Monday, July 27, 2020
*CHAPTER 1*
Tafe tAke tana rusa kuka wiwi,,,,,wiwi
Duk ta hada miyau majina da hawaye ta dame fuska gaba
daya
Rungume take da tiren tallan tata wanda ba komai a cikinsa
sai ihu take kwararawa tana kiran wayyo kudina wayyo ni
kudina
Mutane sai kallonta sukeyi masu tausayi daga cikinsu su
kirata suji abinda ya faru su lallasheta ta tafi
A haka taita saqawa ta lunguna harta iso layin gidansu
Tunda ta iso layin rabi,u wanda bai wuce dan kimanin
shekara goma sha huduba kejiyo sautin kukanta yana duqe
yana faman wanke wanke
Yai niyyar miqewa karaf sukai ido hudu da inna laure
Ta watsa masa wani irin kallo simi simi ya koma yaci gaba
da wanke wanken
Tace munafuki dan iska wlh ka sake tashi baka gama
wanke wankennaN ba saina karya maka qafafu
Ta qara jan tsaki ta hankade labule ta shige Daki
Rabi,u yai saurin tsame hannunsa daga wanke wanken ya
kwasa yai waje da gudu
A bakin kofar zauren sukai kicibus yace waya tabakine
saude?
Ta qara fashewa da wani kukan wanda yafi nada sauti
Rabiu ya qara janta jikinsa kiyi haquri saude fadamin meke
faruwa?
Tadan sassauta da kukan tace kudina yaya kudin tallah na
wani ya kwaceminsu
Rabiu ya dafe kirji ido waje yace garin yaya saude?
Kinsan halin inna laure kuma dukanki zatayi
Ta qara fashewa da kuka wayyo yaya dan allah ka roqeta
karta dakeni
Ya danyi jimm kiyi haquri saude babu yaddah zan iya kixo
muje kawai ta dakekin
Ta qanqameshi wayyo yaya wlh yankani zatayi
Idanunsa suka kawo kwallah ya cije yace zo muje saude
insha allahu bazata dokekiba kinji?
Kai kawai ta daga masa tana share hawaye yaja hannunta
suka shiga ciki
Tsaye take a kofar daki da alamun ta cika ta tumbatsa jira
kawai take a tabata ta bashe
Saude ta qara fashewa da kuka wayyo allah na wlh yaya
dukana zatayi
Inna laure ta zaburo tayo kansu
In dokeki don ubanki laifin me kikayi?
Hala kin dawomin da sauran raguwar alalen ne ko?ta fada
lokacin data shaqo wuyanta
Ina kudun suke in gani?
Ta qara fashewa da kuka tace wani ya kwace kutumar
ubannan wani ya kwace? Aiko yarinya yau zaki daku a
gidannan don wlh saina lahira ya fikijin dadi. Ta jata
kiyyyyyyyy..... A qasa har zuwa bakin rijiya ta janyo igiyar
guga zaki fadamin ina kudina suke ko saina miki dukan
mutuwa da igiyar gugannan?
Cikin kuka tace wlh wani ne ya kwace ya ruga tace lallai
yarinya aiko jikinki zai gaya miki ni zaki kawowa zancen
banza zancen wofi
Tasa qafarta ta tureta ta fadi ta dinga lafta mata igiyar
gugar kamar badan mutum take duka ba
Hankalin rabiu ya tashi yaddah yaga qanuwar tashi keyi
gashi tasa qafa ta take mata ruwan ciki. Wani irin kuka ya
kwace masa ya duqa a wurin yana bata haquri
Inna laure tace au har kanada bakin magana munafiki
xonan daman ai jiranka nakeyi ta shaqoshi ta hadesu guri
guda taci gaba da jibga tamkar zautacciya
Hankali tashe inna mai dan wake ta zagayo gidan ko lullubi
babu a tare da ita
Kai jama,a lafiya maike faruwane a gidannan?
Inna laure ta tsaya da dukan tana huci. Barni da yan iskan
yarannan mai danwake nema suke su samin hawan jini.
Niqi niqi ina fama dasu inkai gwauro inkai mari wai dondai
a samu a rufama kai asiri amman yan iskan yaran basu
gani kawai an mutu an barni da jaraba yanxu ace kamar
saude wai har tasan taje tallah ta boye kudin wai tace wani
ya kwace sbd mugun hali irinna wannan munafukin
annamimin dake koya mata
Inna mai danwake tace eh kam gaskia baku kyautawa
kankuba. Yanxu ku harkunfi son aita jibgarku irin haka idan
kun boye kudin kuci me dasu fisabilillahi
Tadan numfasa tana kallonsu kafin ta qara zaro ido a,a
laure yaya nake ganin yarcan kamar bata motsine""
Ta qara matsawa tana tattabata ta dago da sauri hankali
tashe tace wlh laure bata motsi. Tace kai haba mai dan
wake da gaske kike?
Inna mai danwake ta daga hannun nata ta saki taga ya tafi
ragwaf alamar ba rai
Inna laure ta kwasa da gudu tana gyara daurin zani fadi
take iya karfinta na shiga uku ni laure
Dis is just d begining
[1/6, 9:06 AM] A A Dboy: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[1/7, 5:48 PM] A A Dboy: *YAR TALLA*
*CHAPTER TWO 2*
Inna laure ta kwasa a juge tana fadin na shiga uku ta isa
bakin randa ta ciko tasa da ruwa taxo ta sheqa mata gaba
gaba daya yarinyar ta firgita ta tashi tana fadar wayyo inna
kiyi haquri mai dan wake ta riqeta ke yi shiru da allah aita
kyaleki
Inna laure ta sauke wani nannauyen numfashi ta shiga zare
na mujiya
Mai dan wake ta miqe tana fadin ni na tafi amman dan allah
laure ki dinga kula kisan irin dukan da zaki dinga musu don
karkije ki daure kanki da kanki
Inna laure ta sake jan kwaron numfashi kafin tace insha
allahu zan kiyaye mai dan wake ta fice abinta
Laure ta juya ta shige dakinta ta barsu a nan
Saude ta rarrafa ta nufi dan uwan nata
Wanda ke zaune ya hada kai da gwiwa yanata faman kuka
Saude ta raba jikinsa ta kwanta ya qara janta a jikinsa
sosai
Bata jima da kwanciyaba barci ya dauketa sai faman jan
ajiyar zuciya take
Akai akai
Malam bala yayi sallama ya shigo gidan nasa hannunsa
saqale dana iklima yarinyar da bazata wuce yar shekara
goma sha daya ba
Qanwar saude ce don ita yanxu tana shekara sha biyu ne a
duniya
Malam bala ya shigo tsakar gidan tare da miqama iklima
baqar ledar dake hannunsa ta karba ta shige dakin
mahaifiyarta tana tsallen murna
Malam bala ya kalli rabiu fuskarsa ba yabo ba fallasa yace
bakin munafiki kallon uwar me kakemin? Me mugun halin
tsiya hala wani abun kukai aka dakeku ko?
Inna laure ta hankado labule ta fito kamar an bankadota ai
daman jiranka nake malam wallahi yau saika biyani kudina
in dorama yarinyarnan tallah ta boye kudin wai tace an
kwace
Na rantse da allah ban daukar asara
Malam bala yace ai daman tunda na gansu zazzaune anan
nasan wata ta'asar sukayi
Yan iskan yara masu tsinannan hali wanda sukai gadon
Halin tsiya niko yarannan dada inda zan kai
Su wallahi dana kaisu na huta da bala,in su
Tace ahto nidai kudinane sai an biyani
Babu mai doramin asara alalata ta murtala biyuce da goma
Malam bala yace toya zanyi ai dole na biyaki tunda allah ya
hadani da jarababbun yaya
Kiyi haquri idan na dawo daga kasuwa gobe saina biyaki
miqomin buta nayi alwala
Laure taja kwafa ta juya ta koma dakinta ta dauko masa
butan ya nufi bayan gida
Ta watsama rabiu harara sannan ta wuce dakinta ta samu
iklima ta zazzage baqar ledar sai diban kilishinta takeyi
Ta miqa hannu zata dauka yar tasa kuka tana tirje tirjen
qafafuwa inna laure tayi saurin ajiyewa
Ga abinkinan sarkin rigima. Ai nasandai duk cinki baki iya
cinye wannan kilishin
Yarinyar ta turo baki irin na shaqwababbun yaya taci gaba
tacin abinta
Duhun magaribane ya fara ketowa sauro suka fara duduma
a jikin rabiu ya lallaba ya kwantar da saude saman siminti
Ya lallaba ya nufi dan akurkin dakinsu ya shinfida musu yar
yagalgalallan tabarman kaba irin mai cin jikinnan
Sannan ya dawo ya lallaba ya dauketa da qar
Ya kaita dakin ya kwantar da ita ita kadai ta mamaye
tabarman don haka shi saman simintin dakin ya kwanta
babu ko filo balle abun rufa
Ga duhun dakin. Ya runtse idanunsa dukda yanada yakinin
yunwace ke kwankwasarsa bazata barshi yayi barci ba
Tunanin mahaifiyarsu ya fado masa kamar yaddah kullun
yakeyi kafin ya kwanta
Wasu hawaye suka cika masa idanu masu zafi tabbas
yasan wahalar da sukesha somon tabice
Akan wanda mahaifiyarsu tasha a gurin mahaifinsu
Nasiharta gareshi itace ta dawo masa tamkar yanxu take
masa su tace
Rabiu don allah don annabi ko bayan raina. Ka kula da
rayuwar qanwarka karkabar rayuwarta ta gurbata a duk
halin da kuka tsinci kanku a ciki kaga ita mace ce dole tana
buqatar taimakon wani wanda zai jibanci lamarinta
Nasan kaima kana buqatar taimako amman a duk yanda
rayuwa taxo rabiu yinta ake
Nasan kodani ko bani dole ku rayu bakuda mataimaki sai
allah.
Rabiu kuyitayimin addu,a in rayu kodan saboda ku. Nima
inason in rayu sbd ku
Baisan sanda kuka ya kwace masa ba saida yaji saude
jikinsa tana jijjigashi.
Tace yaya kuka kake?
Yayi saurin hadiye kukan tare da goge hawayensa
Ya lalubo hannunta ya riqe kafin yace ba kuka nakeba
dariyace nake na tadaki ko?
Tace a,a yaya yinwa nakeji cikina sai cixona yakeyi tun safe
banci komaiba na tafi tallah har yanxu
Ya salam ya fada a fili sbd rashin sanin abinyi
Saude ta kwantar da kanta a kan cinyarshi tace kaji cikina
sai kuka yake ko yaya?
Bai tanka mataba ta qara girgizashi cikin muryar kuka tace
yaya abinci zanci
Rabiu ya kwantar da murya yace dakinyi haquri kin kwanta
kinga da safe ba saiki karya ba
Tace wlh bazan iya barciba yace to lallaba ki kwanta ina
xuwa
Ta zame daga jikin nasa sai shi kuma ya miqe ya fita
Duk suna kwakkwance a tsakar gida cikin gidan sauro sbd
lokacin zafine
Sai radio ce keta faman babatunta a banza
Rabiu ya lallaba sadab sadab ya isa har inda suke ya dauko
langar fura ya lallabo ya shigo
Dakin ya zauna yana fadin tashi saude ga fura na samo
miki kisha
Ta tashi da hanzarinta ya lalubo bakinta ya kafa mata
langar furar tasha iya shanta sannan shima yasha kadan ya
rage sauran ya lallaba ya tafi don mayarwa
Yana qoqarin ajewa kenan iklima ta farka tana fadin laure
zansha fura
Rabiu yai saurin durkusawa a wurin jikinsa nata faman bari
Inna laure ta tashi tana haska fitila da niyyar dauko langar
furar
Taga mutum a durkushe wuri guda
Ta fasa wani uban ihu wayyo allah malam baraw barawo
Malam ya tashi a firgice ya rarimo adda yana ina yana ina ?
Kafin ya fito daga ciikin gidan sauron rabiu ya kwasa a guje
yayi dakinsu yana famar rawar jiki
Malam ya fito yana ina barawon yake laure?
Tana rawar murya tace nan nan na ganshi duqe wlh
Malam bala yaja tsaki to idan nan kika ganshi yana ina ?
A,a ka. Haska mana ya dauko touc light ya tafi yana
haskawa har zuwa zaure ya dawo yana fadin kedinnan
Wallahi kinada matsala. Yanxu haka inuwa wani tsuntsun
kika gani kinxo kin rikita mutane da wani barawo
Laure tace malam nifa mutun na gani anan duqe
Yace to idan da mutum kika gani da ban ganshiba ko laya
yayi ya bata? Don allah ki koma ki kwanta kinji
Laure tace niko malam wlh bazan iya rintsawa ba don da
idona naga mutum nan tsugunne
Malam bala ya shige gidan sauransa yana fadin ai saikiyita
zama ke kadai
Sai a lokacin hankalin rabiu ya kwanta ya saki wata ajiyar
zuciya ya lallaba ya kwanta abinsa
Bai jima da kwanciya ba bacci barawo ya sacesa
Qarshe shida na safe laure ta hankado kofar dakin nasu ta
gansu sai sharar barcinsu kawai sukeyi wani takaici ya
kamata ta juya ta debo ruwa cikin kwanon sha ta daga
labulen ta sheqa musu a firgice duk suka tashi sukai wuqi
wuqi kamar ya,yan zakaru
Inna laure ta taba baki cikin masifa tace
Hmmmmm
Ya labarin
[1/7, 5:49 PM] A A Dboy: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[12:17PM, 02/02/2017] 馃檰馃徏鈥嶁檪@lh@ji馃檰馃徏鈥嶁檪: [1/8, 4:40 PM] I love my mum: *YAR TALLA*
*CHAPTER 3*
Inna laure ta tabe baki cikin masifa tace nan har lokacin barcin safe gareku?
Sannunku yayan hutu to saiku tashi
Kai kaje ka jido mana ruwa ke kuma kije ki share mana gida ki tafi kai markadan waina
Ta saki labulan ta juya tai gaba
Babu wanda yace komai cikinsu rabiu yadau jarka ita kuma tadau robar markaden ta fice babu alwala bare wanke ido
Rabiu ya jido ruwa yafi jarka goma
Saida ya ciccika komai na gidan sannan ya fara gyaran gidan
Saude ta dawo daga markaden tana hada wuta iklima ta fito riqe da kofin shayi da qaton biredi a hannunta
Saude tai saurin tashi daga hura wutar
Da take ta kalli iklima tana miqa mata hannu sanmin zo indan gutsira kadan kinji?
Rabiu yai saurin kwAbarta ke da,ala kyale mata abinta
Saude ta bata fuska nidai don allah zanci
Yace toki bari idan na samu kudi zan siyo miki
Ta qara bata fuska nidai zanci
Kullum saikace zaka samu kudi kuma ba samu kakeba
Rabiu yadan kura mata ido kafin yace insha allahu yanxu zan samu kinji?
Kai kawai ta daga masa yana juyawa ta miqama yarinyar hannu iklima tace ban badawa
Ta juya ta shige dakin nasu tana fadin laure wai kinji wai in san mata biredin ni kuma nace ban badawa
Laure ta hankado daki tana fadin au biredin yar tawa kike sama ido
Wato ta kawo miki keme cikin ci ki cinye ita kuma ta fadi ta mutu kenan ko?
Ta shaqo wuyan rigarta tana fadin dan ubanki kin sabacin irin wannan ne ?
Ko sAlon kici kiyita zawo yar banza kawai wuce ki bama mutane wuri ta hankadeta saidata fadi
Ta zuya ta kalli rabiu kai kuma zakaci gaba da aikin gabankane ko kuwa?ko zaka rama matane?
Bai tanka mataba ya duqar da kansa yaci gaba da sharar da yake
Ita kuma taja kujera ta zauna taci gaba da hada kullun wainarta
Malam ya kwalama rabiu kira. Ya ajiye tsintsiyar ya tafi
Ya watsa masa kallon banza kafin yace. Ungo ka bata munafuki wanda yai gadon mugun hali
Rabiu ya amsa jiki na rawa ya fice
Dan guntun biredi ne wanda bazai wuce gutsira biyu ba. Sai dan ruwan shayinda ba ko madara
Rabiu ya miqa mata ta karba cikin rawar jiki
Ta tura biredin duk a baki tana tauna da kyar sbd yaddah ya cika mata baki
Rabiu ya kalleta yace kisha a hankali kar kiyi amai bata kulashiba ta
Ta kafa kai ta shanye ruwan shayin tas tana lashe kofin
Inna laure ta kafa mata dundu wanda yasata amayo duk abinda taci yayo waje cikin takaici tace shegiyar yarinya mai kama da mayyah maqerin kofin zaki tando duk wanda kikasha bai isheki ba? Munafuka tashi kibar wurin kona haureki
Ta saka kafa ta tunkudeta
Saude ta kwasa da gudu ta nufi dakinsu tana kuka mai sauti
Rabiu ya rakata da kallo inna laure ta daka masa tsawa zakaci gabane kokuwa binta zakayi
Dan iska mai kama da igiyar shanya
Rabiu ya durkusa. Ya soma kwashe aman sautin kukan nata na tsinkulansa a kirji
Laure ta gama tuyar wainar ta kukkulla a farar leda naira. Biyar biyar ta zuba mata a cikin bokiti ta dauki ta goma ta miqama rabiu sannan ta kwalawa saude kira
Ta fito tana matsar hawaye laure taja tsaki au kukan kike har yanxu kenan? Baki bugu bane shiyasa tashi ki dauka gatanan ta murtala huduce kiyi maza ki dawo kinsan alala nanan tana jiranki
Saude ta durkusa ta dauki bokitin tana fadin ina tawa?
Inna laure tace eh lallai ai dadin sai yayi miki yawa kisha shayi kici waina ai dadin sai yayi miki yawa yar gidan uban waye ke a garinnan?
Batace komaiba ta lallaba ta wuce rabiu dake kusa da ita ya kamo hannunta ya damqa mata nashi wainar ta fice tana murna
Inna laure taja tsaki tace matsalarkace nidai ko suma zakadingayi sbd yinwa wlh tallah saika gamamin duk ayyukana dondai na rigada na fita haqqinka
Zakara kawai mai neman suna ka bada kwaya kaci tsakuwa
Bai tanka mataba yaci gaba da aikin nasa
Yana gamawa inna laure ta tattaro kayan iklima masu himilin yawa ta watsomasa ta wurgo masa kullin omo maza ka sabe mata kayannan
Rabiu ya durkusa yana tattare kayan bayansa na faman cijewa ya nufi bakin rijiya ya soma wankin
Malam bala ya fito daga dakin hannunsa riqe da wani dan takurerren buhu na zuwa kasuwa harya wuCe yadan dawo kadan yace kai rabiu idan ka gama wankin ka shiga daki ka tattaro nawa ya wurgo masa naira hamsin ga wannan nan kasai omo
Kuma banason wankin banza don wallahi na dawo naga basu fitaba komin dare saika sake wankesu kanajina ko?
Ya karba da hannu biyu gamida daga kai alamar eh
Saidaya kammala na iklimar gaba daya sannan yaje ya siyo omon talatin garin goma sugar goma
Yaxo ya jiqa saidaya kumbura sannan yasa suga ya fara sha
Baiyi cokali biyuba ya tsaya gamida kafama kofin garin idonsa ya cikoda hawaye
Wata rayuwa can ya tuno lokacin da mahaifiyarsu ke jiqa musu gari ta tasasu gaba shi da saude susha. Ita kuma ta zauna a gefe tana kallonsu
Ko cokali daya ba zatayiba duk kuwa da yinwar da zata tashi da ita ta wuni da ita
Tausayin mahaifiyar tasu ya dirsar masa ya tuno yar uwarsa saude yanxu haka yasan da yinwar a cikinta
Yaja numfashi sannan yaci gaba dashan garin
Laure ta giftashi kamar zata wuce don taka me yakeyi ganin garin rogone yasa ta wuceshi kawai ba tare data tankashiba
Shima kuma bai tankataba yasha garinsa ya rage sannan ya tashi ya tattaro kayan mahaifin nasa yaci gaba
Karfe daya na rana saude ta dawo daga tallar wainar tana aje bokitin laure ta miqa mata tiren alale idon yar ya ciko da hawaye wahala ya isheta
Ga wahalar yawo ga azababbiyar rana ga uwa uba yunwa ita kenan tallah ba dare ba rana
Har yaran unguwa sun nada mata suna da YAR TALLA ina kika fito tallah ina zaki tallah ina kika dawo tallah
Saude ta daura tiren saman kai wasu hawaye suka gangaro kuncinta laure ta tafa hannuwa na shiga uku
Muhammadu dan Abdullahi mezan gani ni laure ? Tallar ce bakyason zuwa to dawo ki ajiye ki zauna ki huta yar hutu zoki ajiyemin tunda baki zuwa
Saude ta wuce tana faman sharbar hawaye laure tace uhm hum yarinya kenan ai dama kin adana hawayenki don tallah yanxu kika fara alalata ta murtala hudu ce da goma ki dauki ta gomar kuma wallahi ragin sule idan kikayi a jikinki zan fanshe sannan ko kanxo bance ki dawomin dashiba
[1/8, 4:41 PM] I love my mum: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[1/8, 4:42 PM] I love my mum: *YAR TALLA*
*CHAPTER 4*
Tace kuma wlh ragin sule kikayi a jikinki zan fanshe sannan ban yarda da ki dawomin da ko kanxo ba anan muka tasaya
Saude dai bata kulataba ta wuce tana sharbar kwallah
Rabiu dake wanki ya tsame hannunsa daga cikin ruwan wankin ya dauko kofin garin ya bita da gudu
Ya jawo hannunta ya kaita kan dakalin wani kofar gida ya zaunar da ita gamida sauke tiren tallar a gefe ya zuba mata idanuwansa
Kukan me kike? Tallar ce bakyason zuwa?
Saude ta girgiza kai alamar a,a tana share hawaye da bayan hannunta
Rabiu yace idan ba tallar bace bakyason zuwaba to menene?
Taja majina tanata faman sheshsheqa kafin tace na gaji yaya kafata ciwo take gashi banida takalmi ga zafin rana fasona sai jini yake famanyi
Wani irin abu ya tsikari zuciyar. Rabiu ya tsirama kafar ido
Wasu hawaye suka cika a idanuwansa gashi bashi da ikon iya taimaka mata
Don shi kansa kafar tashi babu takalmi. Tabbas da tausayawa qaramar yarinya kamar saude tayi tafiya babu takalmi
Yaddah ake tsala rana yau ga uwa uba kafar duk ta tsatstsage da faso
Rabiu yasa yatsa ya goge kwallar data tarar masa muryarsa a sanyaye yace
Kiyi haquri kije insha allahu zan samar miki takalmin da zaki dinga sakawa dakin dawo kinji?
Ta daga masa kai ya miqa mata kofin garin ta karba ta shanye ta miqa masa kofin
Ya amsa ya karbi tiren ya dora mata ta tafi
Yana tsaye yana kallonta harta bace
Sannan ya juya ya koma gida
Laure ta watsa masa harara tace ni naci uwar zariyama ballentana bita zaizai
Bai tanka mataba ya duqa yaci gaba da wankinsa harya gama
Ya shanya wankin sannan ya nufi kofar dakinta ya durkusa daga waje
Inna na gama ina alalata
Inna laure ta dago daga kwancen da take saman katifa ita da yarta
Ta watsa masa wani kallo tace abincima wato har kaso biyu zaka dinga ci kenan
Koba dazun na giftaka naga naga kanacin garin kwaki ba? Dallah ni tashi ka bani wuri ta doka masa tsawa
Rabiu ya miqe tamkar almajiri ya nufi bakin rigiya ya janyo ruwa guga guda yayi alwala ya nufi dakinsu yayi sallar asuba da azahar a hade
Sannan ya kwanta nanfa gajiyar daya kwaso ta rufeshi
Saude tasha yawon tallarta harta godema allah amman alalar ko rabi bata samu ta saida ba nanfa idonta ya ciko da hawaye ta soma bin jama,a tana hadasu da Allah su siya
Danladi ya tabo abokinsa ilu kai baba yarinyar canfa tana cikin matsi ina yawan ganinta a cikin tasharnan anya ba zamu far matAba kuwa?
Ilu yace nimafa na dade ina wannan tunanin to amman abinda ke tsoratani yarinyar karamace sosai karkaje ka balloma kanka ruwa
Danladi yace kaiko da mugun baki kake idan zakaxo muje mu fasa kawai kaxo muje malam
Mu jata kangon alhaji sani
Ilu yace kuma hakanefa to taro mana ita ni bari naje na duba mana wurin na tabbatar da tsaro
Ya dire daga kan teburin da yake ya nufi gurinda saude take duqe gaban wani direban j.5 tana zazzage masa alala a kwano ilu ya iso waje yace ke yarinya idan kin gama sayar masa kikaima wancan gashi can zai siya tace to ta miqama direban alalan ya karba ya somaci ita kuma ta rabe gefe tana jiransa ya gama ya bata kudin da kwanon ta qara gaba
Direban ya soma ci gaya dago sai yaga ta kura masa ido ji take dama bakinta yakekai alalar sbd tsabar yunwar dake cinta
Direban yadan daga murya yan mata ya kike kallona ko na miki ne ?
Saude tayi saurin dauke kanta yayi daria yaci gaba da cin alalarsa
Karen matar dake can gefe yace sai oga baka tambayeta ko tana ciki bane
Yace kai share wannan bata inda ke mata dadiba
Karen motar ya sake bushewa da daria yace sai oga allah yabar mana kai
Baice masa komaiba ya qarasa cinye alalar ya wurga mata robar ta zabura ta miqe gamida saka kwanon cikin tiren ta qarasa inda yake domin karban kudin ya kura mata ido yaya akayine?
Tace kudin zaka bani
Ta nawace?
Saude ta numfasa kafin tace ta murtala daya da gomace
Yasa hannu a aljihu ya ciro kudi masu yawa ya dubeta
Yace yanxu idan na baki wadannan kudin zaki barni nayi lalata dake
Saude ta zaro ido tana kallonsa
Ya sake maimaita mata a karo na biyu
Idonta ya ciko da kwalla alamar zatayi kuka
Yace a,a meye abin kuka yanmata karbi kudinki kisan inda kikai kuma karna sake ganin kafarki ta tako inda nake
Idankuwa ba hakaba saina turmusheki
A wurinnan ya miqa mata kudin karbi ki wuce tasa hannu zata amsa hannunta na rawa ya hada hannun da kudin ya riqe yana dariyar mugunta
Meye sunanki yan mata?
Ta janye hannunta jikinta na rawa tabar wurin a hanzarce har tana tafka tuntube wani dan kamasho da yawo giftawa ta wurin ya tintsire da daria yana fadin dan baba kabar iya shege kabi Allah kaji
Ya miqe yana fadin kai garba mufa duniya gaba muka bata ba baya ba
Garba yace shegen sama kura taga biri
Allah ya kauda abin kunya
Yace ba aminba mu abin kunya binta muke tana guduwa Allah ka hadamu da abin kunya duk inda yake
Duk wurin sukasa ihu ana sai oga allah yabar mana kai
Ikon allah mai tsaida wando ba zariya saude dai bata sake bi ta kansu ba ta nufi inda danladi ke zaune saman teburin cikin tasha tace kaika aika a kawo maka alala ko?
Yace eh zubomin ta murtala biyu
Dadi ya kama saude don tasan daga wannan ta siyar tana murna ta zuba masa tasa masa mai da yaji
Ya zauna ya harde gamida lashe alalannen tas yana lashe baki
Saude na zaune tana kallonsa yana gamawa ya dubeta
Kinada canjin naira dubu?
Saude ta waro ido ita tunda takema bata taba riqe naira dubunba ballentana harta samo canjinta
Ta girgiza masa kai alamar a,a
Yace to ya za,ai kenan ko kuma xo muje na samo canjin saina baki kudinki
Ta mike ta tattara kayan ta bishi
Suka soma tafiya ganin suna shirin fita daga tashar yasa ta dubeshi tace
Ina kuma zamuje?
Yace ban gane ina zamujeba canji zan nema in baki kudinki
Saude tadanyi shiru maganar yayanta ya dinga dawo mata cikin kunne tamkar yanxu yake gaya mata
Saude ki kula banda aje tallah ki tafi samo canji banda kuma kibar mutum ya tafi samun canji shi kadai
Kuma karki sake ki yarda wani ya jaki zuwa wani guri koda kuwa nan da canne
Saude ta dubeshi a,a gaskia nidai kazo muje cikin tashar a samu canjin kaban kudina don yayana ya hanani bin wani
Ya hade rai jini da yar iskan yarinya sai kuma akacemiki kowa dan iskane. To karki bini ki karbi kudinki zauna
Ya wuce zai tafi hankalin saude ya tashi tasan kan kudinnan yau inna laure kashetane kawai ba zatayi ba tayi saurin riqo rigarsa tasa kuka
Nidai wlh saika bani kudina
Ya juya a fusace ya danna mata wani mugun zaki ke dan ubanki bazaki sakeniba? Ta qara cacimo rigarsa nidai wlh saika bani kudina idan naje gida a haka dukana za,ayi
Haushi ya kama danladi yasa hannu ya dauketa da wani wawan marin dayasa saidata kife. Ya juya zai wuce wani magidanci ya kwaso a guje yana kiran
Tsaya nan danladi karka sake ka matsa mugu mai kai mata?
Yayi saurin juyowa jin muryar ogansa
Gabansa ya fadi yai saurin juyowa yace wlh oga yar iskan yarinyace wai dan uwar yarinyarnan waini zata tsare nace
Nace taje ta samo canjin dubu tace babu nace muje na samo na bata taqi yarda toya takeso nayi da itane oga ?
Ya tallabo saude gamida fadin yanxu don rashin imani wannan yar qaramar yarinyar zakaima irin wannan marin?
Yanxu wannan yarinyar fisabilillahi meta sani?
Ya zaburo cikin irin muryar yan shaye shayennan yace oga zaginafa tayi yace idan ta zageka kai yanxu zagi nawa kai mata a gabana ko kunyata bakajiba
Yi hakuri yarinya kinji allah ya saka miki bani dubun na canja muku
Yadan sosa qeya a,a ai gurin ilu zan amso dubun na samo canjin mutumin ya girgiza kai yana fadin allah ya shiryeka ya zaro kudi cikin aljihu ya kalli saude. Kudin naki har nawane?
Cikin muryar kuka tace murtala biyu da goma ne
Ya girgiza kai ya bata sannan ya kalleshi na ranta maka ka samo canjin ka kawomin kudina
Dan ladi ya turo baki yana dan harare harare ya wuce kamar zaikai duka
Mutumin ya dubi saude yace wuce ki tafi kinji allah zai saka miki yace ai harda laifin iyayenku mata dake turoku tallah cikin maza basu san da irin mazan da zaku hadu ba don ko cikin masallaci zakukai tallah sbd tsoron allah sai an samu mutanen banza ballentana cikin tasha inda yayan banza ke taruwa wadanda daman can lalatattu ne ya za,ai ace bazai,ai barnaba fisabilillahi balle ke yarinya qarama
Wuce kije allah yayi miki sakayyah
Haka saude ta wuce gida jiki na rawa da yamma lis don tuni rana ta fadi a lungun gidansu ta hadu da rabiu cikin taron jama,a wai ana duban wata
Saude ta lallaba ta janyo hannun rigarsa yayi saurin juyowa yana kallonta yayi murmushi tana fadar
Tun daga nesa na hangoka duk ka keresu tsawo
Rabiu ya dungureta yana daria yace ke kuma sarkin sharri ko?
Daria itama tayi tana fadin anga watanne yaya?
Yace a,a munadai dubawane amman munasaran za,a ganshi kedai ki zauna da niyyar azumi gobe
Tace ai nima tsayawa xanyi yaya ka dagani inga watan
Yayi murmushi yana fadin so kike yau inna laure tayi kujera dake kenan ko? Ya riqo hannunta
Yace wuce mu tafi kinga har yara su fara tsokanarki
Saude ta juya taga dandazon yaran daketa tsalle suna waqa
Yar tallah qazama yar tallah bata wanka yar tallah bata wanki yar tallah bata sallah yar tallah saidai yawon tallah
Ta dago idonta cike da kwalla ta kalli yayanta tace aidai yaya ina sallah ko?
Kai kawai ya daga mata sbd yaddah abin ke sukarsa a zuciya ya daura hannunsa saman kuncinta inda shatin yatsu suka kwanta wurin yayi jajir abinka da jar fata
Muryarsa na rawa yace waya mareki haka saude?
Muryarta na rawa ta shafa wurin tace wanine ya mareni a tasha yaya wai don naqi binsa ya samo canJi
Rabiu yaja numfashi ai gara dabaki bishiba saude shida allah
Sai a lokacin ya lura da jinin daya kwanta a idonta yAja hannunta suka tafi yanajin zuciyarsa na suya fiye da radadin marin da taji
Suna shiga cikin gidan inna laure dake duqe bakin rariya tana tsane gero ta dago ganin kwanikan duk sun baci da qasa
Jar ubannan kai badai barin alalar kikaimin yauba ?
Saude tace a,a na saida wanine ya mareni harna fadi waidon naqi binsa ya samo canji
Inna laure ta daka mata tsawa ke gafara can munafuka tantiriya idan yace ki bishi ya samo canji to sai meye ?
Koyana iskanci dai ai bazaiyi da keba a balla qashi ko,a karya qafa bani kudina ni ki wuce
Saude ta warwaro kudin a habar zani ta miqa mata. Ta karba gamida kirgawa taga sun cika cas ta ninkesu ta soke akai
Rabiu ya dubeta dauki gora kije kiyi alwala kiyi sallah
Inna laure ta zaburo bazatayi
Maza ga kudi kije ki siyo icce ki daura sanwar tuwo kai kuma ka tattara kayan tallar ka wanke
Idon saude ya ciko da kwalla ta kafama yayan nata ido
Laure ta zaburo mata to yar iska gama kallon nasa kixo ki amshi kudin
Ko ubankima bai isa ya hanaki yin tuwonnan ba ballentana wani banza jaki can zakizo ki karba kokuwa sai naxo nayi miki dukan kawo wuqa?????
[1/8, 4:43 PM] I love my mum: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[12:17PM, 02/02/2017] 馃檰馃徏鈥嶁檪@lh@ji馃檰馃徏鈥嶁檪: [1/8, 4:44 PM] I love my mum: *YAR TALLA*
*CHAPTER 5*
Tace to yar iska gama kallon nasa kixo ki amshi kudin don ko ubanki bai isa ya hana kiyi tuwonnan ba ballentana wani banza jaki can zakizo ki karba ko kuwa?
Anan muka tsaya
Rabiu ya turata alamar taje ta karba
Laure ta maka mata rankwashi akai wanda yasata fasa wata uwar qara sbd azaba
Ta wurga mata kudin tana fadin munafuka nafa alamar watarana sai kin nemi kifi karfina a cikin gidannan
Dole saina gyara miki zama ta haureta da qafa
Zaki tashi ko sainaxo na casaki? Yar iska kawai lau yayyar banza kawai
Saude ta yinkura ta tashi gamida ficewa tana kuka
Rabiu ya rakata da idanu yana tausayin kansa rayuwarsu na bashi tausayi
A ganinshi babu yaran da suka taba samun kansu cikin halin kunci kaman yanda shi da qanwarsa ke ciki yanxu. Yace ya allah gamu gareka
Laure ta wurga masa murfin kwano ya zabura gamida dawowa hayyacinsa yayi gaba yana tattara kwanukan
Laure tace daka barta ta tafi kaita tunani ai gara ka bita can kuyita
Kwakwale kwakwalenku dan iskan banza da wofi kawai
Maganar ta soki rabiu yai saurin wuceta sbd yaddah maganar ta daki zuciyarsa matuqa ji yake kamar bata taba masa abinda ya qona masa zuciya irin na yau din ba
Saude ta dawo daga siyo iccen ta zauna ta hura wuta gamida daura ruwan tuwo a lokacin har ta fara sarewa da wahala a jikin murhun ta soma jinyar qafafuwanta ta samu daqar ta kammala tuwon da miyar kuka a bakin murhun taci tata ta miqe tayi alwala ta shige dan akurkin dakinsu domin jero sallolin da batayiba
Washegari aka tashi da azumi don haka saude ta samu sauqin wahalar sosai
Dukda aikace aikacen gidan da tayi itada yayanta bata wata sha wahala ba
Saida azahar inna laure tasata dauki markaden tiya uku aka kai markade aka markado shi ta sake daukoshi akai ji take tamkar wuyanta zai karye sbd nauyi
Data kawo markadenma qin sauke mata tayi ta barta dashi akai
Saude tasa kuka don allah kiyi haquri ki saukemin inna kaina zai karye
Laure dake zaune tana kwadon zogale ta dubeta a harzuqe kin fara ko? Wato nabar kwadon zogalen naxo na sauke miki sbd inajin tsoronki ko?
Ta maida kai taci gaba da kwadonta tana fadin bankadaddiyar yarinya masifaffiya
Iklima dake kwance gefenta tace laure bani ruwa insha karya azuminnan zanyi bazan iya kai azuminnan ba
Laure tace a,a ko aike kikasa kanki tuntuni nake fadin ki ajiye ki ajiye kikaqi waike sai kinyi.
Ta miqe gamida dibo mata ruwan cikin randa mai sanyi ta kawo mata ta miqe tasha iya shanta tayi wurgi da modar
Laure tace a!a mai makon ki bani in mayar sai kiyi wurgi da ita
Iklima tayi tsaki ta janyo kwanon kwadon dake gabanta ta soma ci
Laure taja kwafa sannan ta miqe ta dauko modar ta mayar sai a lokacin ta nufi saude data dafe wuyanta da takeji tamkar zai karye
Laure tace shin zaki tace ko na tace? Donna lura wuyanki ya isa yanka
Saude ta wuce ta nufi rijiya sannan ta dibo ruwan ta taceshi tas tana
Tana gamawa rabiu ya dawo daga markaden qosai
Da alamar shima a gajiye yake
Laure ta dubi saude maxa ki hadamin wuta ki hadamin kaskon suya ki hadamin murfi biyu dayan murhun kuma ki dora ruwan koko
Ba yaddah ta iya haka taci gaba da hada hadar hada wuta babu ko tausayawa
Laure ta soya kosai sannan ta sheqa koko cikin bokiti
Qarfe shida tace su dauka sukai makarantar malam hadi tasan almajirai zasu siya
Rabiu ya dauki kokon ita kuma
Saude ya dora mata kosan
Laure ta kwala musu kira suka dawo
Tace kuma ban yarda da ku daukarmin ko kayan sile ba kuje ku dawo kayan buda bakinku nanan zan ajiye muku suka amsa da to sannan suka fice
Cikin ikon allah kuwa suna zuwa ana kiran sallah
Alhaji bashir wani tsohon mai kudine a cikin layin yaxo zai shiga masallaci ya tsaya wurinsu ya zaro dari biyar ya miqawa rabiu yace ya kirga kosan da kokon ya bada sadaka,,,dadi ya cikasu shi kuma ya shige masallaci abinsa
Rabiu ya kirga kayan gaba daya na dari hudu da hamsinne
Yayima almajiran wurin sadaka da koko da qosan
Ana gama sallar alhajin ya fito rabiu ya fada masa ko kayan nawane yace tosu riqe canjin
Sannan yace musu kullun su rinqayin sadaka da koko da qosan zai rinqa biya
Ya zaro wata dari biyar din ya basu rabiu ya amsa cikin ladabi suka cika da murna
Alhaji bashir din yace kuma ku dinga diba kunaci kunji?suka amsa da to sannan ya wuce abinsa
Suma suka wuce gida rabiu ya canja kudin ya dauki canjin yankan da suka rage yaba laure sauran kudinta dadi ya cikata za,a ringa siyan kayana kenan kaga babu bandaro (kwantai) kenan ta dubi
Saude jiki maza ki dauko muku koko suka tsugunna a tsakiyar gidan tamkar almajirai sukasha sannan saude ta miqe ta dauko musu sanwar dimamen daya rage tun na sahur sukaci suka koshi duk da kuwa miyar kukar tayi tsami ta lalace amman a haka suka cinye tuwon tas. Gaskiane da hausawa sukace da babu kwara ba dadi
Sun gamaci suka tafi sallar asham a masallaci suna dawowa su duka suka kwanta a gajiye kamar matattu
Qarfe uku na dare laure ta tashesu wai su tashi susa sanwar tuwon saidawa na asuba
Saude tasa kuka saboda bacci da gajiya dake cinta
Laure ta haskata da cocila au kukama kika tsayayi kenan ni inanan ina jiranki?
To malam zoka gani da idonka saude na zagina
Malam bala ya zaburo tamkar shayayye
Zagi kuma laure wani irin zagi ba dadin ji?ya hankade labulen dakin ke ba magana ake miki ba yar jakar ubannan shine kika zauna kinama mutane kuka
Idanda uwarkice ta dawo daga lahira ta sanyaki aikin ai bazakiyi kukanba ko?
Fitonan inji wanda kike zagi
Saude tahau rantse rantse abinka da yarinta kuma ta rikice sai fadi take wallahi baba karya take ban zageta ba na rantse da allah ban zageta ba
Malam yace shin zaki fito ko saina shigo dakin?
Rabiu yace kayi haquri don allah baba wallahi bata zageta ba
Malam yace au karya tayi mata kenan?
Ta zabura ta boye bayan rabiu tana kuka tana bashi haQuri amman bai sauraretaba yasa hannu ya fisgota daga bayan nasa ya jata a qasa kiyyyyyyyy
Har waje ya janyo igiyar guga ya shiga laftarta ta ko ina bugu bana hankali ba baya ko duban inda zai doka sai ihu take tana roqonsa
Rabiu ya duqar da kansa qasa baya ko iya motsi hawayene kawai masu zafi dake diga daga idanunsa
Saida yayi mata dukan bala,I ya farfasa mata jiki sannan kuma ya tabbar da ko motsi batayi sannan ya kyaleta harya wuce ya dawo ganin alamun kamar ta suma yasa ya janyo ruwa cikin guga ya sheqa mata ta sauke nannauyen numfashi yace sannan ki tashi maza ki dora tuwon siyarwan don lokacin sahur ya gabato
[1/8, 4:44 PM] I love my mum: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[1/9, 9:55 AM] A A Dboy: *YAR TALLA*
*CHAPTER 6*
Saida yayi mata dukan bala,I ya farfasa mata jiki sannan
kuma ya tabbar da ko motsi batayi sannan ya kyaleta harya
wuce ya dawo ganin alamun kamar ta suma yasa ya janyo
ruwa cikin guga ya sheqa mata ta sauke nannauyen
numfashi yace sannan ki tashi maza ki dora tuwon
siyarwan don lokacin sahur ya gabato
Anan muka tsaya
Rabiu ya miqe ya rarrafa wajenta gamida jawota jikinsa
yana sharar hawaye baisan sanda wani irin kuka maiban
tausayi ya kubce masa ba saida yai mai isarsa sannan
Ya janyeta ya tafi hura wutan tuwon don daman ya iya
tuwon duk da ba sosai ba don tun yana yaronsa inna laure
ke sanyashi kafin saude tayi kwari amman abinda ba
aikinkaba har saude data girma daga baya taxo ta fishi
iyawa
Saidai yau haka ya zage bakin kokarinsa yayi tuwon da
miya laure ta murmula musu naira biyar biyar ta zuba
tuwon a baho miyar a bokiti gamida basu fitila
Rabiu ya dauki kwanon tuwon akai kana ya dauki na miyan
a hannu yace saude ta koma ta kwanta shi zaije ya siyar
har bakin tasha yaje dukda rashin kyan hanyar ya samu
wuri ya zauna inda yan garuwa direbobi da matasa ke zama
Acan yayi sahur dinsa daida akai sallar asuba sannan ya
dawo saidai bai saida duka ba
Laure tahau fada tsohon munafuki ai daman don mugunta
kaqi tafiya da sauden don kaje ka dawomin dashi
Inda kun tafi tare ganinta ai wanda baiyi niyyar siyabama
sai ya siya tunda yana ganin mace amman shine kai ka
kwasa ka tafi
Zan gani duk uban daya daure muku gindi a garinnan yau
zan ganshi don sahur din da za,ai na gobe da ita zakaje
Munafikin bazan da wofi wanda yayi gadon baqin hali insha
allahu qarshenku bazaiyi kyau ba
Yaddah uwarku ta mace a wulaqance kuma haka zaku bita
daya bayan daya
Rabiu ya ajiye mata bahon ya wuce zuciyarsa na faman
suya da tuquqi mai ciwo
Wasu irin hawaye suka dinga zarya a saman kumatunsa
Yana isa dakin tun kafin ya zauna ta zaburo ta nufo dakin
ta hankade labule saika fito munafukin allah kaxo ka jido
mana ruwa ka tashi wannan yar iskan taxo ta fara aikin
gida ita kuma aiba wani kuka ajeba da zaku kwanta kuyi
barci shikuma yai muku aikin gida maza ku taso
Rabiu ya goge hawayensa sannan ya tayar da ita zazzabine
fal a jikinta tausayinta ya kamashi ya kamata suka fito yana
nashi aikin yana nata har suka gama basu suka zaunaba
saida rana ta haske gari gaba daya
Sannan suka kwanta hakanma badon tasoba saidon babu
sauran ayyukan da zasuyi matanne amman da bata barsu
sun kwantan ba
Sun samu barci yakai na awa biyu kafin masifaffiyar ta
tashesu ta turasu markade daganan basu sake samun
zamaba har dare
Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin kunci da takura har
azumi yakai ashirin da tara kowa nasaran gobe sallah duk
inda ka gifta anata yankan kaji
Wasu natakai markaden abincin sallah inda su rabiu da
saude ke tsugunne kan dakalin dakinsu duk sun zubawa
inna laure ido wacce ke zaune a bakin murhu saman kujera
sai faman suyan naman shanu take
Iklima yar baba (sunan da take kiranta dashi kenan)sai
faman kaiwa da komowa take tana miqa faranti ana tsomo
mata
Suna tsugunne harta kammala suyar ta zuba cikin babban
langa ta juye man tayi daki tabar iklima zaune waje tana
yagar nama
Malam bala yai sallama niqi niqi da laidoji a hannunsa
Rabiu ya tarbeshi da sannu da zuwa ya miqa hannu zai
karbi kayan dake hannun nasa ya noqe yana fadin
A,a barshi kawai gyaramin tabirma kawai na zauna a bakin
dakina
Rabiu ya kwasa da hanzari ya gyara masa tabarman ya
zauna
Sannan shima ya koma wurinsa kamar daxun inna laure ta
fito daga daki tana fadin
A,a malam sannu da zuwa ya amsa yauwa laure sannu da
gida taja ta zauna kusa dashi
Mu muka samu kuma malam?
Ya watsa hakorannan kaman an watsa wake miya kamin
yace kayankune na amso muku daga wajen tela sannan na
qara biyawa ta kasuwa na qara hado muku sauran
kayayyaki wasu kudine nai sa,a wallahi akaimin biyan
bashinsu yanxunnan
Inna laure taja ledar tana fadin sannunka kuwa malam bari
mu gani
Ta janyo ledojin tana zazzagewa
Atamface soso yar yayi aka dinka mata ita da yarta kala
bibbiyu sai takalmi danko kowa guda guda sai tsakiya ta
wuya data hannu kowa da nashi sai gyale kowa da nashi
Dadi ya cika laure aiko saita rangada guda aiyiriri wallahi
tallahi malam ka biyamu allah ya qara budi kaji
Shi kuwa sai ji yake kansa na qara fashewa ji yake dada
akwai saura cikin aljihunsa daya qara zazzage mata
saboda yaddah ta kodashi
Laure ta yafito iklima dake zaune tanacin namanta
Iklima ta kwaso da sauri cikin doki ta zauna tsakiyarsu tana
daddaga kayan
Dadi ya cikata ta miqe tana gwargwadawa tana tsallen
murna
Saude dake zaune ta daga kai ta kalli yayanta idonta cike
da hawaye yaya ni ina nawa kayan?
Rabiu ya kalleta cike da tausayawa yace kiyi haquri kema
anjima zan siyo miki naki kinji?
Kai kawai ta daga masa hawayen da suka taru idonta suka
gangaro yasa hannu yana goge mata
Inna laure ta miqe ta tattara kayan ta shige dasu daki
shikuma malam ya dauki buta yai bandaki
Rabiu ya dubi saude murya qasa qasa yace bari inje in siyo
miki naki kinji?
Kai kawai ta daga masa ya miqe ya shiga dakin nasu ya
bude kayan qyaure ya ciro kudin da yake tarawa yan
hamsin hamsin din da alhaji bashir ya dinga bar musu ta
cikon koko da kosai
Tun farkon azumi har zuwa yau ya fito ya fice abinsa
Kai tsaye kasuwa ya wuce ya zaga sosai ya samo mata yan
kanti doguwar riga da wandonta naira dari bakwai sannan
ya siyo mata yar qaramar abayarnan mai hade da kyale
waddah akema laqabi da gemun shaidan lol ya siyo mata
wannan naira dari biyu da hamsin
Sannan yasai mata takalmin dari biyar
Daman kudin dubu dayane da dari hudu ya tara kuma ko
naira bai dawo da itaba don saima da aka biyoshi bashin
naira hamsin
Yayi sa,a daya dawo ba kowa a tsakar gidan don haka ya
wuce dakinsu kai tsaye
Saude na kwance tayi rigingine tana kallon sama daka
ganta zakasan tana cikin damuwa ya zauna gefenta yana
fadin tashi saude ga kayan na siyo miki
Ta tashi cikin doki ya zazzage mata kayan ta daddaga tana
gama gani ta fada jikinsa domin murna shima ya rungumeta
yanajin wani sanyin dadi na ratsa zuciyarsa
Ganin farin cikin qanwar tasa ya fiye masa komai a duniya
Washe gari itace ta kasance ranar qaramar sallah idan ka
duba jama,a sai hada hada ake kowa yana cikin murna da
farin ciki yara da manya
Kowa yana cikin sababbin kaya cikin tsabta da kamshi
Haka gidan malam bala shida matarsa da yarsa suna cikin
wadanda suka raya wannan rana sunsha kwalliya cikin
sabuwar sutura amman banda
Rabiu da saude
Don tunda garin allah ya waye suketa faman aiyukan gida
suna gama aiyukan kuma saude tahau kai abinci gidaje
yara sai tsokanarta suke qazama qazama yau abin ko
kadan bai dametaba sbd itama tasan yau zatayi tsabtar
kamar kowa itama zatayi kwalliyar da take ganin iklima nayi
ta shafa jan baki tayi kwalliya a fuska tana gama rabon
abincin ta zura guga a rijiya cikin rawar jiki don itama tayi
kwalliyarta tayi yawon sallah
Yan matan unguwar tasu sukai sallama da yawansu don
aqallah zasukai goma duk sunsha kwalliya ji take babu na
biyunta
Saude ta amsa musu sallamar dasuketa rerawa
Yar baba nanan?suka tambaya saude tace tananan a daki
suka wuceta suka shige ita kuma taci gaba dajan ruwanta
tana shirin wankane suka fito suna labarin zuwa masallaci
daganan su wuce yawon barka da sallah
Saude tace dan allah larai nima ku tsaya nayi wanka mu
wuce tare
Larai ta watsa mata wani kallo tabdijam waye zaije yawo
dake yar tallah duk nanma wacece qawarki? Tayi shiru tana
kallonsu
Salame tace ai sunanki ta kira kinga kenan kece qawarta
Larai tayi saurin fadar allah ya sauwaqe saidai ko yar
gidansu takebi yar baba yar uwarta yar baba ta turo baki
allah ya sauwaqe niba yar uwata bace yar tallar gidanmuce
yarinyama tace zata bini ba sai inci uwartaba
Lantana tace to a ware kowa ya ware muga wanda zatabi
kowa ya ware ya daddaure fuska
Saude ta hadiye kukan dake neman kubce mata tace ai
nima yara yanxu zanyi wankana insa sababbin kayan da
yayana ya siyo min inyi kyau
Yar baba tace ke matsa can kyan gidan ubanwa zakiyi
kullum sai qazanta jibeta da wani hancinta can sai kace
kajeren wando duk sukasa daria harda tafawa sannan suka
fice
Saude ta dauki ruwanta ta nufi ban daki tana fadin aidai
allah ne ya bani
Tayi wankanta ba soso ba sabulu don dama ta saba ta fito
ta shiga dakinsu batada ko man shafawa ballentana kayan
kwalliya
Don haka kayan kawai ta dauka ta sanya ta saka sabon
takalminta
Da gyalenta tayita juyawa dukda ba kallon kanta takeba
amman ji take tamkar babu wanda ya kaita haduwa
Rabiu ya riqe labule dariya ta kwace masa yaddah yaga
tanata faman juye juye sai kace mai rawa tayi saurin
juyowa
Tace yauwa shigo yaya wai don allah nayi kyau?
Rabiu yai murmushi mai hade da daria kamin yace aike
daman kyakkyawace qanwata ba kayanne zasu fito da
kyankiba kyankine zai fito da kayan kisha kuruminki insha
allahu indai ina raye saina fito da boyayyen kyanki a idanun
duniya dauko kusar can kixo in kwance miki kanki duk shi
ya bata kwalliyar
Saude tayi saurin dauko masa ya zauna ya kwance mata
tas ya sharce mata yasa tsumma ya daure mata shi ya
lulluba mata gyalen ta miqe zata fita
Sai kuma ina?
Tadanyi jim kafin tace waje zani yace to bari inci abinci sai
in sameki kofar me gari zan daukeki muje kiyi kallon sallar
Dadi ya kamata harda tsalle. Ta fice
Inna laure na zaune saman kujera tanacin soyayyen nama
wanda ko qashi batabamasu saudenba ballentana susa ran
tsoka
Cikin rudu da kidima laure ta dauki sallallami laila ha
illallahu muhammadur rasulillahi
Mezan gani yau ni laure saude zonan dan qashin ubanki
Ta zaburo ta shaqurota ta maqure uban waye ya baki
kayannan?
Yar iska kudina kike sata a gidannan ban saniba,,,
Ta dauketa da mari da qarfinta kokuwa maza kika farabi
iye?
Saude ta fara ihu tana kakari sbd shaqar da tayi mata
Laure ta hankadar da ita har kanta ya bugu da bango ta
shiga kwalama
Rabiu kira wanda tundata soma dukan nata yakejin kamar
ya hadiyi zuciya ya mutu sbd baqin ciki ya fito daga dakin
ya nufota yana fadin gani
Laure ta daukeshi da wani mahaukacin mari wanda ya
sashi dafe kunci ta nunashi da dan yatsa cikin bala,I bakinta
har kumfa yakeyi
Gidan ubanwa aka samu wannan kayan sata kukemin a
gidannan ban saniba?
Aiko sai laure tasa ihu yau na shiga uku na lalace abinda
nakeji a waje yau ya shigo cikin gidana ashe da yan fashi
nake zaune ban saniba
Lol
Su laure manya
[1/9, 9:55 AM] A A Dboy: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[12:17PM, 02/02/2017] 馃檰馃徏鈥嶁檪@lh@ji馃檰馃徏鈥嶁檪: [1/12, 5:44 PM] I love my mum: *YAR TALLA*
*CHAPTER 7*
Laure ta dauke shi da wani mahaukacin mari wanda ya sa shi dafe kunci, ta nuna shi da dan yatsa cikin bala,i
鈥淕idan uban wa aka samu wannan kayan sata: kuke min a gidan nan k0 kuma me?" Rabi鈥榰 ya girgiza kai cike da kunar zuciya ya girgiza kai alamar a鈥檃, ta hayayyako masa. 鈥淭o gidan uban wa ta samu wadannan kayan?鈥� Rabi鈥榰 ya hadiye wani abu da ya tsaya masa a. zuciya kafin ya fada mata. yanda a kai ya samu kudin tun kafin ya karasa rufe baki ta sake dauke shi da wani gigitaccen mari cikin zafin zuciya take fadar. 鈥淣i za ka dauka 鈥榶ar iska ni zaka nunawa iyakata, Karya kake Rabi鈥檜 baka isa ba wallahi tallahi kaci karya ka kwana da yunwa baka isa kaja daniba,yandanaga bayan uwar data haifeku kuma bazaku gagareniba, don haka ka taka a sannu wallahi idan kai wasa sai na rufe babinka a duniyar nan k0 sunanka babu wanda zai sake ambata a garin nan.
. janyo Saude ta shiga cire mata kayan tana fadin. 鈥淏an yi niyar ta sanya sababbin kaya ba, kuma kai baka isa ka sata sanya suba.鈥�
Ta cire kayan gaba daya ta hankadar da ita gefe ta wuce daki tana. faman huci.
Rabi鈥榰 ya runtse idanuwansa yana jin zuciyarsa kamar za ta fashe saboda baqin ciki da takaici
kukan Saude ya dame shi a zuciya ya tallabo ta a jikinsa ya wuce daki da ita, ya dauki kayanta masu datti ya saka mata ya ja ta a jikinsa ya rungume yana lallashinta.
鈥淜i yi hakuri ki daina kukan nan haka kinji 鈥� insha Allahu zan siyo miki wasu ki yi shiru kinji
' ban san yawan kuka
Da qyar ya samu ya lallashe ta ta yi shiru, har wani barci mai nauyi ya dauke ta sai ajiyar zuciya take saki akai akai, tausayinta ya dirar wa Rabi鈥檜. Tabbas bacin ita da ta rage masa yana ga da ya gudu ya bar garin, to idan ya gudu bai san halin da gudar qanwar tasa zata shiga ba, a dole ya zauna, dole zai yi hakuri ya ci gaba da fuskantar rayuwar dake tunkarar su.
' Ya runtse idanuwansa wasu irin hawaye masu zafi suka shiga zubo masa a idanuwa suna sauka saman kan Saude wacce baccinta ya yi nisa sosai. yasa hannu yana goge hawayen da suka Bata. masa fuska.
Haka rayuwa ta ci gaba da taflya babu abin da da ya cansa sai ma abin da ya qaru, kullum da wahalar dake kunno kai. A tallar Saude kuwa sai ma abin da yayi gaba.
Wata rana da safe Sande ta dawo daga markade
Ta zauna bakin murhu' tana hadawa Laure wuta, Malam Bala ya fito riqe da hannun 鈥榊ar Baba tana
sanye da sababbin kayan makmantar boko, koran wando da farar riga da koran kallabi da farar abaya, ta sha takalminta sandal da farar safa, ta goya jakar: goyan ta.
Saude ta tsaya da hura wutar tana kallon su cike da sha鈥檃wa yanda 鈥榊ar Baba ta yi kyau cikin sababbin kayan, har bata san lokacin da ta mike ta soma bin su ba don kar ma su Bacewa ganin ta.
Tinqis-tinqis ta ringa bin su har suka iso makarantar ba ta tsaya aka ba ta labari ba hae: cikin oflshin Head Master ta bi su ta yi tsaye tana kallon su.
Malam Bala suka gaisa da Head Master sannan ya gabatar masa da ita matsayin sabuwar daliba, shugaban makaranta: ya riqo hannun 鈥榊ar Baba yana fadin
鈥淎i tuni wannan ta wuce shiga aji daya dan ta kai shekara goma zuwa sha daya, sai dai a kai ta aji uku idan ma ta maida hankali sosai maimakon ta shiga aji'shida sai ta wuce fom one kawai.鈥�
Malam Bala ya shiga yi masa godiya, Head Master ya dubi Saude da ke tsaye tana zaro ido ya ce 鈥淜e kuma fa lafiya, k0 tare ku ke鈥� 鈥�
Malam Bala ya yi saurin juyawa yana kallon inda Saude take tsaye
Yasa sallallami ya mike yana fadin, 鈥淵anzu biyo mu ki ka yi 鈥榶ar jakar uba.鈥� Ya fizgo ta yana rankwashi yana zagi.
Head Master ya yi saurin miqewa ya riko shi yana fadin, 鈥楧on Allah ka yi haKuri Malam ka kyaleta yarinta ce kawai.鈥� _
Malam ya cw, 鈥淗aba, haba yanzu wace yarinta ce wurin wannan iskanci ne dai kawai.鈥�
Head Master ya ce 鈥淎鈥檃 kar ka ce haka kila abin ne ya bata sha鈥檃wa hala ita ba ta makarantar neko?
Malam Bala ya cc, 鈥淏a a sa ta ba ita talla take.鈥�
Head Master ya ce, 鈥淜ai abin nan yana ci mana tuwo a kwarya wai yanzu yarinya kamar wannan a kashe ta a kashe rayuwarta da talla, kullum muna fadakar da iyayen yara a kan su kula da hakkin. 鈥榶a鈥檡ansu a kan su don kiwo ne a gare su Allah ya ba su amma ba sa ji.
Wallahi mafi yawanci 鈥榶anmata wurin talla nw suke lalacewa, don a wurin talla ne yarinya za ta saurari maganganun da ba su kamata ba. A wurin talla ne yarinya za ta ji batsar da tunda take a duniya bata taba jin taba. A wurin talla ne yarinya ke sanin abin da ke faruwa tsakanin namiji da mace, ba tare da shekarunta sun kai ta sani ba.
Malam idan na soma karanto maka illolin talla sai mu kwana anan ba mu idar ba, sai kun je inda matatarar maza suke ka iske mace ta kawo talla kaji
ikon Allah, daga nan sai ka fara ganin namiji ya ci abu ya ce ba zai biya ba yarinya na ta bin sa yaqi ya bayar, ka ga ta riko rigar shi sai ya ba ta ya kwace, ka ga yana gudu tana bin shi daga haka sai ka ga kokawa ta tashi, wata rana sai ka same su suna wasan banza da zabgegen saurayi da gandareriyar budurwa mts!鈥� Mts! Ya ja tsaki cike da takaici yana fadin.
鈥淎bin dai sai gyaran Allah.鈥�
Jikin Malam ya yi sanyi ya yi wa Head Master sallama ya tisa Saude a gaba suka tafi yana jin wani abu na yi masa yawo a zuciya.
Yana yin sallama a gidan Laure ta yo kan su tana ' fadin, 鈥淚na ka kamo wannan watsatstsiyar yarinyar? Tun dazu nake nemanta na karade gaba dayan gidan nan ba ta nan tun dazu na gama waina hatta sandare ina nemanta."
Ta fizgo Saude da ke gabanta tana faman kuka, 鈥淚na ki ka je 鈥榶ar iskar nan? Yawace-yawacen bin ' mazan ne naki ya fara k0 Allah ya baki sa,a, wadanda ma suka fiki basu ci riba ba ballantana ke 鈥榶ar 鈥� tatsutsuwa, daga ki hura mini wuta ki sa qafa ki fice har in gama wainar ta sandare sannan ki dawo
Malam yace, 鈥楪askiya Laure ki qarasa ido kan yarinyar nan don yanzu Malamin makarantarsu 鈥榊ar Baba ya rinka gaya mini irin abubuwan da yaran nan ke yi idan sun tafi wurin talla ki rinqa ja mata kunne
Wallahi kar taje ta dauko mana abun kunyar da ba zamu iya saukewa ba."
Laure: ta ja tsaki tana fadin, 鈥淵o 鈥榶arinya Ma : ta sake ta kwaso abun kunyar ai sAi ta san inda ta nufa, don wallahi korarta za mu yi daga gidan sai dai ta nemi wasu iyayen."
Malam yace, 鈥淕aya mata dai.鈥� Yasa kai ya shige dakinsa.
Laure ta haure ta da qafa, 鈥淭ashi ki sauki tallar ki tafi muguwa kuma Batan sisi kikai min sai na ci ubanki cikin gidan nan kin dai san halina ba ni da kyau ba ni da dadl wallahi." 鈥�
Saude tana kuka ta duka ta dauki wainar ta fito tana sharar hawaye. A waje su kai karo da Rabi鈥榰 yana ta bunzuma sauri yana ganinta ya nufo ta.
鈥淪aude ina ki ka je ana ta neman ki ba inda ban jeba cikin unguwar har kin tada mini hankali.鈥�
Saude tasa bayan hannunta tana goge hawayenta tace, 鈥淎i Baba na bi zau kai 鈥榊ar Baba makarantar boko shi ne da muka dawo Inna Laure ta doke ni.鈥�
Rabi鈥檜 yace, 鈥淭o ke in ban da abin ki me ya: kaiki bin su Baban na dai san ba cewa ya yi ki raka shiba ko?
Taqara share hawaenta tana fadin 鈥淓h, ai ni na bisu Yaya ina san makarantar in tafi can yanzu?
Rabi鈥檜 yace, 鈥淗aba Saude ya za ai ki tafi
kowa sanya shi ake baki ga ita ma Baba ya sanya taba?鈥� 鈥� Ta ce, 鈥淭o, kai ma ka sanya ni yanzu.鈥�
Ya dan yi shiru yana nazarin wasu al鈥檃mura, Saude ta riqo hannunshi tana girgiza shi, 鈥淒on Allah nima ka kai ni ka ji Yaya?鈥�
Ya tsura mata ido yana kallonta zuciyar shi cike da al鈥檃mura masu yawa yasa hannu ya dafa kanta cike da tausayawa ya ce, 鈥淜i yi haquri Saude insha Allahu za ki yi karatun boko, duk rintsi sai na ga kin yi ilimi dole zan cika burin mahaifiyarmu Saude kullum maganarta a kan karatunki ne insha Allahu zan cika mata wannan burin, dole zan nemi kudi k0 dan saboda kek0 dan saboda rayuwarki insha Allahu ba zan bari rayuwarki ta lalace ba, ki je tallar l
Ki dawo kin ji?鈥�
Kai ta daga masa ya sake ta ta wuce sannan shima ya kama hanya ya yi gaba .
Al鈥� amarin ya damu Rabi鈥檜 matuqa a zuciya yana san Kanwar shi ta yi karatu k0 dan wata rana ta taimaki kanta da kanta, koda baya raye tunda Allah kadai ya san gawar fari. To wacce sana鈥檃 ma zai yi yanzu a duniya? Tunanin da ya fado masa kenan, in dai ba ya rinqa' sana鈥檃r Baban Bola ba, sai dai ita wannan sana鈥檃r dole sai kana da jari a hannu ka rinka tara naka kana siyan na wasu kana
hadawa. Ya ja numfashi sosai yana nazari, can abokinsa Halliru Maigini ya fado masa.
Tabbas shi ya kamata ya nema don yanzu ya tabbatar yana da qarfin da zai iya sana鈥榓r ginin, ya mike daga kwancen da yakw: ya fito ya yi gaba, yana jin Inna Laure na Kwala masa kira bai kula ta ba, don yanzu yanda yake jin zuciyarsa idan ta ci gaba da takurawa rayuwarsa gab yake da daukan mataki (Namiji kenan).
Cikin sa鈥檃 kuwa yana zuwa wurin abokinsa ya raka shi har 鈥渨ajen mai gidansa ya amince ya karbe shi ya sanya shi cikin yaransa masu nazari da koyan aiki yace zai rinqa ba shi dari biyar duk safiya, amma ban da ranar da ba a fita aiki ba. Dadi da murna suka kama shi a ganinsa yanzu ya samu sana鈥檃r da zai taimakawa rayuwar Kanwar tasa da ita, don haka har ya qagara gobe ta yi don ya fara . zuwa aikin shi ma ya ga yana rike naira dari biyar tashi ta kan shi. Mahaiflyarsa ta fado masa a rai, wayyo ina ma tana raye tabbas da ya zamo daya daga cikin 鈥榶a'ya masu kyautatawa iyayensu.
Kukan Saude ne ya dawo da shi daga duniyar tunanin da ya lula ya zabura da sauri ya yo waje, ya iske Inna Laure zaune ta dora qafafuwanta kan ta tana ta mintsini ta ko鈥檌na ita kuma sai ihu take, tana roqonta.
Rabi鈥檜 ya jingina da bangon dakinsu yana kallon muguntar da take mata 鈥榶ar Baba ta ruga ta dauko bakin wuta ta mikawa uwar tana fadin, 鈥淜arbi ki dake ta Laure.鈥�
Rabi鈥檜 ya dauke idanuwansa ba zai iya kallon wannan muguntar ba. Sai da Laure ta tabbatar ta yi mata burdun-burdun da tabbuna sannan ta sake ta ta haure ta tana fadin
鈥楾sinanniya 鈥榶ar iska gobe ma idan halin ki ne ki sake Batar min da kudi.鈥�
Saude ta kwaso da gudu ta fada jikin Rabi鈥檜 tana ihun kuka ya ja hannunta suka nufi dakinsu, ya zaunar da ita gaban shi yana lallashinta, yasa hannu yana goge mata hawayen, mur鈥榶arshi a sanyaye yake magana
鈥淜iyi haquri Saude kidaina kuka kinji insha Allahu komai ya kusa zuwa qarshe nan ba da jimawaba
komai zaizama tarihi,yanzu haka nasamu aiki gobe ma zan fara zuwa, share hawayenki nan ba da jimawa ba wadannan hawayen zasu daina zuba kinji?鈥�
Ta daga masa yana gage mata hawayen ya ce, 鈥淭o ki yi murmushi mana kobakiji dada bane?鈥�
Dariya ta shiga qalqalawa tanayi kamar wata tababbiya shi kan shi har ta ba shi dariya ya dungure mata kai yana daria itama tace ala dole saita rama.
Lol kuma sance dani donjin yaddah laure da rabiu zasu kaya
Naku har kullum
Dboy
[1/12, 5:44 PM] I love my mum: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[1/15, 6:40 PM] I love my mum: *YAR TALLA*
*CHAPTER 8*
Rama ya rike hannuwanta duka da ta yunkuro zata dokeshi sai ya tura hannun ta daki kanta, ya yi tayi mata dariya.
Sun shagala sosai kuma kana ganin suka san suna cikin nishadi ba su ankara ba sai dai suka jiyo muryar Laure na fadin
鈥淪annun ku 鈥榶an iska watsatstsu, taBarar ceta motsa kenan shi yasa aka shiga daka k0 jin kira ba ayi dakyau aikana qoqari gara kayi amankaka lashe abin ka, ka ga tuwanka manka kenan. Kuyi iskancin ku san ranku babu mai hana ku, ai dama barewa ba tayivgudu danta ya yi rarrafe ba gado kuki ai dama abun, kun tsotsa,ne ku yi sha鈥檃ninku kun ji.鈥� Ta = saki labulan ta juya ta yi gaba. Rabi鈥檜 ya girgiza kai yana jin tamkar zuciyarsa
Zata fashe saboda bakin ciki, idan akwai abin da ke
daga masa hankali duniya ya dungunzuma masa lissafi to bai wuce a tuna masa abin da ya faru a * baya ba, wanda ke daga masa hankali ya dagula masa lissaii duk wata annashuwa ta shi take take Bacewa Ya jingina da bango yana kallon Saude ya jirkita ta kwanta jikinta a sanyayc. 鈥� Washe gari tunda safe Rabi鈥檜 ya yi jidar ruwansa gamida duk wasu aikace-aikace da ya san zai yi qarfe takwas daidai na safe ya sa kai ya fice abinsa b tare da ya fadawa kowa inda za shi ba.
Saude ta dauki taller wainarta ta tafi sarfiyar yau jikinta jinshi take babu dadi ko kadan da kyar ta samu ta iya saida wainar a hanya ma amai sau biyu tanayi harta samu ta iso gida da kyar, ta mikawa Inna Laure kudin tana neman faduwa, saboda juwar da ke
barazanar kayar da ita. Inna Laure ta zuba mata idanuwa cike da jin haushi kafin ta ce.
鈥淲annan lambon kuma na mene ne kl ke faman yi? Duk na kar ki dauki taller alalan ce k0 me?鈥�
Saude ta girgiza mata kai alamar a鈥檃 tana nishi. Inna Laure ta ja tsaki tana fadin 鈥淭o sai ki wuce ki dauka ga alalan can ta Murtala shida ce da goma
Saude ta langwaBe kai cike da jin jiki ta ce, 鈥淜i yi hakuri don Allah Inna wallahi ban da lafiya bazan iya ba.鈥�
Inna Laure ta waro ido waje tana fadin, 鈥淯ban me ki ka ce? Ni ki ke fadawa ba ki da lafiya Saude? To Allah yasa mutuwa ki kekina dawowa wallahi sai kin dauki tallar nan, 鈥榶ar iska na lure kwanan nan wani tashan balagar tsuntsaye ce ke cin ki, kuma wallahi zan tatsiye miki ita tas za ki tafi ki dauka ki bani wuri k0 kuwa?鈥�
Saude ta wuce tamkar wadda ta yi ciwon shekara goma ta dauka ta fice, tana tafiya tana hutawa k0 ta sule ba ta kai ga siyarwa ba ta zauna saman dakalin qofar wani gida tana faman kakarin amai numfashinta na fita sama-sma tun tana sanin inda
Har ya kai ta flta hayyacinta ta fadi can gefe sime.
Wani mutum da ke tahowa ta Iayin cikin shirin masallaci kasancewar yau Juma鈥檃 ce ya yo kanta a gigice ya jijjiga ta amma ba ta k0 motsi, kafin ka ceme mutane sun taru a kanta ana ta tambayar wanda ya san ta, amma babu saboda kullum dai ana ganinta
tana wucewa babu wanda zai ce ga daga unguwar da take tahowa, tun kafin a tafi masallaci har aka dawo sallar Juma鈥檃, amma ba a samu wanda ya san unguwar su Saude ba.
Yamma liqis Rabi鈥檜 ya dawo daga wurin aikinsa ya yi dumu-dumu da yashi da suminti kana ganinsa kaga mai aikin Kasa, ya yi sallama ya shiga gidan. Laure da ke zaune a bakin rijiya ta dago tna kallonsa ya giftata zai wuce ta zabura ta mike ta cimimiyo rigarsa tana fadin
"Daga gidan uban wa ka ke dan iska tun safe ina gararin neman ka rumfa-rumfa ban gan ka ba daga ina kake?鈥�
鈥淒aga wurin aiki.鈥� Ya ba ta amsa kai tsaye
Laure ta maimaita, 鈥楢iki. Aiki fa ka ce? Eh lallai Wuyanka ya yi kwari wato harka san ka kakkare
Ka tafi wurin aiki, tabbas lallai wata rana sai ka
Shaqeni shi kenan jeka jeka kawai." Ta fada tana . murmushi
Rabi鈥檜 ya wuce dakin su kai tsaye ya cire rigar ya kwanta saboda gajiyardaya kwaso ga shi abinda ba ka sababa. A take bacci barawo ya sace shi, kiran salla ne ya farkar dashi
Ya tashi a gigice saboda rashin ganin Saude ya fita tsakar gidan amma batanan abinda batataBa ba yanufi kofar dakin laure ya duka daga bakin qofar muryarshi da alamun rudani yace, 鈥淚nna ko $aude tadawo?鈥�
Laure ta watsa masa wani kallo kafin tace,鈥淏an saniba tana indata dawo da baka gantaba Ko kudice dazan Goyata?鈥�
Gaban Rabi鈥檜 ya yi mummunar fad'uwa hankalinsa yayi masifar tashi.To inatake?
鈥淪hin ba zaka tafi kanemota baneba zakatsaya kallon jama鈥檃 ne?鈥� Muryar mahaifinsu ta katse masa dogon tunanin dayake ciki
Ya yunkura ya mike jikinsa asanyaye yafice.'shin ta inama zai fara neman nata ne? Wayyo Allah Ya Ubangiji kada kajarabeni da abinda bazan iya daukabaYaAllah kasa duk inda Saude take tana hannu nagari.
Abinda yake fada kenan azuciyarsa,yayanka yayi hanyar rewa
Tasha dukda yanada yaqinin zuwa yanxu an rufe tashar amman babu yaddah zaiyi yanashan kwanar layin nasu ya
Ci karo da jama鈥檃 wani na rungume da Saude wai za,a kaita gidan mai unguwa.
Hankalin Rabi'u ya yi masifar tashi ya tsare su yanavfadin qanwarsa ce su kai masa 鈥榶an tambayoyin da za su yi masa sannan suka ba shi ita ya nufo gida hankali tashe tun a hanya yake ta faman rusar kuka don shi duk a tunaninsa mutuwa ta yl.
, Yana shiga gidan ke Laure ta zabauro masa wai ina kayan tallarta, ita ta sana鈥檃arta take ma. Wani_abu ya zowa Rabi鈥檜 iya wuya yanda ko kadan mahaifinsu bai damu da halin da Sauden ke ciki ba. Ya shimfideta a tsakar gida jikinsa na rawa ya nufi rijiya ya janyo ruwa ya shiga Sheqa mata, cikin ikon Allah ta farfado m har tana magana, ko motsin kirki ba ta yi, saidai sambatun datake tyi iri irin wanda ya zare hankali
Rabi鈥檜 yana kuka ya nufi dakin mahaifin nasu ya durqusa gabansa yana fadin, 鈥淒on Allah Baba ka ba ni kudi in kai ta asibiti ta farfado, amma ba ta motsi kada ta mutu.鈥�
Malam Bala ya ce 鈥楻abi鈥� u ta mutu mana, ai ranta ba a hannuna yake ba, ban da ikon sanyawa ta rayu haka kuma banda ikon hanata kaxo sai wani rawar jiki kake akan ciwon d bai taka kara ya karyba
Don nasan baxai wuce bugun iskaba da masassara
Ka je ka kira Malam Maidala yaxo ya yi mata rukiya ga naira hamsin ka siyo panado ka bata ta sha.鈥� Ya wurga masa kudin.
鈥淭ashi ka tafi.鈥�
Rabi鈥檜 ya mike yana jujjuya kudin a hannunsa wani sabon kuka ya Kara kwace masa ya sa kai ya fita, kamar yanda ya ce haka ya je ya kira Malamin yazo ya dubeta shida kan'shi yace ba iskabane zafin zazza6i ne, don haka a kai ta asibiti. Ya dawo ya sanar da mahaifin nasu, a lokaicn har ya kwanta. _
Don haka a fusace ya tashi yana fadar, Wai menene zaka dame ni da zarya shin wai nina dora mata ciwon ne k0 k0 me?鈥�
Rabi鈥� u yace, 鈥淜ayi hakuri Baba, Malam ya ce ciwonta na asibiti ne zazzaBi ne mai zafl.鈥�
Yace 鈥楾o shine har saika tadani ina baccina, tunda yafada maka zazzabine kaje katsinko ganyen dalbejiya kai mata surace mana, haba ban san matsawa wallahi.鈥�
Rabi鈥檜 ya mike jiki a sanyaye hawaye na faman zarya a kuncinsa, tsanar mahaifin nasu ta qara mamaye masa zuciya gaba daya. A lokacin karfe sha daya na dare ne haka ya shiga dakin ya dauki Saude a kafada ya tafi chemist da ita.
A lokacin Bala mai allura鈥� na' qoqarin rufe , chemist din nasa Rabi鈥檜 ya dube shi, 鈥楧on Allah
Malam Bala marar lafiya na kawo na ga kana kokarin tashi.鈥�
Mal. Bala ya waigo yana kallonsa kafin ya ce, 鈥淎shshal Waye ba shi da lafiyar?鈥�
Ya ce 鈥榃allahi Saude ce tun dazu zazzabi ya
kamata hadda su suma, yanzu haka k0 motsi bata 鈥漼i
Bala mai chemist yace, 鈥淎shsha! Ai kasan ni ban san sunansu na gaskiya ba, 鈥榊ar Baba k0 鈥淵ar Tallar wacce cikinsu?鈥�
Rabi鈥檜 ya' dan ja fasali kafin ya ce 鈥榊ar tallar dai鈥�
Bala mai allura ya ce 鈥業kon Allah, saukota na ganta.鈥� Rabi鈥檜 ya sauko ta yana nuna masa har a lokacin sambatun ta kawai take.
Bala mai chemist ya ce 鈥淎i wannan zafin zazzbine wallahi maleria, wato zazzaBin cizon sauro, gaskiya Rabi鈥檜 ku gaggauta kai ta asibiti don Wannan ciwon bana zama bane hadari ne babba dole ana buKatar likitoci. kamar biyu zuwa uku a kanta.鈥�.
Hankalin Rabi鈥檜 ya Kara masifar tashi ga shi bai ajiye ba, bai ba wani ajiya ba, nairarsa dari biyar ta aikin yau, ita kadai yasan ya mallaka sai hamsin dinda Baba ya ba shi. Ya dubi Bala mai allura yana fadar.
鈥淒on Allah Malam idan da akwai taimakon da zakamin ka taimaka min ai mata kafin zuwa safe na
ga abin da Allah zai yi, amma wallahi yanzu ban da halin tafiya asibiti 鈥�
Bala mai allura ya ce鈥楢i babu wani taimakon da zan iyayi yanzu anan nafada maka hatsarine a wurina na duba ta cikin wannan yanayi da take ciki.鈥�
Rabi鈥檜 ya kifa kansa a ka Saude yasa wani irin kuka mai ban tausayi, ya zai yi da rayuwarsa tunda baidashi baidawada zai taimakamasa yana kallo rayuwar 鈥榶ar uwarsa za ta salwanta, saboda kawai ba shi da shi... Kuka yake sosai.
Sosai kamar ransa zai fita
I will be back in no time
Via Dboy馃憤馃徎
[1/15, 6:40 PM] I love my mum: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[12:17PM, 02/02/2017] 馃檰馃徏鈥嶁檪@lh@ji馃檰馃徏鈥嶁檪: [1/17, 7:43 AM] A A Dboy: *YAR TALLA*
*CHAPTER 9*
We miss 1page cours d page is damage I cnt c writting
clearly
Rabiu ya shiga mazaunin direba ya ja suka tafi. Kai tsaye
Federal Medical Center suka nufa a lokacin har shabiyu na
dare,ne da 鈥榶an mintuna.
Suna zuwa kuwa abin kada ma'aikacin wurin
cikin gaggawa aka wuce da ita Emagcncy Room da ita,
Malam Bala mai allura ya tsaya sai da ya kammala masa
duk wasu 鈥榶an shige da ficen daziayi masa sannan yayi
masa sallama ya tafl office don dama aikin dare yake.
Rabi鈥檜 ya dinga zabga masa godiya kamar zai kwanta
masa, abin har ya soma bashi kunya. 鈥� A asibitin suka
kwana washe garida safe likitan daya dubata yaace yakoma
ya tawo da 鈥榶ar uwarta mace ta kula da ita, hankalin Rabi鈥檜
ya tashi ya ce, 鈥淎i bata da 鈥榶ar uwa.鈥� Likitan ya ceto gaskiya
ba zaiyiwu zamanka wurin jinyaba dole saika samu mace
yar uwarta koma wacece wadda zatayi jinyarta
A dole Rabi鈥檜 ya mike ya tafi zuciyarsa na faman suya, ya
nufi gida a qafa a lokacin karfe takwas 'na safe Yana isa
gidan ya samu Babansu a gidan ya duqa ya gaisheshi
yawaigo cikin Bacci yana kallonsa kafin ya ce
Rabi鈥檜 ka cika dan kanka yanzu gidan uwar wa ka kwana?鈥� .
ya sassauta murya kafinn ya ce 鈥淣a kai
Saude Chemist ne daga nan mai Chemist din ya ce
yana taba ta yace wai dole sai an kai ta asibiti shine ya
daukemu yakaimu asibin acan:aka kwantarda ita,yanzu
haka ita tana can asibitin tama samu sauqi sosai, don har
tana iya gane wanda ke kanta鈥�. Yanxu likitanne ya ce in'zo
in taho da 鈥榶ar uwarta mace, wadda za ta yi jinyarta.鈥�
Kafin Malam yace wani inna laure ta hankado labule ta fito
tana fadar. 鈥淎i k0 sai ka nemi 鈥榶ar iskarda zata zauna
zaman jinyar badai laure ba donni hangar asibitinma banabi
ballantana in wuce ta gefensa, miyau wannan ban iya
hadiya cikin asibiti, don haka ma kar ku sake ku sani a
lissafi
Malam ya ja ihsali kafin ya ce 鈥楴i duk ba ma wannan ba
Laure, shin kudin da za a biya a asibi'n ubanwa ya ajiye
zaibada nidai banidasu kuma ban ajiye ba, nan na ce kar ka
kai ta asibitin nan ammadayake kaibadan arzikibane shine
saida kakaita don kanunamini iyakata. Totundakai
dankankane basai kayi yaddakasoba,鈥榥idai kaga tafiya ta
kwandala ban maganinta.鈥� Yana gama fada ya juya ya fice
Laure ma ta hankada labule ta shige dakinta ta bar shi nan.
Rabi鈥檜 ya mike jikinsa amace ya rasa inda zai saka
Kansa haka yayita gararamba a gari data qarshe da yaga
vashi da mafita
Dole ya juya ya koma asibitin
Lokacin da rabiu ya gama koro masa bayani Mamaki ya
kama, likita yace ynxu yarinya kamar Saude a kasa samun
wanda zaiyi Jinyarta 鈥榖a shi da mafita haka ya. Rubuta
masu sallama aka ba shi allurai da magunguna
Ta ji sauki sosai, dukda ba Karfi jikinta sosai. Suna dawowa
gidan laure ta watsar dasu watsar k0 kallonsu batayiba
Rabi鈥榰 ya dauki naira hamsin ya fita ya siyo mata shinkafa
da wake da mai da yaji ya zauna ya ba ta ta ci sosai,
.sannan ya ba ta magungunanta ta sha, ba ta jima ba bacci
barawo ya sure ta, shi ma ya raba gefe ya kwanta
Washe gari tunda safe laure ta hau tuyar waina markadan
ma da kanta ta kai shi, mamaki ya kama Rabi鈥檜 to wa take
tunanin zai daukar mata tallar wainar?
Ba ta tankawa kowa ba har sai da ta gama tuyar . Wainar ta
daddaura sannn ta mike ta nufi dakin da suke Saude ce
kawai zaune tana shan ruwan shayi da biredin da Rabi鈥檜 ya
siyo mata a waje.
Laure ta tabe baki kafin ta ce, 鈥淎ikin banza harara cikin
duhu da kuwa cikin babbar riga, saiki tashi ga tallar waina鈥�
can na jiran ki idan kin gama
Saude ta yi saurin dagowa tana kallonta idonta ya kaWo
kwalla Laure ta daka mata tsawa.
Ko ba za ki tallar ba ne kika noqe kika kwalala min鈥� Wasu
鈥榶an iskan idanuwan ki can masu kama鈥� ;
Dana kwarkwata, maza ki taso ke nake jira.鈥� Ta saki
labulan ta juya ta yi gaba abin ta.
Hawayen da suka taru a idanuwan Saude suka ziraro suka
biyo kuncinta take shayin ya fita daga ranta ta ajiye ta mike
ta flto har a lokacin babu Karfi ajikinta, donji take tamkar
iska za ta dauke ta.
Inna Laure ta miko mata tiren wainar tana fadar, 鈥淕a ta nan
ta Murtala goma ce ki kawo min kudina cas ban ceki Batar
min da k0 sile biyar ba.鈥�
Saude ta duqa ta dauka tana sharar kwalla, Rabi鈥檜 daya
shigo ya sauke jarkar ruwan da ke kansa yana kallonta
jikinsa a sanyaye ya ce, 鈥淚na kuma zakije keda bakida
lafiya?" ,
Laure ta hayayyako masa -鈥淭o marar kunya ga kai ga fata
ai ba a tambayar me aka yanka k0 idon ka bai gane maka
talla ta dauka bane?鈥�
Rabi鈥檜 ya hadiye abin da ya zo masa iya wuya ' kafin ya ce
鈥淎 gaskiya daukar alhakin zai yi yawa, yarinya daga
sallamo ta daga asibiti jiya, yau kuma a daura mata talla
gaskiya da sake ai ba ita kadai ba ce diya cikin gidan nan
ba, ita ma 鈥榊ar Baban ai ta isa tallar a dora mata mana k0
k0 ita kadai ce diya,
amfanin nawa ake mata a cikin kudin tallar?鈥�
鈥淓h lallai wuyan ka ya isa yanka, tabbas wato kai nan har
girman ka ya kai ka fada mini magana. To ubanka ma ya yi
kadan ballantana kai, uwarku ma ba
ta yi min wahalar kawarwa ba ballantana kai qaramin kwaro
tallar za ta tafi idan ta tafi ka hanata
Rabi鈥� u ya ce, 鈥業n dai cin zalin dan wani wani abun a zo a
gani ne ai sai a yi mu gani idan abun na tsakani da Allah ne
ni me yasa ba za ki dora mini tallar ba sai ita mace?鈥�
Ta zaburo ta yo kansa tana fadar, 鈥淜ai kar fa ka yi min
rashin kunya kaji bari ganin ka ka kawo Karfi wallahi hakan
ba zai hana in dake ka ba, wallahi wancan faskaren zan sa
maka dan iska kawai. Bari uban naka ya zo in ji idan shi ya
sanya ka kai min rashin kunya idan kuma wani ke zoga ka
sai in ji.鈥�
Rabi鈥檜 ya qure ta yana fadar, 鈥淎i wallahi na gama zama
wata Katuwa ta dake ni yanzu tunda na gane abun duk
rashin kunya ne dan an ga babu uwarmu a gida don haka
nima zagewa zan yi yanzu mutum na dukana ina Bare
masa kai sai dai a kwashe shi a sume wallahi.鈥�
Laure ta saki baki tana kallonsa cike da mamaki, yaushe
yaron nan ya zama haka? Yaushe ya koyi ' rashin kunya irin
wannan? Lallai dole ta dauki ' mummunan mataki a kansa.
Bayan sati daya da sallamar Saude daga asibiti da maraice
ta dawo daga tallan alala, tana ajiye tiren
Inna Laure ta mika mata tsintsiya tana fadar, 鈥淢aza
ki share gidan nan ki dora sanwar tuwo da miya ki yi
Wanke-wanke.鈥�
Saude ta amsa da , ta dauki tsintsiyar ta share gidan tas
sannan ta dora sanwar tuwon ta tafi tana wanke-wanke,
Rabi鈥� u ya yo sallama ya shigo, Saude ta bi shi da kallo duk
ya yi gaje-gaje yana rike da bakar leda
Saude ta yi masa sannu da zuwa ya amsa cike da kulawa,
sannan ya wuce ya shiga dakinsu. Sannu a hankali Saude
ta kammala ayyukanta saboda ciwon qirjin da ya addabe ta.
鈥�
Ta nufi dakinsu a gajiye ta kwanta tana faman numfarfashi
da kyar, Rabi鈥檜 ya tsura mata idanuwa gaban shi ya yi wata
masifar faduwa ganin yanda alamun girma suka fara
tsirowa daga jikinta, tabbas girma ya fara zuwar mata ya
zame masa wajibi ya zage ya nemi kudi ya hadiye wani
yawu mai daci wanda ya tsaya masa a makoshi, sannan ya
janyo ledar da ya shigo da ita ya miqa mata, ta amsa, ta
mike tana dubawa. *
Kayan makaranta ne riga da wando da hijabi, dadi ya kama
Saude cike da zumudi ta ce, 鈥淵aya nawa ne?鈥�
Kai kawai ya daga mata ta mike cikin zumudi za sanya
Rabi鈥檜 yayi saurin hanata yana fadar, 鈥楰ar kisa karki
sakasuyanzu.鈥漈azumburo baki tana fadar 鈥淜aidon Allah
gwadawa fanyi
Harareta kafin yace. 鈥淏a dai anan ba, idan gwadawa zakiyi
fita tsakar gida sai ki gwada.鈥� Ta narke masa.
鈥淜ai don Allah Yaya saboda me?鈥�
Rabi鈥檜 ya zuba mata ido kafin ya ce 鈥榃ai ke ba ki san kin
girma ba ne wai har yanzu ?鈥�
Saude ta yi saurin kallon kanta kafin ta ce, 鈥淣i din na girma
Yaya?鈥�
Ya ja wani dan gajeran tsaki ya koma ya kwanta ya juya
mata baya.
Saudc ta zauna kusa da shi tana fadar, 鈥淭o yaushe za ka
kai ni makarantar Yaya?鈥�
鈥淕obe da safe.鈥� Ya ba ta amsa ba tare da ya kalle ta ba. Ta
yi wani ihun murna. ta kwanta gefen shi kanta saman
kafadar shi tana fadar.
鈥淲allahi harna qagara goben ta yi Yaya, in gan ni a
makaranta. To wai kuma Yaya me za a koya mini?鈥�
Rabi鈥檜 ya juyo Ya ja kunnenta yana fadar, 鈥淭o sarkin
tambaya, bari in kin je kya gani, barci nakeji karki matsa
mini da tambaya ki Juya ki kwanta kawai
Saude tace Ai ba ka ci abincin ka ba.鈥�
Jeki鈥� 鈥� dauko idan ta gama . . kwasan nina koshi Ta dan
zuba masa ido 鈥楾o me kaci
Ya zaburo mata, 鈥淜in ga tashi
Kije kin. ji, ban san yawan tambaya.鈥�
ldonta ya ciko da hawaye, muryarta a sanyaye tace 鈥淭o
yanzu da yunwa za ka kwana kenan'?"
鈥淥h! Kaina Saude na ci abinci, naci abinci naci abinci a waje
haba."
Ta yi wani takaitaccen murmushi sannan ta juya ta fita. A
bakin murhu ta iske nasu abkin murhu a Wata dan茅akaiiiyw
lmga wadda ta gaji d1 Salan gandi taga tuwon wanda bai
wuce cin mutum daya ba, shi ma ba dan ya qoshi ba. Haka
Saude ta ta koma daki ta cinye tas sannan ta fita ta maida
kwanon ta dauro alwala ta dawo daki ta yi salla sannan ta
kwanta
Washe gari tunda safe Saude ta yi Shara ta kai markade, ta
dawo sannan ta debo ruwa cikin rijiya ta rafta tayi
wankanta babu soso babu sabulu, 鈥� tana gamawa ta fito ta
nufl dakinsu Laure na kallonta bata dai tanka mata ba, sai
Ma tsakin da take ta faman ja akai akai.
Saude ta dauki kayanta ta sanya sababbi tas sun mata
kyau sosai, Rabi u da ya dawo daga dibar
ruwansa ya shigo yana kallonta cike da sha鈥檃wa yace鈥渢ace
yya nayi kyau
Yace eh
mana Saude ai ke kyakkyawa ce
鈥漈a kada kai tana fadar, 鈥淎mma kullum mutane sai su rinka
ce mini Kazama mummuna har yaran unguwar nan wai ba
za su yi kawance da niba, sai dai da 鈥榊ar Baba, wai ita ce
Kawarsu mai tsabta, ba 鈥榶ar talla ba, amma Yaya ai ka ce
ina da kyau k0?鈥�
Tausayinta ya kara kama Rabi鈥檜, yaji tamkar zai mata kuka
ya daga mata kai alamar eh, babu alamar kuzari a jikinsa.
Saude ta sanya takalmanta sannan ta mike ta dube shi.
鈥淭aso mu jc Yaya, kada rana ta yi.鈥� _
鈥楻abi鈥檜 ya mike suka fita yana riqe da hannunta zuciyarsa
cike da tausayawa. Laure da ke zaune saman kujera 鈥榶ar
tsugunne gaban murhu tana qukkulla waina, ta ga sun fito,
ba ta san lokacin da ta ture tiren ba ta tashi tsaye idonta a
warwaje tana fadar.
鈥淢e nake gani ni Laure, me zan gani haka?鈥�
Rabi鈥檜 ya kafa mata idanuwansa kafin ya ce 鈥淢akaranta
zan kai ta baki gani ne kayan makaranta ne a jikinta." 鈥� '
Laure ta ce, 鈥淜arya ka ke wallahi idan ka ga Saude ta yi
makaranta to ba na numfashi ne, don har abada ba za ku
taBa morar鈥� rayuwar duniya ba, in dai ina raye kuma Saude
talla za ta yi min ban yi niyar ta yi karatun bokon ba, wato
abun ma ya zama gasa kenan, tunda an sa 鈥榊ar Baba kai
ma bari ka kulla ka sanya ta. To ba ka isa ba wallahi ka yi
kadan ka
nuna mini iyakata ban ga bayan ka ba kowaye kai wallahi.鈥�
Rabi鈥檜 ya gifta zai wuce yana fadar, 鈥淭o sai ki gayawa kaji
dan su tantabaru tashi suke."
Laure ta sa hannu ta riko Saude da qarfi tana fadar qarya
ka ke wallahi ba za ka kai ta makarantar ba talla za ta yi
min yau sai na ga qarshen danyan
kanka ba dai kai dan rashin kunya ba ne.
Rabi鈥檜 ya ce 鈥淪akar ta kar ki karya ta, tunda ba ke ki ka
haife ta. ba, ba ki san ciwon taba.鈥�
Laure ta ce, 鈥淎ikin banza ruwa biyun k0 ka manta nan aka
karma uwarku da kwarto cikin daki?鈥�
Ai dama shi dan zina har abada bai ganin kowa da mutunci,
dan iska dan asara.鈥�
Bakin ciki ya cika Rabi鈥檜 zuciya ta zo masa iya wuya cikin
Bacin rai ya ce 鈥榃allahi ni ba dan asara ba ne kuma uwarmu
ba mazinaciya ba ce face ke ce babbar la鈥檃nanniyar da ki
ka tura mata sharri, kuma insha Allahu a sauna sai sharrinki
ya qare
Tun kafin ya rufe bakivLaure ta share shi da wani gigitaccen
mari mai kummatar da qaramin yaro cikin zafin nama
Rabi鈥檜 ya. dago Zai shara mata nasa marin ya ji an rike
hannunsa, cikin Bacin rai Malam Bala ya shiga dauke shi da
nashi marin hagu da
dama. , Rabi鈥榰 ya dafe kunci da baki wanda tuni har ya
fashe jini ya kwararo cikin qunar zuciya Malam ke
Lol ya abin ya kene mu kubiyonii donjin ci gaba sannan idan
naga comment da yawa dan anjima xan iya sake muku post.
[1/17, 7:44 AM] A A Dboy: 馃摎馃摎DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100馃摎馃摎
[1/17, 7:48 AM] A A Dboy: *YAR TALLA*
*CHAPTER 10*
Dan iska wulakantacce Allah ya tsine maka Rabi鈥檜 ban ga
amfanin rayuwar ka ba.
Yanzu uwar taka ce za ta mare ka har ka daga hannu za ka
rama, don kana marar kunya lalatacce. To bari in tsine
maka ka je can ka Karasa lalacewar ka tunda kai din ba dan
mutunci ba ne, yaro jinin sunna ya yi haka alhalin kana dan
iska kishiyar uwa ba uwarka ba ce, k0 k0 hudubar da uwar
taka ta tafi ta bar maka kenan? In ban da na shigo da yanzu
marinta zakai da gaske, 芦 don kana marar kunya.鈥�
Laure ta sa kukan munafurci tana fadin, 鈥淜uma Malam wai
kan abin da bai taka kara ya karya ba yaron nan ya dinga
marina har yana fadar shi zai zamo ajalina wai dan kawai
na ce bai kamata ya sanya Saude makaranta ba da kan shi
ya bari har ka zo ya yi maka magana. Shi kenan yaron nan
ya shiga zagina ta uwa ta uba wai har: yana fadar shi zai
zamo ajalina....鈥�
Ta Kara fashewa da kuka, 鈥榃allahi Malam bazan iya zama
ba, yaron nan ya kashe ni a banza a woli ba, wallahi tafiya
ta zan yi in bar masa gidansu tunda yana da gaskiya gidan
ubansa ne
Malam ya ce 鈥楧a alla bar' wannan magamar
Laure kar ma ki ja yaron nan ya Kara raina ki gidan ubansa
da wa ya fada masa, ina uban nasu yake nan
yaranda akaimin wuru-aka manna min tsiya~
Ya juya yana kallon Saude da Rabi鈥檜 yana fadar, 鈥淏aku
sanibane koba a taba fadi maku bane kama uwarku da
kwarto Kiri-kiri akayi iyayenta suka koreta dalili kenan
tabarku tatafi yawon karuwanci yace wlh kukaci gaba da
takuramin ko matata a shirye nake dana koreku daga
gidannan
Rabi鈥� u ya riqo hannun Saude suka nufi dakinsu suna: shiga
ya jingina kansa da bangon daki yana wani irin kuka maicin
zuciya.
Itakanta Sauden kukan take yanzutafara fahimtar suwayesu
dakuma matsayinsu acikin gidan duk da qarancin
shekarunta hakan bai hana ta fahimci dalilin tsanar da ake
masu ba tasa hannunta ta riko hannun Rabi鈥� u tana fadar
鈥淲ai Yaya da gaske ne abin da aka fada? Yaya
da gaske mahaifiyarmu karuwa ce mu ma bamu da iyaye?鈥�
Rabiu: ya waigo yana kallonta hawaye sun gama bata masa
fuska ya Kara riko hannunta yana girgiza
Ya girgiza mata kai cikin muryar kuka ya ce, 鈥淜arki soma
wannan tunanin Saude nasan kowacece mahaifiyarmu don
ni na rayu da ita :nasan kowace ce ita, ita din mutuniyar
kirki ce knma 鈥榶ar manyan mutane.
Saude ta ce, 鈥淵aya idan har mahaiflyarmu mutuniyar kirki
ce to me yasa ta watsar da mu 鈥榶an uwanta suka guje mu
ta bar mu mu kadai mina rayuwa cikin qunci da wahalar
rayuwa?鈥�
Rabi鈥檔 ya ce, 鈥淪aude mahaiflyarmu na son mu kamar yanda
kowace uwa ke san danta, dole ce ta dolece ta rabata damu
badan tasoba kiyi mata uzuri Saude duk qunci da wahalar
da ki ke ciki bai kai wanda ita . ta shiga ba.鈥� .
Saude ta ce, 鈥淭o,amma 鈥�
Ya daga mata hannu da sauri alamar ba ya san jin abin da
zata fada, sannan ya juya ya fice ya bar mata dakin Wani
kuka ya qara zuwar mata ta kwanta ta ci gaba kukan
abinta. tanajin zuciyarta. na suyakamar garwashi,yamaza
ai Rabi鈥檜 yace mata qarya ne abin da su Baba da Laure
suka fada a , kan mahaifiyarsu alhalin almomi sun nuna
gaskiyar
Shin idan har mahaifiyarsu tana son su me yasa 鈥� ta tafi ta
barsu babu k0 waiwaye? Shin idan mahaifiyarsu mutuniyar
kirki ce me yasa 鈥榶an uwanta suka kore ta? Shin idan har ta
tsare kanta me
Zaisa mahaifinsu ya zargeta harya kyamacesu da zama
yayansa?
Tambayoyin data jeroma kanta ken脿n
Wanda bata da mai amsa mata su
1 page is missing am sorry
ya farkar da ita, don haka ta dauki kayan ta koma gida babu
cinikin ko sisi.
K0 da ta maida alalen Laure ta yi ta masifa, tun fadar, 鈥淣a
lura mugunta ce kawai yau ki ka sa mini
kuma 鈥榶ar iska ke zata karewa a je min kayana ki.鈥� wuce
Saude ta samu ta ajiye kayan ta yi daki da hanzarinta, don
dama barci ne fal a cikin idonta ta samu ta kada kafadunta
ta kwanta, wani bacci mai nauyi k0 ya yi awon gaba da ita.
Inna Laure ba ta ba su alalan ba sai da gari ya ' waye a
lokacin ta lalace sannan ta miqo masu ita waisu karya da
ita. Rabi鈥榰 ya kai ya zubar ya ciro kudi ya siyo masu koko da
qosai suka karya, sannan ya tafi wurin aikinsa, Saude kuma
ta tafi talla.
Da yamma likis Saude ta dawo daga talla, Laure ta ba ta
dakan kunnun jego wanda ta karBo a makotansu da akai
haihuwa, kawai saboda neman suna, shishshigi cusa kai ba
kwarjini. Saude na cikin dakan ta debi gyalenta ta fice ita da
鈥榶arta.
Suna fita Saude ta ajiye dakan ta kwanta bakin turmin tana
hutawa a lokacin Rabi鈥檜 ya dawo daga 鈥� wurin aikinsa shi
ma ya kwaso gajiyarsa ya zauna kusa da ita cikeda
tausayawa ya ce, 鈥淪annu ya jikin na ki ne?"
Saudc ta ce, 鈥淒a sauqi sai dai ciwon kirjin da ya matsa mini
yanzu."
Rabi鈥榰 ya ce, 鈥淎llah ya sauwaqe karbi wannan bari inje
chemist na siya miki magani." . Saude tayi saurin sa hannu
ta karBa tana: dubawa leda ce baqa guda sai farar leda
guda. Ta bude: soyayyar doya ce da kwai a ciki, dadi ya
kama ta yauzu: itce zata ci doya da kwai. wanda tunda take
a duniya bata taba cinta ba. Ta yi saurin kallonsa da Washe
fuskarta tana fadar.
鈥淲ayya Allah na Yaya, yau zan ci doya, tunda nake fa ban
taBa cin taba wallahi.鈥�
Rabi鈥榰 ya yi murmushi yana kallon ta, sai da ya tashi zaibar
wurin sannan ta bude baqar ledar. Ta yi wani tsalle
ta tashi tana fadar.
鈥淲ayyo dadi, Yaya kayan kwalliyana ne?" Ya daga mata
gira, ta buga wani uban tsalle ta dafa shi taba fadar.
鈥淲ayyo Yayana na gode kwarai wallahi dama ina so nima in
rinka lrin kwalliyar su 鈥榊ar Baba, inyi; kyau k0 Yaya?鈥�
Ya daga mata kai alamar eh, tasa dariya ta ciro madubi tana
kallon kanta tana ta faman gwalegwalen idanuwa.
鈥淜ai Yaya wai dama haka nake, Yaya kalli idanuwana 鈥榶an
qanana-qanana, yanzu kuma Yaya wannan bakin nawa har
cokali yana iya shiga ciki?" Ya buga hannun shi saman tafin
hannun shi alamar oho tayi daria
Tace yaya ji haqorina har yayi tsaho da yawa'
Rabl'u ya kwace madubin yana fadar, 鈥淜e tashi kiyi aikinki
saude ta shagwabe masa 鈥渒ai Yaya don Allah ka bari in gani
wallahi ban gama ganiba
Rabiu ya saka madubin cikin ledar yana fadar, 鈥淚dan kin
shigo dakin kin gani ai naki ne bana: wani ba, kin ta gani
harki gaji. Dauki doyarki ki ci kinji
Ta ture doyar can tace tana turje-turjen qafafuwa, Rabi鈥檜 ya
dauki doyar yana fadar, 鈥渂azakici ciba ke nan to bari in
cinye abuna dama ba qoshi na yi ba rago miki.鈥� nayi
Saude ta yi saurin riqo rigar shi tana fadar. 鈥榊i haquri' don
Allah ka ba ni :na daina.鈥�
Rabi鈥檜 ya sakar mata ya wuce yana dariya, ta zauna tana ci
tana lumshe ido har ta gama, sannan ta mike ta ci gaba da
dakan yajinta iya qarfinta. Ta samu ta gama, sannan ta
wucc daki ta janyo kayan kwalliyan tana duddubawa, ta
zauna ta manne fuskarta radau da kwalliya abin kada sabon
shiga, duk ta yi wa fuskarta dame-dame man da kwalli
Washe gari ma tana gama sallar Asuba ta janyo kayan
kwalliyar ta hau ranbadawa a fuska, shi dai Rabi鈥檜 yana
zaune yana kallon ikon Allah. Tana gamawa ta mike ta nufo
shi tana fadar.
鈥淵aya duba ka gani wai nayi kyau?鈥�
Rabi鈥榰 ya yi wani takaitaccen murmushi kafin yace.
鈥淪osaima, don sai yanxu na Kara tabbatar da kamar ki da
Mamar mu daya, sak kamar an tsaga kara wallahi.鈥� '
Saude ta gyara zama tana fadar, 鈥榃ai Yaya don Allah ya
Mamarmu take, baqa ce k0 fara k0 doguwa k0 gajeriya?"
Rabi鈥榰 ya yi murmushi kafin ya ce 鈥淢amanmu fara CE fat
don har ta fiki . kuma doguwa ce mai
Dan jiki kadan, yadda. Kika ganki haka take.鈥�
Ta ce 鈥淭o yaya tana son mu?"
Rabi鈥榰 yace, 鈥淪osai ma kuwa don ranar da zata
rabu damu tasha kuka fitar hankali keko saida a kai da
gaske sannan aka Banbare ki daga jikinta kina ta tsalla ihu
a lokacm kina da shekara shida a duniya.鈥� Saude ta yi wani
murmushi kafin ta ce 鈥淭o Yaya yanzu tana ina?鈥� . Ya girgiza
mata kai yam: fadar, 鈥淎llahu a鈥榓lamu." Ta dan yi jim kafin
ta ce 鈥淭o Yata tafitabar mu?鈥� me akai mata? Kafin ya kai ga
ba ta amsa Inna Laure ta hankado
labule tana fadar, 鈥淭o tif da taya 鈥� talla sai a tashi a tafi
tallah hakanan
Saude ta mike cike da alamun gajiyawa a
fuskarta ta fice ba dan ta so ba. Ta tafi tallar da ta zame
mata waki鈥檃 farilla.
Da daddare ciwon mara hade da ciwon ciki mai tsanani ya
rufe Saude tamkar ba za ta kai ba, ta ringa murkususu a
tsakar daki ita daya a lokacin Rabi鈥檜
bai dawo ba.
Laure na jin ta, amma k0 ta kula ta kanta. Haka Rabi鈥檜 ya
dawo ya same ta hankalin shi ya yi masifar tashi, ya juya ya
koma ya siyo mata magani ya ba ta, amma a banza,
sumanta biyu cikin dare. Yanda suka ga rana haka suka ga
dare daga ita sai Rabi鈥檜 cikin daki babu wanda ya leqo balle
ya ji halin da take ciki, don Malam ma bai san abin da suke
ciki ba.
Cikin ikon Allah ana kiran sallar Asuba, jini ya zowa Saude,
a take kuma ciwon marar ya dauke, don haka ko motsi ba ta
iya yi ba daga inda take ta kwanta sai bacci mai nauyi ya
dauke ta.
Sai a lokacin Rabi鈥檜 ya samu kwanciyar hankali ya tisa ta a
gaba ya rabka uban tagumi yana kallonta hawaye masu zafi
suna biyo kuncinsa zuciyarsa ta cika da tausayinta, har gari
ya fara haske sannan ya 鈥渇arka ya mike ya je ya yi sallah ya
dawo ya samu ya dan kwanta saboda baccin dake cike cikin
ldanuwansa.
Cikin barcinsa ya ji tamkar ana rabka sallallami, Rabi u ya
bude idanuwansa da su kai masa wani irin nauyi saboda
bacci, ya ga Inna Laure na fadar
鈥淢alam! Malamll zo ka ganewa idon ka ikon Allah Malam zo
ka gani.鈥�
Malam Bala ya fito daga dakinsa yana fadar, 鈥淣i
ko kinsan bansan irin wannan kiran natashin 鈥漢ankali.鈥�
Laure ta qara hankade labulen dakin sosai tana fadar, 鈥淎i
wannan idan ma akwai abin da yafi tashin hankali to shi ne
dubi yarinyar nan Saude kalli siket dinta.鈥�
Malam ya qara tura kai cikin dakin tsawon wasu 鈥榶an
sakanni kafin ya ce 鈥楰amar jini nake gani Laure?鈥�
Laure ta turo wuya gaba tana fadar, 鈥淭o duba da kyau jini
ne daman tun jiya nake jin ihun yarinyar nan na dauka wani
iya shege ne ashe yaron nan ne ya haike mata.鈥�
Gaban Malam ya yi wata mummunar faduwa ya juya yana
kallonta a razane bakinsa na fadar, 鈥淜i bari don girman
Allah.鈥�
Laure tabe baki tana fadar, 鈥淕a alama nan.鈥�
Idanuwan Rabi鈥檜 suka yo waje don sai a lokacin
ya lura da yanda jini ya Bata siket din Saude sosai kamar
anyi Barin manja a jikinta abin kaga kaya
masu haske da santsi, hankalin shi ya yi masifar
dugunzuma.
Malam ya ce 鈥淟allai kam yaran nan ka cika la鈥檃nannen Allah
yau kam sai na gwada maka irin nawa rashin imanin ni za
ka jawa abun kunya, ka yiwa qanwarka fyadeee dan iskan to
wlh daga rana irin tayau ka gama haikewa 鈥榶a鈥檡an jama鈥檃.鈥�
Ya juya a zafafe sai ga shi ya janyo wani qaton faskare,
Laure ta riqe tana
fadar. A,a don Allh kayi haquri Malam karka kashe shi.鈥�
Malam ya goce yana fadar, 鈥榃allahi yau sai dai akwashi
gawarsa cikin gidannan inya so nima a kashi yayi kukan
kura gamida yin kansa da faskaren
Wooooohoho jama,a wai ya abin yakene mu kubiyo ni donjin
yaddah wannan taqaddama zataci gaba da kayawaaaaaa
Thursday, July 23, 2020
JARABABBEN KISHI Page 31 to 40 (Te end)
"Na dauki wannan ka koma ka siyo muku Wanda zakuci nima inada bakin cin kaza." bata tsaya ta kalli fuskanshi ba, ta wuce kara fita zaiyi Abeeda tace karka damu Mijina na hkr, (Tabbas indai haka zaa cigaba da zama tabbas ba adalci) Koh sauraran Abeeda baiyi ba ya fita yaje ya siyo mata wasu, Ya wuce dakinta dashi, Wani irin darene Wanda gaba daya sunkasa tantace irinsa, babu Wanda ke dokin wani cikin su, kowa bakinciki yakeyi, (Ni HUMAIRAH mezance saidai fatan azauna ayita hkr). Suhayr sallar dare takeyi kullun har kwanan Abeeda suka kare, Tana Neman tsari Allah ya kareta daga sharrin kishiya. Ya shirya tsaf zashi shago, ya fito yace "Suhayr zan fita," Tace "Allah ya tsare ya kiyayeka yabaka sa a." wani irin dadi yaji Wanda baitaba jiba, tuni ya rungumeta yayi mata"hot kiss "Zan aiko harisu anjima zai kawo muku kayan abinchi." "Toh" tace "nima zani school, kabari kawai inzan dawo zan biyo in kwashi Kayan," komai cikin gdan Saheeb yana tafiya Daidai amma fah baida wani sakewa, Saboda Suhayr ta tsaya kaida fata cewa bata yarda da cuta ba, Wata Safiyar juma'a ne Abeeda na kwance tajiyo Suhayr ta kure waka, *Romantic* na korede bello da tiwa savage Itakuma a rayuwa ta tsani jin wani sauti dazai dame jinta. Tashi tayi koh Sallama ta fada falon Suhayr direct wajen home theatre ta wuce ta zare socket din. Suhayr abun yabata mamaki, baki bude Suhayr tace "ke wace irin karyace mara sanin ciwon kai? Banshiga harkanki ba kishiga nawa? Meye matsalanki da wakana, You must be very stupid Abeeda, you heard me ryt?". Abeeda tace "Kin wani cika mana gda da sauti ki tuna nan gdan mijinane Suhayr ba gdan ubanki ba". Ta nuna Suhayr da yatsa. Tuni Suhayr ta karya Dan yatsan tace, "kinyi kuskuren sako ubana cikin wannan maganan". wayarta ta dauko ta kira Saheeb yana dagawa tace "Saheeb yanzu zanyi kulikulin "Saude" da matarka." Saheeb yayi saurin cewa "Suhayr meya faru???". Tace "Bari na gama da ita tukun sai insamu daman yimaka bayani" Yayi saurin cewa "Noo Suhayr pls don't do that." Karaf ta katse wayan Tace "yau zan nuna miki cewa nima gdan mijinane, bulala ta samu takama Abeeda tayi mata lilis da jiki tace " get out of my room" ta nuna mata hanyan fita. "Yau naji ikon Allah na hana akawoki da redio ne? Zaki takurama rayuwana Yaunaji masifa Banda kaddara data Riga fata ke kin isa in tsaya dake?". Ta dinga sababi ita kadai Saheeb ne yabaro shago yazo kafin yazo tuni Suhayr ta gama da Abeeda, Kiransu yayi gaba daya yace "Suhayr meye dalilin fadannan?" "Saheeb nan dakinane koh dakina ba" yace "kwarai naki ne". Tace "inada ryt din yin yadda nakeso koh banda shi?" Saheeb yace "kina dashi" "Shine wannan kyankyason zata zo har dakina ta kashemu wakar da nakeji?????" Saheeb ya kalli Abeeda yace "Abeeda meyasa kikeson shiga sabgar daba takiba? Karki sake koda wasa Don wallahi Suhayr bazata raga miki ba, Kowa ya zauna a matsayin sa". *Bayan shekara biyu* Saheeb arziki ya bunkasa har kasar waje yake zuwa ya daina bada sako. Lokaci guda ya kankara katon gda flat hudu , (Aiki ga mai yinka) Ga sasan yara Gana mahaifinshi, Gana mai gadi. Suhayr kam ta kammala karatu, Aiki take a GtBank. Abeeda tunda tayi aure narasa dalilin ta na tsayawa. Suhayr tuni ta kara haihuwa, yara biyu lokaci guda, da Sadiq da farouq, Itako Abeeda yarta daya mai sunan mahaifiyar Saheeb. Kwatsam Saheeb ya kara Neman aure, Suhayr tace Sam vada itama ba wata sha'awa dazata bashi, Nanfa Abeeda ta tsaya kaida fata. Itace ta shirya akwati, Suhayr tace "yau naga sabon salo tusa a loudspeaker Hmmm kishiya har wata abun zakwadi ce? Anyi aure komai normal suka koma sabon gdansu Komai na daki saida Suhayr ta canza, Harta TV irin katonnan tasa, Suhayr yace zaiyi musu kaya itada Abeeda tace bataso abata kudinta. Gida yayi albarka da yaya. Duk shekara sai Abeeda ta haihu haka ma amaryar maryam, Itakoh Suhayr tace tagama Allah shi raya mata ukun, Saida saheeb yayi mata hudu ya rufe kofa, yayi farinciki yakuma godewa Allah daya barshi a Raye ya cika burinsa,ISHI novels / JARABABBEN KISHI part 30 JARABABBEN KISHI part 30 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:21 Kowa a cikin gdan yanabama suhayr girma, aunty kasa aunty sama. Har biyota sukeyi sasanta, Dukda tana Kishi amma daga baya taga Ashe abun ba haka yakeba, Inkayi Dacen abokan zama tabbas kayi babban sa'a Ana girma ana hankali, kannin Saheeb duk sunyi aure, haka Suhayr ta tsaya kaida fata, Amrah wan Suhayr ta aura Sulaiman, Rayuwar gdan Saheeb abun shaawa, Shikanshi girma yazo. *Noor yana Nile university dake Abuja, yanbiyu suna Turkish international college*, Ammafa fada tsakanin Abeeda da maryam anayi saboda maryam bata iya gani ta kyale, Suhayr ce tazama alkali, Maryam batada kunya haka takewa umman saheeb Rashin kunya, Suhayr tayi dariya tace "hmmm maryam kenan" ta dafata tace "Wata rana zaki bari nayi abunda yafi wannan Wallahi haka duk Rashin kunyanki nafiki, tunda kika ganni haka toh duniyace, ta horani, Naga ba sarki sai Allah abunda ake bazaa fasaba," Juyowan da maryam zatayi tace. "Bana bukatar wa'azinki, karki kuma shiga sabgan daba takiba". Suhayr ta mutu da manaki batasan lokacin data wanke maryam da mariba, tace "kinzo zamanin nayi sanyi kalau, Dabaki isa ki nunamun Dan yatsaba, Kaza kawai wacce bata gajiya da masifa Banda jaraba irinta maza me saheeb zaiyi dake? Yau nasan darajan iyaye baxan yarda kiciwa umma mutunciba, Never" ta tofa ma maryam miyau Abeeda tace "Suhayr antuna da kenan", babban abunda zatama ta wuce shine ya tofama miyau. Saheeb na tsaye yace "good Suhayr kinyimun Daidai". Da Sauri ya rungumeta. Yace "Duk cikin matana babu wacce rigimanta takaina Suhayr, tunda kikaga tayi sanyi toh Wallahi tayi Wanda yafi wannan muni, Kafin kizo." Nan ya tarsu yayi musu nasiha. Gda yadawo normal kaman da. novels / JARABABBEN KISHI part 31 the end
JARABABBEN KISHI part 31 the end
Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:23
Inna-nallahi wa'inna ilaihir rajiun, Tabbas dukkan
mai rai saiya dandana mutuwa, Allah yayiwa
mahaifin Saheeb rasuwa, sanadiyan mashin daya
bigeshi, Banda yaxo da ajali, koh kujewa baiyiba.
Family din Dan-koli sunyi babban rashi inda
Saheeb yakasa zaune yakasa tsaye. Anyi bakwai
kowa ya watse, Musty shine ke kan komai na
dukiyar mahaifinsu, dayake basuda yan'uba
Bayan kwana biyu suhayr tadawo daga office
karfe shidan yanma, Tajiyo hayaniya dayake da
gajiya sallar kawai tayi ta fita, maryam tagani sai
tada jijiyan wuya take, Tana cewa "don kin tsaya
kaida fata a auroni shine me? Sai naga niba cin
amana nayiba keko, ananar kawarki kikaci kika
aure mata miji Kece keda rabon shan kunya
baniba," Suhayr takasa koda motsi kallon Abeeda
takeyi wacce take cikeda ladama, Muryar suhayr
sukaji tana cewa "maryam banda shirme irin naki,
dani da Abeeda mutu a raba takaimin kaxa, Indai
akan cin amana ne nayafe mata duniya da lahira,
Sanadiyyan aureta nayi ladaman wasu abubuwa
da dama, ciki harda. rage *JARAB EL GHIRA
(flames of jealousy)* Danayi nagane cewa Kishi
ba hauka bane, Nagane cewa kishiya abokiyar
zama ce, tabbas kaman yadda nayi dace Daga
baya Da Abeeda taxo da zafin kai daga bayaba
taga ba riba fadan da kishiya, Maryam inaso kiba
Abeeda hkr Sbd munriga munzama daya, tunda
munada zuri'a". Ana haka saiga zulaihat taho
cikeda isa da takama, Tace "tabbas aunty suhayr
kinyi gaskiya, Munrigada munzama daya saidai
fatan Allah yakara hada kan duk wasu kishiyoyi,
dake fadin duniya, yabamu hkr zama da juna
sannan ya sassauta Kishi a tsakanin mu". Gaba
daya suka rungume juna, daganan kowacce tarike
girmanta, Saheeb koh anzama Alhaji, Saida
yakaisu duka Makkah harda mahaifiyarsa, da
mahaifiyar kowace matarsa, Saheeb yana cikin
farin ciki, a cikin gdanshi burinshi ya cika,
kowacce kokarin faratamai rai takeyi.
********************* Tamat billahi ina godiya ga
Allah mekowa me komai daya bani ikon kammala
wannan Dan kankanin littafin dafatan mun karu
kuma zamuyi amfani da abunda ke ciki. COPY AND SHARED BY SAKEENAT USMAN AND MARYAM AMEERAT YOLAAA
Share this
JARABABBEN KISHI Page 21 to 30
JARABABBEN KISHI part 21 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:49 Kwanan su biyu a asibiti Amma ba suhayr ba labarin ta, abun yana damun Saheeb amma bashida yadda zaiyi, Washe garin ranan da zaa sallamesu Saheeb yace "suhayr bakije kin gaida umma ba gashi har za'a sallamesu" Koh kallonsa batayiba tace "pls Saheeb kadameni wai shin ina ruwana da Rashin lafiyarta? Koh inada matsala da hakanne? Pls Saheeb ka kyaleni, ask you can see am ready to school So inkaje ka gaidata ga abinchi a dinning bissimilah". Koh kallonta baiyiba yace "kitashi kidauko cooler kisamun nawa abincin xankai musu asibiti". "ah ah Saheeb wai meye amfanin su nimrah da bazasu gda su daho abinci ba Tika tika dasu?". Inji Suhayr "Ba matsalanki bane inkinji toh kitashi inkuma bakijiba Zan fita can waje insiya musu". Suhayr tace "Tafi nono fari Kasan da hakan ka tsaya jaka ta dafa ka kai musu?". Tashi yayi don yanajin inya cigaba dajin munanan kalamanta zasu tarwatsa zuciyarsa. Akan hanyansa na zuwa ne yayi musu adar abinchi sunci sun sha Daga bisani aka sallamesu, adaidaita suka hau har gda. Abeeda tayi missing dinsu amma batada yadda zatayi Sunyi exchange na number, Domin sudinga gaisawa, itqma Abeeda takamu da son Saheeb. A hanya suhayr ta hadu da Abeeda tana tafiya tana yanga Packing tayi tace "yanmata ran gari Takawarki lafya". Dariya Abeeda tayi tace " wata sabon gani suhayr". Suhayr tace "Shigo mana kinsan mun tsaya akan titine". Ab茅eda ta shiga sannan tace "suhayr yaushe kikayi aure?" Suhayr tace "Hmm last year badai ke kintsaya ruwan Ido ba? kinganni harda Dana noor" "Nyc name" inji Abeeda. Suhayr tace "Northwest University nake zuwa kefah" Abeeda tace "Aini poly nakeyi, Ina HND ne". "Allah ya taimakemu "Yasu hjy keko Abeeda nadade inason ganinki Inaso ki rakani wajen wannan malamin hajyan Akwai Marsala". Abeeda tace "Suhayr matsalar me dagayin aurenki koh 2yrs bakiyiba?". Suhayr tace "Abeeda kinsan koh kishin danake akan saheeb? Kinsan irin taaddancin dana dinga yi? Akan so ya kara aure? Kafin aurena saida narabashi da yan mata sunkai biyar, bayan aurenmu kuwa bakwai na lalata, Ke har wajen daurin aure" "Wat!!!!!" Zare Ido Abeeda tayi tace "tab Suhayr ke shu'umace". Ta tabe baki tare da cewa "ai nafi haka ke Niko uwarsa bata zuwa gdana bare kuma kanninsa koh yan uwansa" Abeeda tace "tirkashi Ashe dakwai bikin zuwa babu Zane" A zuciyarta tafadi "tabbas Saheeb yayan Amrah shine mijin Suhayr" "OH my God Suhayr kin kade sai kinyi dakinsanin fadamun sirrinki, saina shigo rayuwar Saheeb Na hanaki sakat" A baki tace "OK xan rakaki amma yaushe kika shirya?". Ta danyi jim tana naxari sai kuma tace "ummmm Abeeda mu barshi weekend kinga am free ba school". Abeeda tace "Haka zaayi". Ahaka sukayita hiran har takai Abeeda bakin poly sannan ta wuce nata makarantar. Cikeda farin ciki Suhayr tace "Saheeb bakaiba kara aure, Sai anyimun maganinka Saheeb bawai muzgunama nakeso nayi ba sonka nakeyi Banaso wata taBBEN KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 22 JARABABBEN KISHI part 22 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:07 Abeeda na isa gda tace da hajiya "Hjy kinsan meya faru yau Suhayr nagani Har tayi aure kinsan harta haihu?". "Iyeeh tabdi jam" inji hjy saude. Abeeda tace "Hjy ina Wanda nake baki labarin Rashin kirkinta ?" Hjy saude tace "eh" "Toh Ashe Suhayr ce Hjy duk yadda za'ayi inshiga gdan saina shiga koh ta halin kaka". Hjy saude tace "Yauwa yata haka nakesonki da jarumta, Karki sake ki karaya". Abeeda tayi dariya tare da cewa "Bakiji ba wai zan rakata gurin Malam ai kibari hjy (tsuntsu biyo zan jeho da dutse daya) Itace sakarya hjy" "Yauwa yata" hjy ta rungumo Abeeda tace", "Yar hjy, uwar hjy, yar lelen hjy, yar gaban goshin hjy, Kishiga ya auro hudu kuma ki zauna dasu, indai kisssace yanzu kai ya waye ba boka ba Malam iya ruwa fidda kai Wanda ya iya allonsa ya wanke". "Hjy yanzu zan kira Malam inyimai bayanin komai, yafara aiki tunda nasan a irin kallon da yakemun, hjy dakwai so a ciki" Malam suka kira tayimai bayani yace angama cikin kankanin lokaci zaki zama halak malak dinsa ammafa Saikinci damaran zama a gidan Saboda matar shu'umace duk yadda kike tunani tafiki Sannan ta mamayeshi kwarai Saboda yana masifan sonta Sannan gdan da suke ciki mallakin mahaifinta ne ke harta kasuwancin dayake kudinta ne". "Malam ai wannan duk ba wata matsala bace Masifa kuma ai saimuyita gwabzawa Mekarfi ya kwaci kansa". Malam yace "Angama" Washe gari tun safe Suhayr ta kammala aikinta, Saheeb yana zaune Tunanin Abeeda kawai yakeyi, duk Suhayr tana kallonsa da yanayinsa. Mai aikinta ta goge ko'ina Sun kammala. kusa dashi taxo ta haye kan kafarsa tace "Nurul-Q'alby Lafiyarka kuwa gaba daya ka canza? Kodai akwai matsalane a kasuwa?" Rungumeshi tayi har sunajin numfashin juna. "Talk to me Saheeb Your silence it wat I hate". Dagota yayi yace "my blood ba abunda ke damuna Saidai har yau nakasa cikama zuciyana burinta" "Zare Ido tayi tace "buri kuma? Wani burine Wanda ya wuce mu karasa rayuwar mu nidakai da yayana har abada?" murmushi yayi Amma na ciki na ciki yace "Hakane Suhayr Allah yabarmu tare" "Amin" tace "inaso zanje unguwa Amma bawani dadewa zanyiba Sannan a gda zan bar Noor". Saheeb yace "Amma Suhayr dakin tafi dashi inajin da hankalina yafi kwanciya" "Toh" tace tana dariya tace "your wish is my command". A hanya suka hadu da Abeeda, suka kama hanya sai wani kauye can gaban dawanau Gaban "kwa" in an wuce "Dungurawa" Wato "Doruwar shehu" Cikin unguwan suka shiga sai gasu a kofar gdan Malam din, Sunyi mishi bayani yace dubu talatinne ba yawa Da sauri Suhayr tafito da kudi zunzurutun kudin ta bayar. ( ni HUMAIRAH danida beelybadaru, akaba kudin muyita mata tsayuwar dare) Abeeda tace "Malam kar ayi sanya" yace "karki damu" Kallon suhayr takeyi tace "saikinyi dakin sani don saina maye gurbin duk abinda kika kasa Hakan zaisa nasamu matsayi a birnin zuciyan Saheeb" duk a xuciyarta take xancen. Sun kama hanya kowa da abunda yake sakawa Bayan sati hudu wata guda kenan, Saheeb yarasa sukuni har saida ya binciko gdansu Abeeda, Daga zuwansa yace aure yakeso nanda wata guda Sannan bayaso kowa yasani saboda karya koma kunnen matar sa. Soyayya mai ma'ana ce tashiga tsakanin su Baya iya barci sai yaji muryanta, Kullun saisun gaisa da yan uwansa, harma da umma lokaci guda ta asirce zuciyansu da akhairai. Shiko kanin Saheeb ba wadda yaki jini irin Abeeda, Don yace batai masa ba gwara Suhayr sau miliyan, So gamon jini" Kwatsam mustapha yaji ana zancen yayansa zaiyi aure kuma a boye musty yace "shikam bazai yarda a munafunce Suhayr ba," Gdansu Abeeda anata shiri biki saura satii biyu.I novels / JARABABBEN KISHI part 23 JARABABBEN KISHI part 23 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:11 Shiri akeyi gadan gadan, akalla saida Saheeb yayiwa Abeeda akwati biyar harda kit, Sadakinsa naira dubu hamsin Yabada komai na kawayen amarya. Saheeb ne tsaye yace "Abeeda daga yau baxaki sake ganina ba, sai ranan daurin aure". bata rai tayi "saboda me my Blood?" Yace "Saboda banaso Suhayr ta gane komai saboda tafara mun complain cewa Bata gane yanayina ba kinga karta dagoni" (Rikicin duniya damai rai akeyinsa) "hakane Amma dai zakazo dinner koh?" Cewar Abeeda. Yace "Eh zanzo karki damu" "Toh" tace ta juya tana jujjuya sassan jikinta komai na kadawa, Saheeb ya bita da ido har ta bace ma ganinsa. Shiko musty nazarin yadda zaayi a Raguza aurennen yake, Gashi yakasa zuwa ya sanar da suhayr, kwatsam saijin labarin dinner da aka shirya Yace "toh koh saina sanar da suhayr Kartace na munafunceta". Ayau ne daurin aure tun safe Saheeb ke shiri yakasa zaune yakasa tsaye. Suhayr duk tana kallonsa daga bisani tace "oh my God Dan Allah Saheeb safa da marwan me kakeyi? Saikace Mara gaskiya?" Da sauri ya juyo yace "suhayr kamanya wane irin zancene wannan" (Cewa tayi gulty conscious) " ! dole in tambaya saiwani rawan jiki kake kaman me shirin yin sabuwar amarya?". Dam gabansa ya fadi "Yauwa inaso ka kaini gdansu Abeeda kawata inyi mata godiya". "Godiyan me ????" Ya fada a dan tsorace, sai kuma ya maxe ya ce "Look suhayr yawonki yafara over fah kiyi hkr next week kyaje" tace "Allah yakaimu", Yana fita dagashi sai boxer, Daki ta nufa wata tsaleliyar shadda tagani bugagga Ga wata hula mai shegen tsada. mamaki ne duk ya cikata ina Saheeb zashi? Tab yau akeyinta (Rakumi da kayan tanka). "Saiko na hanashi zuwa koh ina falo ta dawo ta kalmashe kafa, Yazo ya wuce yasa shaddar sa fara kal, kitchen ta nufa da sauri ta debo miyar datayi na manja, fitowa yayi yana duba irin kyan da yayi Baiyi auneba ta taho da sauri Daidai da saheeb ya dago Gaba daya miyar ta kwaremai Gashi miyar da zafi". "Subhanallah!!!!!" Ta fadi tareda da cewa "swthrt am sorry it's a mistake " Kallonta yakeyi kaman yasa hannu aka ayita ihu!!!! "Suhayr kin kyauta kwarai" a zuciyarsa yace "Amma Daga gobe zaki gane kurenki". Daki ya wuce baice da ita uffan ba. Wata shadda yasa tsohuwa sawa daya Yasa hula ya fita, Abokinsa Marwan ne ya zo ya daukeshi a mota. Saheeb yace "My guy kaga abunda suhayr tayi mun? Miya ta watsamun a kaya" marwan yace "Mutumina gaskiya saika zama namiji inba hakaba Suhayr saita zamema annoba Saukinta ma Abeeda itama A ce". Andaura Aure kowa ya shaida, Abeeda sai murna take umman saheeb sai godiya take ga Allah, Yan uwa kowa sai barka yake mata. Musty ne Yakama hanyan zuwa wajen Suhayr don ya sanar da ita, saboda sauri yakalmi daban daban yasa Rigarsa a baibai. (Niko mexanyi banda dariya) take ya fada koh sallama babu "Lafya musty naganka hajaran majaran???". Musty yace "Ina lafya maye ya cinye amarya". zare Ido Suhayr tayi tace "a ina??ABBEN KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 24 JARABABBEN KISHI part 24 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:13 Musty yace "Aunty bafa nufina meye ya cinye Amarya bane Yaya Saheeb yayi aure". "What???" batasan lokacin data mike tsaye ba, tace "musty kana nufin Saheeb dina yayi aure?" Musty yace "Kwarai aunty har an daura ma nima dazu nakeji". Suhayr tace "Tabbas Saheeb yayi kuskuren boyemun komai, amma kuma ban makara ba Naji ma zaayi reception". Ah ina musty ya gaya mata shiri ta tashi yayi tana zubda hawaye, a gda tabar Noor wajen mai mata aiki. "Musty zo muje" motarta ta dauka ta dauki madoki abunyin golf tasaka a bayan boot. gudu takeyi har suka isa wajen da ake partyn. Dayake tinted glass ne bawanda ya ganeta, tace "musty kazauna a cikin motan karka damu bari na shiga don banaso afara komai". Ta fita ta shiga ciki Saheeb ta hango yanata washe baki, Wato yayi amarya, chan ta hango kawarta Abeeda bakaramin razana Suhayr tayi ba, " what!!!!! Abeeda itace ta auri Saheeb????" Take tambayan kanta amma idanunta kodai gizo suke mata. "Nooo in mafarki nakeyi yaka mata in tashi, Nooooo dis won't be possible". ji tayi ankira Saheeb da,amaryar sa Abeeda ai sakato tayi Basu ankaraba duka suka faraji tako ina da sandar golf, kuma gata da bindiga kowa yakasa tunkararta, Tuni Saheeb ya fadi sumanme, itako Abeeda tuni kamanninta suka canza, baki ya kumbura amma Suhayr duka takeyi baji ba gani. saida tayi nasaran sumar da Abeeda Hjy saude lbr ya risketa tuni ta tsure. Loudspeaker ta dauka Tace "ina ma kowa murnan zuwa gaggarumin bakin biki Wannan da kuke gani maciya amana ne, Abeeda kawata ce wadda na yarda da ita amma shine taci amanata, Shikuma wannan da kuke gani ba kowa bane illar mijina kuma uban yayana, nasan dayawa mutane zasu kirani da mahaukaciya tabbas basuyi karya ba, Indai akan miji nane. Wutan kishi na damuna kwarai Bansan wace jaraba bace kecin sa yayi mun kishiya kuma kawata?, Kadan kuka gani". ta fadi tana kallonsu koh motsi basayi. Tiryan tiryan ta sakko tana taku daya bayan daya tace "kafin in irga uku kowa ya bace" ta nuna bindiga, Kan kace me kaman anyi ruwa an dauke. Ta tsallake su tayi waje, Tashiga mota suka koma gda. Suhayr tayi kuka kaman ranta zai fita amma duk abunda tayi tace bata huce ba.KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 25 JARABABBEN KISHI part 25 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:14 Ambulance aka kawo aka kai Saheeb da Abeeda asibiti, Hankalin kowa saida ya tashi ciki harda umman saheeb. Abbansa yace "duk abunda ya faru Halima kece sila kuma ina gaya miki kisa kafar zuwa kashe gobarar da kika hada Da hannunki kuma a gdan danki Don ni ba abunda ya dameni wallahi " Shuru umman saheeb tayi, batace dashi uffan ba, Fuuuuuu tafita Suhayr ce tace "musty muje gdan naku". Hanya suka kama sai dorayi suna tafe kowa ba baka sai kunne A kan kwana ta ajiye shi Sbd kar ace tare suke, Koh Sallama babu Suhayr ta fada dakin umman Saheeb. "Ban taba Sanin cewa ke gurmi bace mai hada guri, umman innace miki uwar banza nasan wallahi banyi laifi ba, Umma tabbas kin saiwa kanki fetir din dasaiya konaki, Kin ziga Saheeb yayi aure don farin cikinki Bakisan akasin haka zaki samu ba, Zama da kishiya baxan iyaba saidai yau kitashi daga dakinnnan kibasu su zauna, sannan ki ciyar dasu Amma bada kudin ubana ba." Shuru umma tayi tarasa bakin magana. Suhayr tace "Dole kiyi shuru saboda kinsan baki shuka alkhairi ba Munafukar tsohuwa". "tub" tayi ta watsawa umma miyau tace "kadan kika gani saikinzo *zaman makoki (na Rashkardam*) Zaki gara ganewa idonki, Zakisan yadda zafin Kishi yake." Kai tasa zata fita kawai taci karo da Abeeda tsaye tace "zafin Kishi koh hauka????? Tambayanki nake?" Suhayr dago jajayen idonta tayi ta hankada Abeeda saida ta fadi. Suhayr ta taka wuyanta tace "ke in bakisan cewa ni yar taaddan mijina bace yau zaki sani, Kinyi gangancin shigowa hurumin daba nakiba, Saheeb is mine Abeeda mine alone" Kakari Abeeda keyi kaman zata mutu. Nimrah ce tace "tabbas bakisan darajar taki uwarba, dabaki zo har cikin gdanmu kinciwa uwarmu mutunci ba" A fisace Suhayr ta juyo tace "nimrah dake nake wayasa bakinki a ciki, oh baki sanni ba amma yau zaki sani bana daukan raini a wajen kowa bare ke" wanka ma nimrah mari tayi tace " Say a word again and I will show you the other meeee" tub tayi ta watsawa nimrah miyau. Kan Abeeda ta dawo tace "saidai wannan tsohuwar ta fita tabar muku dakin, amma badai gdan ubana ba Kinji". itama miyau ta watsa mata saitin bakin Abeeda. Sannan ta fice ta shige motarta saida tasa motar tayi gunji kannan ta figeta, don saura kadan ta take AbbanI novels / JARABABBEN KISHI part 26 JARABABBEN KISHI part 26 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:15 Juyowa yayi yace "tabbas wancan Suhayr ce Lafya take gudu kaman zata tashi sama?" Tabe baki yayi yace "Allah ya tsare." Tsakiyar tanka sheshen falonta ta tsaya tana huci, Tace "tabbas hakurina ya kare, Baxan iya jurewa irin abubuwan da Saheeb yakemun ba harya je ya aura kawata Koda yake bakomai Allah yana sama yana kallo ban gaxa ba, wajen yiwa mijina biyayya ba wajen sauke duk wasu hakko ki waje daya na gaza Wajen Rashin boye garwashin kishina, *JARAB EL GHIRA* (Akaro na farko da suhayr tafara karaya kenan) Saheeb baya ya farfado ya nemi Abeeda ya rasa, bai zarce koh ina ba sai gda koh a mutu koh ayi rai koda Suhayr zata yanka tsokanshi ne saiyaje ya fayyace mata komai. Abinchi takeci takeba noor abaki yana mata kwaranci, "Abba! Abba!!!" Kallonsa tayi tace "Abba baya sonmu karka sake kiran sunan Abba kaji." Hancinsa ta lakuta. "Saheeb yana tsaye yace "abbanka yana sonka sosai, karka sake kayi amfani da Kalmar umma She's rong" Dagowa Suhayr tayi da mamaki tace "what!!!!!? Mekazoyi gdannan? Kafin in rufe idona in bude Ka fit......." bata karasa ba ya rufe mata baki," *"Am going no whr suhayr you can do your worse but today you have to learn me your ears* Bantaba zatan zaki iya aikata munmunan aikin da kika aikata yauba". Hmmm wata dariyar mugunta tayi tace "koh ???". Saheeb yace "Ki tuna Allah subhanahu wata'ala yafadi acikin littafinsa mai tsarki, yace auri bibbiyu, uku uku hurhudu Sannan yace inbazamuyi adalciba muyi daya, Toh kinga inada kwakkwaran hujja ta kara aure". "Dakata Saheeb" cire hannu tayi daga cikin abinchin ta kira mai mata raino tace dauki noor kuje dakin wasa. Kusada Saheeb taxo tace "dole kasamu bakin yimun wa'azi tunda yanzu kasamu masu gdan rana, I don't blame you saheeb I never new that you are *Savege* till today, da baka da komai ai ka hkr da aure saboda jaraba dake cinka, na mamajo Saheeb inkaso kayi Hudu I don't care amma abunda nakeso Kasani, Inhar ka cuceni Daidai da kwayar zarra ban saniba toh Allah kadai zai isarmun ba mutum ba, Sannan indai anan gdan zakasa Abeeda toh bazan taba yarda ba, Sannan inaso muzauna Ayau muyi lissafi kabani uwar kudi kadauki riba, Saika ciyar damu dashi." TirkashiKISHI novels / JARABABBEN KISHI part 27 JARABABBEN KISHI part 27 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:16 Saurin juyowa yayi ya kalleta tace " kwarai yau za ayita ta kare tunda har ka iya kara aure, Nasan katsaya da kafanka kuma gdannan da kake gani na barshi nima Saidai ka kama mana haya mu biyu". Zare Ido yayi cikin rudani, nashiga uku meyasa Suhayr zata yankemun irin wannan hukuncin? "Pls Suhayr kiyi hkr kiyafemun," Tace "Ai ni bakamun ba amma kayiwa kanka, Inace kudi gareka? Kasani yanzu basai anyi nisaba, Zauna muyi lissafi gobe muje ka turamun a account dina". Saheeb bashida bakin magana Sai zufa yakeyi. Anyi lissafi ancire kudi naira miliyan biyu, Kudin da aka bashi jari, Saheeb yayi matukar mamaki ganin riba zunzurutun, riba har tafi uwar kudi yawa Baiyi mamaki ba saboda yasan cewa, ya San yadda yake tafiyar da kasuwancin shi, Murna ya dinga yi itako Suhayr bataso ba. "Toh ina saurare zuwa jibi Don baxan zauna a cikin gdannan ba, Gdanka nakeso inzauna bana ubana ba, Sbd ko wacce mace da gdan miji take takama ba gdan uba ba." "Toh" yace tunda yaga ta sauko, tashi yayi yace "zani gdan umma,Da sauri tace "Wace umma look man you are not going any whr we are sleeping together Harsai ranan daka sama mana gda mubiyu mu koma, In short koh shago bazaka budeba," Saheeb yana masifar son Suhayr shiyasa komi tayi yakanji haushi amma, sonta baya koh girgidi a cikin ziciyarsa. Gdansu Saheeb koh amarya tana chan tayi tsuru tsuru, sai hawaye ke zuba a idanunta. Kowa yaganta saita mikamai buhun tausayi, gaba daya halittarta Suhayr ta canza, Hatta hakoranta na gaba babu guda daya *"Nida ILILEE mezamuyi banda dariya, an maidata tsohuwar karfi da yaji"* Umman Saheeb ce ke lallashi, yan'uwan Abeeda duk sun zo. Umma tadinga basu hkr, Abeeda tace "yanzu wani mataki hjy ta dauka akan Suhayr?". "Wani mataki ta dauka kuwa suda sukeda sojaji da mopol da yan sanda? Ai sune gwamnati", cewa auntyn Zaria kanwar hjy saude ce aure ya kaita Zaria shiyasa ake ce mata auntyn Zaria. "Ke kinsan cewa matarsa yar iskace kika shigemai?" Abeeda tace "Aunty koda Suhayr zata kasheni ne naji nagani, zama da Saheeb ba fashi," Wage baki aunty Zaria tayi tace "Allah yabaku zaman lafya Kuzo mutafi, Ba Wanda yace kala, Sai kanwar babanta "inya samu gdan a kawo miki kayan dakin." "toh" Abeeda tace jiki ba kwari gashi ba Saheeb ba labarinsa. Musty ne yashigo yana waka, mai rabon shan wahala koh a karkashin gado yake saiya iskeshi, Kowa binsa yayi da kallo daga karshe ya fashe da dariya yace " ke kadan kika gani wahala yanzu kika fara sha, yanzu kika tsoma kafa indai Suhayr ce, kin kade, Ji yadda ta canza miki halitta wata rana kar yaki zatayi ta watsaki waje....." "Kai dakata" cewar ummansu "bansan shashanci".Home / JARABABBEN KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 28 JARABABBEN KISHI part 28 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 20:18 Dariya yayi ya fice aguje. Saheeb yadamu kwarai Rashin ganin Abeedah haka itama. Neman gda yakeyi shida Suhayr suke zuwa koh ina, Anyi nasara ansamu gda a wajajen, kofar famfo. Flat ne kato mai falo biyu, akowani falo ana akwai dakuna biyu sai kitchen a ciki Suhayr tace "gda yayi kyau, yanzu zan dawo gdan mijina insakata in wala," kallon ta kawai Saheeb keyi. Yakasa cewa uffan, can yace "Yanzu hankalinki ya kwanta koh?" Juyowa tayi da sauri tace, "Ina ka taba ganin mai kishiya hankalinta a kwance? Ai har abada tana cikin tashin hankali har sai, saitaga tarabu da kishiyar nan lafya, ko kuma kishiyar ta mutu" Kasa cewa uffan yayi yace "muje insamo miki mai kwashe kaya" "Toh" tace acikin zuciyanta tace " hmmm na dauka zakayi magana ne Saheeb Dana fede ma bindi har wutsiya" Sun tare a gda daya Saheeb ya tarasu Don yayi musu fada, Sannan uwar gda ta fadi kwana nawa ta yanke? Zaa dinga raba kwana. "Dan Allah Ku hada kanku Suhayr banason tashin hankali, nayi aurene Don samun natsuwa da kwanciyan hankali, badon indinga raba fadaba,...... "Kai har kanada bakin cemun, kayi aure Don kwanciyan hankali? Daman duk zaman da mukayi daman zaman azaba kakeyi?" Saheeb yace "Ah ah Suhayr kinyi misunderstanding dinane ba haka nake nufiba".... " ai baka ba kwanciyan hankali, tunda ka iya kara aure, kwanciyan hankali sai dai kaji a makota, Kwana kuma kuya shafa kuna iya yankewa", fuuu ta tashi kitchen ta shiga tafara dafa abinci itada hawwa mai aikinta. Tuni kamshi ya bude koh ina gashi Saheeb yunwa yakeji, Tashi yayi ya fita duk akan idon Suhayr, Abu ya ruko a Leda guda daya.. " wato naka kaida amarya toh kayi kadan, kofar taje ta bude tace "Memuka samu ne Ango mijin amarya"? Bata tsaya ba ta amsa ledan taga kaza daya da kemuka, dagowa tayi tace "Ashe adalcin da kake ikirarin zakayi kenan.....
Share this
JARABABBEN KISHI Page 16 to 20
JARABABBEN KISHI part 16 JARABABBEN KISHI part 16 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:41 Duk abunda kawar suhayr ke fade duk a kunnen saheeb, Hannu yadaga sama yace "Allah kasa suhayr tayi amfani da wayannan fatawa" Amma saiyaji akasin haka. A ranan ummu hydar ta tafi tabar suhayr da dumbin tunani. Shi kuma saheeb ya rasa yadda zaiyi, akullun yanada shaawar ganin ya tara mata domin ya tara yaya masu yawa. A haka suhayr taci gaba da tsula tsiyarta, duk inda taji yaje neman aure saita wargaxa, sai da tayi sanandin lalacewar auren daya nema guda 7. Danginsa suma sun bashi mata duk yadda akayi da boyewa sai da ranar daurin aure taje da bindinga tasawa waliyyin a goshi yana daurawa zata aika dan banza lahira. *CIGABAN LABARI* Nan yan'uwa aka fara cece kuce akan saheeb lallai suhayr tafi karfin shi, harta isa ta hanashi qara aure?. Saheeb ne ya juyo cikeda bakin ciki, dajin kunya ga dubban abokansa harda abokan cini kayyanshi Yace "suhayr am disappointed in you, you disgrace me in public? Had I know zaki zaman mu matsala a rayuwana, tabbas daban au........" "Saheeb dakata" wata murya yaji kakkausa Da alamu babu wasa acikin muryan. Juyowan da Saheeb yayi mahaifinsa yagani, Mahaifin nashi yace "Tabbas auren ka da suhayr alkhairi ne, Sannan bakada wata kallaman daxaka aibanci suhayr, Tacika mace jaruma, Sannan Wallahi tayima komai duk abunda akeso mace tadunga yiwa mijinta kasamu". Shidai Saheeb bakin ciki ne ya isheshi, yarasa makemai dadii yaci gaba da cewa" Kaida kanka Saheeb duk randa zan tambayeka cewa ya zaman takewanka da Suhayr? Kakan cemun babu wata matsala, Toh banga dalilin ka na kara aure ba tunda bata gaxa wajen kyautata maka ba". "Amma Abba".... "Bansanjin wani kalma daga bakinka ba ku tafi gida kawai". Sun koma gda ba Wanda yace ma kowa kanzil, Ahaka suka cigaba da rayuwa har Suhayr ta haihu baice da ita komai ba, ko barka bare kuma yadauki da yayi masa huduba tundaga asibiti daya kaita bai kara hada Ido da itaba. Bayan mahaifin Saheeb yazone ta gayamai halin da ake ciki, Yayiwa da huduba yasa masa sunan mahaifinta wato kabir Wanda tayimai lakabi na NOOR wato (haske). Murna a wajen Suhayr bai misaltuwa. Suhayr ta hana kowa zuwa mata barka daga danginta har na mijin, Sannan tafadi ma ummanta bazatayi suna ba kuma baxata koma gda wankaba, Abunda ya daurewa ummanta kai shine yadda Suhayr ke magana ba koh alamar shakka, ta kaleta tace "Suhayr meye dalilinki na Na cewa baxakiyi sunaba? Kuma kinsan yin suna yaxaman mana al'ada" Tace "Umma nace baxanyi sunaba' saboda bazan juri ganin mata acikin gdana ba Sannan meye abun doki dahar sai anyi suna bayan uban d'an baya maraba da zuwansa duniya". Tana magana tana zubda hawaye Wanda duk Wanda ya kalleta saiyasan cewa Rashin kulatan da Saheeb bayayi yana cimata tuwo a kwarya. Umma tace "Suhayr hakanan Saheeb bazai juya miki bayaba saidai inkin yimai laifi" Suhayr tace "Wani laifine umma nayi banda ya wuce naje na wargaxa mai auren da yake shirin karawa? Nibanyi fushiba daya munafunceni bai sanar dani cewan zai'yi aureba sai shi? Nikuma nayi amfani da kishina Wanda bashida maraba da leban wuta na ruguza komai, Kishiya a gdan Saheeb sai bayan raina". Umma Suhayr ce tace "kull inba hakaba zaki tafka kuskuren da sai kinyi Dana sani, wannan maganar inkikayi wasa yan Amin suka amsa toh Wallahi zaki mutu kuma yakara aure ke har hudu sainovels / JARABABBEN KISHI part 17 JARABABBEN KISHI part 17 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:43 "Umma bazan iya jure jin kalamanki ba, Maiyasa bazaki bani goyon bayan yaki da kishiya ba? Wallahi umma kishiya ba abokiyar zama bace" Suhayr ke maganar cikin muryar kuka. Umma tace "Tabbas suhayr kishiya abokiyar zamace idan kikayi dace" Tayi saurin cewa "Umma kiji kalamanki? cewa kikayi idan nayi dace? Nikam kishiya ba kwai bace umma bare in kwankwasa inji irinta, Umma idan kishiya abunyi ce maiyasa bantashi naganta agdanmu ba? Idan kishiya dadii ce maiyasa bakice Abba yakara aureba? Idan kishiya dadii ce meyasa Yawancin marubuta na duniyar yanar gizo ke fada mana illolinsu? Ita kanta *"Humairah B Melody"* tana daya aga cikin victim." Umma tace "Suhayr Karki zurfafa kishi don koba jima koba Dade namiji mai son aure saiyayi, Allah ya hadaki da miji jarababbe saidai kiyi hkr" tayi saurin cewa "Hkuri umma? Nikuma zanyi amfani da jarabata da *jarababben kishina* inci gaba da wargaxa mai tsari". Itadai umman Suhayr cewa tayi "Allah yaganar dake hanya madaidai ciya, Amma duk abunda kike na kyautatawa, tabbas kici gaba Karki fasa namiji wawa ne?. An hado mata sha Tara na arziki harda k'yautan mota tsalleliya daga mahaifinta, Akwati biyar nata' uku na jariri NOOR, Sannan ga kudi masu yawan gaske. Rago biyu Saheeb ya yankawa yaro, mai aikice tayi gyran nama ta soyashi tsaf makota kawai tamikama suma ba dukaba, dangin Saheeb sunyi tsaigumin Rashin kawo musu naman dabatayi ba ( *Nida belly mukace kuma da shegen zalama kuke*) Saheeb yafara sauyawa, yadaina fushi da ita Sun koma kamar da amma fa burinsa yananan na kara aure. Wata safiyane aka buga kofa, Direban gdansu tagani, "lafya naganka da sanyin Safiya?". Driver yace "Eh Alhaji ne yace in sanar miki da cewa kishirya wani sati ansama miki makaranta a *NORTH WEST UNIVERSITY*" "Dan Allah?". Tayi murna sosai, saboda murna saida tabashi tukwaici. Saheeb na shigowa ta karbi ledar dake hannun sa, tayi mishi maraba Yayi wanka ya gabatar da sallah sannan take gayamai cewa ansama mata makaranta, yaji dadii Kwarai yace Allah yabata sa'a Shiri suhayr takeyi zata gdasu tun Asuba ake dauki Tare suka fita da Saheeb ta saukeshi a shago itakuma ta wuce da alkawarin inzata dawo zata biyo tadaukeshi, " I love you Saheeb" tace tana mai kallonshi, yayi murmushi yace "your love to me is like a priceless Gold" itama ta mayar masa da cewa "You are expensive in my life Saheeb I can go on without you in my world". Dariya yayi yace, "Suhayr kenan duk abunda kika fadii nima haka nakeji a zuciyana". Kissing dinta yayi yashafa kan Noor Yace "ka gaida grany da takwara" Har yayi nisa ta kirashi "pls Saheeb banda kalle kalle". Hancinta ya lakuta yace "I promise you dat my love". Akan hanya ta sauka tayiwa Umma siyayya, tufa ta saimata da kayan marmari. Rike take da noor saiga wata mata daganinta baxawarace don bazaka kirata da budurwa ba. Duk'da ba abun mamaki bane samun babban mace kamarta batayi aure ba.KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 18 JARABABBEN KISHI part 18 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:44 Kusada Suhayr ta matso tace "Sannu fah inason yaronki". Washe baki tayi abunka da mai yaro wawa "Tnx alot kin ganshi duk ya kosa yaje yaga grany". Matar tace "Ehyah inbazaki damuba Dan Allah meye sunansa dake kanki". Suhyr tace "Sunansa NOOR nikuma Suhayr". Daidai da an miko mata kayan data siya na kayan marmari. Tace "Dan Allah bawan Allah biyoni dashi". bayan boot ta bude ta zubasu. Tuni suhayr ta manta da wannan matar, motarta ta shige don Suhayr batason zakewa. "Baiwar Allah tsaya". Ina tuni suhayr ta figi mota..... Tana isa bakin gate tayi horn aka bude mata, Packing loge Ta nufa ta jera tata motar da sauran. Waya ta dauka don ta sanar ma Saheeb ta isa amma akasamu akasi yana waya kasar waje, don yayi odan kaya Ta kirashi yafi sau tulin gashin tinkiya amma shuru" Tuni zuciyarta tafara tafar fasa, cewa Saheeb da mace yake waya. K'ara k'ira tayi aka samu ak'asin a 'network' kiran yashiga wayar wata..... Bugu daya aka dauka Ba jira Suhayr ta fara bala'i ta inda take shiga batanan take fitaba "Ka tuna Saheeb you promise me cewa bazakayi waya da wata mace ba pls Saheeb kasan ko yadda nakeji yanzu?. Shuru taji Suhayr tace "mijina abun alfahari answer me pls" "Hello kiyi hkr ba mijinki bane" Damm!!!!!!!! Taji zuciyarta ta buga jin muryar mace Dayake shu'uma tasamu dukda bata Santa ba amma tana bakin cikin ganin mace ta hana mijinta sake wa Koh kuma mace mai shegen kishin tsiya. "Kinyi shuru nace ke wacece?" cikin zafin rai Suhayr take magana. "Islam ce Kuma ni budurwan mijinki ce, gashi kusa dani yana bacci daya tashi wanka zaiyi yayi sallah don bashida cikakken tsarki saimu wuce juffatu muyi shopping". Jiri Suhayr take gani idonta na juyawa, Karfin hali tayi tace "baki isaba yar iskama irinki harkin isa mijina yaxama abokin iskan cewar ki???? Karyarki tasha karya Wallahi kin gamu da ajalinki indai nice yar iska Mara mutunci Mara Sanin ciwon kai" Tsaki tayi tace "kinibibi sakarya indai mijinki ne ke kadai sai ingani. Katse wayan tayi. Mai gadi taba NOOR yashiga dashi tace tana zuwa Mota ta shiga Shagonsa ta nufa cikin ikon Allah yana ciki yana ta sallaman customers. Saida tabari ya sallami kowa tace "Saheeb kataimakeni ina cikin rudani wacece kaba wayanka?" Saheeb dafe kirji yayi yace "nooo Suhayr you most be dreaming tunda na shigo shago Wallahi ko waje ban lekaba". Mamaki duk ya cikata Kira wayar kiji cikin ikon Allah ta kira yadauka taji gashi dai muryan mijinta ne Duk sai taji kunyan ta kamata "Saheeb kayi hkriiii....." "Shhhhh!!!!! Karkiban hkr abunda nakeso dake shine./ JARABABBEN KISHI part 19 JARABABBEN KISHI part 19 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:45 "Abunda nakeso dake kizama mai yimun kyakkyawan zato, Kiyarda dani Suhayr " Suhayr tace "Saheeb kayi hkr amma kaji na rantse maka mace tadau wayanka". Saheeb yace "Haba Suhayr ana samun matsala daga network In mutun yakasa samun ka kawai sai suyi Diverting Call dinka saiya shiga wayar wani Inkuma dashi wacce ta dauka zata duba baxataga lambar ba" Tashi tayi tace "natafi don koh umma bata ganni ba" Saheeb yace "OK love you " kallonta Saheeb keyi Kaunar matarsa kawai yakeyi a ransa. Gida ta wuce ummanta tagani rikeda noor sai kuka yakeyi "Oyoyo umma" Umma ta tarbeta da cewa "dakata Suhayr narasa gane miki, wannan kishin ina rabaki dashi amma kinkiji." Suhayr tace "Umma menayi kuma" Suhayr tabata rai Umma tace "inajin duk Abunda ke faruwa shine kikaje shagonsa koh? kitadamai da hankalinki? In baki ba mijinki farinciki ba Suhayr mezaki bashi? nidai ina baki shaawara ki daina don bashida amfani, Amsheshi kibashi madara yasha". Haka sukayita hira har yamma gashi Abbanta baidawo ba, Tabar sallahu cewa tana gaidashi Zata dawo kafin ya koma. Saida tabiya ta shago ta daukeshi, Suna isa nimrah suka gani a bakin gate Sai cin magani take tana cika tana batsewa. Mai gadine ya bude gate suka shigo, Fitowa Saheeb yayi rikeda noor a hannun shi, ya kalli Nimrah yace "Nimrah lafya kike kuwa? Baki iya ki gaidani ba?" Nimrah tace "Dan Allah yaya kasan tun yaushe nazo gdannan? Kuma umma tace karna dawo saina ganka". Zaro Ido yayi yace "lafya?" Nimrah tace "Inafah kusan sati umma batada lafya bakaxo ka gaidata ba Koh kiranka akayi bakason dauka". Nimrah ta tabe baki ganin Suhayr taxo wajen Saheeb yace "Nidai banga kiranku ba gaskiya" Suhayr tace "nicenan nake kashewa, saboda muna cikin jin dadii ba Wanda ya isa ya hanamu sukuni" "keeehh Suhayr kinsan koh uwa tawuce gaban wasa? Yanxu da mutuwa tayifa? Saheeb ke magana cikin bacin rai. Suhayr tace "Dana shiga uku". Nimrah dake tsaye tana ballama suhayr harara , tace "kuma umma tace inna ganka mutaho tare". Suhayr tayi saurin cewa "Ba inda zashi sai gari ya waye" Nimrah tace "Aikam kinyi kadan inace kema wajen naki uwar kikaje? Kuma sainaga bai hanaki ba". Suhayr tace "ai uwata ce" Nimrah tace "shima Uwarsa ce" Kallonsu kawai yakeyi yana kallon son zuciya irinna Suhayr..... Baice da ita komai ba hannun nimrah ya rike taji kaman ta kurma ihu, tace "Saheeb ina kake shirin zuwa?" shuru yayi nimrah tace "gurin ummansa zashi" tafadi tana mata gwalo. Ciki Suhayr ta shiga tace "lallai sainayi maganin nimrah Saina nuna mata cewa ita karamar yar iskace", Kwafa tayi Sallah tafarayi Sannan ta shiga kitchen tafara girki. Taliyace macaroni ta Dafa Wanda yaji kayan lambu" Wanda ya hada da carrot, pea, harma da cabbage, Ga hanta Sai tadanyi pineapple juice Dan daidai. Farfesu tayi musu na kafan sa Tajerasu a dinning. Jikin mahaifiyanshi ya tsananta, Tuni yashiga rudu asibiti aka wuce da ita, Ruwa aka Samata. Dayake kusa da zoo road ne "Bari naje gda" yacewa kanninsa ya kawo musu abinchi Yana isa gdan yashiga Suhayr yake kwalawa kira Fitowa tayi cikin wasu yan iskan kaya Wanda bashida maraba da ace tsirara Take. Bata nunamai wani abu ba, Saima murmushi datake tana taku daya kan daya, Wanda tuni Saheeb yaji gaba daya jikinsa ya mutu, Kusa dashi ta matso "Wani irin kamshi yaji tuni ya sunkuceta ta sai daki kan gado ya ajeta. Yafara.HI novels / JARABABBEN KISHI part 20 JARABABBEN KISHI part 20 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:48 "Lafya yaya bai dawo ba har yanxu?" Cewar Sarah mai bima nimrah. "hmmm inkika bibiya wannan yar'iskan matar tasa ta hanashi ya fito" cewar Nimrah. Amrah dake zaune tana kallonsu Batace dasu uffan ba don arayuwarta ta tsani ayita cece kuce don ita tace Suhayr bata kai matsayin dazata dinga maganarta ba. Amrah hatsabibiya ce rigimanma don tace Nimrah batai komai ba. Nimrah tace "Amma bari na fita waje inje in siyo mana koda dankaline muchi". Nimrah ce ke magana daga ganin fuskanta kasan cewa akwai damuwa kwarai. Wata budurwace daganinta kasan tasha boko ta koshi tajiyo duk hirarsu. Tace daga gani da matar wansu suke Amma kuma sunban tausayi. Tashi tayi ta dafa kafadan Amrah tace "beautiful yanaga kin bata fuska? Kina neman ki bata kyawunki?" Amrah tace "Kamar yadda kika gani mahaifiyar muce ba lafya Kuma da yayanmu mukazo yaje ya kawo mana abinchi kinga bashi ba labarin sa Kuma baya rasa nasaba da matarsa don taki jinin mu balantana kuma umman mu Kila ita ta hanashi dawowa, yadda kikasan tayimai asiri". "Karki damu ya mai jinkin" ta cewa Nimrah. Nimrah tace "Da sauki bacci takeyi". "OK bari ina zuwa" flask taje ta dauko makare da abinchi ta kawo gabansu tare da cewa "Pls kannina kuci abinchi idan umma ta tashi kubata taci". Mamakin kirki irin nata sukeyi Sarah tace "inba zaki damuba inason Sanin sunanki". Budurwar tace "Ni sunana Atika". "Suna mai dadi" cewar Amrah. Har dare ya tsala Saheeb bashi ba alamansa, Haka suka kwanta a kujera sukasa Kansu a gefen gdon da ummansu take kwance. Washe gari kaman a mafarki Saheeb ya tashi, sai a lokacin yake tunawa da ummansa harma da kanninsa, tagumi yayi kawai sai hawaye Wanda nima Humairah bansan kona meye ba. Nashiga uku kallon Suhayr yakeyi wacce batasan me duniya take ciki ba Duka ya Dada mata ji kake tas!!!!! "tashi tabbas Suhayr zaki iya halakar danii bansan cewa kin kware a yaudara ba, bansan cewa bakida imani ba" Saheeb ke maganar cike da takaici. "Saheeb wat is the matter? You wake me up and you're insulting me? For goodness sake wat have I dont?". Suhayr ta fada itama da bacin rai. Saheeb yace "Ai daman baxaki saniba tunda kinyi succeeding nabar mahaifiyata da kanina da yunwa bayan nagaya miki cewa ummata tana asibiti kizuba abinci inkai musu". "Yanzu mekakeso kace Saheeb? Nabar mahaifiyarka da yunwa? Toh h you are wrong saboda hakkina dake kanka ka sauke, so i don't care". Ta fada tana mai niyyar komawa ta kwanta. Cikin bacin rai yace "Suhayr kafin in irga uku ki tashi kishiga kitchen kidafama umma abinci ki hadamun inkai musu inba haka ba Zan nuna miki true color na". Ya qarshe da tsawa. Haka Suhayr ta tashi Minti arba'in yayi yawa ta kammala. Ya dauki hanya sai asibiti, Yanata tunanin wace karya zaiyi ya gamsar da kanninsa? Yana shiga cikin asibiti wata ya hango ba wata bace Abeeda ce take ba ummansa abinchi a baki. Lokaci guda yaji sonta yashiga cikin zuciyarsa, "Inama Suhayr ce takewa ummata haka Danaji dadii" Abinda yake fada kenan a xuciyarshi. karasawa yayi yace "umma Ina kwana" koh kallonsa batayi ba Kanninsa ma kowa ya bata rai. "pls my sisters kuyi hkr wallahi........" Bai karasaba nimrah tace "nasan yaya tunkafin kaxonan kashirya irin karyar dazaka sharara mana Dan haka bamu da bukatar jin wani Abu daga bakinka" Umma dake kwance tace "kinyimun Daidai Nimrah kai dai kam kaji kunya wllh". Tsayawa yayi jikinsa duk yayi sanyi kunya duk tabi ta isheshi. "umma kiyi hkr tunda yasan yayi kuskure" Abeeda ke magana cikeda ladabi. "Umma albarkarku itace kadai ke tasiri a rayuwar mu Kishi mishi albarka sannan kidinga mishi Adu'a Allah ya tsareshi daga kaidin mace", takarasa tareda kallon Saheeb Wanda yayi nisa a fagen son Abeeda. (Tir kashi Abeeda dai kawar Suhayr ce amma batasan cewa saheeb mijin Suhayr bane kubiyoni donjin sauran labarin
Share this
JARABABBEN KISHI Page 11 to 15
JARABABBEN KISHI part 11 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:14 Bayan wata biyu, suhayr ta kasance mace mai kiyaye duk wani hakkokin mijinta babu abin da ya nema ya rasa daga gareta, matsalarta daya a duniya kishi bata son kishiiya kuma bata kaunar duk wata mace ta rabeshi hakan yasa ta roki alfarmar mahaifinta ya bashi kudi ya ja jari ya bude shagon sai da hula da agogon maza, domin bata son yayi "white collar job" Da hakan zai kawo cudanyrsa da mata ko da kuwa yan uwanta ne bare Kuma nashi. kyawawan dabiunta da kuma son da ta ke masa yasa ta samu love dinsa 100pecent domin duk wuya duk dadi tana jurar yi masa komai, Tana zaune a falo taji ana knocking ta miqe taje ta bude kofar taga wasu yan mata kyawawa, sunsha mai da foundation, kallonsu takeyi shekeke Wanda haka yaba nimrah haushi tace wai ko baki ganeni bane?". Suhayr balla ma nimrah harara tayi tace "mekikazo yi gdana da wayannan masu kama da aljanun?" Suhayr ke magana cikeda isa sa fankama. "kut gaskiya nimrah matan wannan naki batada mutunci mine ma masu kamada Aljannu?" Suhailah ce ke magana tana taunan cingam. "Suhayr magana muke kina kallonmu", Dariya tayi tace "inajiran inji dukane saboda Nace muku masu kamada mami water". "Ke !!!!" Nimrah ce ta dakawa suhayr tsawa "dakata kiji karki ga kinama sauran mutane insunzo gdanki kice zakimun, danni nafi karfin yinki wallahi saidai inyida gyatuminki". Suhayr ce tace "Habawa Nimrah kinso ki tafka babban kuskure wajen tabamun iyaye Wanda nasan sunfimun naki iyayen sau miliyan, ai kinsan bakin rijiya ba gurin gadar makaho bane, Nimrah kafin inbude idona in rufe ki fitarmun da wayannan masu kamada yan ruwan inba hakaba I will surely sure you gals mah true colour". Nimrah tace "Aikam da wuya yau inba'a haifi da Mara Ido ba" inji nimrah Wanda ta runtse Ido bataji bata gani, don tsabar takaicin abinda Suhayr tsyi masu. "Mai gadii John" Yayi saurin shigowa yana cewa "yes mah hjy lafya irin wannan kira". Cikin bacin rai Suhayr tace "How many times have I warn you that I don't want to see any lady in dis house apart from my mum? Haven't I warn you?" John jiki na rawa yace "yes mah," "oya before the count of three I don't want to see any of this things infront of me". Da duka john ya rakasu ammafa nimrah baki yaki mutuwa "cewa tayi "yau kin nunamun gida nakine Suhayr amma saikinyi ladaman cimun mutunci shegiya yar matsiyata." Ciki ta koma ta harde kafa Ashe saheeb nanan suhayr ke cima nimrah da friends dinta mutunci, "Hayaniyyan me nakeji suhayr?" shuru tayi kaman bada ita yakeba can ta dago ts kalleshi tare da cewa "Pls saheeb ka gayawa kanwarka, nasa mata boundary da gdannan". Shima cikin bacin ran yace "kozaki iya gayamun dalili?". Tace "Dalili shine zan iya raunatata inta kara shigomun da kawayenta, masu suffan jinnu gdannan, Akan mema saitaxo gdannan nifa banason shisshigi ka gaya mata," Saheeb ne ke zaune kusa da ita yace "suhayr nimrah kanwata ce kiyi hkr da abunda zan fadi Nimrah nada ryt din zuwa inda nake". Tayi saurin dakatar dashi da cewa "dakata Saheeb inada kishi da banaso kayi tozali dawata mace inba niba, don haka ta kiyayi gidannan, don ko jaririyace ina matukar kayi mata murmushi bare baliga kaman nimrah." Yace "Amma dai kinsan nimrah muharramata ce?". Tace "Koma me CeCe nagama magana" tashi tayi tashiga daki. A ranan ya shiga wani hali ummansa ce ta kirashi tacimai mutunci, sannan da sharadin saiya kara aure ko yana so ko baya so.Home / JARABABBEN KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 12 JARABABBEN KISHI part 12 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:34 Tunani mai zurfi ya shiga amma bashida yadda zaiyi, Suhayr ta hanashi mu'amala da mata harma da yan uwansa, Gashi saheeb yana matukar kaunar matarsa bayason yaganta cikin damuwa, bayason ganin bacin ranta, Amma yana mamakin kishi irin nata, inda za'a bashi littafi da Biro tsaf saiya rubuta kishin suhayr gaba daya. Saheeb Yakama sana'a ba kana hannun yaro acikin manyan plaza dake kan hanyan Hotoro. Dayake wajen center ne inda manyan mutane ke wucewa, Gaba daya kayansa na wajene saidai kayan gida kaman su shadda, huluna, dadai sauransu. Amma fah koda yaushe akan waya sukeyi da sahibar tasa wato suhayr, arana saita kirashi fiye da sau talatin, saboda kishi dake dawainiya da ita Amma hakan bai hanashi yin budurwaba, Daman masu iya magana nacewa duk wayon amarya sai ansha manta, Haka shure shure baya hana mutuwa. Ranan yatashi da wuri daga shago ya kashe wayansa, saboda yanaso yaje family house dinsu ance ana Neman sa, don yasan inya gayawa suhayr saitasan yadda tayi ta hanashi zuwa, adaidaita yahau sai dorayi, Yana shiga aka yimishi cha mijin hajiya! Mijin hajiya!! Mijin hajiya!!!. Yadanji kunya kwarai amma ya maxe Yaga dangi kowa ya hallara abun yayi matukar razanashi, Zama yayi ya gaidasu, "yauwa saheeb abunda ya taramu anan shine gameda matarka suhayr Data hanaka sakat saboda kana zaune a gdansu sannan Kuma tabaka jari". Inna larai ke magana shuru yayi baice kala ba saboda yasan daman za'a Rina, "Dalilin taruwanmu shine munaso ka kara aure". Zare Ido yayi yace "aurefa kukace? Dan Allah karkuyimun haka dududu watanmu nawa da aure zaa kawomun zancen wani aure yanzu Haba Dan Allah kucanza wata shawarar amma ba wannan ba". Ummansa dake gefe tace "dole kayi aure don samun kwanciyan hankali". Bashi da yadda xaiyi dole ya amsa masu ba don xuciyarsa na so ba, a haka yakoma gida cikeda tunani iri daban daban, ta ina ma xai fara sanar da Suhayr wannan xancen?. Da shigarsa yaji kakarin amai da sauri ya yadda ledojin dake hannunsa, Da gudu ya shiga toilet suhayr yagani tafita hayyacinta. "Subhanallah cutie meke damunki haka"? Bata iya bashi amsaba, illah hawaye dake tsirarowa daga idanunta "Saheeb zan mutu ka kaini asibiti". Mota ya dauko yasata suka wuce asibiti. Likitane yace ashiga da ita, amma suhayr dukda ciwon da take bata sassauta kishinta ba, gam ta rike hannun saheeb tare suka shiga anyi mata test kusan kala uku, " congratulations yallaboi madam tana dauke da ciki wata biyar". Saheeb yayi saurin cewa "Likita wata biyar fa kace ya akayi bata saniba Kuma nima haka?" Likita yace "Tana iya yuwuwa inna farine baxata ganeba,haka kaima, amma ya kamata a kula da ita sosai musamman ma abinchi, tadinga cin kayan marmari irinsu zogale dama dai sauran kayan Karin jini A yanzu bata bukatar motsa jiki saboda Dan bai rigada yayi kwari ba". Murna wajen saheeb sai Wanda yagani don ji yake kamar ya hadiyeta don murna.KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 13 JARABABBEN KISHI part 13 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:36 An sallamesu, hjy ikilima musamman taxo don ganin yartata, Sunsha fira tsakanin ya da uwa tuni aka fara siyayyan kayan ahaihuwa. BAYAN WATA Uku ne lokacin cikin Suhayr yana wata na takwas, Dangi fah sun tashi haikan ganin saheeb yakara aure, Domin sunce suhayr tayi musu Kane Kane gashi yanzu arziki yaci uban Nada, sai a cika gida da iyali, Saheeb yafara Neman aure gadan gadan, amma duk abunda yakeyi suhayr bata saniba, Har ansa ranan wata uku duk ya maidata biri boko, makota tashi ga saiga wata mata tashigo, tana cewa, "ke ummu aiman Ashe makocinki aure zaiyi? Duk kishin da ake cewa matarsa nadashi". Ummu aiman sai siginal takewa indo amma itako sai zuba takeyi, Saidata gama tsaf suhayr taji wani irin ciwo na naman cin karfin ta tace,"Baiwar Allah kozakimun kwatancen gdansu yarinyar?". "Kwarai maizai hana". Inji indo. Nanfa indo tayita mata kwatance harta gane. "Ngd" tace tashi tayi taje gda, tace "yau saiya gane cewa, ruwa ba sa'an kwando bane, sai ya gane shayi ruwa ne saina nunawa saheeb cewa yayi kuskure namiji munafiki, ni xai munafurta? Ya qara aure? kabashi dukkan yardarka yacima amana". Gyale kawai ta chanja ta nufi Gidansu yarinyar tayi sallama da uban yarinyar, cike da mamaki ya fito yana kallon Suhayr. Tace "naji labarin cewa, zaka aurawa mijina yarka? toh Kasani yarka zatayi kwanan prison matukar tace zatayi kishi dani, Don saina aikata inda baxata kara jin kamshin mijina ba, sannan inkun shirya yarku tazo gdana, toh Ku kawota na nikafali, don sainayi ajalinta". Uban yarinya yace "aikin banza, kewacece? Aikam saimunyi Shari'a dake har yaumut tanadi". Suhayr tace "Mune gwannati kaje ka tambaya waye Alhj kabir sulaiman inajin kasanshi, toh nice diyarsa daya tilo, Inyazo shi mijin nawa kace yaci gaba da Neman aure nikuma, inci gaba da rusamai tsari". Tura cikinta tayi ta shige mota ta badamai kura, Uban yarinya yace "tab ai aure anfasa, baxai iya da wannan ja'ibar ba Daganinta zata aikata duk abunda tace. Saheeb yaje zance uban yarinyar Yace "karya sake zuwamai gida saboda matarsa taxo tayi barazanar kashe musu ya". Gda yadawo cikin bacin rai ya iske Suhayr yace "Suhayr hankalinki ya kwanta kin raba abunda Allah yahada, Tun kafin muyi aure kike abu daya haryanzu kinki ki daina". Tanadaga zaune tace "kamanta dakwai ranan danace ka kalli kwayar idona? nacema maika gani"? Kacemun *JARAB EL GHIRA? Flames of jealousy?* Toh I can do more than wat you are thinking saheeb, Bantaba Sanin cewa kai munafiki bane sai yau butulu kawai Wanda ke manta alkhairi, Bacin so baya dubi da nasaba da chanchanta, Yaushe zan aureka Saheeb? Amma shine zaka zaga bayana kaci amanata? Kayi hkr da kalamaina, nasan kai mijinane, dole infadi Nasan duk umma ce kesawa ka kara aure, Kuma Wallahi Allah ya saukeni lafya, sainaje har gdan tagayamun dalili, Inace ita kadaice wajen mahaifinka? Ohh shine saboda kiyyaya zatasa ka kara aure toh zan gani, Ga fili gamai doki Saura sukuwa". Mari taji ya sauka a kuncinta, "Karki sake yima mahaifiyata cin zarafi a gabana inke bakisan darajar iyayeba Toh ni nasani Kuma aure ba fashi sainayi Kuma ra'ayinane, bana umma ko Abba ba, Saina cika gdannan da zuri'a mai yawa, saidai ki mutu.SHI novels / JARABABBEN KISHI part 14 JARABABBEN KISHI part 14 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:38 Kuncinta ta rike tana mai kallon saheeb Ido cikin Ido, Cike da takaici tace "tabbas saheeb sai kayi ladaman marina saika San cewa ka mareni Akan wata yar iska? Kayi kuskure wannan. *So ne ko kiyayya*? (Na sanah s matazu,) Saheeb magana nakeyi kana jina, aikam inhar numfashi bakai ba kara aure acikin gdannan, Na yima rana shine zakamun dare"? Wasu zafafan hawayene suke kwaranya a cikin idanunta, Amma saheeb koh kallonta baiyi ba, bare Kuma ya tausaya mata saboda abunda take dauke dashi a cikinta. Fuuuuuu Saheeb ya wuce kaman zai tashi sama kuka suhayr keyi tana cije baki saboda wani ciwo datakeji, Tana cikin wannan halinne taji Sallama Ashe kawartace tashi tayi ta bude kofa "ah ah maraba da mutanen jigawa saukan yaushe ina yaran da oga?". Qawar tace "Tab suhayr uwar biyu kenan wannan ciki naki dakwai bayani". Dariya suhayr tayi a Falo suka zauna tasa mai aikin ta takowo bakuwa abinchi da abunsha, "Kawata naji dadin zuwanki wallahi, inada damuwa sosai", tas ta kwashe komai ta gayawa kawarta. Qawar tace "Tabbas suhayr keme lefi ce yazaki dinga yin Abu irin wannan? Bayan kinsan halin maza insuka so Abu sai sunyi ko'a boyene? Tunda nake da baban hydar ban taba cewa bazan zauna da kishiya ba, dama zai kara auren wallahi Nina shigemai gaba don ganin yayi auren Kuma gashi muna zaune lafya". Suhayr tace "Tab aini *Jarababben kishi*na bazai barniba, Akan saheeb zan iya rasa raina". Ummu hydar tace "Tab bari kiji kadan daga cikin wani littafi na matan aure Dana taba karantawa," Kila ya miki amfani don bance dole ba". " Idan har Kika yarda da cewa namiji ba zai qara aure ba suhayr to wllh kinyi wauta domin basu da tabbas a wannan bangaren, karki yarda namiji yayi miki alqawarin baxai miki kishiya ba, shi kanshi ai bai san me yake gaba ba, idan Allah ya rubuta sai yayi auren nan to fa ya xama dole yayi shi". Ta cigaba da cewa "Idan Kuma kika ce ba zaki rike dan Mijinki ba (dan Kishiya) Nan ma kin tafka shashanci babba, don Idan kin haifi naki 'Ya'yan babu tabbacin cewa xaki dawwama a gidan ko a duniyar ma, Idan kuwa kika ce namiji ba dan goyo bane kin zama sakarya, domin kin mance da cewa ai kece baki Iya yanda ake goyon namijin ba" Idan kuma kika ce Kishiya ba abokiyar zama bace ba, mijinki baxai qaro wata matar ba toh ke naki 'Ya"yan Idan kin haifa jere Za Kiyi dasu a dakin ki? Karki raina uwar mijinki domin tamkar uwa take a gurinki. Da dan numfasa snnan ta cigaba "Idan kina wulakanta dangin mijinki, Toh naki dangin waye zai girmamasu? Idan kika ce ke bakya son kishiya toh sauran Yan mata da zawarawan gari suyi yaya?. Suhayr tabbas yaka mata kifarka daga nannauyan baccin dake dibanki Suhayr shuru tayi don tasan dakaman wuya gurguwa da auren nesa, yadda takeda kishinnan aikam bazai taba yuwuwa ba, Ummu hydar taci gaba da cewa, "Idan kika ce ke bakya son Kishiya toh kisani, da yiwuwar ayi miki kishiyar waje wacce Idan akayi rashin sa'a Kishiyar nan taki ta waje ta aiko miki da "SAKON MUTUWA" (HIV Aids) SUBHANALLAH, Suhayr meyasa baxakiyi amfani da wannan hudubar ba ki gyra, lahiranki?". "Tabbas ummu hydar da kishiyar gda tabbas na kwammace ta waje Inta tashi ta kashemu mu duka". Ummu hydar tace "Kash yayan da kika Haifa Kuma fa?". Cewar ummu hydar. Suhayr kai tsaye tace "Suzama marayu" (Ni kam dai nace Suhayr kin fara bani tsoro)ISHI novels / JARABABBEN KISHI part 15 JARABABBEN KISHI part 15 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:39 Duk abunda kawar suhayr ke fade duk a kunnen saheeb, Hannu yadaga sama yace "Allah kasa suhayr tayi amfani da wayannan fatawa" Amma saiyaji akasin haka. A ranan ummu hydar ta tafi tabar suhayr da dumbin tunani. Shi kuma saheeb ya rasa yadda zaiyi, akullun yanada shaawar ganin ya tara mata domin ya tara yaya masu yawa. A haka suhayr taci gaba da tsula tsiyarta, duk inda taji yaje neman aure saita wargaxa, sai da tayi sanandin lalacewar auren daya nema guda 7. Danginsa suma sun bashi mata duk yadda akayi da boyewa sai da ranar daurin aure taje da bindinga tasawa waliyyin a goshi yana daurawa zata aika dan banza lahira. *CIGABAN LABARI* Nan yan'uwa aka fara cece kuce akan saheeb lallai suhayr tafi karfin shi, harta isa ta hanashi qara aure?. Saheeb ne ya juyo cikeda bakin ciki, dajin kunya ga dubban abokansa harda abokan cini kayyanshi Yace "suhayr am disappointed in you, you disgrace me in public? Had I know zaki zaman mu matsala a rayuwana, tabbas daban au........" "Saheeb dakata" wata murya yaji kakkausa Da alamu babu wasa acikin muryan. Juyowan da Saheeb yayi mahaifinsa yagani, Mahaifin nashi yace "Tabbas auren ka da suhayr alkhairi ne, Sannan bakada wata kallaman daxaka aibanci suhayr, Tacika mace jaruma, Sannan Wallahi tayima komai duk abunda akeso mace tadunga yiwa mijinta kasamu". Shidai Saheeb bakin ciki ne ya isheshi, yarasa makemai dadii yaci gaba da cewa" Kaida kanka Saheeb duk randa zan tambayeka cewa ya zaman takewanka da Suhayr? Kakan cemun babu wata matsala, Toh banga dalilin ka na kara aure ba tunda bata gaxa wajen kyautata maka ba". "Amma Abba".... "Bansanjin wani kalma daga bakinka ba ku tafi gida kawai". Sun koma gda ba Wanda yace ma kowa kanzil, Ahaka suka cigaba da rayuwa har Suhayr ta haihu baice da ita komai ba, ko barka bare kuma yadauki da yayi masa huduba tundaga asibiti daya kaita bai kara hada Ido da itaba. Bayan mahaifin Saheeb yazone ta gayamai halin da ake ciki, Yayiwa da huduba yasa masa sunan mahaifinta wato kabir Wanda tayimai lakabi na NOOR wato (haske). Murna a wajen Suhayr bai misaltuwa. Suhayr ta hana kowa zuwa mata barka daga danginta har na mijin, Sannan tafadi ma ummanta bazatayi suna ba kuma baxata koma gda wankaba, Abunda ya daurewa ummanta kai shine yadda Suhayr ke magana ba koh alamar shakka, ta kaleta tace "Suhayr meye dalilinki na Na cewa baxakiyi sunaba? Kuma kinsan yin suna yaxaman mana al'ada" Tace "Umma nace baxanyi sunaba' saboda bazan juri ganin mata acikin gdana ba Sannan meye abun doki dahar sai anyi suna bayan uban d'an baya maraba da zuwansa duniya". Tana magana tana zubda hawaye Wanda duk Wanda ya kalleta saiyasan cewa Rashin kulatan da Saheeb bayayi yana cimata tuwo a kwarya. Umma tace "Suhayr hakanan Saheeb bazai juya miki bayaba saidai inkin yimai laifi" Suhayr tace "Wani laifine umma nayi banda ya wuce naje na wargaxa mai auren da yake shirin karawa? Nibanyi fushiba daya munafunceni bai sanar dani cewan zai'yi aureba sai shi? Nikuma nayi amfani da kishina Wanda bashida maraba da leban wuta na ruguza komai, Kishiya a gdan Saheeb sai bayan raina". Umma Suhayr ce tace "kull inba hakaba zaki tafka kuskuren da sai kinyi Dana sani, wannan maganar inkikayi wasa yan Amin suka amsa toh Wallahi zaki mutu kuma yakara aure ke har hudu sai yayi".
Share this
JARABABBEN KISHI Page 1 to 10
JARABABBEN KISHI part 1 Posted by Bashir Sani Fesan on 16 Dec 2016 - 13:53 Hannunta ri'ke da bindiga ta setashi akan rawanin dake kan waliyyin da ke shirin d'aura auren mijinta da wata macen tana mai cewa "wallahi tallahi ka kuskura ka d'aura wannan auren,sai na d'aura ranka da mutuwa"! Cikin muryar mai d'auke da tsawa mijinta ya mi'ke yana cewa "ke menene haka kin haukace ne? meye kawo ki nan gurin? wannan ai dabbanci ne". A zafafe ta katseshi ta hanyar cewa "idan akan soyayyarka ne na cancanci in amsa sunan dabba domin bana gani bana ji kuma bani da hankali, akan sonka ina iya aikata komai ko da kuwa d'aukar rai ne, bana 'kaunar ko wacce mace ta ra6eka ko da kuwa ta kasance muharramarka ce, ina kishinka mijina, kishina ya bambanta da kishin da ka sani ina maka kishin da bana kaunar ko da jaririyace tayi maka murmushi ka maida mata martani, mijina me ka nema ka rasa a guna da kake shirin kulla alaka irin tamu ni da kai da wata? duk wani kyautatawa da kulawa da mace ta ke wa mijinta ina yi maka, ta ina na tauyeka a zaman aurena da kai? a zamana da kai sai dana tabbatar na maye maka duk wani gurbi a zuciyarka, me ka nema ka rasa a guna? ta ina na gaza?". Ta tambayeshi idanunta na zubar hawaye. Cike da bacin rai yace "ra'ayi! domin ni ban shirya zama da mace d'aya tilo ba, ra'ayina ne kawai in 'kara aure,saboda Allah da manzonsa [s.a.w] basu haramta ba!'' ya bata amsa A fusace, ta maida bindigar kan goshinsa tana cewa "ra'ayi ko dai *JARABA* irin taku ta maza? toh wallahi tallahi idan har ba'a fasa d'aura aurenan ba sai na kasheka,inya so ni da ita mu rasa ka Idan kai *JARABA* ce tasa zaka 'kara aure toh ni zanyi amfani da *JARABABBEN KISHINA* da nakeyi akan ka in da'kushe duk wani tasirin *JARABAR* dake d'awainiya da kai". "Keeee dakata nagaji dajin munanan kalamanki akaina *SUHAYR* meyasa kika dau kishi kumallonki bayan kinsan irin soyayyar dake tsakaninmu?". " *SAHEEB* bakada abunda zaka iya gamsar dani a halin yanzu, amma naci alwashin ruguza aurennan inko ba haka ba yanzu za'a haifi dan daba idoo". Tuni waliyyi da sauran jama'a suka arce don baxasu yarda ayi musu sawarwarin rayuwarsu ba. *LABARIN SUHAYR DA SAHEEB*I novels / JARABABBEN KISHI part 2 JARABABBEN KISHI part 2 Posted by Bashir Sani Fesan on 16 Dec 2016 - 13:57 Suhayr takasance ya ta biyar daga cikin yayyinta maza da take bii daga ita sai autansu, a wajen iyayenta *Alhaji kabir sulaiman da kuma hajiya ikilima* Mahaifinta yakasance hamshakin mai arziki kuma babban Dan siyasa da'ake damawa dasu acikin gwamnati mai ci, suhayr takasance yar gaban goshi sannan duk abunda zatayi a wajen mahaifinta daidaine, Bayason ganin bacin ranta hasalima dayaga bacin ranta gwara a kunduma mishi ashar, hakan yasamo asaline saboda ita kadaice yarsa mace. Amma kuma takasance mai ladabi ga duk Wanda ya girme mata atakaice zamuce tanada ladabi da biyayya gana gaba da ita. Wata asabar ne sakaliya suhayr ta tashi da dokin zuwa bikin kawarta wacce sukayi Hassan Gwarzo tare, ta shirya tsaf ta shiga dakin mummy don tayi mata sallama, tace "Mummy yakika gani ,shigannan tayi?" Ta fadi tana fari da ido, hjy ikilima murmushi tayi tace "my beautiful daughter you are such a pretty damsel, Allah ya azurtaki da miji nagari Wanda zai kula da surar da Allah ya azurtaki da ita," Tsalle tayi tace "Mummy kina fasamun kai sainaji duk duniya babu wata ya mace datakaini". Mummy tace "tabbas hakane babu koda ita aikam sai ansamu banbanci ko wajen shafa jambaki, Maza yata Allah ya tsare ga wasu yan kudi kibiya koda shop rite ne ki siyamata gift Wanda zaki kaimata". Ta amsa tare da cewa "toh ngd umma Allah yakara girma da tsawon kwana da daukaka" "Amin!" Tuni aka wanke motar dazata fita dashi tana baya direba na tuki a gaba saida sukayi siyayya kana suka wuce *GOLDEN DRAGON* *dake hanyan nasarawa G.R.A inda ake friends Eve* Tun a waje taga wani gaye Wanda kunnenta yajiyo mata sunansa SAHEEB dagani ba tambaya kanwarsa ya rako wajen, tuni taji ya shiga ranta yadda bazata iya rayuwa inba dashi ba. Wucewa tazo yi tace "hey" ko kallonta baiyi ba saboda bawata mace a gabansa inba HUMAIRAH ba wacce aski yariga yaxo gaban goshi bikinsa saura wata biyu. Rashin amsatan da baiyi ba bai wani bata mata rai ba illah wani sonsa dataji yake shiganta kaman yarda iska ke ratsa mutun idan yana bakin rafi. Da shigarta tanata ware ido don ta hango kanwarsa taxauna kusa da ita don dakwai tambayoyi data tanada zatayi mata akan SAHEEB. Can ta hangota kusada amarya maryam wadda suna ganin juna sukayi wani irin shewa aka tuno da school life, janta tayi gefe tace "ke waccan yarinyar kawarkice?" "Eh" maryam tace, Suhayr tace "wallahi wani naganta dashi kaman Dan uwanta wallahi am in love, pls help me kinsanni idan inason abu gaba daya nake ruftawa". Maryam tace "Kash suhayr ai kinyi latti inajin bikinsa bai wuce saura wata biyu ba,"ARABABBEN KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 3 JARABABBEN KISHI part 3 Posted by Bashir Sani Fesan on 16 Dec 2016 - 14:00 Suhayr ta cigaba da cewa "Pls maryam just tell me u r joking ?" Maryam tace "haba suhayr yaushe muka fara yar wannan dake kinsan cewa I can't lie or tell you a joke,it's the truth u better accept it or leave . "Ohsshh' suhayr ta furta sannan tace "yazanyi kenan?" daidai da zuwan wasu friends din maryam hakan yasa ta dubi suhayr Tace "am coming nayi baki". suhayr kujera ta samu ta zauna saboda kafafuwan ta suna Neman kasa daukanta, dafa kanta tayi gaba daya taji ranta yabaci wani irin kishine ke bijiro mata, Wanda bashida maraba da leben wuta..... Ahaka aka fara event amma gaba daya hankalinta da tunaninta yana wajen Saheeb Wanda yaketa zuba love acikin waya shida masoyiyarsa Humairah, Inyana tareda ita gaba daya jinsa yake kaman ba'a duniyaba, saboda dadadan kalaman da Humairah take tanada kullum don ganin farin cikin hubbinta. Daga ciki suhayr tana kallonsa daga waje yadda farinciki da annashuwa yake dawainiya dashi. "Oh ni suhayr mezanyi ganin na lalata alakar dake tsakanin sa da wadda ake ikirarin zai aurah?". Tambayar da takewa kanta kenan agun. "yes!!" tuni wata dabara tazo mata direbanta ta kira tace yadan zagaya tunda bayanxu zasu gamaba. Bayan yan mintuna ta fita harabar waje bata nufi ko inaba sai wajen da Saheeb ke tsaye jikin wata mota, "Salamu alaikum!" tace amma ina yayi nisa, Ta kara masa sallama shiru har saida ta buga saman motan sannan ya juyo. "Yi hkr gimbiya zankiraki yanzu", yana juyowa sai yakasa koda motsi saboda kyawun sura da Allah yayi mata, amma ina is too late to cry went the head it cut off. "Yah lafiya ?" Ya jefe ta da tambaya, Tace "Wallahi nayi running out of battery ne inaso inkira direbana ne, daga yaje yadawo amma shiru" suhayr ta maida martani. "OK badamuwa gashi ki kira" saheeb ya fadi tare da mika mata wayarsa. Wani murmushi tayi Wanda bashi da maraba da Dana mugunta, a zuci tace "ina matukar kishin Wanda nakeso don haka kana bani tausayi don saina rabaka da ita aure kuwa sai an fasa" matsawa tayi daga gun tare da fara yin wayar bogi, bayan ta gama wayar bogin sai ta juyo ganin hankalinsa ba ya kanta ,hakan yasa ta yi flashin layinta da wayarsa, sannan tadau number Humairah a recoeved calls dinsa, sannan ta juya ta bashi wayar sannan tace "gashi ngd Allah yasaka da alkhairi" sai kuma tace "Dan Allah in bazaka damuba inason sanin sunanka" cike da rashin damuwa yace"OK sunana SAHEEB kefa ?" Da sauri ta amsa da cewa "sunana suhayr kabeer sulaiman", "Waw NYC name" suhayr tayi murmushi tace"in bazaka damuba zanso muzama abokai" tare da kallonsa ido cikin ido saheeb yace "badamuwa ngd" domin yasan cewa fadi take kawai ,ina ma zata ganshi har suyi wata abota! A wannan lokacin tafi kowa farinciki domin plans dinta sunkusa fara aiki, a ranta tace "saina rabaka da duk wata ya mace ,hatta uwar data haifeka, balle kuma kanwa ko yaya indai mace ce, bakai ba ita.a duniyaba, saboda dadadan kalaman da Humairah take tanada kullum don ganin farin cikin hubbinta. Daga ciki suhayr tana kallonsa daga waje yadda farinciki da annashuwa yake dawainiya dashi.KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 4 JARABABBEN KISHI part 4 Posted by Bashir Sani Fesan on 16 Dec 2016 - 14:02 A ranar anyi shagali ,nan ta samu shiga wajen nimrah kanwar saheeb saboda ta dinga jin duk wani details, Har wajen mota ta raka nimrah tace "ki gaida su mummy Dan Allah insha Allah zan kawo miki ziyara kamar yadda kikamin kwatance" dariya nimrah tayi tace "Allah yakawoki " suhayr tace "amin" har suka bar harabar wajen tana daga ma nimrah hannu Wanda ba nimrah takema ba da Saheeb take Wanda baima San tana yi ba. Mota tashiga cike da damuwa,direba ya bata wuta. Saheeb yana tuki yace "Nimrah ina kika jajibo waccen yarinyar? karfa ki hada kanki da ita yar gdan masu kumban susace ,kuma kinsan hudubar da baba yake mana, Nacewa mutsaya a matsayin da Allah ya ajiyemu don mu tsira da mutuncinmu". nimrah ta dubeahi tare da cewa' Nasani yaya Saheeb amma itace ta bukaci hakan daga gareni kaga kuma bai kamata na wulakanta taba tunda acikin mutane muke" saheeb ya kaseta da cewa "OK naji, amma nidai nagaya miki waccan yarinyar ta wuce ajinki". nimrah ta bata fuska tare da cewa" "Toh nace naji yaya shikenan" saheeb ya dan dubeta tare da kai hannunsa kan fuskanta yace, "haba my sweet sister don't be upset with me". SAHEEB shine da na farko a wajen iyayenshi sai kanninsa saikuma mata su uku, gabadaya su biyarne wajen iyayensa, Alhaji Garba dan'kolii shine mahaifin Saheeb bawani mai arziki bane amma yanada rufin asiri gakuma wadatar zuciya, Dan kasuwa ne a cikin kasuwar sabon gari dake kano rufuna gareshi Wanda yake saida kayan yari mahaifiyar shi kuwa ZAMAN gda takeyi bata sana'an komai. Yan dangine don zuri'ar Dan koli tanada yawa sannan sun kware a fannin auren zumunchi Wanda hakan yasa yan garinsu ke tsegumi akan cewa iyasu isua tsakaninsu suke ,ba ashiga ba'a fita. Saboda basu yarda bare yazo Neman auren yayansu ba, shi yasa ma aka hadashi aure da Humairah yar gdan wan babansa, Kuma ikon Allah hadin yayi daidai saboda suna kaunar junansu! 鈽� 鈽� 鈽� 鈽� 鈽� Suhayr tunda ta koma gida takasa cin abinchi sai tunani gaba daya yan uwanta sun shiga damuwa ganinta cikin wannan halin, shiko mahaifinta daya dawo daga Abuja ya shiga rudanin ganin halinda take ciki. Ganin sun isheta da tambaya sai kawai ta amsa musu da cewa "da tambayoyinnan dakuke mun kawai Ku tayani da Addu'a don a yanzu ita kadai nake bukata daga gareku" Haka rayuwa ta cigaba da tafiya ,yayin da suhayr bata da aikin yi illa a kullum ta kira Humairah da boyayyen number tana yi mata barazanar saduwa da mutuwarta in har matukar bata fasa auren Saheeb ba. A bangaren Humairah tana ganin abun kamar wasan kwaikwayo amma daga baya taga abun yana Neman fin karfinta, ganin a kullum in ta fita sai suhayr ta bugo tace mata ta ganta waje kaza. Hakan yasa bashiri tasawa iyayenta kuka tana cewa ita gaskiya bazata auri saheeb ba saboda ana baraxanan kasheta. Mahaifinta ransa a bace yace "Baki isa ba domin ba'a taba yar da taki auren Dan'uwanta a danginmu ma kuma baxaa fara a kanki ba" Kwatsam saiga wayar humairah na kara ,jikinta na rawa ta dayka tare da cewa" hello" a tsorace ,a daya bangaren muryar suhayr ce take cewa "Kin janye, ko kuwa saina karar da danginku daya bayan daya sannan in nannadeki, sanin kanki ne cewa saheeb baxai aureki da munin halitta". humaira bata san lokacin da bakinta ya fara fadin "wallahi na hakura na rabu daShi koda kuwa shine autan maxa" Dayake a loudspeaker tasa kuma iyayenta sunji komai, hankalinsu ya tashi, Ba tareda bata lokaci ba, aka hada family meeting aka raba saheeb da humairah, batareda dayansu nasoo ba. Tun daga ranar da suhayr ta je gidansu saheeb, nimra take bata labarin abinda ya faru, shikenan ta fara nuna masa kulawa,tausayawa da kuma uwa uba , soyayya mai tsafta Wanda ba gauraye aciki.I novels / JARABABBEN KISHI part 5 JARABABBEN KISHI part 5 Posted by Bashir Sani Fesan on 16 Dec 2016 - 14:04 Kamar wasa suhayr da saheeb suka zama addicted da juna, saidai kuma tsantsar kishi da take nunawa a kullum, Wanda yin hakan yake damun saheeb, har ya kasa hkr yayi mata magana yace "Gaskiya suhayr yakamata kisani nifa ba d'an kowa bane asalima banda wata Sana'a Dana dogara dashi saina mahaifina, sannan kinga da da wacce zan aura amma aka fasa kuma banso na yaudareki, Kinfini komai suhayr mexai hana kinemi wani daidai dake baniba? Sannan kuma gashi yanzu haka ankara yimun baiko da yar uwata Salma banda bakin dazan musawa mahaifina saboda haka ne tsarin family dinmu Suhayr ina sonki amma gani nake kwarya tabi kwarya, niba abokin burminki bane. " Zancen saheeb ga suhayr ya katse ne dalilin zuwan wata wacce sukayi makaranta da ita, "saheeb barka da rana!" kamar daga sama kalamanta suka dirgo, suhayr ta ware ido tayi tsalle ta watsa mata wani mahaukacin mari tare da nuna ta da yatsa tana cewa "karki kuskura ki sake yiwa mijina magana inba hakaba, zanyi Ajalinki ni wallahi narasa meyasa wasu matan suke shiga hurumin daba nasuba" Oh!!!!!! suhayr ta furta tare dan jan hannun saheeb, ko ta bari ya yi wa budurwar magana taki balle kuma harya bata hkr, ita kuwa cool baby abun ya daure mata kai don a iya saninta saheeb baida mata baiyi aure ba amma ,hakan yasa ta tambayi kanta da cewa "ita wannan din wacece?" (Nidai cewa nayi dadai kin tafi karki fiye kallonsu takara watsa miki wasu tafin) Cike da damuwa saheeb ya fisge hannunsa tare da cewa "For God sake suhayr meyasa kike son ganin bacin raina? Yar class dinmu ce fa, gashi kin mareta batare da tasaan hawa ba balle sauka kuma kin hanani inbata hkr" a fusace suhayr ta amsa da cewa "Saheeb nifa gaskiya inhar zaka dinga yiwa yan mata magana gaskiya zan nisanceka, saboda zan iya kashe ko ma wacece saboda *JARABABBEN KISHIN* dana ke akanka...." saheeb ya katseta ta hanyar cewa " Go ahead suhayr go ahead kisani indai kika aikata kisan kai, hukuma bazata barki da rai ba" suhayr tace" Who cares? suwaye hukumar in bamu ba,so I can do anything and I see no reason da wani zai dakatar dani". saheeb yace" OK haka kikace?, toh shikenan suhayr bana sonki ,kuma inhar kin saurari kalamaina a baya ya isa ki gane komai, Inada wacce nakeso kuma .......", bata bari ya karasaba ta juya fusace ta shiga mota ta tayar tare da barin gun a fusace. Gudu take batare da tana cikin hayyaci ba, ikon Allah ne kadai ya kawota gida ba mutum ba, Da kuka ta shiga gda tana cewa "mummy yace baya sona mummy baya sona Yazanyi?" mummy ta tare da tambayar "wai waye?"suhayr ta amsa da cewa "Saheeb yace baya sona mummy mutuwa zanyi baxan iya rayuwa inbada saheeb ba Mummy wai auren zumunchi zaa mishi" Mummy tace "Ki kwantar da hankalinki insha Allah xaki aureshi". Tun daga ranar suhayr tafara ciwo Wanda aka rasa meke damunta baci basha, Anje asibiti amma sun kasa gane musabbabin ciwonta, Hakan yasa mummy ta bugawa daddyn suhayr waya tagayamai halinda yarsa take ciki kasancewar baya gari. A Daren yabaro Abuja, yana isowa ko ruwa baisha ba, kebewa yayi da suhayr don jin Damuwanta. "Abba cewa yayi baya sona wai auren zumunchi zaayi mishi." wasu zafafan hawayene suka fito daga idanunta. A fusace daddyn yace "Wayeshi ?waye ubansa a garinnan? Kisa ranki a inuwa insha Allah saiya zama mallakinki ke kada" sannan kuma yace" Amma fa nasanki da mugun kishi maybe shiyasa yace baya sonki? da sauri tace "noo daddy watace tayi mai magana nikuma na gaura mata mari shikenan fa, Pls Abba muje inbashi hkr shine farin cikina, banida wani burin Wanda ya wuce in farantawa saheeb rai." Washe gari suka daddy da direbansa sukayi samnako zuwa gdansu saheeb. Sallama akayi da Alh Garba, yafito dayake mahaifin suhayr sananne ne ko'a TV, hakan yasa ba shiri mahaifin saheeb ya saukeshi a falonsa, bayan sun gaisa ,sai daddy ya fara magana kamar haka "Daman nazone akan Dan wajenka yata daya tilo tana gida rai a hannun Allah dukta dalilin danka mai suna saheeb Ka taimakemu yadda Allah ya taimakeka, Farincikin suhayr shine nawa, banida katabus indai tana cikin wani hali, kuma Na Dade da sanin tradition din family dinku amma Dan Allah akan yata a sassauta mana nasan saheeb na kaunar suhayr amma shi gani yake tamkar tafi karfin sa Kuma yata ba haka na tarbiyantar da itaba da amai arziki da talaka duk daya suke gun Allah" Mahaifin saheeb ya bude baki yace "amma fah maganar da muke anyi mishi baiko da yar kanwata salma". daddy ya katseshi da cewa "malam kayi mana wannan taimakon suhayr tanacan kwance ba lafya" mahaifin saheeb yayi jim sannan yace "A gaskiya saina tuntubi yan uwana zan nemeku nan da satii daya".SHI part 6 JARABABBEN KISHI part 6 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:05 Alhj kabir sulaiman Yayi godiya. Ankai ruwa rana, anyi dauki ba dadi a family din dan'koli'. Saheeb yace shifa mace guda bazata kawo rarrabuwan kawuna a cikin family dinsu ba kawai shiya hkr. Ya fadi cikeda damuwa a fuskansa. '"Itako suhayr ta nace babu Wanda takeso saishi cutafa ta karu bawani sauki. Amma daga bisani dole suka hkr, saboda halinda takeciki kowa cikin family dinsu saheeb ya tausayawa Suhayr, ciki harda Alhaji sanusi Wanda ya tsaya kaida fata cewa saheeb baxai auro wacce ba yar dangiba, Daman saheeb yana kaunanta amma gani yake yar manyace mezatayi dashi cima zaune. "Yakaiga duk yar da saheeb zai Neman sai anyi baraxanar kashe yarinyan shiyasa yazama bora, babu yarinyar datake kulashi daman abunda suhayr takeso kenan. "Soyayya sukeyi ba dare ba rana ji sukeyi kaman su Cinye Kansu, Abu daya kesawa ajisu shine inya fiye kallon mata masu wucewa, shiyasa suka koma zance acikin gida. Wata rana ne sun fita yawon bude ido shida suhayr. Sai wata tace ma kawarta "kinga wani gaye mai kyau wallahi harnaji sonsa acikin raina". 'Karaf sai a kunnen suhayr kukan kura tayi tayi kan budurwar cike da jin kishin Saheeb, ta cakumi wuyanta ta tsinka mata mari, idonta duk ya rufe tsabar bakin kishin da take ji. Janyota saheeb yayi yace "ke wace irin macece? Meye gaminki dasu dake suke? kinga suhayr indai abunda zaki dinga yi kena inmun fita toh gaskiya zansa doka kowa ya fita batareda wani ya raka kowa ba" Jinsa kawai take amma idanunta sun kada sunyi jajir kamar garwashi. Suhayr ta rike k'ugu tana huci tace, "Daga yau koda a dakinki kika ganshi zaki kiyayeshi mayya kawai Ina ruwanki da kyawunsa kekika yishi? Masu shegen surutun tsiya da kalle kallen tsiya ke ana babbakan giwa waxai jiyo kamshin Giwa? Toh ki kula mahauniyarki ta kiyayi ramata Kadan namiki nagobe saiyafi na yau idan kika sake mun katsalandan". Tsaki tayi tace "banza kawai juyowan dazatayi, ta nemi saheeb ta rasa, sai neme neme takeyi amma bata ganshi ba! Saboda bakin ciki batasan lokacin da wasu hawaye suka kwaranyo daga idanunta ba, Da sauri ta ruga cikin mota ta kafa kai da sitiyari, jitayi an ruko hannunta a tsorace tace "Ya salam"! ",Karkiji tsoro suhayr saheeb ne masoyinki," Tuni taji dadii acikin ranta, "Meyasa kike kishina dayawa? Ni nakine suhayr karkiji komai" suhayr tace "saheeb zan iya rasa rayuwata ganin kanawa mata magana Toh kaga da in rasa raina indaina ganinka ai is better inne mawa kaina yanci tafadi tana kallonsa cikeda soyayya amma damuwarta bata boye ba. Saheeb yace "Amma suhayr,"shiiiishhh!!!!! tacemai tasa hannu a lebensa, "don't say a word saheeb...." "You deserve more than dis from me, look right into my eyes what can you see?" "Kura mata ido yayi yace mata " * JARAB EL GHIRA (Flames of jealousy)*" 'Tabbas ba karya saheeb ,"abunda kafadi daidai ne" suhayr ta kalleshi tace say a word DAT will make me to be happy now" "Saheeb yace I LOVE YOU wholeheartedly"," Suhayr taji dadii kwarai. "toh yakake gani Saheeb bazan iya komai a kanka ba?" Yace "Zaki iya amma kuma yakamata ki sassauta saboda nifa mijin mace hudu ne???????" Zare Ido! Suhayr tayi tace "karka kuskura inba hakaba zaka iya rasani sannan zan iya amfani da *jarababen kishina* in katse duk wata halaka dake tsakaninka da wata mace" "Look" Saheeb yace "abar maganan" muje ki kaini gida kinsan yau saboda ke banje kasuwaba" "Toh" tace suka kama hanya waka takemai da harshen larabci.SHI novels / JARABABBEN KISHI part 7 JARABABBEN KISHI part 7 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:06 "Kaine masoyina na gaskiya mijina kuma uban yayana Zanyi fito nafito da duk wata mace datake Neman ruguza alakata dakai",..... Kallonta kawai yakeyi Azuciyansa yace tabbas akwai aiki a gabana nida nakeda burin auren mata hudu? Ni maison Tara zuri'a mai yawa gashi suhayr batason taga nayi alaka da wata ya mace. Suhayr ce taji Shurun yayi yawa, ta juya tana kallonsa amma baisan Abunda ke faruwa ba burki taja Wanda yayi saurin dawo dashi daga dogon tunanin dayake yi, "suhayr da lafiyanki kuwa"? "Hmm" murmushi tayi cikeda da takaici Suhayr tace "kai yakamata inyiwa wannan tambayan saboda da alamu Kaine Mara lafya Kusan minti goma kana tunani bayan gani a kusa dakai, Me kanema ka rasa dazaka dinga tunanin wata?". Saheeb zare Ido yayi "suhayr wallahi ba tunanin komai nakeba illah tunanin rayuwa mai daukeda *so da kauna* dazamuyi in munyi AURE, Narasa ta yadda zan nuna miki yadda nakeji". murmushi kawai suhayr tayi don tasan kawai kwaskwarima ce yayiwa kala mansa bawai gaskiya bane amma ta basar, Itadai burinta ya cika ta mallakeshi a matsayin mijinta daganan saitasa kafa yaki da duk wata mace koda kuwa yau aka haifeta, shiyasa fatanta akoda yaushe Allah yabata yaya maxa, saboda mugun kishin da take dashi akan diya mace. (Nikam nace To Allah ya rabamu da irin wannan *JARABABBEN KISHIN*) (Na kuma cewa suhayr kin manta Allah keyi ba mutunba, kana naka babatun Allah na can na shirya maka nasa tanadin, Wanda inya baka bakada bakin kin amsa, inko harka ce bai iyaba lokacin zai nuna maka ikonsa") Ansa ranan aurensu wata biyu, amma fa daqyar Baban Saheeb ya shawo kan danginsu suka amince. Kowa a dangi ya sanda bikin saboda bikine na yar gata ya daya tilo Amma saidai kash daidai sa second daya suhayr bata samu kar buwaba wajen mahaifiyar Saheeb ba. 'Saboda tace duk itace silar rusa mishi aure shida yan uwansa, gashi tana Neman ta rabashi da yan uwansa mata tunkafin tashigo cikin family dinsu. Ita kanta suhayr tasan cewa mahaifiyar saheeb bata kaunanta amma koh a bakin gyalenta, don cewa take wata ranama saikin so ganinsa in hanashi. Biki yanata matsowa anfara shiri gadan gadan Amma babu gdan da zaa sa suhayr , gdane saheeb yasamu ciki da falo Wanda a kalla mutanen gdan da yara sunkai Dari Tuni suhayr ta kai kukanta wajen mahaifinta tuni yabasu gdanshi dake zooo road, gdane Wanda ya amsa sunansa gida. Saidai mahaifiyar saheeb tace Sam bata yarda da wannan tsari ba saboda gudun gori, 'Danta baxai zauna a gdan surukai ba, tasan cewa ai talakane ta Nace tana sonsa. Indai bazata zauna a gdan daya kamaba saidai afasa wannan auren haka umman saheeb tace tun lokacin data samu labarin cewa anbasu gida. Suhayr tashiga tashin hankali dajin wannan sako daga wajen umman saheeb Tace lallai ne ma Zanyi maganin wannan shu'umar tsohuwar cije labe tayi tace yayanta ya rakata gidansu taje da kissa tana bata hkr harda kuka "Wallahi umma duk abunda kike tunani ba haka nakeba, inason saheeb baxanso bacin ransa ba, umma kiyi hkr muzauna a gdan da abbana ya mallaka mana" Umma tace" baxan taba rabuwa da saheeb ba soyayyarsa nakeso ba kudinsa ba, indon kudi nakesonsa wallahi bayida abunda zai mallakamun". Nan tayi tayi mata magiya Da kyar dasa bakin yan uwa umma ta aminche. Biki saura sati daya Anje an fara shirya gida da kayan alatu, Ankawo akwati guda biyu a wulakance tirmin zani hudune kuma duka super print ne sai takalmi kafa daya sai gyale guda daya shima. Shiyasa komai umma suhayr taki basu koh ruwa, Amma duk suhayr bataji komaiba, saima boye kaya da akayi don karyaxama abun zunde a cikin danginsu. Sadaki kuwa dubu goma sha biyar suka kawo sai kace wata bazawara, Duk don suhayr tace tafasa amma ina sonsa Dada karuwa yakeyi acikin zuciyarta. Biki ya rage saura satii daya ne suhayr sunje kasuwa sukayi batan hanya, sukabi ta layinda runfunan su saheeb suke. Mace tagani tanamai magana tuni taji numfashinta na Neman daukewa Zuciyarta na bugawa uku uku!!! Da sauri taja kawarta suka fita daga kasuwar. Waya ta dauka ta kira saheeb tace "ina kasuwa ka fito bakin titi zakagaI novels / JARABABBEN KISHI part 8 JARABABBEN KISHI part 8 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:07 Jikinsa na rawa yafito daman angaya masa anganta a layinsu, Yana isa Suhayr ta balla masa wani irin harara Wanda sai daya shiga taitayinsa, "Saheeb abunda baxan taba lamuncewa ba kenan yin sana'ar dazaka dunga mu'amala da mata, dole ka canza Sana'a Wanda mazane abokan cinikinka Dole kayi nesa da duk wata mace hatta yan uwanka mata saboda kwanciyan hankalinmu baki daya". Saheeb Kallonta ya tsaya yi cikin tsananin damuwa sannan cikin bacin rai yace "bantaba Sanin cewa Suhayr ke mahaukaciya bace sai yau? kina ganin zan bar sana'ar mahaifina ne inyi wata daban? Kinsan cewa Sana'ar koli ita muka gada mukeyi tun iyaye da kakanni, Oh suhayr meyasa kika shigo rayuwata? For the first place am not in love with you amma saboda kaunar danaga kike nunamun ne yasa kikaga na amince miki har kika fara shiga zuciyana a hankali Amma shine zakizo ki ruguzamun rayuwa? Toh ki sani baki isaba Saidai ki mutu! kokuma Abu mafi sauki ki rabu dani auren afasa banayi" Saheeb ya qarasa maganar cikin hargowa. Suhayr Ji tayi kalaman saheeb na Neman haukatata me yasa Saheeb xaiyi mata haka? Bayan yasan zata iya mutuwa akansa, gashi talaka mafi kaskanci a idanunta amma takasa ganin wayannan bayaga soo da kaunansa dake dawainiya da ita. Dishi 2 kawai ta fara gani ta xube a wajen a sume. "Na shiga uku" saheeb yafadi cikin tashin hnkl, wasu mutane suka taimaka masa suka sata cikin mota itada kawarta, sai asibiti. Bayan awa uku ta farfado da sunan Saheeb acikin bakinta, "saheeb karka juyamun baya kishinka wajibine a gareni zan iya jure komai amma banda ganin kanayin mu'amala da mata" Tuni saheeb yafara zubarda hawaye Wanda shikansa besan dalilinsa na zubdasu ba. (Nida ILILEE mukace "sone saheeb ka kamu da son suhayr baka saniba") Rike mata hannu yayi yace "suhayr tabbas ke macece wacce kowani da namiji zaiso samu matsayin mata Bakida wani aibu a tattare dake, ki share hawayenki nime kaunankine," 'Shuru tayi lokaci guda taji ta warke tashi tayi tace "pls and pls saheeb inzakamun magana kadunga sassauta kalamanka a gareni". "Karki damu bazan karaba". Saheeb yafadi hakane don ya faranta mata rai" 'Dariya tayi can ta lura da kallon da Noor take musu tuni tace "maxa ki fita ki bacewa ganina kafin inyi takanki Kallon me kike mai? Karki sake zuwa inda nake, tunda naga take takenki so kike ki fara shiga hurumin daba nakiba". Haka nan noor ta fita don tasan halin kawartata. Shuru shuru zasu dawo ina basu dawoba, gashi zaa fara mata gyran jiki, Hajy rahmatu Maiduguri aka kira taxo ta gyra suhayr umma CE ta dau waya ta kirata tace "suhayr meyasa kika Dade? Bayan kinsan schedule dinmu na yau?" "Umma ganinan tahowa, in the next few minutes," Ta fada. Umma tace "Toh tace saikin dawo". Ta kalli Saheeb, Kallon da suhayr tayi masa yasa saheeb jin wani yanayi ajikinsa, Suhayr tace "Yauwa saheeb dakwai wasu dinkuna danayima sannan daddy yasiyo ma wasu takalma daga England, muje inna saukeka sai inbaka, sannan ga wasu yan kudi kayi amfani dasu nasan kanada hidima". Qin karba yayi sai da ta nuna bacin ranta sannan ya karba. (ILILEE yace inama shine ai tafadi gasassa Nidai dariya Nayi) Har kofar gida takaishi inda umman saheeb ta leko ta taga'. $uhayr tagani sanye da kaya tsadaddu ta dannan wani Abu boot din mota ya bude. Wasu Abu ta dauko a Leda "saheeb gashi zan tafi" ya karba, da sauri ta shiga mota ta figi mota kaman zata tashi sama, Shiko tsayawa yayi yana kallonta harta bacewa ganin sa sannan ya shiga cikin gida sai ji yayi ana cewa angon suhayr, bai tanka su ba ya shiga cikin daki Ya zauna akan katifarsa, "Dakwai aiki agabana, gaskiya suhayr inna ce bazan miki kishiyaba na munafunceki" Banida burin zama da mace daya". (Nace Toh pa kace akwai budiri a gidan Suhayr da Saheeb, muje xuwa dai) novels / JARABABBEN KISHI part 9
JARABABBEN KISHI part 9
Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:08
Ayau Sha Tara ga watan November Wanda yayi
daidai da ranan asabar ne, Dubban Mutane ciki
harda "senator na kano central", suka halacci
daurin auren *Suhayr kabir sulaiman da Angonta
Saheeb Garba Dan'koli* Bikine na manya bikine
Wanda ya amsa sunansa biki. Ba ai wani event
ba saboda suhayr tace bata iya jure kallon da yan
mata zasuyi wa mijinta ba, walima kawai akayi
bayan daurin aure. 'Suhayr tayi kyau dukda ba
wata kyakkyawa bace amma dayake ance ko
amaryar buzuzu ce ranan bikinta kyau takeyi,
Badon farar fataba inajin dasaidai akai kasuwa,
Suhayr gajerace badai sosai ba sannan tanada
idanu Wanda zamu iya kiransu da sexy eyes,
bakinta Dan karami Dan das, tanada jiki Wanda
bazamu iya kiranta da siririya ba, Saikuma hanci
kwarai batada hanci amma tanada kara. Da
misalin karfe Tara na darene yan daukan amarya
suka hallaro Domin daukar amaryarsu, motaci
uku ne Golf guda biyu sai wata space wagon
guda daya. Ga dunbin jama'a yan rakiyar amarya
kowa sai tofa albarkacin bakinsa yake Itako
suhayr fada ake mata sosai Wanda ko wacce
uwa takeyiwa yarta inzata kaita gdan miji. Ciki
harda fada akan jarabebben kishin data sawa
kanta, "Hjy ikilima ce ke magana da kakkausar
murya: "suhayr kishi a jininmu yake Kuma Allah
ne ke halittan kowani bawanda dashi, amma
saiyasa nawani yafi na wani Karki kasance me
nuna kishinki a fili yata ki sassauta kishinki, don
kishi ba hauka bane Wallahi indai kikayi koyi dani
toh tabbas suhayr zaki zama yar gaban goshi a
gdan saheeb". kuka suhayr keyi Wanda saida
tasa kowa na wajen kuka Wanda zan iya cewa
kukan yazame ma kowacce amarya al'ada,
dazaran zaa kaita gidan miji ta dinga kuka
saboda tunanin ta rabu da gida yan uwa da
abokan arziki, kenan saidai ziyara. Mahaifinta
shima yayi mata fada kwarai me shiga jiki. An fito
za'a sata a mota bawata mota mai tsada tanajin
abunda ake cewa Amma bataji komaiba illah
kosawa datayi akaita gdan saheeb, Acikin daya
daga acikin golf din akasa suhayr sai yan uwan
hjy ikilima, Dana mahaifinta suka cika sauran
motacin biyu..... Don ba kawa ko daya data shiga
motar kai amarya daman tun asalinta suhayr
daman bamai jaye jaye bace. *Ankaita gdanta
dake zooo road kowa ta watse saboda mahaifinta
yabada umurnin kar Wanda ya kwana," daga
suhayr sai saheeb aka bari acikin gdansu*
~Kubiyo yar mutan zazzau kuji labarin zaman
auren saheeb da suhayr shin wace waina zasu
toya ?????????gadaishi kowa ya watse ?KISHI novels / JARABABBEN KISHI part 10 JARABABBEN KISHI part 10 Posted by Bashir Sani Fesan on 17 Dec 2016 - 19:11 A Daren yau hankali ya kwanta, suhayr taxama mallakin saheeb, "Suhayr ayaune zamu kafa tarihi a rayuwar mu, yaune muka kasance ma'aurata," Kunyarsa suhayr keji Wanda abaya ba haka takeji akansa ba. "Tashi muyi sallah ko?" Cewar saheeb Wanda farin cikinsa yakasa boyuwa, "toh" tace. Alwala suka dauro suka gabatar da sallah da godiya ga mahaliccinsu, Wanda ya kawosu zuwa wannan lokacin. Sun danyi ciye ciye daga bisani Suhayr ta tashi tahau gado ta kwanta a tsorace don tasan Daren yau shine Daren farko dazata kwanta gata ga namiji Wanda a yanzu shine annurin zuciyarta. Tuni bacci yayi awon gaba da ita, saida saheeb ya kammala ya tashi ya matsa kusa da ita yana mata rada a kunne "cutey kitashi ki cire wannan kayan kinsan sunada nauyi zasu hanaki bacci". Tashi tayi tana cewa "Umma Dan Allah ki kyaleni kinsanfa nagaji dayawa," tana bode Ido saitaga Ashe saheeb ne. Ya mata murmushi rungumeta yayi yace "yar umma daga yau kindaina kwana da umma", dariya tayi tace "hakane saheeb sabo ne kawai kasan bana iya bacci saida umma," 'Saheeb yace "gashi yau xakiyi bacci ba tare da umman ba" dariya sukayi duka, tashi tayi ta dauko kayan bacci tasa amma fah saidata shiga cikin toilet saboda kunyarsa data keji. A Daren yau saidai muce Alhamdulillah saboda saheeb ya cimma burinsa akan masoyiyarshi, Ya maida mugun yawunsa "Assalatun farko saheeb yatashi yayi wanka ya fita zuwa masallacin dake kusa dasu, Bayan yadawone yatadda Suhayr kwance sai faman kuka takeyi, Wanda hakan yaba saheeb tausayi, saboda yasan cewa yayi laifi. Amma hkr yaxama wajibi daman haka auren ya gada, haka ko wacce mace tayi going through. Daukanta yayi cik yakaita toilet ya hada mata ruwan zafi, yataimaka mata ta gyra kanta, tagabatar da sallah. Suka koma suka kwanta farkawa tayi ta shiga kitchen don ganin abunda zata iya dafa musu, Amma taga wayam hakan bai bata mamakiba saboda tasan mijinta bashi gareshi ba. Wani corner ta leka taga kayan garanta daki guda nan tafara tunanin abunda zata samfara amma babu kayan hadi, Tana cikin wannan nazarin ne taji ana knocking kofa, Budewa taje tayi Ali direba tagani yace ina "kwana uwar dakina ya bakon waje?," "Lafya" tace, yace "Daman hjy ce tace in kawo muku abinchi". Tace "shiga dashi mana," Coolers ne na abinchi ya shiga dasu ciki ya a falon. Juyowa yayi yace "sannan tace kiyimun lissafin abubuwan dakikeda bukata yanzu kasuwa nayi" tace "toh" sannab ta lissafa komai a littafi ta rubuta ta mikamai ya tafii. Tsayawa tayi tana tunanin irin sonda iyayenta ke mata, abunda iyayen saheeb ne yaka mata suyi mana wannan hidimar amma sai gashi umma ce dakanta, Duk yanayin da suhayr take ciki saheeb na kallonta. Jitayi an dafata da sauri ta juyo tace "my life sannu da tashi". Sam bata nuna mishi a wane hali takeba, "Suhayr tunanin me kikeyi?" Ya fada yans kallonta. Tayi saurin cewa "Lah my life ba komai kawai tunanin yadda zan faranta maka rai nakeyi". Dariya don yasan kwaskwarima tayiwa kala manta, tace "Kaji mijina muje dinning kaga abunda umma ta aiko mana dashi tace muhuta karmu dafa komai". Daukanta yayi suna dariya cikin nishadii da kaunan juna, Sunci sunyi kat suka koma falo suna kallon Indian film.