🕊 *KAINUWA* 🕊
_........Dashen Allah_
*Haske Writer's Association*
*Na Ayusher Muhd🤸🏻♂*
*Bismillahi Rahmani Rahim*
_All character and event in these novel are Fiction_
May Allah guide us through the right path (Ameen).
_Godiya ta musaman ga masoyana, ina godiya da alfahari daku nagode kwarai da gaske._
Aunty Nah Hafsa Khabeer (Aunty Goggo) Allah ya kara kareki ya biyamiki bukatunki (Ameen)
*1*
*The year 1970*
Gida ya cika taf da mutane duk inda ka duba wasa ake yi, wasu na wasan dokuna wasu na wasan shad'i wasu busa suke yi, wasu waka suke yi, haka wasu wasan kidan kalangu sukeyi.
Hidima dai kala kala irin ta wasan ninmu na hausa na da, kowa ka gani fuskar nan tasa a washe take alamar farin ciki.
Bayi sai murna sukeyi dan irin wannan sha'ani shi ke sa su su fito haka, maroka sai tasu hidimar suke yi.
Gidan sarauta na kasar zazzau kenan wato Zariya.
Zazzau na daya daga cikin manyan masarautu a Najeriya. Masarautar taci kasashe da dama da yaki, Girman kasar Zazzau ada ta kai har Suleja a Jahar Niger.
Masarautar Zazzau ita ce tafi kowace masarauta a yankin Afrika ta yamma yawan makarantun zamani da na addini, shiya sa ma ake mata taken Zazzau, birnin Ilimi.
Zazzau yana d'aya daga cikin Hausa bakwai wanda Bayajidda ya kafa, gari ne na sarauta.
A wannan shekara ta Alif dubu d'aya da d'ari tara da saba'in karni ne na sarautar Abdulsamad wanda ya kasance d'a ne ka AbdulJalal wanda ya mulki kasar shima ta gadon mahaifinsa.
Abdulsamad yana shekara 20 kacal aka daura shi akan mulki sakamakon rasuwar mahaifinsa, suna da yawa a gun mahaifinsu sai dai shine ya kasance d'an sarauniya Kubra sannan yaro ne mai hankali hakan yasa mahaifinsa ya bada wasiyyar shi yakeso a nad'a.
An aura ma Abdulsamad mata a wannan lokacin wace ta kasance 'ya ce ga waziri wato " Safina" wacce ta kasance tun tana yar shekara uku mahaifinta ya bada umarni a koyar da ita tarbiya ta matan sarki, hakan yasa ta taso mace mai tsauri da tsananin jan aji, abinda zai baka mamaki ko Abdulsamad sai ya sara mata a gun ji da kai da mulki.
Safina ta auri Abdulsamad tana yar shekara 15, wacce aka nad'a a matsayin sarauniya, ta kuma bada umarnin a dinga kiranta da *Magajiya*.
Yayanta Hisham shine ya gaji mahaifinsu, wanda aka nad'a sarautar waziri.
Auran Abdulsamad da Safina babu soyayya a ciki sam aurene na umarni, sai dai ita dama Magajiya sam babu soyayya a tsarin rayuwarta abu d'aya aka nuna mata ta auri sarki ta haifar masa d'a wanda zai gajeshi.
Wannan shine abinda iyayenta suka daura ta akai.
A wannan lokacin shekarar Sarki Abdulsamad da Magajiya 20 da aure sai dai har yanzu Allah bai azurtasu da haihuwa ba.
Sarki ya cike mata 4 sannan yana da kwarkwara 9 amma har yanzu ba labarin ko da batan wata.
Wannan abu na matukar damun Sarki da Magajiya, tayi magani harta gaji har yanzu babu labari.
Sai dai alwashi ne tasha babu mai haifar ma Abdulsamad magaji sai ita in har ba ita ba kuwa to lalai bataga wacce ta isa ba.
_Wannan kenan_
Kwatsam Magajiya ta fara abin laulayi haka kuma tace ai likita ya bata umarnin zama a d'aki ba tare da fita ba har sai ta sauka, sannan ya hana mijinta kusantarta saboda mahaifarta batada karfi.
Sam wannan bai damu Sarki Abdulsamad ba shidai farin cikinsa shine zai samu magaji.
Magajiya sam ta daina fitowa haka ma bayinta sai wadanda ta yarda suzo gunta a haka har watan haihuwa tai, nan tace itakam gidansu takesan komawa.
Kasancewar Sarki Abdulsamad bai isa da itaba yasa ta shirya ta tafi.
Har ta sauka sannan aka aikomai da cewa ta haifi namiji.
Fadar farincikin da Hisham yake ciki ma b'ata lokaci ne, wanda ya kasance yau ne ake hidimar sunan d'an nasa wanda aka samai suna Abdulmajid.
Anata hidimar suna a waje sai dai daga kuryar d'akin Magajiya itace zaune akan kasan carpet gewaye da tintin sannan d'akin anyi jere sosai na kayan karfi masu kyau da tsada, tana zaune cikin shigarta ta matar Sarki, gefenta kuma Hisham ne a zaune, su biyu ne kacal a d'akin sakamakon sallamar bayinta datai.
Kallan Hisham tai cikin isa da mulki tace " Yaya baka manta da abinda na fad'a ma bako?"
Dariya yai yace "in banda abinki Magajiya ai ba wanda zai ji wannan sirri dan kuwa ita kanta Sauda(matarsa) na ja mata kunne akan ma karta kuskura ko da wasa tazo gidan nan inkuwa tazo to lallai karta bari su Hadu da Abdulmajid.
Murmusawa tai kadan sannan tace " daga Abdulmajid na rufe haifar wani d'a a gidan nan, babu macen da zata haihu bare ma har a fara tunanin wanda za'a daura akan mulki."
Hisham yai murmushin mugunta yace " Magajiya gaskiya kwakwalwarki tana aiki ya akai kika zo da tunanin karyar ciki? Sanda na sanar dake Sauda na da juna biyu?"
Wani murmushin kasaita tai sannan ta sa hannu akan lab'anta alamar shiru sannan a hankali tace " Yaya kenan ai na fad'a maka tabbas d'ana shine zai gaji sarautarnan, inhar bazan haihu ba dole ne nai amfani da kai jinina."
Wani kallo sukama juna na jin dadin abinda suka kulla, Hisham yace " Nace Sauda ta bari sai nan da wata uku sannan ta dawo."
Magajiya ta jinjina kai alamar gamsuwa tace " gwara ta kara zama saboda kar aganta aga kalar haihuwa aga kuma ba ciki, dan ma matar nada hakuri kaga bata mana musu ba sanda muka bata umarni."
Hisham ya sosa keya yace " inta kawo wargi ai sai ta amshi takardarta."
Murmushin jin dadi Magajiya tai sannan tace " ka sa a kara aikomin da maganin nan dan wanda nake badawa a sa ma matansa a girki ya kare."
Ya dan sa dariya yace " gaskiya Magajiya ke karshe ce, shi yasa nake baki girma da darajaki, amma bakya gani ko an daina basu maganin yanzu ba abinda zai faru? Gani nake mahaifar tasu ma ai ta gama aiki."
Wani murmushi tai wanda ya fahimci cewa tana nufin ta sani amma a kawo.
_Nikam nace Hmmm_
Sarki Abdulsamad kam kana kallansa zakasan yana cikin tsananin farin ciki.
Bayan ya dawo daga hawan doki ne ya shigo fada sai ga wani bawansa ya sanar dashi yayi bako.
Nan ya bada izini akan bakon ya shigo.
Wa zai gani? Amininsa ne wanda suka shaku sai dai dayake shi dan Katsina ne wanda aiki ne ya kawo mahaifinsa garin Zariya, har suka shaku haka kafin daga baya su koma garinsu.
Da sauri ya karasa gun sarki saboda tsananin murna, nan Sarki ya kallesu da ido wanda ya nunama dogaran akan yanaso su fita, ba musu kuwa sukai waje.
Rungume juna sukai cikin tsananin farin ciki Sarki ya kalli abokinsa yace " Amadu ashe zan ganka?"
Wani irin farin ciki sukeji na ganin juna, bayan sun nustu ne suka shiga hirar yaushe gamo.
Can Sarki yace " ko ziyara Amadu? Da alama yanzuma ba saboda ni kazo ba."
Sarki gani yai Amadu yayi kasa da kansa alamar damuwa, cikin kulawa yace "menene?"
Hawaye ne ya ciciko a idan Amadu cikin wata muryar abin tausayi yace " Mai martaba ina cikin wani mugun hali."
Mamaki ne ya kama Sarki yace "Name kenan?"
Ido Amadu ya runtse yace " kanwata aka ma fyade a kasarmu, wanda hakan yasa dangina da na matata duk hankalin mu ya tashi sakamakon habaici da kyamatar mu da akeyi."
Cikin tsananin tashin hankali Sarki yace "kanwar ka badai Basira ba?"
Amadu ya jinjina kai cikin takaici sannan yace " ita kuwa shiyasa naga zamanta acan bazai yiwuba dan ko fita bata iyayi shine nace bari inzo in rokeka ko zaka tambayarmin yayarka Aunty Babba ko zata zauna agunta ko da kuwa na wata d'aya ne, bani da wanda na sani bayan kai a kasar nan, gashi duk samarinta sun gujeta."
Cikin tausayawa Sarki yace " amma garin yaya?"
Amadu yace " da daddare matata ta aiketa siyo maganin zazzabi dan bawa d'ana da bashida lafiya, nikuma bana gari, a hanyarta ta dawowa aka tareta aka mata fyade, duhu yasa batasan waye ba bare ta nunashi."
Sarki yai shiru yana nazari, Amadu yacigaba " Mai martaba in kuwa kanada wani dogari ko bawa da kake tunani ka hadata dashi a musu aure dan kuwa babban abin kunya ne a ma mace fyade ka san bazata taba samun miji ba sai dai wani iko na Allah gashi ta girma shi yasa nake tunani ko wanene ma kawai ka bata a daura auren kafin nan sai ta zauna gun Aunty Babba."
_da yake a wancan lokacin babban abin tashin hankali da kunya ne a ma mace fyade ko ta je gidan mijinta ba tare da budurcin ta ba_
Sarki yai shiru, tausayin rayuwar Basira yakeyi, yarinya ce wacce ba ruwanta ga hakuri.
Bayan dogon nazari ya kalli Amadu yace " kaunar da mahaifinka yakema nawa, da wanda kaima kake min yasa na yanke shawara ni zan aureta sqi dai inaso karka bari zancen fyade a fito a ko ina, mu birne ta a nan inba haka ba kyamatarta za'a dingayi a gidan nan."
Tsananin mamaki yasa Amadu ya kasa magana sai dai wani zazzafan kwalla daya gangaro masa, kai ya girgiza yace " nagode dajin haka sai dai bazan yarda ka auri macen da aka taba a waje ba."
Sarki yai dan murmushi yace" Amadu kenan menene amfanin abotar? Kana tunanin akwai mai rike ma sirrinka bayan nidin? Yanzu in muka mata aure da wani bawan ko dogarin daga yaje ya ga ba cikakiya bace shikenan sai wulakanci, haka ma in sanar dashi mukai bazai fasa wahalar da ita ba."
Amadu yai shiru, Sarki ya dafa shi yace "karka damu a goben nan ma zan aureta sai dai bazan bari a sani ba tukunna har sai 'yan taro sun watse saboda hidimar suna da akeyi."
Amadu ya zube yana godiya, Sarki yace " ka koma kasarka gobe da safe zanyi shigar burtu na zo ba tare da sanin kowa ba sai wanda na yarda dashi."
Amadu wani dadi ya kamashi ya hau godiya sannan yace " nidai zan jiraka mu tafi tare sabida tsaronka."
Sarki yai murmushi yace " idan ka tsaya kuma waye zai sanar dasu maganar auran? Sannan nima banaso asan zanje har can din, sannan ka bari in sa akaika a mota dan nasan a irin a kori kurar nan ka zo."
_A waccan lokacin in har kaga mutum da motarsa to fa lalai d'an wani ne sannan motar ma mu a wannan lokacin tsohon yayi muke daukanta irin mai shafaffen booth din nan ce.._
Sun dade suna tattaunawa kafin Amadu ya mike yamai sallama, godiya da jindadi kam yayi ba adadi.
Nikam nace hmm wata sabuwa....
*ABUTURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA* 🕊
_........Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*Haske Writer's Association*
*Na Ayusher Muhd*
*2*
Shiru Sarki yai yana nazari bayan fitar abokinsa, baiyi zata ba sai jin muryar Aminin nasa yai a kusa dashi alhalin ya dauka ya tafi.
Amadu yace " Amma Mai Martaba ba matanka hud'u ba?"
Idanunsa ya bud'e ya saukesu akan Amadu sannan yace " Amadu kaje ka sanar da Barde ya kaika gida, ni kuma gobe zanzo."
Jin haka yasa Amadu ya fita jiki a sanyaye, Mai martaba yai shiru tare da maida idanunsa ya rufe, ya dade a haka kafin ya bud'e idanunsa sannan ya kira wani bawansa ya sanar dashi akan ya kira masa kaninsa wanda suke uwa da uba daya.
Bai dade da fita ba sai gashi ya dawo shi kuma kanin nasa Kamal na biye dashi a baya.
Yana shiga ya saki fuska tare da cewa " Mai Martaba ina can ina hawan doki ka aika a kirani, Allah yasa ba matsala bane."
Abdulsamad ya tattara hankalinsa kan kaninsa yace " Kamal yanzu ace na baka mata zaka aura?"
Kai ya d'aga mai alamar eh sannan yace "ko ma wace iri ce in har ba mara da'a bace ko wacce ta lalata tarbiyarta da darajarta a waje ba."
Sarki yai shiru kafin yace " in kuma d'aya daga cikin wacce ka lissafo baka so ne fa?"
Kamal yai murmushi kafin yace " maganar gaskiya zan aureta in har umarnine daga bakin Sarki sai dai in har umarnine daga bakin yayana bazayi ba gaskiya."
Ya dade yana kallan Kamal kafin ya daure da murmushi yace " ya kaje gun d'an naka?"
Kamal ya washe baki yace " Abdulmalik yana can yana bacci amma yau kam zai yi kwanciyar gajiya, ai yau kowa na cikin farincikin magajin sarki."
Sarki ya kara fad'ada murmushinsa yana jin dadin kasancewarsa uba kafin ya sallami Kamal.
Bayan fitar kamal ne ya shiru yana tunani ( _a yanda tarihi yake mata guda hudu ne kamar yanda musulunci ya umarta mana sai dai akwai kwarkwara wanda suke zama matan sarki in anci garinsu da yaki ko kuma makamancin haka sannan su wad'an nan basu da gadon sarki in ya mutu_)
Lalai yau ya yanke hukunci ba tare da yasan mafita ba sai dai yayi hakan ne saboda tunanin kare mutuncin aminin nasa.
Matarsa ta karshe ko ince Amaryarsa wacce ya aura a waccan shekarar ita yake tunanin rabuwa da ita badan komai ba sai dan rashin san auransa da takeyi shi kansa yasan tauye mata hakki mahaifanta sukai gun bashi ita, yarinyace 'yar shekara 12 mahaifinta yayane ga sarkin Daura wanda sunyi hadin auren ne a san ransu, ace shi yana shekara 40 amma an bashi yar shekara 12 ai kowa yasan hakkinta aka tauye shi yasa ko tunanin nemanta bai taba yi ba.
Da wannan shawara ya mike tare da ba bayinsa izini akan yanasan a kira Magajiya zuwa turakarsa
**********
Magajiya kam tana zaune sai shigowa ake yan suna ana mata barka, ba amsa wa take ba sai kai kawai da take kadawa cikin isa da takama.
A ranta wani irin nishad'i takeji tabbas tana cikin tsantsan farin ciki dan saura kiris burinta ya cika, wannan burin nata kuwa bai wuce ace d'anta Abdulmalik ya hau mulkin garin na Zazzau ba.
Wata baiwar ta ce ta iso kusa da ita ta rada mata a kunne sakon Sarki, idanu ta juya tare da d'an yin karamin tsaki a ranta, itafa batasan takura akan mai shi baxai zo inda take ba sai dai ace wai taje?
Tafi minti talatin kafin ta mike ta fito.
Turakarsa ta nufa yana xaune akan kilisar dake shimfid'e a gun, nan ta shiga kanta tsaye.
D'agowa yai ya kalleta ta iso ta zauna d'an nesa dashi kadan cikin isa tace " gani ranka ya dade."
Kallanta yai yace " Magajiya na tasoki kina cikin taro ko?"
Kallansa tai ta danyi murmushi tace " da alama kanada magana mahimmiya ne."
Ajiyar zuciya yai sannan yace " ana cikin farin ciki sai dai zan sanar dake wata magana ne."
Kallansa tai tare da tattara hankalinta kansa.
Yacigaba " so nake in ba Rabi'atu takardarta ina tunanin zallintar da mukema yarinyar nan ya isa haka."
Kallansa tai cikin mamaki tace " ban gane ba? Ka taba gani inda sarki ya saki mace?"
Yace " yau xa'a fara a kaina."
Tace " in ka saketa kana tunanin akwai mai auranta?"
Abdulsamad yace " zan saketa ne amma bazan bari tabar gidan nan ba, ni zan rike ta har sai ta samu wanda takeso in aurar da ita."
Kallansa tai har zatai magana ta fasa dan itakam yanzu babu wani abu da zai dameta d'a ne ta samu yanzu dan haka komai ma zai faru sai dai ya faru.
Ganin tayi shiru yasa ya fahimci ta amince nan ya rubuta takardar saki d'aya ya mika mata yace " ki sanar da ita sai ta koma bangarenki da xama ko bangaren Hajiya Umma (mahaifiyarsa)
Jiyai tace " sai dai bangaren Umman dan nikam banasan tarikice."
Sarai maganar tad'an kona ransa sai dai bai nuna mata ba, takardar ta amsa sannan ta mike ta fita.
Itakam Rabi'a bayan Magajiya ta aika tazo ta sanar da ita halin da ake ciki sam bata damu ba sai ma dadi da taji ta kuma ji dadi kwarai da akace zata zauna anan, dan dama tsoronta mahaifinta.
Suna yayi dadi an kashe kud'i, 'yan gari sun sha kalo, anyi hawan doki sosai, jaruman maza sun sha wasa da takubba, masu wasa da kura sun sa mutane nishad'i da sauransu.
Da haka kowa ya koma gida, Magajiya ta dauko unguwar zoma mai kula da ita.
*********
Washegari Sarki Abdulsamad bayan yayi sallar asuba yakira bawansa wanda ya aminta dashi haka kuma shine dama yake jansa a mota ya sanar dashi zasuyi tafiya, suna sallar asuba ya fadama fadawansa akan zai dan yi zagaye cikin gari dan ganin halin da mutanensa ke ciki.
Kasancewar kowa yasan dama al'adarsa ce yasa ba wanda ya kawo komai a ransa, suna fita suka dau hanyar katsina.
*******
A can katsina kuwa Amadu ya sanar dasu akan gobe za'a daura ma Basira aure da zarar anyu sallar azahar a masallaci.
Basira kam batada bakin magana dan ita tun bayan faruwar wannan lamari sam ko magana ta daina yi, ko tambayar mijin batai ba ta mike ta koma ciki.
Matar Amadu ta shigo ta ganta a zaune a bakin irin gadon nan na karfe, ta kalleta tace " Basira bakyaso ne?"
Kai basira ta jijiga mata alamar A'a.
Numfashi ta ja sannan tace " Basira ya kamata ki cire abin nan aranki yau wata d'aya da sati biyu kenan da faruwar wannan al'amari, daga ni har ke rabon da mu fira waje kenan, sai dai ke ko magana ba yi kike ba sai in ta kamaki dole, bakya gani lokaci yayi da zaki cire wannan a ranki?
Murmushin dole tai sannan ta mike, ga mamakin Aunty Karima gani tai ta shiga had'a kayenta a akwati, mikewa tai jiki a sanyaye tai waje, ba shakka tana tausayin yarinyar nan gashi Amadu ya ki fada mata waye mijin itakam tana tsoron kar akai yarinyar nan inda zatasha wahala, dan ma dadinta d'aya ciki bai shiga ba sanda akai fyaden tunda har tayi al'adar ta.
Basira kam kayanta kawai take sawa a akwati tana gamawa ta shiga tai wanka tare da kwanciya akan gadon d'akin, ta rasa me yasa ko tunani ma ta kasa yi idanunta kawai ta rufe.
Bacci ne ya dauketa mai nauyin gaske.
**********
Wajen karfe 12 suka iso dan motar wannan lokacin sam ba gudu ne da ita ba kamar ta yanzu ba, hakan yasa suka dade sosai a hanya.
Basu san gidan Amadu ba hakan yasa suka shuga neman kwatance dan ma ya sanar dasu unguwar dan lokacin ba a sa sunan layi.
Sun dan sha wahala kafin su gane gidan dan ma abun mutane sai sunce gidan su Basira sannan ake ganewa.
Wajen karfe d'aya suka isa gidan lokacin Amadu na waje yana ta leke kudu da yamma ko zai gansu.
Yana hangosu ya saki ajiyar zuciya dan da ya dauka ko an samu wata matsalar ne.
Abdulsamad ko ciki bai shiga ba yace muje masallaci a ayi abunda za'ai in koma dan barin fada ba tare da kwakwaran uzuri ba matsala ne.
Amadu ya jinjina kai sannan suka nufi masallacin kusa dasu dama ya riga ya sanarma liman, bayan sunyi sallah ne aka daura auren Abdulsamad da Basira wanda Liman yama Abdulsalam walici shi kuma Amadu yama Basira an daura aure akan sadaki naira dari 200.
Wannan kenan.......
*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
_Dan Allah wanda yamin magana ban mai reply ba yai hakuri jiya whatsapp d'ina ya samu matsala sai dana sake downloading sai dai sam yaki backup name messages d'ina_
*Na Ayusher Muhd🤸🏼♂*
*3*
Kafin su fito daga masallaci bayan an daura auren mutane har sun cika gaban masallacin, labari har ya kai musu cewa ga wani gara can da baisan me yakeyi ba ya auri Basira.
Sarki na kokarin fitowa wannan Bawan nasa ya sha gabansa ya rusuna tare da sanar dashi halin da ake ciki.
Jikin Amadu ne yai mugun sanyi, jiyai Abdulsamad yace " Ku fara fita in yaso ni sai in fito daga baya."
Amadu yace " ai Mai martaba bakasan gidan ba."
Yace ba komai zan biko a baya ne nima ai.
Jin hakan yasa suka fara fita, nan fa mutane suka saki baki suna kallan bawan, kowa da gulmar dake fada aransa, wasu cewa suke ai dole ya nemo ko ma waye ya bata da kuma alama ma fakiri ne, wasu kuma suce da alama sadaka aka bashi yaji banza shi yasa bazai iya bari ba.
Haka dai kowa da abinda yake tunani, sudai sukai gaba, Mai Martaba na baya cikin mutane yana kuma jin duk abinda kowa ke fada, jikinsa ne yai mugun sanyi lalai ba shakka yayi babban taimakon na auran yarinyar nan dan kuwa da alama ba mai auranta a garin nan.
Sai da mutane sukaga sun isa gida sannan kowa ya watse, shi kuma Sarki Abdulsamad ya shiga ciki.
Bayan sun zauna ne matar Amadu ta kawo musu fura mai sanyi tare da dambu na tsakin massara yasha gyada, Abdulsamad ya dan ci kad'an kafin ya kalli Amadu yace " Amadu ba zan kai Basira gidana ba yanzu."
Gaban Amadu ne ya fadi yace " kana dana sani ko? Na auranta? Ni kai........"
Katseshi Abdulsamad yai yace " ina tsorace mata a bubuwa guda uku shiyasa bazan kaita yanzu ba."
Yadan ja numfashi na manyan mutane kafin yace " in har taje gidan nan a haka zatasha bakar wahala ba tare kuma da sanina ba, ko Magajiya bazata barta haka ba, ganin jiya akai sunan d'anta ace yau na kawo mata? Sannan na saki yarinya jiya ashe wani nake san sakeyi? Sannan ban sanar dasu zanyi auren ba ma sam.
Kaga wad'annan dalilan sune zai sa su wahalar da Basira, gata ita kuma ko harkar gidan sarauta bata sani ba bare ta nemi kwatar kanta."
Shiru Amadu yai kafin yace " Gaskiya ne ni kaga sam banyi wannan nazarin ba nidai dadina Basira ta auri wanda nasan ko bani da rai zai kular min da ita."
Sarki ya d'an murmusa kadan kafin yace " Zan baka kwatancen gidana a cikin gari, zan kuma sanar ma ma'aikatan gidan in yaso kai zuwa gobe sai ka taho da ita ka kaita can, zan tura mata bayin da zasu dinga kula da ita da koya mata abubuwan daya dace, in yaso zuwa ko sati biyu ne sai ta dawo."
Amadu ya shiga godiya, nan Sarki ya mike yace zai wuce.
Amadu ya shiga kwallama Basira kira, da sauri Sarki yace " ya isa haka, bance ka kirata ba ai, ina sauri ne in tazo naje na ganta."
Amadu ya amsa da to, sannan yamai sallama yai waje.
Yana fita ita kuma matar Amadu wacce ta taso Basira da kyar tanata sharar baccinta suka fito, ganin ba kowa a gun yasa tace " Malam ina mijin?"
Basira ya kalla yace " Basira gobe zan kaiki shi yayi gaba."
Matar tace " a ina aka tabayin haka? Yaya shine zai kai yarinya?"
Amadu yace " ni ai da so nai tabi mijinta ma baki alekum to amma tunda haka yace ni na kaita goben"
Zata sake magana yace " kul! Mijin Basira baya magana a canzata dan haka ki kiyayi kanki."
Mamaki ya kamata sai dai bata sake magana ba, Basira kam tana jin haka ta koma ciki tai alwala tai azahar.
*********
A can gidan Sarauta kam ganin Sarki ya dade bai dawo ba yasa Hisham ya shiga amsar matsaloli da dai sauran abinda Abdulsamad ya kamata yai a ranar,dadi kuwa ya kamashi dan ba shakka yana san mulki sosai.
Sai wajen shida sannan suka isa zariya.
Kai tsaye wanka yai sannan ya zauna a kilisarsa aka shiga jeramai abinci kala kala da 'ya'yan itatuwa..
Sai da ya koshi sannan yai bincike akan abinda ya faru a ranar.
***********
Isar Magajiya da mulkinta yasa ta bada umarni bayan auranta dole ne duk matar sarki da kwarkwarori suzo su gaisheta da safe kafin suci abinci anan ne take sawa a kawo musu wani shayi wand sune suke tunanin shayi ne sai dai a zahiri naganin hana daukar ciki ne.
*********
Amadu kam ya kai Basira inda aka umarceshi sannan ya mata sallama akan zai tafi.
Kallansa tai idanunta suna neman cikowa tace " yaya ina ne nan? Na tabbata ba mai hankali mai kudin kuma da zai aureni."
Amadu ya girgiza mata kai yana murmushi yace " a naki tunanin kenan sai dai Basira inaso ki kasance mai godiya ga Allah dan kuaa ya baki mijin da babu kamarsa wanda baki taba tunanin ko gani ba bare aure ba."
Zatai magana taga ya juya baya yana kara kallan falon, daga nan ya kara mata nasiha ya fita zuciyarsa fes da ita.
*********
Sarki kam sam ya manta da Basira sakamakon hidimomin dake gabansa, yau ya cika satinta uku kenan da zuwa garin amma ko keyarsa bata gani va, sai wasu abubuwa da ake koya mata.
Gashi abin haushi komai sai ace sai dai a mata, magana wannan akwai mai nuna mata yanda zatai, itakam duk ta gaji da wannan sabon al'amarin.
Yau watanta d'aya cif, Abdulsamad harya kwanta bacci ya tuno da Basira da sauri ya mike cikin tsananin mamakin kansa da takaici ya fito daga turakarsa, Bayinsa ne suka matso suna tambayaraa ko yana bukatara wani abun ne?
Da sauri ya nemi bawansa Mudan ya kuma umarci bayin da wannan fitae ta zama sirri, nan yai waje shida Mudan.
Kayan fadawa ya saka sannan ya rufe fuskarsa ya hau doki, ba wanda yai tunanin Sarki ne har ya fita.
Gidansa ya nufa, a lokacin ita kuma an sa tayi wanka da wasu turaruka masu kamshi kamar yanda suke sata kullum wai hakane al'adar dole in zatai bacci tai wanka da wad'an nan turarukan sannan ta sha madarar shanu ta kwanta.
Ta fito kenan ta zira doguwar riga tana shan madara taji sallama.
Gabanta ne ya fad'i jin muryar namiji, a hankali ta amsa kamar mai rad'a, nam shi kuma ya shiga.
A zaune ya ganta sai dai idanunwanta sunyi zuruzuru.
Dama ya umarci bayin dake waje su tafi makwancin su, nan na cikin d'akin suma suna ganinshi suka zube suna gaidashi, nan suma ya sallamesu.
Itakam idanuwanta ne duk suka fito jin suna cewa " Mai Martaba barkada shigowa."
Batakai ga nemo amsar tambayar dake mata yawo akai ba taji yace " Basira ba gaisuwa?"
Kallansa tai sannan ta zube da sauri kamar taga mala'ika sai dai ta kasa cewa komai sai gabanta kawai dake mugun fad'uwa.
Murmushi yai sannan ya matso kusa da ita ya d'agata ya, itakam kafafuwanta rawa suke hakan yasa tsayuwar ta fara neman gaggararta, da sauri ya jawota jikinsa tsoro ne yasa ta zaro idanuwa, shikam Abdulsamad yana mamakin girman yarinyar.
Kamshin jikinta ne ya sa ya lumshe ido ba shakka kamshin Magajiya ya ninka nata dadi sosai sai dai baisan meyasa yakijin nata wanu daban ba, ji yake yana ratsa zuciyarsa.
Bata taba tunani ba haka kuma batau zato ba taji yace " kinyi al'ada ne?"
Da sauri ta matsa daga jikinsa ta kalleshi kadan sannan ta sunkuyar dakai, taya za'ai ya mata wannan tambayar? Ko kunya?"
Abdulsamad yace "dole ce ta sani yi miki tambayar."
Baya ta juya da sauri sannan ta d'aga kai alamar eh tare da shigewa uwar d'aka.
Hamdala yai sannan ya shiga ciki shima.
Itakam a bakin gado ta zauna tare da rike hannayenta biyu itakam wacce irin tambaya aka mata yanzu? Mijin da bata taba gani ba taya zai fara mata wannan tambayar?"
Shigowarsa ne yasa tai saurin kwanciya tare da rufe ido, murmushi yai sannan ya karasa kusa da ita ya zauna, hannu ya sa a kafadarta cikin maganarsa ta isa da sanyi yace " Basira na tambayeki ne badan komai ba sai saboda gaba."
Kallansa tai cikin mamaki yai dan murmushi yace "karki damu ni dama nasan ba matsala sai dai ya zana dole na tambaya."
Kasa tai da kanta ta maidashi kan filo, kanta ya shiga shafawa a hankali ya kwanto da kansa jikinta, tsoro ne ya shiga kamata ta tuno abinda ya faru da ita.
Da sauri ta mike ta zauna tare da matse kafafuwanta.
Hawayene ya shiga zubo mata, tana kuka tana girgiza kai.
Sarki ya shiga mata kallan tausayi, Basira cikin kuka tace " tsoro nake."
Matsowa yai kusa da ita ya rungumeta ta kara fashewa da wani kukan, nan ya shiga jijigata yana bata hakuri cikin salon soyayya a haka har yasa jikinta ya mutu nan shi kuma ya gabatar da abinda yake so........
Bayan ya nutsu ne ya jawota jikinsa itakam har yanzu kuka take, hakuri ya cigaba da bata, ta dade sosai tana kuka kafin bacci yai gaba da ita.
Shiru yai yana kallanta, ya sani sarai dolene gobe bayin dake kula da ita su bincika ko jinin da ya kamata ya fita a gabanta sakamakon farkon kusancin ta da maza ya fito, dan sune zasu zama shaidarta nan gaba.
Dubawa yai ya samo reza ya bud'e cinyarsa ya tsaga kad'an sannan ya sa a jikin zanin gadon, sannan ya mike ya fito bayan ya dan sumbaci Basira.
*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼♂*
*4*
Wajen Sallar asuba babbar mai kula da ita a cikin bayi ta shigo dan taimaka mata tai alwala.
Basira tana kwance tana bacci matar ta shigo ta tasheta, sam Basira ta manta abinda ya faru hakan yasa da karfinta ta nemi tashi, jin zafi a gabanta ne yasa ta tuna, saboda tasha wahala sosai sanda aka mata fyade dan sai da matar yayanta tai ta saka ta acikin ruwa mai zafi tana gasata tukun na, mikin daya warke ne taji ya motsa, hakan yasa ta dan ce wash.
Matar ta kalleta tare da yayi zanin gado da sauri, ganin jini yasa ta saki gud'a, Basira kam kallan jinin tai sam bata kawo ba daga jikinta ya fito ba saboda matan da ba ruwansu da zancen nan, hakan yasa batasan sau d'aya yake fitowa ba, itakam matar ce take bata mamaki ganin yanda take gud'a.
Kan kace me? Sai ga ragowar bayin sun taho da sauri, nan suka gani kowa ya fahimta, nan wata ta fita dan d'ora mata ruwan zafi, itakam matar zanin ta yayi ga mamakin Basira gani tai ta ninke ta saka a cikin leda.
Bayan ruwa yai zafi ta taimaka mata tai wanka tai sallah sannan aka kawo mata abinci, Basira nasan taji wai menene matsayin wannan mijin nata wanda yazo jiya sai dai tana kunyar tambayar hakan.
**********
Sarki ne zaune akan kilisarsa Magajiya na d'an nesa dashi tana cin 'ya'yan itatuwa shi kuma yana d'auke da Abdulmajid a hannunsa yana murmushi, can ya nisa yace " Magajiya nayi aure."
Kallansa tai cikin isa tace " aure kamar ya kenan?"
Ya dan murmusa yace " kanwar abokina Amadu ce zata tare nan da sati d'aya zuwa biyu."
Kallan mamaki tamai sai dai isa da ji da kai yasa batace komai ba, sai dai maganar ta kular da ita sosai tayaya kamar ita za'a mata kishiya ba tare da ta sani ba?lalai Abdulsamad yazo da rainin hankali.
Mikewa yaga tayi tare da kiran baiwarta, nan ta shigo da sauri, Magajiya ta kalleta tace "Amso Yarima zan koma."
Abdulsamad ya kalleta sai dai shima baice komai ba sai mika ma baiwa 'yar yai suka fita.
Tana fita ta tura a kira mata Yayanta Hisham.
Zaune take a d'aki ya shigo cikin sauri, ganin yanda fuskarta take a had'e yasa yace "Magajiya lafiya?"
Kofin dake hannunta ta jefo da karfi inda yake saura kiris ya jefeshi hakan yasa yasan lalai yayi laifi, da sauri ya matso cikin sanyin murya yace "kanwata........."
Wani mugun kallo ta bugamai tace " me kakeyi har Sarki yai aure ban sani ba?"
Gabansa ne ya fad'i cikin tsananin mamaki yace "Aure kuma?"
Wani kallo ta kara mai tace " ba nace ka dinga kula da duk al'amuransa ba? Yaya wai meke damunka ne? Ko ka manta da wasiyyar Baba yace?akan ka dinga bin duk abinda na fad'a?"
Yace "Yahkuri Sarauniya uwar Sarki duk wanda yaja dake shine a wahale, tayaya wata mata can da baki santa ba zata kona miki rai bayan ko ta shigo sahun ragowar matan zata shiga?"
Shiru tai tana kallansa, yace " menene naki na kishin wata macen bayan ba haihuwa zatai ba bare musa ran samun matsala nan gaba?"
Shiru tai kafin daga bisani tai ajiyar zuciya sannan ta d'an ja tsaki tace " ko menene dalilina na jin haka? Tunda yake aure ban taba jin haushi ba sai yau."
Hisham yai dan dariya ganin ya shawo kanta yace "kinada yarima magajin sarki sannan kina da ni waziri menene zai saki damuwa?"
Murmushin jin dadi tai sannan tace " zan baka sako ka aikama gidan matarka sannan itama ya kamata ta dawo."
Kai ya jinjina alamar gamsuwa yace " yanzu kam bamai gane ta haihu."
Sukai murmushin jin dadi.
_nikam nace hmmmmm_
Yau ranar kwanan Basira ne a yanda Mai martaba ya tsara sai dai kasancewar bata nan ya kamata ace shi kadai zai kwana, sai dai shikam da daddare ya lalaba ya fita.
Tana zaune ita kadai shiru, gefenta bayinta ne suke ta hirarsu, taji sallama.
Da sauri suka mike suka shiga kwasar gaisuwa sannan suka fita, ya rage saura su biyu.
Zama yai daga gefenta kadan yana shirin magana tai saurin cewa "ina wuni?"
Kallanta yai yace " da alama sai na sa an d'aure masu kula dake."
Dasauri ta kalleshi idanunta sun bayyanar da tsoro tace " me sukai?"
Yace " tunda haryanzu basu koya miki abinda ya dace ba."
Da sauri tace "Barka da dare."
Sannan ta cigaba "wlh na sha'afa ne ba laifinsu bane."
Murmushi yai sannan yace " ke bakya magana dayawa ne?"
Shiru tai batace komai ba, yana kallanta yace "kishirya zuwa jibi zaki koma gidana."
Kallansa tai batace komai ba itakam tana san jin shi d'in wanene.
Jitai yace "Abdulsamad sunana sauran bayani zaki gani inkin isa jibi."
Kai ta d'aga ba tare da ta kalleshi ba, hannu yasa ya rikota suka shiga ciki.
Duk da itakam tana tsoro sai dai bata isa bijire ma wanda ya taimaki rayuwarta ba.
Sai da komai ya lafa sannan bacci yai gaba dashi, itakam shiru tai dan baccin ya bar idanunta ta dade tana tunani kala kala kafin tai bacci.
***********
Magajiya da kanta tasa aka gyara b'angaren da zata zauna sannan tasa aka sanar da Sarki akan komai ya kammala, shikuma ya aika a sanar dasu lokacin da za'a daukosu.
Da daddare aka sata tai wanka, bayan tasa kaya aka miko mata alkyabba irin masu karfin gaske da nauyi irin na da, aka sa mata, mamaki sam ya hanata magana, sarka ta zinare aka sa mata aka sa mata abin kafa da awarwaro, kasa jurewa tai ta kalli baiwar tata tace " amma wannan shigar batai yawa ba? Ni fa na fara tsoro."
Baiwar tai kasa dakai tace " tayaya kaya zaiyi yawa bayan haka al'adar masarautar take? "
Cikin tsananin mamaki tace "Masarauta?"
Kallanta baiwar tai tace " eh mana duk abinda muke koya miki ai abinda zakiyi ko zaki tarar acan mukeyi."
Wani abu ne ya tsaya mata a makogaro, sarauta? Ba shakka ta gane yanzu, wato abokin yaya ne wanda kusan duk labarin yaya baya wuce na Sarki Abdulsamad lalai shine ya aureta kenan, to amma ina ita ina shi? Ta ina? Ita da ba cikakiya ba? Jitai an dafata hakan yasa tai firgigit daga tunanin data tafi.
Baiwar tace " Ranki ya dade ana jira."
Dakyar ta fara d'aga kafarta suka fita.
*******
Haka suka isa gidan tunani duk ya isheta.
B'angarenta aka wuce da ita suna tafe ana gaidasu danma bata ganinsu saboda fuskarta a rufe take.
Har suka shiga aka ajiye ta a kan bakin gado nan kowa ya fita aka barta da baiwarta guda d'aya.
A ka'ida bayan an daura mata aure akwai wasu bukukuwa daya kamata ayi agidan sarautar sai dai Abdulsamad ya turo a sanar da Magajiya akan kar ayi, tayi mamakin jin haka ta aika a tambayeshi dalili ganin al'adar gidance hakan.
Abdulsamad yace " Gani yai ba'a dade da yin taron suna ba shi bayasan almabazaranci."
Magajiya tayi dariya jin haka dan tasan lalai uzuri kawai yake nema na kar ayi amma wannan ai ba hujja bace, hakan kuma ya nuna mata lalai Sarki ba san auran yake ba da alama akwai wani abu a kasa ne.
Basira kam da yake mai san shiru ce zaman bai dameta ba.
Yau tana tashi baiwarta Ta sanar da ita zuwa gaida magajiya.
Batasan dalili ba sai dai tanajin sunan taji gabanta ya fadi, jiki a sanyaye ta fito suka nufi b'angaren Magajiya.
Bayan kowa ya zauna ita da ragowar matar nan ta gaidasu kowa na mata kallan wulakanci kallan wacce ba'aso.
Fitowar Magajiya yasa taga kowa ya nutsu, nan ta juya suka had'a ido kwarjini da cikar zati irin na Magajiya da isa da mulkinta yasa Basira tai saurin dauke ido, gabanta kuwa yaki daina faduwa, addu'a kawai ta shiga yi har Magajiya tazo ta zauna.
Basira ta d'ago suka kara hada ido, gani tai Magajiya ta mata alama da hannu, jiki a sanyaye ta isa gunta.
Magajiya cikib muryar rad'a tace "sau daya zan fada ki tsaya kiji dakyau, yau ya zama rana ta farko kuma ta karshe da zan juyo in ga idanuwanki a kaina banasan kallo."
Cikin inina tace "Tuba tuba nake."
Kowa ya gaida Magajiya sannan aka kawo abinci itakam dakyar ta ci kadab nan aka kawo musu ruwan zafi anmai had'a had'e, itakam Basira komai ya isheta a gun abincin ma da kyar taci ruwan zafi kam da kyar ta iya yin kurb'a d'aya.
Magajiya ta kalleta tace " shanyewa zakiyi ai."
Basira tai kasa dakai tace Ranki ya dade bana iyashan ruwan zafi tun ina karama."
Magajiya tai wani murmushi tace " inkinsha ya kasheki."
Basira gabanta na faduwa da tsoro gashi harga Allah batashan ruwan zafi dan tun tana yarinya datasha tai ta amai haka kuraje suka feso a bakinta tun daga nan aka hanata, an nemar mata magani amma ba'a dace ba sam.
Nan ta d'aga kofin ta fara sha kafin ta shanye kuwa sai amai ya feso, nan ta mike da sauri ta fita ta shiga kela amai kan kace me kuraje sun cika bakinta.
Tsoro ya kama Magajiya gashi ranar kwanan Basira ne, ya zatai in Mai Martaba ya tambayeta dalilin hakan???????
[truncated by WhatsApp]
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼♂*
_Alhamdulila an gama *Nayi Nadama* da *Hamal* Allah ya kara Baseera (Ameen) ni da ragowa 'yan kungiyar Haske na muku bangajiya, Allah ya kare mana ku😍_
*5*
Ganin yanda takeyi yasa Magajiya tace a maidata b'angarenta, nan kowa ya mike ya fita sakamakon sallamarsu da tai.
Suna fita ta aika a kira mata yayanta Hisham, bai dade ba ya shigo nan ta sanar dashi komai sannan ta d'aura da cewa " yanzu in Mai Martaba ya tambayeta ta fadamai tirsasata nai zaiyi zargin wani abu kasan halinsa sarai."
Hisham yai shiru sannan ya ce " bari na kira mai magani ya dubata."
Wani mugun kallo ta bugamai wanda yasa yace " tuba nake ashe fa babu namijin da ya isa shiga b'angaren matan sarki ba tare da izini ba ko an sanshi ba."
Kanta ta d'auke daga inda yake tace " Ka fad'ama Turaki ya tambayar mana kaninsa ko akwai maganin da zai warkar da ciwon tunda naga kanin nasa yasan kan magani."
Nan ya amsa da to sannan ta kara kallansa zatai magana yai saurin cewa "na fahimci komai kinaso kice shi Turakin ya rike maganar a sirri."
Murmusawa tai kad'an sannan ta juya kai.
Hisham ya mike ya fito yana fita waje yai d'an kwafa tare da kallan inda ya fito sannan yai gaba.
Basira kam kwanciya tai ta shiga bargo saboda sanyin dake ratsata itakam batasan gidan nan sam ita duk rayuwarma ba dadi take mata ba inta itace har gwara can inda ta fara zama akan nan dan a kalla a can gidan bayi insuna hira suna sata dariya amma nan kam tanaji tunda ta shigo haryau batai dariya ba.
Tana nan kwance aka aiko mata da magani, ko kallan maganin batai ba dan itakam ta sab ciwonta inta kwana washe gari zai baje.
Bayan tayi isha'i ne wasu bayi suka shigo suka tsaya a inda take, babbar cikinsu wacce suka zauna da ita a can ne, ta matso kusa da Basira tace "Ranki ya dade wanka zaki tashi kiyi."
Basira batai musu ba ta mike saboda a can an sanar da ita yin musu laifi ne kuma yana jawo a rage ganin girmanta.
Ban d'aki ta wuce, ruwan zafi ne aka saka a katan baho an saka abubuwan kanshi kala kala, kina shiga b'an d'aki wani dadad'an kamshi ne zai bugeki, nan ta sata a ruwan zafin.
Bayan sun gama wankan ne suka bata wasu kaya masu kyaubta saka sannan wannan matar ta miko mata wani ruwa a kofi ba musu ta amsa ta shanyi, maganin ba dadi bata koma san dame akayishi ba sai dai tasan akwai zuma a ciki.
Tana gama shiryawa wata mata ta shigo mai d'an jiki haka, tana shigowa suka gaisheta jin suna cewa Jakadiya yasa ta fahimci wacece.
Jakadiya ta kalleta sannan ta gaisheta tace "Ranki ya dade muje ko?"
Basira batai musu ha tabi bayanta.
Sun d'anyi tafiya kad'an kafin su shiga wani b'angare, sosai an tsara b'angaren gashi kato ita da tana tunanin b'angaren Magajiya yafi kyau sai dai yau ta gane wannan yafi, ga girma ga kyau,kofar wani d'aki suka isa sannan Jakadiya ta kwankwasa, daga ciki akace shigo.
Jakadiya ta kalli Basira nan Basira ta shiga dan ta gane hakan ake nufi.
Katon d'aki ne sosai ganinsa yasa tai saurin maida kanta kasa, murmushi ya saki sannan yace " Amarya karaso mana."
A hankali Basira ta karasa inda yake ta tsugunna nesa dashi sannan tace "Barka da dare."
Alama ya mata da hannu akan ta matso kusa dashi, idanu ta d'an zaro kad'an tana tsoron kar ta matsa ya kula da bakinta da ya ke ciki da kuraje har kan d'an leb'enta.
Ganin yanda yake kallanta yasa ta matsa kadan, hannu ya kara nuna mata akan ta kara matsowa, Basira ta rasa yadda zatai a hankali ta matsa sai dai ta sunkuyar da kanta.
Abdulsamad yasa hannu ya jawota kusa dashi yace " bakiga me ke gabana bane?"
Sai a lokacin ta kalli gun, abincinsa ne a gun da 'ya'yan itatuwa.
Ya kalleta yace "Zubamin."
D'agowa tai ta kalleshi wanda hakan yasa ya kalli bakinta, mamaki ne ya kamashi yace "Menene hakan a bakinki?"
Da sauri ta rufe bakin, matsowa yai ya fizge hannuta sannan ya ce bud'e bakinki, tsoro ne ya kamata dan Allah ya bashi kwarjini, bud'ewa tai cikin tsoro.
Idanunshi taga sun canza cikin fada yace "meye hakan?me ya faru da ke? Ai sanda kike can ba haka kike ba."
Bakinta ne ya fara rawa, cikin tsoro tace "banashan ruwan zafi ne sai dazu tsautsayi yasa nasha na dauka na warke."
Kallanta yau cikin kokwanto da sauri tace "tun ina karama na daina sha sam na dauka na daina."
Ta dauka zaiyi fada sai taji yace " kidinga kula yanzu bari nasa a samo miki magani."
Kai ta girgiza tace " ai gobe zai warke."
Jakadiya wacce ke makale a kofa ta saka kunne tana jin komai da sauri ta juya ta fara tafiya cikin sauri kamar zata kifa.
Shikam Sarki daga wannan matsowa ya shiga wani al'amarin daban ya manta da abinci......Lol!
Jakadiya kam bata tsaya ba sai a b'angaren Magajiya tana isa ta nemi izini ta shiga.
Zubewa tai a kusa da Magajiya nan ta zayyane mata komai.
Murmushi Magajiya tai tace "da alama tanada hankali."
Jakadiya tace "nima na kuka da hakan."
Magajiya tace " ya ya? Ya kusanceta?"
Jakadiya tsoro ya kamata itakam sam ta manta ma aiki biyu aka sata ta ji me zatace da kuma ko Sarki ya nemi Basira.
Kallanta Magajiya tai tace " menene?"
Yawo Jakadiya ta had'iya tasan halin Magajiya sarai ba tada kyau ko yayanta ba raga mai take ba hatta Sarki in ranta ya b'aci sai ta san yanda tai ta kona mai nasa ran ita kuwa ina ita ina yi mata laifi? Amma itakam tana ganin me zaisa Sarki ya kusanceta bayan ragowar Matan ma sai ya dade bai kusancesu ba?
Magajiya ta kafeta da ido.
Jakadiya ta saki murmushi tace "ina fa? Yana gama tambayarta yai kwanciyarsa dan ko abinci baicibama.
Magajiya ta saki wata bazawarar dariya tace " nikaina jikina yaban haka saboda Basira yarinyace bata wuce 16 zuwa 17 ba shi kuma na sanshi sarai bayasan kusantar yara ko ya auresu yafiso sai sun girma."
Jakadiya ta sake dariya tace"Ai Mai Martaba ke kadai ce a gabansa Hajiya Magajiya mahaifiyar Yarima Amdulmajid Magajin Sarki."
Kanta ta juya tana murmushin kasaita, nan Jakadiya ta mata sallama tai waje.
********
Magajiya ta yanke shawarar daina ba Basira shayin nan saboda taga abinda ya faru sannan taji Mai Martaba bai fara nemanta ba hakan yasa ta sa Hisham ya samo mata wani wanda ba sai a ruwan zafi ba, dan gwara a samo mata ta ajiye kafin Mai Martaba ya fara tunanin kusantarta.
Jakadiya kam bayan ta dawi ta tambayi wata baiwa wacce take ta hannun daman ta ce, ita ta bari a gun dama ta tafi kai gulma akan ko wani abu ya faru.
Baiwar ta fada mata ai tana tafiya akai abun.
Shiru Jakadiya tai tsoro fal ranta sai can tad'anyi tsaki tace "to ai ba abinda zai faru ma dan inaji Sarki Juya ne inba haka ba matansa nawa haryanzu ba haihuwa? Da ya kwanta dasu da kar ya kwanta duk d'aya ne."
Baiwar tace " wani juya kuma bayan Magajiya ta haihu."
Jakadiya tai dariya a ranta tace " sai dai a rainawa dolo hankali amma ni da nake zuwa gunta banga wani alamar ciki ba, wanda nake gani kuwa baimin kama da ciki ba sannan menene dalilin turani tafiya zuwa Masarautar Kano a daidai watan haihuwarta? Ni nasan akwai wata a kasa.
Murmushi tai a ranta, ganin komai ya zo mata daidai.
**********
_Bayan wata hudu_
Basira kam duk ta rasa me ke damunta bata iya cin abinci gashi shiru ba al'adarta sai dai bata kawo komai a ranta ba haka kuma tana kokarin yin komai daya kamata wanda hakan yasa ba wanda yai tunanin komai.
Sai dai a 'yan kwanakin nan ta fara zargin ko ciki ne ganin yanda cikinta yai tauri sannan ya dan fara tasawa kad'an.
Magajiya kam nasan Basira yanzu tunda taji abinda ya faru, haka zatai ta aika mata da abubuwa, itakam Basira har yanzu ta kasa sakar zuciyarta da matar.
Matsala ta fara faruwane daga sanda kanwar mahaifiyar Magajiya tai tattaki na ziyara ta kawoma 'yar yayarta, wanda a lokacin matan sarki duk suna zaune kwasar gaisuwa.
Kallo d'aya tama Basira tsoro ya kamata dan ta fada dashewa irin na masu cikin nan.
Ido ta kurama Basira wanda har tasan akwai matsala, da sauri Basira ta dauke idanta daga kan matar.
*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼♂*
_Where are u My Dear BillynAbdul? Here is ur special page, tnx for the care Tawan. Allah ya bar zumunci ya kareki daga sharrin masu sharri (Ameen)_
*6*
Suna fita Kanwar Mamanta wato Aunty Lami ta matso kusa da ita tare da cewa " Magajiya nikam waccan wacece?"
Ta fad'a tare da nuna inda Basira ta zauna, murmushi Magajiya tai tace "Ahhh Basira? Kema ta burgeki ne? Bansan meyasa ba amma yarinyar ta shiga raina."
Aunty Lami tai d'an shiru tana tunanin ta inda zata fara, can tace " amma dai ba matar Sarku bace ba ko?".
Had'e rai Magajiya tai tace " wace irin tambaya ce wannan? Baki ga kayan jikinta bane? Ko akwai masu sa kayan Sarki bayan matansa?"
Aunty Lami ta dafa kai, kanta na kasa tace "amma dai ba ciki ne da ita ba ko?"
Kallanta Magajiya tai cikin halin ko in kula ta girgiza kai cikin takaici sannan tace " da alama tsufa ya fara miki illa."
Lami ta d'ago ta kalli Magajiya tace " Magajiya wlh ba haka bane lalai ki binciki 'yar nan, kina me har ciki ya zauna a jikinta haka? Da alama ma cikin nan ya kai wata hudu in bai fi bama."
Kanta ta juya ba tare da ta bata amsa ba dan ta kula nema take kawai ta kona mata rai.
Lami ta kara matsowa tace " wlh Allah da gaske nake, Magajiya kinsan dai da yanda nake, indai naga mace da ciki ko wata d'aya ne sai na gane."
Tasan da wannan sarai sai dai tayaya zatace ciki bayan yarinyar haryanzu Sarki bai fara........
Tunaninta ne ya tsaya ta tuno sanda ita kanta waccan satin taga yanda tai haske har take tsokanarta akan lalai gidan sarauta ya amsheta ganin yanda take kyau haka.
Zumbur Magajiya ta mike cikin firgici ta shiga kwallama wata baiwarta kira, nan ta karaso da sauri.
Baiwar ta zube a kasa, Magajiya tace " jiku shirya zani b'angaren Basira."
Mamaki me ya kama baiwar dan tasan Magajiya bata zuwa b'angaren kowa hatta bangaren Mahaifiyar Sarki sai ta shafa watanni bata ko leka ba.
Basira kam tana dawowa daga gun Magajiya ta hau amai dan abincin dataci acan sam kawai dai ta tura ne amma bawai dan ranta yaso ba, kwanciya tai akan gado dan wani irin jiri takeji.
Mai kula da ita tana kusa da ita tana tambayarta akan ta kira mata mai magani na gidan?
Kai Basira ta jijiga zatai magana sai jin kirarin isowar Magajiya tayi ana yi a kofar ta.
Da sauri ta mike ta d'an gyara fuskarta sannan ta fito.
Magajiya ta gani a zaune tayi zama irin wanda ta saba, tun da ta taho Magajiya da Lami suka kura mata ido har kafarta ce ta hard'e ta kusa fad'uwa.
Da kyar ta karaso, Magajiya ta kalleta cikin dabara tace " ya akai? Bakyajin dadi ne?"
Kai ta girgiza alamar a'a, baiwar dake kula da ita ta matso ta zube a kasa tace " Magajiya dan Allah a kira mai bada magani ta duba Uwar gijiyata wlh ba lafiya ce ta isheta ba."
Gaban Magajiya ne yai wani wawan fad'uwa amma dayake isashiyace sai ta maze cikin gadara tace " je ki kirata."
Da sauri ta mike tai waje, Magajiya ta kalli Basira tace " na d'auke ki kamar kanwata ashe ke ba haka bane?"
Basira ta d'ago a hankali itakam tana tsoron matar nan, daurewa tai tace " ba wani abun damuwa bane kawai dai naci abinci dayawa ne a gunki."
Magajiya ta kafeta da ido, tsoro da fargaba ya cika mata ciki taf.
Suna zaune anan mai bada magani ta shigo.
Nan Magajiya ta bata umarnin duba Basira, hannunta ta kama ta bud'e tafin hannunta ta zuba musu ido, ta sake ta sannan ta bud'e idanunta na hago, nan ma ta saki ta sake bude na dama.
Tana gamawa ta zube a kasa tare da cewa " ina tayaki farin ciki yake Magajiya, babu wani gabanki ba wani bayanki, kece fitila wacce take haskaka gidan nan......"
Katseta Magajiya tai tace " ya isa ni fadamin meke damunta."
Mai magani tai murmushi tare da kara dukufar da kanta tace " Yarima Abdulmajid ya kusa samun kani ko kanwa ima tayaki murna Magajiya."
Ai ba Magajiya ba kowa na gun sai da ya zaro ido, itakam Basira kasa kawai tai da kanta.
Mamakin daya rufeni, gani nai Magajiya ta mata alama da hannu akan ta matso kusa da ita, nan ta taso ta iso, tana zuwa Magajiya ta jawota ta rungumeta tsam tace " Masha Allah! Lalai kinyi abin kwatance a wannan masarauta ba shakka ked'in ta dabance."
Basira kam addu'a kawai take dan gabanta sai fad'uwa yakeyi.
Magajiya ta saketa ta kalli Mai Magani tace " ki biyoni ki amshi tukwicinki mai tsoka.
Nan ta mike ta fito.
Abinda zai baka mamaki kan kace me? Labari har ya cika gidan, Jakadiyar Sarki kam tana jin wannan labarin ta garzayo gun Basira sai data tabbatar sannan ta tafi gunsa yana fada ta sa a sanar mai.
Magajiya kam tana shiga d'akinta ta dafa kanta wanda ke sarawa, idanunta sunyi jaa sosai lalai dabadan tun tana karama an hanata kuka ba lalai yau da sai tayi, sai dai itakam batasan kuka ba, ko da mahaifinta ya rasu batai ba.
Lami ta kalla tace a kira Ya Hisham.
Nan Lami tai waje da sauri ta aika a kirashi.
Hisham na fada ya samu sakon kanwarsa da sauri ya mike ya nemi izini ya taho, a waje yaga mai magani hakan yasa yai tunanin ko batada lafiya ne.
Murmushi yai sannan ya shiga, a tsaye ya ganta ta juya baya.
Nan ya canza fuska cikin kalar damuwa ya matso kusa da ita ya zauna yace " Magajiya lafiya?"
Juyowa tai cikin takaici ta zauna a gun zamanta sannan ta kalleshi tace " ciki gareta."
Cikin rashin fahimta yace " wa kenan?"
Lami tai caraf tace " Basira Amaryar Sarki."
Tashin hankali Hisham ya mike da sauri cikin tsananin mamaki da tsoro yace " ban gane ba? Magajiya ba kince bai kusanceta ba?"
Sosai ya damu dan babban burinsa bai wuce yaga d'ansa akan mulki ba, Magajiya ta runtse ido cikin takaici tace Jakadiya ce ta fadamin.
Shiru sukai kafin daga bisani Hisham yace " ya zama dole a zubda cikin kafin yai kwari."
Magajiya tai shiru sannan tace a kira mata mai magani.
Mai Magani ta shigo cikin farin ciki, gaban Magajiya ta tsugunna.
Magajiya ta kalleta yace " shekararki nawa kina aiki a gidan nan?"
Cikin zumud'i tace "40."
Magajiya tai murmushi tace " muhallin zama fa?"
Tace " a wani d'an daki muke takura nida mijina da 'ya'yana."
Magajiya ta kalleta tace " Zubar dashi."
D'agowa tai da sauri tace " me fa?"
Hisham yace " ke kika dubo tana da ciki hakkinki ne kisan yanda kikai kika zubar dashi, in har kinasan ki cigaba da aikinki kuma kinasan muhallin zama mai kyau ke da iyalanki."
Cikin tsoro tace " Waziri tuba nake amma tayaya zan zubar da kwan Sarki?"
Hisham yace " ruwanki ne ki zubar ruwanki ne ki barshi sai dai 'ya'yanki ina tabbatar miki zasu fuskanci gararin rayuwa dan ko aure basu isa suyi ba in har sun zauna da ransu kenan."
Cikin tsananin tashin hankali ta d'ago ta kalli Hisham.
Lami tace " kinaso mahaifiyarki dake kwance ba lafiya ta rasa inda zata zauna? Ke kuma ki rasa sana'arki?"
Kai ta shiga girgizawa, Lamibta cigaba " in har kinaso bakin ciki ya kashe mahaifiyarki kar kiyi abinda aka saki."
Ganin ta rikice tana roko yasa Magajiya tace " kwana bakwai, kwana bakwai kacal na baki ki tabbatar kin kawon magani mai karfin da zai tafi da cikin, kar kuma kiyi tunanin bazan gane ba dan sai nasa ankai gun mai maganni ya tabbatar da hakan."
Kanta ta shiga d'agawa nan aka sallameta.
Tana fita Lami tace " zatabi umarnin mu?"
Magajiya ta juya kai batace komai ba.
Magajiya tasa a nemo Jakadiya sai dai sama ko kasa an nemeta an rasa bat ta bata dan bata gidan sam.
**********
Sarki kam yana tasowa daga fada yasa a kiramai Basira, dan da shi yaso zuwa ma sai Barde yace in yaje za'ai tunanin yafi san Basira ne wanda hakan zaisa matan su fara tsanarta.
Farincikinsa ma yau kwanan ta ne, tunda yai sallah ya kasa tsaye ya kasa zaune sai jeka ka dawo yakeyi, yana nan a tsaye har ta iso.
Tana shigowa tun bata karasa ciga cikin d'akin ba ya karaso ya rungume ta tsam wani irin nishadi da jin dadi na ratsashi.
Bayan ta zauna ya sa hannunsa akan cikinta cikin tsananin murna, itakam kanta na kasa tana murmushi, cikin tsananin farin ciki yace " in Allah ya saukeki lafiya in har Mace kika haifa zan sa mata suna Fatima Zahra wato 'yar Manzon Allah in har kuma Namiji ne zan sa mai *ABU TURAB*."
Cikin muryarta mai sanyi tace " Har ka zabi suna?"
Yana murmushi yace " sunayen dana fi so kenan haka kuma fatana in ga na saka wad'an nan sunayen."
Murmushi tai sannan tace " meyasa baka sama d'an ka na farko ba?"
Yace " ai shi magaji ne shiyasa na samai Abdulmajid, tun daga kan mahaifinmu ake sa ma Magaji Abdul a gaba."
Murmushi tai sannan ta kara sadda kanta kasa.
Dadi ne ke ratsashi hakan yasa ya kara jawota jikinsa lalai baiji haka ba sanda Magajiya zata haihu, yau jinsa yake daban lalai yana cikin farin ciki.
_Hmmm Allah yasa farincikin ya d'ore_
*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼♂*
*7*
Magajiya tasa Aunty Lami akan duk wani magani datasani ko wani mai bada magani data sani ta je ta amso mata maganin da zai kawar da wannan cikin, babu makawa sai ta sa cikin nan ya bi shada dan itakam bataga wanda ya isa ya haihu ba a gidan, dan kuwa bazata tab'a iya jurar ganin yaro na yawo a gidan ba a matsayin d'an wani ba, ba nata ba.
Basira tana kwance a d'aki tun safe ta kasa cin abinci, sallamar baiwar ta ce wato lantana yasa ta mike zaune, Lantana ta karaso ta gaidata sannan tace " Ranki ya dade Magajiya ta aiko miki da magani da kuma abinci."
Basira tace " nakoshi Lantana sam banajin cin abinci."
Lantana ta matso tace " Kinsan bazataji dadi ba in taji bakici ba kinga na jiya ma data aiko bakici ba sai dataji ba dadi."
Basira tace " to ke kici mana?"
Idanu Lantana ta zaro tace " so kike a yanken hukunci mai karfi? Magajiya ce fa ba wani ba."
Zata sake magana sai ga Aunty Lami ta shigo ba ko neman izini, tana shigowa ta matso kusa da Basira fuskarta a sake aosai tace " haba 'yata tashi ki daure kici mana, ko so kike hankalin Mai Martaba ya tashi?"
Da sauri Basira ta jijiga kai alamar a'a, Aunty Lami tasa aka kawo abincin da kanta ta bata sai dataga taci sosai sannan ta bata maganin da aka kirashi da sunan maganin dazaisa taji karfin jikinta."
Ta dade a zaune ganin Basira ma baccinta take shara yasa ta fita daga d'akin.
*******
Zaune take gaban Magajiya wacce itama shiru tai tana tunani, can Aunty Lami tace " amma Mai maganin nan na kan tudu ya rainamin hankali, sai fa daya tabbatarmin cikin minti 15 zata fara fitsari akai akai in har naga haka inbata kwana d'aya cikin zai zube dan dama nacene ya bada wanda zai dan d'au lokaci kafin cikin ya zube kar a gane."
Magajiya tai tsaki tace " mai Yaya yakeyi?"
Da sauri Lami tace "ya tafi Daura anso wani maganin."
Magajiya tace " itafa matar nan ga gidan nan?"
Lami tace " ita kuma tace a bata zuwa gobe."
Magajiya tai d'antsaki tace nifa banasan jan abin nan dan ji nake kamar akan bushiya nake a zaune."
Lami ta matso tace " karki damu 'yata....."
Wani kallo Magajiya ta mata wanda yasa tai shiru, kanta Magajiya ta juya gefe sannan tace "kayan abincin dana aika ya karene?"
Lami ta d'aga kai, Magajiya tace " zan aika da wani amma sai hankalina ya dawo jikina." dan dama ta sani da zarar taji Lami ta fara cewa 'yata tasan abu take nema.
Basira kam ta fahimci Magajiya ce kawai ke santa a matan sarki dan su kiri kiri suke nuna mata kishin cikin nan, dan haka duk abinda aka aiko mata daga bangaren Magajiya bata wani kokonto take ci.
Mahaifiyar Sarki wacce ta tsufa itama bata gazawa gun aikoma Basira kayan marmari.
Shikam gogan wato Sarki kullum sai yayi aike sau uku akan a dubo lafiyarta, wannan al'amari ya kara dugunguza hankalin Magajiya dan kuwa an sanar da ita, to ita ke yasa sanda akace tana da ciki baya mata wannan aiken? Tsanar Basira da abinda ke jikinta ya kara tsananta a ran Magajiya.
Yayanta ya dawo d'auke da magunguna kala kala nan ya zauna yama Lami bayanin komai, nan ita kuma ta shiga yin hidimominta.
A ranar da aka fara bata maganin an saka mata shine a cikin miyar kubewa d'anya, san tuwo da takeyi yasa taci tuwon nan sosai, sai dai me? Tunda ta kwanta bacci ta ke juyi a kan gado, tsananin ciwo da mararta keyi yasa tai ta murkusus, da sauri Lantana ta fita ta karasa b'angaren Sarki nan ta aika a sanar mai.
Ranar kwanan matarsa ce ta biyu, ai ko fadamata baiyiba yai waje da sauri, sun iso bangaren Basira lokacin ciwon ya mata yawa dan ta fad'o ma daga kan gado, jini ne ya fara zubo mata wanda hakan yasa hankalinta yai tsananin tashi.
Sai dai tsananin ciwon da takeji yasa ta kasa magana, shigowar Sarki ne yasa ta daurw ta fara kokarin mekewa, da sauri ya karaso ya rungumota jikinsa, hawayene kawai ke zubo mata a hankali take cewa "shikenan cikin nan ya tafi shikenan nikam na baka kunya...."
Hannu yasa da sauri ya toshe mata bakinta sannan ya kara jawota jikinsa, d'aya daga cikin bayin Basira wacce Magajiya ce ta turota b'angaren dan kai mata rahoto.
Da sauri ta zame jikinta tai bangaren Magajiya.
Tana shiga ta zayannema Lami halin da ake ciki, da sauri Lami ta shiga ciki ta sanar da ita, ajiyar zuciya Magajiya tai tace " yau da alama zan samu bacci mai dadi."
Lami ta saki dariya tace " nikuma gobe za'a sallameni ko?"
Kanta ta juya gefe bata amsa mata ba sai murmushin jin dadi data saki.
Basira kam tana jikin Sarki ganin ciwon ya lafa yasa ya kira Lantana yace ta taimaka mata ta gyara jikinta.
Basira tana mikewa Lantana taga yanda jini ya zuba sosai, salati ta shiga yi, Sarki ya kalli gun dan harshima ya b'atashi, Lantana ya kalla ya mata alama da ido akan tai shiru hakan yasa tai shiru itakam Basira hawaye kawai take yi.
Shiru yai bayan sun shiga b'and'aki, ji yai idanunsa na neman canzawa, kallan jinin yai yanajin wani abu na tasomai na bakin ciki, ba shakka yasa rai sosai akan cikin nan, yana nan a zaune Lantana ta fito ta debi kaya ta koma.
Can sai gasu sun fito, kuka sosai Basira takeyi wai tana bashi hakuri, mikewa yai yaje kusa da ita ya jawota jikinsa yace " karki damu Allah zai bamu wani."
Shiru tai batace komai ba, ya daure yai murmushi yace " kishirya gobe insa a maidake gida gun Amadu inkin warware sai insa azo a d'aukeki.
Kallansa tai cikin mamaki tace " akan me?sakata kai?"
Dariya yai sannan yace " wani irin saki kuma? Ai ba saki a auranmu cewa nai dai kije inda zaki samu kulawa sosai sannan za'a dinga d'ebe miki kewa, sai ku shirya ku tafi da Lantana."
Murmushi tai sannan ta sunkuyar da kanta kasa.
Magajiya kam an tabbatar mata ciki ya zube shine ma dalilin tafiyarta gida, nan ta aiko mata da kaya kala kala wai ta kai gida, masu murna nayi masu bakin ciki na yi na tafiyar cikin nan.
Sarki ya cika musu mota da kayan abinci ya kuma bata kudi sosai yace " zai zo sai dai bai san yaushe ba."
Sun shirya sun kama hanya.
**********
Matar Amadu kam bata yarda cikin nan ya tafi ba ita kanta basira ganin cikinta na kara tasowa yasa tasan cikin nanan, sai dai ba yanda zatai ta sanar da Sarki tunda dai ba salula babu kuma wanda zata aika, sai dai ta zauna zuba ido akan sanda zai zo.
Matar Amadu dashi Amadun tunda sukaga cikin Basira nanan suka d'aura himma sosai na kula da ita hakama Lantana sosai take kula da Basira.
_Wannan kenan_
( _Dan Allah kuyi hakuri da wannan wlh yau abubuwa ne suka cud'emin da kyar na samu nai wannan, Nagode kwarai_)
*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*8*
Shiru shiru ba sarki ba labarinsa wanda hakan ya kara d'agama Amadu rai gashi lokacin Basira cikinta yakai wata 9, ganin kar Basira ta haihu ba tare da sarki yasan komai ba yasa Amadu ya shirya tsaf ya nufi garin Zariya a akuri kura.
Sai yamma liss suka isa, gidan Sarki ya wuce.
A b'angaren Mai Martaba kuwa aiyuwa sun cab'e mai a fada wanda ya rasa yanda zaiyi, yaso ya aika aje q dubo Basira sai dai Barde ya bashi shawara akan ya kara jinkirtawa ganin kar a gane tsananin san da yake mata wanda kan iya jawo mata tsangwama in ta dawo.
Yau ma kamar kullum yana zaune a fada ana ta fama kawo kara yana hukunci, wasu kuma neman taimako suka zo yi wasu kuma sulhu da dai sauransu, ganin yamma tayi sosai yasa ya sallami kowa akan a dawo gobe, shigowar bafadansa ne yasa ya kalleshi, bafadan ya sanar dashi zuwan Abokin nasa kuma sirikinsa, nan ya bashi izini da sauri.
Amadu ya shigo kansa na kasa sai daya gaidashi tukunna, Sarki ya nemi a basu guri, suna fita ya kalli Amadu yace " Amadu ka jini shiru ko? Wlh al'amura ne suka c'abe min gaba d'aya.
Amadu yace bakomai sannan ya d'ura da cewa " dama zuwa nai na sanar dakai Basira ta shiga watan haihuwa."
Mamaki ne ya kamashi wanda sai da ya bayanna a kan fuskarsa yace "Haihuwa kamar ya?"
Amadu yai murmushi yace "ai cikin bai zube ba."
Mikewa yaga Sarki yayi da sauri ya shiga matse hannayensa yama rasa mai zaiyi can ya matso jusa da Amadu ya d'agashi tsaye ya rungumeshi kam yace " Basira ta kusa haihuwa kenan?"
Amadu yai murmushi yace "kwarai kuwa dan tama shiga watan, haihuwa yau ko gobe, nima sai da Matata ta sanar dani ta kula Basira ta kusa haihuwa sannan nace to ya zama dole yanzu kam inzo in sanar dakai."
Abin mamaki kwalla ne ya taru a idan sarki hannu ya d'aga ya shiga godema Allah.
Abin mamaki fadawa da bayinsa dake waje nan a ka fara zamewa kadan kadan an tafi kai gulma (lol.....)
Sarki yace "aikam yanzu dakai zamu tafi muje in d'aukota."
Amadu yai dariya yace " kai da kake fama da aiki sai dai ka tura kawai a d'aukota."
Shiru yai yana tunani can yace " ka kwana anan zuwa gobe zansan yanda za'ai."
Magajiya na zaune zance ya zo mata, tashin hankalin da ba'a kwatantashi, ba shakka tashin hankalin data shiga ya wuce duk yanda mai karatu zaiyi tunani tana tsaye jitau jiri ma na neman d'ebanta, Hisham kam ba kanta dan kuwa magana ra baci, tsantsan tashin hankalin da ya shiga ya wuce misali.
Gun Magajiya ya taho a sukwane, sunyi jugum jugum su biyu a d'aki, can Magajiya tai d'an ajiyar zuciya sannan ta kalli Hisham tace "duk laifinka ne, kaine ka tabbatarmin maganin nan ba karya ko wasa a ciki."
Hisham yai shiru can yace " duk ba wannan bane abinyi yanda zamuyi yanzu shine abinyi."
Magajiya tai shiru tana tunani, Hisham yace " bafa zai yiwu mu bari a haifi yaron nan ba in ma mace ce da sauki to amma ina muka sani?"
Magajiya cikin kufula tace " aikin gama ai ya riga ya gama kanaji ance ta shiga watan haihuwa?"
Da sauri Hisham yace " to sai me? Ai ko haifarsa tai sai mu halakashi."
Kura mai ido tai can tace " kisa kake so muyi kenan?"
Hisham ya share zufa sannan yace " ai da din ma kisa ne, in kuma kina ganin ba wani abu to shikenan kinfi kowa sanin Abdulsamad haka kawai bazai ba Abdulmajid mulki ba dan yana na fari ko yana d'anki ba."
Shiru tai tana tunani kafin tace " banasan irin wannan maganar ka fita ka bani guri in na gama yanke hukunci zan kiraka."
Mikewa yai ya fita rai a b'ace.
Magajiya ta dade tana tunani kafin daga bisanj ta mike ta fito.
B'angaren Sarki ta nufa, yana turakarsa banda farinciki ba abinda yakeyi, neman izini da akai akan isowar Magajiya yasa gyadan had'iye abinda ke fuskarsa.
Magajiya ta shigo cikin tafiyarta ta isa,zama tai a inda ta saba zama sannan ta kalleshi tace " ina cikin tsananin farin ciki Mai Martaba, nasan ban kaika ba amma natabbata ina bayanka."
Murmushi ne ya bayyana a fuskarsa na tsantsan farinciki yace " nagode Magajiya."
Murmushi itana tai sannan tace " ka gode dame? Abinda za'a haifa kamar d'ana ko 'yata ne zan kula da abinda aka haifa kamar nice na haifesu."
Kallanta Sarki yai sai dai yau idanunsa ya rufe har ransa yake jin dadin maganar ta.
Magajiya ganin ta kamo lagonsa ta cigaba " shine nake tunanin kai ka zauna saboda hidimar dake gabanka inyaso waziri sai yaje ya taho da ita."
Sarki ya kalleta zaiyi magana tace " menene amfanin waziri? Dole ne ya wakilceka ko ya taimaka maka alokacin da kai kake wani abun, banaso mutane su fara tunanin kafinsan matarka a kan talakawa da mutanenka."
Shiru yai yana tunani ba shakka hakan data fa'a shine gaskiya, ya kalleta yace "haka ne sai dai bakya tunanin Hishan zaiji ba dadi ganin kishiyarki ce?"
Kai ta jinjina tace " zaiji mana, sai dai ai a karkashinka yake, sannan in munaso mu girmama Basira shi din ya kamata a tura."
Sosak Sarki ya gamsu haka kuma ya amince da wannan shawara.
Bayan Magajiya ta dawo b'angarenta tasa aka kira Hisham, ta kalleshi tace " gobe ka shirya kai zaka taho da Basira sai dai inaso ka sani banaso inga Basira a gidan nan daga ita har abinda zata haifa."
Tana gama fadar haka ta sallami Hisham ba tare da ta jira abinda zai ce ba.
**********
Washegari kuwa da sassafe Mai Martaba yasa suka kama hanya, mota biyu sukau saboda in an tashi d'aukota yace a taho da Matar Amadu saboda ta kula da ita inta sauka, ganin ita ta gidace ba wai dan baza'a bata kulawa a gidan nasa ba.
A can garin Katsina kuwa Basira tun dare take nakuda mai azabar wahala, banda juyi ba abinda takeyi duk sun jigata daga ita har abinda ke cikinta har matar Amadu, sai asuba ta sauka, ta haifi d'anta santalale mai tsananin kama da Mai Martaba, duk da dai ance jariri ba'a gane kamarsa sai dai wannan kam kallo d'aya zakamai ka san ba Basira bace.
Tana haihuwa wani nannauyan bacci yai gaba da ita, Matar Amadu ta gyara d'an tas sannan ta gyara gun, ganin yaron ya tafi bacci yasa ta zo ta tashi Basira ta gyara ta, sannan tace ta koma ta kwanta bayan ta d'anci dumame.
Shiru Matar Amadu tai tana tunani, ga Amadu bai dawo ba gashi Basira ta sauka, ganin zaman ba shine mafita ba yasa ta mike ta fito tai gidan yayanta dake nan kasan layinsu.
Babban d'an yayan ta samu tace maza yaje ya samu motar da zatai Zariya ya hau, ta bashi sako akan yaje gidan Sarki ya nemi Amadu in bai ganshi ba yace a sanar ma Sarki Basira ta sauka ta haifi Namiji.
Sai dataga ya hau motar sannan ta juyo gida, kazarta ta kama ta yanka ta shiga gyarawa, Lantana na aikin gida.
Rashin sani sam itabatai zaton Amadu na hanya ba.
Su Amadu sun iso wajen azahar nan ya tarar da abin farin ciki wanda ya kasance na babban bakin ciki ga Hisham, sai ma da aka miko mai yaron yana bacci ganin katon yaro nau kama da AbdulSamad yasa hankalin Hisham ya kara tashi, jiyai kamar ya shake yaran ya mutu.
Matar Amadu ce ta kawo musu ruwa da abinci ganin yanda Hishan yake kallan jaririn ne yasa ta tsorata ba shakka kana gani kasan kallo ne na saka mugun abu a rai.
Hisham jin motsin ajiye tire yasa yai saurin kallanta sannan ya canza fuska, itakam tana ajiye wa ta juya tai ciki, zuciyarta fal da tunani.
Bayan yaci abinci ne yace zaije ya samu hakimin nan garin ya kwana a gunsa zuwa gobe tunda bai kamata su kama hanya yau ba.
*******
A can kuwa Sani ya isa Zariya ya sauka ya gangara masarauta, a bakin kofar shiga dogarai suka tambayeshi inda zashi, nan ya sanar dasu gun Kawu Amadu yazo wato yayan Basira wanda yazo jiya, nan suka sanar dashi ai ya koma katsina yau, jiki a sanyaye ya juya, har ya d'anyi nisa sai kuma ya dawo yace " ku sanar da Mai Martaba dama Yafendo ce ta sauka yau da asuba, an samu d'a namiji."
Kallan mamaki dogaran sukamai suka ce Yafendo?wacce kenan?"
Sani cikin halin ko in kula yace "Basira."
Kallan juna dogaran sukai sannan suka kalleshi sukace " da gaske ta haihu?"
Kai ya d'aga alamar eh, gani yai sunyi ciki da sauri ko kulashi basu sake yi ba, tsayawa yai yana mamaki, ganin ba kowa a kofar shikam ya shige ciki.
B'angaren Magajiya sukai tana zaune a kilisarta dan ko abinci ta kasa ci, bayan sun nemi izini ne suka shiga ciki suka zube a kasa suka kwashe komai suka sanar da ita, zumbur ta mike cikin tashin hankali sai dai ganin su waye a gabanta yasa ta daure ta saki fara'a tace " Alhamdulila kun sanar da Sarki?"
Sukace "munje baya fada shiyasa muka garzayo nan."
Tace " dakyau ba sai kun fadamai ba bari ni na sanar dashi da kaina, ko kuma dukanmu kar mu fadamai sai dai kawai mu bari in ta dawo gobe ya ganta da d'a lalai zai sha mamaki."
Kai suka jinjina alamar gamsuwa sannan ta basu tukuici ta sallamesu.
Shikam Sani ciki kawai yai ta shiga har ya ganshi a wajen wasu mutane, a tsatsaye a waje da alama magana mai nahimmanci suke tattaunawa kuma yaga duk wani mutum akewa maganar.
Gun ya karasa ya gaishesu, kallansa sukai cikin mamaki,Barde wanda ke tsaye ya kalleshi yace " Lafiya?"
Sani ya kara sanar dashi yanda ya fadama dogaran.
Barde cikin zakuwa yace " ka tabbata?"
Yace " sosai nidin ai d'an yayar matar Kawo Amadun ne."
Barde ya kama hannunsa cikin sauri sukai gaba.
Gun Mai Martaba ya kaishe yace ya tsaya a waje shi kuma ya shiga ya sanar da Sarki.
Sarki kam wani irin dadi ne yake ziyartarsa ji yake kamar zaiyi me dan dadi, nan ya bada umarni a ba Sani tukuici mai tsoka.
Magajiya ta rasa abinda zatai da sauri ta aika a kira mata Inna Lami(sry zamusa Inna Lami tunda a lokacin ba Aunty.)
Lami tana shigowa ta tsinci labari a sama yana yawo akan haihuwar Basira.
Cikin hanzari ta juya tai waje, gun malaminta ta nufa ta sanar dashi komai.
Kallanta yai sannan yace " yanzu me kikeso ayi?"
Tace "an riga an haifeshi ni kuma ban taba kisa ba kuma itama Magajiya nasan bazataso muyi kisa ba dan haka so nake a nakasar dashi.
Kallanta yai yace" Nakasa wace iri?"
Tace waccece zata hana mutum yai tunanin hawa mulki? So nake a nakasar dashi a yau yanda in sukazo gobe za'a dauka a haka aka haifeshi."
Dariya yai sannan yace " na baki ko na ido? Sune babban nakasu da zasuma mutum."
Lami tai shiru can tace " ido, a hanashi gani yanda ko uwarsa bazai sani ba balle ubansa sai dai muryarsu, tunda munyi iya yinmu akan karyazo duniya amma sai da ya zo."
Tana zaune anan ya gama abubuwansa sannan ya bata wani yace ta binne, nan ta bashi sallama ta mike ta fito cikin farin ciki.
Sai daya gama komai sannan ta shiga gun Magajiya ta sanar da ita.
Magajiya ta kalleta tace "kina ganin zai kama?"
Tace kwarai kuwa kuma nina fada miki gobe ba ido zaizo gidan nan.
Ajiyar zuciya Magajiya tai cikin damuwa......
_Hmmmmmm_
*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*9*
Sosai Barde ya ba Sani tukuici sannan ya kamo hanya.
Shikam Hisham tun da suka isa masauki ya kasa zaune ya kasa tsaye can ya gaji ya koma ya zauna tare da bubuga 'yatsarsa a guda d'aya a kasa alamar yana cikin dogon nazari ba shakka dolene ya d'au mataki sai dai ta ina?kuma ta yaya? Ganin yaron ma yasa hankalinsa ya kara tashi matuka, ba shakka in har Mai Martaba yaga yaran nan to fa su tasu ta kare, tunda shi jininsa ne.
In mun tafi a hanya in jefar dasu a tsakiyar daji ne? Abinda ya fara fad'o mai kenan a zuciya, kai ya girgiza da sauri yace in nai haka kuma ai zasu koma gidan a hankali tunda da kafarsu kuma zasu iya samun taimako.
Insa a je gidan a kashe su yau? Kai ya girgiza yace na tabbata in nai haka sai an zargeni tunda dai ina garin.
Idanunsa ne ya kada sosai na bakin ciki, gashi dare yayi bare ya tafo daura gun mai magani.
Ko guba zan....... Kai ya kada da sauri alamar rashin gamsuwa, idanunsa ya rufe cikin bakin ciki, jiyai daga wajen d'akin da yake wasu na hira "wlh jiya ai munga abin mamaki, tas fa wutar nan ta cinye gidan daga mata da mijin har yaranta biyu ba wanda ya tsira."
Zumbur ya mike yace wuta.....Wani murmushi ya saki na gamsuwa da shawarar data zo mai a yanzu.
Turawa yai a kiramai wani bawansa wanda ya sa aka bashi matsayi a gidan sarauta saboda tsabar yardar da yamai, bawa ne wanda baya ko tambayarsa dalili in ya saka shi abu, baya taba musa mai ba kuma ya neman sanin dalilinsa na sashi abun.
Yana zuwa ya jashi cikin kuryar d'aki ya sa bakinsa a saitin kunnensa alamar rad'a ya fara mai bayani wanda ni da nake tsaye a gun ma bansan mai ake cewa ba.
Itakam Basira da Babynta bayan Magrib suna kwance akan gado Lantana na kasa tana ninke kayan data wanke tana ta shirya musu jaka matar Yayanta ta shigo.
Basira na ganinta ta fara kokarin mikewa, da saurin tace " koma ki kwanta."
Itakam Basira mikewa tai ta zauna, kallan Lantana matar tai tace "Lantana d'an bamu guri."
Da sauri Lantana ta mike tai waje.
Kallan Basira tai sannan tace " Basira."
Yanda ta kirata yasa Basira ta tattara hankalinta gaba d'aya kanta.
Ta cigaba " Wani irin zama kukeyi da Yayar wanda yazo?"
Basira tace " zaman mutunci mukeyi."
Ido ta kura mata sannan tace " gaskiya nakeso ki fadamin."
Basira taja numfashi sannan tace " wlh da gaske nake tana kula dani nidin ce zuciyata taki yarda da ita."
Meyasa? Abinda taji ta fada kenan.
Basira tai shiru kafin can tace " gabana fad'uwa yakeyi in na ganta."
Shiru tai sannan tace " ki nutsu kiji mai zance, tun bayan zuwansu hankalina yaki kwanciya da yanda naga yayanta yana kallan yaron nan, kallo ne na tsana tsantsa."
Basira tai murmushi tace " kedai kila baki fahimceshi bane amma......"
Katseta tai da cewa " Basira zaman gidan sarauta ko ba'a fada ba kasan ba wai zama bane wanda kowa zai soka, bare ke da kika haihu, ki kasance mai hakuri sannan kar ki bari ko kad'an a cutar miki da d'anki."
Murmushi Basira tai tace " ki daina damuwa ba komai insha Allah."
Sun dade a d'akin kafin ta mata sai da safe ta fito.
Wajen karfe 1 na dare Basira ta farka sakamakon kukan da Jaririn yake mata, kuka yake sosai ta mike tana bashi mamma, Lantana ta amsheshi tace kawoshi na fita dashi na lallabashi ki samu ki kwanta.
Nan ta amsheshi tai waje dashi, kamar wasa tana jijashi taga hayaki sosai yana tasowa daga wajen d'akin Amadu.
Cikin tsoro ta koma ciki dayakr ta kofar baya ta fito a kuma nan d'akin Basira yake, Basira ta gani tana ta tari cikin bacci.
Nan ta fara tashinta, dakyar ta samu ta tasheta, ganin yaron nata tari shima yasa Lantana tasa zani ta goyashi.
Basira cikin tsoro tace " menene hakan?"
Lantana tace bansani ba nima sai dai hayaki na tasowa daga can.
Da sauri Basira ta mike ta nufi ciki, tana bud'e 'yar karamar kofar da zata sadata da wajen su Amadu, da yake gini ne irin namu na da, kowa da inda yake sai dai shi yayi dabarar ginewa tsakanin nasu da inda Basira take sai yar 'yar kofa a gun.
Basira na bud'ewa taga wuta sosai tana ci ta b'angaren su Amadu, ihu sosai ta kwalla wanda yasa Lantana tahowa da sauri.
Ganin yanda wuta ke cin b'angarensu Amadu har ta fara gangarowa inda suke yasa ta saki ihu itama, daga waje sukaji mutane an fifito, Basira kam neman cusa kai takeyi b'angaren su Amadu, ganin yanda ta fita hayyacinta tana ihu tana kiran yayanta da matarsa yasa Lantana ta fara jan hannunta.
Fizgewa tai da karfi ta kara nufar ciki, Lantana ta kara riketa tana ihu akan a kawo musu a gaji, nan wasu maza sukai tunanin bi ta baya, suna shiga sukaga yanda Lantana ta kankame Basira tana ihu, nan fa suka kamo Basira sukai waje da ita, ihu take sosai akan a taimako mata yayanta.
Suna kaiwa waje gidan ya kara kamawa sosai ihu sosai Basira take ana ririketa, can ma kawai sai gani akai ta suma.
Mahaifin Sani wanda yazo gun yasa aka kaita gidansa, sosai ranar anga tashin hankali a unguwar, daga Amadu har matarsa sun kone a ciki, dan da alama bacci suke wuta ta taresu.
_Nace Allah ya jikansu Ameen_
*******
Itakam Basira sai wajen asuba ta fardo, kuka kawai takeyi, sai wajen hantsi bayan anyi jana'iza mahaifin Sani ya kalleta cikin tausayawa yace "Basira ya akai wuta ta kama haka?"
Kai ta shiga jijigawa akan bata sani ba, shiru yai sannan yace " da matsala."
Kallansa tai cikin mamaki tace name?"
Yace " Basira wanda suka zo gidanku jiya masu rawani dan bansan matsayinsu ba."
Kai ta gyad'a alamar ta sansu, yace "kinsan ko jana'iza basu zo ba, kawai tambayata yai akan kina raye? na sanar dasu kina raye kina gidana, sai ya tambayan yaron fa? Ni kuma sam banga yaro ba alokacin sai nace mai ban sani ba gaskiya dan nima a rikice nake, abinda yaban mamaki yanda naga idanunsa sunyi alamar bakin ciki na kasa gane bakin cikin namenene a ciki, na rashin mutuwarki ne ko na rashin sanin halin da yaron yake ciki."
Zatai Magana Lantana ta zo da sauri tace " Ranki ya dade nima naga Kafilu(wannan bawan na Waziri) a lokacin da muka fito sai dai abinda yaban mamaki daga nesa na ganshi ina kallo ya juya yai gaba ba tare da yazo inda muke ba."
Basira ta kalleta tace "ya akai kika san shine bayan dare ne?"
Tace " akwai hasken farin wata sannan akwai hasken wuta da take ci."
Basira bata sake magana ba ta mike zata fita, jitai yace " ni zan fita gun amsar gaisuwa."
Basira ta mike ta koma ciki, kallan Abu Turab tai sannan tai shiru tana tunani, randa ta zubar da jini sosai har ta d'auka tayi b'ari shine ya fara zuwa mata, ba shakka ranar abu d'aya taitacu wato tuwon da Magajiya ta kawo mata, sannan ansha sanar da ita akan ta kiyayi Magajiya da Yayanta dan hatta Mahaifiyarsa sai datace mata tai a hankali da Magajiya.
Tuno maganar matar Yayanta tai, zumbur ta mike idanunta duk sun kumbura.
Hijab ta zura tai waje, tana gani yanda mutane suka taro a waje amma da yake idanunta sun gama rufewa yasa tai gaba.
Gidan Hakimi ta nufa inda Hisham yake, basu tsaya mata wasu tambayoyi ba suka mata izini ta shiga wani ya mata jagora, sai da suka kusa zuwa d'akin da yake sai wanda ya mata jagorar yace " bari na kirashi."
Nan yai gaba, daga lungun dake bayanta taji ana magana kasa kasa, jitai ance " ina kallansa ya fita da daddare ni kuma da gulma sai dana bishi wlh a idona ya d'au kalanzir da ashana yai gidan."
Nidai tsoro yasa na juyo, ni dama nayi mamaki sosai danaga Waziri kamar bai damu ba da haihuwar nan bayan kuma kowa yasan abokin takara zai zamewa d'an Magajiya nan gaba."
Jikin Basira ne ya fara rawa, da sauri ta juya cikin kid'ima, tana shiga gida ta kalli Lantana dake cikin mutane alama ta mata da hannu akan tazo, d'aki suka shiga, Basira cikin rikicewa tace " Lantana ke Baiwa ta ce ko?"
Kai ta d'aga, tacigaba " kin yarda da duk abinda zanyi?"
Nan ma ta d'aga kai, Basira tace " zan fara fita, zan tsaya a karshen layin nan in nai minti biyar ki biyoni.
Ba tare da tambaya ba Lantana ta amsa da to, Basira ta kalli Abu Turab tace "Dolene in kareka, nayi rashin yayana da matarsa akan shirme da rashin wayau na dan haka bazan yarda inyi rashinka ba a wannan halin, hawaye ne suka shiga zubo mata, lalai bazata taba yafema Hisham ba in har da bakin Magajiya itama bazata taba yafe mata ba, sannan zata kare d'anta har zuwa lokacin da zai girma ya daukar mata fansar abinda aka mata.
Cewa tai Lantana ta fita, Lantana na fita ta had'e kai da gwiwa ta saki wani irin kuka mai tsananin ban tausayi.
********
Da yake yaran da suna dadewa kafin ma su dinga bud'e idansu sannan ko sun bude ma ba alokacin zasu fara gani ba shi yasa sam Basira batai tunanin an ma d'anta wani mugun abu ba.
**********
Yanda suka tsara hakan ce ta faro, ta goya d'anta ta fita, ta dade da fita sannan Lantana tabi bayanta.......
_To fa abin babba ne🙊_
*ABU TURAB TEAM🤝🏼*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*10*
( Abu Turab an haifeshi a shekara ta alif dubu d'aya da d'ari tara da saba'in da d'aya, shikuma Abdulmajid an haifeshi a alif dubu d'aya da d'ari yara da saba'in, karku manta farkon labarin a shekara 1970 aka fara wanda ya kasance ranar sunan Abdulmajid, a kuma shekarar ne Sarki ya auri Basira har ta samu ciki.)
_Wannan tuni ne_
********
Hisham ya fito sai dai baiga kowa a waje ba, ciki ya koma cikin halin ko in kula dan shi babbar damuwarsa bai wuce ya d'au mataki a kan Basira da d'anta ba dan tuni aka sanar dashi suna raye, ba shakka inya sake wani yunkuri za'a gano bakin zaren shiyasa yake tunanin in suka tafi a hanya ya zama dole ya san yanda zaiyi kafin su karasa garin.
*********
Magajiya tun bayan tafiyar Hisham ta rasa inda zata sa kanta, ya zama dole ta fitoda wata sabuwar hanya ta yanda zatai in har d'an ya dawo, ita ta kasa yarda da komai ma.
Mamaki ne ya kamata jin sallamar Jakadiya, ta dade sosai kafin ta bata izini, Jakadiya ta shigo tare da washe baki, ta matso kusa da Magajiya ta zauna a kasa sannan ta kalleta ta mata jinjina tace " Sai ke Sarauniyar da babu irinta, ba aiba kuma baza'ai irinki ba, kinci dubu sai ceto takawarki lafiya matar sarki, takawarki lafiya mamar sarki, takawarki lafiya Haj......."
Wani banzan kallo Magajiya ta mata tace " me kike aikatawa yanzun?"
Jakadiya ta washe baki tace " wato Ranki ya dade matsala aka samu ai yayatace bataji dadi ba shi......"
Wani mugun murmushi Magajiya ta sakar mata tace "Babu ruwan kwai da aski, abinda nakeso naki shine ke din wacece?"
Yawo ta had'iya sannan tace "taki ce sai dai......"
Magajiya tacigaba " waye ya baki wannan matsayin wanda kike takama dashi?"
Jakadiya tai zuruzuru da ido, da kyar tace " kece."
Magajiya tai wata 'yar bazawarar dariya tace " kinsan da haka ke har kin kai matsayin da zakiyi tunanin yimin karya?ke d'in wacece da har...."
Da sauri Jakadiya ta sa gwiwowinta a kasa tace " Magajita tuba nake, sai dai kafin ki yanke hukunci yakamata ki duba yanda nake miki biyayya, nasani sarai Yarima ba......."
Gaban Magajiya ne ya fad'i ta kalli Jakadiya a tsorace, dama Jakadiya tasan wannan ce kadai hanyar dazaisa ta tsira inhar ta nuna mata ta san sirrinta.
Jakadiya tai saurin rufe bakinta tana waige waige tace "tuba nake ranki ya dade, wannan sirri ne da zan rikeshi har kabari na, tuba nake da subutar baki."
Magajiya ta danyi kifikifi da ido sannan ta daure tace " me kike san cewa?"
Jakadiya tace " tuba nake Ranki ya dade ai sirri ki nawa ne, baza'aji wannan zance daga gareni ba."
Ganin tabbas Jakadiya tasan wani abu sai dai da alama batasan duka ba yasa ta daure tace " tashi kije ni ina bukar hutu."
Nan Jakadiya tai waje da sauri.
Tana fita tai dariyar mugunta tace " ni da gidan nan da matsayina mutu ka raba."
*********
Sarki ya kasa zaune ya kasa tsaye, yau ya kamata su Hisham su dawo sai dai yajisu shiru hakan yasa da kansa yai tattaki zuwa b'angaren Magajiya.
Zagi(wanda yake ma sarki iso sannan yake zama a gaba duk inda zaije ya sanar da isowar Sarki.)
Mikewa Magajiya tai cikin mamaki, masu kula da ita ne suka shigo suka kara sanar da ita, nan ta fito dan tarbarsa.
Sai daya shiga ya zauna, sannan ya kalleta yace " Hisham fa? Bayau zai dawo bane?"
Kallan mamaki tamai wato abinda ya kawoahi b'angarenta kenan?so yake yaji zancen matarsa da d'ansa kenan."
Murmushi ta saki duk da bakincikin da take ciki tace " mai zaisa hankalin Mai Martaba ya tashi bayan na tabbata yanzu suna hanya?na tabbata ka matsu kamar yanda nima na matsu inga d'ana."
Sarki ya d'an kalleta yace " niba saboda haka nake tambaya ba, akwai abinda nakeso najine daga bakin Waziri."
Murmushi tai tace "Angon Karni ai ba sai kayi kara ba, nima d'a na ne."
Kallanta yai yana mamaki, sai dai yana jin dadi sosai na yanda takesan d'ansa.
Yace " Ina AbdulMajid?"
Tace " d'azu Uwar Soro( Mahaifiyar sarki, ko yayarsa ko gwaggonsa. ko uwargidansa, wadda ta wanke shi. wadda ke iya gaya masa duk abin da ake jin nauyin gaya masa, ita ake kira uwar soro.)
Amma ita Mahaifiyarsa take nufi dan a lokacin nasu ita ake kira da Uwar Soro.
Murmushi yai sannan yace " ni zan koma."
Kallansa tai a ranta tace ka gama abinda ya kawoka kenan?
Amma a fili tace " ina godiya da wannan ziyarar Ranka ya Dade."
Yana fita ta d'anyi kwafa cikin takaici tace " ni zaka wulakanta?"
************
Basira kam tana gaba Lantana na baya ta kasa mata magana ganin kawai tafiya takeyi da alama batama san inda takesa kafarta ba.
Abu Turab na bayanta, ko da Lantana tai yunkurin ansarsa Basira taki.
Sunyi tafiya mai uban nisa dan Lantana harta gaji, itakam tafiya kawai take dan hankalinta baya jikinta, tunanin yayanta da matarsa sun mata yawa, sai da taji Abu Turab ya sa kuka sannan hankalinta ya dawo jikinta.
Kallan inda suke tai daji ne sosai juyowa tai ta kalli Lantana sannan ta nemi guri ta zauna ta kunto shi daga bayanta, Lantana ta zo kusa da ita ta tsuguna sannan tasa hannu ta fara danna mata kafarta dataga ta kumbura.
Basira kam shayar dashi kawai take ko magana batayi, idanunta ya kafe kaf ta kasa ko hawaye bare taji sanyi a ranta.
Sai da Lantana ta danna mata kafa sosai sannan ta kalleta tace " bakici abinci ba ranki ya dade."
Basira kai kawai ta girgiza mata, ganin ya koma barci yasa ya fara neman goyashi, Lantana tai saurin amsarsa ta sashi a bayanta suka cigaba da tafiya.
"**********
Shikam Hisham da yamma yai tunanin zuwa gaisuwa sannan ya sanar da ita tafiyarsu gobe, dan ya tabbata in bai je ba sai gulmar abin ta bazu a garin killa ma dogarawan da suka zo su kai gulmar har masarautarsu.
Bayan sunzo gidan ne, ya nemi a kira masa Basira ya mata gaisuwa, sai a lokacin aka farga da rashin su a gidan.
Tashin hankali nan fa aka bazama naimansu, ganin Basira bamai yawo bace sannan ba Lantana ba kuma d'anta, wannan ya kara tadama mutane hankali, tun azahar ake nemansu amma ba labari....
Hisham kam hankalinsa ya kara tashi har ya fara zargin kila ko ta samu mota ne ta tafi Zazzau, wannan al'amari ya kara tada mai hankali sosai da sosai......
*********
Basira kam sai da ta fara hakki sosai sannan ta samu ta zauna, dan tafiya kawai suke sai dai in Abu Turab yayi kuka su tsaya yasha sannan su ci gaba da tafiya.
Lantana ta matso tace "Ranki ya dade dan Allah ki samu ki huta?" ita kanta Lantana hakki take sosai ga magrib ta kawo kai dan rana saura kiris ta fad'i.
Kallan inda suke tai, wani kauyeni da ba mutane sosai, nan suka karasa kauyen.
Wani tsoho suka gani a zaune yana wanke alo da alama rubutu yai, lantana ta gaisheshi tace " Baba dan Allah ka taimaka mana da gun kwana zuwa gobe."
Kallansu yai ya kalli Basira wacce ke tsaye kamar zata fadi, yace " ku shiga ciki kafin wannan ta samu ta kwanta.
Lantana ta shiga mai godiya, Basira kam jiri ne yake d'ebanta, tsohon yace "kuyi sauri ku shiga."
Da kayar Basira ta daure tace "Mun gode."
Sannan suka nufi ciki.