fara'a ta amsamata tace 'yar albarka meyake tafe da ke Allah yasa ba wannan sarkin 'yan iyayin bane yayimiki wani abu.
gimbiya k'ara 6ata fuska tayi tace dada kamar kau kin sani wlh k'ararsa nakawo,
dada tace oh ni Asma'u yanzu yaron nan nake ganinsa miskili ashe shima ya iya mugunta.
yanayin yadda dada tayi maganar yaso yabata dariya, gimbiya kallon bayin tayi da suke tsugenne tace dallah kutashi kuba mutane waje kunzo kun saki kunnawa kuna saurarenmu.
dasauri suka rausaya gaba d'ayansu sukace Allah yahuci zuciyar gimbiya mun barku lafiya, sannan suka tashi suka fita.
dada kallonta take cike da mamaki tace sumayya ashe har yanzu kina nan da halinki na wulak'anci?
gimbiya murmushi tayi tace toh ai sune basusan suba mutane waje suyi maganaba sai suwani yi zaune kuma idan nasakar musu fuska sai surainani.
dada sakin baki tayi tana kallonta har saida takai aya sannan dada tace sumayya na haneki da wannan halin ya kamata kizauna da kowa lafiya domin wata rana mijinki shi zai kasance sarkin garin nan.
murmushi sumayya tayi tace toh ranki yadad'e tuba nake, murmushi dada tayi irin nasu na manya sannan tace ina saurarenki me mijin naki yayi miki?
gimbiya gyara zamanta tayi sannan tace dada daman kasuwanci nakeso inyi shine natambayi yarima yabani jari sai yahanani kuma wai ba zanyiba.
murmushi dada tayi tace in banda abinki sumayya me kika nema kika rasa a gidan nan? kuma na tabbata babu abinda zaki nema wajen yarima kirasa domin nasansa da kyauta.
sumayya 6ata fuska tayi kamar zatayi kuka tace dada nima inaso indinga cin gashin kaina kuma fa k'awatace zata dinga kular mana da kayan ba sosai zan dinga zuwaba ita zata dinga yi mana komai.
dada ganin sumayya ta 6ata fuska yasa taji babu dad'i domin tana son jikartata sosai jininsu ya zo d'aya dan haka tace kikwantar da hankalinki yanzu kiramin shi awaya.
yarima bayan ya fito wanka yashirya cikin shigarsa ta alfarma ya yi kyau sosai wayansa yad'auko yakira shahid inda yashaida masa yazo suje yarakasa gidan gona akwai abinda yakeso yayi a chan.
shahid yace to shikenan ranka yadad'e daman yanzu haka zan fito daga fada sai kafito muhad'e,
yarima yace ohk sai nafito.
cike da k'asaita yake tafiya duk inda yagifta kallonsa ake cike da sha'awa, ana kwasar gaisuwa yarima yau 'yan jin kan suna a kansa ko hannunma basu samu matsayin da yad'aga musuba
lokacin da yafito dogawara duk suka taso d'aga musu hannu yayi alamun a'a har ya kusan kaiwa wajen motar sai yaji wayarsa tana ringing tsayawa yayi daga tafiyar da yake yad'auko wayar ganin mai kiransa kamar ba zai d'agaba har saida takusan tsinkewa sannan yad'aga batare da ya ce komai ba yakanga a kunnensa.
gimbiya sumayya jin baiyi maganaba yasa tamik'a ma dada tace gashi kuyi magana,
dada tana kangawa a kunnenta tace toh sarkin miskilanci bakaji ma zaka iya magana,
yarima jin muryar dada da yayi yasa yad'anyi murmushi yace toh me zan ce?
dada tace eh babu fa abinda zakace yanzu dai kazo ina son ganinka.
yarima yana jin haka yasan da wata a k'asa musamman ma da yaga da wayar gimbiya aka kirasa,
dada tace toh ko nima wahalar yimin maganar ake ji? murmushi yarima yayi yace dada yanzu fita zanyi kibari sai nadawo sai muyi maganar.
dada tace sannu babana toh idan ni kana ganin ka rainani toh sai inkira ubanka shi da ya isa da kai sai yasa kazo.
yarima yace shikenan kakus gani nan zuwa ai abun bai kai ga hakaba,
dada tace ina saurarenka, yarima batare da yabata amsaba yakashe wayarsa kallon shahid yayi da yake tsaye yana kallonsa yace shahid bari inje wajen waccen tsohuwar tana nemana tun kan tajamin sharri wajen daddy.
dariya shahid yayi yace toh ranka yadad'e sai ka fito.
yarima ko da yashiga baiyi mamakin ganin gimbiya sumayya ba dan haka zama yayi bisa kujerar da take opposite d'in wadda su dada suke a bisa, nan yagaishe da dada cike da girmamawa itama ta amsa masa.
daga nan shuru yabiyo baya chan sai dada tace suhail kaban mamaki wlh,
yarima kallonta yake da mamaki ammah baice komai ba.
dada batayi mamakin shurun da yayi ba saboda tasan halinsa dan haka tacigaba da cewa saboda Allah dan matarka tanason tayi kasuwanci sai kahanata?
yarima harara yawurga ma sumayya sannan yamaida kallonsa ga kaka .
kaka tace kai tambayarka nake shine kayi min shuru?
yarima cikin rashin damuwa yace dada ai nad'auka ta baki amsar abinda nace mata.
dada rik'e baki tayi tace wai kai wane irin mutum ne amsar ma bakaji zaka iya bani?
yarima shuru yayi kamar ba zaiyi magana ba chan kuma sai yace toh ai nace mata ban aminceba saboda babu abinda narageta da shi kuma indai kud'ine zan iya bata ammah ban yarda tayi kasuwanci ba ai sai taja mutuncina yazube a idanun mutane, daka ma gimbiya tsawa yayi yace ke ba haka nace mikiba? ??
Gimbiya ta tsorata da tsawar da yayi mata ammah sai tadake tad'auke kanta daga kallonsa.
dada ta6a hannu tashiga yi tace nashiga ukku yanzu a gabana kake mata tsawa ai da had'emu kayi ni da ita kadokemu sai inga kamar zai fi maka sauk'i.
yarima yace Allah yabaki hak'uri ammah dai yakamata kiduba kiga maganar nan bai daceba ace tadinga yawo tana chakud'a cikin maza,
kaka kallon sumayya tayi da taci face sannan tamaida kallonta ga yarima tace ai tace ba sosai zata dinga zuwaba abokiyar kasuwancin ce zata dinga kula da komai dan haka inaso kabata kud'in inkuma baka iya bata sai inkira 'ya'yana su subayar tunda su na isa da su.
Yarima baice komai ba yad'auko cheque yacike mata yamik'a mata yace gashinan kuma duk abinda yafaru kiyi kuka da kanki.
dada tace insha Allahu babu abinda zai faru sai alkhairi, kuma dan bak'in ciki baka ji zaka iya bata cash, yarima suhail mik'ewa yayi yace dada so kike kijasa min ciwon kai, bari intafi ana jirana.
dada tace ka dai ji dashi marar mutunci kawai,
yarima murmushi yayi yace na barki lafiya 'yar tsohuwa, sannan yaficce yabar turakar.
Gimbiya sumayya tana ganin yafita tatashi tahau tsalle da murna daga k'arshe da rungume dada tace nagode sosai ranki yadad'e Allah yak'ara tsawon rai wlh kin gama min komai.
dariya dada tayi tace ni sakarni ja'irar yarinya kawai ammah a gaban yarima bi kikayi kika marairaice kamar da gaske.
itama gimbiya dariya tayi tace ai wlh dan ina neman abu a wajensa saisa nabarsa yaci min mutunci son ransa ban tankaba.
dada rik'e ha6a tayi tace toh daman ashe bashi kad'ai yake rashin mutuncin ba harda ke, toh wlh kigyara domin aure ba abun wasa bane kuma kidaina ganin nasashi yabarki kiyi toh wlh kikama kanki kirik'e mijinki kar kififita kasuwanci akan aure kuma dan kince k'awarki zata dinga kula da komai saisa nagoyi bayanki.
gimbiya sumayya tace naji dada zan kula, nagode sosai.
mik'ewa sumayya tayi tana gyara alkyabbarta sannan takwala ma jakadiya kira, dagudu jakadiya tashigo tare da zubewa k'asa tace na amsa kiranki ya shugabata,
kallonta gimbiya tayi tace kuzo kucigaba da aikinku na kula da dada , jakadiya tace toh ranki yadad'e.
sannan gimbiya tayi gaba tana cewa kakus na wuce, dada tace toh sumayya
gimbiya sumayya tana fitowa nan bayinta suka mik'e suka take mata baya takoma 6angarensu.
Yarima suhail yana fitowa fuskarsa a d'aure yakar6i key d'in mota hannun driver dasauri d'aya daga cikin dogarawansa yabud'e masa motar yashiga.
shahid ganin yarima bai ko kallesaba kamar baisan da shiba ya shige mota dan haka shima yaje yabud'e yashiga yana cewa yau dakanka zaka ja mu?
yarima baice komaiba yaja motar yabar gidan, gudu yakeyi sosai da motar shahid yanata yi masa magiya akan yarage gudu ammah yarima kamar ba dashi ake ba.
cikin k'ank'anin lokaci ya isa gidan gona horn yashiga yi dasauri maigadi yazo yahangame masa gate yashiga da motar yana yin parking fitowa yayi yashige ciki bai ma kula da gaisuwar da ma'aikatan gidan sukeyi masaba.
shahid numfashi yake maidawa cike da jin dad'in sunzo lafiya domin bai kawo ma ransa zasu iso lafiya ba, daga k'arshe dai yabud'e motar yafito nan yatsaya saida suka gama gaisawa da ma'aikatan sannan yawuce cikin gidan.
A parlour yatarar da yarima kwance saman kujera idanuwansa a lumshe ya yi matashin kai da hannuwansa,
shahid tsayawa yayi gefensa yace wai yarima meyake faruwa ne naga tun da kadawo daga kiran da dada tayi maka fara'arka tagushe?
kuma dan mugunta kadinga gudu da mu toh idan kai bakason ranka toh ni inason nawa.
yarima idanuwansa a lumshe bai tanka masaba.
shahid tsaki yaja tare da zama yace kai nifa matsalata da kai kenan sai anayi maka magana kashare mutane kamar ba da kai akeba.
shidai yarima suhail baice komai ba saida yayi kusan minti biyar sannan yabud'e baki dakyar yace shahid wlh sumayya batada mutunci yanzu saboda Allah duk mutuncina ammah tana nema tazubar min dashi.
shuru yayi nad'an lokaci sannan yacigaba da cewa ni duk abinda takemin ban ta6a kai k'ararta ga kowaba ammah ita da mun d'an samu sa6ani toh sai kowa ya sani, ya za'ayi matar aure kuma matar yarima kamarni ace wai nabarta tana business har dada tagoya mata baya ai sai aja mutane suzageni.
Shahid cikin ransa yace ai indai wannan marar mutuncin ce zata aika domin bazan ta6a mance rashin mutuncin da tayi minba ranar da nazo wajenka.
chan kuma sai shahid yace kayi hak'uri kasan mata sai da hak'uri kacigaba da hak'urin da nasanka da shi.
yarima bud'e idonsa yayi da suke a lumshe yayi murmushin da yafi kuka ciwo sannan yace shahid kallon da akemin nine macuci cutar sumayya nakeyi babu Wanda yata6a tambayata yadda zaman aurenmu yake ammah wai ni zan saki matata tadinga yawon kasuwanci garuruwa.
shahid cike da tausayi yake kallon abokin nasa domin yasan ba'a ta6a jin matsalarsa saboda zurfin cikinsa ammah yau shine yake fad'a masa abinda yake damunsa tabbas yasan ba k'aramin 6ata masa rai akayiba, shahid yace dan Allah yarima kacigaba da hak'uri kadinga yi mata fatan alkhairi kar kad'auki mataki insha Allahu dakanta zata daina abubuwan da take.
Yarima shahid maida idanuwansa yayi yalumshe yana jin wani iri a ransa,
ganin haka yasa shahid yatashi yafita yana zagaya gidan gonar....
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Sak'on gaisuwata agareki aduk inda kika kasance my Aysha hak'ik'a ina yinki irin sosai d'in nan, ina tayaki murnar sabon novel d'inki da zaki fara mai suna *K'AUNACE SILA* Allah yasa afara lafiya agama lafiya my dear, Happy Birthday in advanceπππ_
_*Ba zan gaji da sadaukar muku da page ba Masoya ina jin dad'in comments d'in da nake samu daga gareku a group's da masuyimin ta pc wlh ina yinku over, wannan page d'inma kuje da shi nabakushi a kyautaπ sis Nerja'art tana sonku irin sosai d'in nanπ*_
page 5⃣
yarima duka wayoyinsa yakashe dan kar adamesa da kira dan yasan confirm ne sai maimartaba ya nemesa,
bayan sallar isha'i suka bar gidan gonar, shahid ne yakar6i key d'in motar yayi driving d'insu domin cewa yayi ba zai yarda yarima yatuk'asuba gudun kar yak'ara irin driving d'in da yayi d'azun shidai yarima baice komai ba yamik'a masa key d'in.
ko da suka isa yarima cema shahid yayi yazo sufara shiga fada sugaishe da sarki, shahid bai musaba yabi bayansa a jere suka shiga fad'a nan duk mutane suka zube suna kwasar gaisuwa ahaka har suka iso gaban sarki,
dasauri wani dogari yad'auko wani had'ad'en carpet yashimfid'a musu nan sauran dogarawa suka zo suka baza manyan rigunansu suka kare su yarima daga ganin mutane suna cewa azauna lafiya yarima, saida suka tabbatar da sun zauna sannan suka matsa nan su yarima suka gaishe da sarki, sarki fuskarsa d'auke da fara'a ya amsa nan fadawa suka d'auka angaisheku yarima mai jiran gado sarki ya amsa gaisuwarku Allah yaja da ranka.
sannan yarima suka gaishe da su daddy da abban sumayya, nan ma fadawa suka d'auka da angaisheku kuma,
maimartaba kallon yarima yayi da yake durk'ushe k'asa yace yarima tun d'azun nake aikawa akira min kai ammah sai adawo acemin tunda kafita baka dawoba.
yarima suhail murmushi kawai yayi.
ganin bashida niyar yin magana yasa shahid cewa ranka yadad'e munje gidan gona ne tun d'azun muna chan.
maimartaba murmushi yayi irin nasu na sarakai sannan yace Alhmdllh gaskiya ina jin dad'in hakan kuma duk ayyukan alkhairi da kukeyi a gari yana dawo min a kunnena tabbas nasan ko bayan raina nabar magajin da zai gadeni Wanda zai so kuma yatausaya ma jama'arsa tabbas kaine yafi cancanta da kakasance *Sarkin sarakai*
yarima dasauri yad'ago kai yakalli mai martaba har ya bud'e baki zaiyi magana sai kuma yafasa,
gaba d'aya fadawa suka d'auka angaishe da yarima mai jiran gado, angaishe da kwarzon namiji, angaishe da namijin zaki sarki ya gaisheka.
yarima da shahid k'ara gaishe da sarki sukayi sannan suka mik'e dasauri sauran jama'a da fadawa suma suka mik'e nan suka shiga yi ma yarima kirari har saida yafita daga fadar sannan suka zauna.
shahid saida yaraka yarima har wajen turakarsa sannan yayi masa sallama yatafi gida.
yarima yana shigowa dasauri dogarawa suka zube suna kwasar gaisuwa sannan suka mik'e suka take masa baya suna masa kira, takawarka lafiya yarima, Takawarka lafiya babban dodo mai rikita 'yan maza, takawarka lafiya sarkin sarakai, nan bayi da ma'aikata sukaita fitowa suna gaishesa tun yana amsawa har yagaji yakoma d'aga musu hannu ahaka har ya isa part d'insa dasauri wani dogari yabud'e masa d'akin,nan suka d'auka ashiga lafiya yarima, batare da yarima ya juyoba yad'aga musu hannu nan duk suka duk'a sukace munbarka lafiya yarima akwana lafiya, nan suka tashi duk suka watse, sai guards d'insa kawai suka rage yarima yana shiga bedroom d'insa kawai yawuce.
wanka yayi sannan yakwanta.
tun daga ranar suka rage had'uwa da gimbiya sumayya saidai idan tana son wani abu wajensa sannan take zuwa d'akinsa, yarima bai damuwa da rashin zuwanta hidimar gabansa kawai yake sai inyaji yana buk'atarta sannan yake zuwa d'akinta idan ma yaje sai yayi da gaske yake samu tana amince masa cikin 6acin rai suke rabuwa.
A sibitinsa da aka gina masa yana bada gudunmawa sosai baya bari ana wulak'anta masa patients kamar yarda baya bari awulak'anta masa staffs, hatta talakka idan yazo asibitin ana kar6arsa sannan kud'in magani rabi ake kar6a ana yafe musu rabi nan da nan asibitin yayi suna a garin da wajen garin.
Gimbiya sumayya business d'insu suke kud'i suna shigo mata sosai ammah har lokacin bataje tagano boutique d'in nasuba da yake a garin Abuja inda zinat tazuba ma'aikatan da suke kular musu da kayan kullum tsegumi take ma gimbiya akan rashin zuwanta tagano boutique d'in,
yau ma dai kiran gimbiya tayi a waya, gimbiya sumayya da take kishingid'e bayinta zagaye da ita tuface ake bata a baki tana ci ahankali inda gefenta baiwace take karanta mata labarai anutse, wayarta da tahau rurine yasa kowa yanutsu wadda take rik'e da wayar tatsugunna tace ranki yadad'e gashi ana kira,
gimbiya sumayya yamutsa fuska tayi tace wake kirana?
jikin haule yana kyarma tace bestie naga ansa, harararta gimbiya tayi tace ashe ke kin d'anyi karatu ba laifi ai na d'auka jahilace irinsu indo, indo da take tsaye tana ma gimbiya fiffita murmushi kawai tayi batace komai ba,
gimbiya sumayya d'aukar wayar tayi tare da cewa my zinat dafatan kina lfy?
daga chan 6angaren zinat ta amsa da lfy lou kema dafatan haka sarauniya mai jiran gado
'yar dariya sumayya tayi tare da cewa ke ni har na hangoni ko nazama sarauniyar, Allah dai yakaimu lokacin
zinat tace am wai yaushe zakizo yau fa kusan 5 months ammah shuru bakizo kikaga yadda komai yake tafiya ba? saidai kawai kiji alert d'in kud'i.
gimbiya k'ara gyara kishingid'ar tayi tare da cewa zinat wlh nima inso inzo kawai ina tsoron wulak'ancin yarima.
tsaki zinat taja tace ke wlh kina bani mamaki sai kace ba big gurl ba? yanzu saboda Allah duk class d'inki ammah kizauna wai sai yadda miji yayi dake, ke ya dai kamata kizo munfayi customers sosai kuma akwai kayan da nakeso ink'ara d'auko mana saboda haka kifitar da rana kizo,
gimbiya sumayya dogon numfashi taja sannan tace toh shikenan baby kar kidamu zanzo nima ai daman nayi missing d'inki,
dariya zinat tayi tace koma dai mekenan saidai kinzo, kinga sai kimin ko 2 weeks ne,
gimbiya sumayya tace ina ma dai laifi kice 1 week, shima sai munyi daga da yarima sannan zan samu yayarda, koma dai mekenan zamuyi waya.
nan sukayi bankwana, gimbiya sumayya tunani tashiga yi yarda zata samu tatunkari yarima da maganar batare da yak'i amincewaba.
chan kuma sai taja tsaki cikin ranta tace dolema ya amince dan babu yadda za'ayi yak'unsheni cikin gida shi yana yawon gararanbarsa a gari. bari ma yadawo.
gimbiya sumayya kallon haule tayi tace yau inaso kisamin ido ga yarima idan ya shigo kiyi min magana?
haule cike da ladabi tace tau ranki yadad'e umurninki shine abun cikawata.
wajen k'arfe tara gimbiya tagama shirinta cikin kayan baccinta sannan tad'aura alkyabba daga sama tafeshe jikinta da turare mai k'amshi sannan tafito dasauri ma'aikata da bayi suka hau gaisheta tare da yi mata kirari,
gimbiya sumayya sai yatsina take tana ji suna k'ara mata girman kai, baiwarta haule kawai tace tazo tarakata nan haule cikin sauri tataso tatake mata baya har sukaje 6angaren yarima nan ma dogarawa suka shiga gaisheta sannan suka bud'e mata k'ofa, kallon haule tayi fuskarta ba yabo tace zaki iya tafiya.
haule durk'usawa tayi k'asa tace toh ranki yadad'e atashi lafiya,
sumayya tana shiga ganin yarima baya parlour yasa dan haka tashiga bedroom tana bud'ewa yarima da yake tsaye yana sanya kaya da alama daga wanka yafito yakallota, kallo d'aya yayi mata yad'auke kai gimbiya sumayya cire alkyabtarta tayi ta aje gefe tare da takawa inda yarima yake tsaye tace my sweetheart ko intaimaka maka?
yarima bud'ar bakinsa sai cewa yayi a yau kuma? kedai kawai kifad'amin me kikeso?
gimbiya tace haba yarima daga nace zan taimaka maka shine harda tambayar me nakeso?
kenan banda ikon yi maka komai sai idan ina buk'atar wani abu.
yarima a wulak'ance yace ai hakan halinki yake, kema kuma kinsan hakan kike, yana gama fad'in haka yazagayeta yawuce yaje yahaye gadonsa yakwanta.
gimbiya sumayya tsaye tayi tana mamakin halin yarima cikin ranta tace nasan ta yadda zan 6ullo maka, itama takawa tayi tanufi gadon tahau
takwanta tare da rungume yarima tace sweetheart ni bana buk'atar komai sai kai mijina.
yarima murmushi yayi yace ashe anyi miki karatun ta nutsu gaskiya natayaki murna idan har dagaske kin gyaru.
cike da k'ulewa gimbiya tace haba yarima wai meyasa kakeson kaga ka cimun fuska wani fa lokacin har a gaban bayina da kuyangina kake yada min magana.
yarima shuru yayi baice mata komai ba, ganin haka yasa tad'ago kanta takallesa sai ganin idanuwansa a lumshe, shafa sajen fuskarsa tayi tare da yin murmushi tace my dear ba dai bacci zakayi ba,
yarima batare da ya bud'e idonsaba yace ya dai?
gimbiya sumayya bakinta takai cikin nasa nan da nan yarima yacafke suka shiga faranta ma junansu.
saida yarima yadirjeta son ransa sannan yabarka atare sukayi wanka sannan suka kwanta tana rungume a jikinsa, yarima yana mamakin sauyawar da sumayya tayi ahaka bacci yayi awon gaba da su.
da asuba ko da sukayi sallah komawa sukayi bacci sai wajen k'arfe tara sannan suka farka a tare sukayi wanka sukayi breakfast bayan sun gama gimbiya jerawa sukayi da yarima suna tafiya inda dogarawa da kuyangi suka take musu baya har saida yarima yazo wajen motar da zai je wajen aiki da ita sannan sukayi sallama dasauri wani bawa yabud'e masa motar yashiga, saida sukaga tafiyarsa sannan gimbiya tajuya suka koma gida, cikin ranta tana ayyana yadda zata biyo ma yarima ya amince batare da tashin hankali ba.
ko da yarima yadawo wajen k'arfe biyu ita taje tataresa cikin shigarta ta alfarma tafito a sarauniyarta ta asali sannan tarakasa har d'akinsa shidai yarima kansa yad'aure sosai ganin wata irin kulawa da yake samu a wajen gimbiya wadda tun satin aurensu rabon da yasameta,
ita tataimaka masa yayi wanka yashirya duk k'uiyarta ajeta tayi gefe tatattali mijinta
bayan kwana biyu yarima ne kwance da gimbiya manne da juna suna ta wasanninsu, gimbiya ganin yarima yana shirin nemanta yasa tadakatar dashi, yarima kallonta yake da mamaki idanuwansa duk sun canza kala, yarima dakyar yabud'e baki yace ya dai?
Gimbiya turo baki tayi cikin shagwa6a tace sweetheart Please wani taimako nakeso kayi min, yarima zuba mata ido yayi baice komai.
ganin haka yasa gimbiya sumayya yin murmushi tana wasa da gashin da yake kwance a k'irjinsa tace dan Allah so nake kabarni inje Abuja.
yarima da mamaki yake kallonta yace me zakiyi kuma a abuja? Sumayya d'ago kai tayi tana kallonsa tace so nake inje inga boutique d'in da muka bud'e kaga tunda aka bud'e banjeba kuma badad'i ace har tsawon wannan lokacin ban lek'aba,
yarima d'auke kai yayi tare da cewa ba zakije ba, gimbiya a firgice takallesa tace yarima meyasa? dan Allah kar kahana ni.
yarima suhail wani mugun kallo yawurga mata tare da cewa idan ke bakida hankali to ni ba mahaukaci bane, babu yadda za'ayi insaki matata tayi irin wannan tafiyar mai nisa kuma ya kike tunani mutane zasu d'aukeni? kawai akan kasuwanci?
gimbiya sumayya tashi tayi daga jikinsa cikin fushi tace wlh ban ta6a sanin kai butulu bane sai yau duk hallacin da nayi maka kwana biyu ammah baka ganiba? toh bari kaji akan *KUSUWANCI NA* zan iya yin komai dan haka muzuba mugani kuma tafiya tana nan daram ko da baka. ....
wani gigitaccen mari da yarima yad'auketa dashine yasa takasa k'arasa maganar, kallonsa take da mamaki saida 'yan cikinta sukaso sukad'a ganin yadda yake huci,
yarima dakyar ya iya bud'e baki yace ke har kin isa kidinga min shouting haka? ko dan kinga ina lalka6aki? toh bari kiji albarkacin iyayena kawai kikeci kuma babu inda zakije sannan daga yanzu kidinga ladafta maganarki idan kina a gaban *yarima suhail*, yana gama fad'in haka yad'auko rigarsa yasaka yaficce daga d'akin fuskarsa babu alamun annuri a tattare da shi ahaka yawuce yatafi part d'insa.
gimbiya tana ganin ya fita tafad'a saman gadon tacigaba da rizgar kuka takaicinta marin da yarima yayi mata tun da take iyayenta basu ta6a sa hannu suka daketaba sai yau wani yadaketa kuma wai miji.
tashi tayi tajanyo alkyabtarta tasaka tafito fuuuu dasauri kuyanginta suka mik'e zasu take mata baya cikin fushi gimbiya tadaka musu tsawa tace duk wacce takuskura tabiyoni abakin aikinta.
dasauri duk suka koma suka zauna domin sunsan abinda gimbiya tafad'a zata iya zartar da shi.
cikin sauri take tafiya kamar ta6a66a har ta isa 6angaren ummanta duk mutanen da suke gaisheta bata luraba saboda hankalinta baya a tare da ita tana cikin matsanancin bak'in ciki,
ummah da take zaune bayinta suna ta mata hidima saidai ganin gimbiya tayi kamar an jefota, a firgice ummah tatashi daga kishingid'en da take tace sumayya lafiya?
sumayya dasauri tazo tafad'a jikin ummah tare da fashewa da wani sabon kukan nan hankalin ummah ya ida tashi, cewa take sumayya kifad'a min abinda yake damunki mana,
ummah cikin 6acin rai takori ma'aitanta duk suka fita suka bar d'akin, sannan tad'ago kan sumayya cike da damuwa tace shalele wa yata6a min ke?
gimbiya share hawayen fuskarta tayi nan takwashe dukkan abinda yafaru tsakaninta da yarima tafad'a ma sultana sadiya
sultana sadiya ranta ya 6aci sosai musamman ma da taji wai ya mari sumayya, cikin 6acin rai taharzuk'a tamik'e dasauri sumayya tarik"ota tace ummah ina zakije? ummah tace sakarni inje inci mutuncinsa sai yafad'amin dalilin da yasa yamareki ko mu da muka haifeki hannunmu bai ta6a kaiwa ga fuskarkiba da sunan mari sai wani banza zai mareki.
sumayya tace ummana kibarsa kawai ai sai na rama marin da yayi min dan ba zai ta6a ta6aniba azauna lfy, nidai yanzu kisamo min mafita saboda ina da burin tafiyar nan cikin satin nan.
ummah komawa tayi tazauna tare da cewa ai dole ma ne kitafi dan haka taso muje wajen dada nasan yadda zan 6ullo ma lamarin
cike da jin dad'i sumayya tace nagode ummana wlh saisa nake k'ara sonki, murmushi sultana sadiya tayi tace ai dole inso duk abinda kikeso shalelena. nan suka tashi suka d'unguma turakar su dada. .........
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
page 6⃣
suna shiga a parlourn dada batanan saidai ma'aikatanta nan suka zube suka kwashi gaisuwa wajen gimbiya sumayya da sultana sadiya ammah ko kallon arzik'i basu samuba, gimbiya ce a wulak'ance tace dada bata nan ne?
jakadiya tace ranki yadad'e ta d'an shiga ciki ammah yanzu zata fito,
gimbiya kallon sultana sadiya tayi tace ummah muzauna kafin tafito.
sultana sadiya bata musaba nan suka zauna suna jiranta.
bayan kamar minti biyar sai ga dada tafito dasauri duk suka mik'e tsaye hatta ummah da gimbiya saida suka mik'e nan kuyangi suka d'auka angaisheki sultana takawarki lafiya, daganan sukayi shuru domin sun san dada batason ana mata kirari.
nan tazo tazauna saman kujera, sultana sadiya da gimbiya nan suka duk'a suka gaisheta, fuskar dada d'auke da fara'a ta amsa sannan suka zauna saman kujera, dada ganinsu da tayi haka yasa tasan muhimmin abune yake tafe da su dan haka tasallami kuyanginta gaba d'ayansu.
maida kallonta tayi ga sultana sadiya tace daga ganinku akwai abinda yake tafe daku ina saurarenku,
sultana sadiya murmushi tayi takalli gimbiya da tazuba mata ido tana jiran taji abinda zatace, d'auke idonta tayi daga kallonta tamaida kan dada tace ranki yadad'e daman sumayya ce tazo tasameni da maganar da ban ji dad'intaba shine nace ai ke yafi dacewa muzo mufad'a mawa saboda daga sarki sai ke ne shuwagabanninmu.
dada dai zuba ido tayi tana kallonta chan sai tagyad'a kai tace ina saurarenku.
sultana sadiya tace daman sumayya ce tasamen akan ta yi ma yarima magana domin yataimaka yabarta taje tagano yanayin yadda business d'insu yake tafiya saboda tunda suka fara wata biyar kenan ammah bata samu talek'a ba abokiyar kasuwancintata ta matsa
akan ko da sau d'ayane taje taga yanayin wajen kuma akwai wani signing da akeso tayi shine takeso ko kwana biyune tayi toh tunda tafad'a ma yarima haka nan yahauta da fad'a da cin mutunci a k'arshe ma har da marinta yayi,
haka tazomin a firgice shine nace muzo wajenki saboda ke yafi cancanta kishiga lamarin nan.
dada kallon sumayya tayi da idanuwanta suka kumbura saboda kuka, haushine yakamata ganin irin cin mutuncin da yarima yayi ma jikarta, cikin fushi tace wannan bazai ta6a yuwuwaba domin bana son azalunci wani bare ma ace nawane yazalunci d'an uwansa tafiyace kuma da bazan aminceba saboda baidaceba amatsayinta namatar yarima guda ace tana yawo kuma tunda kika taso a nan gidan sarauta bakiga iyayenki suna haka ba kuma kinsan memartaba bazai ta6a amincewa da hakanba,
gambiya sumayya marairaicewa tayi kamar zatayi kuka tace dada dan Allah kitaimaka min,
dada tace toh shikenan ai tunda har yaci mutuncinki toh sai kintafi dan haka kiramin shi a waya.
gimbiya sumayya da ummanta sunji dad'i sosai da jin zancen dada, dan haka sumayya takar6i wayar dada domin takira yarima.
yarima tunda yaje d'akinsa saman gadonsa yafad'a cike da jin haushin sumayya ammah baiyi mamakin hakanba domin daman chan yaba ma ransa da biyu take nuna masa kulawa sai idan tana neman wani abu daga garesa, a gefe guda kuma na zuciyarsa ya ji haushin marin da yayi mata domin shi a rayuwarsa ya tsani hakan.
wayarsace da tafara ringing kamar ba zai d'aukaba saida takusan tsinkewa sannan yad'auko ganin sunan dadane yasa yatashi zaune tare da yin picking d'in wayar yasa a kunnensa yayi sallama,
dada ko amsa masa sallamar batayiba cikin fad'a tace toh marar mutunci kazo kasameni ina jiranka yanzun nan kar kuma kakuskura ka6ata min lokaci domin idan bakazo cikin lokaciba ba kaiba hatta mahaifinka sai ransa ya 6aci, tana gama fad'in haka takashe wayar.
yarima haushine yakamasa jin rashin mutuncin da dada tayi masa kuma wai harda mahaifinsa tsaki yaja yace tabbas wannan nasan had'in sumayya ne lallai yarinyar nan batada mutunci, tashi yayi yashiga toilet yayi wanka cikin sauri yafito yashirya sannan yakama hanyar 6angarensu dada, hana dogarawa yayi surakasa shi kad'ai yatafi yana tafiyarsa ta k'asaita babu alamun fara'a tare da shi tsakaninsa da mutane saidai yad'aga musu hannu ko da daman halinsane hakan.
baidamu da gaisuwar da kuyangi sukeyi masaba yashiga d'akin da sallamarsa ko kallon inda su gimbiya suke baiyi ba yazauna cike da izza.
dada sakin baki tayi tana kallonsa, gaisheta yayi, bata amsa masaba tace me yahad'aka da matarka?
murmushi mai aji yarima yayi yace dada ko gaisuwar ma baza'a amsa min ba?
dada tace bana buk'atarta karik'e abunka, nace me yahad'aka da sumayya,
yarima sai a lokaci yakalli sumayya da sultana Sadiya yayi murmushi yace ashe ummah ce barka da rana.
sultana sadiya kamar tad'aura hannu saman kai tafasa ihu saboda takaicin yadda yarima yayi mata, ganinta a matsayinta na uwar matarsa ammah baya ji zai iya gaisheta cikin girmamawa.
ganin yadda dada tatsaresa da ido yasa yace dada wani abu tace miki ya faru a tsakaninmu?
dada tace kai banason shashanci ashe bakada mutunci, dan rashin imani har ka iya d'aga hannu kamari matarka, toh bari kaji wannan yazama nafarko kuma na k'arshe sannan maganar tafiyar da tace zatayi inaso kasani dole kabarta tatafi dan bak'in ciki d'an abinda take samune yake tsone maka ido.
murmushi yarima yayi yana kallon kaka sannan daga baya yamaida kallonsa ga gimbiya da tatsaresa da ido yace toh kinji dai abinda dada tace sannan yamik'e tare da kallon dada yace toh dada nabarku lafiya.
dada nace nashiga ukku ni Asma'u yanzun suhail saboda Allah baka d'aukeni da daraja ba? ina maka magana zaka tashi?
yarima komawa yayi yazauna tare da cewa sorry dada ba haka bane kawai naga kin yanke hukunci saisa.
da mamaki dada take kallonsa tace kana nufin kai baka aminceba?
yarima suhail shuru yayi kamar ba zaiyi maganaba saboda maganar da yakeyi ta gunduresa ga wani irin haushin sumayya da yakeji da kullum batada buri sai na had'asa da su dada, sai chan yace ammah dada kin yanke hukunci batare da kinji nawa uzurinba.
dada tace karik'e abunka domin babu abinda zaka fad'amin tunda ka gama zaluntar 'yar uwarka ni yanzu amincewarka nakeso
yarima cike da jin haushi yace na amince saboda ke dada, wani murmushin mugunta yayi yace ammah dai duk abinda yafaru ina gargad'inki da kiyi kuka da kanki sumayya.
sultana sadiya a fusace tace insha Allah ba abinda zai faru sai alkhairi bakinka da bak'in nufinka sukoma maka, sumayya tace wlh kau ummah .
yarima murmushi kawai yayi baice komaiba dada tace toh ka kyauta ammah yanzu sai kabata hak'urin marin da kayi mata kuyafe ma juna domin farin cikinku da zaman lafiya mukeso,
yarima wani irin kallo yayi ma dada domin yasan bayan mahaifiyarsa sai dada kawai yasan matan da zai iya ba hak'uri, duba time yayi sannan yace yanzu dai bari intafi saboda kaina ya fara ciwo.
ganin dada batace komaiba yasa yarima yamik'e tare da cewa na barki lafiya ranki yadad'e sannan yawuce cikin takunsa yabar d'akin.
gaba d'aya binsa sukayi da kallo cike da mamakin halin yarima, sultana sadiya ko k'arshen k'ulewa ta k'ule ta cika fam.
dada kallonta tamaido agaresu tace saidai hak'uri kunsan halin yarima suhail wani lokacin hatta ni kaina nuna min yake kamar ban isa da shi ba ammah dai Alhmdllh tunda ya amince kitafi ni nasan yadda zanyi da maimartaba sai kije kifara shiri kifitar da rana koma dai mi kenan zan fad'a miki ammah dan girman Allah kar kidad'e domin kinsan halin mijin nan naki.
Gimbiya sumayya cike da jin dad'i tace insha Allahu dada ba zan dad'eba baifi inyi 1wk ba, dada tace toh shikenan Allah yataimaka sukace Ameen, sannan sultana sadiya da Gimbiya suka k'ara duk'awa suka kwashi gaisuwa sannan sukayi mata sallama suka bar d'akin cike da jin dad'in nasarar da suka samu.
Yarima suhail ransa ya 6aci sosai kawai daman yana 6oyewane dan kar sugane halin da yake ciki yana fitowa direct 6angaren iyayensa yanufa a parlour yatarar da ummi kishingid'e ana mata tausa,
bayi da kuyangi suna ta yi mata hidima, suna ganinsa ko yazube yakwashi gaisuwa, yarima batare da ya tankaba yad'aga musu hannu cikin sauri kowa yatashi suka fita daga d'akin takawa yayi ya isa Saman kujerar da ummi take zaune zuba masa ido ummi tayi tana kallonsa, yarima zama yayi shima yana kallonta da idanuwansa da suka kad'a daga launin fari zuwa na ja saboda 6acin rai sannan yajanye fuskarsa daga kallonta,
ummi tace suhail miyake faruwa ne? kafad'a min damuwarka.
yarima suhail saida yad'auki kusan minti biyu kamar ba zaiyi magana ba sai kuma chan yace ummi yanzu saboda Allah ina auren sumayya ammah ta d'aukeni kamar ba mijintaba ban isa in hanata abu ba sai ta had'ani da dada, kullum cikin kai k'arata take.
shuru yad'anyi nalokaci sannan yakalli mahaifiyar tasa da tazuba masa ido yace wai abun haushin har da mahaifiyarta take goyan mata baya toh ni cewa nayi bata min laifi? duk hak'urin da nake da ita bata gani duk abinda takemin wa nata6a samu nafad'a ma wa? kawai ina kyaletane albarkacin iyayenmu da zumuncin mu.
girgiza kai yayi cike da takaici yace ummi hak'uri ya k'are zan d'au k'wak'waran mataki akai.
Sultana Bilkisu cike da tausayin d'an nata take kallonsa domin tasan halin d'an nata ko da za'a cutar da shi ba ya ta6a damuwa saidai idan an kaisa k'arshe shine zakaga 6acin ransa.
tashi ummi tayi daga kishingid'en da take tarik'o hannun d'an nata tace suhail kacigaba da hak'urin da nasanka da shi insha Allahu komai zai zo k'arshe, wani lokacin dakanta zata daina.
yarima suhail murmushi yayi wanda iyakarsa baki sannan yace ummi har wane lokacin kuma? kiduba kiga tsawon dad'ewarmu ammah kullum halinta k'ara canzasa take ni wlh da ace ina da wadda nakeso da aure zan k'ara domin sumayya da ita da babu, banbancinsu kad'an ne.
ummi zaro ido tayi tace karufa mana asiri yarima wane irin aure? dukafa yanzu aurenku baifi shekara d'aya ba.
murmushin takaici yarima yayi yace ummi ba zaku ta6a fahimtataba.
ummi tace indai baso kake a zargemuba.
yarima suhail jingine kansa yayi a kan kujera tare da lumshe idonsa yana jin wani iri a ransa.
sultana bilkisu kallon d'an nata take cike da tausayi ganin tunda yayi auren nan yabi ya rame tabbas tasan akwai abinda yake damunsa dandai miskilancinsa ya zame masa yana da zurfin ciki sosai.
itama jan bakinta tayi tayi shuru domin tasan d'an nata baya da son hayaniya.
A ranar yarima bai fitaba d'akin ummi yawuni ak'arshema bedroom d'in ummi yakoma yasha baccinsa, ummi hana kowa tayi yashiga.
Gimbiya sumayya suna komawa turakar sultana sadiya kallon ummantata tayi cike da farin ciki tace wlh ummi kin gama min komai, tabbas nayi sa'ar uwa mai son farin cikina.
Sultana murmushi tayi tace ai wlh akanki ba na jin zan iya ragama kowa, wannan mijin naki na tsanesa dandai babu yarda zanyi ne, gimbiya zaro ido tayi tace ummah mijin nawa kika tsana?
sultana Sadiya tace eh man saboda ni naci burin in haifi Wanda zai gaji memartaba ammah ban haifaba saisa tunda aka haifesa naji bana sonsa.
dariya gimbiya tayi tace toh ai yanzu sai kikwantar da hankalinki tunda ni yake aure kuma duk wanda zai gaji masarautarnan ni zan haifa masa.
Sultana tace hakane ammah ai har yanzu naga bawani bayani wlh hankalina tashi yake ganin kunyi shekara da'ya har da d'oriya baki haihuba.
gimbiya tace haba ummah wa yake ta haihuwa yanzu sai mun gama cin zamaninmu sannan zan haihu
sultana sadiya sakin baki tayi tana kallonta da mamaki tace sumayya ban ta6a sanin ke sakara bace sai a yanzu keda kike auren yarima ai kyau ace kinyi saurin haihuwa ko da ace biyune kibari kiyi in yaso daga baya sai ki tsayar da haihuwar sai lokacin da kikeso.
Gimbiya sumayya cikin fushi tace gaskiya ummah ni nagama tsara yadda nakeso rayuwata tatafi kuma na tabbata yarima bazai ta6a k'ara aure ba domin su dada ba zasu ta6a amincewa da hakan ba.
sultana sadiya tace kima daina wannan maganar wlh ko ni ba zan ta6a bari yayi miki kishiba, nidai burina kijanye wannan plan d'in naki kihaifar mana baby,
gimbiya mik'ewa tayi tsaye tana gyara alkyabtarta tace ummah bari inje dai infara shirin tafiyarnan da zanyi saboda jibi nakeso inyita nabarki lafiya.
Sultana Sadiya bin d'iyartata tayi da kallo domin tasan dandai ajanye maganar haihuwarne shiyasa tace zata tafi, murmushi tayi tare da girgiza kai tace sumayya kenan Allah yasa kifahimci abinda nake nufi. .....
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
?ππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_sak'on gaisuwata agareku *Zaynav mtz fan's, Yarima suhail fan's 1&2, Ummun meenal fan's, hibbatullah fan's, janaf fan's, zauren sainah fan's, mummyn khalil fan's Aufana true fan's* da sauran groups d'in da ban samu nalissafobaππ ina jin dad'in comments d'inku Allah yabar k'auna_
_*Wannan page d'in nakune my hafnan, Janaf, Aysha nd ummun meenal ina ji daku cikin zuciyanaππ*_
page 7⃣
yarima sai dare sannan yabaro turakar su ummi yakoma part d'insu, saida yayi wanka yashirya sannan yafito dining yad'anci abinci bayan ya gama kallo yakunna yana yi, bud'e k'ofar akayi aka shigo bai ko d'ago kai ba domin ya san gimbiya ce.
gimbiya sumayya ganin bai kalletaba yasa tatako tazauna gefensa cike da isa tace daman nazo infad'a maka jibine fa zan tafi kuma kasan ba zan iya tafiya mai tsayi a motaba dan haka sai kabada kud'i ayomin Visa,
wani mugun kallo da yarima yawurga mata saida hantar cikinta takad'a, batare da ya janye idonsa a garetaba yace ni na'aikeki?
Gimbiya sumayya itama kallonsa take tace toh naga kai yafi dacewa da kasa ayankar min ticket tunda k'ark'ashinka nake.
yarima shuru yayi kamar ba zaice wani abuba sai chan kuma yace ke ban ta6a sanin bakida hankaliba sai yanzu baizama dole inyi miki hakanba kuma bana tunanin akwai Wanda ya isa yasani dole, dan haka tashi kifitar min daga d'aki tun kan in6ata miki rai.
gimbiya sumayya mik'ewa tayi saida takai bakin k'ofa sannan tajuyo takalli yarima suhail tace koma dai me kenan katabbatar zuwa gobe ka yimin abinda nakeso inkuma bahakaba zan fad'ama dada, tana gama fad'in haka taficce daga d"akin.
yarima suhail takaicine da bak'in ciki suka taru sukayi masa yawa tsaki yaja kawai ak'arshe ma yakashe kallon yatashi yashige bedroom d'insa cike da 6acin rai yakwanta, yanajin wani iri a zuciya ji yake an cucesa da aka za6a masa gimbiya sumayya a matsayin matarsa domin kwatakwata halinta baiyi masaba.
ak'arshe wayarsa yajawo yakira d'aya daga cikin yaransa yace zuwa gobe a tabbatar anyi ma sumayya Visa.
Wanshe kare wajen k'arfe sha biyu da yarima yagama shirinsa fitowa yayi yanufi d'akin gimbiya sumayya inda yataddata a lokacin tafito daga wanka, a wulak'ance yakalleta sannan yawurga mata ticket yace ba dan halinki nasa akayi mikiba dan ganin damanane.
harararsa gimbiya tayi tace eh ahaka d'in dai saida nayi magana, yarima suhail murmushin mugunta yayi sannan yataka inda sumayya take, dak'arfi yajawota tafad'o jikinsa har saida tad'anyi 'yar k'ara sannan yace sumayya inaso kisani darajar iyayena kawai kikeci da badan hakaba wlh da sai kin gane kuskurenki.
gimbiya sumayya tace suhail kadad'e baka nuna min kuskurenaba kuma yadda kake tak'ama da sarautarnan nima ai jinintane, bamuda banbanci ni da kai, kuma idan ka cika d'an halak kata6ani kagani, kuma bari kaji jikina kagama samunsa tunda har kata6amin fuskata jiya yanzu daidai nake da kai.
yarima suhail d'auke ta yayi da mari yak'ara mata wani tare da wurgata saman gado yace banyi niyar kwanciya da ke ba ammah yau zan nuna miki na ciki d'an halakne ni, saman gadon yabita tare da fizge towel d'in da yake jikinta nan suka shiga kokawa ak'arshe yarima suhail yasakarmata nauyinsa.
mugunta yasa mata yadirjeta son ransa, gimbiya sumayya kuka kawai take, yarima saida yagaji dan kansa sannan yabarta,
kayansa yad'auka yasanya bai ko k'ara kallon inda sumayya take kwanceba tana ta ja masa Allah ya isa, fita yayi daga d'akin yakoma part d'insa yayi wanka yashirya sannan yaje fada yagaishe da sarki daga nan yafita yabar gidan.
Tun daga lokacin basu k'ara had'a hanya da gimbiya sumayya ba baima san lokacin da tatafiba sai wajen dada yakeji,
hatta umman sumayya yanzu ko ya gaisheta bata amsawa dan haka shima yadaina gaisheta, ko da ace tana tare da abban sumayya toh abbah kawai yake gaishewa tsakaninsa da ita saidai tahararesa shikuma yanuna ko inkula.
__________________
awata anguwa mai suna yamza wata yarinyace take tafita a nutse kanta a k'asa yarinyar ba zata gasa shekara ashirinba wani gidane tashiga gidan da kagansa kasan bamasu hali bane saidai rufin asiri, da sallamarta tashiga, wata matace da nahango zaune tana wanke-wanke ciki-ciki ta amsa mata sallamar
cike da ladabi zarah tak'arasa inda matar take tare da tsugunnawa tace mama sannu da gida.
harara matar tawurgamata tace ke shine bakiyi min wanke-wankeba kika kama hanya kika fita daga gidan ko?
zarah cike da nutsuwa tace mama dan Allah kiyi hak'uri wlh ganinayi na makara islamiyya shiyasa.
rik'e baki mama tayi tace eh islamiyya fad'amin nida banyi islamiyarba, ke ga ustaziya ko? to wlh inbaki canza haliba haka zakizo kik'are cikin gida, kiduba kiga 'yan uwanki kullum sai sun fita sun samo mana 'yan kud'in da zamuyi hidima ammah ke kina nan jibge a cikin gida saidai aciyar dake ashayar da ke iyakarki kashi, toh wlh indai bakiyi dagaskeba sai kin rasa mashinshini domin wannan girman kan naki babu inda zai kaiki.
zarah shuru tayi batace komai ba domin idan da sabo ta saba da halin iyayen nata,
tsawa mama tadakamata tace watau ga mahaukaciya ina magana shine kikayi shuru kika kyaleni watakau ga mahaukaciya tana magana.
zarah cikin nutsuwa tace Allah yabaki hak'uri mama kawo wanke-wanken in k'arasa miki.
ummah d'auraye hannunta tayi tamik'e tace ai ko bakiceba daman ke zaki idashi tunda baki aikin komai sai karatu saikace alhuda-huda.
mama tana tashi zarah tacire hijab d'inta tarataye saman igiya sannan tazauna tacigaba da wanke-wanken.
tana cikin yi saiga yayarta tashigo babu ko sallama kallonta zarah tayi cike da takaicin ganin irin shigar da take jikinta kayan sun matseta gyalen da tayafa ko dashi k'ara babu, d'auke kanta tayi daga kallonta tacigaba da wanke-wanke tana addu'a cikin zuciyarta Allah yashirya su sugane gaskiya.
muryar yaya rauda ce tajiyo tana cewa zarah ina mamanmu take? batare da takalletaba tace tana cikin d'aki.
Rauda kira tashiga kwala ma mama daga inda take tsaye, mama datake d'aka dasauri tafito kallabinta a hannu tana washe baki tace a'ah 'yar albarka har kin dawo?
Rauda yamutsa fuska tayi tace eh ga wannan ledar da take hannunta tamik'a mata, ummah cike da farin ciki ta amsa tana cewa me muka samu yau?
malam yusuf ne yashigo gidan yana cewa a'a 'yar baba ai naga lokacin da aka safkeki kinga har da 'yan canji mutumin yabani gaskiya yana da kirki.
Rauda yamutse fuskarta tayi tace ammah ai abba nace kadaina tambayarsu kud'i inkana tambayarsu ai sai kaja surainani ,
abba yace 'yar baba bafa tambayarsu nakeba sune suke bani kuma kinga babu kyau maida hannun kyauta baya ko ba haka bane Zainabu?
mama tace hakane malam, yanzu dai mik'o wani abu nan dan musamu daren nan muci mai d'an dad'i-dad'i.
abba yace toh naji yanzu dai menene cikin ledarnan?
mama duba ledar tayi tare da washe baki tace ashe kazace yau shagali zamuyi kenan.
Abba ma washe baki yayi yace gaskiya naji dad'i daman wannan bakin nawa yakwana biyu bai ci namaba, ammah dai 'yar baba Allah yaimiki albarka,
mama tace toh yanzu dai kakawo asiyo kayan miya muyi d'an pepper chicken,
abbah dubu d'aya yamik'a mata yace gashi sai akasiyo har da buredi wanda zamu d'an dangwala romon ai haka zaifi ko?
mama tace eh malam, ai saima autarka tadawo muga ita mi zata kawo mana, ai ni yau naga amfanin haihuwar 'ya'ya mata daman malam ai nafad'a maka 'ya'ya mata dad'i garesu,
malam yace hakane sannan yakai dubansa ga zarah da take tsugunne tana ta wanke-wanke, yamutsa fuska yayi yace Asma'u wlh d'iyar chan duk cikin 'ya'yana ita kad'aice batada k'ashin arzik'i wani ma lokacin ji nake anya jininace?
ummah tayi karaf tace a'ah malam wannan cin mutuncin da me yayi kama idan ba d'iyarka bace toh wanene ubanta? ko akwai wani mijin da na aura bayanka? ko kuma kana nufin ina bin mazan banza.
malam yace a"a zainabu nidai ina nufin kwata-kwata bata d'auko halinaba, kiduba kiga ko farin jinin samarin nan ita batadashi,
ummah tace ah toh yanzu naji bayani, ai malam kakalli wannan munafukar kawai bak'in ciki kawai take yi mana dan kar muci moriyarta kasan yanzu sai kahaifi d'a baka haifi halinsaba, wlh akwai samarin wulak'antasu kawai take tana korarsu sai wannan matsiyacin malamin nata da ta lik'e mawa me na k'asa yaci bare yaba nasama.
malam yace oh ni wlh daman nayi zaton haka ni wlh wannan sakaryar d'iyar bansan yaushe zata waye kamar 'yan uwantaba, Allah dai yashiryata.
mama tace Ameen dai
malam yace yanzu dai dafa mana kazar a d'ansa kayan yaji nasan zatafi dad'i haka bari ind'an fita.
ummah tace toh malam adawo lafiya.
zarah dai zaune take tana wanke-wankenta duk firar da iyayenta sukeyi akan kunnenta hawayene yacika mata ido tana jin wani abu ya tokare mata mak'oshi saboda takaicin halin iyayenta, cikin ranta addu'a take Allah yashirya mata iyayenta da 'yan uwanta sugane gaskiya.
bayan ta gama alwallah tad'aura sannan tad'auki hijab d'inta tashige d'akinsu, lokacin yaya rauda tana shafa da alamu daga wanka tafito.
zarah shimfid'a darduma tayi tad'auko alk'ur'aninta tana karantawa har aka tada sallar magrib sannan tatashi tayi sallah
ido tazuba ma rauda tana kallon yadda take sallah cikin sauri babu alamun nutsuwa atare da sallartata
ko da rauda tagama sallar zarah kallonta tayi cike da nutsuwa tace yaya rauda ya kamata idan kina sallah kidinga nutsuwa domin duk abinda zakije nema yana a hannun wanda kike gabansa a yanzu.
harararta Rauda tayi tace toh malama yimin wa'azi tunda kinfini sani, kinsan Allah zarah idan baki fita daga hancinaba sai na 6a66allaki a cikin gidan nan
kuma da kike maganar sallah ai Allah da zuciyar mutum yake amfani, kuma idan ke kike raba ladar toh dan girman Allah kihanani 'yar bak'in ciki kawai.
tana gama fad'in haka tatashi fuuuu taficce tabar d'akin tana ta mita.......
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
page 8⃣
tashi tayi fuuu tawuce tabar d'akin tana mita ita dai zarah bin rauda tayi da kallo cike da bak'in cikin halin 'yan gidansu a kullum addu'anta Allah yasa sugane gaskiya.
addu'a tayi sannan tatashi tacire hijab d'inta tafito takar6i kayan miyan da suke hannun mama tajajjaga mata sannan tatambayeta idan akwai abinda za'a, mama tace a'a,
sannan tawuce takoma d'aki koda tayi sallar isha'i zama tayi tana ta bitar karatunta sai wajen k'arfe takwas sannan k'anwarta Aysha tadawo gida hannunta d'auke da leda tun daga zaure tafara kwalah ma mama kira
mama da take tsugunne tana hura huta jikinta yana 6ari tamik'e tana washe baki tace a'ah autata har kin dawo.
Aysha tana yatsine fuska tace eh wlh ,
mama kar6ar ledar hannun Aysha tayi tace me kuma muka samu?
Aysha kar6e ledarta tayi tace kai mamanmu ba fa wani abu bane d'inkinane nabiya na amso,
fara'ar da take d'auke a fuskar mama ce taragu tace kina nufin babu abinda kika kawo mana? kiduba kiga 'yar uwarki kaza takawo mana gata chan saman wuta ina mana ferfesu,
Aysha tace oh mama kedai kullum burinki abaki kud'i, jakkarta tabud'e tad'auko 2k tace gashinan kid'auki d'aya kiba abbah d'aya.
mama kar6a tayi tana washe baki tace kai 'yar albarka gaskiya naji dad'i ammah ba zan ba mahaifinkuba dan shima d'azun ya samu kud'i kar ma kikuskura kifad'a masa kin bamu kud'i, Aysha wucewa tayi tanufi d'akinsu tana cewa nidai mamanmu wannan tsakaninku da abbane,
zarah tana zaune saman darduma tana sauraren dukkan abinda suke tattaunawa,
Aysha ce tashigo d'akin tana cewa wash wlh na gaji, jafe jakkarta tayi bisa katifa takalli zarah tace yaya zarah kina nan kina ta bitar karatun?
zarah batare da takalletaba tace Aysha daga ina kike? meyasa kikeso kiga kinyi dare a waje a matsayinki na mace?
Aysha turo baki tayi tace ammah ai mama tasan da tafiyata, zarah aje littafin da yake hannunta tayi tare da tattara dukkan hankalinta ga k'anwarta tace Aysha wannan rayuwar da kika d'aukar ma kanki ba mai 6ullewa bace k'ara tun wuri kigyara tun kan lokaci yak'uremiki gudun kar kiyi nadamar da batada amfani.
mama ce da tazo wucewa tajiyota tana magana lek'owatayi d'akin takalli zarah taharareta tace toh sarkin 6akin ciki mekike ce mata? badai hure mata kunne kikeyi ba dai ko?
zarah kallon mama tayi tace a'a mama kawai ina bata shawarace d's zata fisheta.
salati mama tahau yi tace nashiga ukku ni Zainabu yau Allah yabani d'iya mai bak'in ciki da ni, yanzu 'yan kud'in da take kawo mana ne kike ma bak'in ciki? toh idan suka zauna gidan ubanwa zai dinga ciyar da mu? kinsan dai mahaifinku bai bada abinda zamu ci muk'oshi .
zarah cikin lallashi tace mama kiyi hak'uri ni ba haka nake nufiba, idan na 6ata miki rai kiyi hak'uri.
mama tace daman ai haka zakice munafuka kawai wlh da ace ba ni nahaifekiba da na ce ke ba jinina bace.
zarah dai shuru tayi tana sauraren maganganun mama har mama tagama fad'anta tafita tabar d'akin.
karatunma zarah kasa cigaba tayi saboda haushi nan ta tattare littafan tamaida su ajakkarta, sannan tahaye saman katifarsu takwanta.
Aysha wanka tayo tashirya akan idon zarah wani yakirata a waya tafita tabar gidan, 'yar nokianta ce da taji tana ruri yasa takai idanunta a wajen ganin wanda yake kiranta saka tayi murmushi har dimples d'inta suka lotsa cike da farin ciki tayi picking domin tasan ko bakomai Malam Bello zai d'ebe mata kewa sallamata tayi masa, shima cike da farin ciki ya amsa mata, bayan sun gaisa malam Bello yace gimbiya zarah ya gida?
murmushi zarah tayi tace wai gimbiya dan Allah kama daina kar kaja akamani
dariya malam Bello yayi yace ai gimbiyarce.
zarah tace hmm dan Allah kadaina.
malam Bello yace toh malama zarah ta gida da mutanen gida?
zarah tace Lafiya lou Alhmdllh.
malam musa gyaran murya yayi yace zarah wlh ina sonki so nagaskiya dan Allah kitaimaka kirik'e min amanar kanki domin har ga Allah aurenki nake son yi, dama zaki bani dama da naturo an aje maganata inyaso daga baya idan nak'are karatuna sai muyi aure.
zarah murmushi tayi tace kar kadamu malam ba ma sai ka turoba insha Allahu banda miji sai kai domin ka cancanchi kakasance mijina inko kaga ban aurekaba toh wannan daga Allah ne,
malam Bello dogon numfashi yaja yace Allah yasa haka my zarah, wlh gani nake idan narasaki toh na rasa farin cikina domin kece kawai kika dace da rayuwata.
zarah cike da tausayinsa tace kar kadamu malam insha Allahu ma ba zaka ta6a rasaniba.
Bello cike da jin dad'i yace nagode sosai zarah, yanzu inzo mugaisa ko?
zarah kallon agogo tayi tace a'a malam yanzu dare yayi kadai bari sai gobe.
malam Bello yace toh malama zarah duk yadda kikeso ai haka za'ayi Allah yakaimu, murmushi zarah tayi tace toh malam ahuta lafiya sai Allah yakaimu.
malam bello yace au korata ma akeyi?
zarah tace wane ni inkoreka kawai dai zanyi bacci ne,
bello yace toh gimbiya atashi lafiya
zarah tace Allah yasa, nan sukayi sallama sannan suka kashe wayoyin.
zarah bin wayar tayi da kallo tana murmushi domin har cikin ranta tana jin malam bello ko da tasan mayuwacine iyayenta su amince da shi tunda baida kud'i ammah ta ci alwashin shikad'ai ne mutumin da zata iya aure saidai wani hukuncin daga ubangiji.....kiran da mama takeyi matane yakatseta daga tunanin da takeyi, dasauri tatashi tafita a tsakar gida tasamu mama da abba Zaune saman tabarma suna cin nama suna dangwala romon da bread,
kusa da mama tatsugunna tace mama gani, mama fuskarta a d'aure tace ga naki nan su kuma tunda su suka kawo saisa nafitar masu da nasu yafi yawa,
kar6a zarah tayi tace nagode sannan tatashi takoma d'akinta ,
abbah binta yayi da kallo cike da takaici yace ni inma rasa abinda yarinyarnan take k'unshewa a d'aki kullum tana d'aki ko fitowa batayi tasha iska.
ummah tana yagar nama tace ita dai tasani matsalarta.
zarah tana shiga d'akinsu zama tayi taci naman bayan ta gama tafiddo kwanon sannan tayi ma iyayen sallama takoma d'aki saida tayi wanka sannan takwanta.
duk yadda taso tayi bacci ammah takasa tunanin wulak'ancin da takesha wajen mutanene da halin iyayenta da gwagwarmayar da tasha ne yasa tafara hawaye kullum batada buri da yawuce taga iyayenta da 'yan uwanta sun canza hali musamman ma idan tatuna da lokacin da suna yara haka suka taso a sake iyayensu basa kwa6arsu
Malam musa da Zainab sune iyayensu su ukkune suka haifa, Rauda itace babba sai zarah da take bi mata sai 'yar autarsu Aysha ko da ba wani tserataiya bane irin sosai d'innan a tsakaninsu k'ara ma Rauda itace taba zarah shekara biyar, inda zarah kuma taba Aysha shekara biyu.
Suna da kyau sosai kasancewar iyayensu fulanine na usuli, saidai zarah itace zaka kallah kaga sak mama, inda su Rauda da Aysha suke kama da abbansu saisa zarah tayi musu fintinkau wajen kyau dan ma Suna halin rashi.
sunyi karatu bakin gwalgwado dan dukansu daga secondary school suka tsaya da karatunsu babu wacce tacigaba duk suna gida Zaune, zarah ma ce tashiga makarantar koyan sana'a tayi Catrine (6angaren girki) sannan itace mai zuwa islamiyya ammah su rauda babu wacce take da lokacin zuwa islamiyya sharholiyarsu kawai sukeyi.
abun mamakinma a gaban iyayen nasu ake zuwa ad'aukesu ammah iyayensu ko da sau d'aya basu ta6a nuna 6acin ransuba domin basuda burin da yawuce akawo musu kud'i,
hatta abincin da zasu ci wani lokacin rauda da Aysha ne suke ciyar da su kasancewar Abbah baida tak'amaiman aikinyi daman ginine da kanikanci shima sai idan ya samu yakeyi.
ahakanma iyayensu sun tsani suga talakawa suna ra6ar 'ya'yansu, su ma kansu su rauda basa son talakawa 'yan uwansu saisa duk samarinsu masu kud'ine.
duk wanda zai nuna yana son zarah toh wulak'ancine sai yasha wajenta,
mama tun tana fad'a har tagaji takyaleta,
hantarace da wulak'anci babu wanda bata sha wajensu, ko kud'in wata na islamiyya sai tayi dagaske take samu wajen iyayenta inma basu bataba toh wajen k'anwarta ko yaya rauda take samu su ma sai tasha wulak'anci da gori suke bata.
kayan shafa ma sai sunga dama idan zasu siyo nasu suke had'awa da ita suna d'an siyo mata mai da powder da turare shima a wulak'ance ake bata.
duk aikin gida ita aka sakarmawa inba ka saniba ba zaka ta6a cewa zarah d'iyar gidan bace sai kad'auka *'YAR RIK'O* ce,
wa'azi nasiha babu wanda batayi ma 'yan gidan nasuba ammah sunbi son zuciyansu da na iyayensu.
zarah tun abin yana damunta ammah yanzu ya rage damunta
Malam bello malamin islamiyyarsu zarah ne yana da kirki sosai jininsu ya had'u da zarah saisa suke mutunci, daga baya yanuna yana sonta dakyar yasamu zarah ta amince masa suna soyayya, duk wasu littafan karatun zarah shi yake siya mata.
zarah tun tana nuna bata so ammah daga baya tahak'ura tana kar6a dan tasan iyayenta ba zasu ta6a siya mataba kuma babu inda zata samu kud'i tasiya, shima dan taga yana da hankali da nutsuwa kuma a yadda yake nunawa shi dan Allah yakeyi mata kuma yana so yasamu lada idan ta karanta.
Malam Bello karatu yake a university sannan yana tsare ma wani mutum shago da kud'in islamiyya da ake biyansa a nan yake samun d'an abinda zai rik'e kasancewar iyayensa suma ba masu hali bane sosai.
mama lokacin da tagano zarah tana soyayya da shi har kusan dukanta tayi tace me zatayi da wannan talakkan me nak'asa yaci bare yaba nasama ita dai zarah shuru tayi domin tasan abinda mama take nufi, ammah a ranta itadai bata da burin auren kowa sai malam bello dan shine kad'ai yake taimakonta.
bud'a k'ofar da akayine yadawo da ita daga kogon tunanin da ta lula, Aysha ce tashigo da leda a hannunta tana waya, zarah duba agogo tayi taga kusan k'arfe goma da rabi dan haka tajuya domin tayi bacci cike da takaicin maganganun da Aysha takeyi a waya batare a taji kunya ko nauyin Zarah ba.
ahaka Aysha tagama wayan itama takwanta har sukayi bacci yaya Rauda bata dawoba.
da asuba zarah har tayi sallah ammah Aysha bata tatashi ko da zarah tak'ara tadata cewa tayi dan Allah kikyaleni idan natashi zanyi nace miki.
zarah tace haba Aysha yanzu har sai gari yayi haske sannan zaki tashi kiyi sallah?
Aysha tace ko ma dai yaushe nayi babu ruwanki malama dan haka kikyaleni.
zarah tsaki taja tace Allah yakyauta sannan tacigaba da laziminta har gari yafara haske sannan tamik'e taje tayi wanke-wanke tagyara gida bayan tagama tadawo tayi kwanciyarta sai alokacin Aysha tatashi tayi sallah.
wajen k'arfe goma zarah tafarka lokacin babu kowa d'akin batayi mamakin hakanba domin tasan Aysha ta tafi gantalinta daman ita yaya Raiuda ba gidan takwana ba.
zarah gyara d'akin tafara yi sannan tafito tayi brush tawuce d'akin mama lokacin Abbah yana shirin fita nan taduk'a bakin k'ofa tace Abbah ina kwananku.
Abbah ciki-ciki ya amsa mata, mama kau daman harararta tayi tace yanzu saboda Allah zarah sai yanzu kika tashi baccin?
zarah tace mama ai saida nagama komai sannan nakwanta,
mama cikin fad'a tace haka dai zaki k'are daga bacci sai zaman gida ko 'yan kud'in kashewar baki yarda kifita kisamo saboda bak'in cikin kar muma muci daga wajenki.
zarah shuru tayi mama tace toh yau dai ba ayi karin kumalloba muma nan ruwan Lipton da sauran biredin jiyane muka ci,
Kinga da ace kina da kud'inki ai da kin d'an siyo ko indomie ce kinci irin yadda 'yan uwanki sukeyi, yanzu dai bari inbaki kije kiyo mani cefane
zarah tace toh mama
mama kallon abbah tayi tace malam kabada kud'in cefanen.
abbah laluba aljihun rigarsa yayi yad'auko d'ari biyu yamik'a mata, mama tsayawa tayi tana kallonsa
yace ki amsa mana,
mama tace haba malam me d'ari biyu zatayi mana bamu da fa abinda zamu dafa muci,
abbah yace toh nidai su gareni koma minene kujalabta kuyi abincin.
mama tace gaskiya wannan babu abinda zatayi mana.
abbah yace kihad'a da canjin jiya ai nasan dai anrage wani abu cikin d'ari biyar d'in.
mama tace naira sittin fa ce.
yace toh inbakuso sai inmaida abuna aljihu.
Jin haka yasa mama takar6i kud'in domin tasan zai iya.
bayan ya fita mama kallon zarah tayi tace ni tashi kimik'o min jakkata ko d'ari biyu ce ink'ara dan ma Allah yaso akwai kud'in da Aysha tabani jiya da ban san yau ya zamuyi ba.
zarah tashi tayi taje tad'auko ma mama jakkar tamik'a mata.
mama d'ari biyar tabata tace kisiyo garin d'an wake rabi sai mai rabin gwangwani da tashi da Maggi ko shine musamu abinda zamu saka ma bakunanmu kafin yarana sudawo
kar6a zarah tayi tace toh mama.
zarah tashi tayi taje tasako hijab d'inta sannan tafita taje tayo siyayyar, bayan ta dawo tad'aura girkin.
tana cikin yi mama tafito ta shirya sanye da gyale tace toh idan kin gama kijuye a cikin plastic d'innan zan je gidan mariya barka kuma kar kisaki kici kibari sai nadawo nad'ibar miki.
zarah cike da ladabi tace toh mama Allah yakiyaye hanya.
zarah bayan ta gama gyara gidan tak'ara yi sannan taje tayi wanka tashirya tayi sallah.
bayan ta gama saman katifarsu takwanta tana jiran mama tadawo saboda wata irin yunwa da takeji.
mama sai wajen k'arfe ukku tadawo lokacin bacci har ya d'auke zarah.
maganar mama ce tajiyo sama-sama dan haka firgit tayi tafarka.
mama tsaye take bakin k'ofa tace yanzu dan gidanku zarah bacci kikeyi kinbar mana gida bud'e?
Zarah mik'ewa tayi tace wlh mama ban san lokacin da bacci yad'aukeniba kiyi hak'uri.
tsaki mama tayi tace kullum bakida aiki saidai ayi hak'uri ke da ace bamu hak'uri da ke ai da tuni na 6allaki, ni kizo kikwaso mun kwanika inraba abincin.
zarah tace to mama sannan tabi bayan mama takwaso kwanuka.
Zarah bayan ta gama cin abincinta alk'ur'ani tad'auko tana bitar hardar da zata bada islamiyya har aka kira sallah la'asar tayi sannan tashirya taje d'akin mama tace mama zan tafi islamiyya.
mama harararta tayi tace ke ni banma yarda dakeba anya ma islamiyya kike zuwa? ko dai wajen wannan malamin naku kike zuwa.
zarah raurau tayi da ido tace wlh mama babu inda nake zuwa sai islamiyya.
mama tace eh ai dan kihad'u da shi islamiyyar saisa kike zuwa,
zarah tace a'a wlh mama.
mama tace munafuka kawai kedai kika sani ahaka dai zaki k'arata ni tashi kiban waje.
zarah tashi tayi tafita.
ko da taje islamiyya lokacin ajinsu har anfara taruwa kowa zaune yake yana bitar hardarsa kafin malam yashigo.
sit d'in gaba tazauna kusa da k'awarta khairy kasancewar nan ne wajen zamansu tare da mik'a ma khairy hannu suka gaisa.
khairy kallon zarah tayi tana murmushi tace yau dai na rigaki Zuwa.
itama zarah murmushi tayi tace nima dai nayi mamakin ganinki dawuri
khairy tace ai infad'amiki tun d'azun ina nan ina koyon harda kafin malam bello yashigo kedai nasan kinsha taki hardar.
murmushi zarah tayi tace kedai kicigaba da haddarki.
suna cikin bita malam bello yashigo idanuwansa akan zarah,
suna had'a ido dasauri zarah tajanye idonta, khairy murmushi tayi ahankali tace malam bello yau sabon yadi yasa nasan kuma saboda ke ne.
harararta zarah tayi tace wlh zan fad'a masa..... muryar malam bello suka tsinkayo ya ce khairy surutu kukeyi ko?
khairy tace a'a malam muna wani nazarine.
yace toh ya isa haka, kallonsa yamaida ga 'yan aji yace duk Wanda yasan baiyi hadda ba toh yafita waje dan kar ku6ata min lokaci.
nan aji yayi shuru kowa yafara raba ido, chan wasu mata hud'u suka tashi suka fita.
malam bello kallon zarah yayi yace kufara yau sit by sit zan bi saboda k'urewar lokaci.
nan layinsu zarah suka fara malam bello yana kallon bakin kowa har suka gama gyara biyu yayi musu sannan yacigaba da kar6ar na sauran har aka gama sannan yayi musu k'ari lokacin tashi yayi akayi addu'a.
zarah jerowa sukayi da khairy suna tafiya d'ago kan da zatayi taga malam bello ya tsareta da ido murmushi tasakar masa sannan suka cigaba da tafiya.
khairy da take kallonsu tana murmushi tace wlh k'awata soyayyarku da malam bello tana burgeni.
zarah murmushi kawai tayi sannan suka cigaba da tafiya har sukazo inda suke rabuwa sukayi sallama sannan zarah tacigaba da tafiya.
Zarah lokacin da tazo k'ofar gida mota tagani tsaye batare da takalli nacikin motarba tawuce zata shige gida.
muryar yaya rauda ce tajiyo tana kiranta nan tatako tanufi wajen motar daga nesa kad'an tatsaya takalli yaya rauda da take zaune gaba tace yaya Rauda gani.
ledace tamik'a mata tace shigar min da wannan gida, kar6a zarah tayi har zata tatafi taji mutumin yace sannu ko 'yan mata,
zarah bata tankasaba tawuce zata tafi yaya zarah tace ke dan ubanki bakiji ana miki magana?
zarah kallon mutumin tayi da yatsareta da ita yana murmushi, fuskarta a d'aure tace ina wuni? bata jira ya amsaba tawuce tashige gida tana jiyo yaya rauda tana ta fad'a..
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Sak'on gaisuwata agareku a duk inda kuka kasance *My hafnan, Mamansadiq nd Mrs Dawud* I heart you allπ_
_*My blood sis Aufana yau ranar takice dan haka na mallaka miki wannan page d'in, ina so kisani sonki a cikin jinin jikina yake Allah yabarmu tareπ*_
page 9⃣
Saurayin yaya raudane yashiga lallashinta yace haba baby menene kuma nafad'a a ciki? ni wlh k'anwar ma taki ta burgeni.
Yaya Rauda tace hmm baby kenan bakasan wannan yarinyar ba ai kwata-kwata ita ba wayaiya bace.
murmushi yayi yace har ina shirin ince ina ciki.
wani irin kallo Rauda tayi masa tace k'anwar tawa?
murmushi yayi yace eh man toh menene?
Rauda ta6e baki tayi tace ai wlh ba zai yuwu kajefi tsuntsu biyu da dutsi d'ayaba dan haka abar ma maganar nan baby, yanzu idan katafi sai yaushe zaka dawo?
cije le6e yayi tare da jingine kansa a sit d'in da yake zaune sannan yace 1 week kawai zanyi cike da tsokana yace kinsan matata kwana biyu nayi missing d'inta.
Rauda d'aure fuska tayi tace haba Alhaji Munnir wai meyasa kake min irin haka.
murmushi yayi yace sorry dear kinsan akwai aikin da zanje inyi, yanzu dai fatana kikular min da kanki har indawo.
Rauda tace kar kadamu dear insha Allahu zaka dawo kasameni yadda kabarni,
murmushin jin dad'i yayi yace yauwa baby nagode, 10k yad'auko yamik'a mata yace ga wannan kirik'e kafin indawo,
Rauda kar6a tayi tace nagode baby Allah yamaido min kai lafiya
yace Ameen dear, nan sukayi sallama.
Rauda ba ko sallama tashiga gida kallon zarah tayi da take hura wuta tace ke ina ledar da nace kishigo min da ita?
zarah batare da ta kalli Rauda ba tace tana d'akinmu, Mama da take cikin d'aki jin muryar Rauda yasa tafito tana washe baki tace a'a 'yar albarka ashe kece kika dawo, tun jiya muna ta zuba ido ammah shuru.
Rauda yamitsa fuska tayi tace ammah mamanmu kinsan dai duk ma inda naje toh zan dawo.
Mama tace hakane saidai duk abinda kuke nafison inganku kun dawo gida komai dare kun kwana.
Yaya Rauda batare da tace komai ba tawuce tashige d'akinsu.
wannan 'yar maganar da mama tayi zarah taji dad'inta sosai domin duk abin mama toh tanaso taga yaran nata sun kwana a gidansu, saidai duk maganar da zatayi musu Yaya Rauda idan tasa kanta waje take kwana, idan ma iyayen sunyi magana sai tabasu kud'i tarufe bakin.
Mama kallon zarah tayi tace tashi kije kikar6o min 500 wajen Rauda kizo kisiyo taliya a Zuba naga ruwan ya kusan tafasa,
zarah tace toh mama.
tana shiga d'akin kallon Rauda tayi da take shirin shiga wanka tace Yaya Rauda mama tace kibada d'ari biyar asiyo taliya.
Rauda tace mik'o min jakkata, zarah zuwa tayi tad'auko jakkar tabata nan Rauda tamik'o mata kud'in sannan tashige wanka.
Zarah wajen mama tadawo tace mama guda nawa za'a siyo.
Mama tace siyo biyu sai kikawo min canjin, zarah tace toh sannan tatafi.
_*After 2 weeks later*_
Zarah ce zaune tana tsifar kanta, wayartace tashiga ringing nan tad'auko ganin sunan malam Bello da yabayya a screen yasa tayi picking tare da yin sallama,
daga chan 6angaren ya amsa mata, nan suka gaisa, sannan malam Bello yace dear gani a k'ofar gidanku kifito inganki please.
zarah jim tayi nad'an lokaci sannan taduba agogo taga k'arfe biyar d'in marece. muryasa taji yana cewa zarah ya kikayi shuru ko bakiso nazoba?
zarah tace bahaka bane malam gani nan zuwa batare da tajira jin abinda zai ce ba takashe wayarta,
nan ta tufke kanta da ribbon sannan tajanyo hijab tasaka saida talek'a ganin ba kowa tsakar gida yasa tayi hamdala sannan talalla6a taficce.
A k'ofar gida tasamesa tsaye ya zuba ido domin yaga ta ina zata fito, suna had'a ido dasauri zarah taduk'ar da kanta k'asa tare da yi masa sallama.
fuskar malam Bello d'auke da murmushi ya amsa mata yace zarah na tadoki ko batare da nasanar da ke zuwana ba.
zarah ahankali tace bakomai malam nan tagaishesa ya amsa,
kallon da yakeyi mata duk sai ya gundureta tad'ago kai tad'an kallesa,
murmushi yasakar mata yace kiyi hak'uri wlh ji nayi yau idan ban gankiba ba zan samu sukuniba tunda ko a islamiyya 6oyemin kanki kike bakya ko bari mugaisa, kinsan dai yadda nake sonki.
Zarah murmushi tayi batare da ta ce komai ba.
malam Bello yace shurun da kikeyi fa yana cutar da ni dan Allah kimin magana.
zarah d'ago kai tayi takallesa har ta bud'e baki zatayi magana sai ganin Abbah sukayi tsaye.
A tsorace zarah takallesa bakinta yana rawa tace Abbah sannu da zuwa, wani irin kallo Abbah yawurga mata.
malam Bello dasauri yaduk'a tare da cewa Abbah barka da rana ina wuni?
Abbah yace da ace ban wuniba da ka ganni?
Me yakawoka wajen 'ya ta? duk hure mata kunne da kakeyi a islamiyya bai ishekaba sai ka biyota gida?
malam Bello kansa a k'asa yace kayi hak'uri Abbah wlh ba haka bane,
Abbah yace toh yaya ne?
Malam Bello yace wlh ni tsakani ga Allah son zarah nake kuma ina da burin aurenta.
Abbah yace a haka? Minene aikinka?
Malam Bello yace eh toh gaskiya ni karatu nake ammah ina tsare shago ana biyana.
Abbah yace kana karatu ammah dan rigima kace kana son 'ya ta toh bari kaji d'iyata ba irinka zata auraba domin kwata-kwata baku daceba, bakada abinda zaka iya aurenta dan haka tashi kabar min k"ofar gida.
malam Bello yace kayi hak'uri Abbah insha Allah zan iya rik'on zarah.
Zarah tace dan Allah Abbah kayi.... tsawa Abbah yadaka mata yace wuce kishiga gida ko ranki ya6aci, dasauri zarah tawuce tashige gida tana hawaye.
Abbah kallon malam Bello yayi yace tashi kabar nan kuma kar ka kuskura kak'ara takomin k'ofar gida, Abbah na gama fad'in haka yawuce yashige gida. .
malam Bello yamik'e tsaye daga tsugunnen da yake yatafi yana jin ba dad'i cikin ransa.
Zarah saman katifarsu tafad'a tafara rusar kuka, Abbah ne yashigo gidan yana ta fad'a.
mama ce tafito daga d'aki tace malam lafiya?
Abbah yace ina fa lafiya wlh yarinyar chan idan batayi wasaba sai na sa6a mata a cikin gidan nan, mama tace wa kenan?
Abbah yace zarah mana wai ace tarasa Wanda zata tsaya da shi sai talakka d'an uwanta da baida komai inba wahalaba babu abinda zata tsinta a wajensa.
mama tace hmm malam kenan ai wlh indai zarah ce toh kad'an kagani ita kwata-kwata batada tunani ai ni wlh ban ma San lokacin da tafitaba da bazan bartaba,
mama wucewa tayi tanufi d'akinsu zarah a bakin k'ofa tatsaya tare da d'age labulen d'akin, kallon zarah take da taketa faman kuka cikin fad'a tace ke dan kin raina ni watau da narabaki da wancan yaron baku rabuba ko? shine yanzu dan anyi miki magana shine kike kuka, toh bari kiji ko da ace zakiyi kukan jini bazaki auresaba kuma dole kurabu inma bakiyi hankaliba islamiyyar ma sai inhanaki zuwa, butulun banza inba ma asaraba me zakiyi da d'an uwanki talakka duk kyaun naki baida amfani wlh, hatta k'anwarki tafiki sanin daidai.
zarah dai tana jin mama tana ta fad'anta har tagama tatafi itadai kuka take.
kiran Sallar magrib da akayine yasa tatashi taje tayo alwallah har lokacin fuskarta babu walwala.
bayan sallar isha'i kwance take saman katifa gefenta Aysha ce kunnenta d'auke da earpiece da waya a hannu da alama kallo takeyi.
zarah wayarta tad'auko talalubo number d'in malam Bello takirasa, tana fara ringing yakashe yakira,
zarah tana d'aga wayan yayi mata sallama.
jin muryarsa yasa taruntse ido tana jin wani iri acikin zuciyarta sai a lokacin taji kunyar abinda Abbah yayi masa.
muryarsa ta tsinkayo yana cewa hello zarah bakya ji na?
zarah cikin muryarta da tadashe saboda kuka tace malam dan Allah kayi hak'uri akan abinda yafaru
murmushi malam Bello yayi yace kar kidamu zarah wlh bakomai kawai dai ina tunanin anya zan iya rabuwa da ke? domin ni kaina nasan ina miki wani irin mahaukacin so.
zarah ajiyar zuciya tayi tace malam Bello wlh nima ina sonka kuma ina ji a raina akwai lokacin da iyayena zasu amince mana muyi aure.
malam Bello yace hakane ammah ni fatana kitaimaka kirik'e min amanar kanki har ingama karatuna muyi aure.
zarah tace kar kadamu nariga na amince maka kuma insha Allahu idan da rabo zamuyi aure.
cike da jin dad'i malam Bello yace nagode sosai zarah Allah yamallakamin wannan tauraruwar yarinyar.
dariya zarah tayi daga nan suka shiga yin hira, sai da sukayi kusan awa d'aya sannan sukayi sallama suka kashe wayoyinsu kowa yana jin dad'i a ransa, nan zarah tanemi damuwarta tarasa.
________________
Gimbiya Sumayya lokacin da jirginsu ya safka zinat ce tazo tatarbeta cike da farin ciki suka rungume juna daga nan suka nufi inda motar zinat take suka shiga suna ta hira, zinat tace baby yanzu gida zamu wuce ko boutique din zan kaiki kifara ganowa? Sumayya jingine kanta tayi a sit din da take zaune tace dear muje gidanki kawai yanzu agajiye nake, murmushi zinat tayi tace toh ranki yadad'e angama.
dariya sukasa gaba d'ayansu Sumayya tace abun ma har da tsokana kenan, daidai lokacin tayi horn maigadi yazo yabud'e mata gate tacinna motarta a ciki a parking space tayi parking sannan suka fito suka d'unguma cikin gida.
bedroom suka wuce Sumayya tafad'a saman gado tare da cewa wash.
dariya zinat tayi tace baby keda kikazo ta flight ammah shine har kin gaji? kokuma namance ku jinin sarauta bakwa motsawa dayawa saidai ayi muku komai.
harararta Sumayya tayi tace ke dai kika sani da tsokana, ni yanzu dai taimaka kisa ahad'a min ruwan wanka infarayi tukun,
zinat mik'ewa tayi tanufi k'ofa tafara kwalah ma 'yar aikinta kira, dasauri tazo tare da russunawa k'asa ranki yadad'e gani, zinat yamitsa fuska tayi tace shiga toilet kihad'a ruwan wanka, dasauri tatashi tashiga tahad'a ruwan sannan taficce tabar d'akin.
Zinat kallon sumayya tayi tace baby kitashi kije kiyi wankan ko intaimaka miki,
sumayya mik'ewa tayi tad'auki towel tacire kayan jikinta tawuce tashiga bathroom.
bayan ta fito kwalliya tayi tashirya cikin English wears riga da skirt tafeshe jikinta da turare, kallon Zinat tayi da tatsareta da ido tace dear wannan kallon fa?
Zinat tace Mrs yarima kinyi kyau sosai.
gimbiya sumayya ta6e baki tayi tace har kin tunomin da wannan d'an jin kan, nidai muje inyi lunch domin yunwa nakeji yanzu.
Zinat mik'ewa tayi suka fito suka nufi dining nan Zinat tayi serving d'insu suna ci suna hira.
bayan sun gama saman 3 seater suka dawo suka yada zango, sumayya wayarta tad'auko tace bari inkira su ummah inshaida musu na iso lfy tun kan surigani kira,
Zinat tace hakan fa zaifi.
nan sumayya takira sultana sadiya da dada tafad'a musu ta sauka lafiya.
bayan sumayya ta gama wayar zinat tace toh baki kira miskilin mijin nakiba.
ta6e baki tayi tace kibarsa kawai wannan d'an rainin wayaun ai wlh indai bashi yakiraniba toh ba zan kirasaba _(lallai sumayya kin mance wanene yarima suhail)_
Zinat tace ai wlh kina ma hak'uri da shi ai ni kwata-kwata ban tunanin zan iya zama da irin su mijinkiba.
sumayya tace hmm nima dai dan ina sonsa ai da ban iya zama da halinsa, ke kafin fa intafo jiya saida mukayi drama, yanzu dai tashi muje inga boutique d'in dan na k'agara ingansa.
zinat murmushi tayi tace baby ai nad'auka sai ansallameni sannan zamuje kinsan fa nayi missing d'inki dayawa.
sumayya 'yar dariya tayi tace kidai bari mudawo tukun dan ni yanzu hankalina ya fi karkatuwa da zuwa.
zinat tace ke Alhaji Jamilu fa yana nan Abuja ai kinsan na fad'a miki.
sumayya yamitse fuska tayi tace wanene kuma jamilu,
harararta zinat tayi tace ammah fa ke 'yar iskace baby yanzu Alhaji jamilu kika mance?
yamitsa fuska sumayya tayi tace hmm zinat kenan ai ban mance da shi ba dan mugunta kikaja nabasa kaina shine namijin da yafara sanina,
dariya zinat tayi tace ammah ai lokacin mun samu abinda mukeso, ke ni yanzu haka in kinason ganinsa nasan gidansa sai muje inrakaki.
sumayya harararta tayi tace Allah yakyauta ke nifa yanzu namiji Indai ba mijinaba bana jin zan k'ara amince ma wani,
zinat da mamaki take kallonta tace saboda me? sumayya cikin rashin damuwa tace haka kawai mazan basu gabana.
zinat tace toh wlh ko da sau d'ayane ki amince muje gidan Alhaji jamilu domin yana ta tambayata ke, kinga mun k'ara jari.
sumayya mik'ewa tayi tsaye tace nidai kitashi muje ko mun dawo domin inaso inhuta.
zinat tace toh nima dai kenan yau ba tani akeba, sumayya rik'o hannunta tayi tace haba baby ai ke ta dabance nima fa nayi missing d'inki, muje dai mudawo ai muna tare daga yau har next week.
A motar Zinat suka fita ko da sukaje boutique d'in sumayya ta yaba sosai da kayan da zinat tazuba ciki, nan zinat ta gabatar da sumayya ga ma'aikatan wajen cike da girmamawa suke gaisheta sumayya a wulak'ance take amsawa nan tad'an d'auki kaya set biyu tace tana sonsu.
daga nan suka zagaye gari sai dare sannan suka koma gida, gaba d'ayansu saman gado suka fad'a suna hutawa, zinat kallon sumayya tayi tace baby muje muyi wanka,
sumayya tafara mik'ewa sannan zinat atare sukaje sukayi wankan bayan sun fito su dukansu d'aure suke da towel suna rungume da juna nan suka nufi saman gado suka kwanta........
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_~Sak'on gaisuwa agareku masoya a duk inda kuka kasance inaso kusani Sis Nerja'art tana yinku overππ~_
_*My hafnan nd My leemah H.A.S yau Ranar takuce, page d'innan nakune kuyi yadda kukeso dashi sai wanda kukaso zai karanta, wlh ina ji da ku sosai a cikin zuciyana, Allah yabarmu tareπ*_
page 1⃣0⃣
_*After 3 days later*_
sumayya ce kwance tayi matashin kai da cinyar zinat tana waya da ummanta bayan sun gama sumayya d'aga kai tayi takalli zinat da take ta dannar waya da alama chart takeyi, tace baby mutuminki fa har yau bamuyi wayaba.
murmushi zinat tayi tace toh sai me minene abun damuwa tunda dai bai nemekiba toh kema kisharesa, ke ni jiya da nafita na ga Alhaji jamilu kuma nafad'a masa muna tare wlh bakiga yadda ya rikice min ba wai sai ya biyoni ya zo wajenki.
murmushi sumayya tayi tace ke dai kina son jona ni da Alhaji jamilu,
zinat tace toh ai nasan zamu samu cash masu tsoka a wajensa, ke nifa inda ke da kud'i a nan nafi wayau.
dariya sumayya tayi tace nima haka dear, wlh dan dai ina tsoron kar yarima yagane da nabi maganarki naje munyi sharholiyarmu da shi inyagi abinda nayaga.
Zinat tace haba baby kefa matsalata da ke kenan taya kike tunanin mijinki zaya gane tun farko ma bai ganeba sai a yanzu?
Sumayya jinjina kai tayi alamun gamsuwa sannan tace toh yanzu dai ta ina zamu fara?
zinat murmushi tayi tace ai ya bani number d'insa bari kawai inkirasa sai kuyi magana ko kuma inbaki number d'insa.
dasauri sumayya tagirgiza kai tace a'a kirawo min shi dai da wayanki kinga yanzu nayi aure kar wataran yakirani gaban mijina.
zinat tace hakane nan tafara dialing d'in number d'insa tanaji yad'aga dasauri tasa ma sumayya a kunne, jin muryarsa yasa sumayya yin murmushi tare da kallon zinat.
zinat alama tayi mata na tayi magana.
sumayya kwantar da muryar tayi tace Alhajina dafatan kana lafiya.
Alhaji jamilu da yake kwance jin muryar sumayya da yayi yasa yamik'e zaune tare da cewa sumayya daman kina nan?
sumayya murmushi tayi tace aikam dai ina nan Alhaji ya gida ya kake?
Alhaji jamilu cike da jin dad'i yace lafiya lou baby gaskiya naji dad'in jinki da nayi wlh daman nadad'e ina cigiyarki wajen zinat.
sumayya tace ayya kar kadamu yanzu ai gani.
yace baby toh inaso muhad'u ya za'ayi?
sumayya kallon zinat tayi sukayi murmushi sannan tace toh katuron address d'inka sai inzo
cike d's jin dad'i Alhaji jameel yace yanzu ko zan turo miki ammah please kizo yau,
sumayya tace kar kadamu zan shigo da anjima, yanzu dai ina jira sai ka turo.
nan sukayi sallama suka kashe wayan.
sumayya kallon zarah tayi da tatsareta da ido tace baby nidai ko da na je gaskiya bana iya bari yayi sex da ni.
zinat zaro ido tayi tace haba baby saboda mi? toh kud'in fa?
murmushi sumayya tayi tace kar kidamu dolene ma sai na samo mana kasonmu kin d'auka a banza chan baya yamoreni?
dariya zinat tayi tace toh ai lokacin ma mun yagi kasonmu,
sumayya tace a yanzu ma dole yabamu, bari ma kiga inje inyi wanka, tana gama fad'in haka tamik'e tafara cire kaya.
bayan ta fito wanka shiryawa tayi cikin riga da skirt na atamfa sannan tayafa d'an k'aramin veil, kallon zinat tayi da tatsareta da ido tayi murmushi tare da jujjuyawa tace baby ya kika ganni?
zinat ma murmushi tayi tare da mik'ewa tace kinyi kyau sosai anya kau Alhaji mukhtar zai barki?
dariya sumayya tayi tace muje dai kiyi dropping d'ina.
wani dank'areren gida aka hangame musu gate suka shiga gefe guda zinat tayi parking sannan takalli sumayya da take bin gidan da kallo tace haba baby kema fa gidanki ya tsaru naga sai kallon wannan kikeyi
murmushi sumayya tayi tace balaifi yayi min kyau.
zinat tace toh kifita kishiga ni bari inje koma dai me kenan sai kindawo.
sumayya tace toh tare da bud'e motar tafita nan zinat taja motarta tabar gidan.
ahankali sumayya take takawa tanufi k'ofar da zata sadata a cikin gidan cikin karambani take bin hanya saidai ganinta tayi a parlour lokacin Alhaji jamilu yana kwance saman 3 seater yana kallo, jin anbud'e k'ofane yasa yad'ago ganin sumayya yasa yamik'e dasauri yanufi inda take tsaye, rungumeta yayi yace oyoyoo babyna.
sumayya janye jikinta tayi daga nasa tana murmushi tace baby kwana dayawa.
rik'o hannunta yayi suka zo saman 3 seater suka zauna har a lokacin idonsa cikin nata yace baby ban d'auka zan k'ara ganinki a yanzu ba saboda nisan da kikayi min kin 6oye.
sumayya murmushi tayi tace no ni ina gefe kune dai siyasa ta6oye.
Alhaji jamilu hannunsa na sark'e da nata yace mu muna gefe baby inkinson ganinmu zaki ganmu dan ba irinku muke 6oye mawaba, yanzu dai taso mushiga daga ciki.
sumayya mik'ewa tayi tabi Alhaji jamilu bedroom d'insa suka yada zango saman gadonsa, rungume yayi yakai bakinsa cikin nata suka fara kissing d'in junansu inda hannuwansa suke yawo cikin rigarta.
sumayya dai kawai tana biye masane har yarabata da kayan jikinta romance d'in sunansu suke son ransu daga k'arshe sumayya da taga yana shirin shigarta tadakatar da shi.
da mamaki Alhaji jamilu yake kallonta yace baby saboda me zaki hanani? Please kibarni inyi kinsan fa nakwana biyu banji d'umin jikinkiba.
murmushi sumayya tayi tace dear kayi hak'uri just dai muyi romance d'in juna ammah bana buk'atar sex, ganin yana shirin yin magana yasa tarufesa masa bakinsa da nata cike da kwarewa itama tadinga sarrafasa saida taga ya gamsu batare da sex ba sannan tabarsa.
Alhaji jamil kallonta yayi da take shirin tashi yace baby ina zakije?
murmushi sumayya tayi tace gida zan koma yace haba dan Allah kiyi min ko da kwana d'ayane
sumayya tace a'a Alhaji tafiya dai zanyi inyaso wani lokacin sai indawo.
Alhaji jamil ba dan yasoba yace toh atare sukaje sukayo wanka, duk yadda taso tatafi dawuri hanata yayi saida tayi dagaske sannan yad'auko yamaidata gidan zinat.
A mota ma bai bartaba rungumeta yayi inda hannuwansa suke yawo a cikin rigarta saida yagaji dan kansa sannan yabarta, cheque d'in 1.5 million yarubuta mata yamik'a mata.
cike jin dad'i sumayya takar6a tare da yin godia sannan sukayi sallama tafito daga motar tana d'aga masa hannu har yatafi sannan tashiga gida.
A parlour tatarar da zinat zaune da d'an k'aramin veil a gefenta da alama itama bata dad'e da dawowaba.
daga gefen zinat tazauna tare da cewa wash wlh na gaji.
dariya zinat tayi tace ya dai baby? ai nasan Alhaji jamil ba zai ta6a barinki hakanan ba.
ta6e baki sumayya tayi tace ke ni kawai dai na amince masane ammah banbari yayi sex da ni ba, wlh yarimana yafisa iya sarrafa mace saisa nace miki bana tunanin akwai namijin da zan iya jin dad'insa kamar yarima.
ta6e baki zinat tayi tace haka dai kike gani ammah wlh inkina so zan iya had'aki da guys d'ina zakiga banbanci sosai
sumayya tace bama naso.
zinat tace yanzu dai babu abinda yabamu kenan?
sumayya bud'e jakkarta tayi tafiddo cheque d'in tamik'a mata.
zaro ido zinat tayi tace baby yanzu Alhaji jamilu yabaki kud'in nan batare da yayi miki komai ba?
murmushi sumayya tayi tace kawai dai munsha minti ammah babu abinda yashiga tsakaninmu, ke ni sai bayan natafi nake tunani ai da nayi ma yarima magana da zai bani saboda duk abinsa ammah baya da rowa
zinat yamutsa fuska tayi tace ai k'arama da bakiyi masa magna ba dan banason mutumin nan saboda wulak'ancinsa.
sumayya tace zinat ammah wlh yarima baida rowa.
zinat ta6e baki tayi tace matsalarsa, nidai ynz tashi muje mukwanta inyaso gobe sai muje muciro kud'in mud'ibi kasonmu sai muyi order d'in wasu kayan da sauran kud'in, nima kinga ga 1 million nan d'azun nakar6esu wajen wani guy d'ina.
dariya sumayya tayi tace ai daman tunda nadawo naga veil d'inki a gefe nasan kin fita.
zinat tace ai ina dropping d'inki ban dawo gidanba nawuce chan, yanzu dai nidai agajiye nake muje daga ciki.
Tun daga ranar sumayya idan Alhaji jamilu yakirata take zuwa gidansa ammah bata bari yayi sex da ita tun yana k'orafin har yagaji, ahaka tacika 1 week a garin.
zinat rok'onta tayi kar takoma gida dakyar tasamu sumayya tazauna domin tak'ara ko da kwana biyu ne ammah saida takashe wayarta gudun kar su dada sukirata.
____________
Yarima suhail tunda sumayya tatafi bai damuba harkar gabansa kawai yakeyi domin a ganinsa da ita da babu basuda banbanci, ko da sau d'aya bai d'aga wayaba da zumar yakirata.
ahaka har tayi 1 week ammah bata dawoba,
Dada jin sumayya shuru bata dawoba yasa takirata a waya ammah wayanta a kashe dan haka ta aika aka kira mata yarima.
yarima yana kwance a 3 seater kujerar da take opposite d'insa Shaheed ne zaune duk yadda shaheed yaso suyi hira da yarima suhail ammah yarima ya k'i,
ganin haka yasa shaheed yaja bakinsa yayi shuru dan yasan halin mutumin nasa har korarsa ma zai iyayi, gajiya yayi da shurun daga k'arshe yakalli yarima da yazuba ma ceiling ido da alama tunani yake, yasheed yace yarima meyake damunkane?
shuru yarima yayi yakyalesa.
murmushi shaheed yayi yace ranka yadad'e ko kana tunanin gimbiyarkane.
yarima juyowa yayi yawurga ma shaheed harara sannan yamaida kansa ga kallon ceiling.
dariya ce takama shaheed ammah yadanneta yace Allah yahuci zuciyarka.
K'ofar d'akin aka shiga knocking, Shaheed ganin yarima baida niyar yin magana yasa yabada izinin ashigo.
wata baiwace tashigo dasauri tazube k'asa a bakin k'ofa tace ranku yadad'e Allah yaja da ran yarima mai jiran gado, daman sultana dada ce tace tana nemanka.
shaheed kallon yarima yayi yaga baida niyar yin magana kuma yana jin ta, shima bakinsa yaja yayi shuru.
saida aka d'au kusan minti ukku tana tsugunne sai chan yarima yad'aga mata hannu batare da ya kalletaba alamun tatafi.
dasauri tak'ara duk'ar da kanta tace ranka yadad'e afito lafiya sannan tatashi tafita tabar d'akin.
shaheed kallon yarima yayi yaga baida Niyar tashi, cikin ransa yace yau abun ya motsa kenan, nan yacigaba da kallon ball d'insa.
saida akayi kusan minti goma sannan yarima yamik'e tare da d'auko alkyabbarsa yasaka, batare da yayi ma shaheed maganaba yafita yabar d'akin,
nan mutane sukayita zubewa suna kwasar gaisuwa yau ko d'aga musu hannunma bayayi ahaka har ya isa turakar dada.
ko da yashiga dada tana kishingid'e anayi mata tausa, ganinsa yasa duk suka zube suna kwasar gaisuwa, tsaye yarima yayi har saida suka tashi suka ficce sannan yatako yazo yazauna bisa kujerar da take opposite d'in dada.
dakyar kamar bayason yin maganar yagaishe da dada.
dada cikin fara'a da sakin fuska ta amsa masa, gyara zamanta tayi sannan tace yarima daman akan maganar matarkane yaushene zata dawo?
Yarima kallon dada yayi sannan yamaida kallonsa akan wayarsa da yake dannawa cike da jin haushin maganar da dada tayi,
dada zuba masa ido tayi tana kallonsa baida niyar bata amsa,
sai chan yace ranki yadad'e ai nad'auka kunyi magana kinsan lokacin da zata dawo tunda nidai bata fad'amin kwanakin da zatayiba.
dada baki tasaki tana kallonsa har yagama maganar sannan tace suhail kana dai so kacemin bakuyi waya da itaba tunda tatafi.
yarima shuru yayi bai tankaba,
dada tace ammah wlh da kacika marar kirki har yanzu kana nufin baka huceba kenan.
yarima kallon dada yayi tare da yin murmushi yace dada kenan ni ba fushi nakeba, kawai dai nad'auka kinsan lokacin da zata dawone ammah kiyi hak'uri idan maganata ta6ata miki rai,
dada tace toh yanzu nafahimta ammah dan Allah kakirata kaji yaushe zata dawo saboda sati guda tace zatayi ammah yau kusan kwananta takwas.
mik'ewa yayi yace toh dada, bari inwuce ana jira.
dada tace toh shikenan nidai dan Allah kakirata.
yarima baice komai ba yawuce yafita cikin ransa yana cewa saidai kar tadawo indai sai na kirata zata dawo.
Bayan kwana biyu gimbiya sumayya tayi shirin komawa gida lokacin Kwananta goma, Alhaji jamil da zinat su suka kaita airport a chan ma Alhaji jamil yana manne da ita kud'i masu tsoka yabata, har saida sukaga tafiyarta sannan suka bar wajen.
Gimbiya sumayya ko da tadawo da su dada suka tambayeta akan rashin dawowarta k'arya tayi musu akan wai wata matsala ce tatashi akan business d'insu saida tajira komai yakoma normal sannan tadawo.
ko da tadawo sai da takwana biyu batasa yarima a idontaba dan tayi tunani zaizo d'akinta ammah sai gashi tsawon kwana biyu bai zoba.
dan haka da daddare shiryawa tayi taje 6angaren yarima domin ta san Indai ba ita tajeba toh ba zai ta6a zuwa wajentaba saidai idan yana buk'atarta.
lokacin da tashiga yarima suhail yana shirin bacci ko inda take bai kallaba, takawa tayi taje inda yake still dai bai kalletaba sai ma wucewa da yayi yahaye gadonsa yakwanta.
Sumayya cikin ranta tace toh yau kuma naga yadda zamu kwashe da wannan d'an jin kan, binsa tayi saman gadon takwanta gefensa tace my sweetheart ko welcoming d'in ma bazan samuba, tsawon kwana biyu da dawowata ammah ko kanuna ka damu.
yarima suhail batare da ya kalletaba yace ashe kini dawo?
da mamaki sumayya take kallonsa tace au da ba zan dawoba?
yarima bai tanka mataba yajuya mata baya.
sumayya ganin haka yasa tarungumosa ta ba tace haba yarima wai meyasa kake son wulak'antani ko dai bakaji dad'in dawowataba?
yarima banza yayi yakyaleta cike da k'ulewa.
gimbiya sumayya tace haba yarima wlh banason sharewar nan da kakemin.
yarima suhail yace sumayya ai da baki dawoba dan dabakinan hankalina ya fi kwanciya wlh, ni da kin taimaka kin tashi kinkoma d'akinki dan yanzu banason a dameni hutu nake buk'ata.
sumayya cike da k'ulewa tace kai wlh tsiyata da kai bakasan arzik'iba duk yadda mutum zai nemi yakyautata maka sai ka kushesa nifa kawai tausayinka nakeji ganin lokacin da nad'auka bana nan nasan kayi missing d'ina.
Yarima tashi yayi yazauna yana kallonta a wulak'ance yace sumayya me kika d'aukeni? na fa san abinda nakeyi ni a yanzu bana buk'atarki dan haka kitashi kifitarmin daga d'aki,
da mamaki gimbiya sumayya take kallonsa tace yarima ni kake kora? me nayi maka daga dawowata sai kahauni da fad'a?
wani mugun kallo yarima suhail yayi mata tare da nuna mata k'ofa.
tashi sumayya tayi tare da d'aukar alkyabbarta tasaka sannan tace naji zan fitar maka daga d'aki sauk'inma nima ina da nawa d'akin daman taimaka maka zanyi ammah tunda......
tsawa yarima yadaka mata cikin 6acin rai yace I said get out!!!
sumayya ta tsorata sosai da ganin yanayinsa dan haka dasauri taficce tabar d'akin cike da jin haushin wulak'ancin da yarima yayi mata daga dawowarta......
_STORY,WRITTEN &EDITED BY._
*SIS NERJA'AT.*
_COMPILATION BY._
*HAWWA M.U (®EAL $MASHER).*
?ππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
_Jinjina agareki my hafnan ina tayaki murnar fara new novel d'inki *HIBBATULLAH* akowane lokaci kina a ❤ππ» d'ina_
_~Sak'on gaisuwata agareki my blood sis *Aufana* sonki a cikin jinin jikina yakeππ~_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Wannan page d'in nakine Sainah Ummun Meenal uwa tagari Allah yabar mana keπ_
page 1⃣
garin gazban garine mai albarka da yawan mutane yana d'aya daga cikin garuruwan da ake alfahari da su.
sun kasance suna da babbar Masarautar da babu kamarta wajen girma da kyau sarkin garin ya kasance sarki mai adalci duk kud'in mutum bai isa yazalunci nak'asa da shi ba indai har yazalunta labari yazo ma sarki toh sai yad'auki mataki,
sarki umar yana son talakawansa sosai suma suna sonsa abun mamaki wannan sarki ya manyanta domin zai kai shekaru 76 ammah indai ba ka saniba sai kad'auka d'an shekara 50 ne, domin babu alamun tsufa a tare da shi idan dukiyarce ya tara, idan sarautarce yana d'aya daga cikin manyan sarakuna kai intabbatar muku wannan babbar Masarautar ko da me kazo anfika.
Sarki faruk matarsa d'aya dattijuwa dada, saidai abun mamakin duk mulkin nasa ammah 'ya'yansa biyu dukansu maza ne Ahmad shine babba sai k'anensa Abbas sun taso atare sun kasance suna son junansu.
saidai a tsarin mulkin garin indai sarki yahaura shekaru arba'in (40) saman karagar mulki toh d'ansa ba zai ta6a gadon mulkinba saidai babban jikan gidan, saidai idan babu jika namiji shine d'an sarkin yake hawa mulkin
lokacin da 'ya'yansa suka tasa yaza6a musu mata inda Ahmad ya auri d'iyar sarkin agadaz wato sultana Bilkisu, shi kuma Abbas sarki ya aura masa d'iyar d'an uwansa da yamutu yabari wato Sultana Sadiya.
A cikin babbar Masarautar kowa aka fitar masa da 6angarensa.
Suna zaune lafiya da matansu, inda sultana Bilkisu takasance macece mai hak'uri da tawakkali ga ta macece mai kyauta ta kasance mai son jama'a,
inda Sultana Sadiya takasance akasin haka domin bata son talakkawa suna ra6arta dan ma mijinta a tsaye yake sun d'auko hali irin na mahaifinsu, ammah duk da haka taci alwashin ita take da burin tafara haihuwar d'a namiji.
saidai kash sultana Bilkisu ita tafara samun ciki, hankalin sultana Sadiya ya tashi sosai ganin ita ko 6atan wata bata ta6a yiba,
Bayan wata goma sultana bilkisu tahaifi d'iyarta mace murna wajen iyayen ba'a magana hatta ita kanta sultana Sadiya tayi murna ganin ba namiji bane ta haifa.
ranar suna anyi shagali sosai kud'i sunyi kuka tsakanin masarautar gazban da masarautar agadaz anzuba naira sosai a inda yarinya taci sunan dada wato Asma'u ammah ana kiranta da husna.
Bayan shekara ukku Sultana bilkisu tak'ara haihuwa inda tasamu d'anta namiji kyakkyawa domin ita yabiyo kamar antsaga kara murna wajen su sarki ba'a magana hatta su kansu jama'a sun shaida wannan haihuwar domin sarki sadaka yadinga yi da dukiya sosai,
akasin sultana Sadiya da takasa 6oye bak'in cikinta turakar mijinta taje tasameshi a zaune yana ta kiran waya yana fad'a ma mutane, zama tayi gefensa tana kallonsa cike da takaici har yagama wayar sannan yakalleta fuskarsa d'auke da murmushi yace sultana akwai abinda kike buk'ata ne?
sultana sadiya d'auke fuskarta tayi daga kallonsa tace ranka yadad'e meyasa kake murna dan matar d'an uwanka ta haifi namiji kar fa kamance shine zai hau karagar mulki bayan ran sarki,
da mamaki sultan abbas yake kallonta yace sultana ba dai bak'in ciki kike ma d'an uwana ba dai ko?
d'aure fuska sultana tayi tace bak'in cikin me zanyi masa, naga kana ta murna ne mukuma kaduba kaga ko 6atan wata ban ta6a yiba bamu da d'a ko d'aya kuma kyau ace d'an kane zai gaji masarautanan.
sultan Abbas sakin baki yayi yana kallonta har takai aya sannan yace sultana inaso kisan wani abu wlh da zuciya d'aya nake son d'an uwana ban damu da sarautar da d'ansa zai hau ba domin nima d'ana ne sannan da kike magana akan rashin haihuwa inaso kisani Allah shi yake badawa ga Wanda yaso kuma yahana Wanda yaso ban cire rai ba idan da rabo nima zanga tsatsona, dan haka kar ink'ara jin kinyi wannan maganar, kibinneta daga nan da kika yi ta.
Mik'ewa sultana tayi cikin fushi tace daman nasan ba zaka ta6a fahimtaba ammah nan gaba dakanka zaka fahimci abinda nake nufi. wucewa tayi fuuu tafita tabar d'akin.
Sultan Abbas binta yayi da kallo har tafita sannan yagirgiza kai cike da takaicin abinda matarsa tayi yace Allah yashiryeki sadiya.
Ranar suna yaro yaci suna Umar sunan maimartaba ammah suna kiransa da suhail,
suhail yataso cikin gata domin yana samun kulawa sosai a wajen iyayensa da kakanninsa hatta shi kansa sultan Abbas yana ji da d'an nasu,
akasin sultana sadiya da ta tsanesa bata d'aukarsa sai idan gaban su Dada ne nan take nuna tana sonsa sosai, ammah a cikin zuciyarts ji take ina ma ace yamutu.
ahaka yataso cikin gata tun yana shekara ukku maimartaba yakesawa ad'aukosa akawo sa fada yazaunar da shi kusa da shi saisa suhail yataso ya shak'u da kakansa sosai.
Bayan shekara biyu sultana sadiya tasami ciki murna wajensu da wajebnsu sultan Ahmad ba a magana,
kulawa sultana sadiya take samu sosai daga wajensu maimartaba da mijinta hatta ita kanta sultana bilkisu tana bata kulawa sosai.
inda sultana sadiya take addu'a akan Allah yasa tahaifi d'a namiji.
inda itama sultana Bilkisu take d'auke da d'an k'aramin cikinta.
bayan wata tara sultana sadiya tahaifi d'iyarta mace ta yi bak'in ciki sosai ammah daga baya tahak'ura, murna wajen su maimartaba ba'a magana kowa ya nuna farin cikinsa,
ranar suna yarinya taci suna sumayya, anyi shagali sosai anci ansha.
inda sultana sadiya taci alwashin ta kowane hali sai d'iyarta ta auri sarki mai jiran gado .
bayan wata ukku sultana bilkisu tahaifi d'iyarta mace inda taci sunan mahaifiyarta wato Rahama,
tun daga lokacin babu wadda tak'ara ko da 6atan watane, sumayya da Rahma sun taso a tare komai nasu d'aya bacci kawai yake rabasu.
Yarima Suhail duk halin maimartaba yad'auko yatashi mutum ne mai tausayi kuma mai girmama na sama da shi saidai ya kasance bai da son hayaniya miskiline na sosai baya shiga abinda bai shafesaba baya da yawan fara'a sosai saidai ga wanda bai sansaba zai masa kallon mutum mai girman kai.
In ko kagansa a fada toh maimartabane yasa yaje ammah shi kwata-kwata baida burin yin sarauta, ko da dakagansa komai nasa irin na sarauta yakeyi.
tun da yataso abokinsa d'aya d'an waziri wato shahid tare suka taso tun suna yara sunyi makarantar arabi da boko a garinsu.
bayan sun gama secondary yarima suhail yanuna yanaso yafita waje yayo karatunsa, anyi daga sosai da maimartaba afin ya amince domin cewa yayi shi da zai gaji sarauta mezaisa yafita waje karatu, daga baya dai dakyar aka samu maimartaba ya amince inda yarima yaje india yayi karatunsa na likitanci inda yakaranci surgeon.
bayan shekara biyu akasha bikkin Gimbiya husna inda ta auri d'an chairman d'in garin anyi shagali sosai anyi bikkin da ba a ta6a irinsaba a garin, inda husna tatare a gidan mijinta
yarima suhail yaso yazo ayi bikkin da shi ammah iyayensa suka hana sukace yazauna yayi karatunsa.
Gimbiya Sumayya da Gimbiya Rahama sun shak'u da juna sosai saidai suna da banbancin halayya sumayya tana da wulak'anci sosai kuma ta tsani talaka yara6eta bata abota da kowa sai wanda yakasance jinin sarauta ko d'an wani attajiri.
akasin Gimbiya Rahama da takasance mai son jama'a kuma bata da wulak'anci kowa natane abinda yake had'ata fad'a da sumayya kenan ko a school.
Bayan shekara hud'u yarima suhail yakammala karatunsa yadawo k'asarsa ta haihu ya k'ara girma da kyau miskilancinsa ya k'aru da kagansa ka ga jinin sarauta,
murna wajen maimartaba da iyayensa ba a magana hatta kansu jama'ar gari sunyi murnar dawowarsa.
ba kamar abokinsa shahid da yayi missing d'insa sosai.
gidan sarautar hidima akayi sosai inda dukkan ma'aikatan gidan suka had'u adafa wancan asafke ad'aura wancan,
walima akayi ta azo agani hatta kansu talakawa sun ci sun sha,
Sumayya tun da tad'aura idonta akansa tace ai tayi miji ba zata auri kowaba sai shi ko da taje ma mahaifiyarta da maganar itama tayi murna sosai domin itama burin da take da shi kenan a rayuwarta inda tabata shawara akan taje tasanarwa dada.
sumayya ta d'auki shawarar da mahaifiyarta tabata dan haka tawuce tanufi 6angaren su maimartaba lokacin da tashiga d'akin dada zaune take saman kujera gefenta dama da haggu duk kuyangine suna ta mata hidima,
sumayya bisa kujerar da kaka take zaune taje tazauna tace ranki yadad'e 'yar tsohuwarmu Allah yak'ara miki tsawon kwana,
dariya dada tayi tace Ameen gimbiya ganinki da nayi haka nasan bakinki yana d'auke da magana,
sumayya murmushi tayi tace tabbas hakane ranki yadad'e akwai abinda yake tafe da ni.
kaka sallamar kuyanginta tayi duk suka fita sannan tatattara kallonta ga jikartata cike da kulawa tace ya ke sumayya inaso kifad'a min abinda yake tafe da ke nikuma indai baifi k'arfina zan taimaka miki.
sumayya duk'ar da kanta tayi cike da kunya tace dada daman akan yaya suhail ne,
murmushi kaka tayi jin an ambaci nagaban goshinta tace ina jinki me suhail d'in yayi?
sumayya tace babu abinda yayi saidai nice wlh dada tun tuni nakeson yaya suhail kuma ina tsoron intaresa da maganar dan nasan zai iya min wulak'anci saisa nace bari infara samunki da maganar wlh dada ina sonsa har cikin raina.
dada tunda sumayya tafara maganar kasa rufe baki tayi saboda jin dad'i, saida sumayya takai aya sannan dada tace masha Allah gaskiya naji dad'in labarin nan da kikazo dashi domin daman nima ina da burin hakan a raina ammah tunda har kikafurta da kanki toh ai shikenan.
sumayya kallon dada take cike da jin dad'i tace toh dada shikuma yaya suhail fa idan yace baya sona?
dada tace kikwantar da hankalinki zai ma soki domin babu yadda za'ayi nagida bai k'oshiba aba na waje ke dolene mane yasoki dan haka kikwantar da hankalinki shalele kamar kin zama matarsane kibari zamuyi maganar da shi da maimartaba.
sumayya cike da jin dad'i taduk'a takwashi gaisuwa tare da yin godia sannan tayi ma dada sallama tafito tanufi 6angarensu duk inda ta gifta tun kan ta ida isowa inda bayi da ma'aikata suke ake zubewa kwasar gaisuwa kowa tsoronsa kar tace yayi badaidaiba domin sunsan halin gimbiya sumayya da mahaifiyarta yi musu laifi abune maisauk'i, kowa yau yana mamakin yadda fuskarta take a sake sa6anin da dakullum take a d'aure.
dada ko da tasamu maimartaba da labarin shima yayi murna sosai inda yace zai gana da su gobe.
yarima suhail ne kwance saman makeken gadonsa inda shahid yake gefensa yana ta zuba masa surutu shi dai yarima daga uhm sai uhm-uhm bai cewa komai sai ma dannar wayarsa da yakeyi.
shahid ya k'ule sosai tsaki yaja yace kai fa matsalata da kai kenan sai ana yi maka magana kadinga share mutum kamar ba dakai akeba.
shuru yarima yayi yacigaba da dannar wayarsa takaici yakama shahid dan haka yafizge wayar, ganin haka yasa yarima yamaida idanunsa yalumshe.
shahid baiyi mamaki ba domin yasan halin abokin nasa tun suna yara.
knocking d'in k'ofar da akayine yasa shahid yabada izini da ashigo, wani dogarine yashigo tare da zubewa k'asa yana k'wasar gaisuwa shahid ne kawai ya amsa masa,
dogarin kansa yana k'asa yace Allah yaja da ran yarima mai jiran gado daman Maimartaba ne yake kiranka ya ce kasamesa a turaka,
yarima batare da yabud'e idonsaba yad'aga ma dogarin hannu alamun yatafi.
tashi dogarin yayi yace nabarku lafiya sannan yaficce daga d'akin.
shahid kallonsa yayi yana murmushi yace yau sarautar ta motsa kenan.....
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Sak'on gaisuwata agareku intelligent writer's Allah yabar k'aunaπ_
_My k'anwa janaf Allah yabar min keπ_
_*Wannan page d'in nakine Asma'u Yusuf Beji kiyi yadda kikeso da shi ina godia da kulawarki agareniπ*_
page 2⃣
Yarima suhail saida yayi kusan minti biyar yana a kwance sannan yabud'e idonsa ahankali yamik'e yasafka daga kan gadon, alkyabbarsa yajawo yasa batare da ya kalli shahid ba saida yataka yakusan zuwa k'ofa sannan yace kajirani bari indawo, shahid cike da tsokana yace toh ranka yadad'e
yarima baice komai ba yafita yana tafiyarsa ta k'asaita, dogarawan da suke zaune k'ofar d'akinsane suka zube suna kwasar gaisuwa sannan suka tashi domin sutake masa baya, yarima batare da ya kallesuba yad'aga musu hannu.
ganin haka yasa duk suka tsaya, yawuce yacigaba da tafiyarsa shi kad'ai duk inda yagifta kwasar gaisuwa akeyi, d'aga ma mutane hannu kawai yake idan da sabo sun saba da halin yarima ahaka har yashiga turakar mai martaba da mamakinsa yaga har da iyayensu a zaune,
waje yasamu gefen maimartaba yazauna a k'asa tare da kwasar gaisuwa wajensa da wajen iyayensu nan duk suka amsa masa,
maimartaba gyaran murya yayi yace toh Alhmdllh nasan duk zakuyi mamaki akan dalilin taraku nan da nayi ammah ba abun mamakibane alkhairine muke tafe da shi, ba akan kowaba sai akan yarima suhail,
maimartaba cigaba yayi da cewa domin na riga na yanke hukunci saboda nasan zai kar6i abinda nake tafe dashi na alkhairi, bakomai bane sai akan dubawa da cancantar da naga yayi dan haka naza6a maka matar aure bakowa bace face 'yar uwarka sumayya.
yarima gabansane yaji ya fad'i dasauri yad'ago kai yakalli maimartaba har ya bud'e baki zaiyi magana sai kuma yafasa dan haka yasunkuyar da kansa k'asa tare da runtse idonsa cike da takaicin za6in da maimartaba yayi masa, nan iyayensu sukaita murna suna tofa albarkacin bakinsu akan maganar.
shidai yarima saurarensu kawai yake,
muryar maimartaba ce yatsinkayo yana cewa toh kai uban gayyar bakace komai ba,
yarima suhail kamar ba zaiyi magana ba sai chan yace ranka yadad'e na amshi za6in da kayi min hannu bibbiyu Allah yak'ara tsawon rai.
cike da Jin dad'i maimartaba yace masha Allah, naji dad'i sosai tabbas nasan daman bazan samu matsala daga garekaba wlh ka faranta min nima Allah yakawo lokacin da zan faranta maka,
gaba d'ayansu sukace Ameen, yarima suhail nan yak'ara kwasar gaisuwa sannan yamik'e yafita
umman sumayya kamar tazuba ruwa k'asa tasha saboda murna domin ko bakomai tasan burinta ya kusan ciki ko da taje ma d'iyarta da labarin sumayya har da rawa tataka saboda murna dagudu tafita taje 6angarensu rahama tashaida mata, nan rahama tatayata murna.
yarima suhail yana komawa d'akinsa saman gadonsa yafad'a tare da lumshe idonsa cike da bak'in ciki domin an 6ata masa plan saboda shi baida burin yin aure a yanzu ko ma da zaiyi sumayya bata daga cikin irin tsarin matan da yake da burin aure saidai kawai zai amince ne saboda maimartaba domin baya iya jayayya da shi,
shahid ganin yarima acikin wannan mood d'in yasa bai tambayesa abinda yake damunsaba domin yasan ko da ma ya tambaya toh ba zai samu amsaba saidai idan shi yaso yafad'a masa toh dakansa zai basa labari dan haka yasharesa yacigaba da kallon ball d'insa.
yarima ya dad'e a kwance sannan daga baya yatashi yashige toilet.
bayan sallar isha'i yarima turakar iyayensa yaje inda yatadda mahaifiyarsa kishingid'e wata baiwarta tana mata tausa inda wasu biyu suke gefenta suna mata hira.
suhail yana shiga yatsaya bakin k'ofa ganinsa yasa duk suka zube suna kwasar gaisuwa sannan daga baya suka tashi suka fita suka basa wuri domin yagana da mahaifiyartasa,
sultana bilkisu tashi tayi daga kishingid'en da take nan suhail yataka yaje inda take yazauna sannan yagaishe da mahaifiyartasa cike da fara'a ta amsa masa.
suhail duk'ar da kansa yayi k'asa baice komai ba, ganin haka yasa mahaifiyarsa tace yarima me yake faruwane? kafad'a min damuwarka domin bakada wata uwar da tafini,
suhail d'ago fuskarsa yayi cike da damuwa yace ummi yanzu Sumayya ita zan aura?
murmurshi ummi tayi tace toh menene dan ka aureta ina ce 'yar uwarkace kuma ta cancanta da hakan,
dan haka kakwantar da hankalinka kakoya ma zuciyarka sonta insha Allahu zakuji dad'in zaman aurenku.
cike da damuwa suhail yace ammah ummi kinsan halin Sumayya ko kad'an halinmu bai zo d'ayaba,
ummi tace injiwa yace maka haka? duk abinda kaga tanayi harda yarinta, nidai burina kakwantar da hankalinka tunda ita kaga bata tada hankalintaba kakoya ma zuciyanka sonta insha Allahu zakuji dad'in zaman aurenku.
yarima suhail yace toh ummi nagode, nabarki lafiya.
ummi tace toh my son dan Allah kar katashi hankalinka tunda kaga an amince da aikinka yanzu haka mahaifinka ya sa afara maka ginin hospital d'inka.
murmurshi yarima yayi yace nagode ummi sannan yafita daga turakar yakoma tasa.
Bayan kwana biyu aka tsaida maganar aurensa da sumayya nan da wata biyu masu zuwa, yarima yaso asa lokacin dayawa ammah maimartaba yace a'a, ,sumayya farin ciki tayi sosai agaban kowa take nuna murnarta,
yarima ganin dagaske ake yasa yad'an saki jikinsa har suna d'an ta6a hira da sumayya shima d'in kafin yayi magana d'aya tayi biyar, in ko kaga sunyi waya toh itace takirasa shima daga gaisuwa yake kashe wayarsa.
Bayan wata biyu akasha bikkunsu anyi shagali sosai ak'allah saida akayi events kusan guda biyar ammah dakyar aka samu yarima suhail yaje d'aya daga ciki shima saida ummi tasa baki, ammah sauran duk k'in zuwa yayi k'arshe idan yaga za'a takurasa sai yakashe wayoyinsa yace kar abari kowa yashigo sashensa,
ranar asabar aka d'aura aure, auren da dubban mutane daga nahiya dadama suka hallara,
amarya ta sha kyau har ta gaji, inda amarya tatare a part d'in yarima da aka fitar da shi a cikin gidan sarauta, k'arshen gata an nuna mata babu abinda ba a zuba masu na amfani ba.
kowa yazo sai ya yaba tsarin gidan domin babu wanda zai ce acikin gidan sarautane saboda part d'in yarima antsarasa kamar a turai inda aka fidda ma sumayya 6angarenta sai na yarima sai wani part d'in da aka fara ginawa aka aje sai kuma part na ma'aikata da bayinsu maza da mata.
da daddare saida shahid yayi dagaske sannan yasamu yarima suhail yayi wanka yashirya suka fito suka rakasa gidansa.
suna ta tsokanarsa shidai yayi shuru yakyalesu saboda wani irin haushi da yakeji, hatta su kansu haushinsu yakeji tunda su suka matsa masa sai yaje.
saida suka rakasa har part d'in amaryarsa sannan sukayi masa sallama suka tafi.
yarima suhail 6angarensa yabud'e da mamakinsa yaga dogarawansa zaune a k'asa suna ganinsa suka zube suna kwasar gaisuwa, yarima suhail batare da ya amsaba yace kun iya tafiya ,
k'ara kwasar gaisuwa sukayi sukace toh ranka yadad'e sannan sukace atashi lafiya sai suka tashi suka fita
bedroom d'insa yashiga komai na ciki very need da mamaki yakalli yadda aka shimfid'a masa farin bedsheet mai kyau a saman gadonsa d'auke kansa yayi yawuce yashiga toilet yawatsa ruwa , bayan ya fito yayi shirin kwanciyarsa yahaye gadonsa.
A 6angaren gimbiya sumayya bayan ta gama shirinta su jakkadiya suka take mata baya zuwa turakar yarima, da sallamarsu suka shiga ganin baya parlour yasa suka kwank'wasa masa bedroom,
yarima da yake kwance yabada izinin ashigo, da mamaki yake kallonsu sumayya da suka shigo, nan su jakkadiya suka zube k'asa suna kwasan gaisuwa, ita dai sumayya zuba masa ido tayi tana kallonsa cike da son mijinta,
haydar bai damu da kallon da take masaba yace lafiya kukazo man d'aki?
jakadiya da take durk'ushe tace ranka yadad'e yarima mai jiran gado daman dada ce tace mukawo maka amarya,
yarima suhail shuru yayi baice komaina yamaida idonsa yalumshe.
ganin haka yasa su jakadiya sukace mun barku lafiya gimbiya da yarima Allah yaja da ranku atashi lfy.
Gimbiya sumayya tace idan kun fita sai kurufe mana k'ofan,
yarima suhail yana jinta mamakine yakamasa domin bai ta6a ganin amarya hakaba.
suna fita sumayya tatako ta iso bakin gadon tazauna gefen da yarima yake kwance, suhail batare da ya bud'e idonsaba yace kije kid'auro alwallah,
sumayya turo baki tayi sannan tatashi tashiga toilet d'insa tad'auro alwallah,
lokacin da tafito yarima yana shimfid'a darduma nan yajasu sallah raka'a biyu sukayi sannan yakama kanta yayi mata addu'a.
bayan ya gama yayi mata tambayoyi akan addininta baiyi mamaki ba da yaga bakomai take iya basa amsaba, wata amsarma ba daidai take basaba nan ya Ida tsurewa da lamarin sumayya ammah kuma sai yashare, mik'ewa yayi yanufi saman gadonsa yabarta nan saida yakwanta sannan yace ga nama nan idan zaki ci.
haushine yakama sumayya ganin yadda takejin labari wajen friends d'inta yadda mazajensu suka nuna musu tattalin so a daren aurensu ammah ita ba hakaba, cikin ranta tace lallai yarima halinsa sai shi.
tashi tayi itama taje saman gadon takwanta bayansa saida sukayi kusan minti goma ahaka ammah sumayya taga yarima bai da alaman nemanta dan haka tarungumesa ta baya,
yarima shareta yayi, ganin haka yasa sumayya tajuyosa tare da kwanciya saman jikinsa, yarima bud'e idanuwansa yayi da suke lumshe yawurga mata harara yace ke bakida kunya?
sumayya turo baki tayi tace yarima yau fa daren amarcinmune ammah shine kake shirin yin bacci kabarni hannu takai tana shafa jikinsa.
yarima da mamaki ya gama cikasa kasa komai yayi, jin hannunta yayi yana yawo cikin jikinsa, dasauri yarik'e hannun yace ke bakida kunya?
sumayya tace ammah ai naga ba abun kunya bane tunda munyi aure,
bakinta takai cikin nasa tana kissing d'insa cikin wani irin salo nan da nan yarima yafita hayyacinsa ya'aje sarautarsa gefe yabiye mata suka sha amarcinsu.
yayi mamaki sosai ganin yadda sumayya take zak'ewa babu alamun tsoro atare da ita,
a yadda yasameta bai kawo ma ransa komai ba gudun kar zargi yashiga tsakaninsu dan haka dayasamu nutsuwa janye jikinsa yayi yaje yayi wanka sannan yadawo yayaye bedsheet d'in yayi yakwanta tare da juya mata baya,
sumayya ma tashi tayi taje tayi wanka sannan tadawo bayansa yakwanta tare da rungumarsa ta baya,
da asuba yarima har yadawo masallaci ammah sumayya bata tashi tayi sallah ba, saida yayi dagaske sannan yasamu sumayya tatashi tayi sallah tana ta k'unk'uninta, komawa yayi yakwanta yana kallonta sallarma shaf-shaf tayita ko addu'a bata tsaya yiba tahaye gadon.
dasafe jakkadiya ce tatashesu nan tashigo takwashi gaisuwa sannan tad'auki bedsheet d'in tafita.
turakar dada taje, tun da dada tahangota take fara'a jakkadiya duk'ewa tayi takwashi gaisuwa sannan tace ranki yadad'e ga zanen gadon,
dada tace masha Allah bud'e mugani ko da jakkadiya tabud'e babu komai a jikinsa nan hankalin dada yatashi tace nashiga ukka ya akayi haka kar dai ace yarinyarnan ba budurwa bace.
jakkadiya duk'ar da kanta tayi tace ranki yadad'e ai ita mace budurwa ba dole sai anga jiniba ake gane budurwace wasu basu jinin budulci,
dogon numfashi dada taja tace hakane shikenan yanzu aje awankesa amaidasa ma'ajinsa ammah naso ace kowa ya shaida.
kowa na gidan kasa kunne yayi yaji ana gud'a ammah shuru kuma kowa tsoron tambaya yakeyi, kasancewar al'adarsuce duk amaryar da aka kowa idan budurwace da anga jinin ake ganewa nan za'a d'auki zanen gadon ayi ta yawo ana gwadawa daganan sarki zai bada shanuwa da rago ayanka ma amarya.
yarima suhail har yagama shirinsa ammah gimbiya sumayya tana kwance tana kwasar baccinta haushi ne yakamasa yaja tsaki yace mutum kamar kasa sai bacci, da mugunta yakai mata bugu, firgit tayi tafarka daga baccin
haushi ne yakamata ganin yarima tsaye, d'aure fuska tayi tace haba yarima ya za'ai katasheni bayan jiya kaine kahana ni bacci, gaskiya kadaina domin idan ina bacci ba'a tashina.
yarima da mamaki yake kallonta jin tace shi yahanata bacci bayan itace takawo kanta,
tashi tayi tad'auko alkyabbarta tasaka sannan taficce tabarmasa d'aki,
tsaki yarima yaja sannan yacigaba da abinda yake,
bayan ya gama yafito parlour yatarar da anshirya masa breakfast dogarawansa suna ganinsa suka zube suka kwashi gaisuwa sannan d'aya daga cikinsu yayi serving d'insa,
kad'an yaci sannan yatashi nan suka rufa masa baya sunacewa takawarka lafiya yarima.
tsayawa yayi batare da ya juyoba kamar ba zaiyi maganaba sai kuma yace kuje kawai zan nemeki,
su dukansa sukace angaisheka yarima umurninka muke cikawa Allah yatsare mana kai mun barka lafiya.
daganan yawuce yacigaba da tafiyarsa shi kad'ai duk inda yagifta kwasar gaisuwa ake ahaka har yazo 6angaren gimbiya ko da yashigo parlour saida ma'aikatanta sukayita kwasar gaisuwa ko inda suke bai kallaba yawuce direct bedroom d'inta,
lokacin gimbiya sumayya tana zaune bayinta suna shiryata, bud'e k'ofar da akayine yasa duk suka maida hankalinsu domin suga mai shigowa ganin yarimane yasa suka zube gaba d'ayansu suka kwashi gaisuwa sannan suka mik'e zasu fita
gimbiya sumayya ce tace ina zakuje batare da kun gama shiryaniba,
yarima kallonta yake cike da mamaki sannan yanuna musu k'ofa dasauri dukansu suka fita har suna tuntu6e.
takowa yayi cikin takunsa na k'asaita ya iso bakin gadon, gimbiya sumayya tace haba yarima ya zaka korar minsu alhali basu gama shiryaniba,
zama yarima yayi kusa da ita batare da ya kalletaba yace ke ba zaki iya shiryawaba har sai sun shiryaki?
sumayya ta6e baki tayi tace ammah ai tun ina gaban iyayena su suke min kwalliya, banza yarima yayi yakyaleta dan haka taci gaba da shirinta.
banza yarima yayi yakyaleta.
bayan ta gama kiran jakkadiya tayi tace akawo mata breakfast d'inta a nan, cikin minti biyar ancika mata gabanta da abinci da kayan marmari iri-iri
nan tazauna zata ci kallon yarima tayi tace kaifa ba zakaciba,
yarima batare da ya kalletaba yace no kici kiyi sauri kigama muje mugaishe da su maimartaba,
gimbiya sumayya tace tun yanzu?
yarima bai tanka mataba,
ganin haka yasa tacigaba da breakfast d'inta domin tasan halin mutumin nata magana tsada take masa......
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
?ππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_*Sak'on gaisuwata agareku My Haleema H.A.S nd mummy Zillππ*_
_Wannan page d'in nakune nabaku shi a kyauta my fan'sπ_
page 3⃣
bayan ta gama d'auko alkyabbarta tayi tasaka sannan suka jera ita da yarima suka fito, a k'asa suke tafiya a jere, kuyangin gimbiya suka take musu baya ahaka har suka isa fada nan mutane suka dinga kwasar gaisuwa, d'aga musu hannu kawai yarima yakeyi har suka isa gaban maimartaba dasauri dogarawa sukazo suka kare su yarima daga ganin mutane suna cewa Allah yataimaki yarima da gimbiya azauna lafiya, har saida suka tabbatar da yarima da gimbiya sun zauna sannan suka matsa nan su yarima suka kwashi gaisuwa wajen sarki nan fadawa suka d'auka, sarki ya amsa muku yarima da gimbiya, sarki yana godia yarima mai jiran gado ku ma angaisheku.
sannan yarima yatashi yaje kujerar da take kusa da sarki yazauna, ita dai gimbiya tana tsugunne a k'asa sai yatsina take tana kallon mutane a wulak'ance.
maimartaba ne yad'auko wata alkyabba maikyau da tsada yamik'a ma gimbiya sumayya hannu biyu gimbiya tasa takar6a tare da yin godia sannan tamik'a ma jakkadiya, jakkadiya tazube gaban sarki tace ranka yadad'e gimbiya tana k'ara godia Allah yaja da ran sarki mai adalci sarkin sarakai,
gyad'a kai sarki yayi nan fadawa gaba d'ayansu suka d'auka angaisheki gimbiya sarki ya ji godiar ki.
nan sarki yayi musu nasiha tare da yi musu addu'an zaman lafiya, sannan suka k'ara kwasar gaisuwa suka tashi suka fito, cikin gida suka shiga turakar dada,
nan suka gaisheta itama tayi ma gimbiya kyauta sannan suka wuce 6angaren ummi suka gaisheta itama kyauta tayi ma gimbiya sannan daganan sukaje 6angaren umman sumayya suka gaisa daga nan suka koma 6angarensu
suna shiga yarima yanufi hanyar zuwa 6angarensa ganin gimbiya tana niyar binsa yasa yadakata da tafiyar batare da ya kalletaba yace zaki iya tafiya 6angarenki domin yanzu inason inhuta bai jira jin abinda zata ce ba yawuce part d'insa.
Gimbiya sumayya tsaye tayi takaici duk ya cikata ganin yadda yarima yadizgata gaban bayinta, tsawa tadaka musu tace suwuce subata waje dasauri duk suka bar wajen,
nan gimbiya tanufi part d'inta cike da jin haushi.
haka sukayi sati d'aya suna shan amarcinsu tun yarima bai kulata daga baya sumayya saida tasan yadda tayi yarima suhail yad'an sake mata, ammah idan yana jin 'yan miskilancin ko sarautar takad'a masa toh ko kallon inda take bata yi.
bayan sati guda gimbiya sumayya ce kishingid'e a parlourn ta inda bayinta suke zagaye da ita wasu suna mata tausa wasu fifita, d'aya tana karanta mata labari, wayartace tashiga ruri baiwar da take rik'e da wayoyintane tamik'a mata, cike da Jin dad'i sumayya tayi picking d'in wayar ko sallama batayiba tace haba zinat ai ni fushi nake da ke wai har ayi aurene bakya garin,
daga chan 6angaren Zinat tace toh sarkin k'orafi yanzu dai gani a k'ofar gidanki dogarawa sun hanani shiga kituro a shigo da ni,
cike da jin dad'i sumayya tace yanzu ko zan aiko, kallon d'aya daga cikin bayinta tayi ta yamitse fuska tace ke jeki waje kishigo min da bak'uwata,
dasauri tamik'e tace angama ranki yadad'e
batafi minti biyar da fitaba sai gasu sun shigo da zinat, sumayya tashi tayi daga kishingid'en da take tace oyoyoo k'awata takaina, nan bayi suka zube suka kwashi gaisuwa wajen wadda aka kira da zinat sai yamutsa fuska take tana taunar chewing gum tazauna saman kujera, nan gimbiya sumayya takori duka bayin daga d'akin,
gimbiya sumayya kusa da ita takoma tazauna kafin kace mi ancika gaban zinat da kayan ciye-ciye da na shaye-shaye, sumayya cike da farin ciki tace k'awata kenan ai ban d'auka zan ganki a yanzu ba,
zinat kur6an ruwan inibi tayi sannan ta aje cup d'in tace wlh jiya nadawo garin shine nace ba zan fad'a mikiba surprise kawai zan baki yau.
.
murmushi Sumayya tayi tace kin ko kyauta wlh, na ma d'auka sai kin gama hutawa zaki dawo domin na sanki da son tafiya kihuta, zinat tace ai saboda ke nadawo amarya kinsha k'amshi kinga ko yadda kika koma?
murmushin jin dad'i gimbiya sumayya tayi tace ya nakoma dear?
zinat tace ai kin fito a gimbiyarki ta ainahi ke ni bani insha kifad'a min yadda kuke zaune da wannan miskilin mijin naki.
sumayya gyara zamanta tayi tace ai lafiya lou miskilanci kau saidai abinda yayi gaba, zinat tace ke ya batun first night d'inku,
dariya gimbiya sumayya tayi tace ai babu abinda yagane game da hakan kinsan nayi amfani da magungunan da kikasa aka had'a min wlh har tausayi yabani ganin bai gane komai ba.
ta6e baki zinat tayi tace ke inbanda abinki wa yace miki ana tausayin maza indai kina lalla6a miji ai sai yarainaki, shawarace zan baki daga inda miji yafara d'aga miki murya ke kinuna masa kinfi sa hauka,
sannan ba kowane lokaci zaki dinga ba mijinki kankiba saboda idan kika saba masa da haka toh sai kin gunduresa yaji ya gaji da ke daga k'arshema sai kiga kishiya
zaro ido sumayya tayi tace kishiya kuma? zinat gyad'a kai tayi tace eh man ai wlh namiji ba a basa amana ke nifa saboda tsoron halin maza yasa nakasa aure nake cin karena babu babbaka dukiya ce natara bakin gwargwado a lokacin da kuma naji ina buk'atar namiji ga mazanan birjit sai na za6a, inma macen nake buk'ata kema kin sanni.
dariya sumayya tayi tace hakane k'awata wlh kin kawo shawara mai kyau, ke nima fa sonake inga natara dukiya dan ban had'a kud'i da komai ba tunda ga mulki ga miji kinga dukiya yarage dan haka business zan fara. saidai anya zamu kwashe lafiya da yarima?
harararta zinat tayi tace kefa matsalata da ke wani lokacin baki da ganewa ammah asannu zan ganar da ke yadda zaki fahimta, ammah nagargad'eki da lallashin miji bare ma wannan mijin naki idan yashareki kema kifita harkarsa ke da nice da nasan yadda zan juyasa yakoma a tafin hannuna,
gimbiya sumayya tace hmm ba dai yarima ba anya akwai macen da zata iya juyasa?
zinat tace kefa matsalata da ke kenan bakida ganewa, kedai kigwada kigani dakanki zaki bani labari, yanzu dai taso mushiga daga ciki.
mik'ewa sumayya tayi tana dariya zinat tana binta a baya suka shige bedroom,
a ranar haka zinat tawuni gidan gimbiya sumayya tana k'imsa mata makirci iri-iri har saida taga gimbiya sumayya ta hau ta zauna sannan tabarta.
Tun daga ranar gimbiya sumayya tadaina shiga sabgar yarima shima shareta yayi yacigaba da hidimar gabansa,
yarima tun bai damuwa har abun yazo yafara damunsa yanzu tsawon wata d'aya da aurensu tun satin farko rabonsa da gimbiya domin ko d'akinsa bata zuwa.
yau da dare kasa daurewa yayi dan haka yatashi yasaka alkyabbarsa yafito yanufi 6angaren gimbiya sumayya, da key d'insa yabud'e direct bedroom d'inta yashiga chan tsakiyar gado yahangota ta baje sai baccinta take ahankali yataka yaje yahau saman gadon.
gimbiya sumayya da take bacci jin ana shafata yasa tafarka, da mamaki take kallon yarima, chan kuma sai tad'aure fuska tace lafiya?
yarima cigaba yayi da abinda yake kamar ba zaiyi magana ba sai kuma chan yace sumayya yanzu saboda Allah hakan da kike min kina ganin kin kyauta? hak'k'ina nazo kar6a,
gimbiya sumayya janye idonta tayi daga kallonsa cikin ranta tana jin dad'in shawarar da k'awarta tabata ganin yau dakansa ya aje girman kan yazo d'akinta,
ganin yarima suhail yana shirin rikitata yasa tajanye jikinta gefe tace haba dan Allah yarima wai menene haka nifa a gajiye nake.
da mamaki yarima yake kallonta yace haba sumayya saikace wadda tayi wani aiki nidai yanzu kibari inyi inyaso daga baya sai kiyita baccinki.
gimbiya sumayya komawa tayi takwanta tare da juya masa baya tace ni ba zan iyaba gaskiya, yarima binta yayi yana lallashi dakyar ta amince masa shima saida taita masa k'orafin ta gaji kan dole a k'arshe yahak'ura yabarta batare da ya ida samun nutsuwaba,
toilet d'inta yashiga yayi wanka sannan yadawo yakwanta tare da juya mata baya cike da mamakin yadda sumayya tasauya hali .
gimbiya sumayya ko murna takeyi ganin ta d'an ci nasara har Yarima suhail ya zo d'akinta yau, kuma ya aje girman kai da sarautar ya lallasheta.
Tun daga lokacin yarima shi yake biyota d'akinta ko da ace ya yi mata wulak'anci a wani wajen ita kuma sai ya nemeta take ramawa sai ya-yi dagaske yake samun hak'insa a wajenta ahaka suka haura wata shidda ammah ko 6atan wata bata ta6a yi ba,
dada ta fi kowa damuwa domin tisata gaba take a d'aki tana tambayarta ko akwai abinda take sha ita dai gimbiya a'a take cewa, dada tace a'a gimbiya indai akwai abinda kikeyi, gimbiya saidai tayi dariya tace dada inda ina yin wani abu ai da kun gane, dada saidai tace toh Allah yakawo.
ko da yarima yazo yagaishe da dada bayan sun gaisa dada tace yarima wai har yau ba wani labari?
yarima shuru yayi saida yayi kusan minti biyu sannan yace dada labarin me kuma?
dada tace hmm ciki mana.
murmurshi kawai yayi yace dada ai haihuwa lokacine, idan da darabo zamuyi.
dada tace toh Allah yakawo mai albarka yarima yace Ameen.
sannan yarima yatashi yafita dogarawansa da suke tsaye bakin k'ofa suna ganin ya fito nan suka fara masa kirari yana gaba suna biye da shi tun kan ya isa wajen jerin motocinsa da yasa aka tanadar masa dan yafita dasauri aka bud'e masa dank'areriyar motarsa da take tsakiya nan yashiga baya yahakimce sannan dogarawa suka shiga sauran motocin akasa tashi a tsaka nan aka kama hanya.
asibitoci yaje yakai ziyara yaduba marassa lfy yayi musu kyauta sannan yawuce gidan marayuwa yabada kayan abinci kowa yaji dad'in ziyarar da yakawo domin daman halinsane kyauta,
daga nan suka kama hanyar gida, ko da suka isa bai shigaba saida yatsaya yasa aka tara ma'aikatansa yaraba masu kud'i nan suka zube suna ta godia daganan yawuce part d'insa yana shiga yacire kayan jikansa yafad'a toilet yayi wanka, bayan ya shirya saman gado yafad'a yana hutawa bud'e k'ofar da akayine yasa yabud'e idonsa dayake a lumshe,
ganin gimbiya sumayya ce yasa da mamaki yakalleta domin yasan bata shigowa d'akinsa sai idan tana buk'atar wani abu, maida idanunsa yayi yalumshe,
takowa tayi tahau saman gadon tazauna gefensa ganin baida niyar bud'e ido yasa tace ashe har kadawo tun d'azun nake aikowa adubomin idan kana nan,
yarima batare da ya bud'e idanunsaba yace ya akayi kika shigo min d'aki ba'a fad'a miki nace kar wanda yashigo ba? gimbiya sumayya murmushi tayi tace yanzu dan zan shigo d'akinka har sai anbani izini a matsayina na matarka?
banza yarima yayi yakyaleta, ganin baida niyar tanka mata yasa takwanta a jikinsa ta d'auka zai gwalisheta ammah taji ya yi shuru baice komai ba, dan haka takai hannu tana shafa fuskarsa daga nan tafara kissing d'insa daman abu ga mai nema nan yarima yabiye mata,
ya yi mamaki yadda yau bata hanasa kantaba domin yasan hali da ya fara zata fara cewa ta gaji, ammah yau saida yagaji dan kansa sannan yabarta.
rungume take a jikinsa cikin shagwa6a tace my sweetheart dan Allah inaso kabani 2 million,
yarima baiyi mamakin jin hakan daga garetaba, domin daman yasan za'a rina ba zata ta6a bashi kantaba sai da dalili,
bud'e idonsa yayi yasafkesu akan fuskarta kamar ba zaiyi magana ba sai kuma chan yace mezakiyi da kud'i?
Sumayya batare da damuwaba tace business nakeso inyi kaga zaman hakanan ai baya yuwuwa zamu had'a jari da k'awata zinat zata dinga zuwa tana saro mana kaya, zamu bud'e babban boutique a chan Abuja.
yarima tunda tafara bayanin yatsareta da ido har takai aya sannan yace yanzu ke bakiji kunya ba kice zakiyi kasuwanci akwai abinda narageki da shi ne?
gimbiya Sumayya d'aure fuska tayi tace kai fa matsalata da kai kenan to shi business dole sai marar wadata yakeyinsa?
yarima janye jikinsa yayi yace idan ke bakida hankali toh ni ina da shi kuma ba zakiyi ba, yana gama fad'in haka yawuce yashige toilet domin yayi wanka.
gimbiya Sumayya binsa tayi da kallo cike da takaici tace tsiyata da kai bakasan arzik'iba saida nagama baka kaina sannan kanemi kawulak'antani toh wlh baka isa kahananiba dan haka muzuba mugani,
tana gama fad'in haka tajanyo kayanta tasaka tatashi fuuuuu tafita tabar d'akin.
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_*~Sak'on gaisuwata agareki Mummyn khalil fatana Allah yabaki lafiya, Allah yasa zakkar jikine~*_
_kuna ina Kuzo yau ranar takuce wlh ina ji daku har cikin zuciyana *My k'anwa Safiyya Aliyu, Mrs Abubakar, Ma zeenart, Hafsat Kanty, Cool Angel, Chubby, Asma'u Yusuf Beji, Husnah, Mugirat Musa, Maman Sadiq, My k'anwa Khairyy, Maman Haidar, Hadiza Abubakar, Maman Amira, Kubcy Auwal, Dr Xeey Xeey, Aisha Baba Audu, ummu walid nd Abdul, Maman khaleesat, Sadiya Abubakar, Billy....* da ma sauran wad'anda ban lissafoba, wannan page d'in nabakushi Allah yabar k'aunaπ_
page 4⃣
tana fita daga d'akin yarima part d'inta tawuce ko ta kan su jakkadiya batabiba da suke tsugunne suna ta kwasar gaisuwa wucewa tayi tashige bedroom d'inta, wayarta tad'auka takira zinat, zagaye d'akin tashiga yi tak'agara zinat tad'aga wayar ammah har tatsinke bata d'agaba, tsaki gimbiya taja tace itafa matsalata da ita ayi ta kiranta sai taga gama take d'auka,
k'ara Kiranta tayi bugu biyu tad'aga
ko gaisawa basuyiba tace zinat kinajin wancan d'an rainin hankalin wai bazai barni inyi business d'inba
zinat cikin tsawa tace what! shi har ya isa yahanaki kuma kihanu? gambiya tace hmm yoh ke kina tunanin ma zan hanu?
zinat dariya tayi daga chan 6angaren tace wlh innice yanemi yaraina min hankali tuni zan nuna masa iyakarsa ke ak'arshema zan iya kashe auren tunda dama dashi yake tak'ama,
gimbiya zaro ido tayi kamar tana gaban zinat tace kirufa min asiri ai wlh ba zan iya rabuwa da shi ba saidai nasan ta inda zan 6ullo masa kibarni da shi.
zinat tace toh shikenan nidai ina jira cikin week d'innan inga alert saboda so nake inje ingama komai dawuri indawo,
gimbiya sumayya tace toh shikenan kar kidamu, nan sukayi bankwana.
suna gama wayar gimbiya ummanta takira saida takusan tsinkewa sannan sultana sadiya tad'aga da sallamarta, sumayya ko gaisheta batayiba tace ummana wlh yarima baida mutunci
sultana sadiya a rikice tace nashiga ukku shalele miyake faruwa ne? wlh indai wani cin mutuncin yayi miki zan rufe ido inci masa mutunci shima daga shi har mahaifiyartasa a tafin hannuna suke, kifad'a min abinda yake faruwa.
Sumayya cike da jin dad'in ganin yadda mahaifiyarta take kula da ita, sannan tabata labarin business d'in da takeso tayi da yadda suka kwashe da yarima.
sultana sadiya tace ai bai isaba Indai ina raye ba zaki ta6a yin kukaba ammah kafin ind'au mataki da hannuna kije kifara samun dada kuyi maganar domin nasan ita zata fahimceki sosai inko ta yarda nasan yarima ma zai amince ko da ace baya so.
cike da jin dad'i sumayya tace hakafa za'ayi ummana wlh saisa nake k'ara sonki saboda duk abinda nake so kema kina sonsa.
'yar dariya sultana tayi tace idan ban so abinda kikeso ba toh nawa zan so? kekad'ai fa ce namallaka, ke nifa ba ma wannan ba wai har yanzu ba wani bayani?
sumayya ta fahimci inda mahaifiyarta tadosa ammah sai tanuna bata fahimtaba tace ummah wane bayani kuma?
ummanta tace ke gidanku ni zakiyi ma kwana-kwana? ke ni ban yarda da keba anya bakiyin family planning?
dariya sumayya tayi tace ni babu abinda nakeyi kuma nima insha Allahu sai na shekara biyar sannan zan haihu.
sultana sadiya tace nashiga ukku ke gidanku wa yace miki ana gudun haihuwa a gidan sarauta?
gimbiya cikin shagwa6a tace ummah kema fa saida kika dad'e sannan kika haihu.
ummah tace toh ai nima ba dan ban soba Allah ne bai baniba a lokacin, inma kinsan kina yin wani planning toh wlh kidaina,
gimbiya tace nidai yanzu dai shikenan ummah tunda nace miki babu abinda nake ai sai kibar maganar, ni nafi buk'atar business d'innan bari dai inje muyi magana da dada, ummah ba dai dan ta yardaba tace toh shikenan sai najiki,
gimbiya tana gama wayar wanka tashiga tayi bayan ta fito shiryawa tayi cikin shigarta gwanin sha'awa sannan tafito nan kuyangi da bayinta suka take mata baya har suka shiga turakar sarki,
lokacin da tashiga parlour dada tana kishingid'e ana mata tausa, nan duk ma'aikatan dada suka gaisheta tare da yi mata kirari, tana yatsina ta amsa musu, nan bayinta suma suka zube suka kwashi gaisuwa a wajen dada, gimbiya zama tayi gefen dada tagaisheta,
dada cike da fara'a ta amsamata tace 'yar albarka meyake tafe da ke Allah yasa ba wannan sarkin 'yan iyayin bane yayimiki wani abu.
gimbiya k'ara 6ata fuska tayi tace dada kamar kau kin sani wlh k'ararsa nakawo,
dada tace oh ni Asma'u yanzu yaron nan nake ganinsa miskili ashe shima ya iya mugunta.
yanayin yadda dada tayi maganar yaso yabata dariya, gimbiya kallon bayin tayi da suke tsugenne tace dallah kutashi kuba mutane waje kunzo kun saki kunnawa kuna saurarenmu.
dasauri suka rausaya gaba d'ayansu sukace Allah yahuci zuciyar gimbiya mun barku lafiya, sannan suka tashi suka fita.
dada kallonta take cike da mamaki tace sumayya ashe har yanzu kina nan da halinki na wulak'anci?
gimbiya murmushi tayi tace toh ai sune basusan suba mutane waje suyi maganaba sai suwani yi zaune kuma idan nasakar musu fuska sai surainani.
dada sakin baki tayi tana kallonta har saida takai aya sannan dada tace sumayya na haneki da wannan halin ya kamata kizauna da kowa lafiya domin wata rana mijinki shi zai kasance sarkin garin nan.
murmushi sumayya tayi tace toh ranki yadad'e tuba nake, murmushi dada tayi irin nasu na manya sannan tace ina saurarenki me mijin naki yayi miki?
gimbiya gyara zamanta tayi sannan tace dada daman kasuwanci nakeso inyi shine natambayi yarima yabani jari sai yahanani kuma wai ba zanyiba.
murmushi dada tayi tace in banda abinki sumayya me kika nema kika rasa a gidan nan? kuma na tabbata babu abinda zaki nema wajen yarima kirasa domin nasansa da kyauta.
sumayya 6ata fuska tayi kamar zatayi kuka tace dada nima inaso indinga cin gashin kaina kuma fa k'awatace zata dinga kular mana da kayan ba sosai zan dinga zuwaba ita zata dinga yi mana komai.
dada ganin sumayya ta 6ata fuska yasa taji babu dad'i domin tana son jikartata sosai jininsu ya zo d'aya dan haka tace kikwantar da hankalinki yanzu kiramin shi awaya.
yarima bayan ya fito wanka yashirya cikin shigarsa ta alfarma ya yi kyau sosai wayansa yad'auko yakira shahid inda yashaida masa yazo suje yarakasa gidan gona akwai abinda yakeso yayi a chan.
shahid yace to shikenan ranka yadad'e daman yanzu haka zan fito daga fada sai kafito muhad'e,
yarima yace ohk sai nafito.
cike da k'asaita yake tafiya duk inda yagifta kallonsa ake cike da sha'awa, ana kwasar gaisuwa yarima yau 'yan jin kan suna a kansa ko hannunma basu samu matsayin da yad'aga musuba
lokacin da yafito dogawara duk suka taso d'aga musu hannu yayi alamun a'a har ya kusan kaiwa wajen motar sai yaji wayarsa tana ringing tsayawa yayi daga tafiyar da yake yad'auko wayar ganin mai kiransa kamar ba zai d'agaba har saida takusan tsinkewa sannan yad'aga batare da ya ce komai ba yakanga a kunnensa.
gimbiya sumayya jin baiyi maganaba yasa tamik'a ma dada tace gashi kuyi magana,
dada tana kangawa a kunnenta tace toh sarkin miskilanci bakaji ma zaka iya magana,
yarima jin muryar dada da yayi yasa yad'anyi murmushi yace toh me zan ce?
dada tace eh babu fa abinda zakace yanzu dai kazo ina son ganinka.
yarima yana jin haka yasan da wata a k'asa musamman ma da yaga da wayar gimbiya aka kirasa,
dada tace toh ko nima wahalar yimin maganar ake ji? murmushi yarima yayi yace dada yanzu fita zanyi kibari sai nadawo sai muyi maganar.
dada tace sannu babana toh idan ni kana ganin ka rainani toh sai inkira ubanka shi da ya isa da kai sai yasa kazo.
yarima yace shikenan kakus gani nan zuwa ai abun bai kai ga hakaba,
dada tace ina saurarenka, yarima batare da yabata amsaba yakashe wayarsa kallon shahid yayi da yake tsaye yana kallonsa yace shahid bari inje wajen waccen tsohuwar tana nemana tun kan tajamin sharri wajen daddy.
dariya shahid yayi yace toh ranka yadad'e sai ka fito.
yarima ko da yashiga baiyi mamakin ganin gimbiya sumayya ba dan haka zama yayi bisa kujerar da take opposite d'in wadda su dada suke a bisa, nan yagaishe da dada cike da girmamawa itama ta amsa masa.
daga nan shuru yabiyo baya chan sai dada tace suhail kaban mamaki wlh,
yarima kallonta yake da mamaki ammah baice komai ba.
dada batayi mamakin shurun da yayi ba saboda tasan halinsa dan haka tacigaba da cewa saboda Allah dan matarka tanason tayi kasuwanci sai kahanata?
yarima harara yawurga ma sumayya sannan yamaida kallonsa ga kaka .
kaka tace kai tambayarka nake shine kayi min shuru?
yarima cikin rashin damuwa yace dada ai nad'auka ta baki amsar abinda nace mata.
dada rik'e baki tayi tace wai kai wane irin mutum ne amsar ma bakaji zaka iya bani?
yarima shuru yayi kamar ba zaiyi magana ba chan kuma sai yace toh ai nace mata ban aminceba saboda babu abinda narageta da shi kuma indai kud'ine zan iya bata ammah ban yarda tayi kasuwanci ba ai sai taja mutuncina yazube a idanun mutane, daka ma gimbiya tsawa yayi yace ke ba haka nace mikiba? ??
Gimbiya ta tsorata da tsawar da yayi mata ammah sai tadake tad'auke kanta daga kallonsa.
dada ta6a hannu tashiga yi tace nashiga ukku yanzu a gabana kake mata tsawa ai da had'emu kayi ni da ita kadokemu sai inga kamar zai fi maka sauk'i.
yarima yace Allah yabaki hak'uri ammah dai yakamata kiduba kiga maganar nan bai daceba ace tadinga yawo tana chakud'a cikin maza,
kaka kallon sumayya tayi da taci face sannan tamaida kallonta ga yarima tace ai tace ba sosai zata dinga zuwaba abokiyar kasuwancin ce zata dinga kula da komai dan haka inaso kabata kud'in inkuma baka iya bata sai inkira 'ya'yana su subayar tunda su na isa da su.
Yarima baice komai ba yad'auko cheque yacike mata yamik'a mata yace gashinan kuma duk abinda yafaru kiyi kuka da kanki.
dada tace insha Allahu babu abinda zai faru sai alkhairi, kuma dan bak'in ciki baka ji zaka iya bata cash, yarima suhail mik'ewa yayi yace dada so kike kijasa min ciwon kai, bari intafi ana jirana.
dada tace ka dai ji dashi marar mutunci kawai,
yarima murmushi yayi yace na barki lafiya 'yar tsohuwa, sannan yaficce yabar turakar.
Gimbiya sumayya tana ganin yafita tatashi tahau tsalle da murna daga k'arshe da rungume dada tace nagode sosai ranki yadad'e Allah yak'ara tsawon rai wlh kin gama min komai.
dariya dada tayi tace ni sakarni ja'irar yarinya kawai ammah a gaban yarima bi kikayi kika marairaice kamar da gaske.
itama gimbiya dariya tayi tace ai wlh dan ina neman abu a wajensa saisa nabarsa yaci min mutunci son ransa ban tankaba.
dada rik'e ha6a tayi tace toh daman ashe bashi kad'ai yake rashin mutuncin ba harda ke, toh wlh kigyara domin aure ba abun wasa bane kuma kidaina ganin nasashi yabarki kiyi toh wlh kikama kanki kirik'e mijinki kar kififita kasuwanci akan aure kuma dan kince k'awarki zata dinga kula da komai saisa nagoyi bayanki.
gimbiya sumayya tace naji dada zan kula, nagode sosai.
mik'ewa sumayya tayi tana gyara alkyabbarta sannan takwala ma jakadiya kira, dagudu jakadiya tashigo tare da zubewa k'asa tace na amsa kiranki ya shugabata,
kallonta gimbiya tayi tace kuzo kucigaba da aikinku na kula da dada , jakadiya tace toh ranki yadad'e.
sannan gimbiya tayi gaba tana cewa kakus na wuce, dada tace toh sumayya
gimbiya sumayya tana fitowa nan bayinta suka mik'e suka take mata baya takoma 6angarensu.
Yarima suhail yana fitowa fuskarsa a d'aure yakar6i key d'in mota hannun driver dasauri d'aya daga cikin dogarawansa yabud'e masa motar yashiga.
shahid ganin yarima bai ko kallesaba kamar baisan da shiba ya shige mota dan haka shima yaje yabud'e yashiga yana cewa yau dakanka zaka ja mu?
yarima baice komaiba yaja motar yabar gidan, gudu yakeyi sosai da motar shahid yanata yi masa magiya akan yarage gudu ammah yarima kamar ba dashi ake ba.
cikin k'ank'anin lokaci ya isa gidan gona horn yashiga yi dasauri maigadi yazo yahangame masa gate yashiga da motar yana yin parking fitowa yayi yashige ciki bai ma kula da gaisuwar da ma'aikatan gidan sukeyi masaba.
shahid numfashi yake maidawa cike da jin dad'in sunzo lafiya domin bai kawo ma ransa zasu iso lafiya ba, daga k'arshe dai yabud'e motar yafito nan yatsaya saida suka gama gaisawa da ma'aikatan sannan yawuce cikin gidan.
A parlour yatarar da yarima kwance saman kujera idanuwansa a lumshe ya yi matashin kai da hannuwansa,
shahid tsayawa yayi gefensa yace wai yarima meyake faruwa ne naga tun da kadawo daga kiran da dada tayi maka fara'arka tagushe?
kuma dan mugunta kadinga gudu da mu toh idan kai bakason ranka toh ni inason nawa.
yarima idanuwansa a lumshe bai tanka masaba.
shahid tsaki yaja tare da zama yace kai nifa matsalata da kai kenan sai anayi maka magana kashare mutane kamar ba da kai akeba.
shidai yarima suhail baice komai ba saida yayi kusan minti biyar sannan yabud'e baki dakyar yace shahid wlh sumayya batada mutunci yanzu saboda Allah duk mutuncina ammah tana nema tazubar min dashi.
shuru yayi nad'an lokaci sannan yacigaba da cewa ni duk abinda takemin ban ta6a kai k'ararta ga kowaba ammah ita da mun d'an samu sa6ani toh sai kowa ya sani, ya za'ayi matar aure kuma matar yarima kamarni ace wai nabarta tana business har dada tagoya mata baya ai sai aja mutane suzageni.
Shahid cikin ransa yace ai indai wannan marar mutuncin ce zata aika domin bazan ta6a mance rashin mutuncin da tayi minba ranar da nazo wajenka.
chan kuma sai shahid yace kayi hak'uri kasan mata sai da hak'uri kacigaba da hak'urin da nasanka da shi.
yarima bud'e idonsa yayi da suke a lumshe yayi murmushin da yafi kuka ciwo sannan yace shahid kallon da akemin nine macuci cutar sumayya nakeyi babu Wanda yata6a tambayata yadda zaman aurenmu yake ammah wai ni zan saki matata tadinga yawon kasuwanci garuruwa.
shahid cike da tausayi yake kallon abokin nasa domin yasan ba'a ta6a jin matsalarsa saboda zurfin cikinsa ammah yau shine yake fad'a masa abinda yake damunsa tabbas yasan ba k'aramin 6ata masa rai akayiba, shahid yace dan Allah yarima kacigaba da hak'uri kadinga yi mata fatan alkhairi kar kad'auki mataki insha Allahu dakanta zata daina abubuwan da take.
Yarima shahid maida idanuwansa yayi yalumshe yana jin wani iri a ransa,
ganin haka yasa shahid yatashi yafita yana zagaya gidan gonar....
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Sak'on gaisuwata agareki aduk inda kika kasance my Aysha hak'ik'a ina yinki irin sosai d'in nan, ina tayaki murnar sabon novel d'inki da zaki fara mai suna *K'AUNACE SILA* Allah yasa afara lafiya agama lafiya my dear, Happy Birthday in advanceπππ_
_*Ba zan gaji da sadaukar muku da page ba Masoya ina jin dad'in comments d'in da nake samu daga gareku a group's da masuyimin ta pc wlh ina yinku over, wannan page d'inma kuje da shi nabakushi a kyautaπ sis Nerja'art tana sonku irin sosai d'in nanπ*_
page 5⃣
yarima duka wayoyinsa yakashe dan kar adamesa da kira dan yasan confirm ne sai maimartaba ya nemesa,
bayan sallar isha'i suka bar gidan gonar, shahid ne yakar6i key d'in motar yayi driving d'insu domin cewa yayi ba zai yarda yarima yatuk'asuba gudun kar yak'ara irin driving d'in da yayi d'azun shidai yarima baice komai ba yamik'a masa key d'in.
ko da suka isa yarima cema shahid yayi yazo sufara shiga fada sugaishe da sarki, shahid bai musaba yabi bayansa a jere suka shiga fad'a nan duk mutane suka zube suna kwasar gaisuwa ahaka har suka iso gaban sarki,
dasauri wani dogari yad'auko wani had'ad'en carpet yashimfid'a musu nan sauran dogarawa suka zo suka baza manyan rigunansu suka kare su yarima daga ganin mutane suna cewa azauna lafiya yarima, saida suka tabbatar da sun zauna sannan suka matsa nan su yarima suka gaishe da sarki, sarki fuskarsa d'auke da fara'a ya amsa nan fadawa suka d'auka angaisheku yarima mai jiran gado sarki ya amsa gaisuwarku Allah yaja da ranka.
sannan yarima suka gaishe da su daddy da abban sumayya, nan ma fadawa suka d'auka da angaisheku kuma,
maimartaba kallon yarima yayi da yake durk'ushe k'asa yace yarima tun d'azun nake aikawa akira min kai ammah sai adawo acemin tunda kafita baka dawoba.
yarima suhail murmushi kawai yayi.
ganin bashida niyar yin magana yasa shahid cewa ranka yadad'e munje gidan gona ne tun d'azun muna chan.
maimartaba murmushi yayi irin nasu na sarakai sannan yace Alhmdllh gaskiya ina jin dad'in hakan kuma duk ayyukan alkhairi da kukeyi a gari yana dawo min a kunnena tabbas nasan ko bayan raina nabar magajin da zai gadeni Wanda zai so kuma yatausaya ma jama'arsa tabbas kaine yafi cancanta da kakasance *Sarkin sarakai*
yarima dasauri yad'ago kai yakalli mai martaba har ya bud'e baki zaiyi magana sai kuma yafasa,
gaba d'aya fadawa suka d'auka angaishe da yarima mai jiran gado, angaishe da kwarzon namiji, angaishe da namijin zaki sarki ya gaisheka.
yarima da shahid k'ara gaishe da sarki sukayi sannan suka mik'e dasauri sauran jama'a da fadawa suma suka mik'e nan suka shiga yi ma yarima kirari har saida yafita daga fadar sannan suka zauna.
shahid saida yaraka yarima har wajen turakarsa sannan yayi masa sallama yatafi gida.
yarima yana shigowa dasauri dogarawa suka zube suna kwasar gaisuwa sannan suka mik'e suka take masa baya suna masa kira, takawarka lafiya yarima, Takawarka lafiya babban dodo mai rikita 'yan maza, takawarka lafiya sarkin sarakai, nan bayi da ma'aikata sukaita fitowa suna gaishesa tun yana amsawa har yagaji yakoma d'aga musu hannu ahaka har ya isa part d'insa dasauri wani dogari yabud'e masa d'akin,nan suka d'auka ashiga lafiya yarima, batare da yarima ya juyoba yad'aga musu hannu nan duk suka duk'a sukace munbarka lafiya yarima akwana lafiya, nan suka tashi duk suka watse, sai guards d'insa kawai suka rage yarima yana shiga bedroom d'insa kawai yawuce.
wanka yayi sannan yakwanta.
tun daga ranar suka rage had'uwa da gimbiya sumayya saidai idan tana son wani abu wajensa sannan take zuwa d'akinsa, yarima bai damuwa da rashin zuwanta hidimar gabansa kawai yake sai inyaji yana buk'atarta sannan yake zuwa d'akinta idan ma yaje sai yayi da gaske yake samu tana amince masa cikin 6acin rai suke rabuwa.
A sibitinsa da aka gina masa yana bada gudunmawa sosai baya bari ana wulak'anta masa patients kamar yarda baya bari awulak'anta masa staffs, hatta talakka idan yazo asibitin ana kar6arsa sannan kud'in magani rabi ake kar6a ana yafe musu rabi nan da nan asibitin yayi suna a garin da wajen garin.
Gimbiya sumayya business d'insu suke kud'i suna shigo mata sosai ammah har lokacin bataje tagano boutique d'in nasuba da yake a garin Abuja inda zinat tazuba ma'aikatan da suke kular musu da kayan kullum tsegumi take ma gimbiya akan rashin zuwanta tagano boutique d'in,
yau ma dai kiran gimbiya tayi a waya, gimbiya sumayya da take kishingid'e bayinta zagaye da ita tuface ake bata a baki tana ci ahankali inda gefenta baiwace take karanta mata labarai anutse, wayarta da tahau rurine yasa kowa yanutsu wadda take rik'e da wayar tatsugunna tace ranki yadad'e gashi ana kira,
gimbiya sumayya yamutsa fuska tayi tace wake kirana?
jikin haule yana kyarma tace bestie naga ansa, harararta gimbiya tayi tace ashe ke kin d'anyi karatu ba laifi ai na d'auka jahilace irinsu indo, indo da take tsaye tana ma gimbiya fiffita murmushi kawai tayi batace komai ba,
gimbiya sumayya d'aukar wayar tayi tare da cewa my zinat dafatan kina lfy?
daga chan 6angaren zinat ta amsa da lfy lou kema dafatan haka sarauniya mai jiran gado
'yar dariya sumayya tayi tare da cewa ke ni har na hangoni ko nazama sarauniyar, Allah dai yakaimu lokacin
zinat tace am wai yaushe zakizo yau fa kusan 5 months ammah shuru bakizo kikaga yadda komai yake tafiya ba? saidai kawai kiji alert d'in kud'i.
gimbiya k'ara gyara kishingid'ar tayi tare da cewa zinat wlh nima inso inzo kawai ina tsoron wulak'ancin yarima.
tsaki zinat taja tace ke wlh kina bani mamaki sai kace ba big gurl ba? yanzu saboda Allah duk class d'inki ammah kizauna wai sai yadda miji yayi dake, ke ya dai kamata kizo munfayi customers sosai kuma akwai kayan da nakeso ink'ara d'auko mana saboda haka kifitar da rana kizo,
gimbiya sumayya dogon numfashi taja sannan tace toh shikenan baby kar kidamu zanzo nima ai daman nayi missing d'inki,
dariya zinat tayi tace koma dai mekenan saidai kinzo, kinga sai kimin ko 2 weeks ne,
gimbiya sumayya tace ina ma dai laifi kice 1 week, shima sai munyi daga da yarima sannan zan samu yayarda, koma dai mekenan zamuyi waya.
nan sukayi bankwana, gimbiya sumayya tunani tashiga yi yarda zata samu tatunkari yarima da maganar batare da yak'i amincewaba.
chan kuma sai taja tsaki cikin ranta tace dolema ya amince dan babu yadda za'ayi yak'unsheni cikin gida shi yana yawon gararanbarsa a gari. bari ma yadawo.
gimbiya sumayya kallon haule tayi tace yau inaso kisamin ido ga yarima idan ya shigo kiyi min magana?
haule cike da ladabi tace tau ranki yadad'e umurninki shine abun cikawata.
wajen k'arfe tara gimbiya tagama shirinta cikin kayan baccinta sannan tad'aura alkyabba daga sama tafeshe jikinta da turare mai k'amshi sannan tafito dasauri ma'aikata da bayi suka hau gaisheta tare da yi mata kirari,
gimbiya sumayya sai yatsina take tana ji suna k'ara mata girman kai, baiwarta haule kawai tace tazo tarakata nan haule cikin sauri tataso tatake mata baya har sukaje 6angaren yarima nan ma dogarawa suka shiga gaisheta sannan suka bud'e mata k'ofa, kallon haule tayi fuskarta ba yabo tace zaki iya tafiya.
haule durk'usawa tayi k'asa tace toh ranki yadad'e atashi lafiya,
sumayya tana shiga ganin yarima baya parlour yasa dan haka tashiga bedroom tana bud'ewa yarima da yake tsaye yana sanya kaya da alama daga wanka yafito yakallota, kallo d'aya yayi mata yad'auke kai gimbiya sumayya cire alkyabtarta tayi ta aje gefe tare da takawa inda yarima yake tsaye tace my sweetheart ko intaimaka maka?
yarima bud'ar bakinsa sai cewa yayi a yau kuma? kedai kawai kifad'amin me kikeso?
gimbiya tace haba yarima daga nace zan taimaka maka shine harda tambayar me nakeso?
kenan banda ikon yi maka komai sai idan ina buk'atar wani abu.
yarima a wulak'ance yace ai hakan halinki yake, kema kuma kinsan hakan kike, yana gama fad'in haka yazagayeta yawuce yaje yahaye gadonsa yakwanta.
gimbiya sumayya tsaye tayi tana mamakin halin yarima cikin ranta tace nasan ta yadda zan 6ullo maka, itama takawa tayi tanufi gadon tahau
takwanta tare da rungume yarima tace sweetheart ni bana buk'atar komai sai kai mijina.
yarima murmushi yayi yace ashe anyi miki karatun ta nutsu gaskiya natayaki murna idan har dagaske kin gyaru.
cike da k'ulewa gimbiya tace haba yarima wai meyasa kakeson kaga ka cimun fuska wani fa lokacin har a gaban bayina da kuyangina kake yada min magana.
yarima shuru yayi baice mata komai ba, ganin haka yasa tad'ago kanta takallesa sai ganin idanuwansa a lumshe, shafa sajen fuskarsa tayi tare da yin murmushi tace my dear ba dai bacci zakayi ba,
yarima batare da ya bud'e idonsaba yace ya dai?
gimbiya sumayya bakinta takai cikin nasa nan da nan yarima yacafke suka shiga faranta ma junansu.
saida yarima yadirjeta son ransa sannan yabarka atare sukayi wanka sannan suka kwanta tana rungume a jikinsa, yarima yana mamakin sauyawar da sumayya tayi ahaka bacci yayi awon gaba da su.
da asuba ko da sukayi sallah komawa sukayi bacci sai wajen k'arfe tara sannan suka farka a tare sukayi wanka sukayi breakfast bayan sun gama gimbiya jerawa sukayi da yarima suna tafiya inda dogarawa da kuyangi suka take musu baya har saida yarima yazo wajen motar da zai je wajen aiki da ita sannan sukayi sallama dasauri wani bawa yabud'e masa motar yashiga, saida sukaga tafiyarsa sannan gimbiya tajuya suka koma gida, cikin ranta tana ayyana yadda zata biyo ma yarima ya amince batare da tashin hankali ba.
ko da yarima yadawo wajen k'arfe biyu ita taje tataresa cikin shigarta ta alfarma tafito a sarauniyarta ta asali sannan tarakasa har d'akinsa shidai yarima kansa yad'aure sosai ganin wata irin kulawa da yake samu a wajen gimbiya wadda tun satin aurensu rabon da yasameta,
ita tataimaka masa yayi wanka yashirya duk k'uiyarta ajeta tayi gefe tatattali mijinta
bayan kwana biyu yarima ne kwance da gimbiya manne da juna suna ta wasanninsu, gimbiya ganin yarima yana shirin nemanta yasa tadakatar dashi, yarima kallonta yake da mamaki idanuwansa duk sun canza kala, yarima dakyar yabud'e baki yace ya dai?
Gimbiya turo baki tayi cikin shagwa6a tace sweetheart Please wani taimako nakeso kayi min, yarima zuba mata ido yayi baice komai.
ganin haka yasa gimbiya sumayya yin murmushi tana wasa da gashin da yake kwance a k'irjinsa tace dan Allah so nake kabarni inje Abuja.
yarima da mamaki yake kallonta yace me zakiyi kuma a abuja? Sumayya d'ago kai tayi tana kallonsa tace so nake inje inga boutique d'in da muka bud'e kaga tunda aka bud'e banjeba kuma badad'i ace har tsawon wannan lokacin ban lek'aba,
yarima d'auke kai yayi tare da cewa ba zakije ba, gimbiya a firgice takallesa tace yarima meyasa? dan Allah kar kahana ni.
yarima suhail wani mugun kallo yawurga mata tare da cewa idan ke bakida hankali to ni ba mahaukaci bane, babu yadda za'ayi insaki matata tayi irin wannan tafiyar mai nisa kuma ya kike tunani mutane zasu d'aukeni? kawai akan kasuwanci?
gimbiya sumayya tashi tayi daga jikinsa cikin fushi tace wlh ban ta6a sanin kai butulu bane sai yau duk hallacin da nayi maka kwana biyu ammah baka ganiba? toh bari kaji akan *KUSUWANCI NA* zan iya yin komai dan haka muzuba mugani kuma tafiya tana nan daram ko da baka. ....
wani gigitaccen mari da yarima yad'auketa dashine yasa takasa k'arasa maganar, kallonsa take da mamaki saida 'yan cikinta sukaso sukad'a ganin yadda yake huci,
yarima dakyar ya iya bud'e baki yace ke har kin isa kidinga min shouting haka? ko dan kinga ina lalka6aki? toh bari kiji albarkacin iyayena kawai kikeci kuma babu inda zakije sannan daga yanzu kidinga ladafta maganarki idan kina a gaban *yarima suhail*, yana gama fad'in haka yad'auko rigarsa yasaka yaficce daga d'akin fuskarsa babu alamun annuri a tattare da shi ahaka yawuce yatafi part d'insa.
gimbiya tana ganin ya fita tafad'a saman gadon tacigaba da rizgar kuka takaicinta marin da yarima yayi mata tun da take iyayenta basu ta6a sa hannu suka daketaba sai yau wani yadaketa kuma wai miji.
tashi tayi tajanyo alkyabtarta tasaka tafito fuuuu dasauri kuyanginta suka mik'e zasu take mata baya cikin fushi gimbiya tadaka musu tsawa tace duk wacce takuskura tabiyoni abakin aikinta.
dasauri duk suka koma suka zauna domin sunsan abinda gimbiya tafad'a zata iya zartar da shi.
cikin sauri take tafiya kamar ta6a66a har ta isa 6angaren ummanta duk mutanen da suke gaisheta bata luraba saboda hankalinta baya a tare da ita tana cikin matsanancin bak'in ciki,
ummah da take zaune bayinta suna ta mata hidima saidai ganin gimbiya tayi kamar an jefota, a firgice ummah tatashi daga kishingid'en da take tace sumayya lafiya?
sumayya dasauri tazo tafad'a jikin ummah tare da fashewa da wani sabon kukan nan hankalin ummah ya ida tashi, cewa take sumayya kifad'a min abinda yake damunki mana,
ummah cikin 6acin rai takori ma'aitanta duk suka fita suka bar d'akin, sannan tad'ago kan sumayya cike da damuwa tace shalele wa yata6a min ke?
gimbiya share hawayen fuskarta tayi nan takwashe dukkan abinda yafaru tsakaninta da yarima tafad'a ma sultana sadiya
sultana sadiya ranta ya 6aci sosai musamman ma da taji wai ya mari sumayya, cikin 6acin rai taharzuk'a tamik'e dasauri sumayya tarik"ota tace ummah ina zakije? ummah tace sakarni inje inci mutuncinsa sai yafad'amin dalilin da yasa yamareki ko mu da muka haifeki hannunmu bai ta6a kaiwa ga fuskarkiba da sunan mari sai wani banza zai mareki.
sumayya tace ummana kibarsa kawai ai sai na rama marin da yayi min dan ba zai ta6a ta6aniba azauna lfy, nidai yanzu kisamo min mafita saboda ina da burin tafiyar nan cikin satin nan.
ummah komawa tayi tazauna tare da cewa ai dole ma ne kitafi dan haka taso muje wajen dada nasan yadda zan 6ullo ma lamarin
cike da jin dad'i sumayya tace nagode ummana wlh saisa nake k'ara sonki, murmushi sultana sadiya tayi tace ai dole inso duk abinda kikeso shalelena. nan suka tashi suka d'unguma turakar su dada. .........
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
page 6⃣
suna shiga a parlourn dada batanan saidai ma'aikatanta nan suka zube suka kwashi gaisuwa wajen gimbiya sumayya da sultana sadiya ammah ko kallon arzik'i basu samuba, gimbiya ce a wulak'ance tace dada bata nan ne?
jakadiya tace ranki yadad'e ta d'an shiga ciki ammah yanzu zata fito,
gimbiya kallon sultana sadiya tayi tace ummah muzauna kafin tafito.
sultana sadiya bata musaba nan suka zauna suna jiranta.
bayan kamar minti biyar sai ga dada tafito dasauri duk suka mik'e tsaye hatta ummah da gimbiya saida suka mik'e nan kuyangi suka d'auka angaisheki sultana takawarki lafiya, daganan sukayi shuru domin sun san dada batason ana mata kirari.
nan tazo tazauna saman kujera, sultana sadiya da gimbiya nan suka duk'a suka gaisheta, fuskar dada d'auke da fara'a ta amsa sannan suka zauna saman kujera, dada ganinsu da tayi haka yasa tasan muhimmin abune yake tafe da su dan haka tasallami kuyanginta gaba d'ayansu.
maida kallonta tayi ga sultana sadiya tace daga ganinku akwai abinda yake tafe daku ina saurarenku,
sultana sadiya murmushi tayi takalli gimbiya da tazuba mata ido tana jiran taji abinda zatace, d'auke idonta tayi daga kallonta tamaida kan dada tace ranki yadad'e daman sumayya ce tazo tasameni da maganar da ban ji dad'intaba shine nace ai ke yafi dacewa muzo mufad'a mawa saboda daga sarki sai ke ne shuwagabanninmu.
dada dai zuba ido tayi tana kallonta chan sai tagyad'a kai tace ina saurarenku.
sultana sadiya tace daman sumayya ce tasamen akan ta yi ma yarima magana domin yataimaka yabarta taje tagano yanayin yadda business d'insu yake tafiya saboda tunda suka fara wata biyar kenan ammah bata samu talek'a ba abokiyar kasuwancintata ta matsa
akan ko da sau d'ayane taje taga yanayin wajen kuma akwai wani signing da akeso tayi shine takeso ko kwana biyune tayi toh tunda tafad'a ma yarima haka nan yahauta da fad'a da cin mutunci a k'arshe ma har da marinta yayi,
haka tazomin a firgice shine nace muzo wajenki saboda ke yafi cancanta kishiga lamarin nan.
dada kallon sumayya tayi da idanuwanta suka kumbura saboda kuka, haushine yakamata ganin irin cin mutuncin da yarima yayi ma jikarta, cikin fushi tace wannan bazai ta6a yuwuwaba domin bana son azalunci wani bare ma ace nawane yazalunci d'an uwansa tafiyace kuma da bazan aminceba saboda baidaceba amatsayinta namatar yarima guda ace tana yawo kuma tunda kika taso a nan gidan sarauta bakiga iyayenki suna haka ba kuma kinsan memartaba bazai ta6a amincewa da hakanba,
gambiya sumayya marairaicewa tayi kamar zatayi kuka tace dada dan Allah kitaimaka min,
dada tace toh shikenan ai tunda har yaci mutuncinki toh sai kintafi dan haka kiramin shi a waya.
gimbiya sumayya da ummanta sunji dad'i sosai da jin zancen dada, dan haka sumayya takar6i wayar dada domin takira yarima.
yarima tunda yaje d'akinsa saman gadonsa yafad'a cike da jin haushin sumayya ammah baiyi mamakin hakanba domin daman chan yaba ma ransa da biyu take nuna masa kulawa sai idan tana neman wani abu daga garesa, a gefe guda kuma na zuciyarsa ya ji haushin marin da yayi mata domin shi a rayuwarsa ya tsani hakan.
wayarsace da tafara ringing kamar ba zai d'aukaba saida takusan tsinkewa sannan yad'auko ganin sunan dadane yasa yatashi zaune tare da yin picking d'in wayar yasa a kunnensa yayi sallama,
dada ko amsa masa sallamar batayiba cikin fad'a tace toh marar mutunci kazo kasameni ina jiranka yanzun nan kar kuma kakuskura ka6ata min lokaci domin idan bakazo cikin lokaciba ba kaiba hatta mahaifinka sai ransa ya 6aci, tana gama fad'in haka takashe wayar.
yarima haushine yakamasa jin rashin mutuncin da dada tayi masa kuma wai harda mahaifinsa tsaki yaja yace tabbas wannan nasan had'in sumayya ne lallai yarinyar nan batada mutunci, tashi yayi yashiga toilet yayi wanka cikin sauri yafito yashirya sannan yakama hanyar 6angarensu dada, hana dogarawa yayi surakasa shi kad'ai yatafi yana tafiyarsa ta k'asaita babu alamun fara'a tare da shi tsakaninsa da mutane saidai yad'aga musu hannu ko da daman halinsane hakan.
baidamu da gaisuwar da kuyangi sukeyi masaba yashiga d'akin da sallamarsa ko kallon inda su gimbiya suke baiyi ba yazauna cike da izza.
dada sakin baki tayi tana kallonsa, gaisheta yayi, bata amsa masaba tace me yahad'aka da matarka?
murmushi mai aji yarima yayi yace dada ko gaisuwar ma baza'a amsa min ba?
dada tace bana buk'atarta karik'e abunka, nace me yahad'aka da sumayya,
yarima sai a lokaci yakalli sumayya da sultana Sadiya yayi murmushi yace ashe ummah ce barka da rana.
sultana sadiya kamar tad'aura hannu saman kai tafasa ihu saboda takaicin yadda yarima yayi mata, ganinta a matsayinta na uwar matarsa ammah baya ji zai iya gaisheta cikin girmamawa.
ganin yadda dada tatsaresa da ido yasa yace dada wani abu tace miki ya faru a tsakaninmu?
dada tace kai banason shashanci ashe bakada mutunci, dan rashin imani har ka iya d'aga hannu kamari matarka, toh bari kaji wannan yazama nafarko kuma na k'arshe sannan maganar tafiyar da tace zatayi inaso kasani dole kabarta tatafi dan bak'in ciki d'an abinda take samune yake tsone maka ido.
murmushi yarima yayi yana kallon kaka sannan daga baya yamaida kallonsa ga gimbiya da tatsaresa da ido yace toh kinji dai abinda dada tace sannan yamik'e tare da kallon dada yace toh dada nabarku lafiya.
dada nace nashiga ukku ni Asma'u yanzun suhail saboda Allah baka d'aukeni da daraja ba? ina maka magana zaka tashi?
yarima komawa yayi yazauna tare da cewa sorry dada ba haka bane kawai naga kin yanke hukunci saisa.
da mamaki dada take kallonsa tace kana nufin kai baka aminceba?
yarima suhail shuru yayi kamar ba zaiyi maganaba saboda maganar da yakeyi ta gunduresa ga wani irin haushin sumayya da yakeji da kullum batada buri sai na had'asa da su dada, sai chan yace ammah dada kin yanke hukunci batare da kinji nawa uzurinba.
dada tace karik'e abunka domin babu abinda zaka fad'amin tunda ka gama zaluntar 'yar uwarka ni yanzu amincewarka nakeso
yarima cike da jin haushi yace na amince saboda ke dada, wani murmushin mugunta yayi yace ammah dai duk abinda yafaru ina gargad'inki da kiyi kuka da kanki sumayya.
sultana sadiya a fusace tace insha Allah ba abinda zai faru sai alkhairi bakinka da bak'in nufinka sukoma maka, sumayya tace wlh kau ummah .
yarima murmushi kawai yayi baice komaiba dada tace toh ka kyauta ammah yanzu sai kabata hak'urin marin da kayi mata kuyafe ma juna domin farin cikinku da zaman lafiya mukeso,
yarima wani irin kallo yayi ma dada domin yasan bayan mahaifiyarsa sai dada kawai yasan matan da zai iya ba hak'uri, duba time yayi sannan yace yanzu dai bari intafi saboda kaina ya fara ciwo.
ganin dada batace komaiba yasa yarima yamik'e tare da cewa na barki lafiya ranki yadad'e sannan yawuce cikin takunsa yabar d'akin.
gaba d'aya binsa sukayi da kallo cike da mamakin halin yarima, sultana sadiya ko k'arshen k'ulewa ta k'ule ta cika fam.
dada kallonta tamaido agaresu tace saidai hak'uri kunsan halin yarima suhail wani lokacin hatta ni kaina nuna min yake kamar ban isa da shi ba ammah dai Alhmdllh tunda ya amince kitafi ni nasan yadda zanyi da maimartaba sai kije kifara shiri kifitar da rana koma dai mi kenan zan fad'a miki ammah dan girman Allah kar kidad'e domin kinsan halin mijin nan naki.
Gimbiya sumayya cike da jin dad'i tace insha Allahu dada ba zan dad'eba baifi inyi 1wk ba, dada tace toh shikenan Allah yataimaka sukace Ameen, sannan sultana sadiya da Gimbiya suka k'ara duk'awa suka kwashi gaisuwa sannan sukayi mata sallama suka bar d'akin cike da jin dad'in nasarar da suka samu.
Yarima suhail ransa ya 6aci sosai kawai daman yana 6oyewane dan kar sugane halin da yake ciki yana fitowa direct 6angaren iyayensa yanufa a parlour yatarar da ummi kishingid'e ana mata tausa,
bayi da kuyangi suna ta yi mata hidima, suna ganinsa ko yazube yakwashi gaisuwa, yarima batare da ya tankaba yad'aga musu hannu cikin sauri kowa yatashi suka fita daga d'akin takawa yayi ya isa Saman kujerar da ummi take zaune zuba masa ido ummi tayi tana kallonsa, yarima zama yayi shima yana kallonta da idanuwansa da suka kad'a daga launin fari zuwa na ja saboda 6acin rai sannan yajanye fuskarsa daga kallonta,
ummi tace suhail miyake faruwa ne? kafad'a min damuwarka.
yarima suhail saida yad'auki kusan minti biyu kamar ba zaiyi magana ba sai kuma chan yace ummi yanzu saboda Allah ina auren sumayya ammah ta d'aukeni kamar ba mijintaba ban isa in hanata abu ba sai ta had'ani da dada, kullum cikin kai k'arata take.
shuru yad'anyi nalokaci sannan yakalli mahaifiyar tasa da tazuba masa ido yace wai abun haushin har da mahaifiyarta take goyan mata baya toh ni cewa nayi bata min laifi? duk hak'urin da nake da ita bata gani duk abinda takemin wa nata6a samu nafad'a ma wa? kawai ina kyaletane albarkacin iyayenmu da zumuncin mu.
girgiza kai yayi cike da takaici yace ummi hak'uri ya k'are zan d'au k'wak'waran mataki akai.
Sultana Bilkisu cike da tausayin d'an nata take kallonsa domin tasan halin d'an nata ko da za'a cutar da shi ba ya ta6a damuwa saidai idan an kaisa k'arshe shine zakaga 6acin ransa.
tashi ummi tayi daga kishingid'en da take tarik'o hannun d'an nata tace suhail kacigaba da hak'urin da nasanka da shi insha Allahu komai zai zo k'arshe, wani lokacin dakanta zata daina.
yarima suhail murmushi yayi wanda iyakarsa baki sannan yace ummi har wane lokacin kuma? kiduba kiga tsawon dad'ewarmu ammah kullum halinta k'ara canzasa take ni wlh da ace ina da wadda nakeso da aure zan k'ara domin sumayya da ita da babu, banbancinsu kad'an ne.
ummi zaro ido tayi tace karufa mana asiri yarima wane irin aure? dukafa yanzu aurenku baifi shekara d'aya ba.
murmushin takaici yarima yayi yace ummi ba zaku ta6a fahimtataba.
ummi tace indai baso kake a zargemuba.
yarima suhail jingine kansa yayi a kan kujera tare da lumshe idonsa yana jin wani iri a ransa.
sultana bilkisu kallon d'an nata take cike da tausayi ganin tunda yayi auren nan yabi ya rame tabbas tasan akwai abinda yake damunsa dandai miskilancinsa ya zame masa yana da zurfin ciki sosai.
itama jan bakinta tayi tayi shuru domin tasan d'an nata baya da son hayaniya.
A ranar yarima bai fitaba d'akin ummi yawuni ak'arshema bedroom d'in ummi yakoma yasha baccinsa, ummi hana kowa tayi yashiga.
Gimbiya sumayya suna komawa turakar sultana sadiya kallon ummantata tayi cike da farin ciki tace wlh ummi kin gama min komai, tabbas nayi sa'ar uwa mai son farin cikina.
Sultana murmushi tayi tace ai wlh akanki ba na jin zan iya ragama kowa, wannan mijin naki na tsanesa dandai babu yarda zanyi ne, gimbiya zaro ido tayi tace ummah mijin nawa kika tsana?
sultana Sadiya tace eh man saboda ni naci burin in haifi Wanda zai gaji memartaba ammah ban haifaba saisa tunda aka haifesa naji bana sonsa.
dariya gimbiya tayi tace toh ai yanzu sai kikwantar da hankalinki tunda ni yake aure kuma duk wanda zai gaji masarautarnan ni zan haifa masa.
Sultana tace hakane ammah ai har yanzu naga bawani bayani wlh hankalina tashi yake ganin kunyi shekara da'ya har da d'oriya baki haihuba.
gimbiya tace haba ummah wa yake ta haihuwa yanzu sai mun gama cin zamaninmu sannan zan haihu
sultana sadiya sakin baki tayi tana kallonta da mamaki tace sumayya ban ta6a sanin ke sakara bace sai a yanzu keda kike auren yarima ai kyau ace kinyi saurin haihuwa ko da ace biyune kibari kiyi in yaso daga baya sai ki tsayar da haihuwar sai lokacin da kikeso.
Gimbiya sumayya cikin fushi tace gaskiya ummah ni nagama tsara yadda nakeso rayuwata tatafi kuma na tabbata yarima bazai ta6a k'ara aure ba domin su dada ba zasu ta6a amincewa da hakan ba.
sultana sadiya tace kima daina wannan maganar wlh ko ni ba zan ta6a bari yayi miki kishiba, nidai burina kijanye wannan plan d'in naki kihaifar mana baby,
gimbiya mik'ewa tayi tsaye tana gyara alkyabtarta tace ummah bari inje dai infara shirin tafiyarnan da zanyi saboda jibi nakeso inyita nabarki lafiya.
Sultana Sadiya bin d'iyartata tayi da kallo domin tasan dandai ajanye maganar haihuwarne shiyasa tace zata tafi, murmushi tayi tare da girgiza kai tace sumayya kenan Allah yasa kifahimci abinda nake nufi. .....
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
?ππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_sak'on gaisuwata agareku *Zaynav mtz fan's, Yarima suhail fan's 1&2, Ummun meenal fan's, hibbatullah fan's, janaf fan's, zauren sainah fan's, mummyn khalil fan's Aufana true fan's* da sauran groups d'in da ban samu nalissafobaππ ina jin dad'in comments d'inku Allah yabar k'auna_
_*Wannan page d'in nakune my hafnan, Janaf, Aysha nd ummun meenal ina ji daku cikin zuciyanaππ*_
page 7⃣
yarima sai dare sannan yabaro turakar su ummi yakoma part d'insu, saida yayi wanka yashirya sannan yafito dining yad'anci abinci bayan ya gama kallo yakunna yana yi, bud'e k'ofar akayi aka shigo bai ko d'ago kai ba domin ya san gimbiya ce.
gimbiya sumayya ganin bai kalletaba yasa tatako tazauna gefensa cike da isa tace daman nazo infad'a maka jibine fa zan tafi kuma kasan ba zan iya tafiya mai tsayi a motaba dan haka sai kabada kud'i ayomin Visa,
wani mugun kallo da yarima yawurga mata saida hantar cikinta takad'a, batare da ya janye idonsa a garetaba yace ni na'aikeki?
Gimbiya sumayya itama kallonsa take tace toh naga kai yafi dacewa da kasa ayankar min ticket tunda k'ark'ashinka nake.
yarima shuru yayi kamar ba zaice wani abuba sai chan kuma yace ke ban ta6a sanin bakida hankaliba sai yanzu baizama dole inyi miki hakanba kuma bana tunanin akwai Wanda ya isa yasani dole, dan haka tashi kifitar min daga d'aki tun kan in6ata miki rai.
gimbiya sumayya mik'ewa tayi saida takai bakin k'ofa sannan tajuyo takalli yarima suhail tace koma dai me kenan katabbatar zuwa gobe ka yimin abinda nakeso inkuma bahakaba zan fad'ama dada, tana gama fad'in haka taficce daga d"akin.
yarima suhail takaicine da bak'in ciki suka taru sukayi masa yawa tsaki yaja kawai ak'arshe ma yakashe kallon yatashi yashige bedroom d'insa cike da 6acin rai yakwanta, yanajin wani iri a zuciya ji yake an cucesa da aka za6a masa gimbiya sumayya a matsayin matarsa domin kwatakwata halinta baiyi masaba.
ak'arshe wayarsa yajawo yakira d'aya daga cikin yaransa yace zuwa gobe a tabbatar anyi ma sumayya Visa.
Wanshe kare wajen k'arfe sha biyu da yarima yagama shirinsa fitowa yayi yanufi d'akin gimbiya sumayya inda yataddata a lokacin tafito daga wanka, a wulak'ance yakalleta sannan yawurga mata ticket yace ba dan halinki nasa akayi mikiba dan ganin damanane.
harararsa gimbiya tayi tace eh ahaka d'in dai saida nayi magana, yarima suhail murmushin mugunta yayi sannan yataka inda sumayya take, dak'arfi yajawota tafad'o jikinsa har saida tad'anyi 'yar k'ara sannan yace sumayya inaso kisani darajar iyayena kawai kikeci da badan hakaba wlh da sai kin gane kuskurenki.
gimbiya sumayya tace suhail kadad'e baka nuna min kuskurenaba kuma yadda kake tak'ama da sarautarnan nima ai jinintane, bamuda banbanci ni da kai, kuma idan ka cika d'an halak kata6ani kagani, kuma bari kaji jikina kagama samunsa tunda har kata6amin fuskata jiya yanzu daidai nake da kai.
yarima suhail d'auke ta yayi da mari yak'ara mata wani tare da wurgata saman gado yace banyi niyar kwanciya da ke ba ammah yau zan nuna miki na ciki d'an halakne ni, saman gadon yabita tare da fizge towel d'in da yake jikinta nan suka shiga kokawa ak'arshe yarima suhail yasakarmata nauyinsa.
mugunta yasa mata yadirjeta son ransa, gimbiya sumayya kuka kawai take, yarima saida yagaji dan kansa sannan yabarta,
kayansa yad'auka yasanya bai ko k'ara kallon inda sumayya take kwanceba tana ta ja masa Allah ya isa, fita yayi daga d'akin yakoma part d'insa yayi wanka yashirya sannan yaje fada yagaishe da sarki daga nan yafita yabar gidan.
Tun daga lokacin basu k'ara had'a hanya da gimbiya sumayya ba baima san lokacin da tatafiba sai wajen dada yakeji,
hatta umman sumayya yanzu ko ya gaisheta bata amsawa dan haka shima yadaina gaisheta, ko da ace tana tare da abban sumayya toh abbah kawai yake gaishewa tsakaninsa da ita saidai tahararesa shikuma yanuna ko inkula.
__________________
awata anguwa mai suna yamza wata yarinyace take tafita a nutse kanta a k'asa yarinyar ba zata gasa shekara ashirinba wani gidane tashiga gidan da kagansa kasan bamasu hali bane saidai rufin asiri, da sallamarta tashiga, wata matace da nahango zaune tana wanke-wanke ciki-ciki ta amsa mata sallamar
cike da ladabi zarah tak'arasa inda matar take tare da tsugunnawa tace mama sannu da gida.
harara matar tawurgamata tace ke shine bakiyi min wanke-wankeba kika kama hanya kika fita daga gidan ko?
zarah cike da nutsuwa tace mama dan Allah kiyi hak'uri wlh ganinayi na makara islamiyya shiyasa.
rik'e baki mama tayi tace eh islamiyya fad'amin nida banyi islamiyarba, ke ga ustaziya ko? to wlh inbaki canza haliba haka zakizo kik'are cikin gida, kiduba kiga 'yan uwanki kullum sai sun fita sun samo mana 'yan kud'in da zamuyi hidima ammah ke kina nan jibge a cikin gida saidai aciyar dake ashayar da ke iyakarki kashi, toh wlh indai bakiyi dagaskeba sai kin rasa mashinshini domin wannan girman kan naki babu inda zai kaiki.
zarah shuru tayi batace komai ba domin idan da sabo ta saba da halin iyayen nata,
tsawa mama tadakamata tace watau ga mahaukaciya ina magana shine kikayi shuru kika kyaleni watakau ga mahaukaciya tana magana.
zarah cikin nutsuwa tace Allah yabaki hak'uri mama kawo wanke-wanken in k'arasa miki.
ummah d'auraye hannunta tayi tamik'e tace ai ko bakiceba daman ke zaki idashi tunda baki aikin komai sai karatu saikace alhuda-huda.
mama tana tashi zarah tacire hijab d'inta tarataye saman igiya sannan tazauna tacigaba da wanke-wanken.
tana cikin yi saiga yayarta tashigo babu ko sallama kallonta zarah tayi cike da takaicin ganin irin shigar da take jikinta kayan sun matseta gyalen da tayafa ko dashi k'ara babu, d'auke kanta tayi daga kallonta tacigaba da wanke-wanke tana addu'a cikin zuciyarta Allah yashirya su sugane gaskiya.
muryar yaya rauda ce tajiyo tana cewa zarah ina mamanmu take? batare da takalletaba tace tana cikin d'aki.
Rauda kira tashiga kwala ma mama daga inda take tsaye, mama datake d'aka dasauri tafito kallabinta a hannu tana washe baki tace a'ah 'yar albarka har kin dawo?
Rauda yamutsa fuska tayi tace eh ga wannan ledar da take hannunta tamik'a mata, ummah cike da farin ciki ta amsa tana cewa me muka samu yau?
malam yusuf ne yashigo gidan yana cewa a'a 'yar baba ai naga lokacin da aka safkeki kinga har da 'yan canji mutumin yabani gaskiya yana da kirki.
Rauda yamutse fuskarta tayi tace ammah ai abba nace kadaina tambayarsu kud'i inkana tambayarsu ai sai kaja surainani ,
abba yace 'yar baba bafa tambayarsu nakeba sune suke bani kuma kinga babu kyau maida hannun kyauta baya ko ba haka bane Zainabu?
mama tace hakane malam, yanzu dai mik'o wani abu nan dan musamu daren nan muci mai d'an dad'i-dad'i.
abba yace toh naji yanzu dai menene cikin ledarnan?
mama duba ledar tayi tare da washe baki tace ashe kazace yau shagali zamuyi kenan.
Abba ma washe baki yayi yace gaskiya naji dad'i daman wannan bakin nawa yakwana biyu bai ci namaba, ammah dai 'yar baba Allah yaimiki albarka,
mama tace toh yanzu dai kakawo asiyo kayan miya muyi d'an pepper chicken,
abbah dubu d'aya yamik'a mata yace gashi sai akasiyo har da buredi wanda zamu d'an dangwala romon ai haka zaifi ko?
mama tace eh malam, ai saima autarka tadawo muga ita mi zata kawo mana, ai ni yau naga amfanin haihuwar 'ya'ya mata daman malam ai nafad'a maka 'ya'ya mata dad'i garesu,
malam yace hakane sannan yakai dubansa ga zarah da take tsugunne tana ta wanke-wanke, yamutsa fuska yayi yace Asma'u wlh d'iyar chan duk cikin 'ya'yana ita kad'aice batada k'ashin arzik'i wani ma lokacin ji nake anya jininace?
ummah tayi karaf tace a'ah malam wannan cin mutuncin da me yayi kama idan ba d'iyarka bace toh wanene ubanta? ko akwai wani mijin da na aura bayanka? ko kuma kana nufin ina bin mazan banza.
malam yace a"a zainabu nidai ina nufin kwata-kwata bata d'auko halinaba, kiduba kiga ko farin jinin samarin nan ita batadashi,
ummah tace ah toh yanzu naji bayani, ai malam kakalli wannan munafukar kawai bak'in ciki kawai take yi mana dan kar muci moriyarta kasan yanzu sai kahaifi d'a baka haifi halinsaba, wlh akwai samarin wulak'antasu kawai take tana korarsu sai wannan matsiyacin malamin nata da ta lik'e mawa me na k'asa yaci bare yaba nasama.
malam yace oh ni wlh daman nayi zaton haka ni wlh wannan sakaryar d'iyar bansan yaushe zata waye kamar 'yan uwantaba, Allah dai yashiryata.
mama tace Ameen dai
malam yace yanzu dai dafa mana kazar a d'ansa kayan yaji nasan zatafi dad'i haka bari ind'an fita.
ummah tace toh malam adawo lafiya.
zarah dai zaune take tana wanke-wankenta duk firar da iyayenta sukeyi akan kunnenta hawayene yacika mata ido tana jin wani abu ya tokare mata mak'oshi saboda takaicin halin iyayenta, cikin ranta addu'a take Allah yashirya mata iyayenta da 'yan uwanta sugane gaskiya.
bayan ta gama alwallah tad'aura sannan tad'auki hijab d'inta tashige d'akinsu, lokacin yaya rauda tana shafa da alamu daga wanka tafito.
zarah shimfid'a darduma tayi tad'auko alk'ur'aninta tana karantawa har aka tada sallar magrib sannan tatashi tayi sallah
ido tazuba ma rauda tana kallon yadda take sallah cikin sauri babu alamun nutsuwa atare da sallartata
ko da rauda tagama sallar zarah kallonta tayi cike da nutsuwa tace yaya rauda ya kamata idan kina sallah kidinga nutsuwa domin duk abinda zakije nema yana a hannun wanda kike gabansa a yanzu.
harararta Rauda tayi tace toh malama yimin wa'azi tunda kinfini sani, kinsan Allah zarah idan baki fita daga hancinaba sai na 6a66allaki a cikin gidan nan
kuma da kike maganar sallah ai Allah da zuciyar mutum yake amfani, kuma idan ke kike raba ladar toh dan girman Allah kihanani 'yar bak'in ciki kawai.
tana gama fad'in haka tatashi fuuuu taficce tabar d'akin tana ta mita.......
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
page 8⃣
tashi tayi fuuu tawuce tabar d'akin tana mita ita dai zarah bin rauda tayi da kallo cike da bak'in cikin halin 'yan gidansu a kullum addu'anta Allah yasa sugane gaskiya.
addu'a tayi sannan tatashi tacire hijab d'inta tafito takar6i kayan miyan da suke hannun mama tajajjaga mata sannan tatambayeta idan akwai abinda za'a, mama tace a'a,
sannan tawuce takoma d'aki koda tayi sallar isha'i zama tayi tana ta bitar karatunta sai wajen k'arfe takwas sannan k'anwarta Aysha tadawo gida hannunta d'auke da leda tun daga zaure tafara kwalah ma mama kira
mama da take tsugunne tana hura huta jikinta yana 6ari tamik'e tana washe baki tace a'ah autata har kin dawo.
Aysha tana yatsine fuska tace eh wlh ,
mama kar6ar ledar hannun Aysha tayi tace me kuma muka samu?
Aysha kar6e ledarta tayi tace kai mamanmu ba fa wani abu bane d'inkinane nabiya na amso,
fara'ar da take d'auke a fuskar mama ce taragu tace kina nufin babu abinda kika kawo mana? kiduba kiga 'yar uwarki kaza takawo mana gata chan saman wuta ina mana ferfesu,
Aysha tace oh mama kedai kullum burinki abaki kud'i, jakkarta tabud'e tad'auko 2k tace gashinan kid'auki d'aya kiba abbah d'aya.
mama kar6a tayi tana washe baki tace kai 'yar albarka gaskiya naji dad'i ammah ba zan ba mahaifinkuba dan shima d'azun ya samu kud'i kar ma kikuskura kifad'a masa kin bamu kud'i, Aysha wucewa tayi tanufi d'akinsu tana cewa nidai mamanmu wannan tsakaninku da abbane,
zarah tana zaune saman darduma tana sauraren dukkan abinda suke tattaunawa,
Aysha ce tashigo d'akin tana cewa wash wlh na gaji, jafe jakkarta tayi bisa katifa takalli zarah tace yaya zarah kina nan kina ta bitar karatun?
zarah batare da takalletaba tace Aysha daga ina kike? meyasa kikeso kiga kinyi dare a waje a matsayinki na mace?
Aysha turo baki tayi tace ammah ai mama tasan da tafiyata, zarah aje littafin da yake hannunta tayi tare da tattara dukkan hankalinta ga k'anwarta tace Aysha wannan rayuwar da kika d'aukar ma kanki ba mai 6ullewa bace k'ara tun wuri kigyara tun kan lokaci yak'uremiki gudun kar kiyi nadamar da batada amfani.
mama ce da tazo wucewa tajiyota tana magana lek'owatayi d'akin takalli zarah taharareta tace toh sarkin 6akin ciki mekike ce mata? badai hure mata kunne kikeyi ba dai ko?
zarah kallon mama tayi tace a'a mama kawai ina bata shawarace d's zata fisheta.
salati mama tahau yi tace nashiga ukku ni Zainabu yau Allah yabani d'iya mai bak'in ciki da ni, yanzu 'yan kud'in da take kawo mana ne kike ma bak'in ciki? toh idan suka zauna gidan ubanwa zai dinga ciyar da mu? kinsan dai mahaifinku bai bada abinda zamu ci muk'oshi .
zarah cikin lallashi tace mama kiyi hak'uri ni ba haka nake nufiba, idan na 6ata miki rai kiyi hak'uri.
mama tace daman ai haka zakice munafuka kawai wlh da ace ba ni nahaifekiba da na ce ke ba jinina bace.
zarah dai shuru tayi tana sauraren maganganun mama har mama tagama fad'anta tafita tabar d'akin.
karatunma zarah kasa cigaba tayi saboda haushi nan ta tattare littafan tamaida su ajakkarta, sannan tahaye saman katifarsu takwanta.
Aysha wanka tayo tashirya akan idon zarah wani yakirata a waya tafita tabar gidan, 'yar nokianta ce da taji tana ruri yasa takai idanunta a wajen ganin wanda yake kiranta saka tayi murmushi har dimples d'inta suka lotsa cike da farin ciki tayi picking domin tasan ko bakomai Malam Bello zai d'ebe mata kewa sallamata tayi masa, shima cike da farin ciki ya amsa mata, bayan sun gaisa malam Bello yace gimbiya zarah ya gida?
murmushi zarah tayi tace wai gimbiya dan Allah kama daina kar kaja akamani
dariya malam Bello yayi yace ai gimbiyarce.
zarah tace hmm dan Allah kadaina.
malam Bello yace toh malama zarah ta gida da mutanen gida?
zarah tace Lafiya lou Alhmdllh.
malam musa gyaran murya yayi yace zarah wlh ina sonki so nagaskiya dan Allah kitaimaka kirik'e min amanar kanki domin har ga Allah aurenki nake son yi, dama zaki bani dama da naturo an aje maganata inyaso daga baya idan nak'are karatuna sai muyi aure.
zarah murmushi tayi tace kar kadamu malam ba ma sai ka turoba insha Allahu banda miji sai kai domin ka cancanchi kakasance mijina inko kaga ban aurekaba toh wannan daga Allah ne,
malam Bello dogon numfashi yaja yace Allah yasa haka my zarah, wlh gani nake idan narasaki toh na rasa farin cikina domin kece kawai kika dace da rayuwata.
zarah cike da tausayinsa tace kar kadamu malam insha Allahu ma ba zaka ta6a rasaniba.
Bello cike da jin dad'i yace nagode sosai zarah, yanzu inzo mugaisa ko?
zarah kallon agogo tayi tace a'a malam yanzu dare yayi kadai bari sai gobe.
malam Bello yace toh malama zarah duk yadda kikeso ai haka za'ayi Allah yakaimu, murmushi zarah tayi tace toh malam ahuta lafiya sai Allah yakaimu.
malam bello yace au korata ma akeyi?
zarah tace wane ni inkoreka kawai dai zanyi bacci ne,
bello yace toh gimbiya atashi lafiya
zarah tace Allah yasa, nan sukayi sallama sannan suka kashe wayoyin.
zarah bin wayar tayi da kallo tana murmushi domin har cikin ranta tana jin malam bello ko da tasan mayuwacine iyayenta su amince da shi tunda baida kud'i ammah ta ci alwashin shikad'ai ne mutumin da zata iya aure saidai wani hukuncin daga ubangiji.....kiran da mama takeyi matane yakatseta daga tunanin da takeyi, dasauri tatashi tafita a tsakar gida tasamu mama da abba Zaune saman tabarma suna cin nama suna dangwala romon da bread,
kusa da mama tatsugunna tace mama gani, mama fuskarta a d'aure tace ga naki nan su kuma tunda su suka kawo saisa nafitar masu da nasu yafi yawa,
kar6a zarah tayi tace nagode sannan tatashi takoma d'akinta ,
abbah binta yayi da kallo cike da takaici yace ni inma rasa abinda yarinyarnan take k'unshewa a d'aki kullum tana d'aki ko fitowa batayi tasha iska.
ummah tana yagar nama tace ita dai tasani matsalarta.
zarah tana shiga d'akinsu zama tayi taci naman bayan ta gama tafiddo kwanon sannan tayi ma iyayen sallama takoma d'aki saida tayi wanka sannan takwanta.
duk yadda taso tayi bacci ammah takasa tunanin wulak'ancin da takesha wajen mutanene da halin iyayenta da gwagwarmayar da tasha ne yasa tafara hawaye kullum batada buri da yawuce taga iyayenta da 'yan uwanta sun canza hali musamman ma idan tatuna da lokacin da suna yara haka suka taso a sake iyayensu basa kwa6arsu
Malam musa da Zainab sune iyayensu su ukkune suka haifa, Rauda itace babba sai zarah da take bi mata sai 'yar autarsu Aysha ko da ba wani tserataiya bane irin sosai d'innan a tsakaninsu k'ara ma Rauda itace taba zarah shekara biyar, inda zarah kuma taba Aysha shekara biyu.
Suna da kyau sosai kasancewar iyayensu fulanine na usuli, saidai zarah itace zaka kallah kaga sak mama, inda su Rauda da Aysha suke kama da abbansu saisa zarah tayi musu fintinkau wajen kyau dan ma Suna halin rashi.
sunyi karatu bakin gwalgwado dan dukansu daga secondary school suka tsaya da karatunsu babu wacce tacigaba duk suna gida Zaune, zarah ma ce tashiga makarantar koyan sana'a tayi Catrine (6angaren girki) sannan itace mai zuwa islamiyya ammah su rauda babu wacce take da lokacin zuwa islamiyya sharholiyarsu kawai sukeyi.
abun mamakinma a gaban iyayen nasu ake zuwa ad'aukesu ammah iyayensu ko da sau d'aya basu ta6a nuna 6acin ransuba domin basuda burin da yawuce akawo musu kud'i,
hatta abincin da zasu ci wani lokacin rauda da Aysha ne suke ciyar da su kasancewar Abbah baida tak'amaiman aikinyi daman ginine da kanikanci shima sai idan ya samu yakeyi.
ahakanma iyayensu sun tsani suga talakawa suna ra6ar 'ya'yansu, su ma kansu su rauda basa son talakawa 'yan uwansu saisa duk samarinsu masu kud'ine.
duk wanda zai nuna yana son zarah toh wulak'ancine sai yasha wajenta,
mama tun tana fad'a har tagaji takyaleta,
hantarace da wulak'anci babu wanda bata sha wajensu, ko kud'in wata na islamiyya sai tayi dagaske take samu wajen iyayenta inma basu bataba toh wajen k'anwarta ko yaya rauda take samu su ma sai tasha wulak'anci da gori suke bata.
kayan shafa ma sai sunga dama idan zasu siyo nasu suke had'awa da ita suna d'an siyo mata mai da powder da turare shima a wulak'ance ake bata.
duk aikin gida ita aka sakarmawa inba ka saniba ba zaka ta6a cewa zarah d'iyar gidan bace sai kad'auka *'YAR RIK'O* ce,
wa'azi nasiha babu wanda batayi ma 'yan gidan nasuba ammah sunbi son zuciyansu da na iyayensu.
zarah tun abin yana damunta ammah yanzu ya rage damunta
Malam bello malamin islamiyyarsu zarah ne yana da kirki sosai jininsu ya had'u da zarah saisa suke mutunci, daga baya yanuna yana sonta dakyar yasamu zarah ta amince masa suna soyayya, duk wasu littafan karatun zarah shi yake siya mata.
zarah tun tana nuna bata so ammah daga baya tahak'ura tana kar6a dan tasan iyayenta ba zasu ta6a siya mataba kuma babu inda zata samu kud'i tasiya, shima dan taga yana da hankali da nutsuwa kuma a yadda yake nunawa shi dan Allah yakeyi mata kuma yana so yasamu lada idan ta karanta.
Malam Bello karatu yake a university sannan yana tsare ma wani mutum shago da kud'in islamiyya da ake biyansa a nan yake samun d'an abinda zai rik'e kasancewar iyayensa suma ba masu hali bane sosai.
mama lokacin da tagano zarah tana soyayya da shi har kusan dukanta tayi tace me zatayi da wannan talakkan me nak'asa yaci bare yaba nasama ita dai zarah shuru tayi domin tasan abinda mama take nufi, ammah a ranta itadai bata da burin auren kowa sai malam bello dan shine kad'ai yake taimakonta.
bud'a k'ofar da akayine yadawo da ita daga kogon tunanin da ta lula, Aysha ce tashigo da leda a hannunta tana waya, zarah duba agogo tayi taga kusan k'arfe goma da rabi dan haka tajuya domin tayi bacci cike da takaicin maganganun da Aysha takeyi a waya batare a taji kunya ko nauyin Zarah ba.
ahaka Aysha tagama wayan itama takwanta har sukayi bacci yaya Rauda bata dawoba.
da asuba zarah har tayi sallah ammah Aysha bata tatashi ko da zarah tak'ara tadata cewa tayi dan Allah kikyaleni idan natashi zanyi nace miki.
zarah tace haba Aysha yanzu har sai gari yayi haske sannan zaki tashi kiyi sallah?
Aysha tace ko ma dai yaushe nayi babu ruwanki malama dan haka kikyaleni.
zarah tsaki taja tace Allah yakyauta sannan tacigaba da laziminta har gari yafara haske sannan tamik'e taje tayi wanke-wanke tagyara gida bayan tagama tadawo tayi kwanciyarta sai alokacin Aysha tatashi tayi sallah.
wajen k'arfe goma zarah tafarka lokacin babu kowa d'akin batayi mamakin hakanba domin tasan Aysha ta tafi gantalinta daman ita yaya Raiuda ba gidan takwana ba.
zarah gyara d'akin tafara yi sannan tafito tayi brush tawuce d'akin mama lokacin Abbah yana shirin fita nan taduk'a bakin k'ofa tace Abbah ina kwananku.
Abbah ciki-ciki ya amsa mata, mama kau daman harararta tayi tace yanzu saboda Allah zarah sai yanzu kika tashi baccin?
zarah tace mama ai saida nagama komai sannan nakwanta,
mama cikin fad'a tace haka dai zaki k'are daga bacci sai zaman gida ko 'yan kud'in kashewar baki yarda kifita kisamo saboda bak'in cikin kar muma muci daga wajenki.
zarah shuru tayi mama tace toh yau dai ba ayi karin kumalloba muma nan ruwan Lipton da sauran biredin jiyane muka ci,
Kinga da ace kina da kud'inki ai da kin d'an siyo ko indomie ce kinci irin yadda 'yan uwanki sukeyi, yanzu dai bari inbaki kije kiyo mani cefane
zarah tace toh mama
mama kallon abbah tayi tace malam kabada kud'in cefanen.
abbah laluba aljihun rigarsa yayi yad'auko d'ari biyu yamik'a mata, mama tsayawa tayi tana kallonsa
yace ki amsa mana,
mama tace haba malam me d'ari biyu zatayi mana bamu da fa abinda zamu dafa muci,
abbah yace toh nidai su gareni koma minene kujalabta kuyi abincin.
mama tace gaskiya wannan babu abinda zatayi mana.
abbah yace kihad'a da canjin jiya ai nasan dai anrage wani abu cikin d'ari biyar d'in.
mama tace naira sittin fa ce.
yace toh inbakuso sai inmaida abuna aljihu.
Jin haka yasa mama takar6i kud'in domin tasan zai iya.
bayan ya fita mama kallon zarah tayi tace ni tashi kimik'o min jakkata ko d'ari biyu ce ink'ara dan ma Allah yaso akwai kud'in da Aysha tabani jiya da ban san yau ya zamuyi ba.
zarah tashi tayi taje tad'auko ma mama jakkar tamik'a mata.
mama d'ari biyar tabata tace kisiyo garin d'an wake rabi sai mai rabin gwangwani da tashi da Maggi ko shine musamu abinda zamu saka ma bakunanmu kafin yarana sudawo
kar6a zarah tayi tace toh mama.
zarah tashi tayi taje tasako hijab d'inta sannan tafita taje tayo siyayyar, bayan ta dawo tad'aura girkin.
tana cikin yi mama tafito ta shirya sanye da gyale tace toh idan kin gama kijuye a cikin plastic d'innan zan je gidan mariya barka kuma kar kisaki kici kibari sai nadawo nad'ibar miki.
zarah cike da ladabi tace toh mama Allah yakiyaye hanya.
zarah bayan ta gama gyara gidan tak'ara yi sannan taje tayi wanka tashirya tayi sallah.
bayan ta gama saman katifarsu takwanta tana jiran mama tadawo saboda wata irin yunwa da takeji.
mama sai wajen k'arfe ukku tadawo lokacin bacci har ya d'auke zarah.
maganar mama ce tajiyo sama-sama dan haka firgit tayi tafarka.
mama tsaye take bakin k'ofa tace yanzu dan gidanku zarah bacci kikeyi kinbar mana gida bud'e?
Zarah mik'ewa tayi tace wlh mama ban san lokacin da bacci yad'aukeniba kiyi hak'uri.
tsaki mama tayi tace kullum bakida aiki saidai ayi hak'uri ke da ace bamu hak'uri da ke ai da tuni na 6allaki, ni kizo kikwaso mun kwanika inraba abincin.
zarah tace to mama sannan tabi bayan mama takwaso kwanuka.
Zarah bayan ta gama cin abincinta alk'ur'ani tad'auko tana bitar hardar da zata bada islamiyya har aka kira sallah la'asar tayi sannan tashirya taje d'akin mama tace mama zan tafi islamiyya.
mama harararta tayi tace ke ni banma yarda dakeba anya ma islamiyya kike zuwa? ko dai wajen wannan malamin naku kike zuwa.
zarah raurau tayi da ido tace wlh mama babu inda nake zuwa sai islamiyya.
mama tace eh ai dan kihad'u da shi islamiyyar saisa kike zuwa,
zarah tace a'a wlh mama.
mama tace munafuka kawai kedai kika sani ahaka dai zaki k'arata ni tashi kiban waje.
zarah tashi tayi tafita.
ko da taje islamiyya lokacin ajinsu har anfara taruwa kowa zaune yake yana bitar hardarsa kafin malam yashigo.
sit d'in gaba tazauna kusa da k'awarta khairy kasancewar nan ne wajen zamansu tare da mik'a ma khairy hannu suka gaisa.
khairy kallon zarah tayi tana murmushi tace yau dai na rigaki Zuwa.
itama zarah murmushi tayi tace nima dai nayi mamakin ganinki dawuri
khairy tace ai infad'amiki tun d'azun ina nan ina koyon harda kafin malam bello yashigo kedai nasan kinsha taki hardar.
murmushi zarah tayi tace kedai kicigaba da haddarki.
suna cikin bita malam bello yashigo idanuwansa akan zarah,
suna had'a ido dasauri zarah tajanye idonta, khairy murmushi tayi ahankali tace malam bello yau sabon yadi yasa nasan kuma saboda ke ne.
harararta zarah tayi tace wlh zan fad'a masa..... muryar malam bello suka tsinkayo ya ce khairy surutu kukeyi ko?
khairy tace a'a malam muna wani nazarine.
yace toh ya isa haka, kallonsa yamaida ga 'yan aji yace duk Wanda yasan baiyi hadda ba toh yafita waje dan kar ku6ata min lokaci.
nan aji yayi shuru kowa yafara raba ido, chan wasu mata hud'u suka tashi suka fita.
malam bello kallon zarah yayi yace kufara yau sit by sit zan bi saboda k'urewar lokaci.
nan layinsu zarah suka fara malam bello yana kallon bakin kowa har suka gama gyara biyu yayi musu sannan yacigaba da kar6ar na sauran har aka gama sannan yayi musu k'ari lokacin tashi yayi akayi addu'a.
zarah jerowa sukayi da khairy suna tafiya d'ago kan da zatayi taga malam bello ya tsareta da ido murmushi tasakar masa sannan suka cigaba da tafiya.
khairy da take kallonsu tana murmushi tace wlh k'awata soyayyarku da malam bello tana burgeni.
zarah murmushi kawai tayi sannan suka cigaba da tafiya har sukazo inda suke rabuwa sukayi sallama sannan zarah tacigaba da tafiya.
Zarah lokacin da tazo k'ofar gida mota tagani tsaye batare da takalli nacikin motarba tawuce zata shige gida.
muryar yaya rauda ce tajiyo tana kiranta nan tatako tanufi wajen motar daga nesa kad'an tatsaya takalli yaya rauda da take zaune gaba tace yaya Rauda gani.
ledace tamik'a mata tace shigar min da wannan gida, kar6a zarah tayi har zata tatafi taji mutumin yace sannu ko 'yan mata,
zarah bata tankasaba tawuce zata tafi yaya zarah tace ke dan ubanki bakiji ana miki magana?
zarah kallon mutumin tayi da yatsareta da ita yana murmushi, fuskarta a d'aure tace ina wuni? bata jira ya amsaba tawuce tashige gida tana jiyo yaya rauda tana ta fad'a..
_Comment_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Sak'on gaisuwata agareku a duk inda kuka kasance *My hafnan, Mamansadiq nd Mrs Dawud* I heart you allπ_
_*My blood sis Aufana yau ranar takice dan haka na mallaka miki wannan page d'in, ina so kisani sonki a cikin jinin jikina yake Allah yabarmu tareπ*_
page 9⃣
Saurayin yaya raudane yashiga lallashinta yace haba baby menene kuma nafad'a a ciki? ni wlh k'anwar ma taki ta burgeni.
Yaya Rauda tace hmm baby kenan bakasan wannan yarinyar ba ai kwata-kwata ita ba wayaiya bace.
murmushi yayi yace har ina shirin ince ina ciki.
wani irin kallo Rauda tayi masa tace k'anwar tawa?
murmushi yayi yace eh man toh menene?
Rauda ta6e baki tayi tace ai wlh ba zai yuwu kajefi tsuntsu biyu da dutsi d'ayaba dan haka abar ma maganar nan baby, yanzu idan katafi sai yaushe zaka dawo?
cije le6e yayi tare da jingine kansa a sit d'in da yake zaune sannan yace 1 week kawai zanyi cike da tsokana yace kinsan matata kwana biyu nayi missing d'inta.
Rauda d'aure fuska tayi tace haba Alhaji Munnir wai meyasa kake min irin haka.
murmushi yayi yace sorry dear kinsan akwai aikin da zanje inyi, yanzu dai fatana kikular min da kanki har indawo.
Rauda tace kar kadamu dear insha Allahu zaka dawo kasameni yadda kabarni,
murmushin jin dad'i yayi yace yauwa baby nagode, 10k yad'auko yamik'a mata yace ga wannan kirik'e kafin indawo,
Rauda kar6a tayi tace nagode baby Allah yamaido min kai lafiya
yace Ameen dear, nan sukayi sallama.
Rauda ba ko sallama tashiga gida kallon zarah tayi da take hura wuta tace ke ina ledar da nace kishigo min da ita?
zarah batare da ta kalli Rauda ba tace tana d'akinmu, Mama da take cikin d'aki jin muryar Rauda yasa tafito tana washe baki tace a'a 'yar albarka ashe kece kika dawo, tun jiya muna ta zuba ido ammah shuru.
Rauda yamitsa fuska tayi tace ammah mamanmu kinsan dai duk ma inda naje toh zan dawo.
Mama tace hakane saidai duk abinda kuke nafison inganku kun dawo gida komai dare kun kwana.
Yaya Rauda batare da tace komai ba tawuce tashige d'akinsu.
wannan 'yar maganar da mama tayi zarah taji dad'inta sosai domin duk abin mama toh tanaso taga yaran nata sun kwana a gidansu, saidai duk maganar da zatayi musu Yaya Rauda idan tasa kanta waje take kwana, idan ma iyayen sunyi magana sai tabasu kud'i tarufe bakin.
Mama kallon zarah tayi tace tashi kije kikar6o min 500 wajen Rauda kizo kisiyo taliya a Zuba naga ruwan ya kusan tafasa,
zarah tace toh mama.
tana shiga d'akin kallon Rauda tayi da take shirin shiga wanka tace Yaya Rauda mama tace kibada d'ari biyar asiyo taliya.
Rauda tace mik'o min jakkata, zarah zuwa tayi tad'auko jakkar tabata nan Rauda tamik'o mata kud'in sannan tashige wanka.
Zarah wajen mama tadawo tace mama guda nawa za'a siyo.
Mama tace siyo biyu sai kikawo min canjin, zarah tace toh sannan tatafi.
_*After 2 weeks later*_
Zarah ce zaune tana tsifar kanta, wayartace tashiga ringing nan tad'auko ganin sunan malam Bello da yabayya a screen yasa tayi picking tare da yin sallama,
daga chan 6angaren ya amsa mata, nan suka gaisa, sannan malam Bello yace dear gani a k'ofar gidanku kifito inganki please.
zarah jim tayi nad'an lokaci sannan taduba agogo taga k'arfe biyar d'in marece. muryasa taji yana cewa zarah ya kikayi shuru ko bakiso nazoba?
zarah tace bahaka bane malam gani nan zuwa batare da tajira jin abinda zai ce ba takashe wayarta,
nan ta tufke kanta da ribbon sannan tajanyo hijab tasaka saida talek'a ganin ba kowa tsakar gida yasa tayi hamdala sannan talalla6a taficce.
A k'ofar gida tasamesa tsaye ya zuba ido domin yaga ta ina zata fito, suna had'a ido dasauri zarah taduk'ar da kanta k'asa tare da yi masa sallama.
fuskar malam Bello d'auke da murmushi ya amsa mata yace zarah na tadoki ko batare da nasanar da ke zuwana ba.
zarah ahankali tace bakomai malam nan tagaishesa ya amsa,
kallon da yakeyi mata duk sai ya gundureta tad'ago kai tad'an kallesa,
murmushi yasakar mata yace kiyi hak'uri wlh ji nayi yau idan ban gankiba ba zan samu sukuniba tunda ko a islamiyya 6oyemin kanki kike bakya ko bari mugaisa, kinsan dai yadda nake sonki.
Zarah murmushi tayi batare da ta ce komai ba.
malam Bello yace shurun da kikeyi fa yana cutar da ni dan Allah kimin magana.
zarah d'ago kai tayi takallesa har ta bud'e baki zatayi magana sai ganin Abbah sukayi tsaye.
A tsorace zarah takallesa bakinta yana rawa tace Abbah sannu da zuwa, wani irin kallo Abbah yawurga mata.
malam Bello dasauri yaduk'a tare da cewa Abbah barka da rana ina wuni?
Abbah yace da ace ban wuniba da ka ganni?
Me yakawoka wajen 'ya ta? duk hure mata kunne da kakeyi a islamiyya bai ishekaba sai ka biyota gida?
malam Bello kansa a k'asa yace kayi hak'uri Abbah wlh ba haka bane,
Abbah yace toh yaya ne?
Malam Bello yace wlh ni tsakani ga Allah son zarah nake kuma ina da burin aurenta.
Abbah yace a haka? Minene aikinka?
Malam Bello yace eh toh gaskiya ni karatu nake ammah ina tsare shago ana biyana.
Abbah yace kana karatu ammah dan rigima kace kana son 'ya ta toh bari kaji d'iyata ba irinka zata auraba domin kwata-kwata baku daceba, bakada abinda zaka iya aurenta dan haka tashi kabar min k"ofar gida.
malam Bello yace kayi hak'uri Abbah insha Allah zan iya rik'on zarah.
Zarah tace dan Allah Abbah kayi.... tsawa Abbah yadaka mata yace wuce kishiga gida ko ranki ya6aci, dasauri zarah tawuce tashige gida tana hawaye.
Abbah kallon malam Bello yayi yace tashi kabar nan kuma kar ka kuskura kak'ara takomin k'ofar gida, Abbah na gama fad'in haka yawuce yashige gida. .
malam Bello yamik'e tsaye daga tsugunnen da yake yatafi yana jin ba dad'i cikin ransa.
Zarah saman katifarsu tafad'a tafara rusar kuka, Abbah ne yashigo gidan yana ta fad'a.
mama ce tafito daga d'aki tace malam lafiya?
Abbah yace ina fa lafiya wlh yarinyar chan idan batayi wasaba sai na sa6a mata a cikin gidan nan, mama tace wa kenan?
Abbah yace zarah mana wai ace tarasa Wanda zata tsaya da shi sai talakka d'an uwanta da baida komai inba wahalaba babu abinda zata tsinta a wajensa.
mama tace hmm malam kenan ai wlh indai zarah ce toh kad'an kagani ita kwata-kwata batada tunani ai ni wlh ban ma San lokacin da tafitaba da bazan bartaba,
mama wucewa tayi tanufi d'akinsu zarah a bakin k'ofa tatsaya tare da d'age labulen d'akin, kallon zarah take da taketa faman kuka cikin fad'a tace ke dan kin raina ni watau da narabaki da wancan yaron baku rabuba ko? shine yanzu dan anyi miki magana shine kike kuka, toh bari kiji ko da ace zakiyi kukan jini bazaki auresaba kuma dole kurabu inma bakiyi hankaliba islamiyyar ma sai inhanaki zuwa, butulun banza inba ma asaraba me zakiyi da d'an uwanki talakka duk kyaun naki baida amfani wlh, hatta k'anwarki tafiki sanin daidai.
zarah dai tana jin mama tana ta fad'anta har tagama tatafi itadai kuka take.
kiran Sallar magrib da akayine yasa tatashi taje tayo alwallah har lokacin fuskarta babu walwala.
bayan sallar isha'i kwance take saman katifa gefenta Aysha ce kunnenta d'auke da earpiece da waya a hannu da alama kallo takeyi.
zarah wayarta tad'auko talalubo number d'in malam Bello takirasa, tana fara ringing yakashe yakira,
zarah tana d'aga wayan yayi mata sallama.
jin muryarsa yasa taruntse ido tana jin wani iri acikin zuciyarta sai a lokacin taji kunyar abinda Abbah yayi masa.
muryarsa ta tsinkayo yana cewa hello zarah bakya ji na?
zarah cikin muryarta da tadashe saboda kuka tace malam dan Allah kayi hak'uri akan abinda yafaru
murmushi malam Bello yayi yace kar kidamu zarah wlh bakomai kawai dai ina tunanin anya zan iya rabuwa da ke? domin ni kaina nasan ina miki wani irin mahaukacin so.
zarah ajiyar zuciya tayi tace malam Bello wlh nima ina sonka kuma ina ji a raina akwai lokacin da iyayena zasu amince mana muyi aure.
malam Bello yace hakane ammah ni fatana kitaimaka kirik'e min amanar kanki har ingama karatuna muyi aure.
zarah tace kar kadamu nariga na amince maka kuma insha Allahu idan da rabo zamuyi aure.
cike da jin dad'i malam Bello yace nagode sosai zarah Allah yamallakamin wannan tauraruwar yarinyar.
dariya zarah tayi daga nan suka shiga yin hira, sai da sukayi kusan awa d'aya sannan sukayi sallama suka kashe wayoyinsu kowa yana jin dad'i a ransa, nan zarah tanemi damuwarta tarasa.
________________
Gimbiya Sumayya lokacin da jirginsu ya safka zinat ce tazo tatarbeta cike da farin ciki suka rungume juna daga nan suka nufi inda motar zinat take suka shiga suna ta hira, zinat tace baby yanzu gida zamu wuce ko boutique din zan kaiki kifara ganowa? Sumayya jingine kanta tayi a sit din da take zaune tace dear muje gidanki kawai yanzu agajiye nake, murmushi zinat tayi tace toh ranki yadad'e angama.
dariya sukasa gaba d'ayansu Sumayya tace abun ma har da tsokana kenan, daidai lokacin tayi horn maigadi yazo yabud'e mata gate tacinna motarta a ciki a parking space tayi parking sannan suka fito suka d'unguma cikin gida.
bedroom suka wuce Sumayya tafad'a saman gado tare da cewa wash.
dariya zinat tayi tace baby keda kikazo ta flight ammah shine har kin gaji? kokuma namance ku jinin sarauta bakwa motsawa dayawa saidai ayi muku komai.
harararta Sumayya tayi tace ke dai kika sani da tsokana, ni yanzu dai taimaka kisa ahad'a min ruwan wanka infarayi tukun,
zinat mik'ewa tayi tanufi k'ofa tafara kwalah ma 'yar aikinta kira, dasauri tazo tare da russunawa k'asa ranki yadad'e gani, zinat yamitsa fuska tayi tace shiga toilet kihad'a ruwan wanka, dasauri tatashi tashiga tahad'a ruwan sannan taficce tabar d'akin.
Zinat kallon sumayya tayi tace baby kitashi kije kiyi wankan ko intaimaka miki,
sumayya mik'ewa tayi tad'auki towel tacire kayan jikinta tawuce tashiga bathroom.
bayan ta fito kwalliya tayi tashirya cikin English wears riga da skirt tafeshe jikinta da turare, kallon Zinat tayi da tatsareta da ido tace dear wannan kallon fa?
Zinat tace Mrs yarima kinyi kyau sosai.
gimbiya sumayya ta6e baki tayi tace har kin tunomin da wannan d'an jin kan, nidai muje inyi lunch domin yunwa nakeji yanzu.
Zinat mik'ewa tayi suka fito suka nufi dining nan Zinat tayi serving d'insu suna ci suna hira.
bayan sun gama saman 3 seater suka dawo suka yada zango, sumayya wayarta tad'auko tace bari inkira su ummah inshaida musu na iso lfy tun kan surigani kira,
Zinat tace hakan fa zaifi.
nan sumayya takira sultana sadiya da dada tafad'a musu ta sauka lafiya.
bayan sumayya ta gama wayar zinat tace toh baki kira miskilin mijin nakiba.
ta6e baki tayi tace kibarsa kawai wannan d'an rainin wayaun ai wlh indai bashi yakiraniba toh ba zan kirasaba _(lallai sumayya kin mance wanene yarima suhail)_
Zinat tace ai wlh kina ma hak'uri da shi ai ni kwata-kwata ban tunanin zan iya zama da irin su mijinkiba.
sumayya tace hmm nima dai dan ina sonsa ai da ban iya zama da halinsa, ke kafin fa intafo jiya saida mukayi drama, yanzu dai tashi muje inga boutique d'in dan na k'agara ingansa.
zinat murmushi tayi tace baby ai nad'auka sai ansallameni sannan zamuje kinsan fa nayi missing d'inki dayawa.
sumayya 'yar dariya tayi tace kidai bari mudawo tukun dan ni yanzu hankalina ya fi karkatuwa da zuwa.
zinat tace ke Alhaji Jamilu fa yana nan Abuja ai kinsan na fad'a miki.
sumayya yamitse fuska tayi tace wanene kuma jamilu,
harararta zinat tayi tace ammah fa ke 'yar iskace baby yanzu Alhaji jamilu kika mance?
yamitsa fuska sumayya tayi tace hmm zinat kenan ai ban mance da shi ba dan mugunta kikaja nabasa kaina shine namijin da yafara sanina,
dariya zinat tayi tace ammah ai lokacin mun samu abinda mukeso, ke ni yanzu haka in kinason ganinsa nasan gidansa sai muje inrakaki.
sumayya harararta tayi tace Allah yakyauta ke nifa yanzu namiji Indai ba mijinaba bana jin zan k'ara amince ma wani,
zinat da mamaki take kallonta tace saboda me? sumayya cikin rashin damuwa tace haka kawai mazan basu gabana.
zinat tace toh wlh ko da sau d'ayane ki amince muje gidan Alhaji jamilu domin yana ta tambayata ke, kinga mun k'ara jari.
sumayya mik'ewa tayi tsaye tace nidai kitashi muje ko mun dawo domin inaso inhuta.
zinat tace toh nima dai kenan yau ba tani akeba, sumayya rik'o hannunta tayi tace haba baby ai ke ta dabance nima fa nayi missing d'inki, muje dai mudawo ai muna tare daga yau har next week.
A motar Zinat suka fita ko da sukaje boutique d'in sumayya ta yaba sosai da kayan da zinat tazuba ciki, nan zinat ta gabatar da sumayya ga ma'aikatan wajen cike da girmamawa suke gaisheta sumayya a wulak'ance take amsawa nan tad'an d'auki kaya set biyu tace tana sonsu.
daga nan suka zagaye gari sai dare sannan suka koma gida, gaba d'ayansu saman gado suka fad'a suna hutawa, zinat kallon sumayya tayi tace baby muje muyi wanka,
sumayya tafara mik'ewa sannan zinat atare sukaje sukayi wankan bayan sun fito su dukansu d'aure suke da towel suna rungume da juna nan suka nufi saman gado suka kwanta........
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍π»_
πππ
_*YARIMA SUHAIL*_
πππ
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE π HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS π CURDLES π GIGGLES π AND MARRIEGE THINKπ
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_~Sak'on gaisuwa agareku masoya a duk inda kuka kasance inaso kusani Sis Nerja'art tana yinku overππ~_
_*My hafnan nd My leemah H.A.S yau Ranar takuce, page d'innan nakune kuyi yadda kukeso dashi sai wanda kukaso zai karanta, wlh ina ji da ku sosai a cikin zuciyana, Allah yabarmu tareπ*_
page 1⃣0⃣
_*After 3 days later*_
sumayya ce kwance tayi matashin kai da cinyar zinat tana waya da ummanta bayan sun gama sumayya d'aga kai tayi takalli zinat da take ta dannar waya da alama chart takeyi, tace baby mutuminki fa har yau bamuyi wayaba.
murmushi zinat tayi tace toh sai me minene abun damuwa tunda dai bai nemekiba toh kema kisharesa, ke ni jiya da nafita na ga Alhaji jamilu kuma nafad'a masa muna tare wlh bakiga yadda ya rikice min ba wai sai ya biyoni ya zo wajenki.
murmushi sumayya tayi tace ke dai kina son jona ni da Alhaji jamilu,
zinat tace toh ai nasan zamu samu cash masu tsoka a wajensa, ke nifa inda ke da kud'i a nan nafi wayau.
dariya sumayya tayi tace nima haka dear, wlh dan dai ina tsoron kar yarima yagane da nabi maganarki naje munyi sharholiyarmu da shi inyagi abinda nayaga.
Zinat tace haba baby kefa matsalata da ke kenan taya kike tunanin mijinki zaya gane tun farko ma bai ganeba sai a yanzu?
Sumayya jinjina kai tayi alamun gamsuwa sannan tace toh yanzu dai ta ina zamu fara?
zinat murmushi tayi tace ai ya bani number d'insa bari kawai inkirasa sai kuyi magana ko kuma inbaki number d'insa.
dasauri sumayya tagirgiza kai tace a'a kirawo min shi dai da wayanki kinga yanzu nayi aure kar wataran yakirani gaban mijina.
zinat tace hakane nan tafara dialing d'in number d'insa tanaji yad'aga dasauri tasa ma sumayya a kunne, jin muryarsa yasa sumayya yin murmushi tare da kallon zinat.
zinat alama tayi mata na tayi magana.
sumayya kwantar da muryar tayi tace Alhajina dafatan kana lafiya.
Alhaji jamilu da yake kwance jin muryar sumayya da yayi yasa yamik'e zaune tare da cewa sumayya daman kina nan?
sumayya murmushi tayi tace aikam dai ina nan Alhaji ya gida ya kake?
Alhaji jamilu cike da jin dad'i yace lafiya lou baby gaskiya naji dad'in jinki da nayi wlh daman nadad'e ina cigiyarki wajen zinat.
sumayya tace ayya kar kadamu yanzu ai gani.
yace baby toh inaso muhad'u ya za'ayi?
sumayya kallon zinat tayi sukayi murmushi sannan tace toh katuron address d'inka sai inzo
cike d's jin dad'i Alhaji jameel yace yanzu ko zan turo miki ammah please kizo yau,
sumayya tace kar kadamu zan shigo da anjima, yanzu dai ina jira sai ka turo.
nan sukayi sallama suka kashe wayan.
sumayya kallon zarah tayi da tatsareta da ido tace baby nidai ko da na je gaskiya bana iya bari yayi sex da ni.
zinat zaro ido tayi tace haba baby saboda mi? toh kud'in fa?
murmushi sumayya tayi tace kar kidamu dolene ma sai na samo mana kasonmu kin d'auka a banza chan baya yamoreni?
dariya zinat tayi tace toh ai lokacin ma mun yagi kasonmu,
sumayya tace a yanzu ma dole yabamu, bari ma kiga inje inyi wanka, tana gama fad'in haka tamik'e tafara cire kaya.
bayan ta fito wanka shiryawa tayi cikin riga da skirt na atamfa sannan tayafa d'an k'aramin veil, kallon zinat tayi da tatsareta da ido tayi murmushi tare da jujjuyawa tace baby ya kika ganni?
zinat ma murmushi tayi tare da mik'ewa tace kinyi kyau sosai anya kau Alhaji mukhtar zai barki?
dariya sumayya tayi tace muje dai kiyi dropping d'ina.
wani dank'areren gida aka hangame musu gate suka shiga gefe guda zinat tayi parking sannan takalli sumayya da take bin gidan da kallo tace haba baby kema fa gidanki ya tsaru naga sai kallon wannan kikeyi
murmushi sumayya tayi tace balaifi yayi min kyau.
zinat tace toh kifita kishiga ni bari inje koma dai me kenan sai kindawo.
sumayya tace toh tare da bud'e motar tafita nan zinat taja motarta tabar gidan.
ahankali sumayya take takawa tanufi k'ofar da zata sadata a cikin gidan cikin karambani take bin hanya saidai ganinta tayi a parlour lokacin Alhaji jamilu yana kwance saman 3 seater yana kallo, jin anbud'e k'ofane yasa yad'ago ganin sumayya yasa yamik'e dasauri yanufi inda take tsaye, rungumeta yayi yace oyoyoo babyna.
sumayya janye jikinta tayi daga nasa tana murmushi tace baby kwana dayawa.
rik'o hannunta yayi suka zo saman 3 seater suka zauna har a lokacin idonsa cikin nata yace baby ban d'auka zan k'ara ganinki a yanzu ba saboda nisan da kikayi min kin 6oye.
sumayya murmushi tayi tace no ni ina gefe kune dai siyasa ta6oye.
Alhaji jamilu hannunsa na sark'e da nata yace mu muna gefe baby inkinson ganinmu zaki ganmu dan ba irinku muke 6oye mawaba, yanzu dai taso mushiga daga ciki.
sumayya mik'ewa tayi tabi Alhaji jamilu bedroom d'insa suka yada zango saman gadonsa, rungume yayi yakai bakinsa cikin nata suka fara kissing d'in junansu inda hannuwansa suke yawo cikin rigarta.
sumayya dai kawai tana biye masane har yarabata da kayan jikinta romance d'in sunansu suke son ransu daga k'arshe sumayya da taga yana shirin shigarta tadakatar da shi.
da mamaki Alhaji jamilu yake kallonta yace baby saboda me zaki hanani? Please kibarni inyi kinsan fa nakwana biyu banji d'umin jikinkiba.
murmushi sumayya tayi tace dear kayi hak'uri just dai muyi romance d'in juna ammah bana buk'atar sex, ganin yana shirin yin magana yasa tarufesa masa bakinsa da nata cike da kwarewa itama tadinga sarrafasa saida taga ya gamsu batare da sex ba sannan tabarsa.
Alhaji jamil kallonta yayi da take shirin tashi yace baby ina zakije?
murmushi sumayya tayi tace gida zan koma yace haba dan Allah kiyi min ko da kwana d'ayane
sumayya tace a'a Alhaji tafiya dai zanyi inyaso wani lokacin sai indawo.
Alhaji jamil ba dan yasoba yace toh atare sukaje sukayo wanka, duk yadda taso tatafi dawuri hanata yayi saida tayi dagaske sannan yad'auko yamaidata gidan zinat.
A mota ma bai bartaba rungumeta yayi inda hannuwansa suke yawo a cikin rigarta saida yagaji dan kansa sannan yabarta, cheque d'in 1.5 million yarubuta mata yamik'a mata.
cike jin dad'i sumayya takar6a tare da yin godia sannan sukayi sallama tafito daga motar tana d'aga masa hannu har yatafi sannan tashiga gida.
A parlour tatarar da zinat zaune da d'an k'aramin veil a gefenta da alama itama bata dad'e da dawowaba.
daga gefen zinat tazauna tare da cewa wash wlh na gaji.
dariya zinat tayi tace ya dai baby? ai nasan Alhaji jamil ba zai ta6a barinki hakanan ba.
ta6e baki sumayya tayi tace ke ni kawai dai na amince masane ammah banbari yayi sex da ni ba, wlh yarimana yafisa iya sarrafa mace saisa nace miki bana tunanin akwai namijin da zan iya jin dad'insa kamar yarima.
ta6e baki zinat tayi tace haka dai kike gani ammah wlh inkina so zan iya had'aki da guys d'ina zakiga banbanci sosai
sumayya tace bama naso.
zinat tace yanzu dai babu abinda yabamu kenan?
sumayya bud'e jakkarta tayi tafiddo cheque d'in tamik'a mata.
zaro ido zinat tayi tace baby yanzu Alhaji jamilu yabaki kud'in nan batare da yayi miki komai ba?
murmushi sumayya tayi tace kawai dai munsha minti ammah babu abinda yashiga tsakaninmu, ke ni sai bayan natafi nake tunani ai da nayi ma yarima magana da zai bani saboda duk abinsa ammah baya da rowa
zinat yamutsa fuska tayi tace ai k'arama da bakiyi masa magna ba dan banason mutumin nan saboda wulak'ancinsa.
sumayya tace zinat ammah wlh yarima baida rowa.
zinat ta6e baki tayi tace matsalarsa, nidai ynz tashi muje mukwanta inyaso gobe sai muje muciro kud'in mud'ibi kasonmu sai muyi order d'in wasu kayan da sauran kud'in, nima kinga ga 1 million nan d'azun nakar6esu wajen wani guy d'ina.
dariya sumayya tayi tace ai daman tunda nadawo naga veil d'inki a gefe nasan kin fita.
zinat tace ai ina dropping d'inki ban dawo gidanba nawuce chan, yanzu dai nidai agajiye nake muje daga ciki.
Tun daga ranar sumayya idan Alhaji jamilu yakirata take zuwa gidansa ammah bata bari yayi sex da ita tun yana k'orafin har yagaji, ahaka tacika 1 week a garin.
zinat rok'onta tayi kar takoma gida dakyar tasamu sumayya tazauna domin tak'ara ko da kwana biyu ne ammah saida takashe wayarta gudun kar su dada sukirata.
____________
Yarima suhail tunda sumayya tatafi bai damuba harkar gabansa kawai yakeyi domin a ganinsa da ita da babu basuda banbanci, ko da sau d'aya bai d'aga wayaba da zumar yakirata.
ahaka har tayi 1 week ammah bata dawoba,
Dada jin sumayya shuru bata dawoba yasa takirata a waya ammah wayanta a kashe dan haka ta aika aka kira mata yarima.
yarima yana kwance a 3 seater kujerar da take opposite d'insa Shaheed ne zaune duk yadda shaheed yaso suyi hira da yarima suhail ammah yarima ya k'i,
ganin haka yasa shaheed yaja bakinsa yayi shuru dan yasan halin mutumin nasa har korarsa ma zai iyayi, gajiya yayi da shurun daga k'arshe yakalli yarima da yazuba ma ceiling ido da alama tunani yake, yasheed yace yarima meyake damunkane?
shuru yarima yayi yakyalesa.
murmushi shaheed yayi yace ranka yadad'e ko kana tunanin gimbiyarkane.
yarima juyowa yayi yawurga ma shaheed harara sannan yamaida kansa ga kallon ceiling.
dariya ce takama shaheed ammah yadanneta yace Allah yahuci zuciyarka.
K'ofar d'akin aka shiga knocking, Shaheed ganin yarima baida niyar yin magana yasa yabada izinin ashigo.
wata baiwace tashigo dasauri tazube k'asa a bakin k'ofa tace ranku yadad'e Allah yaja da ran yarima mai jiran gado, daman sultana dada ce tace tana nemanka.
shaheed kallon yarima yayi yaga baida niyar yin magana kuma yana jin ta, shima bakinsa yaja yayi shuru.
saida aka d'au kusan minti ukku tana tsugunne sai chan yarima yad'aga mata hannu batare da ya kalletaba alamun tatafi.
dasauri tak'ara duk'ar da kanta tace ranka yadad'e afito lafiya sannan tatashi tafita tabar d'akin.
shaheed kallon yarima yayi yaga baida Niyar tashi, cikin ransa yace yau abun ya motsa kenan, nan yacigaba da kallon ball d'insa.
saida akayi kusan minti goma sannan yarima yamik'e tare da d'auko alkyabbarsa yasaka, batare da yayi ma shaheed maganaba yafita yabar d'akin,
nan mutane sukayita zubewa suna kwasar gaisuwa yau ko d'aga musu hannunma bayayi ahaka har ya isa turakar dada.
ko da yashiga dada tana kishingid'e anayi mata tausa, ganinsa yasa duk suka zube suna kwasar gaisuwa, tsaye yarima yayi har saida suka tashi suka ficce sannan yatako yazo yazauna bisa kujerar da take opposite d'in dada.
dakyar kamar bayason yin maganar yagaishe da dada.
dada cikin fara'a da sakin fuska ta amsa masa, gyara zamanta tayi sannan tace yarima daman akan maganar matarkane yaushene zata dawo?
Yarima kallon dada yayi sannan yamaida kallonsa akan wayarsa da yake dannawa cike da jin haushin maganar da dada tayi,
dada zuba masa ido tayi tana kallonsa baida niyar bata amsa,
sai chan yace ranki yadad'e ai nad'auka kunyi magana kinsan lokacin da zata dawo tunda nidai bata fad'amin kwanakin da zatayiba.
dada baki tasaki tana kallonsa har yagama maganar sannan tace suhail kana dai so kacemin bakuyi waya da itaba tunda tatafi.
yarima shuru yayi bai tankaba,
dada tace ammah wlh da kacika marar kirki har yanzu kana nufin baka huceba kenan.
yarima kallon dada yayi tare da yin murmushi yace dada kenan ni ba fushi nakeba, kawai dai nad'auka kinsan lokacin da zata dawone ammah kiyi hak'uri idan maganata ta6ata miki rai,
dada tace toh yanzu nafahimta ammah dan Allah kakirata kaji yaushe zata dawo saboda sati guda tace zatayi ammah yau kusan kwananta takwas.
mik'ewa yayi yace toh dada, bari inwuce ana jira.
dada tace toh shikenan nidai dan Allah kakirata.
yarima baice komai ba yawuce yafita cikin ransa yana cewa saidai kar tadawo indai sai na kirata zata dawo.
Bayan kwana biyu gimbiya sumayya tayi shirin komawa gida lokacin Kwananta goma, Alhaji jamil da zinat su suka kaita airport a chan ma Alhaji jamil yana manne da ita kud'i masu tsoka yabata, har saida sukaga tafiyarta sannan suka bar wajen.
Gimbiya sumayya ko da tadawo da su dada suka tambayeta akan rashin dawowarta k'arya tayi musu akan wai wata matsala ce tatashi akan business d'insu saida tajira komai yakoma normal sannan tadawo.
ko da tadawo sai da takwana biyu batasa yarima a idontaba dan tayi tunani zaizo d'akinta ammah sai gashi tsawon kwana biyu bai zoba.
dan haka da daddare shiryawa tayi taje 6angaren yarima domin ta san Indai ba ita tajeba toh ba zai ta6a zuwa wajentaba saidai idan yana buk'atarta.
lokacin da tashiga yarima suhail yana shirin bacci ko inda take bai kallaba, takawa tayi taje inda yake still dai bai kalletaba sai ma wucewa da yayi yahaye gadonsa yakwanta.
Sumayya cikin ranta tace toh yau kuma naga yadda zamu kwashe da wannan d'an jin kan, binsa tayi saman gadon takwanta gefensa tace my sweetheart ko welcoming d'in ma bazan samuba, tsawon kwana biyu da dawowata ammah ko kanuna ka damu.
yarima suhail batare da ya kalletaba yace ashe kini dawo?
da mamaki sumayya take kallonsa tace au da ba zan dawoba?
yarima bai tanka mataba yajuya mata baya.
sumayya ganin haka yasa tarungumosa ta ba tace haba yarima wai meyasa kake son wulak'antani ko dai bakaji dad'in dawowataba?
yarima banza yayi yakyaleta cike da k'ulewa.
gimbiya sumayya tace haba yarima wlh banason sharewar nan da kakemin.
yarima suhail yace sumayya ai da baki dawoba dan dabakinan hankalina ya fi kwanciya wlh, ni da kin taimaka kin tashi kinkoma d'akinki dan yanzu banason a dameni hutu nake buk'ata.
sumayya cike da k'ulewa tace kai wlh tsiyata da kai bakasan arzik'iba duk yadda mutum zai nemi yakyautata maka sai ka kushesa nifa kawai tausayinka nakeji ganin lokacin da nad'auka bana nan nasan kayi missing d'ina.
Yarima tashi yayi yazauna yana kallonta a wulak'ance yace sumayya me kika d'aukeni? na fa san abinda nakeyi ni a yanzu bana buk'atarki dan haka kitashi kifitarmin daga d'aki,
da mamaki gimbiya sumayya take kallonsa tace yarima ni kake kora? me nayi maka daga dawowata sai kahauni da fad'a?
wani mugun kallo yarima suhail yayi mata tare da nuna mata k'ofa.
tashi sumayya tayi tare da d'aukar alkyabbarta tasaka sannan tace naji zan fitar maka daga d'aki sauk'inma nima ina da nawa d'akin daman taimaka maka zanyi ammah tunda......
tsawa yarima yadaka mata cikin 6acin rai yace I said get out!!!
sumayya ta tsorata sosai da ganin yanayinsa dan haka dasauri taficce tabar d'akin cike da jin haushin wulak'ancin da yarima yayi mata daga dawowarta......