Yarima suhail bayan gimbiya sumayya ta fita dafe kansa yayi cike da jin haushin sumayya da take nema taraina masa wayau, watau ta ma san ya yi missing d'inta? to kenan ita batayi missing d'insaba tana nufin taimakonsa ma zatayi. tabbas yasan ya yi *BABBAN KUSKURE* da ya amince ya aureta domin ko kad'an batasan minene aureba
tsaki yaja yace Allah yashirya sannan yakoma yakwanta yana mamakin halin sumayya.
Sumayya a fusace takoma d'akinta cike da bak'in cikin wulak'ancin da Yarima yayi mata, ace kamarta daga ta je tataimaka masa shine yakoreta
tana shiga bedroom tamurza key nan tafad'a saman gado tafara kuka.
tun daga ranar aka koma 'yar gidan jiya ba mai kula d'an uwansa kowa harkar gabansa yakeyi
_______________
A 6angaren su zarah har yanzu babu abinda yasauya daga halaiyar 'yan gidansu, malam bello yanzu islamiyya kawai suke samu suna had'uwa
yauma bayan ta taso daga islamiyya tafiya take a nutse kanta sadde a k'asa daga bayanta taji ana mata sallama kamar ba zata amsaba sai kuma chan ta amsa batare da ta tsayaba mutumin cigaba yayi da binta yace dan Allah 'yan mata kitsaya kisaurareni mana,
Zarah ahankali tad'ago kai takalli mutumin da bazai gaza shekaru ashirin da biyarba, k'ara d'aure fuskarta tayi tace lafiya malam kaketa bina?
Murmushi mutumin yayi yace ni dai sunana hamza ina zama chan waccan rumfar mai kayan miyar kullum ina ganin giftawarki idan kin dawo islamiyya kuma gaskiya ina sonki saisa natunkareki nafad'a miki domin insamu matsugunni a zuciyanki wlh ina sonki, ina k'aunarki ina begenki, wlh indai baki amshi tayin soyayya taba zan iya mutuwa.
zarah baki tasaki tana kallonsa maganganunsa har sukaso subata dariya tadake tace ka gama?
hamza yace eh nagama ina dai son inji daga gareki domin kema nasan nayi miki
Zarah d'an murmushi tayi tace nagode sosai da tayinka ammah saidai kayi hak'uri domin ina da wanda nake......
katseta hamza yayi yace dakata malama ai daman abinda naji ma tsoro kenan saisa tun tuni nak'i tunkararki da maganar ammah wlh bakiyimin adalciba danma kin samu ance ana sonki wanene anguwarnan bai san halin gidankuba waye baisan ku 'yan iska bane, dan ma kin samu antaimaka ance ana sonki.
zarah murmushin takaici tayi sannan tace toh nagode kuma so ne bazan ta6a sonkaba, tana gama fad'in haka tawuce tabarsa tana jinsa yana ta yada mata bak'ak'en maganganu ammah tasharesa cikin ranta ko wani irin abune yatokare mata mak'oshi tabbas tasan abinda bawan Allahn nan yafad'a gaskiyane a game da gidansu, ahaka ta isa gida da tunani iri-iri cikin ranta.
*BAYAN SATI 'DAYA*
Rauda yau kasancewar ta tashi da matsanancin ciwon kai da zazza6i kwance tawuni bata iya komai, da kaganta kasan tana jin jiki tuni ta fita hayyacinta saboda Amai da take yawan yi
su mama sun tusata a gaba kowa tausayinta yakeji ganin irin wahalar da take sha kallonsu kawai zakayi kasan suna cikin matsanancin tashin hankali.
zarah ko kuka kawai takeyi tana rik'e da hannun yayartata ko kad'an bata yarda tamatsa daga kusa da itaba domin ita tana da k'wallafar 'yan uwanta.
mama ce tahad'o mata ruwan bunu tare da indomie matsa mata sukayi sai taci, ba dan tasoba tadaure tamik'e dakyar tayi loma ukku shima dan taga hankalin dangin nata a tashe, kafin kace mi dagudu tamik'e tanufi toilet tadinga kwarara amai dasauri zarah tabita tarik'eta tana mata sannu har saida tagama, Aysha ce tad'ebo musu ruwa a buta nan zarah tataimaka mata tawanke jikinta sannan suka fito takoma takwanta.
zarah kallon su mama tayi da sukayi jugum tace mama dan Allah kice ma yaya Rauda tatashi muje asibiti domin bai dace tazauna da ciwo ba.
mama dogon numfashi taja tare da cewa hakane zarah nima abinda nake tunani kenan domin cikin d'an lokacin nan duk ta fita hayyacinta.
Rauda dakyar tabud'e baki tace a'a ba zanje asibitiba kubarni a nan kawai in muturwace inyita a gida.
zarah da Aysha fashewa sukayi da kuka ganin yarda 'yar uwar tasu take jin jiki, mama tace A'a Rauda dole fa kitashi muje asibiti.
Zarah tace mama ni zan rakata kice tatashi mutafi.
mama tace ke mezaki iya idan kinje? Ni dai zan tafi da ita.
Zarah tace dan Allah mama kibarni muje tare, mama ganin yadda zarah duk hankalinta yake a tashe dan ko abincin kirki bata samu taciba dan haka tace toh shikenan kushirya kutafi.
Mama tataimaka ma Rauda tacanza kaya, Rauda cema Zarah tayi tad'auko handbag d'inta akwai kud'i a ciki dan kar a buk'aci wani abu.
Aysha ce tafita tasamo musu adaidaita nan suka tafi General Hospital d'in garinsu.
basusha wahala ba wajen ganin likita, ko da Rauda tashiga zarah zaune tayi tana jiran fitowarta,
Rauda take zaune opposite d'in kujerar Doctor Xeey Xeey cike da kulawa doctor Xeey Xeey take mata tambayoyi ita kuma tana bata amsa nan Dr Xeey Xeey tarubuta mata taste tace taje tayi kuma tatabbatar yau ta kawo mata.
Rauda Kar6a tayi tafito dasauri zarah tamik'e daga inda take zaune tana jiran fitowar 'yar uwartata.
tace Yaya Rauda sannu.
Rauda dakyar tace Zarah taste ne tabani muje lab.
zarah tace toh yaya Rauda.
ko da sukaje lab aka d'ibi jininta sannan aka bata 'yar roba tayi fitsari a ciki nan akace sujira nan da 30 minutes result zai fito.
zama sukayi suna jira har minti talatin yacika aka basu nan Rauda taje takaima Dr xeey xeey sakamako.
Dr xeey xeey tana dubawa murmushi tayi sannan tayi 'yan rubuce-rubucenta bayan ta gama tad'ago kai takalli Rauda tace toh Alhmdllh ina tayaki murna domin kina d'auke da ciki tsawon wata biyu nasoma ace tare kukazo da mijinki.
Rauda da tunda Dr ta ambaci ciki tarikece cikin d'aga murya tace doctor ciki?
Dr xeey xeey tagyad'a mata kai tace of course dan haka za'a maida miki folder d'inki a ANC kidinga zuwa awo tunda har yakai kusan 2 months batare da anduba lafiyarsaba zaki dinga zuwa awo.
Rauda zufa ce tafarayi dasauri taduk'e k'asa tare da fashewa da kuka.
da mamaki Dr xeey xeey take kallonta tace menene abin kuka? kyautar da Allah yabakice bakyaso ko mi?
Rauda cikin sheshek'ar kuka tace Dr dan girman Allah kitaimaka kiciremin cikin nan wlh bana sonsa.
Dr xeey xeey fara'ar da take fuskarta tagushe cikin fad'a tace akan wane dalili zaki cire ciki idan ke bakyaso toh mijinkifa? ni gaskiya bana zubar da ciki.
Rauda cike da tashin hankali tace Doctor yadda Allah yataimakeki nima kitaimaka min wlh bana son cikin nan idan nakoma da shi gida bansan da wane ido zan kalli iyayena ba.
Doctor da tunda Rauda tafara maganar tazuba mata ido tana kallonta cike da 6acin rai tace idan na fahimceki kina nufin cikin nan na shegene baida uba ko?
Rauda shuru tayi batace komai ba.
ganin haka yasa Doctor tacigaba da cewa toh bari kiji ni bazan ta6a zubar miki da cikiba k'ara ma kiyi hak'uri kihaife abinki ammah kuma kin cuci abinda yake a cikinki domin kin samesa ba tahanyar da tadace ba, k'arama kiyi hak'uri kihaifesa domin kar zunubin yak'aru dan haka tashi kije nidai nabaki shawara haihuwar shi zai fiye miki.
Rauda dakyar tamik'e jiki ba kwari tafito daga office d'in doctor.
tana fita kallon zarah tayi nan hankalinta yak'ara tashi sai alokacin taji wata irin kunya tsaye tayi takasa k'arasawa wajen da zarah take tsaye.
ganin haka yasa zarah tamik'e cikin sauri ta isa inda Rauda take cike da tashin hankali tace yaya Rauda lafiya naganki a haka me yake faruwane?
Rauda hawaye suna zuba daga idonta dakyar tabud'e baki tace zarah ciki gareni.
Zarah a firgice taja da baya cike da tashin hankali tace yaya Rauda ciki kuma?
Rauda gyad'a mata kai tayi tare da mik'a mata takardar da doctor tabata, jikin zarah yana kyarma ta amsa taduba, aiko nan tafashe da kuka tace yaya Rauda meyasa kuka za6a ma kanku irin wannan rayuwar? meyasa kuka za6i son abun duniya kuka 6ata rayuwarku, kingani ko yanzu gashinan kiyi cikin shege cikin da ke kanki bakisan ubansaba kun d'auki alhakinsa idan kika haifesa me zaki ce masa?
Rauda da take kuka dasauri tarik'o hannun zarah tace zarah wlh nima bansan ya zanyiba yau ne karo nafarko da nafara nadamar abinda nake aikatawa dan Allah kizo muje murok'i wata doctor d'in tacire min shi.
zarah fizge hannunta tayi daga rik'on da Rauda tayi mata tana ja da baya tare da girgiza kai, cikin kuka tace yaya Rauda badani za"a had'a bakiba ayi kisan kai meyasa kikeso kikashe ran da baida alhakin kowa saima shi da yake da naku?
kiji tsoron had'uwarki da ubangiji ga laifin zina ga na kisan kai, kituna tsayuwar ki gaban Allah ranar gobe k'igama, baki tsoron garin zubar da cikin kije kirasa ranki?
Yaya Rauda wani irin nadamane taji ya zo mata nan tak'ara fashewa da wani sabon kukan tare da rik'o hannun zarah da itama take kuka tace zarah nafasa zubarwa wlh nayi nadamar abinda na aikata a yanzu kuma ba zan zubar da cikinba.
zarah cike da jin dad'i tace nagode sosai Yaya Rauda da kika fahimceni.
Yaya Rauda d'an tsagaitawa tayi da kukan da take tace saidai kuma inaso kiyimin taimako guda.
zarah dasauri tace Yaya Rauda kifad'i abinda kikeso zanyi miki.
Rauda tace inaso kafin muje gida kifara rakani wani waje
zarah da mamaki take kallonta tace yaya Rauda ina zamuje?
Rauda rik'o hannunta tayi tace muje kawai zarah.
zarah batayi musuba tabi bayanta.
mai adaidaita tatsaida musu tafad'i anguwar da za'a kaisu zarah dai shuru tayi tana mamakin inda zasuje.
Rauda ce tadinga gwada ma mai napep hanya bayan sunzo anguwar, bakin gate d'in wani gida aka safkesu nan Rauda tabiyasa kud'insa sannan tayi Knockin d'in k'ofar maigadi ganin Rauda ce yasa yabud'e saboda daman ya saba ganinta nan suka shiga ciki, ita dai zarah binta kawai take
cikin wani parlour suka shiga da sallamarsu ammah bakowa ciki Rauda kallon zarah tayi tace Zarah shigo muzauna,
zarah girgiza kai tayi tace a'a yaya Rauda nan gidan wanene.
Rauda ganin zarah duk ta rikice yasa tace kar kidamu bawani abu inaji suna ciki kizo kizauna.
Zarah a tsorace tabi Rauda suka zauna nan Rauda tad'auko wayarta tayi kira itadai zarah kawai ji tayi ta ce gani cikin gidan ka sannan takashe wayar.
zarah a tsorace tace yaya Rauda wai nan gidan wanene me zamuyi?
Rauda har ta bud'e baki zatayi magana sai ga wani mutum ya fito daga cikin gidan, da kallo duk suka bisa fuskarsa d'auke da murmushi yazo yazauna d'aya daga cikin kujerun d'akin tare da washe baki yace baby daman kina tafe baki fad'amin ba? kallon zarah yayi da itama take kallonsa yace sannu 'yanmata halan ke sister d'intace naga kuna kama?
duk tambayoyin da yayi musu babu wanda yatanka mushi sai ma ido da suka zuba masa.
Rauda fuskarta a d'aure tace Alh umar nazone infad'a maka ina d'auke da cikin wata biyu.
nan fara'ar da take fuskarsa tagushe yace ciki kuma rauda?
Rauda hawayene suka fara zuba daga idonta tace eh ciki.
dariya yayi irin ta rainin wayau yace lallai Rauda toh garin yaya kika bari har ciki yashigeki? toh wai ma wanene yayi miki cikin?
Rauda da mamaki take kallonsa tace Alh Umar in bakaiba wanene nake huld'a da shi? ai kaine uban d'an saisa nazo nafad'a maka.
d'aure fuska Alhaji umar yayi tare da daka mata tsawa yace ke banason sakarci kingama zuwa kinbi 'yan iska sannan kizo kice d'a nane,
Rauda cikin kuka tace wlh d'ankane
Alh umar a harzuk'e yamik'e tsaye yace toh bari kiji duk wanda yatsaya miki a garin nan bai isa yasa in amshi cikin kiba a matsayin d'ana kije dai kigano uban cikinki dan haka kutashi kufitar min daga gida.
Zarah ranta ya 6aci sosai jin kalaman da Alh umar yake jifan yayarta dasu ga Yaya Rauda kuka kawai takeyi, cikin 6acin rai tamik'e tsaye tare da nunasa da yatsa tace kai malam kar karaina ma mutane wayau kana nufin k'arya akeyi maka ba cikin naka bane? ai ni wlh naga wautar yaya Rauda da ta iya ba jakki irinka kanta, ni ai ko a k'afa aka d'aura min kai sai na kwance.
Alh umar ransa ya 6aci sosai cikin fushi yake ke karkinemi kigaya min magana wlh yanzu insa ad'aureki ni nace tabani kanta ba kwad'ayi yaja mataba?
zarah cikin d'aga murya tace kai kar kasaki kak'ara d'agamin murya kuma idan bakasa and'aureniba toh ba'a haifekaba.
Alh Umar a zuciye yad'aga hannu zai mari zarah cikin zafin nama zarah tagoce.
yaya Rauda da take zaune tana mamakin yadda zarah take balbala fad'a tabbas tasan ankai zarah k'arshe domin zarah tana da hak'uri sosai, da sauri Rauda tamik'e tare da rik'o zarah tace zarah ki kyalesa tunda dai har ya k'aryata alhali kuma ya san gaskine toh yaje shi da Allah.
Zarah fizge hannunta tayi tace yaya Rauda kikyaleni ya za'ayi mutum yana akan gaskiyarsa a tauye masa hak'i wlh dole yakar6i cikin nan.
Alh umar dariya yayi yace ke yanzu har kina tunanin zan kar6a ko? toh muzuba agani wanene zai ci nasara.
Rauda cikin kuka tace umar *LAIFI NANE* da na amince na mallaka maka kaina ammah inaso kasani ba zan d'auki matakiba saidai kaje kai da Allah domin shine kad'ai zai kwatarmin hak'k'ina kuma kai shedane kaine karabani da budulcina kayaudare kace zaka aureni, wlh a yanzu na tsaneka kaje kawai
rik'o zarah tayi tace zarah wuce mutafi zarah har ta bud'e baki zatayi magana Rauda tadaka mata tsawa tace kiwuce nace miki!
Zarah ba dan tasoba tabi bayan Rauda suka fita suka bar Alh umar a tsaye cike da takaicin bak'ak'en maganganun da suka yada masa.
Ko da suka fita zarah kallon Rauda tayi cikin 6acin rai tace haba yaya Rauda ya za'ayi kina da gaskiyarki sannan kibari atauye miki hak'i.
Rauda cikin kuka tace zarah ina kokwantone domin bansan ainahin cikin na waneneba.
Zarah cikin tashin hankali tace ban fahimcekiba yaya Rauda.
Rauda share hawayen fuskarta tayi sannan tace zarah ba zan 6oye mikiba wlh mutum biyune kawai nasan ina mallaka ma kaina.
zarah tace yaya Rauda wannan wace irin rayuwace toh wanene gudan?
Alh munir ne wlh bayan su bana huld'a da kowa.
Zarah tace toh yaya Rauda me zai hana shima muje wajensa?
Rauda jinjina kai kawai tayi nan suka samu mai adaidaita Rauda tafad'a masa anguwar da zai kaisu........
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....✔*
_Jinjina agareku sis Mugirat marubuciyar *KISHI KO HAUKA* da sis Ummie Adnan marubuciyar *HAUWA JIDDAT* gaskiya inajin dad'in novels d'inku basirarku da k'wazonku suna burgeni kunyi namijin k'ok'ari a wajen rubutunku Allah yak'ara basira da zak'in hannu acigaba da sambad'o mana, *KISHI KO HAUKA DA HAUWA JIDDAT* duk Wanda bai karantaba anbarsa a baya dan haka kugarzaya kukaranta, muje zuwa😍👍_
_~Gareka *DR ZAIN* 👍 ina jin dad'in novels d'inka Allah yak'ara basira da zak'in hannu, nagode sosai da kyautan pages d'in da nasamu, *'YAN GUDUN HIJIRAH* labari maicike da darussa duk wanda bai karantaba anbarsa a baya~_
_*Yau page d'in nakune Mummyn Afrah nd Meena Abbah Wlh ina ji daku irin sosai d'innan, jinjina agareku marubutan *NI DA MIJIN YAYATAH gaskiya kunyi namijin k'ok'ari a cikinsa Allah yak'a basira da zakin hannu I heart u all😘*_
page 1⃣2⃣
Ko da suka isa nan ma maigadi bai hanasu shigaba saboda ya san Rauda sosai.
hango Alh munir sukayi a parking space yana shirin shiga motarsa ganin Rauda tare da zarah yasa yatsaya yana kallonsu fuskarsa d'auke da murmushi har suka iso wajen da yake su dukansu fuskarsu a d'aure take,
Washe baki Alh munir yayi yace Rauda kece tafe tare da sister d'inmu? ya dai ko itama tana cikine? ai daman na fad'a miki kud'ine abokan rayuwa nasan daman itama zata amince, yanzu dai mushiga daga ciki muyi magana ko tafiya zakiyi kibarni da ita?
Rauda cikin fushi tace ni ba wannan yakawomuba nazone in shaida maka ina d'auke da cikinka tsawon wata biyu.
Alh munir saida yafirgita jin ta ambaci ciki ammah yadake yayi 'yar dariya ta rainin wayau yace ciki kuma? Haba kina big gurl ya za'ayi kibari kiyi cikin shege kuma dan kin rainani shine sai kice cikinane?
zarah cike da k'ulewar dariyar da yayi musu tace idan ba cikin ka bane toh na uban wanene?
Alh munir tsagaitawa yayi daga dariyar da yakeyi yace ke kardai kisaki kizageni naga kamar kunya bata ishekiba,
Zarah dariya tayi tace girma dai ya riga da ya fad'i akwai marar kunya bayanka? kabaro iyalanka kazo kana 6ata rayuwar 'ya'yan wasu kuma ciki dole kakar6esa dan baida uba bayan kai.
Alh munir cikin 6acin rai yace baku isa kulik'a min d'an shegeba ita ai tasan wad'anda take bi saitaje tagano wanda yayi mata ciki ammah ni wlh babu wanda ya isa yace cikinane kuma barakiji rauda daga yanzu kar ma kik'ara nuna kin sanni ko da ahanyane, motarsa yabud'e yad'auko kud'i yamik'a masu yace ga wannan kinje kisamu kicire cikin tunda daman kwad'ayi yaja miki sannan kufitarmin daga gida tun kan ranku ya6aci.
Zarah kallon Rauda tayi da taketa aikin kuka ran Zarah ya 6aci sosai, sannan tamaida kallonta ga Alh munir takar6i kud'in tawatsa masa a fuska tace karik'e kud'inka bama so, eh dole kace haka tunda ka ci moriyar ganga, saidai inaso kasan wani abu kaima kana da 'ya'ya kuma kana da mata dan haka kasaurari naka, kar kamance Allah ba azzalumin bayinsabane kuma fad'an ubanginine abinda kayi sai anyi maka, murmushin takaici Zarah tayi kwallah duk ta cika mata ido tace alhaki kwikwiyone muje zuwa, rik'o hannun Rauda tayi har sun fara tafiya sannan tatsaya batare da ta juyoba tace kuma ciki ba zamu ta6a zubar da shiba sai ta haifesa anan zamu gane wanene ubansa kuma ko jinin wanene dole mukai ma matarsa tareni cikin shege.
Tana gama fad'in haka taja Rauda suka fita sukabar gidan.
Hankalin Alh munir ya tashi sosai domin tunda yaga zarah yasan zata iya yin komai ma, chan kuma sai yayi murmushi yace naga ta yadda za'ayi inkar6i dan shege, yana gama fad'in haka yakoma cikin gida fitarma yafasa
Suna fitowa Rauda duk'ewa tayi k'asa tacigaba da kuka, zarah share k'wallar idonta tayi tace yaya Rauda kinga abinda nake guje muku kingani ko yanzu gashinan dukansu babu wanda takar6i cikin kowa ya ce banasa bane.
Rauda tsagaitawa tayi daga kukan da takeyi tace tabbas zarah nagani kuma nasan *NATAFKA BABBAN KUSKURE* da na'amince nabi son zuciyana yanzu gashinan najawo ma kaina babar matsalarma bansan ya zanyi intunkari su mama da cikiba bansan ya zasu d'auki lamarinaba, zarah kawai kitafi gida.
Zarah cike da tausayi tad'ago yayartata daga tsugunnin da tayi tace haba yaya rauda meyasa zakice haka duk abinda yafaru kid'aukesa a matsayin *K'ADDARA CE* kar kidamu nayi miki alk'awali ni zan tsaya miki ga su mama har sai sun fahimceni *KIYARDA DANI* yaya Rauda.
Rauda kallon k'anwartata takeyi cike da gamsuwa ta jinjina kai domin tasan zarah tana da hankali zata iya shawo kan iyayen nasu, share hawayenta tayi tace shikenan Zarah na yarda da ke ammah naga illar abinda na aikata.
Zarah murmushi tayi tace kikwantar da hankalin yaya Rauda nidai fatana kidaina wannan rayuwar da kikeyi kikoma mutuniyar kirki
Rauda tace zarah insha Allahu nadaina domin nakoyi darasi tun a nan yanzu dai muje gida fatana su Abbah su fahimceni.
Mai adaidaita suka samu suka fad'a masa inda zai kaisu har k'ofar gidansu yasafkesu suka sallamesa.
Rauda tsaye tayi takasa shiga gidan ganin haka yasa zarah tarik'o hannunta suka shiga lokacin Abbah da mama Suna zaune tsakar gida Suna cin abinci, jin sallamarsu yasa Aysha tafito daga d'aki rataye da d'an k'aramin veil da alama fita ma zatayi.
Mama ce tace Rauda har kun dawo? yanzu daman muke maganarku da malam muna cewa shuru har yanzu baku dawoba.
Zarah da Rauda tsaye sukayi suna kallon juna kowa hankalinsa a tashe, mama da abbah zuba musu ido sukayi suna kallonsu domin daga ganin yanayinsu babu alamun gaskiya a tattare da su, jikin Mama ya yi sanyi tace Rauda lafiya naganku haka?
Rauda kuka tafarayi tare da zaunawa k'asa tace mama kuyafemin wlh na cutar da rayuwata tabbas ban d'aukoma kaina hanyar da zata 6ulleba a yau nayi nadamar dukkan mugun halin da nayi a baya na cuci kaina ina tsoron had'uwata da ubangijina.
Mama cikin tashin hankali tace Rauda meyake faruwa? Zarah kuyi min bayani menene yafaru?
Zarah murmishin takaici tayi tana hawaye tace mama tarbiyar da kukabamuce kar kuzargemu duk abinda yafaru tunda kwad'ayi da son abun duniya gareku.
abbah tsawa yadaka musu yace kuyi mana bayani mana me yake faruwa? sai wani kwana-kwana kukeyi mana
Rauda ce tad'ago kai takallesu tace Abbah mama kuyi hak'uri ina d'auke da ciki tsawon wata biyu.
Mama dafe k'irji tayi dak'warai tace Rauda ciki? Abbah ma yace ciki? ??
Aysha cikin tashin hankali tace yaya Rauda ciki kuma?
Zarah kallon iyayen nasu tayi tace eh ciki gareta.
Mama k'asa tasulale tazauna tace nashiga ukku Rauda gidan ubanwa kikayi ciki
Yaya Rauda ta kasa cewa komai face kuka da takeyi.
Abbah hularsa yacire yafara fifita yace idan baki fad'amin inda kika samo cikiba sai na karyaki a cikin gidan nan.
Rauda cikin kuka tace Abbah kar kuga laifina duk abinda yafaru ku ma kuna da naku laifin a ciki domin baku bamu tarbiya tagari ba, ko da nafara wannan rayuwar ko da sau d'aya bamu ta6a ganin kun nuna rashin jin dad'in hakan ba saboda kwad'ayinku da son abin duniya
tabbas ayanzu nayi takaicin kasancewarku iyayenmu nayi Allah wadai da hali irin naku, wlh nayi nadamar abinda na aikata natuba insha Allahu daga yanzu na sauya rayuwata, kallon Zarah tayi da take tsaye ta jingine da bango idonta a lumshe hawaye kawai suke fita, Rauda tace kukalli baiwar Allahn nan itace kawai tafita zakkah a cikinmu kawai kasancewarta mutuniyar kirki yasa muka tsaneta muka hantareta ammah baiwar Allahn nan hakan baisa tak'imuba a kullum k'ara jawomu take a jikinta tana mana wa'azi a k'arshe ma sai munemi muci mutuncinta ammah hakan baisa tabarmu ba, muna mata kallon bagidajiya ashe itace wayaiyar tamu tabbas Zarah rayuwarki ta burgeni natayaki murna da son zuciya bai rud'ekiba har kika fad'a wannan mummunar rayuwar da iyayenmu sukaja muka fad'a, tabbas yanzu nagane *DUK TSUNTSUN DA YAJA RUWA* shi ruwa kan doka.
Rauda nisa tayi sannan tamaida kallonta ga Aysha tace Aysha kitaimaki kanki kema kigyara rayuwarki tun kan rayuwa tajuya miki baya domin a yau nagane mecece rayuwa kowane saurayi naje ma maganar ciki saidai yawulak'antani yacimin mutunci a k'arshe zarah ce taso takwatar min 'yancina.
Aysha dasauri tacire veil d'inta tare da duk'ewa kasa tafashe da kuka tace wlh yaya rauda nad'auki darasi a wajenki nima nadaina abinda nake, maida kallonta tayi ga su Abbah da sukayi jugum tace tsakaninmu da ku Allah ne kad'ai zai mana *SAKAYYA* domin bamu dace da iyaye nagariba dakanku kuke turamu muna aikata 6arna wlh da ace ana canza iyaye da babu abinda zai hanani canza nawa
Zarah dasauri tabud'e idonta tana kuka tace kun gani ko mama? Abbah kunga halin da kuka jefamu a ciki kuma wlh ranar lahira sai Allah ya tambayeku game da kiyon da yabaku, yanzu gashinan duniya ta juya muku baya, idan yaya Rauda tahaihu kundinga kallon abinda tabari kutuno kuskuren da kuka tafka, girgiza kai tayi cike da takaici tace da ace akwai inda zamuje da muntafi munbar muku gidanku muje muyi rayuwa mai tsafta.
Mama fashewa tayi da kuka tace wlh son zuciyane da sharrin shaid'an suka ja mana kuma insha Allahu muma mundaina kuyafe mana,
Aysha mik'ewa tayi tazo inda Zarah take tace yaya zarah tabbas kin ciri tuta a cikinmu duk abinda muke aikatawa baisa kin k'yamacemuba sai ma soyayyar da kike nuna mana, Dan Allah kiyafe min abinda nayi miki.
zarah murmushi tayi wanda yafi kuka ciwo tace bakomai Aysha Allah yayafe mana gaba d'aya.
Rauda mik'ewa tayi tsaye tace dan Allah kuzo muje mubar musu gidan nasan ba zamu rasa wajen zama ba Allah yana tare damu. Aysha tace hakane yaya Rauda mun amince mutafi.
mama k'ara fashewa tayi da kuka tace nashiga ukku dan girman Allah kar kutafi kubarmu wlh muma mun tuba, mama kallon Abbah tayi da yayi jugum sai zufa yakeyi tace haba malam dan Allah kace wani abu mana kar sutafi.
Abbah dakyar yabud'e baki yace Zarah, Rauda, Aysha kudawo kuzauna muyi magana,
tsaye sukayi sukak'i motsawa zarah ce tayi k'arfin halin cewa yaya Rauda kuzo muje muzauna.
A tare sukazo suka zauna har a lokacin mama kuka takeyi, Abbah ne yayi gyaran murya sannan yace.......
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Masha Allah *Mummyn Afrah nd Meena Abbah* ina tayaku murnar kammala novel d'inku mai suna *NI DA MIJIN YAYATAH* hak'ika kun wa'azantar, kun fad'akar sannan kun Nishad'antar damu, gaskiya tsarin rubutunku da fasahar da kuka zuba ta sun burgeni, Allah yabada ladan abinda aka fad'a daidai, kurakuren da suke ciki Allah yayafe muku, inaso kusani ina muka son so, Allah yabar k'auna my Aunties😘_
page 1⃣3⃣
Abbah gyaran murya yayi sannan yace maganar barin gida duk bata tasoba a yanzu muma mungane kuskurenmu tabbas duk abinda mutum yashuka shi zai gir6a wlh banga laifinkuba tabbas bamu dace da mukasance iyayenkuba, Abbah girgiza kai yayi yace kaicona da nabari son abun duniya yarud'eni har nawatsar da tarbiyar yarana alhali ni iyayena bahaka sukayi min ba, son zuciya da kwad'ayine suka ja mana dan Allah kuyi hak'uri da mummunar d'abi'ar da muka d'auraku akanta, wannan ya zama darasi a garemu ayi hak'uri a yafi juna.
mama cikin kuka tace dan Allah kuyafe mana insha Allahu yanzu zamu gyara tsarin gidanmu da komai zakuyi alfahari da mu.
Zarah ce tace bakomai wlh mun yafe muku duniya da lahira muma kuyafe mana.
kallonta tamaida ga su Rauda da basu da niyar yin magana tace yaya Rauda dan Allah kuyafe ma su mama tunda sun gane kuskurensu.
Rauda da Aysha cikin kuka sukace shikenan mun yafe musu Allah yayafe mana gaba d'ayanmu.
gaba d'aya suka amsa da Ameen.
sannan Abbah yace toh Alhmdllh da Allah yataimakemu muka farka tun kafin lokaci yak'ure mana naji dad'in hakan, insha Allahu zanyi k'ok'ari duk wani hak'inku da yarataya kaina inga na safke muku shi, saidai matsala d'aya yanzu cikin da yake jikin Rauda bansan ya zamuyi da Shiba.
Mama ma tayi nisa sannan tace mezai hana azubar da shi?
Zarah da sauri tagirgiza kai tace a'a mama bai dace azubar da shi ba karfa mumanta shi fa d'an baida alhakin kowa sai ma su da yakeda alhaki akansu da suka samesa ba ta hanyar halak ba, ga laifin zina ga na kisan kai ai k'ara tahak'ura tafauwala ma Allah lamurranta saboda Allah yana sane da halin da take ciki kuma komai rubutaccene ya riga ya tsara ma kowa yadda rayuwarsa zata kasance, shin baku tsoron wajen zubar da cikin tarasa rayuwarta? idan taje me zatace ma ubangijinta ranar gobe k'iyama? Shin kunsan yadda rayuwa zata kasance a nan gaba ko kuna tunanin nan gaba zata k'ara haihuwa? yakamata mumik'a lamurranmu ga Allah ubangijinmu mucigaba da rok'onsa tare da neman gafararsa Allahu gafurur rahim ne.
Dukkansu jinjina kai sukayi alamun gamsuwa da bayanin Zarah, Abbah yace tabbas Zarah nagamsu da bayaninki Allah yayafe mana kuskurenmu wlh ke d'iyar kirkice, kekuma Rauda Allah yasafkeki lafiya.
Gaba d'ayansu sukace Ameen, mama tace Allah yayi muku albarka Allah yaraya mana ku.
cike da jin dad'i sukace Ameen mamanmu,
muma muna alfahari da ku Allah yabar mana ku.
daga nan suka shiga tsara yadda zasu tafiyar da rayuwarsu, Aysha da Rauda 'yan kud'in da suke hannunsune suka tattara suka ba iyayen nasu sukace asiyo kayan abinci,
tun daga ranar suka rabu da samarinsu gidan yagyaru, inda Aysha takoma islamiyya suna zuwa tare da Zarah, Rauda kuma tacigaba da rainon cikinta, a gida Zarah takeyi masu k'arin karatunsu Rauda da Mama.
cikin ikon Allah Abbah yasamu d'an aikin da ake biyansa duk wata da taimakon Allah yake samu yana rik'e gidansa gwalgwadon k'arfinsa,
su kansu a yanzu suna jin dad'in sauyawar da suka samu ta rayuwa.
_______________
Yarima Suhail yau tunda yatashi jinsa yake wani iri ga tsananin buk'atar sumayya da yakeyi daurewa kawai yake tsawon wata biyu kenan rabonsa da ita.
yau bayan yadawo wajen aiki yayi wanka ya shirya cikin shigarsa ta alfarma fitowa yayi yanufi part d'in sumayya domin yau ji yake hak'urinsa ya k'are baya iya cigaba da daurewa
Yarima d'akinn sumayya yashiga lokacin sumayya tana zaune a parlour tsakiyar kuyanginta suna ta mata hidima.
ganinsa yasa dukansu suka zube suna kwasar gaisuwa yarima baibi ta kansuba yashige bedroom d'in sumayya, da harara sumayya tabisa sannan tamik'e tabi bayansa.
tana shiga ta tarar da shi zaune saman gado batare da ta tanka masaba taje tazauna itama kusa da shi nan wajen yad'au shuru.
ganin baida niyar yin magana yasa sumayya tace lafiya?
Harara yarima yawurga mata tare da cewa lafiyar kenan, hak'ina nazo kibani.
'yar dariya gimbiya sumayya tayi sannan tace sai a yau za'a waiwayeni? ai nad'auka anrufe shafina, ko ka mance lokacin da nazo d'akinka kakoreni? ai nad'auka nagama amfani a wajenka ashe ina da sauran amfani.
yarima suhail wata muguwar harara yawurga mata cikin 6acin rai yace sumayya da ace akwai yadda zanyi inguje ma kusantarki da nayi domin nima ba dan nasoba nake nemanki domin kwatakwata ke ba ajina bace dandai *K'ADDARA CE* kawai tasa na amince ma aurenki, wlh kikiyayi ranar da zaki kaini k'arshe domin zan d'auki mummunan mataki akanki.
Sumayya ta6e baki tayi cikin rashin damuwa tace kai fa matsalata da kai bakasan arzik'iba sai kanaso ataimaka maka maimakon kalalla6ani shine kakemin fad'a da gori. wlh nima ashirye nake nakad'auki kowane irin mataki nasan dai duk abinka ba zaka ta6a k'ara aureba dan su dada ma nazasu amince ba.
yarima har ya bud'e baki zaiyi magana nan wayansa tafara ringing ganin ummi ce yasa yasaita nutsuwarsa sannan yayi picking tare da yin sallama.
chan 6angaren sultana sadiya ta amsa masa tare da cewa yarima kazo kasameni inason ganinka.
yarima suhail cike da ladabi yace ummi lafiya dai ko?
Ummi tace lafiya lou kawai inaso mutattauna ne akan kayan da kace aware akai gidan marayu da gajiyayyu.
yarima shuru yayi nad'an lokaci sannan yace toh ummi ganinan zuwa, nan yakashe wayar tare da mik'ewa ko inda sumayya take bai k'ara kalloba yaficce yabar d'akin.
sumayya haushi yakamata saboda ba haka tasoba taso ace sai tagama ja masa rai sannan zata amince masa domin itama buk'ace take da shi kawai dai tana daurewane domin tanuna masa kuskurensa na wulak'antata da yayi, tsaki taja tare da mik'ewa tsaye tace nasan dai dole zai dawo gareni.
yarima ko da yafita direct turakar iyayensa yaje a parlour yatarar da k'anwarsa Gimbiya Rahma a tsakiyar kuyangi sun zagayeta suna mata fifita da tausa inda ita kuma take waya.
ganinsa yasa gaba d'ayansu suka zube k'asa suna kwasar gaisuwa, Rahma ma dasauri tamik'e tsaye tare da d'an rissinawa cike da girmamawa tace barka da shigowa.
Yarima batare da ya tanka musuba yayi musu nuni da k'ofa alamun sufita.
gaba d'ayansu suka mik'e suka fita daga d'akin, Rahma ma har zata fita yace ke dawo.
Rahma dawowa tayi tazauna kujerar da take opposite d'in wadda yake zaune, kallon yayan nata take taga baida niyar yin magana gashi duk ya canza, ahankali tace yaya suhail bakada lafiya ne?
Yarima suhail ahankali yamaido kallonsa gareta kamar ba zaiyi magana ba sai kuma can yace tashi kije kihad'o min ruwan lipton da lemun tsami kar kizuba komai ciki.
Rahma mik'ewa tayi tare da d'an rissinawa sannan taffice daga d'akin.
Yarima jingine kansa yayi akan kujerar da yake zaune tare da lumshe idonsa shi kad'ai yasan abinda yake ji.
ummi tana fitowa daga d'akinta ganin yarima a haka yasa tayi tsaye tana kallon d'an nata ahankali tace suhail daman ka shigo shine baka fad'a min ba?
Yarima suhail ahankali yabud'e idanuwansa da suka rikid'a suka koma launin ja yasafkesu akan fuskar ummi tare da yin d'an guntun murmushi yace sorry ummi ban dad'e da shigowaba.
ummi tsaye tayi tana kallon d'an nata yanayinsa yasa saida gabanta yafad'i a rud'e tace suhail me yake damunkane bakada lafiya?
Yarima murmushi yayi yace lafiya ta lau ummi.
ummi kasa cewa komai tayi saidai binsa take da kallo tana nan tsaye Rahma tashigo da wani plate d'auke da ruwan lipton da lemon a gefe, gaban ummi ne yashiga fad'uwa ganin Rahma ta aje gaban yarima tare da duk'awa tana matsa lemon d'in cikin cup d'in,
tausayin d'antane yakamata domin tabbas tasan abinda take tunani shi yakasance, ahankali taga yarima suhail yad'auki cup d'in yana sha yana yamitsa fuska duk Wanda yagani yasan ba dan dad'i yake sha ba kawai dai dan ba yadda ya iya.
ganin haka yasa ummi tawuce tana jin wani iri a cikin ranta bata zarce ko'inaba sai turakar mijinta bata damu da gaisuwar da akeyi mataba domin kwatakwata ma hankalinta ba anan yakeba.
ko da tashiga lokacin yana zaune saman gado hannunsa rik'e da newspaper yana dubawa, jin anbud'e d'akin yasa yamaida kallonsa ga k'ofa, yanayin yadda yaga matar tasa ta shigo yasa ya aje newspaper d'in da take hannunsa yazuba mata ido.
Sultana bilkisu itama tsaye tayi tana kallonsa ta bud'e baki zatayi magana kenan sai hawaye suka fara zuba daga idonta, Sultan Ahmad cike da rud'ewa yamik'e yanufo inda matar tasa take yace bilkisu lafiya me yake faruwane?
Sultana Bilkisu fashewa tayi da kuka tace ranka yadad'e kagafarceni akan abinda zan fad'a domin hak'urina ya k'are ace d'ana tunda yayi aure baida kwanciyar hankali kaduba kaga duk mulki, sarauta, kyau, dukiya babu wanda *YARIMA SUHAIL* yarasa saidai abu d'aya shine kwanciyar hankali.
Sultan Ahmad zuba ma matar tasa ido yayi yana kallonta domin yasanta akwai hak'uri duk abinda za'ayi mata batanuna 6acin ranta saidai idan ankaita bangone, Sultana bilkisu cigaba tayi da cewa tun lokacin da d'ana yayi aure baida kwanciyar hankali domin kwatakwata bai samun nutsuwa, kula da tattali a wajen matarsa Sumayya, ba wai shi yafad'a minba kawai dai nafahimci haka kaduba kaga yadda yarame koda yarima baya fad'in matsalarsa saboda zurfin cikinsa ammah yanayinsa kawai zaka kallah kagane yana cikin matsala, girgiza kai tayi tace ya za'ayi ace da matarsa ammah yana shan ruwan lipton da lemon, ranka yadad'e ina tsoron ranar da d'ana zai kasa jurewa har yafara neman mata, bawai fata nakeyi masaba kawai dai ina tsoron hakan domin shima mutum ne kamar kowa,
rik'o hannun sultan Ahmad tayi tare da durk'usawa k'asa tace ranka yadad'e idan maganganuna sun 6ata maka rai kayi hak'uri ammah ina tausayin halin da d'ana yake ciki, Sultana Bilkisu tana kaiwa nan tasake fashewa da wani sabon kukan.
Sultan Ahmad cike da tausayi yarik'o hannun matar tasa yamik'ar da ita tsaye yarungumeta yace Bilkisu nima ina lura da lamurran Suhail narasa ya zanyi ne domin ko bakomai d'iyar d'an uwana yake aure narasa ya zanyi in magance matsalarnan domin ina tsoron abinda zai samo min matsala ni da d'an uwana.
Gimbiya Bilkisu d'ago kanta tayi tana kallon mijin nata tace ammah shi d'anka fa kaduba kaga matsalar da take shirin 6ullomasa dan Allah kataimaka kaduba lamarin yarima Suhail domin yana buk'atar taimakonmu.
Sultan Ahmad rik'o hannun matarsa yayi sukaje bakin gado suka zauna yace Bilkisu nima inajin Suhail sosai a cikin raina kikwantar da hankalinki zanyi shawara muga yadda zamu 6ulloma lamarin cikin ruwan sanyi kema inaso kije kiyi tunani a kai kidaina sanya damuwa a ranki kinji.
Sultana Bilkisu cike da gamsuwa da maganar mijin nata ta jinjina kai tare da yin murmushin jin dad'i, shima Sultan Ahmad murmushin yayi sannan yashiga goge mata hawayen da suke fuskarta.
godia tayi masa tare da mik'ewa tsaye, kallonta yayi yace Bilkisu ina kuma zakije? ai nad'auka zuwa kikayi kitayani hira?
murmushi tayi tace kayi hak'uri d'ana yana parlour yana jirana bari inje insallamesa sai indawo.
Sultan Ahmad shima murmushi yayi yace toh shikenan sai kin dawo.
Sultana Bilkisu d'an rissinawa tayi cike da girmamawa tace nabarka lafiya sannan tajuya tafita tabar d'akin,
Yarima Suhail ko da yagama shan lipton d'in komawa yayi yajingine kansa da kujerar da yake zaune yana jiran mahaifiyartasa tafito anan bacci yafara d'aukesa.
Sultana Bilkisu ko da tashigo ganin d'an nata yana bacci yasa tazauna gefensa tare da d'aura kansa saman cinyarta.
ahankali suhail yabud'e idonsa sanin mahaifiyarsa yasa yasakarmata murmushi tare da maida idanuwansa yalumshe,
itama sultana Bilkisu murmushin tayi nan tashiga shafa gashin kan d'an nata cike da so da k'aunarsa, a gefe guda na zuciyarta tausayinsace ta baibayeta.
**** **** *****
mama ce da su zarah zaune tsakar gida suna k'ulla zo6o da kunun aya suna fira cike da nishad'i, Aysha ce takalli zarah tace wai yaya zarah yaushene ma zakuyi walimar saukarku ta alk'ur'ani?
Murmushi zarah tayi tace kedai Aysha kin cika zumud'i sai fa nan da sati biyu kinga ai da d'an sauran lokaci.
Mama tace kud'in ma da kikace kina buk'ata suna nan ajiye tun jiya Abbanku yabani inbaki idan kin tashi tafiya islamiyya sai kituna min inbaki kikai dan kar ma inta6asu.
Zarah cike da jin dad'i tace nagode sosai Allah yak'ara girma da rufin asiri.
gaba d'ayansu sukace Ameen, Rauda tace toh anko d'in da zakuyi fa?
Zarah murmushi tayi tace bazanyi wannan ba yaya Rauda domin bazan matsa ma kaina ba abinda nakeda hali shi zanyi saidai in naje suhanani shiga taron.
Mama tace a'a zarah baridai muga abinda hali zaiyi idan da hali ai sai ayi miki.
zarah tace a'a mama kar kud'aura ma kanku d'awainiya abarsa kawai.
Mama tace zarah kibari dai muga abinda hali zaiyi idan da rabo ai za'ayi.
Aysha tayi karaf tace aikam dai dole ayi anko d'innan dan walima zamuyi sosai, nima zan bada gudumuwata.
Dariya Rauda tayi tace jarin sana'arki zaki bamu ko?
Aysha tace sosai ma ai har nafara tari ribar nake zubawa asusu.
dariya suka sanya mata zarah tace gaskiya nagode sosai 'yar uwata da k'aunar da kike nunamin.
Aysha murmushi tayi tace wannan kuma halinkine domin ke kike nuna mana k'auna ta gaskiya.
A islamiyya zarah ce da k'awarta zaune suna d'an ta6a hira kafin malam bello yashigo, khairy kallonta tayi tace wai k'awata me kike shirya mana na walimar nan?
murmushi zarah tayi tace abinda hali yabani domin ba zan matsa ma kainaba abinda nake da halinsa shi zanyi dan ni ko ankoma bana tunanin yinsa.
Khairy zaro ido tayi tace kai zarah dan Allah kiyi anko d'in kinga kowa fa zaiyi ya za'ayi ace kekad'aice ba zakiyiba.
zarah murmushi tayi tace ba zan damuba domin kowa da bazarsa yake taka rawa, abinda Allah yahoremin shi zanyi.
Khairy jinjina kai tayi cike da gamsuwa da maganar k'awartata sannan tace toh Allah yashige mana gaba.
zarah tace Ameen ya rabb, shigowar malam bello ne yasa ajin aka nutsu daga nan aka fara darasi.
bayan angama anyi addu'a antashi zarah tace muje khairy inkai ma malam kud'in walimana,
a office suka samu malam hambali bayan sun gaishesa ya amsa musu, zarah tace malam ga kud'in walimata,
malam hambali yace zarah banda kud'in da kika biya ko k'arine muka samu?
zarah da mamaki take kallonsa tace ni kuma nabiya kud'i? da yaushe?
murmushi malam hambali yayi yace Malam bello yazo yakawo kud'inki.
Zarah da khairy kallon Juna sukayi sannan sukayi ma malam hambali sallama suka fita daga office d'in.
A wajen islamiyya suka hango malam bello tsaye ya zuba ma k'ofa ido da alamu zarah yake jira yaga fitowarta,
zarah saida suka d'anyi gaba sannan tad'auko wayarta takira malam bello tace gamu muna jiranka.
suna gama wayar malam bello yazo yasamesu fuskarsa d'auke da murmushi yayi musu sallama nan suka amsa masa tare da k'ara gaishesa.
zarah tace malam naje biyan kud'in walima shine aka shaida min ka biya nagode sosai ammah gaskiya bazanso kadinga matsama kankaba tunda kaga kaima karatu kake dan haka ga kud'inka na maido maka.
malam Bello yace a'a zarah ni dan Allah nayi miki dan haka bazan kar6aba, kuma kidaina maganar karatu nake koma me nakeyi ai dan ina da halin yi miki da ace banda su ai da bazan mikiba.
zarah tace hakane saidai ina tsoro kar asamu matsala aurenmu yak'i yuwuwa, malam Bello murmushi yayi yace kar kidamu ko da ace ban aurekiba wannan nasan *K'ADDARA CE* kuma wani baya auren matar wani dan haka kikwantar da hankalinki.
murmushi zarah tayi tace nagode sosai malam da taimakon da kakeyi min Allah yataimakake kamar yadda kake taimakona.
malam Bello yace kar kidamu ai yi ma kaine, yanzu muje inrakaki gida naga magrib ta gabato kuma k'awarki ta tafi ta barki,
zarah murmushi kawai tayi nan suka jera da malam Bello suna tafiya suna hira har saida yarakata har k'ofar gida sannan sukayi sallama yatafi itakuma tashiga gida.
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
page 1⃣4⃣
Zarah ko da tashiga gida d'akin mama tashiga ta tarar da mama tana linkin kaya ganin zarah yasa tasakarmata murmushi tare da cewa 'yan makaranta andawo?
zarah ma murmushi tayi tace eh mama dafatan mun sameki lafiya?
mama tace lafiya lau, nan zarah takama mata suka cigaba da linke kayan, cike da nutsuwa zarah tad'auko kud'in tamik'a ma mama tace mama ga kud'in da kuka bani.
mama da mamaki take kallonta tace zarah ya haka? ya naga kin maido kud'in?
murmushi zarah tayi tace mama daman da naje inbiya shine akace malam bello ya biyamin kuma na kai masa kud'in yace bazai kar6aba shi dan Allah yayi min nayi-nayi yakar6a ammah ya k'i.
mama tace Allah sarki gaskiya yana d'awainiya dayawa mungode sosai Allah dai yabiyasa, yanzu kud'in ki aje wajenki kinga sai kiyi anko d'in da su,
zarah tace toh mama nagode sosai Allah yak'ara girma da rufin asiri.
mama cike da jin dad'i tace Ameen 'yar albarka nidai fatana a kullum Allah yakawo muku mazaje nagari kuyi aure.
zarah dagudu taficce tabar d'akin cike da jin kunya, mama dariya tayi sannan tacigaba da linkin da takeyi.
tun ana saura kwana hud'u ayi walimar aka bugo Invitation card aka gayyaci mutane da dama daga cikin wanda aka kaima katin gayyata har da maimartaba.
A gidansu zarah suma shirye-shirye suke daidai k'arfinsu, Abbah bakin gwalgwado yasiyo mata abinda zata raba ma abokanta da 'yan uwa.
malam Bello ma ba'a barsa a bayaba domin carton din lemu yasiyamata yakai mata dakyar yasamu zarah takar6a.
ana gobe za'ayi walimar gidansu zarah tun dare aka fara shirye-shiryen abinda za'a raba ma mutanen da suka gayyata kasancewar da k'arfe goma za'ayi walimar.
_______________
yarima tun daga lokacin yafita harkar sumayya ganin tana neman rainasa akan hak'insa yasa yajefar da ita gefe yacigaba da hidimarsa, sumayya tun tana daurewa itama taji bata iya daurewa.
yau ma kwance take tana ta juyi saman makeken gadonta tsaki kawai takeja tana neman mafita, chan tayi nisa tace daman ace zinat zatazo da nad'an samu sauk'in abinda nakeji, ammah bari inkirata ko ta flight ce tabiyo tazo yau, wayarta tajawo takira zinat ammah kashe wayartake,
tsaki sumayya taja tare da wullar da wayar tace matsalata da ita kenan ayita nemanta ba'a samu.
Sultana Bilkisu ce zaune a turakarta tana kallon wata drama a faskekiyar TV d'in da take manne a bangon d'akin, gefenta kuyangine zaune k'asa suna jiran jin umurni daga wajen mai d'akintasu.
Sultan Ahmad ne yashigo da sallamarsa dasauri duk suka zube suna kwasar gaisuwa, cike da fara'a ya amsa musu, nan suka tashi suka ficce daga d'akin ahankali yataka yaje inda matarsa take zaune tazuba masa ido fuskarta d'auke da murmushi,
shima murmushin yayi tare da zama kusa da ita, rik'o hannunsa sultana bilkisu tayi cike da kulawa tace daddynsu suhail barka da dawowa muje daga ciki.
sultan Ahmad tallabo fuskarta yayi yace sultana ai banje ko'inaba yau ina fada daga chan naje wajen dada munata shan hira.
Sultana Bilkisu tace Allah sarki, ya wajen memartaba duk kwanan nan bamu gaisa da shiba duk lokacin da zanje gaishesa toh yana chan fada.
sultan Ahmad yace lafiya lou, daman nima sawa yayi aka kirani yayi min magana akan wata walima da aka gayyacesa shine yace ni inwakilcesa inje tunda gobene zaya fita, kuma babu dad'i ace babu Wanda yaje daga wajensa.
Sultana Bilkisu tace tabbas hakane k'ara ko kaine kaje, murmushi sultan yayi yace ai tare da ke zamuje goben, yarima ma zan kirasa domin yashirya muje tare.
Sultana Bilkisu cike da farin ciki tace Allah yakaimu da rai da lafiya.
Sultan Ahmad yace Ameen, taso mushiga daga ciki akwai maganar da nakeson muyi,
dariya Sultana Bilkisu tayi tace kai Abban suhail kawai dai kace mushiga ciki ammah nasan babu wata magana da zamuyi.
wanshekare chan makarantarsu zarah cike take mak'il da mutane, daga wajen islamiyyar aka kafa rumfuna inda daga tsakiya aka tanadi wajen da za'a gudanar da walimar.
Rumfa d'aya aka fitarma da Yarima Suhail, Sultan Ahmed da Sultana bilkisu dukkansu sanye cikin kayan alfarma sai dogarawansu da kuyangi da suka zagayesu, nan aka cika musu gabansu da kayan ciye-ciye da shaye-shaye,
shi dai yarima suhail tun da yazauna dannar wayarsa kawai yake ko da sau d'aya bai d'ago kai ba, domin tun da yazo yaga anzuba masa ido mata da maza suna kallonsa saisa yajawo wayarsa yashiga dannawa.
inda daga bisani mai gabatar da shiri yafita yafara bayan ankira shugaban makaranta ya bud'e taron da addu'a nan aka fara gabatar da kowa, bayan angama aka fara kiran d'aliban da zasuyi walimar da d'ai-d'ayansu suna fitowa sugabatar da karatu.
Daga chan gefe nahango zarah da k'awarta khairy zaune cikin anko d'insu sunsha dogayen hijab d'insu.
zarah kallon khairy tayi da take ta kalle-kalle tazungurota tace ke wai mekike kallo tun d'azun kin zuba ma waje guda ido?
Murmushi khairy tayi tace wlh wancan yarima din nake kallo ya burgeni sosai kiduba kiga yadda ya hakimce, harararta zarah tayi tace kekuma rashin aikinyi miye abun kallo, ke nifa tunani nake anya zan iya fita inyi karatun nan? wlh jikina yayi sanyi sosai kuma nasan ganin mutanen da nayine.
Dariya khairy tayi tace nifa tsiyata da ke tsoron mutane gareki, kidaure kisa ma ranki babu kowa wajen insha Allahu zakiyi karatunki batare da fargaban komai ba.
zarah murmushi tayi tace nagode sosai khairy Allah dai yasa zan iya.
khairy tace Ameen.
kiran khairy da akayine yasa tamik'e tanufi filin tazauna bisa kujerar da aka tanadar masu nan aka mik'a mata lasifika tafara karatu.
tunda aka kira khairy zarah hankalinta ya tashi sosai nan gabanta yashiga fad'uwa, addu'a tashiga yi cikin zuciyanta ahankali taji nutsuwa tazo mata.
bayan khairy ta gama kiran sunan zarah aka yi, k'in tashi zarah tayi saida aka maimata kiranta sannan tamik'e ahankali tana tafiyarta a nutse, duk wanda yake wajen kallonta yakeyi yanayin yadda take takunta a nutse ta sadda kanta a k'asa ahaka ta isa filin taron tazauna, nan aka mik'o mata lasifika.
amsa tayi nan tad'anyi shuru na d'an minti biyu saida tasaita nutsuwarta sannan tafara karatun cikin muryarta mai dad'in saurare inda take karanta suratul bak'ara daga izif na ukku _Sayak'ulus-sufaha'u minan-nasi ma wallahum ank'iblata humullazi kanu alaiha_...... cike da nutsuwa take karatun, wajen yad'auki tsit kowa saurarenta yakeyi, yarima suhail tunda aka fara bai d'ago yakalli kowaba ammah lokacin da zarah tafara ji yayi yanason ganin wadda ta mallaki muryar, ahankali yad'ago kansa yasafke idonsa akan zarah da take karatu a nitse, kallo d'aya yayi mata yajanye kansa bai k'ara kallontaba har tagama sannan tamik'a lasifikar tare da mik'ewa tabar wajen.
gaba d'aya aka d'auki kabbara daga nan aka cigaba da kiran saura suna fitowa sunayi har aka gama.
bayan angama aka kira wasu daga cikin d'alibai sukayi drama ta larabci, da suka gama aka kira zarah tayi tafsirul alk'ur'ani kowa na wajen ya jinjina mata, da tagama nan aka d'auki kabbara, yarima suhail magana yayi ma iyayensa sannan yasa aka kira masa shugaban makarantar yadamk'a masa kud'i daganan yawuce yashiga motarsa yabar wajen.
daga bisani aka fara raba kyautukan da aka tanadar ma wad'anda sukayi walimar.
ko da akazo kan zarah, Sultana Bilkisu ce akakira tazo tabata itama ta azamata kyauta ta musamman sannan akayi musu pic's.
zarah har da k'wallarta ganin kyautukan da tasamu dan ko na makaranta kusan guda ukku tasamu sannan wanda mutane sukayi mata.
bayan angama raba kyautuka nan akayi d'an bayani sannan aka rufe taro da addu'a aka fara watsewa,
sultana bilkisu kallon d'aya daga cikin kuyanginta tayi tace taje tatafo mata da zarah,
ko da taje tafad'ama zarah zarah bata musaba tabiyota.
tun da suka tafo sultana bilkisu tazuba mata ido ganin yadda take tafiya a nutse har suka iso nan zarah taduk'a ta gaishesu, cike da fara'a Sultan Ahmad da Sultana Bilkisu suka amsa mata, sultana tace 'yanmata ya sunanki?
ahankali tace zarah,
sultana tace nice name, nan sultan Ahmad yad'auko 50k yabata.
cike da ladabi zarah ta amsa tare da yi masu godia sannan tawuce tabar wajen itadai Sultana Bilkisu binta kawai take daga kallo daga bisani suka tashi suka koma gida.
Zarah tattara mutanenta tayi tatafi dasu gisansu tabasu abinci na musamman sannan taraba musu kayan da tatanada, ita kanta ta jinjina ma 'yan gidansu ganin namijin k'ok'arin da sukayi dan sufitar da ita kunya, bayan anci ansha nan aka watse kowa yana murna.
nan zarah tad'auko kyautukan da tasamu taba iyayenta nan aka bud'e ana gani ana murna, kud'in da tasamu tadamk'a ma iyayenta rabi, sauran taraba taba 'yan uwanta rabi tad'auki sauran rabin, nan sukayi ta mata godia,
___________
Sultana Bilkisu ce zaune gefen Sultan Ahmad suna hira chan ta nisa tace Daddyn suhail wlh walimar da mukaje ta burgeni da alama makarantar akwai karatu sosai.
murmushi sultan Ahmad yayi yace nima ta burgeni sosai
sultana bilkisu tace ka san wani abu wlh yarinyarnan ta yi min sosai,
sultan murmushi yayi yace ai naga alama saisa kika aika aka kiramiki ita,
sultana bilkisu d'an guntun murmushi tayi tace inama yarima ya amince ya aureta, wlh da naji dad'i domin daga ganinta kasan ta fito daga gidan mutunci wlh inason yarinyar takasance surukata, kallon sultan Ahmad tayi taga yana ta dannar remote yana canza channel, hannu takai taruk'o remote d'in nan yajuyo yakalleta kwallah duk ta cika mata ido.
sultana bilkisu murmushi tayi wanda yafi kuka ciwo tace daddyn suhail nasan sumayya d'iyar d'an uwankace ammah kataimaka ka amince da yarima ya auri zarah domin inaji ita alkhairi ce, ina ji ajikina aurenta zaisa yarima yasamu nutsuwa da kwanciyar hankali.
sultan Ahmad rik'e hannun sultana yayi yace Bilkisu ba wai na k'i bin maganarkibane kawai dai ina tsoron abinda zaije yadawo, kina tunanin suhail zai amince yasota? kina tunanin su memartaba zasu aminta da hakan?
murmushi sultana bilkisu tayi tace insha Allahu zasu amince yarima bamuda matsala da shi domin mu muka haifesa, indai su memartaba sun amince toh komai ya yi daidai, kabani izini inje gidansu yarinyar mugana da iyayenta inyaso daga baya sai muyi tunanin yadda zamu 6ullo ma lamarin.
dogon numfashi sultan Ahmad yaja yace toh tayaya kike tunanin zasu amince batare da ansha wuyaba?
murmushi sultana tayi tace kafara bani izini inje gidansu yarinyar ingana da iyayenta, muji idan zasu amince mana subamu aurenta.
shima sultan murmushi yayi yace nabaki izini Allah dai yashige mana gaba.
cike da jin dad'i sultana tace Ameen.
_*BAYAN SATI 'DAYA*_
Sultana Bilkisu ce naga tayi shiga ta alfarma ta yi kyau sosai bayanta kuyangi biyar ne suka take mata baya, wajen wata dank'areriyar mota daga cikin jerin motocin ukku da take tsakiya naga ta nufa tunkan ta isa aka bud'e mata baya, dan haka tana shiga aka maida aka rufe.
kuyanginta d'ayar motar suka shiga nan aka tada motar, dasauri maigadi yahangame musu k'aton gate d'in suka fita daga Amir palace.
bayan 'yan mintina suka isa islamiyyarsu zarah,
a mota sultana bilkisu tazauna tatura dogari yaje yayi mata magana da shugaban makarantar.
bayan kamar minti ukku sai ga dogarin ya fito bayansa shugaban makarantane yana ta zuba sauri.
duk'awa yayi yana gaishe da sultana bilkisu cike da fara'a ta amsa, nan kuyangi da dogarawa suka d'auka sultana ta amsa gaisuwarka kaima angaisheka,
sannan sultana tace inason k'arin bayani akan d'alibarku mai suna zarah musa.
dasauri d'aya daga cikin dogarawan yace sultana tanason sanin wacece ita, ina ne gidansu.
shugaban makaranta washe baki yayi yace toh toh zarah musa ai gidansu yana chan gaba da nan kad'an.
sultana bilkisu signal tayi ma driver da ido.
driver yace yimin kwatancen gidan yadda zan gane, nan shugaba yayi masa kwatance saida yafahimta sannan yaduk'a yace angama ranki yadad'e
sultana bilkisu kallon kuyanga tayi tace tamik'o mata jakkarta, dasauri kuyanga tamik'o mata nan sultana tad'auko bandir d'in 'yan 1k tamik'a masa tace ga wannan kun k'ara wajen hidima.
jikin shugaba yana kyarma ya amsa tare da duk'awa yana godia nan suma dogarawa suka hau yi ma sultana godia.
sultana izini tabada aka tayar da motar suka kama hanyar gidansu zarah.
ko da suka isa driver tsayawa yayi yatambayi wasu matasa da suke zaune a majalisa, basusha wahalar gane wadda yake nufiba kasancewar kusan kullum zarah ta gabansu take wucewa taje islamiyya kuma tadawo, sukace yak'ara gaba kad'an yashiga hannunsa na dama gida na ukku, nan yayi musu godia sannan sukacigaba da tafiya.
A k'ofar gidansu zarah yayi parking, daidai lokacin malam musa ya dawo gida, ganin dank'areriyar mota k'ofar gidansa yasa mamaki yacikasa dasauri ya ida isowa, daidai lokacin driver yafito daga motar, malam musa sallama yayi mashi yace wani gida kuke nemane?
driver yace eh gidan su wata zarah musa.
malam musa yace toh toh ai nan ne nine mahaifinta.
driver zuwa yayi daga bayan mota yayi knocking d'in glass d'in, jin knocking yasa sultana bilkisu tawane glass d'in.
driver duk'awa yayi yace ranki yadad'e nan ne ga ma mahaifinta nan.
sultana bilkisu kallon mahaifin zarah tayi dasauri shima yaduk'a yagaisheta domin yanayinta kawai da yagani da dogarawan da suke tare da ita yasa yagane daga babban gida take.
sultana bilkisu cike da fara'a ta amsa.
malam musa yace ranki yadad'e ko dai wata zarah d'in ce kuke nema?
murmushi sultana tayi tace zarah dai taka, munaso kayi mana izini mushiga ciki sai mutattauna abinda yake tafe da ni.
malam musa jikinsa yana 6ari yace bismillah kushigo,
dasauri dogarawa sukazo suka bud'e mata murfin motar tafito nan kuyangi suka take mata baya, akabar dogarawa tsaye wajen motocinsu,
malam musa yana gaba har cikin gida, suna shiga yafara k'walama mama kira yana zainabu! zainabu!!
dasauri mama tafito daga d'aki tana malam lafiya? ganinsa tare da wasu mata yasa tayi tsaye tana malam bak'i mukayi?
malam musa yace kinyi wani tsaye kiyi sauri kid'auko musu tabarma mana, ina yarannan suke? .
mama tace basunan sunje gidan kitso sannan takoma d'aki tad'auko sabuwar tabarma tazo ta shimfid'a tace bismillanku.
sultana zuwa tayi zata zauna dasauri kuyanginta suka k'ara kakkafe tabarmar suna cewa ranki yadad'e azauna lafiya sarauniya, bayan ta zauna nan kuyanginta sukayi tsaye gefenta.
ganin haka yasa su mama suka ida fahimtar koma daga ina wannan tafito toh motar wani babbace, Dan haka mama tazo taduk'a tagaisheta.
fuskar sultana d'auke da murmushi ta amsa, nan kuyangi suka d'auka 'sultana ta amsa gaisuwarki kema angaisheki'
malam musa jikinsa yana 6ari yace bari inje insamo musu ruwa susha.
sultana murmushi tayi tace kabarsa nagode kazauna kawai muyi magana akan abinda yakawoni.
dasauri mama taje tad'auko wata tabarmar tashimfid'a ita da malam musa suka zauna.
sultana kallon kuyanginta tayi tace mero kubamu waje zamuyi magana.
dasauri duk suka zube sukace angaisheki sultana atashi lafiya sannan suka tashi suka bar wajen.
sultana kallonta tamaida ga su malam musa tace kune iyayen zarah ko?
malam musa da mama sukace eh ranki yadad'e .
sultana bilkisu tace toh Alhmdllh ni matace ga d'an sarkin garin nan, agaskiya ba zan 6oye mukuba tun lokacin da mukaga d'iyarku wajen walimarsu da sukayi a islamiyya nan muka ganta kuma mun yaba da halinta da tarbiyarta dan haka muke neman ma d'anmu *yarima suhail* aurenta.
ba mamaba hatta shi kansa malam musa ya firgita a tsorace suka d'ago kai suka kalli juna jin an anbaci yarima suhail Wanda suke jin sunansa a bakin mutane, dasauri suka maida kallonsu ga sultana bilkisu,
atare suka had'a baki sukace zarah ta auri yarima suhail?
sultana gyad'a kai tayi tace indai kun amince zaku bamu aurenta.
shuru sukayi na d'an lokaci sannan malam musa yace ranki yadad'e kiyi hak'uri gaskiya ba zamu iya amincema buk'atarkiba.......
_*Comments d'inku shine k'warin gwiwana Indai babu more comments toh hakan zai tabbatar min da baku tare da ni dan haka nima zan dakata da rubutawa daga wannan page d'in, dan haka muje zuwa*_
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_*Jinjina agareki My Dala inaso kisani akoda yaushe ina ji dake😘*_
_Sak'on gaisuwa agareka *Mu'az* a duk inda ka kasance wannan *page* d'in mallakinkane kayi yadda kakeso da shi nagode sosai da kulawa_
page 1⃣5⃣
Malam musa yace gaskiya ba zamu iya amincewa da buk'atarkiba domin kunfi k'arfinmu ku masu kud'ine mu kuma talakkawane, kinga ba zaiyuwuba ace masu sarauta kamarku sun had'a zuri'a da muba.
sultana bilkisu tace kar kudamu ai anzama d'aya kar kumance da talakka da maikud'i duk Allah ne ya haliccesu kuma shi yakeba Wanda yaso yahana wanda yaso, jahiline kawai zai iya gudun talakka, ammah duk wanda yasan abinda yakeyi toh ba zai gujesaba domin yasan wake azurtawa da hanawa, a lokaci guda Allah zai iya maida talakka mawadaci sannan yamaida mawadaci talakka, toh tayaya kuke tunanin zamu gujeku? saidai idan kuna tunanin d'iyarkune kar mucutar da itane, insha Allahu ba zamu nuna banbanciba zamu kula da ita kamar yadda zamu kula da 'ya'yanmu da muka haifa a cikinmu, burina kutaimaka ku amince kubamu auren zarah.
mu musulmaine munsan girman alk'awali dan haka nayi muku alk'awali zamu kula da ita bakin gwalgwado.
gaba d'ayansu shuru sukayi suna saurarenta, yanayin yadda sultana tayi maganar yasa suka yadda da ita, kuma sunsan adalci da kirki irin na sarkin garin indai shi zuri'arsa suka biyo mutunci toh ba zasu samu matsalaba.
chan Abbah yakalli mama yace tataso suje suyi shawara dan haka mama tatashi suka shiga d'aki suka bar sultana zaune wajen tana dannar waya,
a chan d'akin abbah yakalli mama yace zainabu abun nan yad'aure min kai kina ganin zai yuwu mubasu d'iyarmu? nifa ina tsoron su wulak'anta mana ita domin su masu arzikine mukuma talakkawa.
mama jinjina kai tayi tace nima abinda nake tunani kenan gaskiya kar mubasu domin bamusan yadda gaba zata kasanceba, ace duk matan garin nan surasa wadda zasuce sai zarah, so suke sujamana zagi da surutun mutanen gari.
malam musa jinjina kai yayi yace ni bama dai wannan ba kiduba kiga bayanin da tayi mana tabbas daga gani tasan daraja da mutuncin mutane daga jin kalamanta, ta ni bandamu da surutan mutaneba saidai inajin tsoron su wulak'antamin zarah domin yarima suhail ya wuce ajin zarah wajen komai, ammah kuma ina jin nauyinta bana iya hanasu zarah.
ummah tace hakane malam ko dan matsayin da darajar da ke garesu kaduba kaga bata nuna mana k'yamaba nima wlh ta wajena babu matsala domin halayyarta ta yi min kuma nasan indai d'antane takeson hadawa da zarah toh bamuda matsala saboda da alama zai kasance mai irin kyawawan halinsu saidai ba a nan takeba matsalar tana wajen zarah.
malam musa jinjina kai yayi yace tabbas zarah itace matsalar ina tsoron taki amincewa saidai nasan zarah akwai biyayya zata iya bin ra'ayinmu ko da ace bataso, dan haka idan kinga hakan ba matsala toh muje mu amsa mata,
mama tace toh nan tabi bayan malam musa suka fito, yadda sukabar sultana haka suka dawo suka taddata, suka koma mazauninsu suka zauna.
kallonsu sultana tayi tace dafatan kun yanke hukuncin da kuke ganin ya dace wlh Indai baku aminceba zamu iya hak'ura domin ta yuwu zarah ba matarsa bace.
malam musa yace ranki yadad'e mun ma amince domin darajarki da martabanku yasa bama iya ji zamu iya hanaku zarah fatanmu dai zaku rik'eta kukular mana da ita tsakani ga Allah.
sultana bilkisu tunda taji ya ambaci sun amince wani irin farinciki yakamata kasa 6oye murnarta tayi tace gaskiya naji dad'i kuma nagode sosai insha Allahu zamu kular muku da ita, sannan zanje muyi magana da iyayensa koma dai mekenan zamuyi waya, takalli mama tace bani number d'in wayanki nan mama takaranto mata sannan sultana bilkisu takira kuyanginta suka dawo, fuskarta d'auke da fara'a tace naso ace naga d'iyartawa ammah tunda batanan zamu had'u wani lokacin.
mama tace a'a ranki yadad'e ai sai inje inkirata tana chan bayan layin nan sunje kitso, sultana tace a'a kibarta kawai zamu gaisa wani lokacin, kar6ar jakkarta tayi a wajen d'aya daga cikin kuyanginta tazaro 100k ta aje musu sannan tamik'e tace bari inwuce.
Abbah yace a'a kibar kud'inki mu dan Allah mukayi.
sultana murmushi tayi tace karkadamu nima dan Allah nayi domin babu kud'in da zasu iya sayan zarah, kuyi hak'uri kyautace.
Abbah da mama sukayi godia, har wajen mota suka rakata saida sukaga tafiyarta sannan suka dawo cike da farin ciki.
Mama kallon Abbah tayi tace malam toh yanzu ya kake ganin za'ayi idan zarah tadawo? kana tunanin zata amince?
Abbah murmushi yayi yace kar kidamu kibar komai a hannuna.
mama tace toh Allah yashige mana gaba.
Abbah yace Ameen.
daidai lokacin su zarah suka shigo gidan suna dariya, mama da Abbah kallon juna sukayi sannan suka maida kallonsu ga 'ya'yan nasu suna murmushi, su zarah isowa sukayi tare da duk'awa sukayi ma iyayennasu barka da rana, mama tace 'yan albarka har kunyo kitson?
sukace eh mama, gaba d'ayansu suka mik'e zasubar wajen, abbah yace kudawo kuzauna munason magana da ku.
A tare suka zauna suna jiran Jin abinda iyayennasu zasu ce, Abbah ne yayi gyaran murya yace duk inda kuka tsinci kanku kukasance masu dogaro ga Allah, kurik'e gaskiya sannan duk mijin da Allah yaza6a muku kukar6esa hannu biyu domin ita rayuwa ta yuwu abinda mukeso ba alkhairi bane wanda bamuso zai iya kasancewa shine mafi alkhairi, gaba d'ayansu shuru sukayi suna sauraren mahaifin nasu da suka kasa gane dalilinsa nayi musu wannan nasihar,
mamace tacigaba da cewa ku 'ya'ya matane ba zaku dauwama a k'ark'ashinmu ba wata rana dole kubarmu kukoma k'ark'ashin mijinku a kullum addu'anmu Allah yahad'aku da mazaje nagari kuyi aure.
Abbah yace tabbas zancenki hakane zainabu sannan yamaida kallonsa ga zarah yace saidai kuyi hak'uri domin munyi wani karambani a matsayinmu na iyayenku munyi abinda muke gani kamar daidaine saidai a wajenku bansan yadda zaku d'aukesaba musammanma ke zarah!
gaba d'ayansu mamakine yacikasu sun ma rasa gane inda zancen abbah yanufa, zarah ce ta nisa tace Abbah bana tunanin akwai abinda zakuyimin yazama laifi wlh duk hukuncin da kuka d'auka kaina daidaine domin kun cancanci hakan.
Abbah dogon numfashi yaja yace hakane zarah ammah kiyi hak'uri da maganar da zata fito daga bakina, zarah munyi miki miji.
zarah a razane tad'ago kai takalli abbah muryanta yana kyarma tace abbah miji kuma? Aysha da Rauda sukace miji!!!
Abbah gyad'a kai yayi cikin rashin damuwa yace tabbas miji kuma nasan zaki sosa kema bakowa bane face d'an sarkin garinnan *Yarima Suhail*
zarah a tsorace tamik'e tsaye tare da ja baya tace abbah aura min wani zakayi ba malam bello ba?
Abbah yace zarah kidawo kuzauna inyi muku bayanin komai,
zarah hawaye tafara tare da dawowa tazauna, nan abbah da mama suka kwashe labarin zuwan sultana bilkisu da yadda sukayi da ita babu abinda suka 6oye masu hatta kud'in da tabasu.
Zarah fashewa tayi da kuka tace Abbah kuyi hak'uri wlh bana sonsa shima nasan ba zai soniba dan Allah kubarni in auri wanda nakeso wlh malam bello shine za6ina.
Aysha da Rauda murmushi sukayi suna jin wani irin dad'i a ransu.
mama ce tace haba zarah ya kamata kid'auki k'addara muma ba a son ranmu hakan takasanceba dan dai babu yadda zamuyine kinga ba zamuk'i amincemataba tunda har tazo gida tanemi alfarmarmu.
Zarah mik'ewa tayi tsaye tana kallon iyayen nata tana girgiza kai, cikin kuka tace kawai dai kuce kun siyar da ni, yanzu kud'i zasusa kubayar da ni? bakwa tsoron suwulak'antani? wlh bana sonsa kuma ba zan ta6a sonsaba inma dan kud'insu yasa kukayi min haka toh wlh saidai kumaida musu kud'insu domin ban aminceba, ni malam bello zan aura.
Yaya Rauda tace zarah wai minene haka kikeyi?
zarah cikin d'aga murya tace kubarni yaya rauda ba zan ta6a amincewa ba.
Aysha tace yaya zarah su abbah fa kike d'aga ma murya.
Zarah dasauri tatoshe bakinta da hannuwanta tana girgiza kai tace kugafarce ba zan iyaba, tana gama fad'in haka tashek'a da gudu tashige d'aki tafad'a saman katifarsu tana wani irin kuka saikace wadda aka aikoma da sak'on mutuwa.
gaba d'ayansu jikinsu yayi sanyi musammanma su Abbah da mama da basu d'auka abun zaiyi zafi hakaba.
Rauda ce takalli iyayennasu tace Abbah kuyi hak'uri 6acin rai ne yasa zarah tayi haka ammah ai tana da sanyi natabbata zata sauko daga fushin da take.
mama tace kar kudamu nasan halin d'iyata ni zan shawo kanta da kaina.
Abbah dai girgiza kai yayi takaici duk ya cikasa
Aysha ce tace Abbah kayi hak'uri zata safko yanzu tad'auki zafine saisa, ammah fa naji dad'i da zata auri yarima wlh ya had'u sai ma da nagansa a wajen safkarsu.
Rauda tace wlh kau ni har nahango sunyi match sosai, cike da murya Aysha tace yayata zata zama *Gimbiya Zarah* matar *Yarima Suhail* dak'uwa mama tayi mata tace gidanku munaso murarrasheta tasafko sai kinja ta jiyoki.
Aysha cike da farin ciki tarik'e bakinta da hannu tace afwan na daina.
mama kallon Abbah tayi tace malam kar kadamu insha Allahu Zarah zata safko ni zanma je na lallasheta har tafahimcemu.
malam murmushi yayi yace toh Allah yasa tafahimta inma dai bata aminceba zan fasa basu domin ba zanyi mata doleba, duk yadda kukayi da ita sai kufad'amin yanzu dai bari intashi infita koma mekenan sai nadawo
gaba d'ayansu sukace adawo lafiya.
bayan Abbah ya fita Rauda kallon mama tayi tayamutsa fuska tace mama yau naman kaza nakeson ci, murmushi mama tayi tace Rauda kin cika kwad'ayi tashi ga 1,500k kuje wajen dauda mai kaji yayanka yafige sai kuzo kuyi mana pepper kowa yaci.
Rauda cike da jin dad'i tace toh mama yanzu ko zamuje muna godia.
Aysha ma cikin murna tace Allah yabarmana ke maman gimbiya.
Mama duka takaima Aysha tagoce suna dariya ita da rauda, mama tace sai naci gidanku inbakuyi wasaba.
mik'ewa mama tayi tace kuyi sauri kuje kudawo ni bari inshiga wajen d'iyata in rarrasheta.
mama ko da tashiga lokacin zarah ta ci kukanta, kwance take kanta yana kallon ceiling d'in d'akin hawaye kawai suke zuba ta gefen idonta, mama gefen inda zarah take kwance tazauna tana mai k'arema zarah kallo da duk idanuwanta sun kumbura.
A hankali mama tace zarah kuka kikeyi ko? shuru zarah tayi batace komaiba, mama cigaba tayi da cewa kiyi hak'uri zarah wlh muma ba'a son ranmu hakan takasanceba dan dai babu yadda zamuyi mubijire ma buk'atarta domin yadda tazo ta aje girma da matsayinta tana rok'onmu mu amince mata muba d'ansu aurenki, hmm zarah munsan zakiyi tunanin ko k'wad'ayine yasa mukayi miki haka ammah wlh ba haka bane *k'addara ce* kawai, domin kowane iyaye suna burin ganin farin cikin 'ya'yansu koya suke suna son ganin farin cikin yaransu ko da ace zai tauye nasu farin cikin, canzawar yanayinki yasa abbanki ya ji ba dad'i domin har ya fara tunanin yaje da kansa yafad'a musu ya fasa badake, domin kowane iyaye suna burin ganin 'ya'yansu sun auri mijin da yacancanta mutumin da zai kular masu da 'ya, wanda yake sonta kuma danginsa suma suna sonta.
zarah lumshe idanuwanta tayi hawaye suna zuba tana jin wani iri a ranta, mama cigaba tayi da cewa saidai mu kuskuren da mukayi a baya har yanzu akwai sauran tabonsa bai warkeba a zuciyan zarah, zarah har yanzu kallonmu take a matsayin kwad'ayayyun iyaye, idan barinki ki auri wanda kikeso zaisa kigane cewa ba dukiyarsu muke k'wad'ayiba toh mun amince kije ki auri bello domin shima mutumin kirkine saboda farin cikinki shine namu fatanmu kigane cewa tuni iyayenki sunbar wacchan rayuwar da sukayi a baya, ko da ace za'a kallemu a matsayin k'ananun mutane masu magana biyu toh bazamu damuba saboda munfi buk'atar naku farin cikin.
zarah dasauri tatashi tarungume mama tare da fashewa da sabon kuka tace mama kuyafemin wlh ba haka nake nufiba, na amince da za6inku bana fatan ayi ma iyayena kallon marassa cika alk'awali koda ace zan mutu toh nagwammace inmutu ta dalilin faranta ma iyayena rai, tabbas nasan bazaku ta6a yimin za6in da zai cutar da ni ba wlh na hak'ura da malam bello wanda kuka za6amin shine zan aura, tana kaiwa nan tasake fashewa da kuka tace mama kuyafemin.
mama ma hawaye takeyi cike da tausayin d'iyartasu tace zarah bakiyi mana komai ba saima mu da mukayi miki.
zarah girgiza kai tayi tace mama kidaina cewa haka duk abinda kuka yanke akaina daidaine kuma cancanta da matsayine sukaja hakan.
mama rungume d'iyarta tayi tana hawaye tausayin zarah duk ya kamata, lallashin zarah tashiga yi har saida taga tayi shuru.
zarah mik'ewa tayi tace bari inje inba baba hak'uri nasan fushi yake da ni, mama tace ai baya nan ya fita.
zarah komawa tayi tazauna tace toh idan ya dawo zan je.
Mama murmushi tayi tace Allah yayi miki albarka zarah wlh kin cika d'iyar kirki, Allah yayi muku albarka gaba d'ayanku.
Zarah murmushi tayi tace Ameen mama.
Mama mik'ewa tayi tace bari inje nasan yanzu su Rauda zasu dawo
zarah batace komai ba, tana ganin mama ta fita yasa tatashi tashige toilet tare maida k'ofa tarufe anan tafashe da sabon kuka mai tsuma zuciya duk tausayin kanta da na malam bello yakamata domin tasan so d'ayane yakeyi mata batasan yadda zai fahimci maganarba idan taje masa da ita, saida taci kuka mai isarta sannan tawanke fuskarta tare da tad'auro alwallar magrib tashinfid'a darduma tad'auko alk'ur'ani tana karantawa domin samun sauk'in abinda takeji a ranta.
Bayan sallar isha'i zarah zaune tayi a d'akinsu har lokacin fuskarta babu walwala duk yadda su Rauda sukaso tasaki jiki ammah ta k'i, abincima dakyar tad'anci kad'an.
wajen k'arfe takwas tanajin dawowar Abbah saida tadaidaici daidai lokacin da yagama cin abinci sannan tataso tanufi d'akinsa jikinta a sanyaye tayi sallama.
Abbah da yake zaune hannunsa rik'e da redio yana sauraren labarai amsa mata sallamar yayi tare da rage k'arar redion.
Zarah shigowa tayi taduk'a k'asa muryarta tana rawa tace Abbah dan Allah kayafe min abinda nayi maka wlh na amince zan auri za6inku domin nasan ba zaku ta6a cutar da rayuwataba duk hukuncin da zaku zartas akanmu daidai ne burinku a koda yaushe kuga farin cikinmu, wlh akoda yaushe ashirye nake da incika umurninku domin 6acin ranku daidai yake da rugujewar farin cikina.
Abbah murmushi yayi cike da jin dad'in maganar zarah yace wlh zarah bakiyimin komai ba, indai baki sonsa kifad'a min wlh bazanyi miki doleba zan aura miki wanda kikeso domin farin cikinki nafi buk'ata.
zarah girgiza kai tayi tace Abbah wlh wanda kaza6amin shi nakeso ashirye nake a koda yaushe in amshi za6inka.
Abbah kasa 6oye farin cikinsa yayi yace nagode sosai zarah Allah yayi miki albarka kema Allah yabaki wad'anda zasuso farin cikinki, insha Allahu wannan auren zakiji dad'insa, Allah yayi muku Albarka gaba d'ayanku, zarah cike da jin dad'in addu'an da abbah yayi musu tace Ameen Abbana nagode sosai.
Zarah tunda takwanta kasa bacci tayi juyi kawai take abin duniya duk ya isheta tana tunanin yadda za'ayi ta auri wanda bata so, tunowa tayi da yarima suhail lokacin da yazo walimarsu yadda yake shan k'amshi, ba ya ma kallon kowa, tsaki taja tace wannan d'an jin kan zan aura, hawaye ne suka zubo mata tunawa da tayi da malam bello ta yaya zata fuskancesa da maganar zata auri wani ba shiba batasan yadda zai fahimci maganarba, tana ta sak'e-sak'e a ranta a haka bacci yayi awon gaba da ita batare da tashirya yinsaba........
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
?👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Yau page d'in nakune k'annena nakaina *JANAF nd SAFIYYA ALIYU* inaso kusani ina sonku irin totally d'innan Allah yabarmu tare😘_
Page 1⃣6⃣
Sultana Bilkisu ko da takoma gida cike da farin ciki tasamu Sultan Ahmad take bayyana masa yadda sukayi da iyayen zarah, shima farin cikinsa yanuna a fili yace gaskiya naji dad'i ammah kuma ba'a nan takeba,
murmushi sultana tayi tace nasan kana tunanin matsalar da zamu fuskantane wajensu memartaba da yarima?
Sultan Ahmad shima murmushi yayi yace tabbas hakane ammah Insha Alkahu komai zaizo da sauk'i kibani lokaci nima inyi tunanin yadda zamu 6ulloma lamarin domin maganar nan tana buk'atar tunani mai zurfi a cikinta.
Sultana Bilkisu Cike da damuwa tajinjina kai tace hakane nima zanje inyi tunani domin musamo mafita.
Sultan Ahmad tausayin matarsa yakamasa domin yasan yadda take son d'an nata, yace kidaina damuwa indai Allah ya k'addara akwai aure tsakaninsu toh za'ayi inkuma babu toh hak'uri zamuyi domin wani baya auren matar wani fatanmu dai Allah yashige mana gaba.
Sultana Bilkisu cike da gamsuwa da maganar mijin nata tace Ameen.
Gimbiya sumayya duk yadda taso tadaure kar tabada kanta ga yarima ammah kasawa tayi a daddafe tayi kwana biyu.
bayan sallar la'asar shiryawa tayi sosai tafito tanufi 6angaren yarima tana shirin shiga sai gashi ya fito da alamu fita zaiyi, kallo d'aya yayi mata yad'auke kai yana shirin ra6awa ta gefenta yawuce dasauri Gimbiya Sumayya tasha gabansa tace haba yarima wajenka fa nazo.
fuskar yarima babu alamun fara'a yace me zanyi miki?
Gimbiya kallonta takai ga dogarawansa da guards d'insa da duk kansu yake sunkuye suna jiran ogan nasu, ga kuyanginta da suke bayanta tsaye, kallonta tamaida ga yarima tace am daman, nan tafara kame-kame tace ko dai zamu shiga...... Yarima hannu yad'aga mata yace whatever ma dai you should meet me later, bai jira jin abinda zataceba yawuce dogarawan da guards d'insa suka take masa baya.
Gimbiya sumayya takaici duk yacikata ganin yadda yarima yadisgata gaban guards d'insa hararar kuyanginta tayi da kansu yake sadde a k'asa tacemunafukai kun zuba min na mujiya duk sai nad'au mataki a kanku.
dasauri duk suka zube k'asa suna cewa Allah yahuci zuciyar gimbiya, Allah yaja da ran gimbiya.
wucewa tayi fuu dasauri suka tashi suka take mata baya sunayi mata kirari.
ko da takoma part d'inta saman gadonta tafad'a tare da dafe kanta tsaki taja tace wannan mutumin bansan irinsaba anya yarima bai fara bin mataba? ya za'ayi yad'auki tsawon wannan lokacin batare da maceba? gabantane yashiga fad'uwa cikin d'aga murya tace No! i dont think yarimana akwai macen da zai iya kulawa wlh ba halinsa bane, chan takaima katifa bugu da hannunta tace inma akwai zan bincika domin nasan yarima baya iya kai tsawon wannan lokacin without ya yi making sex da niba ko da ace bana so, inma har naga akwai wadda yake tare da ita toh wlh ba zan bartaba sai na kasheta!!!
wayarta tajawo takira zinat bugu biyu tad'auka, muryar sumayya tana rawa tace wai ke zinat yaushe zaki dawo k'asarnan?
dariya zinat tayi tace kinyi missing d'ina ko?
tsaki sumayya tayi tace ke ni tambayarki nake.
zinat murmushi tayi tace Allah yahuci ran gimbiyar yarima very soon zan dawo nima ai nayi missing d'in k'asata.
Sumayya tace hmm Allah yasa dagaske kike, nidai in kindawo kifara biyowa ta wajena.
'yar dariya zinat tayi tace sai kin ganni, sumayya dai badan ta yadda da maganar zinat ba takashe wayanta tare da komawa takwanta tana sak'e-sak'e cikin ranta.
Da daddare ganin ta kasa bacci yasa tamik'e tajawo alk'yabbarta tad'aura saman kayan baccinta tafito batare da ta nemi rakiyar kowaba tanufi 6angaren yarima addu'a take Allah yasa kar yadisgata domin ita tasan yau duk wulak'ancin da zaiyi mata ba zata damuba Indai zai biya mata buk'atarta inyaso daga baya sai tarama.
lokacin da tashiga ganin yarima baya parlour yasa direct tanufi bedroom d'insa, tsakiyan gadon tahangosa kwance idanuwansa a lumshe, cikin ranta tace lallai ma bacci yake
ahankali tataka tanufi gadon tahau takwanta a saman jikin yarima, muryarsa taji yace me kike buk'ata?
dasauri tad'ago kai takalli fuskarsa har a lokacin idanuwansa a lumshe suke ita tayi azan bacci yake, komawa tayi takwanta tace zuwa nayi intayaka bacci.
yarima dakyar yabud'e idonsa yasafkesu akan fuskarta yace sumayya kitafi kawai daman ai bake ketayani baccin ba saidai idan akwai abinda kike buk'ata.
Sumayya tallabo fuskar yarima tayi tace dear ni bacci kawai nazo muyi.
yarima janyeta yayi daga jikinsa yace ohk muyi baccin.
takaici yakama sumayya ganin yadda yake faujewa kamar bai fahimci abinda take nufiba, komawa tayi jikinsa tace wai yarima meyasa kakemin haka?
yarima kallonta yayi yace me nayi miki?
Shagwa6e fuska tayi tace naga yanzu kamar ka daina buk'atata, ka ma fita harkata, baka kula da ni bakasan yadda nake kwana nake tashiba baka tsoron hak'in aure?
yarima wata muguwar harara yawurga mata yace sumayya ashe kinsan hak'in aure? murmushin takaici yayi yace ammah ni kike tauyemin hak'ina.
sumayya haushine yakamata ganin yadda yarima yake neman wulak'antata cikin ranta tace kayi kagama ba zan damuba tunda ni nakawo kaina.
shafa sajensa tayi tace sweetheart yanzu dai shikenan na amshi laifina, yanzu kafad'i abinda kakeso zanyi maka.
yarima shuru yayi yakyaleta, marairaicewa sumayya tayi tace kayi magana mana.
Yarima murmushi yayi yace da zaki taimaka kibarni inyi bacci da nafi buk'atar hakan.
haushine yakama sumayya domin bata d'auka haka zaice mataba, ganin yadda tayi kicinkicin da fuska abun yaso yabashi dariya ammah yadake yace ya dai?
Sumayya d'auke kai tayi daga kallonsa tace suhail yanzu naga kamar ka daina buk'atata ko kasamu watane?
murmushi yarima yayi domin ya gano inda gimbiya tanufa yace Sumayya akanme zanta bibiyarki aini yanzu jikinki bai dameniba please kikyaleni ina buk'atar hutawa yanzu kinsan bana son yawan magana.
Sumayya fashewa tayi da kuka tace Suhail kaji tsoron Allah hak'ina fa? idan kai baka buk'atata nifa?
yarima d'aure fuska yayi yace ai banga alamun kina buk'ataba ni hak'ina nawa kika tauye?
gimbiya cikin kuka tace toh wlh ba zan yaddaba nidai nace kayi hak'uri.
Yarima cike da rashin damuwa yace shikenan naji zan taimaka miki, idan kin shirya toh bismillah.
Sumayya dai haka tabiyema yarima wulak'anci iri-iri yayi mata ammah lalla6asa tayi itadai burinta ya yabiya mata buk'atarta.
bayan komai ya lafa yarima tashi yayi yaje yayi wanka yazo yakwanta Sumayya mirginawa tayi jikinsa zata kwanta dasauri yarima yatureta yace kar kisaki kira6eni batare da kin tsarkake jikinkiba.
takaici yakama sumayya takoma gefe takwanta domin ita batayi shirin wanka yanzuba sai da asuba, cikin ranta tace yanzu ko zan fara rama wulak'ancin da kayi min.
da asuba saida yayo alwallah sannan yatadata dakyar tatashi saida yaga ta mik'e sannan yawuce masallaci.
tun daga ranar da sumayya taga tasamu biyan buk'atarta sai tadaina zuwa wajen yarima shi abunma dariya yake basa ganin sai tana buk'atar wani abu take zuwa wajensa, yarima bai wani damuba yace shi hakan ya fiyemasa da tazo tadameshi da surutu da haukanta.
*BAYAN KWANA BIYU*
yarima suhail ne a gidan gona tare da shaheed cikin wani k'ayataccen lambu, suna zaune bisa wani lallausan carpet da aka shimfid'a musu suna shan iska, daga chan nesa da su kad'an k'osassun guards d'insane tsaye, hannun yarima suhail rik'e yake da cup mai d'auke da ruwan inibi ammah ba sha yakeba, shaheed da yake zaune yana cin tufa kallonsa yakai ga wata 'yar tsuntsuwa da tad'auke hankalin yarima.
murmushi shaheed yayi cike da zaulaya yace ranka yadad'e tsuntsuwannan ta burgekane asa guards d'inka sukamo maka ita?
yarima suhail shima murmushi yayi tare da kai cup d'in bakinsa yad'an sha ruwan inibin batare da ya kalli shaheed ba yace kawai ina kallonta ne ammah...
shaheed jira yayi yaji abinda yarima zai ce ammah yayi shuru, ganin haka yasa yace ammah ta burgeka ko?
yarima suhail aje cup d'in hannunsa yayi tare da juyowa yad'an kalli shaheed sannan yamaida kallonsa ga tsuntsuwar yace eh kusan haka.
shaheed ma kallonsa yamaida ga tsuntsuwar yana shirin yin magana nan wayan yarima suhail tafara ringing dasauri d'aya daga cikin guards d'insa yazo yad'auko tare da russunawa yamik'a masa.
Suhail kar6a yayi ganin Daddynsane yasa cikin sauri yayi picking tare da yin sallama.
daga chan 6angaren daddy amsa masa yayi tare da tambayarsa yana ina?
yarima cike da ladabi yace daddy ina gidan gona.
daddy yace toh kazo gida kasameni domin akwai maganar da nakeso muyi me muhimmanci.
Suhail baikawo komai a ransaba yace toh daddy ganinan zuwa.
bayan ya gama waya da daddy kallon shaheed yayi yace muje gida daddy nason ganina.
ko da yadawo direct turakar iyayensa yaje a parlour yasamu daddy da ummi zaune da alama jiransa suke, dasallama yashigo tare da samun waje k'asa gefen daddy yazauna nan yak'ara gaishe da iyayen nasa suka amsa masa.
daddy ne yayi gyaran murya yace suhail wani taimako ne mukeso kayi mana ammah bamu san ko zaka iyaba.
yarima suhail d'ago kansa yayi yakalli daddy yace daddy kunfi kar6in haka a wajena ni mai cika umurninku ne.
daddy jinjina kai yayi yace nasan haka, sannan yace suhail aure mukeson muk'ara maka.
A firgice yarima suhail yad'ago kai yakalli iyayen nasa yace aure kuma daddy? Ina fa da aure.
ummi tace munsan haka wannan ma za6inmu ce mukeso ka aura, halinta da tarbiyarta sunyi mana, sumayya 'yar uwarkace kasan muna sonta, kawai alkhairine muka hango a tattare da k'arin aurenka, wannan alfarma ce muka nema a wajenka.
yarima suhail cike da tashin hankali yace kugafarce ni ummi ba wai nak'i bane kuduba kuga sumayya had'ani akayi da ita ba za6ina bace za6in memartaba ce, kuma a yanzu kuna neman kuhad'ani da wata, indai auren kukeso inyi toh na amince zanyi ammah kubari insamo za6in zuciyata.
Sultan Ahmad da ummi kallon juna sukayi sai chan sultan yace yarima ba wai munk'i ta takaba wannan auren za6inmu ne kaima kana da ikon auren za6inka a nan gaba ammah mudai muna buk'atar ka amince ma za6inmu insha Allahu akwai alkhairi a cikinsa.
Yarima shuru yayi na d'an lokaci yana tunani cikin ransa ko haushi yakamasa ammah baya ji zai iyayi ma iyayensa musu sai da yayi kusan minti biyu a haka sannan yad'ago kai yakalli iyayen nasa da suka zuba masa ido suna sauraren jin amsar da zai basu ahankali yabud'e baki yace daddy na amince zan aureta.
ummi da daddy farin ciki yakamasu kasa 6oye murnarsu sukayi sukace gaskiya munji dad'i sosai suhail yadda kafaranta mana kaima Allah yafaranta maka insha Allahu ba zakayi da nasaniba a cikin auren da zakayi.
yarima suhail murmushi kawai yayi batare da yace komai ba domin shi kad'ai yasan abinda yakeji a ransa na bakin ciki.
Daddy ne yanisa yace saidai wani hanzari ba guduba wannan auren bamusan kowa yasan mu muka had'asa munaso kanuna kaine kakeson yin auren, matsalar ma yanzu bamusan yadda yakamata a tunkari su memartaba da maganar ba.
gyad'a kai yarima yayi yace shikenan daddy ni zanje insamesa nasan abinda zance masa.
ummi tace a'a suhail kabari dai musamo mafita domin amincewarsu a lokaci guda kamar zatayi wahala.
d'an guntun murmushi yayi yace kar kidamu ummi kubarmin komai a hannuna.
ummi tace to yaushe zakaje kagano matar taka? na tabbata kaima zaka sota
haushi yak'ara kama yarima jin wai ummi ta ce zaiso wata, girgiza kai yayi yace no ummi ba sai najeba.
nan yayi musu sallama yataso yafito ransa duk a 6ace duk gaisuwar da mutane suke duk'ewa suna k'wasa bai amsama ko mutum d'ayaba yawuce yakoma part d'insu yana shiga 6angarensa guards d'insa yayi ma warning kar subari kowa yashigo ko da kuwa gimbiya sumayya ce.
koda yashiga saman gadonsa yazauna tare da dafe kansa yana jin wani iri a ransa ganin duk an watse masa budget domin kwata-kwata bai shirya k'ara aure yanzuba yafiso sai yasamu macen da yakeso sai ya aureta, tsaki yaja tare da kaima katifa naushi cikin d'aga murya yace wacece wannan wadda iyayena sukeson had'ani da ita me ke gareta da har tarud'esu taja duk wani plan d'ina ya watse tashi yayi yashige toilet tare da sakarma kansa shower.
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Wannan page d'in nakune my *Blood Sis Aufana nd Mummy Sainah Ummun Meenal* hak'ik'a kunfi k'arfin page a wajena, fatana Allah yabarmu tare 'yan uwa nagari😘_
*PAGE* 1⃣7⃣
Bayan ya fito shiryawa yayi sannan yahau saman bed d'insa yakwanta tare da jawo wayoyinsa yakashesu gudun kar adamesa da kira, nan yayi ta tunanin yadda zai 6ulloma lamarin, domin kwata-kwata bayaso yasa dada cikin maganar gudun kar tatarwatsa komai.
kiran sallar magrib ne yafarkar da shi daga tunanin da yakeyi, jiki babu k'wari yaje yad'auro alwallah yaficce masallaci.
Bayan sallar isha'i yarima fada yaje domin yagana da memartaba, lokacin memartaba da wazirine kawai cikinta suna tattaunawa akan wasu kud'i da za'a ware akai gidan marayu da gajiyayyu, yarima gaishesu yayi, nan suka amsa masa cike da sakin fuska da fara'a, sannan yasamu gefe d'aya yazauna yajanyo wayansa yana dannawa yana jiran sugama.
ganin yarima a wannan lokacin ya tabbatar ma da memartaba fa akwai magana dan haka cikin sauri ya sallami waziri.
Bayan waziri ya fita memartaba kallonsa yamaida ga yarima yace suhail na tabbatar akwai magana me muhimmanci da take tafe da kai domin kwata-kwata ban saba ganinka a wannan lokacinba.
yarima murmushi yayi yace ranka yadad'e tabbas hakane akwai maganar da take tafe da ni.
memartaba murmushi yayi yace ina saurarenka ka sanar da ni.
yarima kunyace takamasa yafara kame-kame yace am dama ranka yadad'e..... sai kuma yayi shuru.
memartaba murmushi yayi a karo na biyu yace suhail kayi min bayani mana.
ahankali suhail yad'ago kai yakalli memartaba cike da nutsuwa yace ranka yadad'e kagafarceni daman aure nakeson k'arawa ammah idan ka amince.
memartaba cike da mamaki yace aure kuma suhail? yarima gyad'a kai yayi yace ammah amincewarka nafi buk'ata ranka yadad'e domin ba zan iya zartas da hukunci batare da amincewarkaba.
memartaba shuru yayi nad'an lokaci yana nazari sai kuma chan yace suhail ba zan hanaka raya sunnar ma'aikiba, idan nace zan hanaka aure to natauye maka hak'inka kuma bazanyi jayayya da maganar ubangijiba domin shine yayi umurni da muyi aure, saidai bansan ko kuna samun matsalaba da matarka domin baku ta6a kawo k'arar junaba, inma akwai wata matsakar ba zance dole sai nasantaba domin wannan sirrinkune, ko da aure nufine na ubangiji, yanzu dai katashi katafi gida zanyi shawara in Allah yakaimu gobe zan nemeka.
yarima rissinawa yayi yace Allah yak'ara maka tsawon rai nagode sosai atashi lafiya,
memartaba gyad'a kai kawai yayi, ahankali yarima yamik'e yabar wajen yana sak'e-sak'e cikin ransa yadda za'a kwashe da su dada domin shi k'wata-k'wata baya jin ta gimbiya sumayya dan ashirye yake da yafad'a mata.
ko d's yakoma shirin bacci yayi yakwanta duk yadda yaso yayi baccin ammah ya kasa juyi kawai yake saman gado takaici duk ya cikasa ganin kamarsa ammah ace sai anza6a masa matan da zai aura, takaicinsa ma ba'a ma basa za6in kansa saidai aza6a masa saikace wani k'aramin yaro, tsaki yaja. haka yayita tunane tunane da sak'e-sak'e cikin ransa a zaciyansa sai yaji yana burin ace memartaba bai aminceba, wani irin dad'i yaji nan yasaki murmushi mai sauti ahankali yace Allah ma yasa memartaba yace a'a, ahaka bacci yayi awon gaba da shi.
*WANSHE KARE*
Yarima suhail cikin sauri yagama shirinsa kasancewar yayi late a gurguje yad'anyi breakfast sannan yaficce yanufi wajen aikinsa.
Bayan sallar la'asar zaune yake a parlour d'insa yana kallon wrestling cike da nishad'i kasancewarsa yanason kallon irin boxing da wrestling, wayarsa ce fara neman agaji, tsayar da kallon yayi tare da d'auko wayansa ganin memartaba ne yasa yayi picking dasauri tare da yin sallama.
amsa masa memartaba yayi sannan yace kazo turakata kasameni, cike da ladabi Yarima yace toh ranka yadad'e.
mik'ewa Yarima suhail yayi yaje yad'auko alk'yabbarsa yasaka sannan yafito nan guards d'insa suka take masa baya har turakar memartaba da sallamarsa yashiga.
mamakine yakamasa ganin iyayensa da na sumayya sai dada, cikin ransa yana mamakin dalilin da yasa aka tarasu. a k'asa yazauna tare da gaishesu.
memartaba ne yayi gyaran murya yace toh Alhmdllh nasan zakuyi mamakin tarakun da nayi, toh ba wata babbar magana bace dan kufad'i ra'ayinku domin wannan taron duk akan suhail akayisa saboda yazomin da wani babban zance.
shuru memartaba yayi nad'an lokaci sannan yace suhail yana da burin k'ara yin aure .
gaba d'ayansu suka rikice a firgice dada tace aure kuma? wane irin aure? duka-duka yaushe akayi aurensa da sumayya?
Sultana Sadiya tanaso tayi magana ammah bata iyawa saboda memartaba yana wajen,
wani k'ululun bak'in cikine yatsaya mata harara tashiga wurga ma yarima suhail.
Memartaba murmushi yayi yace dan baidad'e da yin aureba wannan ba matsala bane domin yana da ikon auren sama da mata d'aya kuma baidace atauye masa hak'insaba inda matsalar take shine yasafke ma kowace mace hak'inta da yarataya a wuyansa,
kallonsa yamaida ga sultan Ahmad da Abban sumayya yace toh ku iyayensa kuyi magana ya kuke ganin ya dace.
Abban sumayyane yayi karaf yace ranka ya dad'e abarsa yayi aurensa tunda yana da iko kar a tauye masa hak'insa.
Daddyn suhail yace ammah...... dasauri Abban Sumayya yakatsesa yace yaya dan Allah kar kace wani abu abarsa kawai yayi aurensa Bayan wannan ma yana da ikon k'aro wasu matan biyu.
Sultana bilkisu da Sultana Sadiya sudai basuce komai ba saidai binsu da suke da ido, sultana sadiya haushin mijinta taji ganin za'ayi ma d'iyarsa kishiya ammah bai damuba sai ma turawa da yakeyi.
dada ce cikin 6acin rai tace suhail inbanda abunka miye na gaugawa shi fa aure lokacine, kaduba kaga mutuncin matarka 'yar uwarka.
memartaba murmushi yayi yace dada kubarsa yayi aurensa tunda yana da burin yi.
dada tace ranka ya dad'e gaskiya ni ban aminceba ban yarda yawulak'anta min jikaba daman nasan yanayin zamansu kuma kaduba kaga..... memartaba d'aga mata hannu yayi yace ya isa haka k'ara auren da zaiyi ba shine yake nufin zai wulak'anta sumayya ba kuma na yarda da suhail nasan ko fiye da mata biyu aka basa zai iya kula dasu domin yana da hankali.
dada shuru tayi batace komai ba.
memartaba yace ko akwai me magana acikinku?
gaba d'ayansu sukace a'a ranka ya dad'e.
memartaba kallonsa yamaida ga Yarima suhail da yake zaune k'asa kansa sadde a k'asa yana sauraransu domin shima kansa baiso amincewarnan da akayiba dan dai ba yarda zaiyi ne kuma yanason cika umurnin iyayensa, muryar memartaba ce yaji yace suhail ka fad'ama iyayen yarinyar zamu tura a neman maka aurenta, dafatan dai ka fad'a ma matarka zaka k'ara aure?
Yarima Suhail girgiza kai yayi yace a'a ranka yadad'e bata saniba, memartaba yace toh shikenan kaje kasanar da ita nasan sumayya batada matsala zata amince.
Yarima Suhail yace toh ranka yadad'e.
memartaba yace zaku iya tafiya idan ba mai magana.
gaba d'ayansu duk'awa sukayi suka kwashi gaisuwa sannan suka tashi suka ficce.
Yarima bai koma 6angarensuba motarsa yashiga yaficce yatafi asibiti saboda akwai theater d'in da zai yi ma wasu.
Sultana Sadiya cike da tashin hankali takoma 6angarensu a parlour tayada zango tare da korar duk ma'aikatan da suke ciki nan tafara saffa da marwa tana jiran Sultan Abbas da yatsaya suna magana da Daddyn yarima.
Bayan kamar minti biyar sai gashi ya shigo, da mamaki yatsaya yana kallonta yace lafiya Sadiya naganki haka?
Cike da 6acin rai tace haba Abban sumayya wannan wane irin cin mutuncine yaron nan yakeson yi mana, kaduba kaga duka yaushe akayi bikkinsu dukaba shekara d'aya da rabi kenan ammah wai aure zai k'ara.
Murmushi Sultan Abbas yayi yace toh menene dan zai k'ara aure?
Sultana Sadiya tace kai wai naga kamar baka damuba d'iyarka fa ce za'ayi ma kishiya saikace bakasan ciwontaba?
Murmushin takaici Sultan Abbas yayi yace sadiya nine bansan ciwon Sumayya ba? nine mahaifinta kuma ita da suhail basuda banbanci dukansu 'ya'yanane kuma bari kiji dakaina ma zan iya zuwa inneman masa aurenta dan haka idan zaki sa d'iyarki tanutsu tabi mijinta toh inkuma taje garin haukanta takashe aurenta toh baruwana dan haka shawara tarage taku, yana kaiwa nan yaficce yabarta nan tsaye.
da harara sultana sadiya tarakasa tace ai zamu gani, wayarta tad'auko takira sumayya.
Lokacin Sumayya tana kishingid'e tsakiyar kuyanginta nan aka mik'o mata wayar tayi picking tace ummah ya dai?
ummah cikin fad'a tace ke jakkar inace mijinki yana nan yana shirin k'ara aure.
'yar dariya sumayya tayi tare da mik'ewa tanufi bedroom d'inta tana cewa haba dai yariman nawa? taya zaiyi aure?
Sultana Sadiya ta k'ule sosai cikin tsawa tace ke wace irin bahuwace? ina fad'a miki ammah baki ma damuba.
Sumayya zama tayi saman bed d'inta tace ummah ai nad'auka tsokanata kike.
Sultana Sadiya tace wace irin tsokana yanzu muka zauna da iyayenku akayi maganar har da memartaba kece kawai baki saniba.
Sultana Sumayya a firgice tamik'e tsaye tace ummah yariman nawa zaiyi aure batare da na saniba?
Ummah tace k'warai kuwa sumayya abun bak'in cikinma har da mahaifinki cikin masu goya masa baya.
sumayya k'asa tazauna tare da fashewa da kuka tace ummah yanzu yarima ne zai yaudareni yak'ara aure?
ummah tace ai saisa naso kihaihu ammah kika k'i d'aukar shawarata daman abinda nake guje miki kenan domin nasan halin yaudarar maza saboda basuda tabbas.
Sumayya cikin kuka tace wlh bazan yaddaba babu macen da zata auri yarima duk ma wadda tayi gigin shigowa wlh sai na kasheta domin bazan zauna da kishiyaba.
ummah tace kisa kuma sumayya? kibari mubi komai a hankali nima kinsan ba zan ta6a amincewa ayi miki kishiyaba domin farin cikinki shine nawa.
Sumayya cikin kuka tace kuma dada tasan da maganar? Ummah tace babu fa Wanda bai saniba.
K'ara fashewa tayi da sabon kuka cikin d'aga murya tace wlh k'aryane babu macen da ta isa ta auri mijina wlh ko ma wacece sai na kasheta, tana fad'in haka tayi wurgi da wayarta tare da duk'ewa tana wani irin kuka me tsuma zuciyan mesaurare dasauri tatashi tafito tanufi 6angaren yarima ammah tana shiga taga baya nan.
dan haka tafito tadawo d'akinta tana wani sabon kukan nan tafara watsi da kayan d'akinta dan dressing mirror d'inta batabar komai ba duk ta watsesu k'asa masu fashewa sunayi masu zubewa sunayi sumbatu tafarayi wlh sai nakashe ko wacece ba zan ta6a yadda a auremin mijiba saman gado tafad'a tana me cigaba da risgar kuka,
ma'aikatanta tsaye sukayi daga wajen d'akin sukayi cirko-cirko suna jinta ammah ba mai iya shiga d'akin gudun kar suma 6acin ran yashefesu.....
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_*Wannan page d'in na sadaukar da shi agareku Mamansadiq, Mummyn khadija nd Mrs Dawud ina alfahari da ku a kodayaushe, godia ta agareku bazata ta6a gushewaba wlh ko da page ko ba page nariga na ajeku waje guda acikin zuciyata😘*_
*PAGE* 1⃣8⃣
Jin abun gimbiya ya k'i k'arewa yasa haule tafita dagudu tanufi turakar yarima tana zuwa nan guards suke shaidamata baya nan, juyowar da tayi zata koma taji tsayuwar motar yarima dagudu tafita tanufi inda yake.
yarima yana fitowa daga mota daidai lokacin haule ta iso dasauri tazube gaban yarima yarima kallonta yake cike da mamaki, tace ranka yadad'e kagafarceni daman gimbiyace tana cikin d'aki.
yarima shuru yayi kamar ba zaiyi magana ba sai kuma chan yace me yasameta?
Haule duk'ar da kanta tak'ara yi tace ranka yadad'e gaskiya bamu saniba mun dai jiyota a d'aki kamar tana kuka.
yarima baice komai ba domin yagane dalilin da yasa sumayya yin hakan, wucewa yayi yabar wajen, da har zai shige part d'insa domin baiyi niyar zuwa wajentaba, chan kuma sai yafasa yanufi 6angarenta har a lokacin kuyanginta suna tsaye cirko-cirko anrasa mai iya ta6uka wani abu.
ganin yarima yasa suka zube suna k'wasar gaisuwa sannan suka tashi sumi-sumi suka fita sukabar d'akin.
ahankali yabud'e bedroom d'in yashiga mamakine yakamasa ganin yadda tawatse komai na d'akin, sannan yasafke kallonsa kan sumayya da take raku6e k'asa saikace wadda tayi rashin iyayenta tana ruzgar kuka, jin anshigo yasa tad'ago kai ganin yarima yasa tamik'e dasauri tanufi wajensa tare da rungumesa tana shashek'ar kuka tace yarima kafad'a min cewar abinda naji ana fad'a akanka k'aryane.
yarima da yake tsaye yace sumayya me kikaji akaina?
sumayya d'ago kai tayi takallesa tace aure wai zaka k'ara.
janye idonsa yayi daga kallonta yace hakane aure zanyi.
gimbiya turesa tayi a firgice tare da matsawa tace suhail aure? ni zakayi ma kishiya?
Yarima Suhail murmushin mugunta yayi yace tabbas aure zanyi sumayya domin ke tuni kikayi wasa da damarki.
cikin d'aga murya sumayya tace enough suhail! enough!!! nan tafashe da sabon kuka tace dan Allah kafasa auren nan wlh zan kula da kai.
ta6e baki yarima yayi yace kin rin rasa damarki dan haka k'ara kawai kiyi hak'uri koma wacece tashigo kikar6eta hannu biyu kuyi zaman lafiya.
sumayya cikin k'araji tace ank'i d'in, wlh babu wadda ta isa ta auremin miji domin gidan nan ba za'a ta6a samun zaman lafiya ba.
yarima suhail fuskarsa babu alamun wasa yace kidinga tace maganar da kike a gaban yarima suhail domin kinsan wanene ni bana son raini, sannan indai kinason zaman gidana dole kiso abinda nakeso kuma kuyi zaman lafiya.
gimbiya sumayya a fusace tace Idan ank'i fa?
murmushin mugunta yarima yayi yace igiyar aurenki zata fara rawa, yana kaiwa nan yajuya yaficce yabar sumayya tsaye sake da baki tana binsa da kallon mamaki, yana fita tasake rushewa da kuka tace nashiga ukku yanzu ni suhail zai yaudara?
kamata ace zaiyi ma kishiya har yana ik'irarin sakina.
saida taci kuka me isarta sannan tajawo wayarta da tawullar taga har screen d'in yatsage dan haka tad'auko d'ayar takira zinat har tatsinke ammah zinat bata d'agaba.
A fusace gimbiya tamik'e tad'auko alk'yabbarta tasaka tafito nan duk kuyanginta suka take mata baya duk wanda zai ganta a lokacin yasan tana cikin 6acin rai, tana fitowa bata zarce ko'inaba sai sai turakar iyayenta, a parlour ana ta kwasar gaisuwa bata kalli kowaba ganin ummanta bata parlour yasa tashige bedroom.
lokacin sultana sadiya tana zaune saman bed d'inta tana waya, ganin yadda sumayya tashigo yasa arikice tamik'e tsaye tace sumayya lafiya?
dagudu sumayya tazo tafad'a jikinta tare da fashewa da sabon kuka tace ummah nashiga ukku yanzu ni suhail zaiyi ma kishiya.
Sultana Sadiya rarrashinta tashiga yi tace haba sumayya kiyi hak'uri man kinsan dai tunda memartaba ya amince toh babu wanda ya isa yace a'a dan haka kibarsa kawai yayi auren munga ta yadda amaryar zata zauna lafiya, sai tasan tashiga rayuwarki dakanta zata fita tabar miki gidan.
sumayya kallon sultana sadiya take cikin rashin gamsuwa, ta bud'e baki zatayi magana kenan nan wayarta tafara ringing ganin zinat ce yasa takalli sultana sadiya tace ummah ina zuwa.
mik'ewa tayi tafito tashiga d'ayan bedroom d'in sannan tayi picking d'in wayar ko sallama batayiba tafashe da kuka tace zinat nashiga ukku.
zinat a firgice tace sumayya me yake faruwane?
sumayya kasa magana tayi sai ma kuka da takeyi, zinat cewa take sumayya kiyi min magana mana please nima inbaso kike inyi kukanba.
sumayya tsagaitawa tayi daga kukan da take tace zinat yarimana kasheni yakeson yi wai aure zai k'ara.
'yar dariya zinat tayi tace yoh d'an wannan zaisa hankalinki yatashi?
sumayya daina kukan tayi tace zinat kin ko ji abinda nace?
zinat tace na ji man ba aureba? yaje yayi kema ai wani sauk'in ne zaki samu domin yanzu zaki samu right d'in zuwa inda kikeso kinga business d'inmu zaya ha66aka, koma wacece kibarta tashigo wlh dakanta zata bar miki gidan.
sumayya tace haba zinat kamar ya inbari yayi aure ya za'ayi kamata ace anmini kishiya
zinat tace haba sumayya matsalata da ke kiyita abu kamar baki wayeba, kinsan ni kaina ba zan amince ayi miki kishiyaba dakanmu zamu fitar da ita gidan.
Sumayya jinjina kai tayi tace yanzu nafahimceki baby, zinat tace yauwa dear ai nasan zaki fahimceni nan zinat taita k'unsa mata makirci saida taga sumayya tad'auka sannan sukayi sallama takashe wayarta.
sumayya dawowa tayi wajen sultana sadiya tace ummah shikenan nad'auki shawararki ammah wlh bazan ta6a bari amaryar tasamu zaman lafiya a gidanaba.
cike da jin dad'i sultana sadiya tace gaskiya naji dad'i da kika fahimceni ai inma kin bari tazauna lafiya toh baki haihuba kibarshi kawai daga shi har amaryar tasa sai sun san sun ta6o tsuliyar dodo.
dariyar jin dad'i sumayya tayi tace za'a fara babban wasa dominba mai ta6a gimbiya sumayya azauna lafiya, muje zuwa.
__________________
Zarah duk yadda taso tacire damuwa a ranta ammah ta kasa kawai dai tana 6oyewane dan kar iyayenta sukaranto halin da take ciki, ga malam bello da kusan kullum sai ya kirata ammah takasa fad'a masa matsalar da ake ciki.
shi kansa ya sha tambayarta abinda yake faruwa domin jin yadda duk tacanza masa saidai tace bakomai.
Yau Zarah ita kad'aice gidan kasancewar mama taje asibiti raka yaya Rauda awo, Aysha kuma taje bikkin k'awarta da akeyi.
ji tayi bata iya barin malam bello batare da yasan halin da ake cikiba dan haka wayarta tad'auko tanaso takirasa ammah ta kasa sai juya wayar take a hannunta ta rasa yadda zatayi daga k'arshe dai tadaure takirasa.
malam bello baiyi picking ba har saida tatsinke tana shirin tak'ara kiransa sai gashi ya kira, zuba ma wayar ido tayi ta rasa yadda zatayi tad"auka domin batasan abinda zatace ba, saida taga takusan tsinkewa sannan tayi picking tare da yin sallama.
malam bello ya amsa mata nan suka gaisa sannan Zarah tace malam idan kana kusa dan Allah kazo akwai maganar da nakeso muyi.
Cike da jin dad'i malam bello yace ganinan ko zuwa kinsan dama nakwana biyu bansaki a idonaba fatana dai ba laifi nayiba.
Zarah duk yadda taso tamaida kukanta kasawa tayi muryarta tana rawa tace babu komai sai kazo, dasauri takashe wayar batare da taji abinda zai ceba takife kanta saman katifarsu tashiga rera kuka cike da tausayin malam bello da kanta domin batasan yadda shima zai fahimci maganarba
bayan kamar minti biyar wayarta tashiga ruri ganin malam bellone yasa dasauri tamik'e taje toilet tawanke fuskarta sannan tafito tasaka hijab d'inta tafita jikinta duk a sanyaye.
A k'ofar gidansu tasamesa tsaye yana jiranta kanta yana sadde k'asa gudun kar yagano yanayin da take nan tayi masa sallama
malam bello fuskarsa a sake ya amsa mata tare da tambayarta mutanen gida tace duk suna lafiya, daganan shuru yabiyo baya sai chan malam bello ya nisa yace Zarah Allah yasa ba laifi nayiba dan fitama zanyi nafasa nace bari infara amsa kiran gimbiyata sannan sai inwuce
Zarah runtse idonta tayi tana jin wani iri a ranta jin kanta yafara sarawa yasa tajingina da bango.
malam bello rikicewa yayi yace Zarah lafiya? meyake faruwane? wani abu yasamu su abbah? Please kifad'amin matsalarki.
Zarah batare da ta bud'e idontaba tashiga girgiza masa kai hawaye suna zuba cikin muryar kuka tace ko d'aya malam bello babu abinda yafaru, inaso ne kayafe min wlh ba a son raina hakan takasanceba saidai dan ba yarda zanyi kuma banaso ink'i bin umirnin iyayena kayi hak'uri da..... sai kuma tayi shuru tare da fashewa da kuka.
malam bello jikinsa ya yi sanyi sosai yace Zarah da me zan hak'ura? kiyi min bayani, su Abbah basu amince da ni inkasance surukinsuba ko?
Zarah dakyar tabud'e idanuwanta da suka kumbura saboda kuka tace su abbah sunyi min miji muhak'ura da juna haka Allah yak'addara kai ba mijina bane.
Malam bello murmushi yayi Wanda yafi kuka ciwo yana kallon Zarah da taketa kuka yace Zarah daman kan wannan 'yar maganar kike ta faman kuka?
Zarah tsagaitawa tayi da kukan da take tace bakaji abinda nace bane? miji fa akayi min?
Malam bello daurewa yayi cikin rashin damuwa yace najiki mana, toh menene Zarah? dole kiyi hak'uri kibi za6in iyayenki domin ba zan ta6a yadda inbaki shawara akan kibijire ma iyayenkiba, Allah daman ya k'addara ba matata bace ke, ita rayuwa duk yadda tazo maka kayi hak'uri kakar6eta domin shi aure nufine na ubangiji babu mai auren matar wani kar kimance mune muke haukanmu ammah Allah yariga da yatsara ma kowa yadda rayuwarsa zata kasance wlh nabaki goyon baya kiyi ma iyayenki biyayya insha Allahu zakici ribar biyayyar da zakiyi musu kema kuma Allah zai baki wad'anda zasuyi miki biyayya domin su iyaye sun wuce abin wasa yakamata muguji fushin iyaye, ni yanzu shawarar da zan baki itace kiyi ma iyayenki biyayya insha Allahu zakici moriyar hakan.
Zarah da tunda yafara maganar tazuba masa ido hawaye kawai suke zuba daga idonta dakyar tabud'e baki tace yanzu kana nufin ka rabu da ni?
malam bello murmushi yayi wanda iyakansa baki sannan yace tabbas Zarah narabu da ke domin ko nine bazan iya bujirema umirnin iyayenaba saidai inaso kisani sonkine da nake yajawo hakan kuma har abada bazan daina sonkiba saidai inyi addu'an Allah yarage min sonki a cikin zuciyana, fatana Allah yasa wanda zaki aura yasoki fiye da yadda nake sonki, kema inaso kiyi min alk'awali d'aya shine zai tabbatar min da kina sona.
Zarah cikin kuka tace wane irin alk'awali kakeso inyi maka wlh indai shi zaisa kagane ina sonka toh na amince koma minene kafad'a.
malam bello d'an guntun murmushi yayi sannan yace inaso kiso mijinki fiye da yadda kike sona sannan kinuna masa kulawa kar kisa6a masa kiyi masa biyayya indai ba hanyar Allah yanemi yakauceba.
Zarah girgiza kai tashiga yi tace bana tunanin zan iya son wani fiye da yadda nake sonka bazan iya d'aukar alk'awalin da nasan bazan iya cikawaba.
malam bello juyawa yayi cikin dabara yagoge hawayen da suke shirin zubo masa sannan yace wannan zai shaida min da cewar bakya sona.
Zarah girgiza kai tashiga yi tace malam kar kace haka wlh ina sonka shikenan na amince zanyi duk abinda kace.
malam bello juyowa yayi yace dagaske kin d'aukar min alk'awali?
gyad'a masa kai tayi tace eh saidai kayi hak'uri ba zan iya tursasa zuciyana taso wani fiye da yadda take sonkaba.
murmushi malam bello yayi yace natabbata zaki ma soshi indai ya amsa sunansa namiji wanda yadace mace taso, dan haka ina miki fatan alkhairi zarah idan nasa6a miki kiyafemin domin inaso wannan takasance had'uwarmu tak'arshe.
zarah fashewa tayi da wani sabon kukan tare da durk'ushewa k'asa cikin kuka tace nagode sosai malam bello hak'ik'a kai masoyinane nagaskiya tabbas duk macen da ta aureka tayi dacen miji fatana Allah yabaka wadda zata soka fiye da ni, bazan ta6a daina yi maka addu'a ba domin kabani gudunmawa sosai a rayuwana wlh *K'ADDARA CE* kawai tarabani da kai ammah ka cancanci kasancewarka mijina.
malam bello murmushi yayi yace kar kidamu zarah daman kyaun kowane musulmi ya yarda da k'addara me kyau da marar kyau, ina miki fatan alkhairi nabarki lafiya .
juyawa malam bello yayi yatafi yana jin wani k'unci acikin ransa ji yake inama yayi kuka ko yasamu sauk'in abinda yake ji, yana jin kukan zarah tana ta kiransa ammah yak'i juyowa gudun kar shima yaga yanayin da take yayi kuka.
zarah da take tsugunne tana kuka tare da k'walah masa kira saida taga yayi mata nisa sannan tatashi takoma gida tafad'a saman katifarsu tacigaba da kukanta.
Tun daga ranar zarah da malam bello suka daina waya saidai text shima na gaisuwane kawai sukeyi, daurewa kawai take tacigaba da addu'a akan Allah yaza6a mata wanda zaifi zama alkhairi, su yaya Rauda su suke k'ara kwantar mata da hankali da tayi hak'uri tacigaba da addu'a.
**** ***** ***** ****
memartaba kamar yadda yafad'a hakan kuwa akayi domin kiran yarima suhail yayi yace yafad'a ma iyayen yarinyar zuwa gobe zasu aiko da komai na neman aure domin basuson aja lokaci dayawa.
yarima suhail a firgice yad'ago yakalli memartaba yace ranka yadad'e duk dawuri za'ayi haka? nad'auka za a bi Komai ahankali.
murmushi memartaba yayi yace suhail kenan toh me zamu jira? k'ara dai muyi komai dawuri domin banaso ana d'aukar lokaci dayawa ammah indai iyayen yarinyar suka nemi aja lokaci toh lafiya lau saidai bazanso hakaba
yarima yace toh ranka yadad'e.
memartaba yace koma mi kenan kaje kuyi magana da waziri domin shine zaije yanemo maka auren sai ku yanke shawarar yadda zaku tafiyar da komai.
duk'awa suhail yayi yakwashi gaisuwa sannan yayi ma memartaba sallama yatashi yafita yanufi 6angaren iyayensa.
yana shiga daidai lokacin daddynsa yana shirin fita ummi tana bayansa cike da girmamawa yagaishesu sannan suka koma suka zauna, nan yake fad'a musu yadda sukayi da memartaba gabad'ayansu sun nuna farin cikinsu.
ummi tace toh zan kira iyayen yarinyar infad'a musu halin da ake ciki, sannan driver d'in da yakaini shine zai kai su waziri.
suhail ahankali yace toh ummi.
daddy murmushi yayi yace son kaima ai yakamata kaje kagano matar taka domin baidaceba ace baka san wadda zaka auraba.
yarima suhail sosa kansa yayi yace ranka yadad'e ba ma sai najeba hakan ma lafiya lou zan zauna da ita, ko da ace ban santaba a yanzu, zan santa bayan aurenmu.
ummi tace haba suhail ammah..... hannu da daddy yad'aga matane yasa tayi shuru, daddy yace shikenan zaka iya tafiya.
yarima godia yayi ma iyayensa sannan yatashi yafita cike da jin haushin auren had'in da ake shirin k'ara masa a karo na biyu.
daddy kallon ummi yayi bayan yarima ya fita yace kibarsa kawai tunda ya amince zai aureta kar mumatsa masa akan dole sai yaje yaganta.
ummi jinjina kai tayi tace hakane ranka yadad'e fatana dai suhail yasota domin zarah ta cancanci kowane namiji yasota.
murmushi sultan Ahmad yayi yace zai ma sota insha Allah yanzu dai bari inje muyi magana da waziri yadda za'a tafiyar da komai.
cike da jin dad'i Sultana Bilkisu tace adawo lafiya ranka yadad'e.
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Yau Ranar takuce *'yar mutan zariya mummyn uswan nd Mummyn Fadyl* wlh ina ji daku irin sosai d'innan😘_
*PAGE* 1⃣9⃣
ummi kiran mama tayi a waya lokacin mama tana zaune tsakar gida ita da abbah suna cin abinci, mama jin wayarta tana ringing yasa tad'auko ganin sunan sultana bilkisu da yabayya yasa tazaro ido tare da cewa malam sultana ce take kirana.
Abbah yace toh toh d'aga muji abinda zatace, mama saida ta saita nutsuwarta sannan tayi picking d'in call d'in tare da yin sallama.
daga chan 6angaren sultana bilkisu ta amsa mata cike da fara'a, nan suka gaisa cike da girmama juna, ummi tace ya su zarah dafatan duk suna lafiya?
mama tace lafiya lou, nan ummi take shaida mata akan maganar neman auren zarah da za'a zo gobe.
mama kallon abbah tayi da yake sauraren firar tasu, alama yayi mata da tace toh.
mama tace toh ranki yadad'e Allah yakaimu.
cike da jin dad'i ummi tace Ameen mungode sosai, ammah idan mahaifinsu yana kusa kiban shi inaso muyi magana inkuma baya kusa idan yadawo zan kira,
mama tace ranki yadad'e yana ma kusa gashi, nan tamik'a ma abbah waya.
Abbah kar6a yayi tare da yin sallama nan suka gaisa cikin mutunta juna, sultana bilkisu tace yauwa daman akan tsaida rana ne agaskiya mu a Royal family d'inmu ba'a yin baiko ad'auki lokaci shine nakeson in rok'eka alfarma dan Allah kar asa lokaci dayawa,
Abbah Jim yayi yakasa cewa komai.
sultana bilkisu tace kayi mamakin jin haka ko? kuyi hak'uri wlh tsarin masarautarmu ne haka.
Abbah cike da damuwa yace ranki yadad'e gaskiya hakan bazai yuwuba domin mu ba halinmu d'ayaba idan mukace ayi bikkin cikin gaugawa toh gaskiya zamu cutu tunda bamu fara tara komaiba da dai ataimaka asa ranar da d'an nisa domin musamu muyi mata abinda Allah yahore mana.
daga chan 6angaren ummi murmushi tayi tace kar kadamu ni zan d'aukema zarah duk wani abu da iyaye yakamata suyi ma 'ya'yansu wlh ko da ba d'ana zata auraba zan iya yi mata haka.
Abbah yace a'a ranki yadad'e kar hidimar tayi yawa kibari dai zamuyi.
ummi tace kar kadamu tunda nace zanyi kubarsa kawai wannan yazama sirri tsakanina da ku domin bana fatan wani yasan da hakan saboda gori da wulak'anci
maganarta tayi ma abbah dad'i sosai ganin yadda take Royal Family ammah bata d'auki kanta komai ba tasan abinda yadace da wanda bai daceba, muryar sultana bilkisu yaji tana cewa bawai ina nufin naraina k'arfinkuba wlh ko d'aya ko da ace ba zarah bace zan iya yi ma wata barema zarah da zata auri jinina dan Allah ka amince ma buk'atata a karo na biyu, malam yace toh ranki yadad'e mungode sosai Allah yabiyaki da gidan Aljannah,
ummi tace Ameen nice da godia da kuka amince min sai kunjimu, agaishe da su zarah.
malam yace haba bakomai ranki yadad'e, su zarah zasuji.
bayan sun gama wayar Mams kallon Abbah tayi tace malam toh yanzu ya za'ayi? wannan neman aure ba ko shiri.
Abbah yayi murmushi yace gaskiya mutanen nan suna da kirki sosai bamuda abinda zamu biyasu da shi saidai muyi musu addu"a.
mama tace hakane da ace haka masu kud'i suke da ansamu sauk'in wani abun ammah yanzu sai kaga maikud'i sai d'iyan masu kud'i, Hajiya da Alhaji, d'an malam Audi me goro sai 'yar Malam idi mai icce, bakowane iyaye suke amincewa 'ya'yansu su auri 'ya'yan talakawa ba,
Abbah yace hakane abun ne yanzu sai addu'a domin masu son talakawa suna ra6arsu basuda yawa wani lokacin ni abun har mamaki yake bani ince toh wai su mancewa suke da Allahn da yabasu zai iya amshewa a duk lokacin da yaso? ko suna mancewa Allahn da ya azurtasu shine yayi talakka kuma ba dan baya son saba, ko suna mance fad'arsace cewa shi yake azurta wanda yaso yakuma hana wanda yaso, Allah dai yasa mudace.
mama tace Ameen y rabb.
Abbah yace toh yanzu sai kurubuta duk abinda kuke buk'ata na tarar bak'in sai insiyo muku, ko kuma kuta6a kud'in nan kud'ibi yadda zasu isa kuje kasuwa yanzu kusiyo abinda kuke ganin ya dace dan ni yanzu fita nakeson yi zan ma biya gidan yaya manu inshaida masa dan yasan da zuwansu gobe yashigo da wuri,
mama tace toh malam Allah dai yashige mana gaba, bari inje insanar da yaran chan.
Bayan Abbah ya fita mama tashi tayi tanufi d'akinsu zarah lokacin zarah tana kwance saman katifarsu gefenta Rauda da Aysha ne zaune suna hira itadai bata sanya musu baki ammah tana saurarensu.
shigowar mama ne yasa suka tsagaita daga hirar da sukeyi mama kallonsu tayi tana murmushi tace 'yan albarka kuna nan kuna hira?
murmushi Aysha da Rauda sukayi sannan Rauda tace eh mama akwai abinda kike buk'ata da za'ayi ne?
mama tace a"a bakomai sannan tamaida kallonta ga zarah da take kwance tace gobe in Allah yakaimu za'a zo neman auren zarah, wani irin fad'uwan gaba yaziyarci zarah ahankali tamaida idanuwanta talumshe tana jin wani iri a ranta.
Rauda da Aysha murna suka shiga yi suna kai wlh munji dad'i mama ashe zamusha bikki, bikkinma na princess zarah inji Aysha tare da kallon zarah taga idanuwanta a lumshe suke.
mama tace toh yanzu dai Aysha kitashi kishirya zamuje kasuwa musiyo abinda yadace dan haka Rauda ke zaki rubuta abinda kike ganin yadace asiyo.
Rauda tace toh mama nan tamik'e tad'auko paper da biro tashiga rubutawa.
Bayan su mama sun tafi Rauda kallon zarah tayi tace sister nasan abinda kikeji game da auren nan musamman ma da yakasance ba wanda kikeso bane zaki aura, kiyi hak'uri kikar6i k'addararki insha Allahu zakici ribar hak'urin da kikayi. zarah bud'e idanuwanta tayi da suka cika da k'wallah ahankali tabud'e baki tace yaya Rauda bawai nak'i ta taku bane wlh na amince saidai ina tsoron abinda zaije yadawo domin bana tunanin shima yana sona nasan dai had'in iyayensane inma bahakaba tun daga yanayinsa kinsan yafi k'arfin kasancewa mijin zarah, zarah duk yadda taso ta6oye kukanta kasawa tayi fashewa tayi da kuka tare da kallon Rauda da tazuba mata ido tace Yaya Rauda kiduba kiga ko da sau d'aya baizo da sunan mugaisaba kingako wannan aure namu kawai za'ayisane ammah yarima suhail ya wuce ajin zarah duk kyawawan 'yan matan da suke garin nan arasa wadda za'a basa sai zarah?
yaya Rauda cike da tausayin k'anwartata tarik'o hannun zarah tace inji wa yace zarah ba maikyau bace? kema kinsan kanki kuma natabbata shima zaya soki domin kina da halayyar da yadace kowane namiji yaso mace saboda su, wlh zarah kin cancanci asoki, murmushi Rauda tayi tace nayarda da k'anwata zata iya sace zuciyar kowane namiji.
Zarah jikin Rauda tafad'a tare da k'ara sautin kukanta tace a'a yaya rauda kar kice haka wlh wannan yana da jin kai tun daga ma yanayinsa da nagani a wajen saukarmu kuma kema nasan kinga haka saidai idan zaki 6oye gaskiyane kuma fa su Abbah sunce mana yana da mata.
Murmushi yaya rauda tayi tare da shafa kan k'anwartata tace zarah nayarda dake nasan zaki iya k'watar ma kanki 'yanci.
zarah mik'ewa tayi tashige toilet tamaida tarufe tacigaba da kukanta kamar wadda aka aikoma da sak'on mutuwa saida tayi me isarta sannan tawanke fuskarta tafito bata damu da kallon da rauda takeyi mataba tayi kwanciyarta tare da maida idanuwanta tarufe ganin haka yasa rauda takyaleta.
Tun da asuba da sukayi sallah shirye-shirye suke natarar bak'i inda aka rabama kowa aikin da zaiyi, girki sukayi masu rai da lafiya kala biyu, aka soya kaji kafin kace mi gida ya gaure da k'amshi sannan suka had'a drinks iri-iri .
wajen k'arfe sha d'aya suka gama komai kowa yaje yashirya ammah banda uwar gayya saida yaya rauda tace zata je ta sanar da su mama sannan tatashi taje tayi wanka suka d'auko mata atamfarta cikin kayan da ta d'inka da kud'in da tasamu na walimar safkarsu tasaka.
wajen k'arfe 12 lokacin su Abbah da d'an uwansa malam manu suna zaune waje suna jiran isowar bak'i, motocine guda ukku suka tafo a jere a k'ofar gidansa sukayi parking dogarawane suke fitowa daga ciki dasauri duk suka nufi wajen motar tsakiyar suka kare tare da baza manyar rigunansu suka bud'e wa su sultan Abbas(Abban sumayya) da waziri suka fito nan dogarawa suka take masu baya suna ranku yadad'e takawarku lafiya.
ganinsu yasa su Abbah suka mik"e suka nufi wajensu domin sun gane waziri, ganin sun nufosu yasa d'aya daga cikin dogarawan yace ranku yadad'e ga maigidan nan, suna isowa waziri da sultan Ahmad suka mik'a musu hannu cikin sakin fuska suka gaggaisa, Abbah yace bismillah kushigo daga ciki.
basuyi musuba sukabi bayansu a zaure suka zauna saman k'atuwar tabarmar da aka shimfid'a dogarawa a k'ofar gidan suka tsaya.
Nan suka k'ara gaisawa sannan su Abbah suka shiga gida suka kwaso kulolin abincin da aka shirya.
A gabansu su sultan Abbas suka jerasu, sultan Abbas yagabatar da kansu a matsayinsa na k'anen mahaifin yarima sultan sannan yagabatar da wazirin sarki,
nan shima malam muda yagabatar da kansa a matsayin yayan mahaifin zarah sannan yagabatar da malam musa a matsayin mahaifin zarah,
Nan suka shiga tattaunawa akan maganar neman auren dakyar suka samu abbah ya amince akan ayi bikkin nan da sati shidda masu zuwa dan shi cewa yayi sai nan da wata ukku,
dubu d'ari ukku sultan Abbas yabada yace kud'in nagani inaso da na neman aure,
abbah yaso arage kud'in saboda shi aganinsa sunyi yawa ammah sukak'i,
dubu d'ari suka bayar sukace ga kuma sadakin zarah, nan waziri yaba dogarawa izini da su kwaso kayan da suke cikin boot d'in mota,
nan aka fara shigowa da kwalayen biscuits, chewing gum sai sweets, sai alkyabba kala ukku da atamfa biyar akace na amarya ne, sai shadda yadi goma-goma kala ukku akace na uban amarya ne, sannan sai atamfofi kala biyar su kuma na uwar amarya.
Abbah rasa bakin godia yayi nan sukayi ta jero musu addu'o'i, dakyar suka samu su sultan abbas suka amince suka d'an ci abincin sauran akaba dogarawa suma sukaci,
bayan sun gama Abbah shiga yayi gida yace su zarah suje sugaisa, gaba d'ayansu suka fito zarah rufe fuskarta tayi da gyale saikace sabuwar amarya, nesa dasu kad'an suka tsaya suka tsugunnah cike da girmamawa suka gaishesu, cikin sakin fuska suka amsa musu tare da tambayarsu ya gida? sukace lafiya lou.
Waziri ne yace ina amaryar tamu cikinku? Aysha ce tayi saurin nuna zarah da take k'ara sunkuyar da kai tace gatanan.
Sultan Abbas da Waziri sukace masha Allah amaryartamu dai ta cika kunya dayawa toh Allah yasa alkhairi Allah yakaimu lokacin saidai kinyi hak'uri domin kinsan cikin danginsa zaki zauna kinsan dai yanayin gidan namu na sarauta.
Abbah yace haba bakomai ai shi aure babu inda baya kai mutum duk inda mace tatsinci kanta hak'uri zatayi tazauna.
gaba d'ayansu sukace hakane Allah yasa alkhairi.
su zarah tashi sukayi suka koma cikin gida, inda su Abbah sukayi musu rakiya har wajen motarsu gaba d'ayansu godia sukeyi ma juna irin karamcin da suka nuna ma juna, saida su Abbah sukaga tafiyarsu sannan suka dawo gida.
shigowa sukayi da kayan nan sukaita gani suna mamakin ganin neman aure kawai aka kashema wannan mak'udan kud'in, nan abbah yake fad'a musu yadda suka tsaida shawara lokacin da za'ayi auren, itadai uwar gayya tana d'aki ta k'umshe kanta harda kukanta.
Abbah shadda kala d'aya da dubu ishirin yaware yaba yayannasa, sannan ya d'ibar masa kayan sa ranar bikkin dayawa, malam muda godia yayi cike da jin dad'in kyautan da k'anen nasa yayi masa.
A chan 6angarensu Sultan abbas da Waziri a cikin mota sukaita labarin kirkin iyayen zarah,
ko da suka isa a fada suka safka lokacin memartaba da suhail sai mahaifin suhail ne zaune a fadar suna lissafin wasu kud'i.
nan sultan Abbas da Waziri suka labarta musu irin kirki da karamcin da suka samu daga wajen iyayen zarah.
Yarima suhail yana saurarensu shidai baice komaiba.
memartaba murmushi yayi tare da kallon yarima suhail yajinjina kai yace natayaka murna za6enka yayi kyau sosai, tun daga nan nasan d'iyar mutuncice zaka aura, ko da mahaifinka daman yafad'amin ba d'iyar masu kud'i bace wlh naji dad'i sosai domin suma talakkawa suna da 'yancin shiga gidan sarauta kuma ta haka mutane zasu k'ara tabbatarwa bamu banbanta kowa dukansu namune.
yarima suhail murmushi kawai yayi,
nan su sultan Abbas suka d'auka Allah yaja da ran sarki me adalci
Sultan abbas ko da yafito daga fada turakarsu dada yaje yagaishe da mahaifiyartasa lokacin sultana bilkisu da sultana sadiya sunje gaisheta,
nan sultana bilkisu tagaishesa suka gaisa cike da mutunta juna, inda sultana sadiya taketa had'e fuska ita ala adole fushi take domin tun kafin yatafi saida sukayi 'yar rigima akan zuwan da zaiyi neman ma Yarima suhail aure cike da 6acin rai suka rabu.
Dada tace har kun dawo kenan?
Sultan Abbas murmushi yayi yace eh ranki yadad'e gaskiya mutanen suna da mutunci sosai dan sun karramamu yadda yakamata, nan yake basu labarin irin tarbar da akayi musu yace ko da iyayenta masu k'aramin k'arfine ammah sunyi k'ok'ari sosai wajen ganin sun tarbemu a mutunce.
Sultana Sadiya ce tayi karaf tace au wai duk jin kan na yarima ammah akan d'iyar talakkawa yak'are?
Sultan Abbas murmushi yayi yace inbanda abinki sadiya ai talakka da me kud'i duk d'ayane.
Dada tace ina akwai banbanci domin bakowane talakka ake amince mawaba, ga yaron nan kaifi d'ayane ba a isa abashi shawara yad'auka ba.
ita dai sultana bilkisu tana saurarensu batace komai ba.
Sultana Sadiya tace ma dada Ranki yadad'e ai harda laifin mahaifiyarsa da ace tana yi masa magana ai da gyara.
Dada tace a'a kar kice haka rabani da suhail ni nasan halinsa natabbata ko itama bai zama dole yaji kowace maganartaba ni nasan halinsa.
Sultana Bilkisu murmushi kawai tayi, Sultan abbas yace ranki yadad'e aikin gama ai yariga da yagama addu'an zaman lafiya kawai za'ayi musu.
Dada tace hakane duk wad'annan surutan basuyi fatanmu dai kamar yadda kace sun karramaku toh muga karamcin da mutuncin atare da ita.
sultan abbas yace hakane ranki yadad'e, Sultana sadiya bahaka tasoba taso ace dada tahau tazauna tace ba zata amince ayi aurenba.
_Comments_
*nd*
_Share_
_Sis Nerja'art✍🏻_
👑👑👑
_*YARIMA SUHAIL*_
👑👑👑
_*Written By~Sis Nerja'art*_
_*DEDICATED TO MY DAUGHTER ZARAH*_
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION ®*
*[onward together]*
*{ we give the readers of ours the best out of the bests,,our inks are melodious and dropping a kinda lights to readers }*
THE PEN OF LOVE 😘 HEART TORCHING ❤ TEARS OF SORROWS 😭 CURDLES 🙂 GIGGLES 😁 AND MARRIEGE THINK💑
*JUST GIVE US FOLLOW....*✔
_Yau page d'in mallakinkune ku kad'ai *Umm Abideen nd Queen Meenali* hak'ik'a ina muku so na hak'ik'a, chancantar kuce taja da haka😘_
*PAGE* 2⃣0⃣
A chan gidansu zarah duk inda yakamata araba kayan baikonta anraba kowa yayi murna sosai tare da fatan alkhairi.
k'awarta khairy tsegumi tashiga yi mata akan tabar malam bello zata auri wani daban itadai zarah shuru tayi.
duk yadda khairy taso zarah tafad'a mata wanda zata aura zarah k'iyawa tayi, sai Aysha ce take fad'a mata.
khairy murna tayi sosai har da tsallenta tace da girman kujerarki gimbiya zarah ai ni wlh tun lokacin da nagansa naga kunyi matching, gaskiya guy d'in ya had'u ba k'arya gaskiya natayaki murnar samun miji irin yarima suhail ana ta shi waketa malam bello kud'i, kyau, nasaba, mulki, aji babu wanda yarima yarasa.
murmushin takaici zarah tayi tace khairy kenan bakisan micece soyayyaba wlh son da nake ma malam bello ya wuce yadda kike tunani, kuma wannan d'in da kike maganarsa bana tunanin zai soni, ko da sau d'ayane bai ta6a zuwa muka gaisaba, wannan aurenfa iyayensane suka nema masa ni, wlh nayi da nasanin walimarnan da nayi a islamiyya domin itace silar faruwan komai, kukan da take dannewane yaci k'arfinta,
khairy rungumota tayi jikinta tana lallashinta tace a'a zarah kidaina cewa haka, domin haka Allah yak'addara yarima shine mijinki ba malam bello ba kiyi hak'uri kid'au k'addara kicire malam bello a ranki kisamarma yarima matsugunni a cikin zuciyanki.
dasauri zarah tad'ago kai takalleta tace khairy taya kike tunanin suhail zai samu matsugunni a cikin zuciyana?
murmushi khairy tayi tace na tabbata zai samu domin ta ko wane fanni ya dace kisosa dan daganin yanayinsa ma ya iya soyayya.
zarah ganin abin na khairy har da tsokana yasa tashareta.
A chan 6angaren yarima zaune yake yana dannar laptop d'insa da alama wani abu me muhimmanci yakeyi gimbiya sumayya ce tashigo ba ko sallama, ko da sau d'aya yarima bai d'ago takalletaba.
daga nesa da shi kad'an tatsaya tare da yamitsa fuska tace suhail kenan gaskiya kabani mamaki ace duk mulki, kyaun da Jan ajin ammah ace d'iyar talakawa zaka aura, gaskiya najiye maka haushi ammah fa dakunya ace talakka itace zata kasance kishiyata natabbata ko matsayin baiwata bata kaiba.
yarima d'ago kai yayi yawurga mata wata irin muguwar harara wadda har saida sumayya tatsora, yace ke dad'ina da ke wani lokacin k'walwarki a toshe take in banda abinki me yahad'a kud'i da soyayya ina so kisancewa kud'i basa siyan soyayya kuma bari kiji ahaka nakesonta dan haka kifitar min daga d'aki ko in 6a66allaki ,
sumayya ganin babu alamun wasa a fuskarsa yasa tafita tana k'unk'uni,
tsaki yarima yaja sannan yacigaba da aikinsa a cikin zuciyansa ko yana mamakin halin sumayya da kwata-kwata ta kasa gyarawa.
shaheed a wajen mahaifinsa yakeji sunje neman aurensa baiyi mamakin rashin fad'a masa da baiyiba domin yasan halinsa,
ko da yaje yi masa Allah yasa alkhairi yarima suhail ko kallonsa baiyiba, shaheed ba haka yasoba yaso yarima yabiyemasa ko dan yaji yadda akayi yasamu mata shi da mata basa gabansa.
*BAYAN SATI BIYU*
a gurguje sultana bilkisu shiryawa tayi itada wata aminiyarta Hajiya sa'adatu sukaje gidansu zarah inda ta rok'i iyayen zarah alfarma akan subata zarah tanaso taje da ita ayi mata gyara sosai sannan akoya mata yadda zata dinga tafiya, magana, girki dadai sauransu a gidan sarauta saboda a matsayinta na matar yarima guda ana buk'atar ace ta san yadda ake komai na gidan sarauta.
dakyar tasamu su mama suka amince zarah ma harda kukanta kafin tabisu.
sultana bilkisu gidan hajiya sa'adatu sukaje da ita, zarah tun da suka shiga gidan mamaki yacikata ganin irin daular da aka zuba a gidan babban gidane sosai mai d'auke da part ukku.
part guda aka fitar mata da shi kasancewar darene akace taje tahuta gobe za'a kawo mata wad'anda zasu dinga yi mata hidima da koya mata komai, zarah dai jikinta rawa yake har saida ummi tagane halin da take ciki.
murmushi ummi tayi tare da rik'o hannunta sukaje bakin gado suka zauna, ummi kallonta tayi tace zarah kinutsu kicire tsoro a ranki ba zamu cutar da ke ba duk abinda kikaga zamuyi miki dan gudun magana ne kinsan gidan sarauta yadda yake, dan Allah kiyi hak'uri kibamu had'in kai.
zarah da kanta yake sunkuye k'asa wani irin nauyin ummi ne taji sa6anin da dasuka tafo da ita wani irin haushinsu da takeji,
batare da ta d'ago kai takalletaba cike da kunya tace toh.
ummi cikin jin dad'i tace yauwa nagode insha Allahu gobe zaku fara gudanar da komai akwai wad'anda zasu dinga kula da ke duk abinda kikeso kiyi musu magana zasuyi miki, ummi jakkarta tabud'e tad'auka waya IPhone7 tamik'a ma zarah tace ga waya akowane lokaci kike buk'atar gaisawa da 'yan gidanku sai kugaisa nima zan dinga kiranki.
zarah batare da ta k'ar6aba tace ranki yadad'e ina da waya.
murmushi sultana bilkisu tayi tace da zaki taimaka kidaina cemin ranki yadad'e da naji dad'i.
ahankali zarah tad'ago kai takalleta, murmushi sultana bilkisu tayi tace kikirani da ummi, itama zarah murmushi tayi tace toh ummi insha Allahu hakan zan dinga Kiranki.
cike da jin dad'i sultana bilkisu tace yauwa daughter toh ina wayan taki?
zarah tashi tayi tabud'e akwatin kayanta tad'auko rugwagwar nokia d'inta tace gatanan.
kar6a ummi tayi tace wannan wayan yanzu ta gama amfani bari insaka miki number d'in wayan su mamanki a wannan,
zarah tace toh ummi.
nan ummi tasaka mata number d'in mama da abbah, sannan tad'ago takalli zarah tace daughter bari insaka miki harda number d'in yarima in case ko da ace zakuyi waya.
zarah da tunda ummi ta ambaci yarima gabanta saida yafad'i dakyar tace toh.
bayan ummi tasaka numbers d'in mik'a ma zarah wayar tayi tare da k'ara kwantar mata da hankali saida taga hankalinta ya d'an kwanta sannan tayi mata bankwana tafita taje tayi sallama da Hajiya sa'adatu tatafi.
Bayan ummi ta fita zarah mik'ewa tayi tana k'arema d'akin kallo tana mamakin dukiyar da aka zuba sannan daga bisani taje toilet domin tad'auro alwallah tayi sallar isha'i da karambani tasamu tayi alwallar tafito.
bayan ta gama sallah tana zaune saman darduma aka yi knocking d'in k'ofa nan tabada izini ashigo, hajiya sa'adatu ce tare da 'yar aikinta d'auke da kuloli, nan zarah tagaisheta,
cike da sakin fuska hajiya sa'adatu ta amsa tare da cewa yi hak'uri mun barki ke kad'ai ko?
murmushi zarah tayi tace lah bakomai mummy, hajiya sa'adatu umurni taba mai aikinta ta aje ma zarah abinci sannan tace kiyi hak'uri da kad'aici, inma kina buk'atar kallo toh zaki iya kunnawa akwai komai a parlour, sannan kayan da zakiyi amfani da su duk suna cikin wardrobe
zarah tace toh mummy nagode, nan hajiya sa'adatu tayi mata sallama tafita tabar d'akin.
abincin zarah tazuba taci sannan tatashi tashiga toilet nan ma da karambani takunna shower tayi wanka,
bayan ta fito gaban dreesing mirror tazauna tashafa mai tana ta mamakin kayan kwalliyar da tagani jibgi guda a saman dressing mirror d'in,
koda tagama wardrobe taje tabud'e mamakine yakamata ganin jibgin kayan da ke akwai, doguwar rigar bacci tajawo bak'a tasaka sannan tadawo parlour tak'are masa kallo takunna kallo tana yi domin yarage mata kad'aici,
tana zaune tana kallo saida taji tafara jin bacci sannan takashe tare da mik'ewa tashige bedroom tafad'a saman makeken gadon da yake d'akin saida tayi addu'a sannan takwanta nan bacci yayi awon gaba da ita.
da safe knocking d'in da akeyine yatadata daga baccin da takeyi saboda tunda tayi sallar asuba takoma bacci, dakyar tabud'e idonta tare da safkowa tazo tabud'e k'ofar, cike da girmamawa 'yar aikin tagaisheta tare da cewa ga breakfast d'intanan saman dining sannan zata gyara mata d'aki, zarah tace toh ammah kibar gyaran zanyi.
'yar aikin tace a'a ranki yadad'e aikinane kuma umurnine daga shugabata, zarah batace komai ba takoma ciki tabar 'yar aikin tana gyaran parlour.
wanka tashiga tayi lokacin da tafito tatarar har ta gyara mata bedroom d'in,
zama tayi gaban dreesing mirror tayi simple makeup sannan tatashi tabud'a wardrobe tad'auko less riga da skirt tasaka tayi mamaki sosai ganin yadda d'inki yakar6eta kamar an aunata.
bayan ta gama parlour tadawo tazauna a dining tahad'a breakfast tayi, sannan takoma bedroom tad'auko wayanta takira su mama domin sugaisa,
tana cikin wayan ne taji anbud'e k'ofar anshigo juyowar da zatayi taga hajiya sa'adatu ce dan haka tayi sallama da yaya rauda da suke waya tare da tsinke kiran, cike da ladabi taduk'a tagaisheta.
fuskar hajiya sa'adatu d'auke da fara'a ta amsa mata tare da tambayar ta tatashi lafiya ya kuma bak'unta?.
murmushi kawai zarah tayi batace komai ba, hajiya sa'adatu tace dafatan dai kinyi breakfast?
zarah tace eh mummy,
hajiya sa'adatu tace yauwa haka nakeso, nafison kisaki jikinki kidaina bak'unta domin nan ma gidane,
zarah tace toh mummy.
hajiya sa'adatu tace idan kin gama kisamemu a parlour muna jiranki.
zarah tace toh nama gama,
bayan hajiya sa'adatu tabiyo suka fito parlour, mamakine yakama zarah ganin wasu mata sanye da kaya iri d'aya su ukku sai wata mata zaune saman kujera.
tana fitowa matan suka duk'a suna gaisheta, zarah duk sai taji wani iri ganin irin gaisuwar ban girman da suke yi mata kasa amsawa tayi, nan itama zarah ta duk'a tagaishe da matar, nan ta amsa mata cikin sakin fuska tare da kallon hajiya sa'adatu tace ranki yadad'e wannan ce?
hajiya sa'adatu tace eh itace,
matar kallon zarah tayi tana murmushi sannan tamaida kallonta ga hajiya sa'adatu tace ranki yadad'e tunda dai ku customer's d'inane kawai kubiya 1.5 million, domin banason inyi jayayya da ku tunda ni nakema 'ya'yanku gyara, ko in antashi bikkinsu ninake zuwa ina musu duk abinda yadace kuma kunsan aikina, bana son intsaya ciniki da ku saisa nace abani hakan.
murmushi hajiya sa'adatu tayi tace shikenan za'a baki mudai fatanmu kifito mana da ita kinsan matar yarima ce.
dariya matar tayi tace ai hajiya tafad'a min komai dan haka bakuda matsala ai kunsan aikina cikin k'ank'anin lokaci nakeson incanzata domin daga ganin yanayinta ba zamusha wahala ba,
hajiya sa'adatu tace hakane Allah yataimaka ynz kibada account number d'in da Za'a turo miki kud'in ko kinfi son cash?
matar tace a'a kudai min transfer d'in fa wannan account number d'in da nata6a turo miki.
hajiya sa'adatu tace toh badamu sannan takalli zarah tace zarah ina fatan zaki bata had'in kai kuyi komai kugama lafiya.
zarah kanta yana sunkuye k'asa tace insha Allahu mummy.
hajiya sa'adatu tace yauwa d'iyata, sannan hajiya sa'adatu tanuna matan ukku da suke tsaye tace wad'annan kuyangin sultana bilkisune ita taturosu domin sudinga miki hidima dan haka duk abinda kikeso zasuyi miki Allah yataimaka.
gaba d'ayansu sukace Ameen.
bayan hajiya sa'adatu ta fita matar kallon zarah tayi tace sunana hajiya kubra nice wadda zan dinga koya miki kwalliya, girki, yadda zaki dinga tafiya irin ta k'asaitattun mata sannan kula da miji, kissa da duk wani abinda yakamata, sannan zan miki gyaran jiki sosai dan haka kid'aukeni a matsayin 'yar uwarki domin zaki kasance tare da ni natsawon wani lokaci, dan haka tun daga yau zamu fara.
zarah murmushi tayi tace toh Aunty kubra nagode.
hajiya kubrah tace kar kidamu aikinane dan haka yanzu zamu fitar da lokacin da zamu dinga gudanar da lecture d'in,
zarah cike da jin dad'i tace toh.
tun daga ranar hajiya kubrah tatsara yadda zasu dinga gudanar da komai,
tafara koya ma zarah yadda zata dinga tafiya mai aji, ita kanta zarah yanayin tafiyar ta burgeta, batasha wuyaba wajen ganin ta koya.
idan zarah tayi wanka zama take hajiya kubra tana mata kwalliya tana gwadamata kayan makeup d'in da amfanin kowane d'aya, idan tagama mata sai hajiya kubra tatambayeta amfanin kowane daga cikinsu, tans mamaki sosai ganin yadda kan zarah yakeja dan tana da saurin fahimta.
alkyabba ma sai da tadinga koya mata yadda zata sanyasu, da yadda zatayi tafiya Idan tana sanye da alkyabba dan har sa kuyangi hajiya kubra take suna takema zarah baya tayi tafiya tagani.
duk bayan sallar la'asar suke zama tana koya mata yadda zatayi magana, da shagwa6a da yadda zata dinga tarbar miji da yi masa rakiya, da yadda zata dinga narke masa kai hatta kwanciyar aure saida tadinga koyama Zarah, zarah tun tanajin kunya tana ma hajiya kubra kallon marar kunya har daga k'arshe tad'an sake mata.
girki kala-kala hajiya kubra take koya ma zarah dan a rana sai suyi girki kusan kala goma gobe kuma sai tasa zarah tamaimaita kuma tana maimaitawa lafiya lau.
A 6angaren gyaran jiki tana yi mata sosai zarah ta canza sosai dan ita kanta tana mamakin kyaun da tak'ara da haske fatarta Idan kata6a kamar jini yazubo saboda ja da tsantsi duk inda tagifta k'amshi take fitarwa medad'i .
turaren tsugunni ma ana had'amata tana yi, hajiya kubra bata wani d'irka mata magungunaba tace saboda ita budurwace da ni'imarta bata buk'atar k'ari saidai tana sata tana cin 'ya'yan itatuwa (fruits) sosai sai kuma dahuwar 'yan shila da takeyi mata akai akai
a gurguje *BAYAN SATI UKKU*
Nan da nan komai na zarah yazanza idan kaganta sai kad'auka 'yar gidan wani mai muk'ami ce, ita kanta hajiya sa'adatu ko da tazo taganta tayi mamaki sosai ganin canjin da tayi cikin k'ank'anin lokaci,
ita kanta zarah tana jin dad'i idan taduba taga yadda takoma saidai duk lokacin da tatuna saboda Wanda akeyi mata gyaran mutumin da baisan da zamantaba baisan wacece itaba, duk sai taji haushi da takaici sun kamata tarik'a ji ina ma ace malam bello ne, saidai ta6oye tasha kukanta ita kad'ai.
kusan kullum sai sunyi waya da su mama da 'yan uwanta. da sultana bilkisu dan sultana bilkisu ta WhatsApp taturo mata pics d'in kayan d'aki tace taza6i design d'in da takeso da colour d'in da takeso, lefe kuma cewa tayi zarah tayi hak'uri domin ba za'a je kai lefentaba za'a aje mata a gidanta saidai kayan da zatayi hidimar bikki za'a aika mata da su,
A cikin satin ne hajiya kubra tak'ara zage damtse wajen gyaran jikin zarah kasancewar a yanzu saura sati guda yarage ayi bikkinsu,
akwati guda aka kai gidansu zarah cike da kaya kala ashirin, kayane na azo agani da alkyabba da shoes nd bags akace wanda zarah zatayi hidimar bikkine saboda masarautarsu ba'a kai lefe saidai a ajema amarya kayanta a gidanta, kowa ya yaba sosai da kyaun kayan ana ta santinsu, ko da su yaya rauda suka kira zarah a waya nan suke fad'amata kayan da aka kawo mata, zarah dai bata damuba saboda ita aganinta basu take buk'ataba burinta abarta taje taga iyayenta. da 'yan uwanta.
ko da sultana bilkisu tayo mata waya nan take tambayarta idan akwai events din da takaeso tayi, zarah cewa tayi bazatayi komai ba ko ma I.V card bazata rababa domin batada abokai sosai, sultana bilkisu bata takuramata ba saboda ko da tatuntu6i yarima da maganar shima cewa yayi ba dai halarci party ko d'ayaba, sultana bilkisu kyalesa tayi tace tunda dai ka amince da auren ai babu matsala.
kud'i sosai yarima suhail yadunk'ula yaba sumayya domin tayi amfani da su, gimbiya sumayya runtse ido tayi tace bazasu ishetaba, dan haka saida yak'ara mata sannan tatafi tana cewa idan ban amsaba ai wata zakaje kaba.
sultana bilkisu ganin har bikki saura sati guda ammah yarima baidamu da yaje yaga matar da zai auraba ko da sau d'ayama baya maganarta ko ma ita tayi masa maganarta sharewa yake dan haka wayarta tajawo takirasa tace yasameta tanason magana da shi.
sultana bilkisu ko da yazo matsa ma yarima suhail tayi akan dole sai yaje yaba zarah kud'i wad'anda zatayi hidimar bikki da su, yarima saida yaga ran ummi yana neman ya6aci sannan ya amince zai je gobe idan Allah ya kaimu.
yarima ko da yakoma 6angarensa zama yayi saman kujera takaici duk ya cikasa, tsaki yaja yace sai asa mutum yayi aure kuma amatsamasa dole sai yaje, wayarsa yajawo yakira shaheed bayan shaheed yayi picking yace ranka yadad'e ina mik'o gaisuwa.
tsaki yarima yaja yace kaiwai bakasan kayi ma mutane sallama ba.
dariya shaheed yayi tare da yin sallama,
nan yarima ya amsa masa, daga nan kuma bai k'ara cewa komaiba.
ganin yarima baida niyan yin magana yasa shaheed yace kaifa tsiyata da kai sai kakira mutum kuma kakasa yin magana.
tsaki yarima suhail yaja yace gobe idan Allah ya kaimu kashirya muje wajen wannan yarinyar ka san ummi ce ta matsamin sai naje dole.
cike da jin dad'i shaheed yace Allah yakaimu, _domin shima yana burin ganin matar da yarima zai aura_, chan sai yace kai yarima bakada dama yanzu matar da zaka aurace kake cema yarinya?
tsaki yarima yaja tare da kashe wayarsa domin shi yanzu haushin kowa ma yakeji.
murmushi shaheed yayi tare da bin wayar da kallo yace yarima kenan jin kanka ya yi yawa.