Nabil da yashiga dakin mahaifinshi kwanciya yayi yarufe Ido tinani yake akan nacin da Mata sukeyi akansa na suna Sansa afili yace bana sanku kukuma Kuna Sona meyasa kukemin haka bazanyi aureba bani da lokacinku rufe Ido yayi yafara bacci lokaci daya ciwan mararshi yatashi tin Yana daurewa yanaso yayi bacci har abin yagagara juyi kawai yake tayi lokaci daya yahada gumi duda sanyin esin da ke dakin
Ana Haka alhaji sani yashigo dakin Yana ganin halin da Dan nasa yake ciki lokaci daya yarude yakarasa wajanshi labil baka da lfyne meyake damunka
Saboda azabar ciwan da yakeji ko mgn yakasa hannu yasa Yana nunawa baban nashi mararsa
Dasauri alhaji sani yadau waya yakira Dr dake duba iyalinshi ya,fadamasa yai maza yazo dansa ba lfy cikin kankanin lokaci Dr yazo yafara dubashi yaimasa abinda yadace lokaci daya bacci menauyi yakwasheshi
Dr yace yallabai da matsalafa in har Baku dauki matakiba akan nabil Nan gaba kadan ze iya rasa kwayoyin haihuwarsa gabadaya saboda wannan temakwan da ake bashi zedena aiki Dan yanzu magani baya Masa aiki se allura itama nangaba kadan zata Dena aiki ajikinshi saboda Yana da karfin shaawa me zafi agaggauta yimasa aure Dan asamu mafita Kar abin ya illata lfyarshi Dan har aiki abin ze iya sawa aimasa nangaba
Numfashi alhaji sani yaja yace to Dr ngd insha allahu zaaimasa aidolema aimasa Dan kullin burina Naga gudan jinin nabil aduniya
Sallama sukayi da Dr yatafi
alhaji sani dakin matarsa hajiya Fatima yatafi
Yakarasa wajanta yazauna cikin damuwa yafara fada Mata abinda Dr yace akan dansu nabil
Hajiya Fatima tace anzo wajan alhaji aini tintini naso aiwa nabil aure ko zedena wasu abubuwan da yakeyi Amma nasan ban Isa nace wani Abu akan nabil ba kayarda danhaka nai shuru da bakina Kuma da matsala nabil yatsani Mata bayasan Mata tin abin baya da muna yanzu abin nashi yafara bani tsoro gani nake kamar nabil na da aljanu kyama sosai yake nunawa Mata Nima Dan uwarsace babu yanda zeyi Dani muke zaune inuwa Daya dshi Yan uwanshi matama dandai Babu yanda Suma zeyi dasu yake hurda dasu ko hanya bayaso yahada da mace bare Kuma ai maganar aure dazu dazunnan yaiwa Yar mutane duka har targade yaji Mata Dan taganshi yashigo tarude tarasa inda zatabi ya hukuntata Kuma wace macace zata iya Zama da nabil inba Wanda batasan ciwan kantaba irinshi kokuma ta aureshi Dan kudinshi Amma inhar mace me hankalice da tinani wlh bazata auri nabil ba komai kudinku Kai dshi
Alhaji sani yace kefa matsalata dke Kenan indai akan nabil ne alheri baya fita abakinki ai nafiki sanin raayin nabil Kuma da Babu wannan matsalar tashi da tataso da bazan Masa aureba har se ranar da yasoyi Dan kansa bare harnazo wajanki neman shawara Kuma yanzu zanbawa Dana shawara akai Kuma zedauka ko bayasan mace zan bashi shawara ya auri kowace macace inde zatamai maganin matsalarsa tashi yayi yafice cikin fishi
Hajiya Fatima tace Allah yaganar dku Kai da danka alhaji daga Kai harshi kunyi nisa zankira baffah na fadamasa halin da ake ciki nasan Kai bazaka fada masaba
Shatuwace takwashi zugarta sukayi dawa cikin gonakin mutane du gonar da sukaga tamusu Haka zatasa sushiga suyi musu barna sannan subar wajan du sanda tarayo Mata gonakin mutanene wajan wasanta ita da zugar kawayen ta gonar wani me mangwaro da goba suka shiga magwaran yanuna sosai sukai Masa barna sosai Kuma sukaki barin gonar suna tawasa aciki har me gonar yazo ya samesu yaga barnar da sukai Masa ransa yayi mugun baci sosai Kara dogo yadauka yahau dukan du Wanda yasamu Dakar suka,samu suka gudu du yasansu yagane fuskokinsu rainshi abace yatafi wajan megari yakaimai Karar abinda su shatuwa sukai Masa
Megari sawa yayi akakira iyayan yaran da su kansu su shatuwa har da iya seda tazo cewa tayi se tazo taga me zaayiwa jikarta
Gaba dayansu sunzo sun amsa Kiran megari Nan magari yasa me gona yafadi barnan da su shatuwa sukai Masa
Budar bakin iya tace to yanzu malam me kakeso aimaka wayace karka zagaye gonarka kai Mata kofa yanda Babu Wanda ze iya shiga lefinkane da kayi da yarannan bazasu shigarma gonaba har simaka barna yarannan kwatakwata nawa suke yaran da basugama hankaliba Dan abin kunya kakwaso jiki kakawo kararsu wajan megari yanzu Dan Allah bakaji kunyaba tsofai tsofai dakai
Megona yace ke tsohuwar banza kishiga hankalinki Daman Ina da labarinki inkinwa mutane sunbarki saboda tsufanki Ni inkinmin ba barinki zanyiba kwatakwata shekara nawa Kika bani da zanji tsoran yimiki mgn har naraga maki saboda girmanki ke ko tsoran Allah bakyaji zomuje kiga barnar da jikarki tasa akaimin agona Kuma wlh da nazone akan ajamusu kunne karsu kuma Amma wlh yamzu se anbiyani tinda Babu mutunci gobema kukara barin su suje gonar mutane suyi musu barna
Megari yace Wai ba afada kukeba kuke wannan abinba Karna karajin bakin wani anan iya gaskiya bakya kyautawa haba iya meyasa kike Haka tsufa haukane du abinda kikewa mutane in ankawo Miki Karar shatuwa nasani mutane nazuwa su fadamin ninake Basu hakuri saboda zaman mutuncin da kukayi da iyayanmu nake barinki Amma wlh Daba hakaba da matakin da zan dauka akanki ke da iyalinki da se kinyi mamaki sosai yanzu tinda kingoyi bayan jikarki shikenan zaayiwa mangwaransa da goba kudi ki biyashi ke da iyayan yaran da taja sukaje sukayi barnar Kuma du sanda suka Kuma harku iyayansu se mundau mataki akanku suma Kuma yaran bazamu barsu sutafi hakaba se nasa anmusu bulala yanda Nangaba bazasu kumaba
Kafin megari yagama yanke kudin da su iya zasu biya Sega wasu masu gonar Suma sunkawo karar su shatuwa Haka megari yahada yasa iyayan yaran da na shatuwa suka biya kudadan barnar da sukayiwa masu gonakin megari yasa dogarinsa yaiwa su shatuwa bulala sosai ihu shatuwa take kurmawa haka iya ma take kurma ihu daga anzubawa shatuwa bulala Haka iya zata takarkara tazuba nata ihun du sukabi suka cika wajan da ihu
shidai umaru mahaifin shatuwa takaici yahanashi mgn ga takaicin uban kudin da akasu suka biya gana shatuwa da na iya tinanin irin hukuncin da zeyiwa shatuwa in sun koma gida yakeyi
Nabil be farka daga bacciba se wajan magariba Yana tashi yafito bega kowaba bangaransu yashige yaje yai wanka yafito Yana zaune afalo alhaji sani yashigo shi da hajiya Fatima suka zauna kusa dshi
Alhaji sani yace nabil yajikin naka
Yace da sauki daddy
Nan alhaji sani yafadawa nabil abinda Dr yafada Akan cutarsa yaku Gaya Masa shawar da suka yanke nayi Masa sure
Dariya nabil yayi sosai sannan yahade Rai yafara mgn yace daddy kafasan matsalata da raayina natsanar du wata yarinya mace Ni Babu wani aure da zanyi wlh Dan Zan iya lahanta Yar mutane abanza wlh Dan ko gida daya Bata Isa mu zauna tareba Ni fa daddy bani da raayin aure bazan yiba mezanyi da mace nasan daddy wannan ba raayin kabane raayin mommy ne da wannan tsohon faffah Yama gangara kowa yahuta yaki mutun se shegen taurin Rai yaki mutuwa wlh du sanda tsohonnan yamutu Babu kukan da zanyi Kuma in har aka dauramin aurannan da kowace yarinyace sedai faffah yazauna da ita ko mommy ko Kai daddy Danni bani kuka aurawaba Bari kuga yauma Ni ba agidannan Zan kwanaba a otal Zan kwana muna da cashiya da bazaniba Amma saboda kun batamin Rai Dole nabar muku gidan Wai yau meyake faruwa da nine ake tabatamin Rai gobe America Zan tafi nahuta da nanjeria gabadaya Dan nasan wannan tsohun zeyi kirana naje Kuma bazaniba Nan da sati biyu ma muna da fatin da zamu agidan gonarka na mazagai
tashi yayi yaje yashirya yai ficewarsa ko sallama bewa iyayan nashiba yai ficewarsa yabarsu zaune afalo
Hajiya Fatima tace kunfi kusa alhamdulillah tinda har mahaifinka be bariba bare Kai kaga tafiyata ai bani da tacewa akan Dan gwal tashi tayi tabar alhaji sani Tai tafiyarta abinda zemata anfani
Alhaji sani kanshine yadau caji Yana ta tinanin yanda ze yiwa nabil aure saboda bayaso yarasashi afili yace nabil kayi hakuri banaso narasaka Dan Zan shiga wani Hali kilama Nima nabika Dan bazan jure rashin ganin,kaba nabil yanzu menene abinyi ita Fatima Ina zuwa wajanta zatahau gayamin bakar mgn tahau yiwa mutane waazi Zan ta rarrashinka nabil har seka yarda da mgnar aurannan
Yau nabil yadawo daga America satinsa biyu Acan shi da abokansa beso dawowaba saboda fatin da zasuyi na murnar ranar haihuwarsa a gidan gona na mazagai zaayi Dan Haka yadawo shi yace anan yake so yayi shagalin murnar ranar haihuwarsa saboda San gidan gonar da yakeyi kwansa biyu da dawowa aka hada shagalin
yau akeyin taran yagaiyaci manyamanyan abokansa du zasuzo bakaramin kudi akakashe awannan taran murnar haihuwar tasaba fadama Bata bakine du wannan abinba akeyi hajiya Fatima da malam usuman kakan nabil du Basu saniba taro yayi taro kowa yazo shikadai kawai ake jira motocinsane suka jero Akan layi sababbi dal alhaji sani ne ya canjamai su motocin masu dankaran kudi daga kasar waje aka kawosu shigarsama tawannan ranar daban take Haka motocinnan suka shigo garin mazagai dagudu suna badawa mutane kura kowa se kaucewa yake lokacin shatuwa da zugar kawayanta sunfito zasu Wasa sukazo zasu shige tagabansu motocin saura kadan su buge shatuwa akwai wani ruwa dake tare ahanya takai motocin sukabi tacikin ruwan gabadaya wannan ruwa yabatawa shatuwa jiki motar har tana gogarta shatuwa seda tafadi kasa ta kurje abin yayi mugun batawa shatuwa Rai motar da nabil yake ciki ita tafi ballatsawa shatuwa ruwa ko su tsaya suka shigesu warsu dagudu
Abin yamugun konawa shatuwa Rai tace Kan uba wayannan suwaye yau senaga ko suwaye musamman wannan motar da tafi kowacce Kyau aciki wlh bazan yardaba Sena Rama yau zasuga mezan musu
Kawayan nata sukace Kai jikan faffah usuman ne wlh karki yarda sekin Rama muje murakaki muma zamu tayaki
Dagudu sukabi motocin har motocin suka shiga gidan gonar ahankali su shatuwa suka faki idan mutane suka shiga gidan gonar Suma Babu Wanda yakula dasu
nabil aka budewa kofa yafito habawa Nan guri yadau shewa anamasa oyoyo su shatuwa Baki suka saki suna kallan ikwan Allah namiji suka gani da wata shiga Wanda Basu santaba harda su sarka yahade Rai sewani Shan kamshi yake
Me shatuwa zatayi inba dariyaba sauran kawayantama dariya suka fara nabil jiyayi kamar anamasa dariya juyawa yayi bega kowaba cigaba yayi da tafiya wajan da aka tanadar Masa Dan zama
Anfara gudanar da shagali du su shatuwa nagani wajan tayoyin motar da nabil yafito ciki shatuwa taje dakanta tanemi kusa ta fanfasa duka hudun bayan tagama Kai tsaye wajan nabil tadosa tabayanshi taje da ruwan kwata dauke ahannunta acikin wani gwangwani tabayanshi Tatsaya
tace Kai Dan daudu rabi aljani rabi namiji rabi Dan daudu juyo kaganni nicenan shatuwa masifa tsokana jikar iya ikwan Allah kowa yaci tuwo Dani Miya yasha
Nabil cikin mamaki dajin maganar shatuwa yajuyo ai shatuwa batayi watawataba tajuyemai ruwan kwatarnan akansan da jikinshi
Tace baamin ban ramaba da yau banrama abinda kaminba dako bacci bazan iyayiba saboda takaici gababa in kazo garinran in kaganni kakara watsamin ruwa ka bugeni nafadi su jinmai kuyi Masa Wakar danace zamuyi masa
Nan suka faramasa Waka dandaudu meshigar Mata rabi aljani rabi namiji Dan daudu matamaza meshgar mahaukata kowa yatabomu semun Rama katabo shatuwa jikar iya ikwan Allah
Dan mamaki da takaici wata Kara nabil yasa yaikansu dagudu zedaka kallone yakoma kansu kowa na mamakin meya hadasu Kuma yaakai yaran suka shigo wajan dakyar Nabil yakama shatuwa sukuma yaransa suka Kama kawayan shatuwa kida nabil yasa aka kashe
Nabil yace yau Wana irin hukunci zan muku yau me zan muku nahuce ni kuka batawa ranar haihuwata ke Yar kyauye mezubin mahaukata nikika yiwa haka da ruwan kwata Kika batawa jikina kusake Wakar da naji kunayi min
Shuru kawayan shatuwa sukayi suka kasa mgn saboda yanda nabil ya tsoratasu dukansu jikinsu rawa yake Dan sun tsorata dashi sosai
Shatuwa tace au Wai tsoransa kuke Amma kun bani kunya wannanne zebaku tsoro Toni Bari naimaka dandaudu meshigar Mata rabi aljani rabi namiji nandaudu matamaza kowa yatabamu se munrama
nice shatuwa
Kafin takarasa nabil yadauketa da wani mahaukacin Mari Dan bakin cikin abinda Tai Masa yarasa wana kalar hukunci zemata hannu yasa yashake Mata wuya menai muku meyasa Mata kuke Bina kintaba ganina a Ina Kika sanni sekin fadamin meyasa Mata du inda naje se sunbini se Kuma sun batamin Raina kifadamin Kona sumar da ke meyasa Kika batamin ranar haihuwata kinsan dogwan burin da nadauka Akan wannan ranar kinsan daga Ina nadawo Dan wannan ranar inajin kwatar da aka zubamin nasan wlh Babu meyimin haka se mace Ni bana shiga harkarku Mata Amma ku se kun shiga tawa meyasa kifadamin
Shatuwa takasa mgn Dan azaba se Ido da take zarewa Dan azaba sakinta yayi yakama hannunta na dama yamurde se da hannun yaikara ya tambatar yakarya hannun shatuwa sannan yasaki hannunta
wani mahaukacin Kara shatuwa tasaki Dan azaba tace mugu maye ze kasheni Daman matamaza dandaudu nada karfi haka kasheni zakayi da kakemin wannan tambayar Ni Ina nasani ni kasan mekamin dabaka tsokaneniba da bazan biyoka naramaba ka karyamin hannu wlh Nima Sena karya naka ko Nan gabane ta karasa mgnar tana mai da numfashi Dan azaba
Kuma Dan taurin Kai irin na shatuwa bakinta yaki mutuwa rashin kuya take tamasa shikuma Yana dada tinzira zuciyarshi na dada baci kowa Ido yazuba musu anrasa me Basu hakuri saboda tsoran nabil da bakar zuciyarshi Dan in ransa yabaci abin bakyau baa iya rarrashinsa
Nabil yakalli yaransa yace mekuke jira da wayannan mahaukatan kudakarmin su harse sun jigata kekuma bakinki yaki mutuwa ko to Bari kiga mezansa aimiki yanzu waiyau Ni nabil nine nataba mace haka da hannuna Amma yarinyarnan kin cuceni kingama Dani natsaneki kece mace tafarko da nafara tabawa da hannuna Kuma insha allahu kece takarshe Sena barmiki tarihi yau kamar yanda Kika barmin ya kalli yaransa kubarsu Haka ai sunyi sanyi ku je ku kwasomin buhunhuna acan dakin kukawomin kuga me zanmusu
Ana kawo buhunhunan yace kubude kufara samin wannan marakunyar da na karya ku kullemin ita kusata abutdin mota ku rufeta ita kadai sauranma du ku zirasu abuhu kusasu abut dasu zamu tafi ni nasan inda zamu kaisu
Andaga shatuwa kenan zaasata abuhu kakansa malam usuman yashigo gurin yaga danyan aikin da jikansa yasa yaransa sunayi cikin tashin hankali yadaka musu tsawa
Yace ku kisankai zakuyi nashiga uku nabil ze jamin mgn zaman garinnan zefi karfina adalilinka rainawa zaku kashe da banzoba mekuke Shirin aikatawa Haka nabil abin naka yakai Haka tinda labari yazomin kashigo garin katara mutane awajannan hankalina yaki kwanciya nace Bari nazo nagani wace tsiyar kake aikatawa Dan nasan halinka Dole sekayi abin fada me wayannan yaran sukai maka har wajan susu ashirin yanzu da ban zoba duka kashesu zakuyi ko Yaya nidai nasan indai akasa mutun abuhu baze shaki iska sosaiba nabil kafadamin mezakai da yarannan ko kafara satar mutane bamu saniba
Nabil yace shikenan hanaruwa gudu kazo komai yakuma baci faffah me yakawoka Nan Wana munafikinne yaje yafada ma meyasa daddy ya sai gidan gona anan yanzu Dan Allah faffah me yakawoka wajannan kokazo kunyatani acikin abokaina wlh faffah Ina raga maka Dan Kai Kaka nane Babu yanda zanyi dakai kasan me sukai min yau kasan wace ranace awajena Kai basanin mahimmanci ranar kayiba bazaka ganeba ko na fadama nifa kasan dokata na tsani Mata banasan Mata meyasa zasu zo su yimin haka Ni Babu abinda zanyi dasu Kano Zan kaisu nayardasu acan Nan yafadawa faffah abinda su shatuwa sukai Masa
Faffah yace nabil meyasa baka da hakuri meyasa kake wulakanta mutane du wannan halayan naka Babu meshi akaf iyalina sekai a Ina kasamo wannan mugun halin kayi kuskuran kula yarinyarnan bakasan itama wacece itaba yanda kake fitinanne itama haka take fitinanniya agarinnan da datayi maka Haka da baka kulataba kazo kafada min ko ka kaiwa iyayanta Kara ko megari Amma yanzu kaga abinda zuciya ta ebeka kayi ka karya musu yarinya kawayanta kasa anmusu mugun duka yanzu da ban zoba Ina zaka dasu kukama masu bin nashi manyan banza se abinda yace muku kuyi kukeyi saboda Kuna karkashinsa ana biyanku kudi acikinku kusan dukanku kun girmeshi Amma anrasa mebashi shawara tagari Dan Kuna tsoransa kace bansan ko yau wace ranace awajankaba nikuwa nasan ko waje ranace yau awajanka ba bikin murnar haihuwarka kakeba yau to nazo tayaka murna nakuma karama biki Daya akan Wanda kakeyi yau Zan karama wani farinciki yanda nasan bazaka taba mantawa da ranarba yanzu da ka karyata me kake nufi kana nufin ka karya banza baka isaba nabil baka karya banzaba kasan karya yarinyarnan me kahadawa kanka ranar auranka ka hadawa kanka wlh yanda ka karyata Kaine mijinta baka karya banzaba yau ka karyataka yau zaka aureta Zan daura maka aure da ita kaga taro biyu kenan Ni nakarama biki Daya Kar Wanda yatafi anan du kubiyomu zuwa gidan megari Dan halartar daurin auran nabil azamanku na abokansa muna gaiyatarku daurin auran nabil sani DAN MINISTER kuzo mutafi
Faffah kanlan mazan da yazo dasu yayi yace Kai kaje ka kiramin umaru baban shatuwa da Kuma iya kakarta suzo gidan megari cikin gaggawa ana nemansu Kai Kuma kaje kataho min da me gyaran karaya zuwa gidan megari
Yan uwan alhaji sani ne wayannan mutanan majiya karfi faffah sasu yayi suka daukarmai nabil cak suka samaishi amota akasa shatuwa itama amota da zugar kawayanta suka ja zuwa gidan megari du abokan nabil da sukazo fatin nashi suka bi bayansu zuwa gidan megari Dan ganewa idansu wannan auran mamakin da zaa daurawa nabil shi
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama*鉂ゐ煈�
*'YAR KWALLIYA*馃コ馃拑
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹
馃憼
馃拕馃拝 *DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
5-6
Megari nazaune akofar gida akarkashi wata katuwar bishiya shi da jamaarsa segani sukayi motoci nata jeruwa suna tsayawa akofar gidan shi kallan ikwan Allah suka tsaya yi can Kuma sukaga faffah da yafito awata motar gakuma nabil ga shatuwa du anfito dsu amotar anrukosu zuwa gaban megari ana Haka Sega umaru da iya Suma sun iso wajan
Salati umaru baban shatuwa yafara yace wlh nasani shatuwa ce iya kinganiko abin naki shatuwa yaci gaba har da tsokano gari guda Daman ana cewa muzo ana kiranmu akofar gidan megari nasan shatuwa tayi halin wlh badaniba yau iya sedai koke inzaki iya baruwana wlh
Megari yace iya Isa umaru kajira muji meke faruwa ko mu Nan bamusan meyafaruba ganinsu kawai mukayi
Baffah yace du ku kwantar da hankalinku bawani abin tashin hankali bane sosai alheri ne yakawomu dukanmu Nan yanzu megari Ina neman alfarma dakai da liman da mahaifin shatuwa umaru da Kuma wayannan dattawan garin namu da suke wajannan inaso mudan koma gefe Dan da bayanin da nazo dshi zan muku alheri ne insha Allahu Allah yasa ku goyi bayana Amma Banda iya tadan jiramu tukunna in mungama tantaunawa itama akirata afada Mata aji raayinta
Megari yace to alhamdulillah du kutashi muje wayanda yace yanaso suji mgnar
Haka du suka tashi zuwa wani daki dake soran megari du suka samu waje suka zauna
Baffah ne yafara mgn yai sallama yabude da addu'a yace wani abune yau yafaru tsakanin jikana da shatuwa agidan gonar Dana sani Nan yabasu labarin abinda yafaru tindaga farko har karshe Kuma Ni na hango wani Abu alheri ne inhar kungoyi bayana Dan shima jikan nawa irin shatuwa ne ko ma nace yafi shatuwa da mugun Hali Dan tawani wajan halinsu yazo Daya tawani wajan kuma sun banbanta ta halaye Dan Haka hadin da nakeso ayi zezo dedai kowa acikin susu biyun zasu gyara junansu insha Allahu Dan na hango alheri alamarin Ni malam usuman mahaifi ga alhaji sani Kaka ga nabil Ina neman alfarma agabanku malam umaru mahaifin shatuwa yabawa jikana auran yarshi shatuwa adau rashi yau anan kofar gidan megari saboda abinda yafaru tsakaninsu Dan sukara hankali gaba ga tawagar munan nazo da ita ta Yan daurin aure Ina bawa malam umaru hakuri Akan abinda jikana yaiwa yarshi shatuwa insha Allahu ba ze kumaba Kuma Ni malam usuman namaka alkawari agaban su megari nabil da mu damgin nabil zamu rike shatuwa tsakani da Allah har karshan rayuwarta
Megari yace to fa wannan mgn batamu bace takace umaru Dan Kaine mahaifin shatuwa mu shawara ce tamu aciki Kai muke jira umaru muji raayinka akai
Malam umaru yace to gaskiya Ni wannan hadin auran baze yuwoba ban yarda dashiba Dan kowa yasanni agarinnan bawani kudi gareni ba se rufin asiri Kai Kuma baffah kowa yasanka Kai da ahalinka masu kudine barinma danka sani yafi kowa kudi azuriarka Kuma kowa yasan jikanka nibil da irin halinshi in yashigo garinnan itama Kuma shatuwa kowa yasanta da ita da iya da irin halinsu gankiya Ina gudun abinda zeje yadawo kunfi karfinmu ta ko Ina faffah shima Kuma nabil yafi karfin shatuwa ta ko Ina Dan da ba akasar Nan yai karatuba akasar waje yai karatu shatuwa fa da ko makarantar Allo batayiba bare ta boko wannan hadin baze yuwuba da matsala babba in akayishi kagafa faffah tashin farko haduwarsu me yafaru bare Kuma aka hadasu gida daya suyi zaman aure tare Kuma basan junansu sukeba Kuma nawa shatuwa take Bata wani girmaba Ina da dogwan buri akan shatuwa in Allah yabani iko Ina da burin shatuwa tayi karatu me zurfi sosai Kuma inaso in gyara ta ta Dena wannan halin nata Kuma yanzu ya zaayi da iya da ko tinanin rabuwa da shatuwa batayi ba Dan da kauna me karfi tsakaninta da shatuwa bazama ta taba Yarda da maganar aurannanba Dan bazata yarda arabata da shatuwa ba se dai kukira iya kuji nata ko zata yarda
Baffah yace karka damu umaru mudai yardarka kawai mukeso da sa albarkarka amatsayinka na uba awajan shatuwa iya kuma Ni da megari munsan yanda zamuyi mu rarrasheta ta yarda da auran Kai dai in tashigo kayi shuru karkasa Baki amaganar
Yace to shikenan Bari naje na kirata tashigo taji meyake faruwa
Umaru fita yayi yakira iya tashigo megari da baffah sukai Mata bayani nanfa Tai tsalle tadire tace batasan zanceba Babu me rabata da shatuwa bare har ai Mata aure da wani Dan gayu Kuma yanda ya karya Mata jika shima nabil se ta karyashi da kanta tace Ni iya fadan yadawo hannuna Ina yake Dan kwal uban yaro Naga shatuwa du tafadamin abinda yafaru da yaran kanku kirani ku fadamin Daman jira nake kufito na kwashe ubansa da Mari nazata dashi aNan ashema babushi yau Babu me rabani da jikanka usuman wlh banki mu doku Ni da Shiba Dan senayi zaman Yan bori Akan kafarsa shima har se na karyashi Zan tashi ai Naga yaran me kirar aljanu da yakoma kala biyu gaba Daya kamar ba Dan hausawaba Kuma kubude kunnanku kuji shatuwa dai bazan taba yarda da wannan auranba bazaaje akashemin jikata abanzaba afa garin masu kudinnan da naji ana fada shi uban yaran yake abawa dansa shatuwa suje su su sayarmin da ita sukara wani kudin Akan kudin da suke dshi
Megari rarrashin iya yayi da dadin Baki Amma fur Taki yarda
Baffah yace haba kekuwa aishatu Kaka wajan shatuwa ia bakisan yanda nake san shatuwa ba tana burgeni yarinya me kirki ga ladabi ga biyaiya na yaba da irintarbiyar da kika bawa shatuwa Dan Haka naso muhada iri da ke Baki iya tawashe Jin anyabi jikarta tin daganan suka hango alamun nasara ki temaka ki yarda da wannan hadin auran Dan Allah Kuma Kinga yau mukeso ashige da ita gidan mijinta dake Abuja Kuma Ni da kene yankai amarya da ango ke zakije kiga inda akakai jikarki da kanki acan zatayi jinya agidan mijinta zakina zuwa kina ganinta akai akai kema kina tayani ganin irin zaman da zasuyi Kuma in kin yarda da auran har kujerar aikin hajji Zan biya Mana Ni da ke muje mu rokarmusu zaman lfy Kinga har uban nabil da mahaifiyarsa du kikai musu kakar abinda da dansu yaiwa shatuwa Kinga se su jamasa kunne ko
dakyar baffah yasha Kan iya ta yarda da auran tate adaura Allah yabada zaman lfy kowa na wajan yayi murna umaru shima hamdalah yayi shatuwa zatabar gabansu yahuta da ba da hakuri da rigimar iya megari yafi kowa murna yahuta da sharia kullin
Megari yace alhamdulillah iya mungode sosai da wannan alfarmar da kikai Mana yanzu muje nasa ayi shinfida kowa ya zauna agudanar da daurin auran itakuma amarya shatuwa ashigo da ita ciki me gyaran karayar Naga ya iso tin dazu yashigo ya dorata kafin agama daura auran muntura Akira mahaifiyar shatuwa itama tasawa yarta albarka Kan atafi da ita
Nan aka shigo da shatuwa me Dori yadorata tana ihu tana komai iyama na ihu har aka Gama Dora karayar hannunta
Akofar gida Kuma Ana gudanar da daurin auran shatuwa da nabil baffah ne waliyin nabil malam umaru shine waliyin shatuwa baffah hannu yasa a aljihun nabil yaciro damin kudi ya irgi dubu dari biyu yamikawa megari yace ga sadakin shatuwa kowa ya sheda megari yasa hannu yakarba yasa albarka yanunawa kowa baffah yamayarwa da nabil sauran kudinsa
nabil yakoma hoto bakinshi yamutu yakasa mgn gani yake mafarki yakeyi wani iri yakeji zuciyarsa nayi be zataba be nufaba seji yayi anacewa Allah ya yarda aure ya dauru tsakani nabil sani da shatuwa umaru jikar iya ikwan Allah Akan sadaki nera dubu dari biyu lakadan ba ajalanba
kafin nabil yagama mamaki se jiyayi abokansa Yan tsokana sun dagashi sama suna tayashi murna suna ta Masa dariyar mugunta da tsokana
Megari ne yashiga yafasawa iya angama daura auran tafito ita da amarya zasu tafi Abuja haka mahaifiyar shatuwa tana hawaye taiwa yarta nasiha du da tasan bawani dauka zatayiba Haka aka fito da amarya shatuwa aka sata amota tare da iya akatafi
Baffah ya dada bawa kawayan shatuwa hakuri Akan abinda yafaru tsakaninsu da nabil yakuma musu alkawarin zuwa ganin gidan shatuwa in komai yanutsa hakama yabawa suwaiba mahaifiyar shatuwa hakuri tayi hakuri itama zata tagano inda yarta take in ankwana biyu Haka faffah yakama hannun nabil yasashi amota tare da tawagarsa ta Yan fati suka dunguma zuwa Abuja raka ango da amarya
Hajiya Fatima da alhaji sani sunacan basusan meyake faruwaba faffah ne yakira Amina yayar nabil yace Tai maza tataho gidansu tajirasu komai dare sunanan tahuwa zebata wata Amana yakira Hajiya Fatima itama yace Mata tashirya gashinan tare da Baki abinnan da takira tafada Masa komai yakankama Dan Haka tashirya gasunan sauran bayani se yazo ya tambayeta sani dansa nagari tace eh yace to du sujirashi gasunan
Sedare suka Isa Abuja zokiga zare Ido wajan iya da shatuwa sunga birni ko Ina da hasken wutar nepa kamar ba dareba ga dankara dankaran gidaje agarin anazuwa gidan su nabil Nan kallo yakoma sama iya dada zare Ido take saboda ganin dankareran gidan Dan baffah Haka aka bude musu gate motocinsu suka shige wajan fitowa amota ansha fama da iya cewa tayi bazata fitoba ayanke Mata Kai abinda yadada Bata tsoro ganin sojoji da bindigogi ahannunsu tadada tsurewa Dakar Amina tazo ta lanlabata tashiga
Baffah godiya yayiwa tawagar abokan nabil sannan kowa yashige gidansu sukayi sallama da ango mijin amarya shatuwa
Baffah Kama hannu nabil yayi zuwa cikin gidan da sallama ya shiga afalo yasamu hajiya Fatima da alhaji sani da su iya waje yasamu yazauna ya zaunar da nabil kusa dshi baffah yafara mgn yai sallama yace to sani da Fatima kubude kunnanku kuji me nazo dashi musamman Kai sani Dan nasan daga gunka matsalar take Nan yaimusu bayanin abinda yafaru tindaga zuwan nabil ma,agai har daura auransa da akayi da shatuwa wannan da kuke gani me karaya ahannu itace amaryar tashi Kuma itace Wanda ya karya din itakuma wannan tsohuwar itace iya kakar shatuwa tazo taga inda jikarta zata zauna yanzu amarya zata zauna a bangaran nabil cakin gidannan Kuma adakin nabil har se tawarke sannan acikin gidajanka kabasu Daya sutare acan Dan Haka ga amananan ankawo muku ta Yar mutane kuji tsoran Allah kukula da ita kamar yanda zaku kula da danku nabil
MINISTER yace baffah meyasa kahada wannan auran kafasan nabil wlh baze taba yarda da wannan Yar kauyanba Kuma nasan nabil basanta zeyiba Kuma baffah na sanka Baka tambayi nabil ko yana san ta ko baya san ta kawai ka yanke hukunci ne ka aura Masa ita wlh daga ganin yarinyarnan Bata da kunya Kuma bazasu zauna lfyba ko ta ilimin nasan nabil yafita da komai kagan tafa yarinya kamar aljana se zarzare Ido take tin da suka shigo ko ita kakar tata Naga se wani huhura hanci take tana wani zarzarewa mutane Ido wlh in har akabar nabil da yarinyarnan ancuceshi Kai nabil kana santa ko baka Santa kafada kowa yaji Dan Allah baffah inyace bayaso kabarshi yasaketa kowa yahuta Dan wannan aljanar yarinyar ba ajinsa bace
Nabil yace daddy bakinciki ya hanani mgn tin daga lokacin da yake hada auran nakasa cewa komai Dan ganin komai nake kamar amafarki Ni abinda yafi konamin Rai wai a cikin aljihuna baffah yaciri kudi yabiya sadakin wannan mahaukaciyar yarinyar wlh daddy nakuma tsanar mace arayuwata Mata sun yimin abinda bazan taba mantawaba natsani yarinyarnan ranar da nafara ganinta na tabata ta zamemin Bala,I ta zamemin alakakai arayuwa Wai yau mace akakawo gidanmu azaman matata inba Wanda ya haifi ubanaba waye zemin Haka na barshi ban dau matakiba aduniyarnan bazan taba san taba Kai bama itaba du wata mace wlh na tsanesu illa uwata da Yan uwana Mata sune kawai ban tsana Suma sun Zama Dolene awajena daddy yau baffah ya kunyatani Wai Ni nabil nine baffah yasa aka dinga daukana agaban yarana da abokaina da wayannan mahaukatan yaran cancak kamar wani yaro anasawa amota ana ta rikeni Wai Kar na gudu Ni baffah yaiwa auran Dole dabaka ta da hankalinkaba baffah saboda Ni har abada bazanyi aureba Dan ko anyimin bani aka daura waba mommy da daddy ka daurawa aurannan ko Kuma kanka ka daurawa tin amazagai nakeso nai kuka ko naji Dadi azuciyata Amma nakasa Daddy zuciyata zata fashe in har aka barni da mace azaman matata faffah Zan hutar da Kai Zan saketa yanzu Ni nabal sani Zan
Kafin yakarasa iya tace wlh karma kafara baka Isa kamayar min da jika bazawaraba inaji Ina gani da ban yarda da auranba Amma yanzu na yarda da auran shatuwa da Kai Kuma wannan ikirarin da kayi na ka tsani du wata mace wlh kajawa kanka Zama daram Kai da shatuwa Dan Haka ka karya min jika bass kamar kasamu rake to karike wlh baka karya banzaba se nasa shatuwa tarama Kuma ko ban sataba nasan shatuwa Yar halakce Ni tagado zata rama Kuma wlh da Wasa ka tabamin jika se narama Mata itama Kuma kafin natafi Sena Mata nasiha akanka du abinda Kai Mata tarama Kar ta barka kana kiramin jika mahaukaciya kaifa me kala biyu Dan Allah jibeka ko gashin kanka abin kallone jibi wani wando Rabin duwawu du awaje ana ganin wandanka naciki jibi wasu uban sarkoki awuyanka sunfi kala biyar jibi yatsun hannunka zobunan da suke hannunka dubi shigar taka babu ta arziki da ubanka yake Kiran jikata Yar Kauye me kirar aljanu Kai kumafa me kirar me za a kiraka me kirar aljani ifiritu Zan kiraka ko dandaudu ko me tabin hankali da ubanka yake cewa jikata ba ta da ilimi indai irin ilimin kane wlh gara ta zauna Haka da Wanda na koya Mata jikata ba jahila bace Dan Ni Nan nice na ke koya Mata karatu har me kwanciyar tsakar daki du na koya Mata kai Kuma na dawo wajanka sani kake kowa wlh inkai Wasa Zan tsinkeka da Mari Dan Naga baka da mutunci tinda nashigo Naga kana harararmu kaganni Nan wlh shegen karfine da Ni bankiba daga Kai har Dan nake mu daku Dan jina ne ke dakaukau saboda karfi Kuma Nima nayi alkawarin senayi zaman Yan bori Akan kafar danka tinda ya karya min jika Kuma wlh ko yasaki jikata Bata sakuba Zama daram Dan Bazata koma mazagai ana kiranta da bazawara da kuke kiramin jika Yar Kauye kowa asalinsa Kauye Dan kwal ubanka daga Ina ubanka yake in ba da ga kauyenba anzo birni anyi kudin Alla ya Isa anci burudi da shayi da abin Yan gayu an manta da kauye usuman kajawa danka da jikanka kunne wlh Basu sanni bane labarina sukeji Zan gwada musu halina in suka kaini bango
Kafin baffah yai mgn MINISTER yace lanlai tsohuwar Nan daga ganinta Bata da mutunci Ni kike gayawa wannan mgnar lanlai in baaraba aura nabil da wannan yarinyar ba wlh kashemi Dana zakuyi ke da jikarki yanda kike San jikarki Haka Nima nake san Dana nabil Ni Kuma azamana na mahaifin nabil bangoyi auran nabil da jikarkiba Dole ya saketa Kuma Nima zanwa Dana nasiha in jikarki tamasa rashin kunya yarama Kar ya barta nama San Dana nabil shima Dan halakne ze Rama kakuma balballata Ni nasaka kaji nabil wlh wuya kadai se tasa jikarki ta gudu ji wani suna Wai shatuwa ko dadin ji Babu Dan Allah baffah karka Hana nabil sakin yarinyarnan wlh ke tsohuwa karki Kara kiran Dana Dan kwal uba nagaya Miki
Kafin kowa yayi mgn shatuwa tatakarkara takurma wani uban ihu se da nabil ya toshe kunnansa tace nashiga uku Ni yanzu ma nagane me ake nufi tin amazagai ban ganeba se yanzu har fadan da babarmu taimin Wai nabi mijina Ni du ban ganeba Ashe Wai aure akaimin iya kina Ina aka auramin wannan dandaudun Mata matamazan aka auramin iya Kika Bari haka tafaru Daman shi abbah ba Sona yakeba neman Kai yake Dani su megari ma Haka du basa Sona Wai ma Kuna nufin anan garin Zan zauna billahillazi ba Zan iyaba tinda muka shigo garin Banga gonakiba Kuma Ni bazan iya rayuwa Babu dawa da gonaki Babu kawayena Kai dandaudu wayacema Ina sanka Allah yakiyaye na auri rabi mutun rabi aljani yanda baka Sona Nima bana sanka yanda ka tsaneni Nima na tsaneka Kuma nadau alwashi se narama abinda kami wlh bazan taba hakuraba bakasan shatuwa jikar iya ikwan Allah ba
Nabil yace nashiga uku kaina zefashe Dan Allah baffah kakawo karshan rigimar Nan Dan Allah badan niba kaji tausayi na baffah karabani da mahaukayar Nan wlh na tsaneta ko ganinta banaso nayi karka min Haka Dan Allah baffah Kai mgn kayi shuru tin dazu
nabil yaje yarike wa baffah kafa
Baffah yace nabil wlh wlh wlh kaji na rantse har sau uku aure ya dauru Babu me Rabashi se Allah tinda shine komai yake hannunsa Amma wani Dan Adam wlh be Isa yaraba auranka da shatuwa ba Babu shi Kuma baayishiba Kai da ubanka kubude kunnanku kuji Ni Ni usuman mahaifin sani Kaka awajanka nabil in har ka kuskure ko da Wasa kasaki shatuwa wlh wlh wlh Sena tsinewa ubanka sani yabi duniya ya lalace Kuma bani bashi har abada kuma nacireshi acikin yarana gabadaya in kanasan ubanka kabar mgnar raba aure ko mgnar saki in Kuma bakasan ubanka gafili ga medoki ka saketa kaga aiki da cikawa Kai da ubanka me daurema gindi naji kana gigin ambatan saki wlh daga yanzu mgnar tafita bakinka gaba daya Kai da shatuwa mutu karaba Kai zaka binneta ko ita ta binneka kace katsani du wata mace ko to ga macenan ku zauna gida daya tare in kaso Dan Allah kamutu tana warkewa zaku bar gidannan Kai yanda kakeji da rashin mutunci hakama shatuwa takeji dshi ga tanan ku kashe junanku daga ita har Kai da kuke cewa ba kwasan juna aure dai ya dauru Babu batun rabuwa kuje Kai da ita ku koyi San junanku Kai sani shawara ta rage taka kace bakasan wannan auran ko to kaiwa danka fada yazauna da matarsa lfy ko kabi San danka ya saketa Ni Kuma mahaifinka na tsine maka
Gaba daya Kan MINISTER ya daure wani uban gumine yake ta ketomai ajiki du sanyin esin da ke falan Amma yajike da gumi se gogewa yake jiyayi gaba daya ya tsani shatuwa arayuwarshi da kakarta iya yanzu ya zeyi tinda har baffah Yana Kiran ze tsine Masa Akan wannan aljanar yarinyar Baki narawa yafara mgn yace Dan Allah baffah bekai hakaba Amma Ni da zakabi tatawa da kasa nabil yasa
Iya CE tataso tazo gaban MINISTER tace au baka sadudaba ko bakayi sanyiba du da dokar da ubanka yasa maka ko tu Bari kaga tinda kaki jin mgnar ubanka Ni Bari na fara wankeka da Mari tukunna
hannu tadaga zata mareshi kafin hannunta ya Kai fuskar MINISTER nabil yayi kukan kura yataso cikin fishi yarike hannun iya jikinshi se tsuma yake Dan masifa da bacin Rai da yake cin ransa yace ke tsohuwa ki nutsu kishiga taitayinki kafin na koya Miki hankali uban nawa Zaki Mara haba zance kike wlh Ina gani ki mararmin ubana Ina wajen Ashe ban haifuba ko da Wasa Kar ki Kuma gigin daga hannu da sunan mararmin uba kema inaga ban karyakin bane Dan Haka kikaki yin sanyi har kike cewa Zaki ramawa jikarki Nima se kin karyani ko ta Bari kiji somin tabi hannunta ya matse da karfi iya tasaki Kara Dan azaba Kuma ki jawa jikarki kunne tashiga hankalinta da Ni takuma iya bakinta in bahaba Zan canja Mata kamanni ke ko kunya bakijiba ubana na MINISTER kidaga hannu Zaki mareshi kin san waye shi a kasarnan Kinkuwa San me mukamin MINISTER na man fetir yake nufi koni DAN MINISTER kin Isa kisa hannu ki mareni bare ubana dada matsa hannun iya yayi takuwa da wata karar me karfi
Haba wa cikin fishi shatuwa tataso tararumi wata kwalbar fulawa da ke gefen TV zata kwadawa nabil tana jefuwa cikin zafin nama MINISTER yataso yatare Dan karya samu nabil seji akai kau agoshin MINISTER lokaci daya jini yaballe Yana zuba agishin sa ran nabil dada baci yayi jiyayi zuciyarshi zata fashe Daya hannunsa yasa yadafe kirjinsa jiyayi jiri na ibansa lokaci daya idansa yakada yayi jajir besan lokacin da yasaki hannun iyaba shima yafara neman abinda ze kwadawa shatuwa da besamuba idanshi yarufe yayi kan iya yabi ze daka azaman shatuwa ihu iya tafara tana neman dauki Dan nabil yayi Bali,in Bata tsoro dagudu Tai bayan kujerar da baffah yake azaune
tana cewa nashiga uku yau Naga ikwan Allah usuman Daman Haka jikanka yake ka hadashi aure da jikata ko dai shima Yana shaye shayennan na zamani da matasa keyi wannan wanna kalar aurene Kai nifa sirikarkace jikata kake aure usuman zefa lahantani kanaji kana gani in wannan zakin yai wasan kura Dani wlh ragargazani zeyi
Tsawa baffah ya dakawa nabil ya tsashi tsaye yace Kai karka yonan ko dawasa bare har kakuma tabata kaikuma sani kadan kagani ku bacemin dagani afalannan Kai da danka zamuyi Zama na musamman Ni da Kai sani kekuma shatuwa bakiga me kikaiwa sirikinkiba ko Baki San uban mijinki bane
Shatuwa tace Ni bashi nai niyar samuba wannan dandaudun nai niyar jifa shikuma yatare Masa na fasa Masa goshi ban saniba tsautsayine se hakuri Kai Kuma wlh Sena zubar maka da jini tukunna zakasan nice shatuwa
MINISTER hannun nabil yakama suka bar falan Yana tafe Yana masifa
Du wanna ruwan masifar da akeyi hajiya Fatima da Amina na wajan sun kasa mgn se Ido da dariya da mamaki
Baffah yace Amina jeki Basu wajan kwana Kan gobe bangaran nabil Zaki kaisu kimusu du abinda yadace ko abinci Basu ciba du kibasu suci in kin Gama dsu kizo nabaki Amana ke da mahaifiyarki kinji Yar albarka
Tace to baffah suka fice zuwa bangaran nabil
Hajiya Fatima tace baffah yau naci dariya Naga ikwan Allah
Baffah yace rabu da su Ina sane nahada aurannan insha Allahu shine silar shuryuwar nibil da sani Dan Allah kiga abin kunyar da sani da iya suka yi gaban yarannan memakwan suyi musu nasiha suhada kansu su zauna lfy Sema dada Bata abin sukayi kowa nawa nashi muguwar huduba Akan zaman auransu sani idansa yarufe San dansa yake du mgnar da tafito daga bakinshi fada yake Haka iya San jikarta itama yarufe Mata Ido du abinda yafito daga bakinta fada take Fatima ke da Amina ga amananan nabaku na shatuwa ku temaka ku gyarata ku wayar da ita asata amakaranta in tawaye itace zata gyara nabil Kuma itace zata cusawa nabil Santa azuciyarshi da San Du wata ya mace azuciyarshi takuma nuna Masa darajar mace da mutuncinta awajanshi da kansa ze sauka daga Kan akidarsa ta kin Mata yakuma so shatuwa ammafa se anyi Dan karamin yaki sosai agidan nabil Kuma fa se kunyi hakuri da halayan shatuwa Dan yarinyar bataji Kuma Bata da tsoro ko kadan Dan Haka na hadata da nabil zata iya da shi rashin tsorantane yasa na hadata da shi Dan Naga nabil na da wata baiwa kusan kowa tsoransa yake tin da Kika kirani awaya Kika fadamin halin da nabil ke ciki nake ta tinanin matar da Zan zaba Masa Kuma Sega wannan abin yafaru tsakanin sa da shatuwa da Kuma kalaman da naji yanayi Kan mace yasa na hada wannan auran Allah yasa kin fahinceni Fatima
Hajiya Fatima tace nagane baffah Kuma naji dadin hadinnan Allah yabamu ikwan rike amanar Yar mutane yanzu inda matsalar take awajan alhaji take Dan shima yadace yaba da gudun mawa wajan hada Kan shatuwa da nabil Amna se gashi shima bayasan auran saboda dansa bayaso kasanshi du abinda nabil keso shi yakeso in da nabil yace Yana Santa shima alhaji ze sota yagoyi bayan auran Amma yanzu tashin farko kaga me yafaru da idanka Ni nataba ganin wannan Bala,in ranar da aka kawo amarya akwashi wannan ruwan masifar haka memakwan ayi farin ciki se abin yakoma bacin Rai Allah ya kyauta
Baffah yace rabu da shi se gone zamu hadu da sani yanzu zanje na kwanta gobe in Allah ya kaimu zamu karasa yanda zaayi Dan gobe in komai yalafa zamu koma Ni da iya
Kai 馃ぃ馃ぃ Yan DAN MINISTER fans ku da kuke tashirin zuwa biki kunga yanda aka kwashe ranar da aka Kai amarya shatuwa to Ina Kuma ga ranar da ake Shan biki Ashe zakusha raban fada tsakanin iya da MINISTFR da shatuwa da Nabil馃ぃ se kunzo
su hasana lawan
da su maman munur
da su shafa Umar
da Aisha ummu Minal
da hajiya Rashida
maman Abdulhakim
Yar mulki
maman Haifa
Amina isima il
maman baby
ummu hasim
maman kairat zariya
maman yaseer
momin twins daweesu novel grp ayishat daweesu novel grp
Asha biki lfy nidai Ina daga gefe馃ぃ
Ngd sosai Yan DAN MINISTER fans grp da irin ruwan shirhin da kikaimin tin daga ranar da nafara DAN MINISTER zuwa yanzu
da sauran grp grp da sunayansu na manta godiya nake Allah yabar zumunci da du wayanda na manta sunansu Dan Allah kuyi hakuri ngd sosai Allah yabar so da kauna