BABI NA GOMA SHA DAYA.
Sosai yake kaiwa da komowa cikin dakinsa, hannayensa sarke a kirjinsa, lokaci-lokaci ya kan ja tsaki kamar harshensa zai tsine. duk sanyin da A-C din dake dakin take bayarwa hakan bai hana gumi samon mazauni saman goshin sa ba.
Sosai ya cigaba da zarya a dakin cikin rashin mafita akan abin da ya addabi zuciyarsa sosai yake jin zafi da raɗaɗi a zuciyarsa da ruhinsa sosai ya ji komai da ya faru dashi kwanakin baya sun hanashi sukuni ya naji a ransa bai taba ganin 'ya mace da ta raina masa hankali ta ci masa mutunci kamar wannan kankanuwar ƴarinyar wanda ko a zaben mata aka saka ta ba in da zata kai labari kwaila ma irin ta wacce sam bata san Darajar da mace ke da ita a wannan duniyar rayuwar ba ta yanzu ba amma har ta dubi tsabar idon sa ta gaya masa haka.
"Noo Impossible".
Abinda ya fadi kenan cikin daga murya mai sauti yana faman kai wa kirjinsa naushi kamar a nan mai laifin take.
Kamar wanda aka tsikara haka ya zari Key din Motarsa ya fara tafiya cikin sassarfa kamar zai tashi sama a haka har yafice daga cikin dakin sosai yake taka benen da zai kai shi zuwa kasa sashin babban falon cikin gidan kallo daya zaka yi fuskarsa ka fahimci halin da yake ciki na kunar rai sosai yake zakar wani abu a ransa wanda yake da tabbacin shi kadaine mafita gareshi dole ya dauki mataki dole ya dan hukuncin da zai dauka dole ya nuna mata tayi kadan ba kowan kowa bace a cikin jerin mata ba ta kai Level din da zata raina shi ba ba ta kai matakin 'ya mace da zai kalla har ya yaba ta raina masa hankali ba da wannan sakar zucci har ya fice daga sashin cikin gida ya doshi Mota Parkig ya fara kokarin fiddo da motarsa komai yake yin sa a hanzarce haka ya figi motar mai gadi na ganinsa ya doso shi da sauri ya mike ya nufi Get din ya bude sosai yake kallon fuskar Huzaif yanayin da ya ganta sai da gabanda ya fadi sosai.
"Allah Yakyauta".
Abin da ya fadi kenan yana margaya kai ya mai da Get ya rufe bayan Huzaif ya fice.
Sosai yake gudu kan titi zuciyarsa na faman wassafo masa abubuwa ma bambanta sosai yake jin komai na zuwa masa a bazata wanda ya hakikance ba wanda ya assasa hakan sai wacce kwailar yarinƴar wacce ko kyautarta aka bashi ba abin da za tayi masa a rayuwarsa illah wahala.
Cikin mintin nan da ba su haura talatin ba ya isa Kofar Asbitin baban alis sosai yake kallon asibitin bayan yayi parking ya fito yana mai wasa da Key din motartashi gaban motar ya usa ya yi tsalle ya hau gabanta ya zauna gami da harɗe hannayensa duk biyu a kirji ya kure kofar asibitin da kallo yana tunanin abin yi domin shi dai zuciyarsa ce ta kawo sa amma bai san takamaiman abin da zai gudanar ba abubuwa biyu suke masa sukuwa da tunanin sa haushin Mariya da kuma son ganinta wanda duk ya ajje a hurumi daya wanda sam ba su da alaƙa da juna numfasawa yayi gami da zaro wayarsa daga aljihu yana shuga dandannawa kamar mai kokarin kira kamar wanda ya ga takaici sai kuma ya ja tsaki gami da maida wayar aljihunsa yana faman sakin numfashi.
*****
"na rasa me zan yi komai ya kwance mani".
Abinda ta fadi kenan tana tura laɓɓanta cikin bakinta tana faman ya mutsa fuska kamar wacce aka sanya shan magani.
Sosai yake kallonta da yanayin da take ciki na yanayin rashin kwanciyar hankali komai ya bayyana a fuskarsa na tsananin damuwa har zurmawa tayi kamar wacce ta tashi daga gudawa.
"na rasa ta ina zan miki bayani ki fahimta, na rasa mai zance miki wanda zai ganar dake komai da komai kin kasa daukar abin da nake fada miki, ya zan yi dake Mariya?".
gyaɗa kai kawai take yi tana faman dauke kwallar da taji suna kawo mata farmaki.
"Hakuri Dr.Aqeel. bani da komai da zai taimaka min domin samun natsuwa ta ka tuna yau kwanansa Biyar ban gan sa ba, yau kwanan sa biyar ban san a wani hali yake ba, dole dole ne na damu sosai da sosai zuciyata taki hakuri taki natsuwa".
Ta karashe cikin karfin hali kamar mai som fashewa da kuka kai ta cigaba da gyaɗawa.
"ban san abin da yasa yaki jin magana ta ba, ban san abin da yasa bai yi amfani da abin da nace ba komai da komai Dr.Karami yace zai amma yaki yarda da hakan".
Ya fadi yana kallon Mariya wacce gabadaya hankalin ta na wajan Habeeba wacce take sharar barcin ta hankali kwance kamar bata da wata matsala a duniyarta mai da kai tayi wajan Mu'azzam wanda shi barci yake yi. sosai take jin tausayin sa na damunta a rai sosai take tausayawa rayuwarsa.
Mikewa tayi ba tare da ta dubi Dr.Aqeel ba ta fara tafiya sannu hankali sai ka rantse rashin jini ne ke damunta.
"Uhmm nace ba".
Ya fadi yana mai kallonta cak! tsaya ba tare da ta juyo ba.
"ina zaki kuma?".
"waje zan fita".
ta bashi amsa tare da kara saurin tafiyarta don ba ta so ta sake furta ko da kalma daya ne gareshi
So take ta je waje ko za ta samu sa'ida a zuciyara ba wai ta yarda dari bisa dari bane a,a kawai dai zaman dakin ne ya fara gunduranta dalilin Dr.Aqeel ba ta son a daidai wannan lokacin ace maganar wani na ratsa mata kunnuwa tana bukatar natsuwa ko yaya ne amma ta lura Dr.Aqeel ba zai bata wannan damar ba sam! Ba ta san me yake nufi da ita ba ta rasa ina zata sa kanka ko yaya ne ta samu hutun rai da ruhi.
"MACE ƘYANƘYAWA".
Sautin muryaar da taji ne ya sanya ta katse tunanin da ta afka sosai gabanta taji ya bugu har sai da ta sanya hannu ta dafe tana ambaton 'innalillahi wa'inna ilaihir raji'un'
Sosai ta fiddo da idanuwanta waje tana mai sauke so akan sa sosai taji komai yana kwance mata cikin kwakwalwarta.
Gabadaya idanuwansu suka sarƙe sosai suke ƙallon junansu an rasa mai dauke kallonsa daga dan'uwansa fuskar Huzaif ba abin da take saki sai murmushi sabanin ta Mariya da take a cungune waje daya kamar wacce aka aikowa da mutuwar wani cikin dangi
A hankali ya fara kokarin saukowa daga kan motar shi yana faman sakin murmushi wanda daka gan shi kasan akwai alamun tambaya akan sa.
Sosai yake tunkaro ta gabanta na sake tsananta faduwa komai take ji na kanta na wargaje mata ba abin da zuciyarta keyi sai ɗaci sosai.
Ba ta son ganinsa, bata muradin ganinsa cikin duniyar rayuwarta, ylta tsani shi a zuciyarta tun daga kalaman sa take jin wani irin ɗaci tun daga kasar ruhinta a dalilinsa sai dai wani bangare na zuciyarta sam yaki kin yarda da Huzaif domin kullum cikin tono mata sunan yake.
"Yaa Allah!".
Ta fadi tana mai haɗe laɓɓanta waje tana cusa su cikin bakinta a hankali take daura hakoranta akai tana dannawa kanta a kasa tana jin saukar numfashin Huzaif kusa da ita hakan yakara tsinka mata zuciya ji take kamar ta kurma ihu don haushi.
"wai ke mai yasa kullum in za a ganki, sai an ganki tare da kunci ne?".
Ya fadi yana kallonta sosai yana kallon yanayin Emotion dinta da ya sauya lokaci guda yana kallon yarda fuskarta ke wanzar da haushi da ƙi kuma ya tabbata akan sa ne Murmushi ya saki ganin tana kokarin barin wajan ya kai hannu ya riko mata nata hannu.
Ai ji tayi kamar an daura mata garwashin wuta a hannun nata nan da nan jikinta ya dau wani irin Shock har sai da komai ya motsa a jikinta da sauri ta dago kanta sosai take kallon Huzaif da rinannun idanuwanta ji take kamar ta tsinke shi da mari don takaci da bakin ciki bakin tane ya fara motsi alamun son magana laɓɓanta dake cikin bakinta har wannan lokaci ta shiga motsa su.
"Don Allah ka rabu dani!".
Ta fadi cikin murya mai sauti da karamar tsawa a cikinta tana mai dauke kallonta daga gareshi bayan ta watsa masa wani mugun kallo.
Sosai yake mamakin yar mitsilar yarinyar nan, da yarda take yin komai nata cikin rashin tsoro ko fargabar abin da zai je ya dawo ya lura akwai tsoro a zuciyarta sai dai bata barinsa yayi tasiri a zahirinta ba.
A hankali ya saki hannunta da ya rike gami da jan guntun tsaki mara sauti amma hakan bai hana Mariya ji ba ko kallonsa ba tayi ba amma ta lura yaji haushin abin da tayi masa gyaɗa kai tayi ta fara hanzarin barin wajan amma maganarsa ce ta sanya ta saurin tsayawa.
"mai yasa baki son mai sonki da alheri, na lura wani naki ne bashi da lafiya amma kin ki bani damar da zan samu ikon duba shi, ko da yake ban san abin da kike tunani akai na ba ni dai ban dauke ki na ajje a zuciyata ba akan wani mugun nufi sai dai na ajje ki a zuciya a dalilin tausayinki da jin kai".
Sosai maganganunsa suka shiga shigarta ta ko ina sosai take jin sautinsu na haifar mata da wasu lamura a kasar zuciyarta sosai take jin tasirinsu a kasar ruhinta sosai zuciyarta ta fara kokarin gasgatawa tunaninta ya karbi lamarin a saukake sosai take ajje numfashi a duk wani kalma daya da ya furta a hankali ta fara kokarin kallonsa idanuwanta a dan tsuke bata bari tasirin maganganunsa sun fito zahiri ba ta fara motsa laɓɓanta.
"bana tsammanin zan yarda waki bugun ya sake gintawa a tsakaninmu kasan ance dukan farko shine duka kuma ka lalata damar ka tun a karo na farko don haka ina mai rokan ka ka fice mani daga rayuwa bana so komai ya faru tsakanina da kai kaji ko kawai ka kama gabanka kowa yayi rayuwarsa ba abin da ya hada kifi da kaska balle kuma har su da zauna inuwa daya".
yanayin yarda ta ajje furucinta cikin halin-ko-in-kula yayi matukar kara zafin zuciya gareshi sosai yake kallonta yana jin rashin wayon da ya nuna akanta har ya tsaya yar yarinyar nan na fada masa abin da ta so a ranta tsaki yaja sam bai lura ta wuce ba sai da ya fara motsa baki yana son yin magana sannan ya lura bata wajan naushi ya kai sa iska gami da cizon Laɓɓa sosai ya ke kallon kofar aasibitin domin ya hango shigarta sosai zuciyarsa take shiga kunci a hankali yana mamakin yarda akayi yake wahalar da kansa akan wannan halintar wanda ko a farkinsa ban yi zaton zai ganta har ta samu damar shiga rayuwarsa ba dole ya san abin yi dole ya dau mataki akanta domin tsana yake hangowa tasa a idanunta ya tabbata ta tsanshi haushi sa take ji a ranta har a bayyane a fuskarta.
"l'm Huzaif!".
Ya fadi yana nuna kansa da dan yatsansa yana mai sakin murmushi gami da gyaɗa kai ya juya ya koma motarsa da gudu ya fuzge ta ya bar harabar asibitin.
*****
Sosai Dr.Karami yake aikinsa cikin kwanciyar hankali da kware a harkar cikin kwanaki talatin da biyar komai ya fara kamo hanyar samun waraka ga Habeeba ba wai Mariya kadai ba hanta su Dr.Aqeel sunyi matukar yin farinciki da hakan domin sosai suke ganin komai na zama Normal izuwa wannan lokaci Habeeba ta fara samu sauki sosai don yanzu duk na fizge fizge da rashin magana ya kau sai da lokaci-lokaci in kana hira da ita tana kau ce hanya cikin hirar zaka ji tana wani zance na daban wanda bashi kuke yi ba hakan ya so damunsu Mariya sai dai Dr.Karami yana kwantar musu da hankali gami da sanar da su dole hakan sai ta faru gareta a hankali komai zai daidaita kamar bata tabayin cutar ba.
Kamar ko yaushe yau mariya ce zaune ita da Dr.Karami suna hira domin shakuwa ce ta shiga tsakaninsu sosai da sosai Mariya tana matukar girmamashi gami da kunyarsa hakan yasanya Dr.Karami yake jinta a ransa sosai take burgeshi komai nata yanayi masa musamman da ya lura tana da hankali gami da natsuwa sosi a rayuwarta gata da gamun kai.
Dr.Karami ya numfasa bayan ya gama wayar da yake yi ya dubi Mariya da take ta faman wasa da Mu'azzam dake hannunta shikuma yana faman ƙyalkyala dariya.
Murmushi yayi yana gyaɗa kai kafin ya motsa laɓɓansa.
"Na lura sosai da sosai ki ke son Mu'azzam, anya za ki iya rabu dashi kuwa in wani abu ya taso na zuwa wani waje".
Kasa tayi da kai alamun jin kunya sosai ya kureta da ido.
"kin fiye kunya Mariya anya kuwa".
ya sake fadi yana dariya.
A hankali ta dago kanta ta kalle shi sannan ta ajje kallonta gefe.
"Uhmm Dan'uwana sosai nake son sa ban son rabu dashi ko na sakanne".
"kenan yanzu ko lokacin aurenki yayi ba zaki iya rabu dashi ba a matsayin ki na 'ya mace yar gidan wani".
Ji tayi kamar ta tsune kasa don kunya dalilin aure da ya ambata gabadaya sai ta rikece sai motsu motsu take yi ta rasa abin yi gabadaya.
"wai shin ina zancen makarantarki ya kwana ya kamata ace kin koma makaranta Mariya zaman haka ba zai haifar miki da ɗa mai ido ba ke 'ya mace ce sosai karatu ke da muhimmanci a rayuwarki ya kamata ace kin mai da hankali sosai zuwa ga karatun ki ita ce dama daya jal da kike da ita ko don taimakawa iyayenki wata rana kece babba ko da dai ke yar gidan wani ne amma duk da hakan kiyi karatu".
Sosai kalamansa suke samun masauki a zuciyarta sosai take jin dadin yanayin furucinsa cikin sanyin murya mai cike da karfafawa zata so ace hakan ta kasance gareta zata so ace ta samu wannan damar za ta so ace tayi karatu na sosai da sosai domin ta lura karatu a rayuwar zamanin nan yana da muhimmanci sosai musamman 'ya mace ko ba don komai wasu abubuwan na rayuwa da suke gudana a duniyar nan ya kamata ace mata suna samun wannan damar domin wasu fannonin 'YA'YA MATA ya kamata ace a wajan ba maza ba musamman harkar likitanci ko ba komai taimako ne na al'umma ku hakan zai wuce takaicin da wasu ke yi wa mara hali a rayuwarsu.
Sosai take jin tausayin kanta da na iyayenta da kaninta Mu'azzam ta sani ƙaddara ta fado rayuwarsu gami da talauci da ya hana su gudanar da wasu abubuwa sosai da ya kamata ace sunayin sa ba wai rayuwar jindadin duniya take nufi ba a,a wasu abubuwan a rayuwar dangin rai dole yayi a karan kansa ba wai sai ya tsaya wani yayi masa ba musamman duniyar zamanin nan a yanzu in baka dashi ba mai yi da kai balle ya ya jikanka ta sani a duniyar nan in baka dashi kai da banza duk daya ne ta gani an aikaice akan ta anyi mata.
Hawayen da suka zubo mata ne ta sanya hannu ta dauke su sosai take gyaɗa kai ta na son yin magana amma ji tayi wani abu mai nauyi ya saukar mata a kirhi sosai take jin komai na rashin dadi na wanzuwa a gareta sosai take tuno rayuwar da tayi a makaranta da irin yarda ake korota dalilin rashin kuɗi sosai take tuno yarda ake mata gori a makaranta kowa ya gujeta ba ta da kawa ko daya domin ta fita zakka a cikin yaran makaranta kullum cikin rashin babu take ba ta ga watan da zai ya kare ba a ƙore ta ba ta ranar da zata zo har ta fadi ba a tuhume ta da rashin babu ba akan wani abun bukata a makaranta.
Kasa tayi da kai sosai take jin kuncin rayuwar da take yi sosai take hango ƙaddarar da take da wainiya da rayuwarta ita da ahalinta.
"Mariya!".
Sautin muryar Dr.Karami ta sauka cikin kunnuwanta wanda gabadaya ta mance ma da wanzuwan sa a wajan a dan razane ta dago da koɗaɗɗun idanuwanta ta sauke akan sa.
"karki ce da ni ba ki son karatu, karki ce dani maganar da nayi miki ne ta sanya ki kuka".
Kai ta shiga girgizawa sosai hawaye da sauka a kuncinta a hankali tashiga motsa laɓɓanta.
"ko daya ba ruwanka komai naka gaskiya ne mai kyau ne sai dai...".
Shiru tayi gami da yin kasa da kai sosai ya kafe da ido don ya gama fahimtar inda ta dosa da batun nata amma nauyi ya hanata fadi tausayinta sosai yake ji komai nata na rayuwa yake tausayawa.
"Karki damu Mariya nayi miki Alkawari...".
"Dr.Karami".
Sautin Muryar Dr.Aqeel ne ta katse masa maganarsa tsaye yake ya harɗe hannu a kirjisa fuskarsa kadaran kadahan gabadaya ke kallonsu sosai yake son fahimtar abin da zuciyarsa take sanar dashi sosai yake kallon yarda Mariya take kuka wanda sam bai da sauti sai na hawaye sosai ya fara jin wani iri a kasar ruhinsa da zuciya zargin Dr.Karami yake da shiga rayuwar Mariya ya kunsa mata wani abun wanda yasanya shiga damuwa sosai.
"na lura cikin yan kwanakin nan wani lamari ne yake tsakaninka da Mariya, in dai har za ku zauna tare bana taba ganinta ta tashi da dadin rai".
gabadayan su suka dubi Dr.Aqeel wanda shi kansa sai da ya tsargu sosai akan maganar da yayi duk sai yayi wani zuru zuru dashi yana faman yake.
Dr.Karami yayi murmushi domin ya rasa ina zai ajje zancen Dr.Aqeel bai fahimci in da ya saka gaba ba gabadaya tunaninsa ya tsaya akan zarginsa yake yi kenan da kuntata rayuwar Mariya? girgiza kai yayi kafin ya fara duban Mariya sannan ya dubi Dr.Aqeel.
"ce maka tayi ina takura mata hala?".
Sosai Dr.Aqeel yake nuna nadamarsa akan abin da yace ya san tabbas maganar da yayi ba ta da hurumin da za a ajjeta sosai ya shiga girgiza kai yana faman ajje yake kamar wanda aka baiea kyautar bazawara.
"Noo ba haka nake nufi ba".
Sosai su duka biyun suka kureshi da ita musamman Dr.Karami da ya fara hasaso wani abu da zuciyarsa ke sanar dashi amma yaki yarda da hakan mikewa yayi a hankali yana mai duban Mariya.
"ni zan tafi sai gobe kuma ki kula da kan ki sosai".
Gyaɗa kai kawai tayi alamun amsawa sai dai har ga Allah bata so tafiyarsa ba har a ranta tana jin dadin zama dashi amma ta lura Dr.Aqeel yana yi mata kanzagi akan hakan kamar ba ya so zaman da suke yi a tare tashi tayi tana duban Dr.Karami da yake yiwa Dr.Aqeel Sallama.
"Nagode sosai gobe Allah ya kiyaye hanya ya tsare".
ta na gama fadin haka ta gyarawa Mu'azzam kwanciya a kafadatar ta yi hanyar dakin da Ummanta take tana faman saka da warwara akan Dr.Aqeel gabadaya ta lura dashi ya fiye takura sosai duk da dai shi mai ALHERI ne amma wani lokacin abin da yake yi sam bai dace ba ya kamata ya san wani abu guda ba kowa ne zai iya daukar irin halin da yake nuna wa wanda zai san shi ba sai yaga kamar tsana ce kawai ko da ita a karan kanta ta fara dasa ayar tambaya akansa mafiya yawan lokaci in dai suna tare da Dr.Karami yana yi mata wasu abubuwa kamar natsana ita da Dr.Karami din ta rasa in ya dosa ta rasa menene nufin sa da hakan din.
Tsaki ta ja kamar harshenta zai tsinke ta karasa shiga dakin kwance ta sameta tana barci samun waje tayi ta zauna izuwa lokacin Mu'azzamn barci ya fara tafiya dashi sosai tashi tayi ta shimfiɗar dashi ta sannan ta samu gu ta zauna ta zabga tagumi ta fada duniyar tunanin mahaifinta wamda ba ta san a wani hali yake ba cikin duniyar rayuwarsa tun fitarsa kwanakin baya da yayi har yau ba alamun sa ta rasa ina ya tafi ta rasa mai yasa mahaifinta yayi mata haka ta ba so yayi misa da ita a kowani hali suka tsinci kansu tasani rashin abubuwa yana taka muhimmiyar rawa a duniyar rayuwarsu sai dai ba yarda za suyi ta sani rashin babu ne yasanya mahaifinta fita amma bai dace ace tsayin wannan kwanakin ba asan a inda yake ba har gida taje amma ta sami labarinsa ba sai ma rashin mutunci da Goggo Marka ta aikata mata da kuka ta baro gidan.
Sosai take jin faduwar gaba game da mahaifinta duk lokacin da take tunanin sa komai take ji bai mata dadi a rai ta rasa mai za tayi ta rasa mai ya dace tayi sosai kwakwalwarta ke caji wanda ita kanta ta san tunanin da take sanyawa kanta ya fi karfin kanta sai dai bata san mai za tayi ba komai a cakuɗe yake cikin duniyar rayuwarta.
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA BIYU.
Sosai idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir kamar wanda aka watsawa garwashin wuta. Sosai yake jin wani zafi da zugi a kasar zuciyarsa sosai da sosai kirjinsa yana wani irin bugawa kamar zai rabe gida biyu numfashi yake ajje wa lokaci-lokaci mai tsananin zafi da zugi.
Shisha din dake girke a tsakanin kafafuwansa ya zubawa ido sosai kamar wanda yake son fahimtar wani abu game da ita a hankali ya kamo yar igiyar da ake amfani da ita ya kai bakinsa ya zuga tsayin sakanni talatin kafin ya zare daga bakinsa gami da sakin wani hayaki wanda ya turke masa fuska gabadaya ya kasance ba ka hango kansa ma sosai hayakin yake tuntulowa daga bakinsa da hancinsa sai da hayakin ya debi lokaci kafin ya tsagaita da tuntulowa sosai idanuwansa suka kaɗa har da yar guntuwar kwalla kwance a ciki.
Gyaɗa kai yake faman yi ba abin da yake yi masa shawagi a duniyar tunaninsa da zuciyarsa sai wani lamari da ya kasa gasgata shi ya rasa a ina zai ajje shi domin samun saukin raɗaɗin zuciya dana ruhi sosai yake jin nauyi a kirjinsa sosai komai ke kwance masa na tunani sosai yake jin abubuwan da suke addabarsa suna amsa kuwwa gami da sauti a kunnuwansa kirjinsa yake ji yana kara nauyi sosai numfashi ma dakyar yake samun ajjeshi.
A hankali ys ajje igiyar shisha din ya fara yinkurin mikewa wani irin nauyin kirji ya sake tokareshi daga hanzarin da ya so amfani dashi da sauri ya koma ya zauna ya na mai sakin numfashi da sauri-sauri kamar wanda aka sanyawa Oxgyen sosai yake jin bacin rai in ya tuna kalma guda da yanayin da take furtata akansa sosai yake jin ɗaci a ruhinsa akan duk kan wata kalma da ta fito daga bakinta sosai yake jin zafin tsakin da tayi masa a daidai wannan lokaci.
Mai yasa... Mai yasa mai dauki mataki tun a waccan lokacin ba, mai yasa ya bari damar ta subuce masa mai yasa yake kasa aiwatar da duk wani kudiri da ya daukarwa kansa in har yana kusa da ita ya rasa dalili.
Zancen da yake ta saƙawa kenan a kasar zuciyarsa sosai yake ganin tana yi masa kwarjini a idanuwa sosai yake kasa aiwatar da komai in yana gabanta.
Kai ya shiga girgizawa yana faman taunar laɓɓansa kamar su ne masu laifin sosai yake jin komai ya cushe masa sosai yake ganin kwanciyar hankalinsa na guje masa sosai komai ke shirin ƙwaɓe masa a rayuwa a dalilinta a matsayinta na kaskantaciya wacce bai dauka a bakin komai ba.
"Ni Huzaif ni ta wulakanta".
da sauri yake girgiza kai ya nasake furta.
"ya zama dole nasan abin yi zuciyata ba zata yafe mani ba sam! na lura da hakan".
Haka yake ta sakin zance kamar wani zararre tsayin lokaci kafin ya mike cikin karfi hali ya fada Toilet ruwa ya watsa wa kansa nan ya fito ya shirya domin ya lura in har yana zaune a waje daya komai zai iya hanashi sakat! musamman kan maganar yarinyar da yake ji a ransa ya tsana tsana mai tsanani.
*****
"Please Khairiyya!".
Ya fadi cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa a gareshi sosai yake jin zafi a zuciyarsa sosai yake jin ko ina na zuciyarsa na yayyagewa sosai kansa ke sara masa komai ya kwance masa sosai ya shiga tashin hankali mara yankewa wanda yake tsammanin zai iya tafiya da numfashin sa.
Sai da ya gama ja-in-ja da numfashin sa kafin ya daga laɓɓansa daƙyar.
"Ina cikin Matsala sosai da sosai na rasa ya zan yi komai yake kwance mani na tunani na komai zai iya faru ki taimaka ki zo".
A wannan karon muryarsa ta rage sauti sannan kuma tana rawa hannayensa duk biyun ya daura akan sa bayan ya sauke wyar daga kunnansa sosai yake jin tashin hankalin da ya tunkaro shi sosai yake jin bugun zuciyarsa na sauyawa daga kwanciya hankali zuwa akasinsa.
"ban san abin da ya sanya ni gamu da ita cikin duniyata ba, ban san abin da yasa ta shigo rayuwata ba ban san abin da yasa ranar ta zo mani a haka ba ban san mai yasa tsautsayin da nake gudu yake kokarin fado mani ba ban san gangancin da ya kai ni wannan ranar har hakan take dauko mani tashin hankali wanda ba zan iya dauka ba".
Gabadaya ya zube kan cafet din dake tsakar dakin yana faman sakin numfashi a hankali ji yake yi kamar gabadaya tashin hankalin duniya a kansa ya kare.
Marikin kofar da yaji an murza ne ya sanya shi saurin buɗe idanuwansa da suke rintse sosai yake kallonta da yanayin da ta shigo dashi kau da kai yayi gami da jan gudun tsaki wani haushi ne yaji ya tokare masa wuya ji yake kamar ya tashi ya rufe ta da duka sai yanzu yake dana sanin kiranta bai san dalilin da yasanya shi kiranta ba wani haushi yake ji a game da ita gabadaya yake ganin muninta da wani haushi nata yana tun karoshi mai da idanunsa yayi ya rufe.
Ita kuwa ganin irin Halin-ko-in-kula da ya nuna mata sai ta dauke kai tana mai jan tsaki a hankali ta fara taku har ta isa kan daya daga kujerun falon ta zauna kafin ta dube shi sosai kallo take masa na TUHUMA sosai take ganin sauyi gareshi sosai take ganin komai nashi ya sauya ba yarda ta san shi ba kyaɓe baki tayi kafin ta motsa laɓɓanta da suka sha Pink din jambaki.
"Huzaif".
Ta fadi a hankali tana kara kureshi da idanuwanta manya masu kalar madara sai faman kaɗa su take yi.
Bai motsa ba balle ta saka ran masawar sa sosai taji haushin haka amma bata nuna ma sai ma sake kiransa da tayi nan ma bai amsa mata ba hakan ya kara kular da ita a zafafe ta mike ta fara kokarin barin falon tana fadin.
"A rayuwa na kijin wulakanci zan iy daukar komai amma ban da wulakantawa kuma wannan zai zama karo na karshe wallahi!".
tana gama fadin haka ta rike murfin kofa tana kokarin murɗawa ta fice.
Huzaif da yake fama da zafin zuciya ya kokarta buɗe idanuwansa ya sauke akanta.
"Khairiyya".
ya fadi a raunane ita kanta sai da taji wani iri a jikinta a sanyaye ta saki kofar gami da juyowa ta dube shi tana harɗe hannayenta a kirji.
"Taimako nake bukata don Allah".
Da mamaki take dubansa tana juya maganar tasa akanta kafin ta yi taku uku sannan ta tsaya.
"Huzaif taimako fa kace?".
Kai ta shiga girgizawa tana faman sakin yaƙe.
"me ke damunka har kake neman taimako a duniyar nan?".
Ta sake fadi tana mai kafeshi da idanu sosai.
"Nima ban sani ba komai ya kwance mani kawai ji nake kamar bani ba...".
Da hanzari ta tare shi.
"Ban gane ba Huzaif?".
Tashi yayi daga kwancen da yake a hankali ya mike tsaya sosai yake kallon Khairiyya sosai yake hango zata iya taimaka masa sosi yake ganin ita kadaice zata iya yi masa komai da yake bukata.
Gyaɗa kai yayi kafin ya ciji laɓɓansa hannunta ya kamata ya fara kokarin ja da sauri ta fizge tana masa kallo mai dauke da TUHUMA shima kallonta yayi wani iri kafin ya sake jan hannun nata suka fice daga cikin falon.
******
Sosai ya zuba musu ido yana jin wani iri a gameda su gabadaya zuciyarsa ta ki yarda da su sosai gabansa yake faduwa ji yake kamar akwai mugun nufi a tattare da su sosai ruhinsa da zuciyaesa suke nuna masa shakka akansu idanuwansa sosai yake dubansu da su tun da yayi Parking a harabar asibitin ya tokare a jikin motarsa kira BMW yanayin su kawai yake kallo yake hango rashin gaskiya da kuma tashin hankali a tattare da su a hankali ya fara takunsa cikin natsuwa idanuwansa na kan su har izuwa lokacin kofar da zata sada shi da cikin asibitin ya dosa sai da ya zo daidai da su gabadayansu idanuwansu suka sarƙewa juna wani irin kallo suke duban junansu dashi kamar wanda suka san juna da jimawa zuciyoyinsu sai fama kawo musu wani lamura suke ma bambanta wanda su akaran kan su ba su na me nene ba.
Kau da kai Dr.Karami yayi da sauri yana gyara zaman niktayal din wuyarsa ya cigaba da takunsa ba tare da ya sake bi ta kan su ba har ya isa cikin asibitin.
Sannu a hankali ya fara takunsa yana ajje wa dakin su Mariya yanu fa yana kokarin sa kai itama ta sanyo kai zata yo waje kamar daga taji a kirjinsa da sauri cikin yanayi na firgici ta ja da baya tana mai zare idanu.
"Subhanallah!".
Ta fadi cikin tsanani kaɗuwa sosai take kallonsa shima idanuwansa na kanta sosai yaji wani irin Shock a ko ina na hanyar jininsa har sai da ya runtse idanuwansa domin ji yayi gabadaya kansa ya shiga juyawa kamar wanda wayar wuta ta zukar wa jini yayi low sosai
"Don Allah...".
Ta fadi tana mai rawar baki idanuwanta ta sauke su kasa sosai da sosai take jin ko ina na jikinta na sauri jininta yana kara gudu zuciyarta na kara sauti wajan bugawa.
Hannu ya daga mata yana mai sakar mata murmushi gami da lumshe idanuwansa sosai yake fuskartar natsuwar da take dashi sosai yake jin tana burgeshi duk da kananun shekarunta amma hankalinta na yanayin natsuwarta kamar mai shekaru sama da ashirin ko da yake duk wanda ya ganta ba zai taba bata haura shekaru sha biyar domin Mariya tana da tsayi da kuma kaurin jiki irin matan nan ne masu diri da cikar matantaka sosai ta ko wani fanni sosai jikinta yake bayyana irin baiwar kirar jikin da Allah ya bata ko ina na jikinta sosai ya cika sai dai ace yarinya ne a jikinta rintse idanuwansa yayi jin zuciyarsa na hasaso masa abubuwa ma bambanta da sauri ya zare tunani ya ajje gefe yana mai sauke numfashi.
"Yaa Allah! Mariya zaki fasa min kirji ko".
Ya fadi yana mai haɗe girarsa kamar gaske yanayin da ta dan razana ta dago kamt da sauri tana kallonsa lokaci guda idanuwanta sukayi rau-rau kamar za su zuvda hawaye.
"Don Allah...".
Da sauri ya kai dan yatsarsa bakinsa gami da furta.
"Shiit".
Yanayin yarda yayi salon sai ta saki baki tana kallonsa sosai taji ya burgeta da yanayin da murmushi ya sauka a fuskarsa ta tabbata wasa yake yi mata kasa tayi da kai ta dag laɓɓanta.
"Ban sani ba, ban san kana taho wa ba na rokeka...".
"Nace kiyi shiru mana!".
Ya fadi muryarsa da dan sauti a cikinta. Gyaɗa kai ta shiga yi tana kokarin giftashi ta wuce ya tae ta da cewa.
"Ina kike kokarin zuwa?".
Shiru tayi tama rasa mai za tae dashi sai juya faka din dake hannunta take mai dauke shara.
Sosai ya gane in da ta dosa amma so yake yi tayi magana da kanta amma ya lura magana ma wuya take mata
"koma ciki to tunda ba in da zaki".
Da sauri ta dago kanta tana kallonsa yanayin da taga ya ci mur ta san da gaske yake baki ta fara motsawa.
"Shara...".
Abin da ta fadi kenan ta tsuke bakinta ta sake yin kasa da kai tana cigaba da wasa da fakar dake hannunta gabadaya taji gajiya na saukar mata sosai ta matsu ta bar wajan amma ta lura Dr.Karami sai ya ga kafarta ta zubda ita kasa sannan zai rabu da ita.
"Ya jikin Umma?".
"Da sauki".
Abin da ta fadi kenan domin ta lura in dai yayi magana bata amsa ba hakan ne zai sanya ya hanata tafiya.
"Madallah! zaki iya tafiya".
Kamar wacce take jira da sauri ta fara jan jikinta har tana kokarin tuntuɓe sosai yake kallonta yana kallon yarda take ajje taukunta duk da dai cikin yanayin tsoro take amma hakan bai hana bayyanar da natsuwa a takunta ba sai da ya ga fitarta sannan ya numfasa ya karasa shiga dakin.
Tunda Mariya ta fice take gayyato natsuwa tana yafawa kanta sodai tsoro da kunyar Dr.Karami suke samun mazauni a zuciyarta sosai komai nashi yake burgeta sosai take jin wani iri in suna tare sosai zuciyarta ke natsuwa in suna tare amma a zahirince tsoro ne ke bayyyana a fuskarta ta rasa dalili ko da yake zata iya ajje hakan a matsayin Kwarjini da yake mata sosai musamman yanayinsa da cikar halintar mazanataka da yake dashi sosai take jin wani iri in tana gabansa sai ta raina kanta sai taga kamar dan tsako ne a gaban rakumi.
Har tasa inda za ta zubda sharar bata daina zancen zuci ba saura kadan ta afka cikin dan wajan da aka tanada don zubda shara ita kanta sai da taji kunya da sauri ta zubda sharar ta juyo domin komawa cikin asibitin taku kadan tayi da yake kanta a kasa yake sam ba ta lura da wanda yake gabanta ba gabadaya ta ji ta ci karo da mutum sosai ta tsoro zuciyarta lokaci guda ba wanda ta kawo mata sai Dr.Karami tunanin ya kawo mata wato yana biye da ita kenan lokaci guda ta sake tsora a ranta tana fatan Allah yasa bai ga halin da take ciki ba a dalilinsa.
Tunaninta ya tsaya lokacin da taji wani wari gami da kamshin tuarare sun haɗe waje daya sun ba da wani kamshi mara dadi don sai da taji zuciyarta ta fara tashi da sauri cikin tsananin haushi da takaici ta dago kanta ta sauke kan mutumin da ya kusan tafiya da numfshinta da sauri ta ja baya tana mai zare ido bakinta na ƙarkarwa sosai take kallonsa gabadaya take jin tsoro da dukan zuciyarta na karu yanayin da ta ga idanuwansa sun kaɗa sunyi jajir har wani launi duke sauyawa nan da nan ta shiga waige waige domin neman hanyar cetar kai sai dai sam hankalin mutane da suke kai kawo baya kan su da sauri ta ja da baya tana ambatar sunan Allah a zuciyarta lokaci guda ta ji wani irin takaici da haushinda ya sake turnuke ta kau da kai tayi domin ta fusakanci rainin hankali tsantsa yake son kawo mata sabo ya rainata ya raina girmanta ya ganta kankanuwa shiyasa ya sami lasisin da zai shigo rayuwarta ya yi abin da yake so saboda ya mai da ita marashin 'yanci in ba wai tanuna masa zahirin ta bane ta nuna masa ita ma mutum ce kuma ta san darajar kanta ba za su zauka lafiya.
"Na rokeka da Allah da Annabi ka fice daga rayuwata amma ka ki ji ko to bari in hadaka da Iyayenka kila a dalilin su ka bar ni".
Ta fadi tana kara tsuke fuska sosai idanuwana kansa amma sam bata ga yanuna wani alamun yin wani abuba sai ma kara wani yaƙe yake yi saman fuskarsa haka kular da ita sosai.
"ban san mai nayi maka ba, ban san mai yasa kake kokarin shigowa rayuwata ba, ban dan abin da ka gani a duniyata ba har kake kokarin shigowa na rokeka ka fita harkar ta bana bara ma da kai ko miskala zarratin".
"Mariya!".
Sautin muryarsa da ta doki kunnuwanta sosai hakan ya kara tsinka mata zuciya amma hakan bai sanya tsoro ya bayyana a fuskarta ba.
"karka sake kiran sunana kuma ina mai rokon ka da karka sake batar sunana mai so ka ajje sunan Mariya a matsayin wanda baka taba sani ba ko a Mafark...".
Gabadaya taji hannunta cikin nasa ya sarƙe waje daya ba ta san lokacin da ta saki fakar dake hannunta ba cikin tashin hankali tana kokarin kware baki ta kurma ihu taji ya saka dayan hannunsa ya rufe mata baki nan ta kara hargitse tana faman zille-zille domin kwatar kai amma ina ta kasa domin ji take kamar wacce aka daure da sarƙa idanuwanta suka kara yo waje sai faman nishi take yi amma ko a jikinsa sai ma faman murmushi da yake yi idanuwansa na kara hargitsewa waje guda a hankali ya zare hannunsa daga bakinta hakan ya ta damar sakin ihu amma ba mai sauti ba ganin irin alamu da yayi mata alamun shiru.
"kin fiye tsiwa Mariya".
Ya fadi yana kara sarke hannayensu waje daya yana murzawa kadan sosai take jik wani iri a jikinta ko wani sashi na hanyar jininta take jin yana tsayawa cak! da aiki sosai sumar wucin gadi ta ziyarceta a hankali ta fara rintse idanuwanta tana jin tashin hankali na samun ma sauki a kowa ni sashi na jikinta zuciyarta na kin abin da yake mata tsanarsa take ji sosai da sosai tana jin haushinsa na samun matsuguni a zuciyarta.
Sosai wani sashin zuciyarra ta shiga biya mata karatu.
'Ke fa mace ce akan mi zaki tsaya wani namiji gardi yana rike miki hannun kin san illar haka kuwa shin ko kin manta kalamansa da yake fadi miki a haduwarku ta farko'.
Sosai zancen zucin ta yayi tasiri a ko ina na sashin jikinta abin zuciyarta take sanar da ita a yanzu shi kawai ke amsa kuwwa a kunnuwant sosai take jin tana da karfin gwuiwar aikatawa in dai ita kadai ce hanyar da zata kwai kanta da mutuncinta.
Tun da Mariya ta kulle idanuwanta ya zuba mata idanu sosai yake kallonta sosai yake kallon fuskarta da laɓɓanta da suka tsuke waje daya sun yi jajir da su hancinta dan madaidaici mai tsayi idamuwanta da suke rufe haƙa suka kara bayyanar da girmansu yake sosai yake jin zuciyarsa na sauya salon wasu lamurka sosai yake jin komai na kwance masa sosai yake kallonta tana burgeshi.
Mariya da ta buɗe idanuwanta a daidai lokacin shi kuma ya shigar da laɓɓansa cikin bakinsa yana lasa ba ta san lokacin da ta daga hannu ta sauke masa zara-zaran yatsunta a kan kuncinsa ba ji kake Tasss!!.
"ji ba yar iskan ba ce ka sani ni 'yar mutunci ce kuma iyayena masu mutunce ne sun san daraja da kimata ba wai sun haifeni bane don kowa ni dan duniya ya zo wajena ya yashe ka sani ni da kake gani nafi karfin ka wallahi bar ganina karama wanda yake baka lasisin zuwa gareni da mugun nufinka to ka sani nayi maka nisa wallahi na wuce da saninka ni ba irin 'ya'yan da ake ribata bane har a bata masu rayuwa don haka ka kiyaye".
Ta karashe cikin yanayi na rashin tsoro ko abin da zai je ya dawo a da sauri ta fizge hannunta tana tsartar masa da yawu ta wuce abin ta.
gabadaya komai nashi yaji ya tsaya na jikinsa sosai ya ji sa wata duniya wacce mai san ta mene ne ba sosai sosai yaji kansa na juyawa sosai yaji komai ya kwance masa gani yake yi kamar bashi ba gani yake yi wannan lamarin da ya faru kamar ba gaske ba gani yake yi ko a mafarkinsa ban yi tunani haka ta kasance ma dan yatsansa ya saka a baki sosai ya ciza shi kamar zai tsinkeshi zafin da yaji ya ziyarce shi ne ya sanyashi sauri buɗe idanunsa ganin lamarin gaske ne bai san lokacin da wasu kwala suka taru masa a idanu ba da sauri yayi kokarin mai da su yana mai dafe kirjinsa ba abin da yake hangowa sai hannun Mariya lokacin da ta daga ta sauke a fuskarsa ba abin da kunnuwansa ke jiyo masa sai yarda sautin marin ke sauka a kan fuskarsa.
Sosai kalaman da ta furta suke dawo masa sosai yake jin wani irin yanayi na zarya cikim gudu suna samun masauki a ransa sosai yake jin wani katon abu mai nauyi na samun masaukin a zuciyarsa da kasan ruhinsasosai yake jin wani irin abu maɗaci da bauri na sarƙe masa harshe sosai kalmar MUTUNCIN tana dashi yake amsa masa kuwwa a ko wacce dakika gyaɗa kai ya shigayi gabadaya ya kasa motsawa lokaci mai tsayi ya dauka a haka har zuwa lokacin mai gama tantacce abin da ya faru dashi gskiya bane.
"Uhm ai ita dama WUYA MAKARANTAR KARE ce wallahi".
Abin da muryar Khairiyya ta fadi kena tana dosa in da yake sosai take masa wani irin kallo na raini da takaicin abin da ya faru sosai take jin ɗaci a ranta musamman yarda taga komai ya faru akan idom ta ba abin da y kara tsikar mata da zuciya sai Yainyar da ta gani wai akanta Huzaifa yake zaucewa ta rasa ma mai ya dace tayi ji take kamar ta tsinke shi da mari amma ina! ba za ta iya ba a hankali ta fara riko hannunsa ta na murzawa sannu a hankali ta fara jansa tamkar rakumi da aƙala har suka isa wajan motar gidan baya ta buɗe ta turashi cikin wani irin yanayi kamar wanda akayi wa dukan shan gishiri.
Sai da ta kare masa kallo sosai da sosai tana kallon yarda ya rintse idanuwansa kirjinsa na harbawa da sauri-sauri kamar zuciya zata fasa ta fito kau da kai tayi jiki a sage ta koma gidan gaba wajan zaman direba ta shiga ta tada motar cikin wani irin yanayi ta fizgi motar har sai da kura ta tashi ta fice daga harabar Asibitin.
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA HUDU.
Hannu bibbuyu ta zabga tagumi idanuwanta kan Mu'azzam. sosai take kallonsa tana jin wani irin abu na sauka kan zuciyarta da ruhinta, sosai take jin wani abu mai kama da ruwa yana kwaranya a ko wani sashi da loko na ma'ajiyar zuciyarta, komai take ji yana yi mata wani iri sosai take jin kauna da so mai girma na saukar mata akan kaninta ba abin da take nisawa a ranta sai yarda duniya lokaci guda take shirin juye mata da wata irin ƙaddara mai girma a rayuwarta. sosai take jin duniyar na wargajewa da dukkan wani farinciki mai girma, da ta san tana samu cikin kankanuwar rayuwarta.
Ya za tayi kenan in ta rasa wadannan madogaran rayuwarta ta mai duniyarta za ta kwaso mata in ta rasa wadannan mutane masu matukar muhimmanci a duniyarta.
Wasu hawaye masu zafi matuka taji suna sauka akan fuskarta da can cikin zuciyarta da ruhinta.
Ta sani kuma ta dade jimawa cikin duniyarta ba ta da sa'a a rayuwarta domin kuwa sosai ta fuskata ƙaddara mai kaifi ce ta fado mata da abubuwa masu matukar tashin hankali da yankewar farinciki Babanta ya tafi ya barta ga Ummanta bata da lafiya ga karamin kaninta wanda shi ƙaddara ta sunkuto shi cikin wannan duniyar mai dauke da kwamatsai rashin dadi ina ma tana da dama ina ma tana da iko ina ma ta san zai fado duniyar nan a haka da bata yarda ba da bata amince ba ina ma ace ana tuntuba kamin a sako dan'uwa duniya da ta roki ubangiji bai sako kaninta ba sai dai ba yarda ta iya komai na Allah tabbatacce ne a duniyar dangin rai kana naka yana nashi.
Hannu ta sanya tana mai dauke zafafan hawaye da take jin su a ko ina na sashin zuciyarta tana dauke su wasu na biyo bayan su tana jima cikin wannan yanayin kafin ta motsa ganin Mu'azzam yayi barci ta kai shi makwancinsa ta kwantar bayan tayi Hugging din sa a ko ina na fuskarsa sosai take jin kauna mai girma a tsakanin ko ina na sassan jikinta akan shi sosai take hango wa a duniyar nan bata da kowa dangin yan uwa sai shi dole ta kula dashi dole ta so shi domin shi kadai ne take zaton zai shafe duk wani daci da kunci da ukuba da take ji a zuciyarta na rashin yan uwantaka.
A hankali ta fara takawa har inda Umma take kwance ta na barci hankali kwance kallo daya zakayi mata ka tabbatar akwai alamun warakar natsuwa a tare da ita. Idanuwanta sosai ta buɗe akanta tana kallonta kamar wacce aka ce in ta dauke idanuwanta za a gudu da ita zuciyarta taji tana wani amsawa da wasu abubuwa mabambanta wanda ita kanta ba za ta ce me nene ba.
Wani murmushi ya subuce mata kalaman Dr.Karami suke mata yawo a kunne a jiya bayan ya zo ya duba Umma.
****
Kallonta yake yi sosai yana yawatawa da idanuwansa masu wani irin yanayi mai matukar kashe jikin wanda ake kallo sosai take jin kallon nasa na shiga duk wani sassa na jikinta yana haifar mata da wasu abubuwa wanda ba ta san a mizanin da za ta ajje su ba sosai take jin bugun zuciyarta sosai take jin yarda zuciyar ta ta take tsalle a duk wata dakika daya na kallon da Dr.Karami yake yi mata ta rasa mai yasa take jin haka ta rasa dalili lokaci da dama ana kallonta mutane masu muhimmanci a idanuwanta amma bata jin haka sai a kansa shi kadai kwallin kwal!.
"Mariya".
Yarda Dr.Karami ya ambaci sunan sai taji aduniyar rayuwarta bata taba jin wanda ya kira sunan da wani irin yanayi mai matukar amsa kuwwa a kwakwalwa da kashe jiki da sanya zuciya tsalle tsalle kamarsa ba sosai take jin duk wani sashi na jikinta na wani irin amsawa da narkewa kamar ana narka roba a wuta wani numfashi take ja mai matukar girma wanda take ji kamar in har batayi jarumtar jan sa ba numfashin katsewa zaiyi daga gareta kanta a kasa tana faman wasa da kasar rigar atamfar ta da take jikinta wanda kallo daya zaka yi mata kasan taji jiki sosai da sosai.
"kin fiye kunya da yawa. Ya kamata zuwa wannan lokaci ki saki jikin ki da ni domin an zama daya".
Wani irin kuwwa taji maganar tasa ta nayi cikin kwakwalwarta ji take kamar kasa ta tsage ta zurma ciki sam bata son yarda Dr.Karami ke mata amma kuma ta na son ta zauna dashi sosai a waje daya domin mutum ne mai saukin kai da kokarin kwantarwa da mutum hankali.
A hankali take daga kai domin ita dai ba ta san mai zata ce dashi ba bama ta san yarda kalaman nasa su ke zuwa ba cikin kwakwalwarta ita dai kawai sautin muryarsa take jin na amsa amo nata.
"kin ga dai yau kuna cikin kwana na Arba'in da takwas kin ga kenan yau saura kwana goma sha biyu su cike KWANA SITTIN da nace in Allah ya yarje mana komai zai daidaita a wajan Umma. Shin ya kike ganin jikin nata me kike karanta game da ita?".
Ya dasa aya yana mai dubanta sosai cikin idanuwansa yana faman murmushi yana gyada kai sosai yake jin Mariya na samun masauki a zuciyarsa da duk kan wani sashi na jikinta sosai yake jin ta tamkar uwa daya uba daya suke sosai yake jin wani abu mai girma yana samun waje a filin zuciyarsa yana zama wanda a kullum yana jin yarda yake daɗuwa ba wai raguwa ba murmushi ya sake yi.
"ban san mai zan ce miki ba, ban san ya kike rayuwarki bs, ban san mai yasa ba ki sakin jiki da mutum ba, ban san mai yasa kike gujewa mai...".
Sosai yaji kalmar da zai fadi tayi nauyi a bakinsa ta danne harshensa da wani gingimeman abu mai girma sosai yake buɗe idanuwansa akanta wani irin bugu yake jin kirjinsa nayi bai san mai zuciyarsa take kokarin yi ba bai san abin da take kokarin dauko masa ba wanda sam bai yi tunanin haka ba.
A hankali take dago kanta tana kokarin ajje idanuwanta akansa cikin yanayi na TUHUMA tana jin yarda zancen da yake yi ya yanke wanda take jin alamun akwai dalili kamar wani abu ne daban ya hana shi furta abin da yake kokarin cewa ko da dai ita akaran kanta ba ta san ina ya dosa ba kallo daya tayi masa ta kau da kanta jin yarda jikinta da zuciyarta sukayi wani irin tsalle.
Girgiza kai ta shiga yi tana tura laɓɓanta cikin bakinta tana tsotsa kamar wacce ta samu alawa ta rasa mai zata ce masa bata san abin da ya dace ta ce dashi ba sosai take hango wasu abubuwa da suke rikirkita mata lissafin kwakwalwarta a idanuwansa sosai take jin abu mai girma game dashi sosai take hango kwarjini da haiba na dandatsa ko ina na cikin idanuwanta in ta dube shi can kasan makoshi ta fara kokarin furta wani abu a hankali laɓɓanta suka shiga motsawa.
"Ban san yarda zan fuskance ka na ce da kai komai ba, ban san da harufan da zan yi amfani wajan cewa da kai komai ba amm...".
Da sauri taja numfashi gami da tafiya da sauran abin da tayi niyyar cewa.
Sosai ya ware idanu yana kallonta yana ganin yarda take datse laɓɓanta kamar wacce take tsoron furta wata kalma mai muni gareshi.
"Fadi mana ko ya kike zo da maganar ki zan fahimta ba zan ajje ta a mizanin da bata dace ba".
Ya fadi yana kara ware idanunsa sosai akanta wani matsayi yake jin ta na kara samu a gareshi sosai yake hango natsuwa da kula da kai tatttare da ita a hankali ya mike kan kafafuwansa yana duban in da Umma ke kwace tana barci Mu'azzam kusa da ita murmushi yayi kafin ya juyo ya dubi Mariya da take tsaye kikam! kamar wacce aka dasa gabadaya ta gama tafiya cikin wani irin yanayi, ba abin da take roko a ranta illa Dr.Karami ya tafi ko ta samu damar jan numfashi mai dauke da iskan Rahama.
"na tafi Mariya tun da yau na lura azumin magana kike yi".
Yana gama fadin haka ya fara taka kafafuwansa kamar da gaske tafiyar yake yi so yake yi ta dago ta kalle shi haka kuwa akayi tana jin tafiyar tasa tayi nisa gabadaya ta dago da idanuwanta aiko sai suka sarke da nashi ba ta san lokacin da ta saki kara ba gami da ja da baya tana runtse idanuwanta sosai ta sanya tafukan hannunta ta kara rufewa wata irin kunya take ji tana yawatawa a dukkan sasssan jikinta ji take kamar kasa ta tsage ta shige.
Sosai ta bashi dariya ganin yarda tayi a hankali ya taka ya fice daga dakin yana faman sakin murmushi wanda shi kansa mamaki yake yi komai na Mariya na burge shi sosai da sosai.
****
"Yaa Allah!".
Abin da ta furta kenan tana sakin murmushi gami da dafe kai bata san abin da ya shiga kanta ba gabadaya take jinta wani iri sosai take jin ta a wani irin yanayi in tana zaune ko suna tare da Dr.Karami rintse idanuwanta tayi gami da jan numfashi wani kamshi ne taji numfashin nata ya jawo mata ya kai mata cikin hanci a dan firgice ta ware idanuwanta tana Ambaton Allah tsoron ta daya Allah yasa ba Dr.Karami bane domin ko tantama bata yi wannan kamshin nasa ne amma bisa mamaki ba kowa da ta gani ajiyar zuciya tayi tana dungurin kanta domin ta tabbata sharrin tunani ne kawai da na zuciya suke mata haka.
*****
Dakiku masu dama ta dauka cikin motarta kafin ta fara kokarin buɗewa ta ziro kafafuwanta zuwa waje nan ma sai da ta ajje dakiku sannan ta fara kokarin ziro da gangar jikin zuwa waje ta mike kan kafafuwanta sosai take yawatawa da idanuwanta izuwa wajen da take tsaye tana faman yatsine fuska duk da bakin glass din da ya rufe mata idanu hakan bai hana bayyanar yarda take yi da fuskarta ba cikin wani irin yanayi ta tura murfin kofar gami da sanya mata secure kafun ta fara kokarin jan kafafuwanta.
Sanye take da wasu kaya riga da wando fitted sosai wandon ya matse ta wanda iyakarsa gwaurinta mai kalar pink rigar dake jikin yar shara-shara ce mai kalar white da hannayen rigar ves ne wanda hakan ya bayyanar da rabin kirjinta sosai da ilahirin damatsan hannayenta fuskarta dauke take da Make-up sosai hakan ya kara ƙawata fuskarta ta laɓɓanta sun sha pink din jan baki sai daukar idanu suke gashin kanta ya ci gyara sosai sai fama daukar idanu yake yi ta barbaza shi a gadon bayanta a hankali take takawa saman takalamanta masu matukar tsine sosai komai nata motsawa yake a duk lokacin da tayi taku daya.
Sannu a hankali har ta isa cikin wajan wanda kallo daya zakayi masa ka tabbatar da wani babban ma'aikace bene mai dauke da hawa goma sha biyu daga yanayinsa in ka kalla sai ka rantse ba a kasar najeriya yake ba.
Kofar da zata sada ta cikin wajan ta dosa mutane da yawa masu harkokin gaban su sai bin ta suke da kallo na mamaki har ta isa kofar glass da take watayawa da mutane domin zuwa duk wani bene da suke bukata.
Ba tayi kokarin barin baban Falon dake kasa na cikin ma'aikatar ba domin ba ta bukatar haka koma ta bukata dole tayi hakuri a dalilin rashin sanin in da ta dosa ko ta shiga yau ne karo na farko da ta tako kafafuwanta zuwa cikin wannan waje yau ne farko da ta fara ajje idanuwanta akan wannan waje a zahirance yau ne kuma take bukatar duk wasu mafarkanta su tabbata yau ne take so ace sun yi gaba da gaba da shi yau ne take so komai ya zo kamar yarda ta jima tana burin abubuwa daban-daban kafin wannan rana tana so ace wannan rana ta kasance cikin ranakun da nasarrorin ta za su fara shawagi cikin duniyarta yau ne take da yakinin lissafinta zai fara aiki kamar yarda ta tsara komai nata...
"Madam!".
abin da securty din wajan babbar kofar da suke zaune daya daga cikin su ya fadi kenan yana mai mikewa bisa kafafuwansa ya tsaya gabanta.
Da sauri ta dawo daga duniyar tunanin da take yi ta sauke idanuwanta gabadaya akansa tana wani yatsine fuska gami da da sauke glass din fuskanta kadan manyan idanuwanta farare fes suka sauka akansa sai da ta gama kare masa kallo kafin ta gyaɗa kai cikin nuna halin-ko-in-kula gareshi.
Shima bai damu da irin kallon da take masa ba haka ya sanya abin binciken dake hannunsa yana yawatawa dashi a sassan jikinta kafin ya dago kai ya dubeta yana mai bata hanya domin karasawa wani murmushi ta saki wanda ita kadai ta san in da ya saka gaba a hankali ta kama Handle din kofar ta tura cikin wani irin taku na musamman wanda kallo daya zakayi mata kasan akwai abin da ta taka karan takun takalmanta bisa tayal din dake shimfiɗe a harabar wajan duk ya karkato da mafiya yawancin mutanen da suke zazzaune suna gudanar da aiyukansu kowanne mutum daya akwai table a gabanda da kuma fiyal fiyal gefe guda kuma kwafuta ce girki tacin glass dinta take ƴawatawa da idanuwanta a dukkanin sassa da kowa ni mutum dake zaune sosai ta lura ita suka zuba wa idanu murmushi ta saki har gefen kumatun ta na loɓawa sosai taji wani abu na yawatawa a cikin kirjinta wanda take jin sa ba abin da ke cikin sa sai hango abubuwan da take tsammanin za su faru.
"Heyy".
Abin da ta fadi kenan gaban wani table da wata mace ke zaune hankalinta gabadaya ya ta'allaka ga aikin da take yi sanye take da jallabi mai kalar Ash ta nannaɗe fuskarta da kallabin jallabiyar fuskarta fayau ba wata kwaliyya ta azo a gani amma hakan bai hana bayyanar tsantsan kyan da Allah yayi mata baiwarsa ba.
A hankali ta fara dago kanta ta na saukewa a in da ta ji maganar sosai ta ware idanu ganin wacce take gabanta cikin yanayi na mamaki da wani irin haushi da ya kasa boyuwa har sai da ya fito cikin idanuwanta gyaɗa kai tayi kafin ta mai da kanta kan Aikin ta.
"Dr.Abdurrazaq Erena".
Abin da ta fadi kenan tana mai wani kara bayyanar da wani murmushi dake fuskarta wanda kallo daya zakayi masa ka san ba a so ba.
Ba tare da ta dago da kallonta ba murya kasa kasa.
"Hawa na biyar hannunki na dama office mai lamba Uku".
Ba ta tsaya ansa ta ba ta dauko kafafuwanta ta fara tafiya a haka har ta hau Abin da zai kaita wajan cikin yan sakanni ta isa bayan ta sauka ta kalli kwatance da kayi mata wata kofa glass ta hango sannan ta kalli samanta murmushi ta saki ta fara takawa a hankali ta isa sakatariya ta gani zaune tana ta faman aikinta hankali kwance kwankwasa kofa glass din tayi kadan tana mai kallonta cikin wajan a hankali ta dago kai ita ma ta sauke a kanta murmushi akan fuskarta lokacin da ta dago amma tana cin karo da wacce ke gabanta ta tsuke fuska hadi da jan guntun tsaki tana kau da kanta.
Sai da ta shafe sakanni kafin tayi mata alamun ta shigo a hankali ta taka ta shiga ta dan yi kasa da glass dinta ta shiga motsa laɓɓanta.
"Please wajan Dr. Abdurrazaq Erena nake bukatar zuwa".
Kallon ban gane ba sakatariyar tayi mata tana mai kwaɓe baki kafun ta kau da kai hadi da fadin.
"Ya san da zuwan ki ne?".
Shiru tayi ba tare da cewa komai ba na yan dakiku hakan ya kullar da sakatariyar da sauri ta shiga duba cikin kwafutar dake gabanta tana yawatawa da idanuwanta cikinta.
"Duk yau a cikin jerin mutanan da za su zo gare shi ban ga alamun da ke a ciki ba".
Ta fadi tana mai dago kanta ta saukewa gareta.
a dan harzance ta sauke glass din ta sosai idanuwanta kan sakatariya kallonta take yi tana karantar yanayin da alamun so take ta samu wani tangarɗa da zata jona mata amma cikin nuna na fiki.
"ki je ki ce masa Areefa Saifullah ita ce take son ganin sa ya san da zuwana".
Yanayin yarda take maganar a dake da yanayin bacin rai ya sanya sakatariyar ware idanu sosai gami da tallaɓe haɓa tana kallon yarda wannan mai kalar gangar ke mata magana akai.
A hankali ta mike saman kafafuwanta masu sanye da wasu takalma masu matukar tsine kamar za su karye a hankali ta fara taku da dan guntun suket dinta wanda iyakarsa guiwa kadan taɓe baki Areefa tayi tana bin dumemiyar matar da kallo wacce tayi biyunta.
Mintina kalilan sai gata ta dawo tana faman tsuke fuska.
"ki Shigo kofa ta uku ita ce in da yake ciki".
Gyaɗa kai kawai tayi gami da wucewa tana taku ko ina na jikinta rawa yake yi lokaci guda ta canza tafiyar da take yi ita dai sakatariya sakin baki tayi tana kallon ikon Allah har sai da Areefa ta bace mata sannan ta saki ajjiyar zuciya ta koma ta cigaba da aikin da take yi.
"Areefa Saif...".
Abin da ya fadi kenan yana hanzarin mikewa cikinsa har ɓari yake yi ya zagayo izuwa in da take tsaye hannunta rike da Handle din kofar sai faman yawatawa da idanuwanta take yi cikin Office din har ya iso ya tadda ita nan tsaye sai faman sakin wani murmushi yake yi hakan ya bayyanar da wawulan hakorin sa daya na gaba da ya cire amma in ba ka gane ba sai kayi zaton wushirya ce ta buɗe sosai a jerin hakoransa masu dan duhu kadan.
"Ban yi zaton ai yau zaki zo ba, domin Alhaji Abdulwahab ce mani yayi sai nan da gobe".
Ya fadi har lokacin idanuwansa na bin duk wani sashi na jikinta yana kallo kafun ya yi mata nuni da kujerun dake cikin office din alamun taje ta zauna sosai take kallonsa ta cikin glass dinta tana karantar yanayinsa sosai take hango komai kamar ma ya yuwu kallonsa take yi tun daga fuskarsa har kafafuwansa babban mutun ne don a kalla zai baiwa shekaru hamsin baya amma hakan bai nuna a fuskarsa ba saboda yanayin huta da jindadi da suka taimaka ma jikin nasa baki ne amma ba can ba yana da idanuwa masu dan girma sun dan yi ja kadan hancinsa ba dogo bane yana da fadi haka ma bakinsa mai dauke da manyan laɓɓa masu kalar baki baki haka zai tabbatar ma da yana shan wani abu.
Ba tare da ta ce da shi kala ba ta doshi cikin Office din sosai tana wata irin tafiya ta firgita duk wani namiji da yake gabanta har ta isa ta zauna ta ajje jakar dake hannunta gami da daura kafa daya kanta daya a hankali ta sauke glass din dake fuskarta gabadaya shima ta ajje shi kan Table din dake gaban kujerun ajje numfashi tayi alamun gajiya gami da dan dafe kai.
A hankali ya fara takowa in da take kallo daya zakayi masa kasan sosai Areefa ta tafi da guntun imaninsa jikinsa sai ɓari yake yi fuskarsa tana sakin murmushi idanuwansa kamar za su fado kasa.
"Areefa Saif...".
Ya sake fadi cikin salo na yin kasa da murya kamar wanda yake rokon wani abu a gareta.
Kaɗa idanu tayi gami da dan daga girarta tana mai yawatawa da idanuwanta akan sa zuciyarta nayi mata wani tsalle na murna da jin wani dadi amma bata bari hakan yayi tasiri a fuskarta ba domin a gimtse take ba alamun dariya.
A hankali ta fara motsa laɓɓanta da wani irin yanayi tana mai kaɗa idanuwanta.
"Ya kamata ace ka koma ka zauna domin time dina a tsare yake akwai in da zan je ne".
Ta fadi tana da murmushi a fuskarta da sauri ya ja gefe gami da ware idanuwansa sosai ba tare da yace komai ba ya koma can inda kujeransa take mai juyawa ya zauna gami da saka kan biro a bakinsa yana cizawa kujerar na watayawa dashi idanunsa akanta sai faman sakin murmushi yake yi a hankali ta kau da kai gami da tura masa fiyal din da ta zo dashi.
Hannusa guda ya kai yana janyo fiyal din yana mai sauke idanuwansa akansa buɗewa yayi a hankali yana yawatawa da idanuwansa a cikin tsayin minti daya kafun ya mai da ya rufe ya dan bugeshi kadan ya dago kansa ya dubi Areefa wacce ita ma hankalinta na kansa ta na kallon yarda yake duba fiyal din.
"Komai yayi daidai zaki iya fara aikin zuwa On Monday in kuma akwai Time din da kika zaba zaki iya amfani dashi...".
Hannunta ta dan daga kadan tana dan murmushi.
"No ba ni da wani lokaci sai wanda ka yanke mani domin ina bukatar fara aikin ne akan lokaci ba tare da zabina ba sai zabin da kuka bani".
Ta karashe tana mai mikewa kan kafafuwanta gami da daukar jakarta ta.
"Ina Godiya".
Ta fadi tana mai kara sakar masa murmushi shi dai idanuwansa har zuwa lokacin suna kanta kamar wanda aka jona wa mayen karfe har ta fara taku amma bai motsa ba motsin Handle din da ya ji ne ya fargar dashi da sauri ya ware idanu yana kokarin tashi amma ina kafun ma ya kai ga tashi ta fice daga cikin Office din komawa ya yi ya zauna jikinsa ba kwari hannu bibbiyu ya tallaɓe haba da su yana kallo kofar yana faman sauke numfashi a hankali.
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA UKU.
Kai komo kawai take yi a tsakar dakin ako wani takunta daya sai ta dubi Huzaif tana mai ajje numfashi sosai da sosai take jin haushinsa da takaici akan abin da ya aikata sosai take kallon abin a matsayin babban kuskure mai girma sosai a idanuwant sosai take ganin wautarsa da ganganci da kuma yada zuciya kare ya dauke.
Numfashi ta ajje bayan ta tsaigata da kai komon da take yi sosai ta ajje ganinta akansa.
"kasan kuwa abin da ka aikata kasan kuskuren da ka aikata ya girmama sosai a idanuwa...Well bana tunanin kai lamarin ka dauke shi a matsayin kuskure mai girma a idanuwanka".
Ta fadi tana mai cizon laɓɓanta bayan ta turasu cikin bakinta sosai zuciyarta ke zafi da raɗaɗi akan komai da ya aikata sosai take jin abu mai nauyi ya tsaya mata a kirji ya samu gurbin zama sosai take jin tamkar ita ce akayi wa wannan cin kashin.
"Bana tsammanin Huzaif din dana sani ne wannan bana tunani Huzaif din asali ne wannan anya kuwa ba wasu abu akan ka ba na tunanin abin da kake sha zai sanya ka aikata wannan kuskuren mafi girma a idanuwana".
Ta sake fadi tana mai girgiza kai sosai take jin komai da ya faru yana dawo mana ina ma tasan hakan zata kasance da tabbas sai Mariya ta raina kanta kamar ta yarinya karama har tasan ta daga hannu ta mari namiji namijin ma Huzaifa.
"Kaico!".
Cikin wani irin sauti ta furta kalmar tana jin ɗacin lamarin ako ina na zuciyarta da ruhinta.
Harɗe hannayenta tayi a kirjinta tana kallon yarda komai na Huzaif ya canza sosai take ganin lalacia tsakanin idanuwansa da zuciyarsa sosai take hango gazawa a gareshi kau da kai tayi domin in har ta cigaba da dubanda da ganinta tabbas zuciyarta zata iya bugawa don tsananin takaici.
"Yaa Allah ta ya ya zan dubi wannan lamarin a wani MIZANIN HANKALI ya dace na ajje wannan lamarin bana tunani ko mai tabuwar kwakwalwa zai iya abin da ka aikata...".
"KHAIRIYYA".
Muryar Huzaif ce ta karaɗe dakin cikin wani irin sauti mai tsoratarwa cikin rashin tsammanin samun maganarsa ta ji ya ambace sosai ta saki zaren kalamanta ta saki baki tana kallonsa sosai take jin gabanta na bugawa gabadaya ganinta ta ajje a fuskarsa komai na shi take kallo da yarda tashin hankali da bacin rai suka nuna a filin komai nashi har zuwa lokain idanuwansa a rufe suke hannayensa saman fuskarsa sai faman juya su yake yi.
"Excuse me. Please".
Abin da ya sake fadi kenan idanuwansa a rufe tana kallon yarda laɓɓansa suke rawa sosai wajan furta ko wani harafi guda na kalaman da ya furta.
"ki bar ni naji da abin da ke kokarin yayyaga mani zuciyata please ki barni naji da abin dake kokarin tafiya da ruhina sosai da sosai nake jin bani bane Khairiyya bana zaton ni Huzaif".
Yanayin yarda laɓɓansa ke rawa da yarda kalaman nasa suke turereniya ga junansu hakan zai tabbatar maka akwai tashin hankali mai girma a zuciyarsa da ruhinsa wanda bai yi zaton wanzuwansa ba a duniyarsa sosai komai na tashin hankali ke bayyana kansa a ko ina nasa.
Rintse idanuwa Khairiyya tayi sosai da sosai take jin wani abu mai nauyi na samun gurbi a zuciyarta sosai da sosai take jin zata iya daukar kowa ni tashin hankali da take hangowa cikin idanun Huzaif ba za ta iya daura ganinta ta cigaba da ganin halin da yake ciki ba ba za ta iya cigaba da jin numfashin sa mai cike da tashin hankali ba.
A hankali ya fara kokarin daga dan yatsar sa dake fama karkawa sosai yake jin wani iri cikin zuciyarsa da inda take zaune a kirjinsa gani yake kamar wauta ya tafƙa sosai a duniyarsa amma ban yi amanar haka a zuciyarsa ba hango Mariya yake yi a matsayim wacce take kokarin kashe kan ta da kanta domin kuwa sosai ta dauka wa kanta fitinar da ba zata iya saukewa kanta ba sosai yakke ganin hauka cikin komai da take aikatawa sosai yake ganin rashin kunya da fitsara tsantsa cikin idanuwanta dole ya dau mataki ko ba komai ya koya mata rayuwar duniyar nan da yarda 'ya mace bata isa ta galaba akan ko wani ɗa namiji ba dole ta san waye HUZAIF ABDURRAZAQ.
A hankali ya mike yana duban Khairiyya da ta zuba masa idanu sosai murmushi yayi gami da dauke kan sa.
"You can go".
Abin da ya fadi kenan ya fara daga kafafuwansa cikin wani irin yanayi mai cike da abubuwa marasa dadi ga zuciyarsa Toilet ya nufa har zuwa lokacin idanuwan Khairiyya na kansa sai faman suke numfashi take yi a sauri-sauri sosai take jin wani iri a zuciyarta sosai take hango abin da zai dauko mata tashin hankali ya ajje mata a rayuwa sosai take hango abin da zai hanata rawar gaban hantsi a duniyar Huzaif sosai take hango komai na wargaje.
Numfashi take ajjewa mai dauke da abubuwa masu yawa da take zaton za su sayo mata tashin hankalin rayuwa a hankali ta daga jakarta zuwa kafatar tana faman gyaɗa kai kawai take yi tana tana jin wani abu mai nauyi na sakar mata a zuciya da duk wani gurbi na cikinta a hankali ta fara takunta domin ficewa daga dakin zuciyarta na wassafo mata abubuwa ma bambanta.
********
Sosai da sosai take jin wani irin tashin hankali na kokarin samun masauki a ko ina na sassan jikinta sosai take jin yarda kwakwalwarta ke kwala ihu akan tunanin da ya zo mata a bazata sosai take jin wani sauti mai kara sosai yana amsa kuwwa a kunnuwanta sosai.
Bugun zuciyarta yake kara sauri sosai da sosai takun da take yi da kafafuwanta suke aika mata da wani lamari na daban wanda yake kara hargitsa tunaninta idanuwanta a rintse suke komai take hangiwa komai da komai da ya faru yake dawo mata baya kamar yanzu ne yake faruwa a gigice take ajje numfashi mai tauri a kokarin janyo mata ruhi zuwa waje.
Bata san lokacin da tayi cilli da fakar dake hannunta ba ta sanya hannayenta zuwa kunnuwanta ta rufe su ji take kamar za su tarwatse dalilin sauti da ke musu sukuwa a ko wacce dakiƙa.
"Yaa Allah!".
Abin da ta furta kenan a kasan laɓɓanta cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa a gareta jin gina tayi da kofar da zata sadata da cikin dakin gabadaya taji kafafuwanta na kokarin gaza daukar gangar jikinta ji take yi kamar jikin ba nata bane sosai take hango fuskarsa tun ranar farko komai yake dawo mata har izuwa wannan lokacin sautin saukar marin da tayi masa take ajin yana samun wajan ajje sautinsa a bangarori masu yawa daga sassa na jikinta sosai take hango wautar ta cikin aikata wannan kuskuren mai girma da zuciyarta ke ganin tayi sosai take ganin girmar lamarin na kara girmama a zuciyarta da tunaninta.
'Mai ya kai ta, mai ya kai ta aikata wannan danyen aikin, ta ya ya ma haka ta faru gareta tun da take ba ta taba marin wani mai girma kamarsa ba ko da bai kai shi ba bata taba mai yasa tayi haka ina tunaninta ya kai ta lokacin ina zuciyarta ta cilla a lokacin mai yasa bata hana ta ba'.
Gyaɗa kai kawai take yi cikin daukar tashin hankalin da taji yana kawo mata hari, ta tabbata ba zai yafe mata ba, ta tabbata ba zai rabu da ita ba, ta tabbata zai shigo duniyar rayuwarta.
Ta ya ya ta wacce suffa zai zo mata?
Tunani da zuciyarta ke ta hasko mata ke tana kara gigita mata kwakwalwa da lamarin da take kara girmamashi.
Abu taji mai dumi na saukar saman kumatunta ko bata tabbata ba ta san Hawaye ne bayan HAWAYEN ZUCIYA da taji ma tana yi abin har ya kai ga bayyana dole ta firgita da lamarin ita Mariya ta mari wani wanin ma mai girma girman da ya dace ace ta ganshi ta daraja shi amma ina! ZUCIYA BATA DA K'ASHI.
'Akan mi akan wani dalilin zaki damu kan ki. Kina zaton in da ya cimma buri akan kudirinsa a kan ki tashin hankalin da za ki shiga mai ya girmema wannan ba kawai don mari har zaki bari tashin hankali ya yi girma mafi girma gareki karki yi sake har wannan kankanin abun ya hanaki abubuwa cikin rayuwarki'.
Wani sashi na zuciyarta ne taje tana amayo mata sautin zantukan nan.
Sosai tayi shiru tana nazarin kalaman sosai komai taji yana kokarin dawo mata daidai a hankali ta fara gyaɗa kai tana jin yarda zuciyarta ta cigaba da wanzar mata da wasu batutuwa masu girma a gareta.
'Shin in da ya keta miki haddi mi kik zaton zai faru dake a duniyarki'
Numfashi mai girma ta ajje gami da buɗe idanuwanta gabadaya sosai take kallon kanta sosai take kallon yanayin kankatarta tana kara nasarin abin da ta aikata a hankali komai da zuciyarta take fadi mata ya fara tasiri sosai a kanta sosai da sosai zuciyar ta dake komai na tsoronsa ya kai sai dai abu daya da take jin sa a zuciyarta duk a dalilinsa sai dai bata dan me nene ba bata san a me zata fassara shi ba sai dai zata iya barin sa a matsayin 'Mala' har zuwa nan gaba.
A hankali ta fara daga kafafuwan ta da taji sunyi mata nauyi kamar an daura mata wani abu da yai karfin girman jikinta sosai take kokarin amfani karfin zuciya tana jansu tana sanya hannayenta tana dauke guntayen hawaye da suka zobo mata sosai take takaicin zubarsu akan wani can wanda bai san darajarta ba mai san kimarta ba mai san martabar ta ba...
"Mariya".
kamar daga sama taji sautin muryar ya sauka a kunnuwanta da sauri ta ja kafafuwanta da take ja daƙyar ta ajje su waje guda ko ba a fada mata ba ta san waye hakan ya hanata juyawa domin adaidai wannan lokaci tana bukatar zaman kadaici ita kadai ba ta so ta sake daukar wani abu da zai so canja masa lissafin da take faman yi azuciyarta runtse idanu tayi jin takunsa na isowa gareta sosai take nuna rashin so wani abu a yanzu sosai fuskarta ta bayganar da haka.
A hankali ya isa gareta hannayensa sarƙe a juna jikinsa sanye da wani lallausar boyel mai kalar fari anyi masa dinki babu wuyar rigar an mata aiki da jare mai kyallin gold sosai kayan suka dace da jikinsa kansa sanye da hula ita ma dai kalar kyallin Gold ne doguwa ya dan rangwafar da ita kamar yarda yarbawa suke yi fuskar nan tashi fayau ba zaka ce ya hau shekaru talatin a duniya.
Sosai yake karantar yanayin ta da yarda ya hango damuwa dauke a fuskarsa sosai yaji rashin jin dadi a ransa ciza laɓɓansa yayi kafin ya gyaɗa kai.
"akwai abin da ke damunki Mariya".
Ya fadi yana sake kafeta da idanuwansa manya sosai take jin rashin son magana a daidai wannan lokaci amma ba za iya ajje Dr.Aqeel a matsayi marashin girma gareta ba tana jin sa sosai a ranta da irin ALHERI da yayi a rayuwarta.
"Uhmm bakomai kawai dai...".
"Mariya mana".
Ya fadi cikin muryar mai sauti da rarrashi a cikinta.
A hankali ta dago kanta ta dube shi na yan sakanni kafin ta kau da kai tana hango yanayin kulawa sosai cikin idanuwansa gareta tana hango yarda ya nuna alamun damuwa da damuwarta.
"Baabana".
Ta fadi murya na rawa yanayin da tayi maganar zai tabbatar maka kamar iyakar gaskiyarta ta fadi ko da dai ba karya tayi ba lamarin bacewar Baabanta cikin rayuwarta yana cikin sahun abin da take zaton ƙaddara zata kawo mata na rashin natsuwa.
"Yaa Salam!".
Dr.Aqeel ya furta cikin rauni sosai kafin ya daura hannunsa akai yana mai cigaba da cewa.
"Please Mariya ya kamat ace ki na sanyawa zuciyarki natsuwa gami da kwakwalwarki ke fa karamar yarinya ce sam bai dace ace har kin fara cin karo da irin wannan lamarin ba a rayuwarki kwakwalwarki ba komai zata iya dauka ba tsorona kar damu tayi miki yawa sosai wani abun zai iya kama ki na rashin dadin rai Please Mariya Rayuwarki tana bukatar komai mai dauke da sauki".
Yanayin da yake ajje furucinsa da rauni a ciki da kuma rarrashi sosai hakan ya taba zuciyar Mariya ji take yi kamar ta rushe da kuka ita a karan kanta ta san sosai take cikin SIRAƊIN RAYUWA sosai take ganin yarda rayuwarta ke zuwa a a hagu ita kanta ta dani komai na duniyarta ba mai natsuwa bane ta sani sosai da sosai ƙaddara ke dawainiya da ita a duniyarta.
"Mariya komai zai shige in har baki dau komai da zafi ba, rayuwarki tana da muhimmanci ga rasu rayuka masu yawa sosai wasu rayuka za su shiga tashin hankali mai girma in har ba ki rangwantawa kan ki ba".
A dan tsora ce ta dago tana dubansa sosai taji kalamsa sosai take fahimtar in da ya saka gaba rintse idanu tayi kafin ta buɗe su ta fara kokarin daga laɓɓanta.
"Ta ya ya hakan zata kasance, ta ya ya zuciya zata iya daukar wannan lamari mai girma ta ya ya karamar kwakwalwata zata iya daukar wannan lamarin mai girma, bana tunanin zan iya amfanar da wasu rayuka a halin da nake ciki bana tunanin ƙaddara zata iya bani wannan damar bana zatom ƙaddara zata juya daga shafin da ta buɗe mana mai dauke da kaya mai girma na rashin kwanciyar hankali bana zaton hak...".
A hankali ta rintse idanuwanta tana tura laɓɓanta cikin bakin ta sosai take jin abu mai nauyi yana samun gurbi a zuciyarta sodai take jin kirjinta na nauyi da girma a cikinsa.
"Bana tunanin Mahaifin ki zai guje ku a halin rayuwar da kuke ciki. Bana tunani zai samu kwanciyar hankali don ya bar ki bana tunanin saboda gazawa ce ko halin da mahaifiyarki take ciki ya sanya shi bacewa daga rayuwark...".
"Dr.Aqeel mai yasa kake cewa haka, mai yasa kake kokarin sanar dani abin da zuciya ta ba zata iya samun wajan ajjewa ba".
Nisawa tayi tana jin yarda zuciyarta ke wani karfi a duk fitar kalma daya daga bakinta.
"Mai yasa mai tsaya mun tafi tare ba, mai yasa da zai tabi bai tabbatar mani da in da zai je ba, mai yasa ya boye mani wani abu kuma ya san zuciyata ba iya dauka za tayi ba mai yasa ya tafi tsayin kwanaki fiye da arba'in ba tare da ya waiwayo mu ba ina jin zafi a zuciyata ina son Baabana sosai da sosai yarda baka zato ina bukatarsa kusa da ina ina bukatar kullum na dinga kallonsa yana wanzuwa a DUNIYARMU a kullu yau min. Ban so ya tafi wata duniya ba ta daban wacce ba musan a wani hali yake ba kullum tashin hankalin rashin sa kara girna yake yi a ko wani sashi na zuciyata".
Yanayin yarda take ajje kalmominta sosai suke taɓa zuciyarsa zuciyarsa yake jin tana wani iri tana saukar da wani lamari mai nauyi gareshi sosai tausayinta ke kara samun gurbi a ko ina na zuciyarsa sosai yake jin ba zai iya cigaba da kallon yarda komai na muryarta da zuciyarta ke kara rauni ba.
"Yaa Salam! Mariya kiyi hakuri don Allah komai zai zo karshe, kuma Mahaifinki zai dawo gareki na sani duk in da yake kuna ransa domin ku ne rabin rayuwarsa ko ina ya ajje kafarsa dole ya kasance tunaninku yana zuciyarsa".
"Amma...".
"Haba mana Mariya".
Ya tare da sauri domin sam ba ya bukatar ya sake jin wani furuci nata mai rauni ya daki kunnuwansa. A hankali ya fara juyawa domin komawa Office dama ita ya fito dubawa sosai yake jin yarda numfashinta ke sauka a hankali har ya bar wajan.
A hankali ta daga kai ta bashi da kallo sosai idanuwanta suka cika da kwalla suna kokarin zubowa bayan hannunta ta saka ta dauke su ta kwashe mintina a tsaye a wajan kafin ta kokarta jan jiki sosai take jin nauyi a ko ina na sassan jikinta musamman kirji don ji take kamar dutsen Dala aka daura mata kanta a kasa take tafiya sam bata lura da wanda ya ke gabanta ba sai da ya ga ta kokarin tureshi sannan yayi gyarar Murya a dan razane ta dago kai sau kadan ta bugi kirjinsa ta ja baya kadan tana mai jikin kunya sosai da sosai.
Ya lura da haka Murmushi yayi kafin ya fara kokarin magantuwa duk abin da suke yi da Dr.Aqeel akan idanunsa komai ya faru sosai ya ji nauyi mai girma a ransa da zuciyarsa musamman yarda ya ji muryar ta na amon kalamai mausu dauke da rauniya da gazawar zuciya.
"Mariya".
Ya fadi a dan tausashe. Ba ta dago kai ba balle kuma ya saka ran amsawarsa ko da dai ba sosai yake bukatar amsawar ta ta don ya sani dole ya ji rauni a muryarta ko da kuwa ta amsa din shi kuma abin da baya so kenan a ransa.
"Me ya sa?".
Kan ta ne taji ya daure sosai da abin da ya fadi ba ta san ina furucin masa ya dosa bata san mai zata iya cewa a matsayin amsa gareshi ba ta san tambaya yayi amma kuma bata san mai ya dace ta fadi a matsayin amsa ba sosai take jin tsauri a furucin nasa sosai take jin komai na kwance mata domin ita dai ta san ba zata ce ga abin da ya dace tace dashi ba.
Gyaɗa kai take faman yi sai motsa laɓɓanta take yi amma bata da abin cewa.
"Na rasa dalilin da baki daukar shawara, zuciyarki sam-sam bata daukar abin da ake sanar dake, Me ya sa?".
Sosai take jin nauyinsa a zuciyarta sosai take jin kamar bata kyauta masa ba don a yanayin da take jin furucinsa ya tabbatar mata kamar bai ji dadi ba. Amma kuma ba ta san dalili ba, ta san abin da yasa yayi wannan furucin ba, sosai ta fuskanci akwai abin da yake nufi da furucin nasa.
A Hankali ta fara kokarin dago kai domin kallonsa amma tana jin yarda gabanta ki bugwa da sauri sauri a hargitse ta kalle shi idanuwansa na kanta sosai yake kallonta fuskarsa ba ta san a wata matsaya zata ajje taba. Bata hango haushi a ciki ba kuma ba ta hango fara'a ciki ba. A hankali ta fara daga laɓɓanta da taji sun mat nauyi sosai bayan ta kau da idanuwanta daga gareshi.
"Hakuri...".
"Bana bukata ni ba abin da kika yi mani, kuma ba abin da nake son ji daga gareki ba kenan".
Yanayin da yayi maganar tasa sosai taji faduwar gaba don ta hango damuwa a cikinta sosai da sosai rintse idanu tayi ba ta so, ba ta so ko kadan ace ta dalilin ta mutum mai ALHERI ya shiga damuwa rashin kyautawa take hangowa a gareta.
"Ban san mai zance da kai ba, ban san ina ka dosa da maganar ka ba, bani da abin cewa domin maganar taka sosai na rasa inda zan ajje ta kayi hakuri don Allah".
Maganar ta ta tayi rauni sosai hakan ya sanya shi sassautawa a muryarsa don ya fuskanci kamar taji damuwa a maganarsa.
"Ban so na shiga rayuwarki don ta kura miki ba, ban son abin da zai kara rikitar miki da tunani, bukatata kawai shine damuwarki a ranki ki rage ta sam! hakan bai da ce ba a matakin shekarun ki Mariya sosai take jin rashin dadi a rai na da lamarin daukar ki nake kamar kanwata ban son abin da zai dinga saki damuwa bana jin dai har kasar ruhina".
Hannayensa ya yarfar cikin yanayi na rashin jindadi kafin ya sake cewa.
"ki shiga ciki don Allah ki wutar wa ranki Umma ta tashi na bata magani haka Mu'azzam ya faka amma ya koma don haka ba abin da za kiyi yanzu illa ki zauna ki ragewa kan ki tunani in kuma kina da abin yi ki je kiyi don karki zauna kuma ki fada wata duniyar ta tunani na san halin ki Please Alkawari".
Ya karashe cikin muryar rarrashi sosai da sosai taji wani iri a ranta hakan ya haifar mata da kasa mai yawa daga cikin abin da ke damunta a rai.
Kanta a kasa ta wuce shi sumui-sumui kamar maras gaskiya sai da ya ga shigewarta sannan ya saki ajiyar zuciya mai cike da tausaya kafin ya saki murmushi don ya lura ta amince da abin da yace kuma za tayi din rufe idanuwansa yayi na yan sakanni kafin ya buɗe su fuskarsa da fara'a kamar koyaushe ya fara taku domin ficewa.
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA BIYAR.
Sosai yake jin rashin natsuwa da kwanciyar hankali suna samun waje a filin zuciyarsa. Sosai yake jin wasu abubuwa masu kama da kibiyar ajali ga zuciyar na sassoke masa kirjinta. Sosai yake jin duk wata natsuwa tana fallewa da gudu daga filin rayuwarsa ta duniyarsa. Komai tafe yake da tashin hankali a yanzu cikin duniyarsa sosai yake tsammanin ba shi da wani farinciki a rayuwarsa cikin rashin zato da tsammani yake kallon komai na rugujewa a duniyarsa na farinciki kamar tubalin toka.
Sosai yake jin zuciyarsa na zafi da raɗaɗi in ya tuna abin da faru dashi kwanakin baya sosai yake ji kamar zuciyarsa zata yayyage daga kirjinsa yana jin yarda kunci ke wanzuwa a duk tuni da yayi akan abin da ya faru dashi sosai yake jin wani makaƙi mai daci daga makogoronsa har saman harshensa.
"Mu'iz ban san abin da yake damu na ba, ban san abin da ya ke kokarin dauke min farinciki da walwalar duniyata ba sosai komai ya ke kwance mani sosai nake jin bacin rai a cikin kokon zuciyata da ruhi...".
Sosai yaji wani nauyi mai girma ya na samun mazauni a kirjinsa gami da saman harshensa gabadaya yaji maganar da yake kokarin karasawa ya kasa hakan laɓɓansa wanda suka dan bushe kadan ya tura cikin bakinsa yana cizawa hadi da rintse idanuwa ji yake yi kamar ba gaske ba gani yake yi kamar a mafarki ne komai ke faruwa dashi bai taba kawo wa kansa ƙaddara mara armashi zata fado masa ba ya yi zaton shi mai sa'a ne a duniyarsa dama rayuwarsa baki daya.
A hankali ya dago kansa dake sunkuye hannunsa rike da igiyar shisha da ya gama bankawa cikinsa a tunanin sa zata dawo masa da duniyarsa kamar da a tunaninsa komai zai wuce kamar ba ayi ba a tunanin sa za tayi masa maganin matsala ko ma yace matsalolinsa da suka tokare masa duniyar farincikinsa amma abun ya ci tura.
Nisawa yayi sosai har sai da kirjinsa ya harba.
"ba zan iya ce maka ga kwanakin da na dauka cikin wannan yanayin ba amma dai zan iya tuna ranar. Ranar da takasance mani SANADI ga duniyar natsuwa ta ranar da ta kasance mani tamkar BAKAR RANA mai cike da kwazazzaban tashin hankali...".
Nisawa yayi sosai yana kokawa da numfashinsa ji yake yi yana yawo dashi a wata duniya yana kokarin barin gangar jikinsa.
Mu'iz da ya tallabe haɓa idanuwansa kan Abokin nasa yana kallon yarda yake sauyawa lokaci guda mamaki abin yake bashi yarda yake ganin tashin hankali da wani abu wanda shi kansa bai san menene ba cikin idanunsa a hankali yake gyaɗa kai yana kara gyara zaman hannayensa a haɓarsa.
"Ban san in da bahagon zancen nan naka ya dosa ba ya kamata ace ka fito ka fada min dalili ba wai abin da kake ji nake so ba a'a yarda akayi komai naka nake ganin yana canzawa lokaci guda Me Ya Sa?".
Ya ida yana mai yawata idanuwansa kan abokin nasa sosai so yake yi yana hango wani abu wanda zai bashi karin haske akan lamarin amma sam bai gani ba sai tsagwaron tashin hankali da yake cikin idanuwansa da suka kaɗa sukayi jajir matuka.
"Mu'iz me ya sa ka kasa fahimta ta ya kamata ace duk wannan furucin da nake yi ka san in da na dosa ba wai ka nuna halin-ko-in-kula ba".
Ya fadi yan gyada kai fuskansa na kara bayyanar da kuncin da yake ciki sosai zucyarsa ta fara kwaso masa wani lamari tana ajjewa a kokon kansa cikin mazaunin tunaninsa.
To da yake wannan hayagagar yace wa Mu'iz me mai zai ce masa me zai ce masa dalilin kuncinsa shi sai yanzu yake ganin wautarsa kamar yarda Khairiyya tace dashi taga rashin wayonsa da dabara akan wannan lamarin ba ta san abin da yasa yake zuzuta kankanin abu irin wannan ba wanda shan ruwa ma ya fishi sauki matuka.
Girgiza kai ya shiga yi yana jin wani sashi yana kambama lamarin sosai wanda hakan yake kara masa kunci a ransa da ruhinsa sosai yake jin wani hali na daban mai dauke da tsanani musamman in zuciyarsa ta bankado masa abin da ya faru gami da sunan da yake ji a ko wani sakan yake amsa masa kuwwa yake kara haifar masa da wasu abubuwa a zuciyarsa da ma gangar jiki baki daya.
"kai nake sauraro".
Mu'iz ya katse masa tunanin da ya afka ciki yake yawata dashi wata duniyar ta daban.
Mikewa yayi daga cikin kujerar da ya cusa kansa ya saki igiyar shisha tayi kasa hannayensa duk biyu ya cusa cikin cikakkinyar suman kansa yana cakuɗawa gami da yatsine fuska kamar zai fashe da kuka a hankali ya fara taka kafafuwansa yana yawatawa cikin dakin idanuwansa a rintse sosai kafin ya sake buɗe su ya sauke kan Mu'iz wanda shi ma idanuwansa na kansa.
Ba wanda ya sake kokarta cewa komai cikin su tsayin lokaci mai nisa iyakar nazarin Huzaif ya kasa samun abin da zai ce da Mu'iz wanda shi yake damunsa haka shima Mu'iz din yayi shiru ne domin jin abin da yake dawainiya da abokin nasa amma da alamun bashi da niyyar furta ko da kalma daya ce.
*****
"Sosai da sosai zan yi kewarki nan da yan kwanaki Mariya".
Dr.Karami ya fadi hankalinsa da idanuwansa na kan Mu'azzam dake hannunsa yana yi masa wasa shi kuwa sai bangale baki yake yi.
Wani iri bugu Mariya taji kirjinta yayi wanda hakan ya haifar da tsayuwar abin da take yi sosai taji numfashinta yana sama da kasa kamar zai fice daga jikinta bakinta ta dan buɗe kadan daga sunkuyen da take domin samun daidaituwar numfashi ji take kamar numfashin da take shaƙa ta hanci yayi kadan gareta a hankali take juya fida din Mu'azzam da take wankewa cikin ruwan dake girke gabanta. A hankali kalaman Dr.Karami taji suna haifar mata da wani irin yanayi gami da narkar mata da duk wani kuzari nata sosai ta fara jin wani gumi na keto mata daga cikin hanyoyin gashin dake jikin ta laɓɓanta ta tura cikin bakinta tana cizawa kadan-kadan jin furucin take kamar cikin duniyar mafarkinta jin su take kamar ba a zahiri ba ciza laɓɓanta da tayi hakan ya tabbatar mata da eh gaskiya ce tabbacciya.
"Ba ki so ko?".
Ya fadi jin shirun nata ya yi yawa kallonta yake yi da duk kan idanunsa yana ganin yanayin da ta shiga ya tabbatar masa da haka din.
A dan razane ta dago kai ta dube shi kafin ta mai da kanta kasa tana yawata hannayenta cikin ruwan dake gabanta a hankali take girgiza kai tana motsa laɓɓanta alamun tana son cewa wani abu amma ta kasa shima ya lura da hakan.
"kawai shikenan ma tun da ba kya son tafiya sai ki zauna ke ma ki zama ma'aikaciyar asibiti ".
Yanayin yarda yake ajje furucinsa fuskarsa dauke da murmushi zai tabbatar da tsokanar da yake yi mata.
A karo na biyu ta sake dago kanta a dan razane kafun ta ware idanuwanta kadan akansa .
"Uhmm...".
Sai kuma tayi shiru tana juya harshenta cikin bakinta idanuwanta akan Mu'azzam wanda shi izuwa wannan lokaci ita yake kallo.
"ko Bakya so?".
Ya sake fadi da muryarsa dauke da dariya sosai yana kallon yanayin da take shiga wanda hakan ba karamin burgeshi yake yi ba sosai ya fahimci sanyin hali da rashin son magana irin nata sosai yake ganin magana tana yi mata matukar wuya in suna tare amma kuma yanayin ta da yanayin da take furta komai nata ba karamin tafiya yake da zuciyarsa ba ga ta dai ba wata babbar mace bane amma yanayin da da salon da take komai sai ka rantse wata mace ce babba wacce ta baiwa shekaru talatin baya.
"Na fa gaji Malama in kin gama ki zo ki amshi Mu'azzam tun da na lura zaman nan din bai ishe ki ba".
Ya fadi cikin murya mai sauti yana mai kau da kai fuskarsa dauke da dariya amma yanayin muryar da yayi amfani da ita sai ka rantse bacin rai ne a cikinta.
Cikin hanzari ta mike jikinta har rawa yake yi zuciyarta na tsalle fuskarta lokaci guda tayi rauni sosai alamun ba ta so yanayin da ya nuna ba cizon laɓɓanta tayi muryarta a raunane.
"Uhmm yi hakuri".
Ta fadi dakyar tana mika hannu za ta amshi Mu'azzam gocewa yayi kafin ya juya ya kalle ta sosai yana murmushi.
"Kin fiye tsoro da yawa ban san dalili ba kina da shariya Mariya mai yasa ko ni ne...".
ware idanun da tayi akan sa ya sanya shi sauri yin shiru yana dariya kafin ya juya ya fara tafiya ba tare da ya bata Mu'azzam din ba.
Sosai take ware idanuwanta akansa tana kallon yarda yake ajje takunsa a duk takunsa daya tana jin yarda zuciyarta da ruhi gami da gangar jiki ke amsawa kamar ita yake takawa da takalmar kafafuwansa sau ciki masu kalar ruwan kasa sai daukar idanu sukeyi da yanayin kyalli kirar kamfanin Gucci rintse idanu tayi sosai gabadaya taji tana juyawa kamar wacce aka saka a majanjawa take walagigituwa da ita ta dauki dakiku masu yawa a wajan kafun ta ware idanuwanta sosai wanda har zafi-zafi taji su na yi mata gyaɗa kai tayi gami da zubda ruwan da ta gama wankin fidar Mu'azzam ta dauki karikitan ta fara takun kan kafafuwanta a hankali kamar wacce kwai ya fashewa a ciki.
Sosai tayi nisa cikin tunani kawai ajje kafafuwan ta take a duk in da taji sun sauka duk taku daya sai taji numfashin ta na janta tana kwato shi.
"Mariya".
Cak! ta tsaya kanta a kasa sosai taji muryar ta dakar mata kwanya gami da kara kawo mata wani abu na daban kuma zuciyarta lokaci guda ta buga.
Kwanaki kusan uku kenan rabon da taji ko da muryarsa ta rasa dalili a zuciyarta tajima tana nazari anya ba laifi tayi masa ba ya dauke kafafuwansa yake guje mata ya daina son saka ta a idanuwansa sosai take lura da wasu halaye nashi na daban masu tsauri wanda a iya zaman ta dashi ta fuskanci haka mutum ne shi mai saurin fushi ga zuciya abu kadan ne yake sanya shi janye jiki ga mutum.
Takun da taji nasa yana tunkaro ta hakan ya kara sautin bugun zuciyarta ta shiga kokawa da numfashin ta ta san shi mai alheri ne kuma ta gani sai dai ta rasa mai yasa cikin lokaci kalilan take jin wani irin abu game dashi sam bata so su kasance tare domin kuwa halayensa da yake amfani dasu sam ba su dace da ita ba sosai take jin ba dadi bata son mutum mai tsauri da sauri fushi akan abun da bai taka kara ya karya ba.
Ita dai a iyakar tsawon lokacin da suka dauka cikin asibitin nan daidai da rana daya ba ta tsammanin tayi abun da zai bata masa rai sai dai bata sani ba ko cikin rashin sani tayi masa ba daidai ba wanda sam bai kamata ace ya kama ta da laifi akan hakan ba.
"Mariya".
Ta ji ya sake kira wannan kiran sai dai ya bambanta dana farko domin taji muryarsa da wani irin sauti wanda ta kasa tattance shi.
A hankali ta fara motsa laɓɓanta tana kokawa da numfashinta da taji yana sarkewa.
"Na'am".
Sosai taji hucin numfashinsa a kusa da ita a dan tsorace ta ware idanuwanta da suke kasa kafafuwansa ta hanga sanye da takalma ash-colour sau ciki sai faman daukar idanu suke yi a hankali ta fara dauko idanunta tana bin sa da kallo tun daga kasa jikinsa sanye yake da suit Blue mai turuwa sai farar rigar dake ta ciki nektayal dinsa kalar ash-colour yarda takalminsa suke hannunsa duk biyu sanye suke cikin ajihun wandonsa saitin idanunsa ta sauke nata ganin sosai taji numfashin ta yayi sama da kasa ya koma daidai amma duk da hakan bai daina tsalle tsalle ba wani abu ne mai girman gaske take hangowa cikin idanunsa wanda tajima tana ganin hakan amma na yau ya bambanta sosai da sauran lokacin can baya kamar wacce ya rikewa idanu sam ta kasa daina kallonsa idanuwansa sarke da juna duk da nashi na cikin farin glass wanda ya kara ƙawata fuskar tashi duk da dai akwai rashin fara'a a cikinta.
"Uhmm...Dr.Aqeel...".
Hannu ya daga mata ya wanzar da wani murmushi mai zafi a zuciyar mai yinsa girgiza kai yake yi kamar wanda aka fada masa wata magana da bai yarda da ita ba har zuciyarsa.
"Bana bukatar jin komai Mariya na lura kin yasar dani daga duniyar ki sam-sam kin daina tuna ni a rayuwarki sosai ki ka zare ni daga cikin duniyar rayuwarki ban san dalili ba..Uhmm...ni dai na san ban yi laifi ba amma kuma naga an dauki fushi dani Me Ya Sa?".
Sosai take jin maganganunsa na haifar mata da wani irin yanayi mai wanzar da daci a zuciya sosai take jin haushin kalaman nashi ya fiye son kan sa da yawa ta lura da haka domin duk cikin kalamansa ba abin da ke yawarawa sai son kai ba ta san dalilin da yasa Dr.Aqeel yake yi mata haka ba bata san me yasa yake kokarin canza matsayin da ta samar masa a filin zuciyarta ba sosai take ganin girmansa domin kuwa bata ta ba manta alherin da ya saka mata a duniyar rayuwarta ba ita da makusantarta ba zata taba manta yarda ya dauke su ya kai su wani matsayi ba a lokacin da wasu suke kin su suke jifansu da wulakantaccen kallo sun mai da su marasa yanci da martaba a idanunsu shi ne yayi kokarin ganin an daina kallon su haka ta sanadinsa komai ya wanzu amma ba ta san me yasa yake kokarin canza komai nasa ba cikin kankanin lokaci wanda ko da wasa ba ta taba zaton hakan ba a filin zuciyarta.
Nisawa tayi gami da sanya hannunta guda tana dafe goshinta sosai take jin kanta na sarawa da duk wasu kalamai nashi sosai take jin rashin jindadin haka bata so zuciyarta ta canza mata matsayin Dr.Aqeel sosai da sosai take kallonsa a matsayin da take kallon Dr.Karami...
Rintse idanu tayi wani abu mai girma taji ya danne mata zuciya yana kokarin karyata zancen da take yi a yanzu.
Yaa Allah!
Ta fadi a can kasan makoshinta wanda take jin sa yana wani irin bauri-bauri.
"Ban san a wani matsayi kika ajje ni ba sosai da sosai nake ganin kin canza matsayin da nake dashi a idanunki da zuciyarki a can baya Me Ya Sa?".
Ya sake fadi cikin wata irin murya wacce ta sanya Mariya saurin girgiza kai sosai take hango rashin adalci a furucinsa sosai take hango rashin dacewar hukuncin da yake yankewa a kanta sam! hakan bai dace ba ya kamata ace ya yi mata duba natsanake kuma ya ajje komai nasa na tunani a MIZANIN HANKALI kafun ya yanke mata hukunci sosai take ganin tsaurin hukuncin nasa wanda ta tabbata bai dace da ita ba.
Gyaɗa kai ta cigaba da yi tana tura laɓɓanta duk biyun cikin bakin ta.
"Dr.Aqeel bana zaton abin da kake fadi haka yake, bana zaton akwai adalci a wannan hukuncin da kake yankewa akaina. Ya kamata ace kayi nazarin komai sosai kake da matsayi na musamman a zuciyata ba zan manta alheri ba domin kuwa in har na mance alheri hakika na zama BUTULU wanda ba zan so haka ba".
Yanayin da take furta duk kalma daya a furucinta tana faman rintse ido zai tabbatar maka da sosai take jin wani abu mai girma a zuciyarta wanda ba komai ya haifar da haka ba sai yarda lokaci guda take kallon mutumin da bata yi zato ba zai sauya daga yarda ta sansa a can baya.
"Yaa Rabb!".
Abin da ya fadi kenan yana mai ware idanuwansa akanta sosai yake kallon yarda laɓɓanta ke motsawa kalamai masu taushi suna fesowa daga bakinta yana kallon yarda take cijewa da raunin da yake kawo mata hari amma sai tayi amfani da jarumar zuciyarta wajan fadi masa abin da take ganin shi ne ya dace sosai da sosai.
Gyaɗa kai yake yi yana faman yawatawa idanunwa a fuskarta dake fuskartarsa amma idanuwanta a dan kulle kadai wanda zara-zaran gashin idanunwan nata ya hana ya gane yanayin da kwayar idanuwan nata suke.
Shirun taji yayi yawa har kafafuwanta na kokarin kasa daukar gangar jikinta a hankali ta dago idanuwanta ta sauke su fes akansa batare da ko ɗar! ba yanayin kallon da ta gani yanayi mata ya kara rura wutar bugun zuciyarta amma taki bari hakan yayi tasiri a zahirance cikin karfin hali ta fara motsa laɓɓanta.
"Ban san abin da yasa kake kokarin daura min laifin da ban san dashi ba. Ban san abin da yasa kake kokarin canza komai ba. Kai kan ka kasani dole na damu da kai amma kuma kai na lura gabadaya ka sauya daga in da na san ka ban san dalili ba...Uhmm in laifi nayi maka kayi hakuri".
Ta karashe fuskartar da wani murmushi wanda ita a karan kanta ba ta san yarda akayi ya samu gurbin zama a fuskar ta ta ba.
Ta fara gajiya da tsayuwar da take yi ta lura sam! shi gajiya bata fara rauni a kafafuwansa ba a hankali ta fara taku akan kafafuwanta da take jin su kamar na roba ne suke kokarin narkewa amma karfin zuciyar da tayi amfani dashi ya hana hakan tabbatuwa.
"Zuciyata...".
Muryar Dr.Aqeel taji ta saki ihu da fadin haka wanda hakan ba karamin sakata cikin wani yanayi yayi ba matuka!
Cak! Ta tsaya da takun da take yi lokaci guda taji wani irin abu mai kama da ruwa yana bin sassan jikinta yana haifar mata da wata irin kasala mai kokarin zubda ita kasa a hankali taja jiki ta isa kofar dakin da suke ta dafa ta sosai take jin duniyarta na juyawa da sauri-sauri kamar zata watsar da ita wani waje mai nisan gaske.
Nisawa yayi yana kallon irin halin da ta shiga duk da jarumtar da ta sakawa kanta amma hakan bai hana wanzar da halin da ta faɗa ba nisawa yayi gami da cigaba da furucin nasa.
"Sosai take tausayin ki sosai take son ta ga kina cikin farinciki mai armashi...".
Nisawa yayi wanda hakan ya sanya Mariya sakin Gwauron numfashi ta ciza laɓɓanta.
"Nasan da haka da dadewa shiyasa na baka matsayi mai girma a zuciyata kamar yarda kake fadi mani matsayina a gareka".
Ta fadi tana mai yawatawa da hannunta saman kirjinta da take jin yana bugu kadan-kadan.
Da sauri ta ja kafafuwanta ta fada cikin dakin bayan ta sakar masa wani yaƙe wanda take zaton wai murmushi ne tayi masa wanda ta karyata hakan.
Sosai ya shiga gyada kai yana bin kofar da kallon kafun ya daga hannayensa duk biyun ya dafe kan sa da su yana mai faman juya kwayar idanunsa gami da ciza laɓɓansa.
Bai san abin da yake kokarin faruwa dashi ba. Bai san mai yake koƙarin saka shi cikin wani hali ba sosai yake ji a ransa akwai abin da ke shirin faruwa dashi a zuciyarsa zuciyarsa ta jima tana sanar dashi amma ya kasa gasgata haka ya dauki hakan a matsayin hauka irin ta zuciya mai kwashe kwashe bai san mai yasa yarinyar nan tunaninta yake wahalar masa da zuciya ba sosai yake kokarin yakice komai amma hakan ya gagara ganin haka yake a matsayin wauta na zuciya sosai yake ganin rashin hankalinta sosai yake son kin amsa komai da take yi domin kuwa rashin dacewar haka ya ke gani a filin rayuwar duniyarsa.
Ya kaucewa ganinta ko zai samu sassaci akan komai ya gujewa haduwarsu domin ko zuciyarsa zata daina yi masa wannan labarin kanzon kurege da kullum take masa ya daina wanzuwa in da take ne a tunaninsa haduwarsu ne ke haifar da haka ashe ba hakan bane domin kuwa rashin haduwarsu hakan ya kara rura wutar abin da zuciyarsa take kokawar kawo masa filin rayuwarsa wanda sam ya ki amincewa da haka wanda ita kuma zuciyarsa ta hakikanace abin da take sanar dashi dole ya yarda dashi domin kuwa shi kadaine zai sassauta masa komai na filin zuciyar tasa dama filin rayuwarsa gabadaya...
Girgiza kai yake yina faman karyata zuciyarsa a hankali ya fara jan kafafuwansa da yake jin sun masa nauyi sosai, yana barin wajan domin ya lura zuciyarsa so take ta haukata shi da abin da yake zaton ba zai taba tabbatuwa ba har gaban abada...
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
*Ita gobarar zuciya ruwa ba zai kashe ba, so ne ginshikin halinta. ba kowa ke sani ba*
--ISA AYAGI😘
BABI NA GOMA SHA BAKWAI.
Abu mai girma taji ya zo mata wuya ya tsaya cak! Numfashi ma da kyar ta ke jansa don ji take kamar zata shiɗe a hankali ta kai hannayenta duk biyun ta dafe kanta da take ji yana kokarin tawatsewa sosai take jin kirjinta na buga a duk sakan sai take hango tashin hankalin da ta gan shi a ciki sosai take hango yanayin fuskarsa mai dauke da kayan damuwa masu girma sosai.
Sosai take jin wani abu mai kalar tausayi yana saukar mata a wani sashi na zuciya yana haifar mata da wani yanayi mai sanya kasala da sanya wani wani ciwo mai girma.
Ba ta san ya zata yi ba, ba ta san me take ji game dashi ba, ba ta san mai zuciyarta ke kokarin yi gareta ba, ba ta san mai yasa tunanin wannan mutumin yake kokarin samun waje a filin zuciyarta ba, ba ta san mai yasa komai ke kokarin wargaje mata da tunaninsa sa ba ta tsane shi bana ta son ko ganin fuskarsa a filin rayuwar duniyarta sosai take jin ɗaci da bauri a zuciyarta duk lokacin da ko sunansa taji sai taji kamar ta kurma ihu amma a halin yanzu wani irin yanayi take ji game dashi sosai KUDIRI da tayi akansa a zuciyarta taji yana kokarin rushewa sosai taji bangarori na sashin zuciyarta sun kasu kashi biyu suna faman tamka muhawara wanda hakan ba karamin sanya ta tashin hankali yayi ba wanda ita kanta ba ta san mai ya dace tayi ba, ba ta san mai ya dace tayi akan wannan lamarin na zuciya ba.
A hankali take sauke hannayenta daga kanta idanuwanta take rintsewa tana buɗewa a hankali gani take yi komai da yake faruwa da ita a yau kamar mafarki ne ba gaskiya ba za ta so ace a cikin barci ne komai ke faru da ita za ta so ace ba a zahiri bane za ta so ace kamar tatsuniyar kanzon kurege ne wannan lamarin.
Sosai take jin wani sashi na filin zuciyarta na halittar wani abu mai girma wanda yake kara tsuke mata da zuciya a duk sakan sosai take jin jikinta na samun wasu abubuwa da su ka danganci zuciyarta sosai take jin duk wani sashi na jikin ta na amsar abin da zuciyarta ke halitta ba ta san a yarda zata dauki abun ba bata san a wani irin ma'aunin hankalin ta zata ajje wannan lamarin ba komai take ji sabo na halitar kansa da kansa a zuciyarta da gangar jikinta.
Nisawa take yi a hankali tana faman fizgar numfashi wanda take jinsa kamar yayi mara karanci sosai a gareta.
A hankali ta fara kokarin tashi saman kafafuwanta tana jin yarda suke wani irin kokarin kasa daukar gangar jikinta sosai take ji wani abu mai sanya rauni a duk sassar jiki da zuciya yana samun gurbin zama a jikin nata.
Safah da Marwa ta shiga yi cikin rashin tsammanin abin dake faruwa da ita ba ta san mai zata ce ba mata san wani irin tunani ya kamace ta ba bata san mai rayuwart take kokarin dauko mata ba ta jiho filin duniyarta bata san wani irin tashin hankali bane ƙaddara ke kokarin dauko mata a wannan lokaci zuciyarta! Sosai take ji kamar ba ta ta ba sosai take ji kamar wata zuciyar ce ta daban ta sauya a filin kirjinta.
Komai take jin sa ba dadi sosai take jin saman harshenta na haifar mata da wani ɗandano mai bauri gareta sosai take jin zafin da zuciyarta da can kasar ruhinta suna kokari kwatar kansu a kansa.
A hankali ta fara taku har ta isa inda Mu'azzam ke kwance idanunusa biyu da alamun farkawa tayi daga barcin da yake yi sai faman wasa da hannayensa yake yi yana kaiwa bakinsa yana tsotsa alamun yinwa yake ji.
Sosai ta ware idanu akansa tana kallon sa mamaki ne sosai ya bayyana a gareta bata ji mptsinsa ba kuma da alamun ya jima da tashi daga barcin a hankali ta mika hannayenta ta dauko shi gami da rungumeshi sosai ajikin ta sosai take jin wani irin yanayi game dashi sosa take jin so irin na DANGANTAKAR YAN'UWANTAKA na ratsa ko ina najinta sosai take jin so dan'uwan nata a duk lokaci tausayin sa da jikan ke kara samun gurbi a filin zuciyarta na kara haifar mata da so mai tsanani game da shi idanuwata take saukewa akan nasa tana faman sakin wani murmushi wanda ita kanta ba ta san tayi shi ba shima Mu'azzam din murmushin yake saki don akwai shi da arhar dariya.
"Ehem! Nikam ina jiye miki ranar da za ta zo ta kasance ta rabuwa da Mu'azzam ban san ya zaki yi ba?".
Kamar daga sama ta tsinkayi muryar Dr.Aqeel na dukan kunnuwanta sosai taji wani irin faduwar gaba ta ziyarce ta a hankali taji takunsa na iso gareta sosai take ji a jikinta idanuwansa na kanta sosai take jin komai na jikinta ya zama kamar ba nata ba ita kam! ba ta san abin da ke dawainiya da ita ba a duk lokacin da Dr.Aqeel ya fado duniyar rayuwarta sosai take shiga wani yanayi na rashin gane kanta.
A hankali ya karo ya ja kujera ya zauna yana fuskantar ta sosai fuskarsa kunshe da murmushi
"Umma ba ta tashi bane har yanzu?".
Ya fadi yana kai dubansa ga tsintsiyar hannunsa mai dauke da wani hadadden Agogo Gold-Colour kirar Rolex sai faman sheki yake yi yana kara wa hannun nasa wani irin kyau na musamman.
"Uhmm ba ta tashi ba. amma... Ai kai kace sai nan da awa uku kuma naga daga lokacin da kayi mata allurar zuwa yanzu ba a ci awanni uku".
Yanayin yarda take ajje kalmomin da take kokarin furtawa da laɓɓanta a hankali hakan ya shagalar da shi sosai komai cikin natsuwa da hankali take yin sa kamar mai tsoron kuskuren fadin wata kalma daya da bata dace ba gyaɗa kai yayi gami ya sake kai dubansa ga Agogon hannunsa.
"Yaa Allah! Kin ga shaf! na mance Wallahi".
Ya fadi yana fama yatsine fuska gami da dafe kai.
Yanayin da yake nunawa sai ya sanya Mariya sakin baki tana kallonsa sosa take kallon yanayin da yake nunawa kamar karamin yaro sai faman turo baki gami yake yi yana cizon laɓɓansa.
Ta gefen idanu ya kalle ganin yarda ta saki baki tana kallonsa sai ya cigaba da abin da yake yi don ya lura abin da yake yi din ne ya shagalar da ita cikin kallonsa sam bata lura ba tsayin lokaci har Mu'azzam dake hannunta ya kusan zuwa kasa cikin hanzari Dr.Aqeel ya kai hannayensa duk biyun ya tallebe shi wanda ita ma a daidai lokacin ta zabura ta kai hannunta domin gyarashi aiko sai hannayensa suka sarkeda na juna wani irin Shock ne gabadaya ya kama jikinsu da sauri Mariya tayi baya gami da sakar masa da Mu'azzam din idanuwanta a warwaje sai faman yarfe hannayenta take yi fuskarta na ya mutsewa kamar zata yi kuka.
Yaa Salam!.
Abin da ya fadi kenan cikin zuciyarsa da wani irin yanayi wanda ya kasa gane na menene sosai ya rungumi Mu'azzam amma har zuwa lokacin jikinsa bai daina sanar dashi Shock din daya ji ba.
Bugun zuciyarta sosai ya kara sauri sosai take jin wani tashin hankali yana samun waje a jikinta da zuciyarta da can kasan ruhinta sosai take jin wannan yanayi mai ABOTA da bakon lamari wanda tun da take bata taba jin irinsa ba mutane da yawa suna sarkewa bisa rashin sani amma bata taba jin irin wannan yanayin ba.
Wani fili na zuciyarta ya shiga sanar da ita:-
'shin kin manta waye kuka yi haka dashi. shin kin manta ɗa namiji ne kuma hakan sam bai dace ba mace da namiji su taba juna in har ba muharraman juna bane'
Astagafurullah wa'atubu ilai!
Abin da ta fadi kenan cikin zuciyarta wani irin tsoro taji ya game jikinta da sauri ta fara ware idanunta domin karantar yanayin sa bata fuskanci komai ba domin hankalinsa ma bai gareta yana can wajan Mu'azzam yana gyara masa kwanciya a jikinsa hakan da ta gani ya sanya ta samun natsuwa domin abin da zuciyarta ta fara hasaso masa ba hakan bane.
"Amma dai yanzu Mu'azzam ya tashi ko. Naga yanayin barci game dashi".
Kai ta shiga gyaɗa masa kamar yana kallonta domin ta kasa cewa komai bakin ta take jin yayi mata nauyi sosai tsoron magana take yi domin bata san mai zata ce ba jin jikinta take yi har yanzu shock din bai sake ta ba.
A hankali ya dago idanuwansa jin bata ansa masa ba sosai yake kallonta ya ganin yanayin da take ciki sosai ta fahimci ita taji abin da ya ji a jikinsa sosai ya gane haka murmushi yayi kafun ya ce.
"Magana nake yi fa ko akan Mu'azzam din masa sai an yi halin rashin son maganar?".
Ya fadi har lokacin fuskarsa akwai murmushi ita ma wani yaƙe ta dauko ta daurawa fuskarta a tunaninta wai murmashi ta mai da masa kafun ta kokarta motsa laɓɓanta.
"Uhmm yanzu ya tashi kai kuma.ka shigo".
Ta fadi tana mai nuna kamar shine dalilin rashin yin komai akan Mu'azzam.
Ya gane in da ta dosa don haƙa ya mike a kafafunsa yana kallonta ya mika mata Mu'azzam a hankali takai hannunta ta anshe shi.
"Sai anjima".
Ya fadi yana mai shafar kan Mu'azzam dake ta faman kallonsa yaka dariya.
A hankali ya fara taka kafafuwamsa ya ficewa dag cikin dakin sosai yake jin wani irin yanayi a jikinsa sosai yake jin ranar yau a gareshi ta fita daban sosai yake jin yanayi mai zubi da wani yanayi mai armashi a jikinsa a haka har ya karasa ficewa daga cikin dakin.
Wani ajiyar zuciya ta saki tana mai lumshe idanuwanta ta bude su akan Mu'azzam wanda ya kafeta da idanu kamar yasan abin da take yi ja masa kumatu tayi ya bangale mata baki sukayi hanyar Toilet din dake cikin dakin domin gyara masa jikinsa.
*****
Tun ranar da ya hadu da Mariya ya sake jin filin duniyar rayuwarsa ya sake hargitsewa sosai yake jin ciwon da zuciyarsa take masa yana kara girma matuka gaya sosai yake hango tashin hankali mara musaltuwa na kara wanzuwa gareshi.
Juyi yake yi saman gadonsa lafiyayye wanda yaji kayan shimfida amma duk da wannan taushin gadon da laushi da yake dashi hakan bai hana shi jin sa kamar akan ƙaya yake kwance ta take faman sassoke shia ko wani sashi na jikinsa.
Bai sa mai ya dace ya yi ba, Bai san abin da ya kamata ace ya aikata ba domin ceton kansa, sosai yake jin kwanyarsa ta toshe gabadaya tunaninsa ya daina kawo masa abin kirki na a zo a gani.
Zuciyarsa sosai yake jin tana kara ciwo mai girma a cikin filin ta sosai yake jin zafi da raɗaɗi a duk sakan sosai yake tsoron abin da zai faru dashi nan gaba in har zuciyarsa ba ta saman masa mafita ba sosai yake hango rayuwarsa gajarcewa take yi a duk sakan...
handle din kofar dakinsa da yaji an kama ya sanya shi saurin buɗe idanuwansa da suke kulle yana.jin tunanin da yake ta faman yi na kanzon kurege ya tsaya cak!.
Mu'iz ne ya shigo fuskarsa kawai zaka kalla ka gane akwai abin dake damunsa yanayin kallon da yake wa Huzaif zai tabɓatar maka akansa yake samun damuwa a filin zuciyarsa.
"Ban san wata irin rayuwa kake kokarin rakitowa kan ka ba, Ban san mai yasa kake kokarin sanyawa kan ka abin da zai hanaka walwala a duniyarka ba, Ban san mai yasa ka kasa kokari wajan yaki da abin dake damunka ba?".
Mu'iz ne yake fadin haka muryarsa cike da damuwa hannunsa harɗe a jikinsa ya jingina a kofar dakin ba tare da ya karo cikin dakinsa amma idanuwansa masu ciƙe da damuwa suna kan Huzaif dake ta faman juyi kan gadon gabadaya lokaci guda ya hargitsa shimfidar gadon.
A hankali Mu'iz ke takowa saman kafafuwansa jikinsa na bayganar da yanayin sanyi da halin da abokin nasa yake ciki a haka ya iso bakin gadon ya zauna yana kallons sosai kafun ya kai hannunsa ya ja babban bargon da ya lullube kansa dashi jikinsa daga shi sai Boxer da singilet murɗanɗan jikinsa mai cike da kirar mazantaka sosai ya bayyana kau da kai Mu'iz yayi ganin yarda da yake ciki.
"Ban san mai yasa kake haka ba ban san mai ka dauki rayuwa ba ban san mai yasa kake daukar abu da girma ba wanda bai dace sam ace hakan ba haba Huzaif mana".
Ya fadi da rarrashi a muryarsa a hankali yake jan numfashi yana ajjewa kafun ya numfasa.
"ji ka don Allah a hakan kake tunanin zaka cigaba da zama a Huzaif din da a ka san ka, haka kake tunanin zaka samu walwala a rayuwarka ba tare da kayi maganin abin da ke damun ka ba kana tunanin wannan halin da ka jefa kan ka zai maka maganin matsalarka kayi ganganci Huzaif...ba ma wannan ba sosai nake mamaki Huzaif da har zaka kasa fada min abin dake damun ka nayi mamaki a zuciyata yanayin da ka nuna ace abu na damunka amma a matsayina na abokinka shakiki amma ka kasa sanar dani gaskiya bakayi ABOTA adalci ba dake tsananinmu".
Numfashi ya ja mai zafi kafun ya ciza laɓɓansa.
"Ka tashi ina son magana da kai in kuma bani da wannan matsayin sai naji in san in da dare yayi mani".
Yanayin yarda yayi maganarsa da muryarsa mai zurfi da zafi a cikinta ya sanya Huzaif motsawa yana faman cizon laɓɓansa a hankali ya ja jiki ya riko hannun Mu'iz.
Da sauri Mu'iz ya kalle shi hawaye ya gani suna sauka a idanun Huzaif da sauri ya ware idanu ya na kallonsa yana mai kara rike hannunsa sosai.
"Haba mana Huzaif! me nake shirin gani haka wai shin meke damun ka ne haka wai kuwa kasan yarda kake kuwa kana kallon kanka a MADUBI kuwa ka ga halin da ka jefa kan ka Huzaif Hawaye Huzaif hawaye a idanun ka By God Sake don Allah karka ce mani abun har ya kai haka kar kace mani matsalar da kake ciki har ta kai matakin da zaka zubda mata da hawaye...Yaa Allah!".
Janye hannunsa yayi daga na Huzaif sosai yake ware idanunwasa yana jin yarda gabansa ke bugawa cikin wani irin mataki mai girma.
"Ban san abin dake damu na ba, Mu'iz abu daya na sani Mariya ita ce ta dalilinta komai...".
"Mariyaa!"
Mu'iz ya fadi muryarsa da sauti sosai a cikinta da mamaki yake duban sa cikin wani irin yanayi wanda shi kansa bai san yarda zai fassara shi ba.
"WACECE ITA?".
Mu'iz ya fadi muryarsa da zurfi a cikinta yana mai kallon Huzaif da izuwa lokacin hawayen da yake zubda sun tsaya illa numfashi mai girma da yake ta faman ja kamar zai kufce masa.
"Ban san ya akayi kudin ƙaddara ya rakito mani ita ba ban san mai yasa kaddara ta kinkimomin ita ba ta jeho cikin rayuwata ba sosai nake cikin tashin hankali mai girma Mu'iz ban san ya zan kwatatta maka yanayin da nake ji a zuciya ta ba abu ne mai girma nake jinsa ya samu gurbi a filin zuciyata wanda ban san menene ba ban taba jin irinsa ba koma.na taba ji ban taba jin mai girma kamar wannan ba".
Zuciyar Mu'iz ce ta buga a hanzarce har sai da ya kai hannunsa ya dafe kirjinsa tsayin mintina masu auki kafun ya ja numfashi mai zafi ya fesar ya dubi Huzaif da yayi shiru numfashin sa sai kai kawo yake yi a hankali
'U'r in Love'.
Mu'iz ya fadi a zuciyarsa da wani murmushi mai girma a fuskrsa kafun ya nisa.
"Tashi ka zauna ka bani labarin yarda abun ya kasance".
Mu'iz ya fadi fuskarsa da murmushi yana mai bubbuga bayan Huzaif sakato yayi Huzaif din yayi ganin yarda Mu'iz ya nuna masa a hankali ya ja jiki ya tashi ya zauna tsakiyar gadon har da tankwashe kafafuwansa hannayensa tallabe da haɓa ya warsa idanuwansa kan Mu'iz da shima idanuwansa na kansa sun shafe fiye da mintina goma a haka kafun Mu'iz yayi kokarin kau da shirun.
"Bani labari mana Huzaif".
Ya fadi yana kafe shi da idanu
Sosai Huzaif ke kallonsa gabadaya ya rasa inda Mu'iz ya nufa sosai maganganunsa suka rikita shi ya rasa ina zai ajje su ya rasa ina suka nufa sai faman sauke ajiyar numfashi yake yi yana kallon Mu'iz
"Ban gane ba Mu'iz me kake nufi".
Ya tsine fuska yayi kafun ya gyaɗa kai.
"Bani labarin wacece Mariya".
tsura yayi da idanu yana tunanin mai zai ce da Mu'iz ta yaya zai ba shi labarin Mariya mai zai ce masa ya hada su kai ya shiga girgizawa yana cizon laɓɓansa a hankali shiru ya shiga tsakanknsu kafun ya kokarta sanar da Mu'iz yarda ƙaddararsa ta watso masa Mariya cikin duniyar rayuwarsa take kokarin rikita masa komai da komai.
"Yaa Allah!".
Mu'iz Ya fadi yana mai girgiza kai cikin wani irin yanayi wanda Huzaif ya kasa gane in da hakan ya dosa.
"Ban san mai yasa kake haka ba ban san mai yas kake rayuwa haka ba ban san yaushe zaka yi wayo ba a rayuwarka ba ban san mai yasa kake daukar rayuwar duniya a abun azo a gani ba".
Kau da kai Huzaif yana mai yatsine fuska don ya lura da inda maganganun Mu'iz suka dosa.
"Mtss".
Ya ja dogon tsaki kafun ya dubi Mu'iz a karo na ba a dadi.
"ni ba abin da nake bukata ba kenan so nake ka samo mani mafita ba wai wani zance na daban ba".
"tsiya ta da kai kenan Huzaif ya kamata ace ka fuskanci rayuwa tun yanzu kai ga ka da son yin abu amma sam abin bai yi maka kyau".
Cikin rashin fahimta yake kallonsa yana nazarin kalamansa.
"Na rokeka ka rabu dani Pease I don like this at All wallahi ya kamata ace ka gane ni sosai izuwa wannan lokacin...Mtss".
"Huzaif you sport to no u'r in love...Yaa Allah abu kamar almara ban san ya zan fassara maka ba halin da kake ci amma dai akwai alamun so tattare da kai...".
Ihu Huzaif ya fadi yana mai kaiwa Mu'iz wani wawan naushi a fuska da sauri ya kau ce cikin hanzari yana mai tashi daga kusa dashi cikin yanayin mamaki da kuma murmushi a fuskarsa shi dama ya san sa haka ta faru.
"U'r so stupit Mu'iz baka da hankali wallahi na lura kana hauka sosai Yaa Allah ni kake wa wannan maganar kan uban ce...".
Wani sarawa kansa yayi da sauri ya sanya hannu ya dafe yana mai yatsine fuska yana jin yarda zuciyarsa ke raɗaɗi da zafi.
"Please I beg u in the name of Allah to leave me alot I don't wanna see you please and please...".
Kansa ne ya sake dauka wata irin jiwa yaji tana sama da kasa dashi da sauri ya koma ya kwanta yana tattare jikinsa waje daya kamar mai jin sanyi sosai yaji numfashinsa na kokarin kwace masa wani irin tashin hankali yana zuciyarsa ta bankado masa lokaci guda gabadaya yaji duniyar na sukuwar doki dashi sosai yake hango tashin hankali ta yaya hakan za ta faru ta yaya Mu'iz zai kawo masa wannan mahaukacin tunanin nasa ya fada masa yace hakan ce take faruwa dashi ina! ba zai taba yuwuwa ba ai wannan hauka ce da rashin hankali kamar shi Huzaif ace wai son ta yake yi kaicon wannan mummunar labari.
Wata irin zabura yayi ya dire daga kan gadon ya isa gaban Mu'iz dake tsaye kamar wanda aka dasa mamaki ne ya cika shi ganin yanayin da Huzaif ya nuna game da maganar da yayi masa wanda in da yasan haka ce zata faru ba zai fada masa ba.
wuyar rigarsa da yaji an shaƙa ya sanya shi katse tunanin da yake yi da zuciyarsa.
"Ban san baka da hankali ba sai yau, Ban san kwakwalwarka ba ita kadai bace akan sai yau, ni zaka kawo wa wannan takaicin da bakin cikin rayuwata ashe dama ba so na kake ba ashe dama zaman tsana muke yi tsakanina da kai Well..Well ban yi mamaki ba Mu'iz dama ance makashinka yana nan tare da kai ba tare da ka sani ba yau ka nina min true colour din ka kuma na gani".
Yanayin yarda yake maganar zai tabbatar maka ba ya cikin hayyacinsa idanunsa gabadaya sun canza kamar ba nasa ba sosa jikinsa ke rawa hakan da Mu'iz ya gani ya tabbatar masa Huzaif ba ya cikin natsuwarsa yake wadannan sambatun masu kama da mai hauka tubaran dole yayi masa zuri'a domin ba ya cikin tunaninsa a hankali ya sa hannunsa ya zare na Huzaif dake wuyansa a hankali ya ja shi ba tare da gardama ba har ya isa dashi kan gadon ya kwantar dashi yana mai jama masa bargon ya lullubeshi sosai jikinsa ya wanzar da wani irin zafi sosai yana faman karkarwar sanyi sai jan numfashi yake yi da sauri sauri
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA SHIDA.
Juyi kawai yake yi kan kafcecen gadon sa yana faman kai komo da zuciyarsa da ta hana idanuwansa barci ko na yan mintina ne yayi iya yin sa amma abun ya ci tura sosai yake ganin komai na dawo masa kamar yanzu fuskarsa yake hangowa tana yi masa shawagi a cikin idanuwansa in ya rintse guntun murmushin da ta sakar masa a waccan lokacin yake hangowa na yi masa barazana sosai yayi nisa cikin tarkon ta da yake tsammanin ta ɗana masa ba wai aiki kawai ta zo nema kamfanin sa na AFC ba har da da faraunatar zuciyarsa wacce cikin dakiku ta zabare masa ita ta tafi da ita bai sai hakan ya afku ba sai cikin wannan sulusun daren wanda ya dace ace yana kwance yana barci domin baiwa zuciya da gangar jiki hutu amma ina! hakan ya gagara.
A hankali ya kai hannunsa wajan makunnin wutar dakin ya kunna haske ya gauraye dakin agogonsa kirar Rolex da ke ajje saman yar karamar dirowa dake girki gefen gadonsa ya dauko ya duba karfe 3:15am. ya nuna masa sosai ya ware idanunsa yana jin yarda kirjinsa ya buga kadan maidawa yayi ya ajje sannan ya juya gefen hannunsa na hagu kafun ya dan tashi kadan ya jingina da fuskar gadon sosai hannu bibbiyu ya tallaɓe haɓarsa abun duniya yake ji duk ya addabar masa rayuwa ya surkutar dashi cikin yan awanni da ba su haura goma sha tara bs komai ganinsa yake yi kamar wanda akayi shekara goma sha tara kafun ya tabbata sosai yake jin wani iri a duk wani sassa na jikinsa da zuciyarsa sosai yake hangowa kansa tashin hankali in har abin da zuciyarsa ke sanar dashi bai tabbata ba sosai yake ganin komai zai iya faru in har Areefa Saif ba ta bashi dama ba.
Zuciyarsa yaji ta fara yo masa kuwwa da zancen amincewa daga bangaren Areefa tana mai sanar dashi in dai da kudi komai zai kasance kamar yarda ya fuskanci ita kanta Areefa din zata so jindadi da hutu kamar yarda hakan ya nuna ba tare da yaji daga gareta ba. Ba ya zaton zai samu matsala in dai ta bangaren kudi ne tabbas za suyi masa abin da yake so kuma a lokacin da yake so ko tattama ba zai yi ba yana da kudi yana da kadara wacce zai iye sayr zuciyar Areefa da komai nata da ta mallaka ya zama dole ta yarda dashi ya zama dole ma ta amshi bukatarshi hannu bibbiyu ba tare da tsaya yawo da hankalin sa ba.
Gyaɗa kai ya shiga yi yana hada hannayensa waje daya yana lakwasasu suna ba da wani sauti mai amsawa sosai yake sakin murmushi mai karfi a fuskarsa sosai yake jin wani farinciki na samun gurbi a filin zuciyarsa sosai yake hango amincewar abin da yake bukata daga Areefa sosai yake ganin yarda ta amshi bukatarsa cikin lokaci kalilan ba tare da ya samu wata tangarɗa ba gareta.
A hankali ya koma ya kwanta yana kai hannunsa wajan makunnin wutar yana kashewa rufe idanunwansa yayi har lokacin fuskarsa bata rabu da murmushin da yake yi ba sosai yake hango Areefa a wannan lokacin tana yi masa shawagi a duniyar idanuwansa da suke rufe sosai yake hango wani tattausar murmushi na samun gurbin zama a fuskarta tana jefa masa wani kallo wanda yake kara rugurguza duk wani sashi na filin zuciyarsa yana jin yarda wani abu mai girman gaske yana wanzar da mazauni a filin zuciyarsa ta shi, sosai yake ganin rashin samun Areefa tamkar rasa rayuwarsa sane da duk wani buri da kudiri nasa da ya kafa akanta gani yake yi in har ya rasa abin da yake bukata a gareta tamkar yayi wa rayuwarsa babban gibi ne wanda ba ya tsammanin yana da abin da zai cike masa wannan gibin.
Cikin wannan yanayi barci barawo ya zo yayi awon gaba dashi ya jefashi wata duniya mai dauke da Areefa a cikinta...
****
A hankali ya shiga rage sautin wakar 'Don't Judge Me' ta Chris Brown dake tashi cikin sifukun motar wayarsa dake hannunsa ya shiga latsawa a yan sakanni ya kai ta zuwa kunnansa yana faman jan numfashi kamar wanda yayi gudun tsira sosai fuskarsa ke bayyanar da halin da yake ciki na damuwa sosai kunci ke wanzuwa a fuskarsa da kwayar idanuwansa.
Laɓɓansa yake turawa cikin bakinsa ya na cizawa kamar ba a jikinsa suke ba sosai yake jin wani irin yanayi da zuciyarsa take haifar masa a duk sakan daya na jan numfashinsa.
A hankali ya sauke wayar fuskar na kara ya mutsayewa cikin yanayi na damuwa da rashin abin yi sosai yake jin komai na kwance masa sosai yake jin lissafin kwanyarsa na wargajewa cikin yan dakiku bai san abin da ya dace yayi ba, bai san me nene ya kamata ace yayi ba a daidai wannan lokacin ba yana bukatar mataimaki yana bukatar wanda zai tayashi zaman jajen zuciyarsa daga halin kuncin da take ciki...
Kamar wanda aka zungura da sauri ya sake dauko wayar da ya ajje gefe cikin yan dakiku ya kai ta kunnansa bayan ya binciko lambar da zai kira.
A hankali yake jan numfashi yana motsa laɓɓansa zuciyarsa yake jin tana wani irin mataki da ya tabbata gaf take da kamuwa da cuta mai girma gareshi dama gabadaya gangar jikinsa.
"Khairiyya...".
Ya fadi cikin wani irin sauti mai rauni sosai a hankali ya sanya hannunsa daya yana dafe kansa da yake jin yana kokari wargajewa.
Yana jin yarda numfashinta ke sama da kasa daga bangarenta sosai yake so ya fahimci wani abu cikin yanayin da take ciki zuciyarsa ta cilla shi wata duniyar tunani ya shiga nazarin yanayin da yaji Khairiyya sosai zuciyarsa take sanar dashi wani abu na daban da bai yi tsammani ba.
Girgiza kai yayi cikin yanayi na kin yarda da zancen zucin nasa kafun ya nisa cikin yanayi na damuwar zucci.
"Ban san mai nayi miki ba kika gujeni tsayin kwanaki Khairiyya, tun da nake dake daidai da kwana daya ba mu taba kin sa junanmu a idanuwanmu ba, amma cikin wannan lokacin gabadaya na lura sauyawa kike yi me yasa?".
Ya ida muryarshi da sanyi a cikinta sosai yayi shiru yana jiran tsammani daga bangaren ta amma shiru kusan mintina biyu a hankali ya sauke wayar yana duba screen amma ba alamun yankewar wayar har yanzu akan kira take.
"Uhmm...".
Ya kokarta nisawa domin tunatar da ita yana kan layi in mantawa tayi take wata sabgar ta daban.
Jan numfashi yaji tayi mai karfi kafun ta fara magana da wata murya wanda da ka jita zaka gane akwai abin da ke damun mai muryar.
"Huzaif...".
Ta fadi da sauti kafun ta sake jan numfashi ta dora.
"Bakomai kawai dai...kawai gani nayi kana bukatar a baka fili a duniyar rayuwarka domin daidaita halin da kake ciki na damuwa...".
Da sauri ya tare ta.
"Haba mana Khairiyya wacce irin magana ce kike yi haka wanda sam bata dace ace ta fito daga gareki ba".
Ya karashe yana mai jan numfashi sosai ya hasaso wani abu mai kama da bacin rai a cikin kalamanta sosai ya fahimci akwai abin da ke dawainiya da ita a zuciyarta.
"Yi Hakuri...".
"Huzaif!".
Ta fadi da sautin murya mai nuna da bata so abin da yace ba.
"me kayi mani kake bani hakuri, wanda ni ban sani ba?".
"Ban ce nayi miki wani abu ba amma kuma muryarki ta fallasa asirin zuciyarki da halin da kike ciki".
Yana jin yarda ta saki numfashi mai karfi kafun yaji maganarta ta doki dodon kunnuwansa.
"bana gari nayi tafiya kuma gaskiya ban san ran dawowa nan kurkusa ba...".
Bai bari ta ida batun nata ba ya tare da sauri.
"What! me kike nufi Khairiyya kin yi tafiya ba tare da na sani ba mai haka ke nufi shin kin manta halin da nake ciki kuma kin san ina bukatar taimako daga gareki amma ki kayi min haka Well..shikenan..shikenan".
Ya karashe cikin wani irin yanayi mai sanya daci akan harshe da zuciya
Ita kan ta haushin nr cinkoshe a zuciyarta take faman kokawa dashi kar ya kufce ya yo waje domin ta tabbata komai zata iya gayawa Huzaif akan bacin rai da cin kashin da yayi mata. Sosai take jin bacin rai da takaici wanda ta hakikance haka a matsayin raini tsagwaron sa da rashin sanin darajar ta.
Alkawari tayi sai ta bashi mamaki sai ta nuna masa asalin wacece ita sai ta ganar dashi 'YA MACE irin ta ba kowa yake dauka ya wulakanta ba sai ta nuna masa suma 'YA'YA MATA akwai daraja garesu ba wai ledar pure water bace duk in da ka gilma zaka tsince ta kuma ka zabi wanda tayi maka.
"Sai Anjima!".
Ta fadi a zafafe gami da kashe wayar bakidaya.
Sakato yayi da baki bayan ya sauke wayar ya kafe Screen din da kallo wani abu yaji yanayi masa yawo akai ji yake yi duniyar na juyawa dashi a hankali komai na kwancewa akansa runtse idanu yayi mamaki ne da tu'aji yake kunno wa daga zuciyarsa sosai yake ganin kamar a mafarki wai Khairiyya ce tayi masa haka ita ce take fada masa magana cikin bacin rai abin da tun da suke da ita bata taba yi masa ba sosai take nuna kulawa da tattali gare shi amma a yanzu lokaci guda komai ya wargaje.
Gyaɗa kai ya shiga yi yana hango rashin sa'a rayuwarsa wanda ƙaddara ta kinkimo ta kawo masa lokaci guda kuma take kokarin tarwatsa komai na ginin rayuwarsa da yayi a baya mai cike da kayan kwanciyar hankali da jindadi.
Sosai ya jima cikin shiru hannayensa rungume da kansa zuciyarsa sai faman harbawa take yi da wani irin yanayi wanda ke kara hargitsa masa tunanin kwanyarsa sosai ya fuskanci rayuwarsa gaf take da tarwartsewa koma yace ya tarwatse domin kuwa shi dai bai ga amfanin haduwa da wannan yarinyar ba wacce ta dagula masa lissafi da komai nashi kuma take kokarin zautar dashi bai san abin da ya dace yayi mata ba bai san mai ya kamata ace yayi akan ta ba domin daidaituwar komai nasa sosai yake kasa aiwatar da niyyarsa gami da kudirinsa akan ta bai san mai yasa hakan na tunaninsa ya zama abokin sa a kowani lokaci dare rana dama cikin barcinsa ba wanda hakan ba karamin tashin hankali yake shigar dashi ba sosai ya fuskanci yarinyar ta samu gurbi a filin zuciyarsa tayi kane-kane ta hana zuciyarsa sak! da ruhinsa sosai take haifarsa masa da wani ciwo mai girman gaske a duk wani sashi na zuciyar tashi har da kasan ruhinsa.
Numfashi yaja mai karfi kafin ya kai hannunsa saitin kirjinsa inda yake tsammanin nan ne zuciyarsa take girke wani irin bugu takeyi a hankali a hankali wanda hakan ya tabbatar masa ta kamu da ciwo mai tsanani har yake kokarin sumar da ita.
Girgiza kai ya shiga yi yana jin yarda idanuwansa suke kokarin tara wani abu cikinsu wanda ko shakka ba yayi hawaye ne wanda shi kan sa bai san ya akayi har hakan take kokarin faruwa da shi ba da sauri ya sauke hannunsa yayi wa motarsa Key gami da kure karar sautin sifukun cikin motar yayi hakan ne ko zai samu sa'ida da saukin tunanin zuciyarsa sosai ya fizgi motar kamar zai tashi sama.
*****
A hankali yake tafiya yana jin yarda kafafuwansa ke wata irin karkawa kamar za su fice daga jikinsa sosai ya ke jin tashin hankalin da zuciyarsa take hakilo akai kamar zai tarwatsa masa kirji sosai yake jin lissafin tunaninsa na kwanya na kara wargajewa.
Bai san mai zai yi ba bai san abin da zuciyarsa take kokarin tunkuɗa shi yayi ba sosai ya barwa zuciyarsa gangar jikinsa take sarrafawa.
"Yaa Allah!".
Abin da ya fadi kenan a wahale kafun ya buɗe idanuwansa da yake jin su tamkar wanda aka daura musu wani abu mai girma sosai sun kaɗa suyi jajir.
Mutum ya gani tsaye yana kallonsa sosai fuskrsa na bayyanar da wani irin yanayi wanda shi ya kasa fahimta shima kallonsa yake yi da duk ganinsa sosai yake jin zuciyarsa tana sanar dashi ya san shi ya taba ganinsa ko ba ma a zahirance ba zai iya kasancewa a cikin mafarki sosai ya cigaba da ware idanuwansa akan sa yana karaton a inda ya san shi lokaci guda zuciyarsa ta canko masa.
Tabbas ya san shi sun taba haduwa kuma ko shakka ba yayi cikin asibitin nan ne suka hadu kwanakin baya can gyaɗa kai yayi kafun ya dan kauce gefe har lokacin idanuwan Dr.Aqeel na kansa sosai yake kallonsa yana karantar yanayin da yake yana kallonsa a ciki sosai ya fuskaci ba cikin hayyacinsa yake ba akwai abinda yake dawainiya dashi wanda ya kasance ba mai sauki ba ne.
Daga kafada yayi kafun ya gyaɗa kai alamun ko a jikinsa a hankali ya fara taku kan kafafuwansa yana jin wani abu na samun gurbi azuciyarsa akan Huzaif sosai yake jin abu sosai yake jin gabansa na bugawa a hankali ya tsaya da tafiyar da yake yi ya waigo ya sauke kallonsa kan Huzaif har yanzu yana yarda ya bar shi sai hannu da yaga ya saka cikin sumar kansa yana cakuɗawa.
Sosai Dr.Aqeel ke jin Huzaif bai kwanta masa azuciya ba sosai yake jin wani abu daban game dashi sosai yake jin abu mai girma na samun masauki game dashi tsaki ya dan ja kadan yana mai tsuke fuska, hada idanu sukayi tsakaninsu wani irin kallone ya sarke a idanuwansu kallo na rashin fahimta kallo ne na ba kayi mani ba.
Da sauri Dr.Aqeel ya janye idanuwansa a dan haryarce yayi hanyar Get din domin fita yana TUFKA DA WARWARA game da Huzaif sosai yake jin hankalinsa bai kwanta dashi ba...
"Yah Dr.Aqeel".
Kamar daga sama yaji muryarta na fadin haka ko bai ma dauki muryar ba mace daya ce ya sani ta na ambatar sa da wannan sunan a hankali ya lumshe idanunwa yana buɗe su kanta yana ware idanuwansa sosai lokaci guda ya jefa tunanin da yake yi a kwandon shara ya sanyawa fuskarsa murmushi mai karfi hannayensa ya sarke a kirjinsa yana jiran karasowarta fuskarta ita ma da murmushi numfashi taja lokacin da ta iso gareshi.
"Daga ina kike Mariya?".
Ya fadi yana mai tsare ta da idanu da alamun tuhuma.
Gyaɗa kai tayi kafun ta numfasa tayi kasa da kai.
"Umma ce take bukatar wannan".
Ta fadi tana mai nuna masa bakar ledar dake hannunta dauke da kankana da ayaba.
Ware idanu yayi kafun ya gyada kai
"Naje dakin ai bakya nan ita kuma ta zaga bandaki ganin ki da banyi a dakin ba shi yasa ma na fito waje".
Ware idanu tayi tana murmushi.
"Sai kace wacce za a sace shine ka biyo sahu".
"Uhmm Mariya kin ga wuce muje ciki nan ai a hanya muke ko".
Ya fadi yana mai kafeta da ido ba ta ce da shi komai ba suka fara takawa yana gaba tana biye dashi a baya sosai take kallon yarda yake tafiya cikin kwanciyar hankali da natsuwa lokaci guda ta dubi kanta sai taji wani iri a zuciyarta yanayin shi da ita sun bambanta sosai.
Sosai hankalin ta yayi nisa wajan kallon Dr.Aqeel tana tunanin yarda har ya amince ya shigo rayuwarta a yarda take wanda take ganin rashin dacewar haka kamar akwai nakasu a tarayyar sosai...
Ba ta kai ga gama lissafin tunanin ta ba kamar ance ta daga kanta wa zata gani da sauri taja da baya tana Ambaton Allah idanuwanta a warwaje wani irin bugu taji kirjinta yayi har sai da ta kai hannunta ta dafe rintse ido take yi gani take kamar a mafarki ba gaske ba sosai tsoro da wani irin yanayi yake bayyana a jikinta sosai take jin wani abu mai girma na saukar mata a zuciyarsa sosai taji zuciyarta ta ta shiga tsalle cikin wani irin yanayi wanda ta rasa a mizanin da za ta ajje shi ba abin da ke mata yawo aka sai sautin marin da tayi masa a can baya gani take kamar yanzu komai ya afku sosai taji ranta na baci da wani irin abu mai girma a hankali ta buɗe idanuwanta tana sauke su akansa sosai ta hango yarda idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir sosai take hango wani abu mai kama da tashin hankali cikin idanuwansa gabadaya take ganin yanayinsa a firgice yake sosai take hango yarda ya sauya ba kamar da ba yarda ta ganni sosai ta hango rauni mai girma a tattare dashi ba tare da jarumatar da ta san shi da ita ba
"Yaa Allah!".
Ta furta cikin karfin hali domin ji take komai yana wargaje mata na tunaninta sosai take jin wani abu na yawata mata cikin gangar jikinta gami da zuciya da ruhi wanda ta kasa gane menene haka din.
A hankali ta fara kokarin taks kafafuwanta da take jin sun sunyi mata nauyi sosai ji take kamar dutsen dala aka daura mata numfashi take ja yana kufce mata sosai tayi kokarin jan kafarta har ta iso in yake jingine jikin motarsa tana kokarin gifta shi kamar sautin muryarshi taji ya ambaci sunanta da sauri ta waiga ta sauke masa idanuwanta shima ita yake kallo da wani yanayi wanda ta kasa fassara ko na mene ne abu mai nauyi da girma ta ke hangowa cikin idanuwansa wanda hakan ba karamin narkar mata da jiki yake yi ba gabadaya taji tunanin kwanyarta na wargajewa.
Muryar Dr.Aqeel ta jiyo kamar daga sama hakan ya farfado da ita daga sumar da take tsammanin tayi sosai ta dago kanta ta dube in da yake dan nesa da ita tsaye hannayensa cikin aljihun wandonsa wani kallo taga yana yawatawa dashi a kanta wanda hakan ya kara firgitata sosai da sauri tayi kasa da kai kafun ta dago ta dubi Huzaif wanda ya gama zama kalar tausayi wani kallo ta watsa masa wanda ita kanta ba ta san ya akayi tayi masa shi ba.
A hankali ta fara takawa kafafuwanta na rawa sosai abu mai girma take jin ya danne mata zuciya yana kara luguiguita mata da gangar jiki da ruhi kanta a kasa ta isa wajan Dr.Aqeel wanda take jin kallon da yake watsa mata kamar ana watsa mata garwashi wuta.
"Waye waccan?".
Taji muryarsa ta ambata da wani irin yanayi wanda ta tabbata bacin rai ne a cikinta sosai da sosai ba ta san mai zata ce masa ba bata san wata irin amsa ya dace ta ba shi ba sosai ta fuskanci yana cikin yanayin bacin rai wanda ta rasa mai yasa hakan ya bayyana shin ko dai ya san Huzaif ne ko dai ya san wanene shi.
Tambayoyin da su dinga mata shawagi kenan cikin kwanya suna kara haifar mata da tashin hankali mai girman gaske.
"Dake fa nake Mariya kika yi shiru wanene waccan kin san shi ne?".
Sosai taji muryarsa ta kara buɗewa da sautin fushi a cikinta wani kaɗawa taji cikinta yayi ba ta taba zaton akwai ranar da za taji muryarsa haka ba bata taba zaton akwai ranar da zata ji magana irin haka mai dauke da daci a cikin ta ba girgiza kai ta shiga yi a hankali kafun ta kokarta jan numfashi.
"Ban san shi ba kawai dai...".
"Kawai dai me?".
Ya tare ta da sauri har lokacin muryarsa ba ta canza ta koma yarda ta santa ba.
Wani karfi taji ya zo mata cikin zuciya da sauri ta dago idanuwanta a rintse ta sauke su saitin Dr.Aqeel kafun ta juya ta kalli inda Huzaif yake tsaye har yanzu tana hango irin tashin hankalin da yake ciki.
"Gani nayi kamar yans cikin Matsala sosai naga haka a idanunsa shiyasa na ji ba dadi...".
Ba wai don ya yarda da maganar ta bane dari bisa dari domin zuciyarsa taki yarda da abin da yake gani jan numfashi yayi mai tauri yana kokari ajje maganar tata a zuciyarsa yana yarda da cewa ita ta hango tashin hankali game dashi ne shiyasa ta nuna jajantawa gareshi duban Huzaifa yayi daga inda yake tsaye yana hango tashin hankalin da yake ciki idanunsa sosai ya fuskanci wani abu cikin Maganar Mariya kuma zuciyarsa na karyata abin da yake zargi ba tare da yace da ita kala ba ya juya ya cigaba da tafiya jan numfashi tayi ita ma tana sake kallon Huzaif kafun ta kau da kai hadi da hadiye wani abu mai girma da ya tsaya mata a wuya ta daga kafafunta ta bi bayan Dr.Aqeel zuciyar cunkushe da abubuwa ma bambanta wanda ta kasa gane in da suka sanya gaba..
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA TAKWAS.
*In ka rike mani za na rike maka ribar zama yarda da juna farin cikina zana sanar maka kai ka damu dani.*
--Usaini Danko
A hankali yake ajje komai na shi kan table din dake girke cikin kayataccen office din sa kallo daya zakayi masa ka gane hanzarin da yake yi cikin aikinsa gabadaya hankalin sa bai wajan abin da yake yi idanuwansa na wajan kofar office din ji yake yi ajikinsa akwai wanda zai shigo zuciyarsa tana sanar dashi hakan.
Bayan ya kammala komai a hankali ya fara takawa kan ƙafafuwansa don ji yake yi kamar abin da yake muradin gani kum zuciyarsa na sanar dashi tabbatarsa kamar ba zai tabbata ba gareshi sosai yake ganin tafiyar lokaci wanda yake hango kurewa a cikin sa duk dakika daya gani yake yi kamar tafiyar awa daya ce.
Wajan sakatariyarsa ya dosa yana faman jan numfashi.
"Sir Morning".
Abin da ta fadi kenan bayan ta dago kanta jin alamun mutum kusa da ita.
Hannu ya daga mata alamun amsawa kafun ya shiga waige-waige na yan dakiku sannan ya sauke idanuwansa akanta yana mai nisawa.
"Areefa ta shigo aiki yau kuwa?".
Mamaki taf! A fuskarsa take dubansa sosai take lura da canjin ogan nata tunda Areefa ta shigo cikin ma'aikatar nan gaɓadaya hankalinda da natsuwarsa suka karkata akanta ba ta san mai hakan ke nufi ba...ko da dai bai kamata tayi mamaki domin ta san waye Dr.Erena tuni ta diga masa ayar tambaya katotuwa.
Kaɗa idanu tayi kafun ta motsa tika-tikan laɓɓanta wanda suka sha jan jambaki sai faman kyalli suke yi.
"gaskiya bana zaton ta shigo don ban ji duriyar ta ba yau sam".
Ta karashe tana mai kafeshi da idanuwa sosai ta sosai kai taga ya shiga girgizawa yaka faman cizon laɓɓansa gami da haɗa hannayensa waje daya yana lankwasawa suna bada wani sauti mai zurfi.
A hankali ya fara taka kafafuwansa da sanyi a cikin su amma yarda yake tafiyar cikin hanzari bai bayyanar da haka din ba kofar fita daga sashi ya dosa yana faman hanzari cikin tafiyarsa cikin kankanin lokaci ya sauka daga benen zuwa tsakiyar cikin company din idanuwansa ya ware yana yawatawa cikin sashi da sashi na ko ina.
Ya jima cikin wannan yanayin kafun ya isa wajan daya daga cikin ma'aikatan da suke nan din ko wanne da bangaren sa kamar office.
"Mufeeda Please ko kin ga Areefa ta shigo yanzu?".
ya fadi har lokacin idanuwansa ba su tsaya waje daya ba.
Dago kanta tayi jikinta sanye da abaya kamar ko yaushe dubansa tayi da wani irin yanayi kafun ta kau da kanta sosai taji sunan da ya ambata ya shiga kuwwa cikin kwakwalwarta sosai take jin sunan yana haifar mata da wani irin yanayi mai girma gareta zuciyarta taji tana zaro mata wani labari mai girma da ta daɗe da binne shi a filin zuciyar ta ta sunan Areefa take ji kamar a mafarki abubuwa da yawa take ji a ranta game da sunan.
Nisawa tayi cikin wani irin yanayi mai girma kafun ta dago kanta ta sauke ga Dr.Erena wanda shi a wannan lokacin sam! hankalinsa baya kanta sai faman watsa idanuwansa yake yi cikin ko wani sashi na ma'aikatar har izuwa babbar kofar.
"Areefa".
Kamar daga sama taji bakinta na nanata sunan da wata irin murya mai zurfi da wasu abubuwa masu girman gaske.
"Ban san taba ban ma taba ganin ta ba!".
Muryarta da zurfi a cikinta tashiga fadin haka da alamun bacin rai tattare da ita musamman yanayin da fuskarta ta sauya lokaci guda bacin rai sosai ya samu masauki a ko wani sashi na filin zuciyarta da ruhinta.
sosai yaji sautin muryar Mufeeda akansa wanda tunda suke da ita bai taba jin tayi magana mai zafi haka ba sosai yake kallon ta cikin yanayi na mamaki kafun ya nisa.
"bakuwar da ta zo last week fa nake magana wacce kuke matsayi daya da ita".
Sosai yake yawatawa da idanunsa akanta yana kallon yarda komai nata ya sauya lokaci guda kai ya shiga gyaɗawa kafun ya juya ya doshi babban kofar da zata sadaka da reception din Company din.
Tsaye yayi hannayensa zube cikin aljihun bakar suit dinsa sai faman yawata idanuwansa yake yi ta in da zai hango can wajan Parking ya tsayar da ganinsa yana bin motocin wajan da idanunsa daya bayan daya bai dire a ko ina sai kan wata bakar marsandi wacce kallo daya zakayi mata ka gane sabuwa ce fil.
Ajiyar zuciya ya ajje hakan ya tabbatar masa da Areefa na cikin Company din nan amma kuma ya akayi bai ganta ba har sashinta ya duba nan ma bai ganta ba ya tambayi abokan aikin ta suma sunce ba su ganta ba mai hakan ke nufi?.
A hankali ya fara juyawa kan kafafuwansa domin koma cikin Company zuciyarsa cike da tunnain Areefa da dalilin da yasa bai ganta ba cikin Company kuma alamun ya nuna ta na ciki tunda ga motarta nan hakan ya tabbatar masa da zuwan ta da wannan tunanin ya koma ciki bai sake duban kowa ya hau matattakalar da za ta haura dashi zuwa sashin sa.
Mufeeda dake zaune tun dazu ta zabga tagumi tun da ya zo ya sanar da ita wacce yake nema ya fada mata sunan da yake cigiya shikenan taji ta komai nata ya canza sosai taji wani iri a jikinta har ma da zuciyarta sosai take jin wani abu mai nauyi mai dauke da bacin rai ya samu masauki a zuciyarta a hankali take ajje numfashi tana duban Dr.Erena zuciyarta na kara tabbatar mata da abin da take zargi.
Gyaɗa kai takeyi tana yatsine fuska gami da tura laɓɓanta cikin bakin sai da ta dauki lokaci mai tsayi a haka kafun ta ajje komai gefe ta cigaba da aikinta amma ta zuciyarta sai kawo mata abubuwa take yi wanda yake kokari addabatar ya hana ta aikinta.
Tana cikin kokawa da zuciyarta kamar daga sama taji sautin takalmi ya karaɗe cikin wajan gabanta ne ya buga ko ba a fadi mata ba tabbas ta gane ko wacece mai wannan tafiyar bata dago kanta ba sai dai aikin da take yi cikin Computer ta tsayar dashi cak! hannayenta ta janye daga madannan computer din ta hade su waje guda tana sarke su a hankali kafun ta dago kanta a daidai lokacin ita kuma ta karaso daidai wajan da take hannunta rike da jaka mai kalar Gold da wasu yan duwatse masu kyalli da akayi mata ado da su jikinta kananun kaya ne wando da riga sai abayar da ta daura a kai gaban rigar abuɗe yake ta yane kanta da gyalen abayar fuskar nan ta sha Make-up sosai hanyarta a kunnan ta sai faman sakin murmushi take yi da alamun wayar da take yi din tana jefa cikin nishaɗi.
Kuri Mufeeda tayi mata da ido tana saka dan guntun biron dake hannunta cikin bakinta rana jujjuyashi tana yawatawa da idanunta sosai akan Areefa da ta tsaya daidai saitinta bugun zuciyarra na karuwa sosai da sosai abin da take zargi ne take ganin tabbatarsa zuciyarsa na kara hasko mata abubuwa da dama da suke kara tabbatar mata da zarginta.
Yaa Allah!.
Abin da ta fadi kenan lokaci guda tana dafe kanta da taji yana sarawa runtse idanuwanta tayi sai sai da ta dauki sakann kafun ta buɗe su har zuwa lokacinAreefa na nan tsaye sai dai ta gama wayar ta sauke duban Mufeeda tayi wacce ita idanuwanta na kanta lokaci guda sua sarke a idanuwansu sosai suke kallon junansu wasu abubuwa ne masu girma suke wanzu a zuciyoyinsu sun dauki mintoci a haka kafun Mufeeda ta kau da idanuwanta gami da yin kasa da kai ita kuwa Areefa kafadun ta daga gami da nuna halin-ko-in-kula ta ƙyaɓe baki tana mai daga wa Mufeesa hannu ta raba ta ta wuce cikin takunta na musamman da duk lokacin da zata shigo cikin Company din take yin sa.
*******
Sosai hawaye ke kwaranyo zuwa saman fuskarta sosai take jin zuciyarta na zafi da raɗaɗi sosai take jin tashin hankali wanda ba ta tsammanin ba mai girma baɓe a rayuwarta ba ta san ya zata koyi rayuwa ba a yanzu bata san ya zata koyi rayuwa ba batare da wadannan dangin ran ba bata san ya zuciyarta zata koyi kewarsu ba sosai take jin abu mai girma na samun waje afilin zuciyarta yana zama duk jikin ta take jin yayi sanyi yana haifar mata da abubuwa masu girma da kara dagula mata lissafi ba ta san ya rayuwa zata kasance mata ba nan gaba ba ta san wata irin rayuwa zata buɗe ba a shafin duniyarta in ta bar wannan wajan.
Hannunta ta sa ta shafe hawayen da suke sake balle mata wasu na bin wasu hada kayan su take yi cikin yanayi wanda ita kan ta ba ta san ya zata fassara shi ra san dai akwai tashin hankali mai girma da zai zo mata ko ma tae ya zo mata ba ta san ya zata dauke shi ba ta san ya za ta ajje tashin hankalin nan a zuciyarta za ta bar su za tayi kewarsu ta tabbata dole ne su rabu rabuwa ta har abada wanda bata tsammanin za su sake hadu a duniyar nan domin da ma can matsayin su ba daya bane ta sani sam ba su dace da zama a inuwa daya ba har su shaku ta sani zuciyarta...zuciyarta ba tayi mata adalci ba ba ta yi mata daidai ba ta sani tayi sake sosai da ta bar zuciyarta ta shaku da mutanan da ta san tabbas su rabu ko tana so ko bata so domin duniyarsu ba daya bane suna da tazara mai girma a tsakaninsu akwai katanga mai girma da tayi musu SHAMAKI a tsakani yau ta ga ILLAR SABO a rayuwarta tabbas sabo shi ake yi wa kuka dole tayi jinyar zuciyarta wanda ba ta san ranar da zata warke ba daga ciwon da ya kamata mai girma wanda laifinta ne da tayi sake har ta bar zuciyarta da gangar jikinta sukayi saboda da wadannan mutanan masu ALHERI da YAƘANA.
"Mariya!".
Taji muryar Umma na ambaton ta cikin yanayi mai cike da rauni da kuma rarrashi.
Da sauri ta sanya hannunta ta shafe hawayen da suke saukar mata kafun ta kokarta janyo yaƙe muryarta na rawa ta ansa mata gami da juyowa ta na fuskantar ta kallon ta take da duk wani rauninta dake cikin zuciyarta tana jin yarsa ruhinta da gangar jikinta suke haifar mata da wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa sosai take kallon Ummanta da yanayin da take ciki ta rame sosai sai dai kallo daya zaka yi mata kasan tana samun kulawa komai nata yayi normal duk wani abu dake damunta ya kau yanzu lafiya kalau take tana iya magana sosai cikin hankalinta ba tare da an samu matsala ba ko ya ya take sosai tayi wa Allah godiya da wannan ni'imar da yayi musu sosai take sake gode masa tafi kowa farinciki da wannan lamarin tafi kowa farin ciki da samun lafiyar Ummanta sosai take jin zuciyar na rage duk wani nauyi mai girma abu daya yake kara dakula mata lissafi in ta tuna shi Mahaifinta sosai take shiga tashin hankali mai girma sosai komai nata ke kara hargitsewa in ta tuna rashin matsaya da take dashi akam mahaifinta kullum cikin tunaninsa take ba ta san mai yasa ya tafi ya bar su ba a daidai lokacin da suke bukatarsa a filin duniyarsu ba ta san mai yasa ya bar su tsayin wannan lokacin ba bata san mai yasa ya dauki kafarsa ya bar su ba batare da ya sanar da su in da ya dosa ba sosai take shiga tashin hankali mai girma in ta tuna wannan lamarin.
Nisawa tayi kafun ta amsa kiran da Umman nata tayi mata.
"Ban san mai kike nufi da wannan kukan ba Mariya, Ban san mai kike so kuma ki daukowa kan ki ba, na lura sosai kike jin dadin zubda hawayenki baki san hakan yana matukar sanya ni cikin damuwa ba".
Shafe hawaye tayi sosai take jin maganganun Umma a zuciyarta sosai take fuskarta gaskiyar abin da Umma ta fadi sai dai bata san ya za tayi da abin da yake a zuciyarta ba sosai take jin rashin dadi ba ta san ya za tayi ta hana idanunta zubda hawaye ba.
"Umma Kiyi hakuri ban san ya zan yi in hana su zuba ba ne sosai take jin kewa a raina sosai nake jin rashin jin dadi a ko ina nawa saboda su mun shaku Umma suna da alheri sosai a duniyar su ban san yaushe za mu sake haduwa ba in muka rabu...".
Zuciyarta tayi rauni sosai muryarta ta karye hakan ya sanya ta yin shiru tana mai toshe bakin ta da taji kuka na shirin kufce mata.
"Yaushe zaki girma Mariya mai yasa kike abu kamar wata yarinyar da ke goye wa ya gaya miki kun rabu kenan har abada shin ce miki akayi daga nan lahira zaki tafi ba a duniyar zaki zauna ba to bari kiji mutum da mutum suna rabu sai su shafe shekaru masu yawa har su fiddo tsammanin sake hadƴwa amma cikin iko na Rabbi sai ki ga sun hadu har sun sake wata rayuwar a filin duniyarsu don haka ki daina YANKE TSAMMANI akan abin da bakin san yarda zai kasance ba Allah kawai za ki saka a lamarin ki ba fa rabu rigima a kayi ba balle ki ce tsakanin juna ba za a so sake haduwa ba ALHERI ne ya hada ku kuma kin san shi alheri a ko ina yake ba ya tafiya a banza".
Ba wai tana maganar nan ba ne don ta yarda ita akaran kan ta a,a kawai dai so take yi ta kwantarwa 'yar ta ta da hankali domin yanayin da taga ta dau lamarin mai gira a zuciyarta ko da yake tana da gaskiya zama lafiya aka ce yafi zama dan sarki zaman da akayi cikin aminci da mutunta juna dole a ji ba dadi wajan rabuwa ko zama da mutum kayi kullum kuna fada dole in za ku rabu kaji rashin dadi a ranka ta dani ita a akaran kanta abin da Mariya tayi ba ta ga laifin ta ba domin ta lura akwai sabo da shakuwa sosai a tsakaninta da likitocin asibitin tana kallon yarda suke mutunta ta da ahalin ta tana kallon yarda 'yar ta ta take ganin girman su da ba tare da raini ko wani abun kiba fiye da KWANA SITTI da tayi a asibitin nan kamar yarda taji likitan na fadi ta san dole ne su shaku sosai shakuwar da ba za su so rabuwa ba amma ba yarda za suyi rayuwa ta gaji haka aka rabu da mutum ma zuwa lahira kuma aka hakuri balle wannan a na cikin duniyar sai dai ace ba waje daya ake zaune ba.
Gyaɗa kai tayi cikin yanayi na tausayawa shiru ne mai dan tsayi ya ratsa cikin dakin ba abin da kake ji sai ajjiyar numfashin Mariya lokaci lokaci tana jan hanci da alamun kuka a ciki kawai daurewa take yi ba ta taba zaton za su rabu ba ba ta taba zaton magaɓar rabuwarsu a wata rana ba za ta tabbata kamar yarda Dr.Karami ke fada mata ashe da gaskiyar wannan ranar za ta zo filin duniyar su kowa ya kama gabansa ashe duk maganganun da yake mata masu shige da WASIYYA gaskiya ne amma ta kasa sanya hakan a zuciyarta taki yarda ta maganar tsa da take kallo a matsayin kanzon kurege bata san ruɗi da ya dauke ta ba bata san abin da ya shigar mata kai da zuciya ba ya hana ta hadda ce karatun Dr.Karami yanzu ga ranar ta zo ga cikin ta tsamo tsamo amma ta kasa yin komai sai nauyin zuciya da tashin hankalin da ta ke hangowa...
Sallamar da ta amsa kuwwa cikin dakin ne ta dakatar da ita daga zancen zuccin da take sosai taji wani irin bugun zuciyarta ya canza salo sosai taji wasu katangun tashin hankali suna kokarin rikito mata akai wani kuka mai karfi taji yana kokarin kufce mata bakin ta na rawa ta shigo kokarin amsa musu amma hakan ya gagara da gudu tayi hanyar Toilet din dakin hannayenta rufe da bakin ta kuka sosai take jin yana taho mata ta na shiga ta mai da kofar ta rufe durkushewa tayi a tsakiyar Tiolet gami da sakin wani irin kuka mara sauti mai matukar taba zuciya da ruhi da duk wani mai jinsa.
Sosai Dr.Karami yaji gabanda ya buga yanayin da ya ga Mariya a ciki idanuwansa ya sauke kan Umma da tayi kasa da kai sosai take jin wani iri a zuciyarta raunin da ta gani game da 'yarta ya haifa mata da tausayi mai girma a zuciya ta sani 'yarta ta shaku da su sosai shakuwar da sai anyi dagaske kafun a rabu dole zuciyoyi su shiga halin damuwa dole gangar jiki su shiga hali na rashin jin dadi sosai da sosai.
Kallon kallo suka shiga yi tsakanin su Dr.Karami da Dr.Aqeel sosai suke jin wani iri a zuciyoyin su musamman Dr.Karami don ji yakeyi kamar ya falla da gudu ya bita ya rarrashe don ya san tabbas ba abin da yake damun ta sai maganar rabuwarsu ba tun yau ba ya lura sosai take nuna dauwa da tsoro duk ranar da ya yi mata maganar rabuwar su bai san abin zai yi tsanani haka ba ko d yake shi tashi zuciyar yanzu haka ciwo mai girma yake jin yana fama dashi jarumta ce kawai take hana shi bayyanar sirrin dake ransasosai yake kewar Mariya duk da dai a ransa ba ya tunanin rabuwa za suyi ba ya hangowa rabu sam-sam cikin wannan lamarin amma dai yau a wannan rana shi a karan kan sa yana jin ba dadi don ji yake yi kamar wanda ya tashi daga cuta saboda rashin kwarin jiki.
Duban Dr.Aqeel yayi wanda shi dai yanayin ya nuna akwai abin dake damun sa a ransa sosai da sosai fuskarsa ta nuna rashin walwala jikinsa yayi sanyi sosai idanuwansa sun kada kadan kamar mai son fashewa da kuka.
Ba tare da yayi masa magana ya doshi kofar Toilet yana kwankwasawa a hankali yana kiran sunanta sosai yake jiyo shasshekar kukanta wanda haka ba karamin taba masa zuciya yayi ba sosai yake jin tausayi da wani abu mai matukar girma suna wanzu a filin zuciyarsa a hankali ya cigaba da kwankwasa amma ko alamun za ta yi magana juyowa yayi ya kalle su suma shi suke kallo musamman Umma wanda ta gama karantar yanayin su su duka sosai take jin tausayinsu duk su ukun na samun waje a zuciyarta ji take ina ma tana da wata dama da zatayi amfani da ita domin fidda su cikin wannan yanayi amma ina! ta san ba ta dashi gyaɗa kai tayi tana kau da kai daga barin kallon Dr.Karami.
A hankali ya rike Handle kofar ya turo sai ya ganta abude take da sauri ya karasa turawa yana mai sanya ƙafafuwansa da yake ji kamar za su zubda shi kasa saboda raunin da ya ji sunyi sosai.
Durkushe ya hango ta hade jikinta waje daya sai faman jan numfashi take yi mai zafi sosai zuciyarta take jin tana wani irin harbawa kamar zata faso kirjin ta ta fito waje komai take ji yana kwance mata komai na cikin duniyar take ji yana sauya mata lokaci guda.
"Mariyaaa!".
Ya fadi muryarsa da wani irin rauni mai girma idanunwansa a kan ta a hankali ta shiga kokarin dago idanunta da suka kaɗa sosai sukayi jajir kamar wanda aka watsawa barkono wani irin bugu zuciyarsa tayi wanda hakan sai da ya sanya shi sanya hannu ya dafe kansa duniyar yaji tana juya masa lokaci guda kau da kansa yayi don ba zai iya kallon idanuwanta a yarda suke ba wasu abubuwa ne masu girma yake ji game da kallonta suna faru dashi a filin zuciyarsa.
"Ban san mai ya kike haka ba, ban san mai kike wahalar da kan ki haka ba, Haba mana Mariya mai yasa kike zurfafa lamarin nan haka rabuwarmu ai ba ta na nufin mun rabu har abada bane a,a muna nan tare a duniya daya har zuwa numfashinmu na karshe."
Ba ta san ya zata dauki maganar ta sa ba bata san ya zata daura su a MIZANIN HANKALI ba sosai take jin zuciyarta taki aminta da zancen sa sosai take jin kawai fadi yake yi domin ganin ta daina kuka rintse idanunta tayi kafun ta mike kan kafafuwanta cikin wani irin yanayi mai rauni.
"Ta ya ya kake so na anshi maganar ka ta ya ya ka ke so na gasgata abin da kake cewa bayan nasan dole mu rabu dole mu raba duniya bana zaton maganganunka za suyi tasira Yah Dr.Karami kawai ka fito fili kace mani yau ce rana ta karshe a duniyarmu da muka hadu yau ce rana ta karshe a garemu yau ne za mu rabu da juna...".
Wani irin nishi tayi kafun ta gyaɗa kai hawaye su zubo mata wanda Dr.Karami yake jin su kamar saukar ruwan zafi a jikinsa.
"Ban san ko zaka yi maki alkawaro ba sosai na yi sabo da kai a duniya ta ban sani ba ko za kayi mani adalci a duniyarka ka kasance dani mu ke mutunci ba zan taba mance alherin ka ba kai da sauran Al'umma sosai nake hango matsayin ka a matsayin dan uwa na jini ban da yan uwa so nake ka zama dan uwa gareni ka kasan ce mani dan uwa bayan Mu'azzam don Allah in kayi mani haka zan yarda kuma zan rike duk abin da kace mani in har ka rike mani abin da nace da kai".
Rintse idanu yayi sosai zuciyarsa da kwakwalwarsa yake jin suna wani shawagi dashi a wani mataki wanda bai taba jin kan sa a ciin sa bai san mai zai ce mata ba bai san wani kalamai zai yi amfani da su wajan yi mata magana ba abu daya ya sani shine ba zai iya rabuwa da ita ba zai so ace yarda take maganar nan shim ya fadi mata shima haka yake ji ransa kamar yarda take ji.
Nisawa yayi kafun ya kokarta dubanta yana sani murmushi mai karfin gaske.
"Na yarda tuni na yarjewa zuciya ta zan ci gaba da zama dake a duniyata har zuwa karshen numfshi ne na yarda na aminci da maganarki na rike miki alkawari ke ma ki rike mani kamar yardakika fadi".
Shafe hawayenta tayi kafun ta saki wani murmushi kamar yarda ta ga yanayi mata.
Alamu yayi mata da kai su fice daga Toilet din tana yatsine fuska alamun kyankyami kunya taji kai a kasa ta bi bayan sa zuciyarta na rake duk wani nauyi da ya tokare mata kirji tun lokacin da aka sanar da su sallamar su da akayi.
Bin su sukayi da kallo Umma ta dubi Mariya tana harararta kasa tayi da kai kafun ta dubi Dr.Aqeel wani kallo taga yana yi mata wanda sai da ya sanya gabanta bugawa da sauri tayi kasa da kai tana cizon laɓɓanta abubuwa da yawa suna rikita mata kwakwalwa a tsakanin Dr.Aqeel da Dr.Karami abubuwa da yawa take hangowa a tsakanin su wanda ta kasa gane menene iya tsayin tunaninta da tsayin lokacin da ta diba tana nazarin su ta kasa gane mai suke nufi da wasu abubuwa da ta lura suna yi mata....
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA GOMA SHA TARA.
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'una mai nake shirin gani ni marka? Hafsi! Hafsi!! Hafsi!!!."
Goggo Marka dake zaune bakin kofa tana kadin zarenta ta mike tana tafa hannaye tana fadin haka idanuwa warwaje lokacin da ta ji sallamar su Mariya jikin ta har ɓari yake yi ta shiga dubansu kamar wanda ta ga wani mugun abu.
Cak! Suka tsaya suma suna dubanta musamman Mariya da idanuwanta su kayo waje tana duban ta ganin yanayin da ta nuna juyawa tayi ta dubi Umma kafun ta sake mai da kallonta zuwa wajan Goggo Marka.
"Mariya Habeeba daga ina kuma haka?".
Ta fadi cikin yanayi na mamakin ganin su.
Suma mamaki ne ya cika musu zuciya sosai da sosai sun rasa abin yi gabakidayan su sai bin ta da kallo kawai suke yi suna faman gyaɗa kai a hankali Mariya ta ja jiki a sanyaye ta isa bakin kofar dakin su da yayi kaca-kaca kamar wani kudundubi kofar dakin su har an girgiɗe ta labulan kuwa an yi fata-fata dashi ta na hango tsakar dakin yarda ya zama kamar wajan wasan yara sosai taji ranta ya sosu matuka gaya tsaki ta ja kadan kafun ta ajje kayan da suke hannunta wani irin duba tayi wa Goggo Marka da tayi tsaye fuska cike da mamaki sosai Hafsi da ta fito da daurin kirji kai ba dan kwali gashin kan nan nata yayi wani kerere kamar dambun karangiya sai fama yawatawa da idanunta take tsakanin Umma da Mariya cikin yanayi na mamaki kallo daya zakayi mata ka gane a firgice ta fito daga cikin dakin barci ne a idonta.
Kau da kai Mariya tayi kafun ta isa in da Umma tayi tsaye kamar wacce aka dasa kallo daya zakayi wa fuskarta ka gane bacin ran dake kunshe a zuciyarta ansar Mu'azzam tayi ta goya sannan ta dubi Umma tana mai rike mata hannu suka baro wajan suka iso kofar dakin nan bari ta samu damar dan gyara wajan sannan ta dauko zani cikin kayansu ta shimfiɗa wa Umma ta zaunar da ita daga nan ta shiga dakin tsaye tayi tana bin sa da kallo wani haushi da takaici gami da tukukin bakin ciki suka cika mata zuciya sosai take ganin yarda dakin ya sauya gabadaya kamar dakin mahaukata kallo take tana tunanin ta ina ma zata fara gyaransa don ta san tabbas wannan dakin ba zaunuwa zai yi ba haka kwafa tayi sannan ta fito daga cikin dakin Umma ta duba cikin yanayi na damuwa.
"Bari na siyo tsintsiya Umma domin wannan dakin ba zaunuwa zai yi ba dole a gyara shi".
Gyada mata kai kawai tayi itama ba tare da ta sake cewa komai ba ta duba cikin kayan su gudan duba ta dauko cikin kudin da Dr.Aqeel ya bata ta fice daga cikin gidan bisa mamaki har yanzu suna nan ba su tafi ba baki ta saki tana duban su kafun ta taka ta isa wajan su.
"Uhmm wai har yanzu...".
sai kuma tayi shiru ba tare da ta karasa abin da tayi niyyar cewa ba ganin irin kallon da Dr.Karami yake yi mata na alamun tuhuma.
"ina zaki je kuma da wannan ranar daga dawowarku?".
Shiru tayi kamar ba za tayi magana ba can ta nisa.
"tsintsiya zan sayo dakin zan share yayi kura ne sosai da sosai ba zai zaunu ba".
ta karashe tana mai yatsine fuska kamar za tayi kuka sosai take jin wani iri a ranta ba ta so ta fito ta tadda su ba ba ta so a wanna lokacin ta sake saka su a idanuwanta ba ta so ace yarda ta baiwa zuciyarta hakurin kewarsu na dan lokacin nan suma sun yi hakan sun tafi ba za ta so wani sabon lamari ya sake afkuwa ba a nan wajan domin ba zata manta tsawon lokacin da suka shafe a nan wajan ba tun isowarsu ake abu daya sai da Umma tayi da gaske sannan suka shiga cikin gidan bayan sun yi sallama amma kuma abin mamaki ta fito ta tadda su.
"Bari naje na sayo Umma na jira na".
Ta fadi cikin yanayi na damuwa domin ba za iya tsayuwa tana kallon su ba sosai take jin zuciyarta na zafi da raɗaɗi ba ta jira cewarsu ba ta fara tafiya cikin yanayi na sanyi jiki sosai ko da ta isa shagon mai tazara kadan da gidan su makalewa tayi taki dawowa tana hango su ba ta ga alamun suna da niyya tafiya ba sam! ita kuma ba ta so su sake gamuwa a cikin halin da take ciki a yanzu so take ta bai wa zuciyarta hakuri so take ta fara koyon zaman kadaici tun yanzu don ta san tabbas dole wata rana su dau lokaci mai tsayi kafun su hadu kuma ya zame mata tilas ta yi abin da Ummanta ba za ta shiga damuwa ba dole ta kau duk wata damuwa a zuciyarta don ganin walwala ga Ummanta.
Numfashi taja kafun ta hango sun shiga motarsu ta lura sosai kamar sun damu da rashin dawowarta kuma ta san saboda su taki dawowa don haka suka yanke hukunci tafiya hakan yayi mata dadi sosai da sosai sai da taga sun fice daga layin su sannan ta tako cikin sarsarfa domin a tunanin ta kila su dawo.
*****
"Mun shiga uku".
Cewar Hafsi tana daura hannu akai idanuwa warwaje kafun ta sake jan numfashi mai dauke da tashin hankali.
"ki ka ce mani sun tafi kenan har abada ba za su dawo ba, amma kuma ga su sun dawo kuma kin ce mani Habeeba ta zama MAHAUKACIYA amma dube ta kalau ba alamun hauka a tare da ita".
Goggo Marka da ta yi zaman yan bori kofar daki ta zabga tagumi tana duban Habeeba da ɗan dake hannunta wasu katangun tashin hankali taji suna rigizo mata akai ji take yi duniyar na juya mata ba ta yi zaton haka zata faru ba bata taba kawo hakan akan ta ba ta yi zaton sun tafi kenan ko duriyar su ba za a sake ji ba a duniyar nan tuni ta saki jiki take shan sharafin ta ganin lokaci sai tafiya yake yi kuma ba su dawo ba hakan ya kara gasgata mata zatonta amma yau rana tsaka irin wanna mugun abu ya zo mata wani numfashi taja ta fesar kafun ta dubi Hafsi murya kasa-kasa domin bata so Habeeba ta ji maganganun da suke yi.
"tuni fa aka tabbatar mani da ta haukace ita da 'yar ta ta da mijin nata...".
Da sauri Hafsi ta katse ta.
"Injiwa ya fada miki to wallahi duk wanda ya fada miki hakan karya ne ki dube su fa su duka kalau suke ba abin da ke damun su".
Nisawa tayi ta kai hannunta ta na susar kanta.
"ina ganin mugun abu kenan da gaske Habeeba ba hauka tay...".
Sallamar da Mariya tayi ne ya katse musu hirar da suke yi sukayi wuri-wuri da ido alamun rashin gaskiya kallo daya tayi musu ta kau da kanta a jikinta take ji akwai maganar da suke yi wanda ya dangance su kunuwanta sun jiyo mata kalmar hauka da Goggo Marka take fadi a zancen hakan ya tabbatar mata da Ummanta suke yi wato hauka tayi kenan daukar ta suke a matsayin mahaukaciya wani kunci taji ya tokare mata kirji sosai taji ranta na ɓaci amma sai ta share su ta baiwa banza ajiyarsu ta isa in da Umma kenan zaune ta zabga tagumi da alamun ita ma ta ji hira da suke yi a kanta don idanunta har sun tara kwalla kadan.
Sauko da Mu'azzam tayi barci ya ke yi hankali kwance a haka ta mikawa Umma shi ba tare da tace da ita kala ba ta dauki tsintsiyar da ta sayo ta shiga dakin a hankali ta fara tattara kayan su waje daya ta na fitowa da su waje zuciyarta na kunci da bakin ciki sosai take jin tausayin kan su sosai take hango irin kalar zaman da za suyi a gidan nan duba da tayi da halin Goggo Marka yana nan yarda yake ba sauyawa tayi ba sai abin da ya ci uban na da sosai take ganin za su fuskanci yanayin rayuwa a gidan musamman yanzu da suka kasance su kadai ba mahaifinta wanda shi kadai suke samun sauki a wajan sa to yanzu baya nan Allah kadai yasan halin da za su shiga cikin wannan halin ta hau tsaftace dakin yayi kura sosai bayan ta kwashe komi ta samo ruwa ta yayyafa a dakin saboda ba simitin in tana sharewa kuma kura na tashi sosai a haka cikin jarumta ta kammala sharewa sannan ta fito ta barshi ya sha iska kayan su ta ajje su gefe domin sun yi datti sosai suna bukatar zama na musamman domin wanke su sai da ta zauna ta huta sannan ta sake fita ta sayo kayan wanki sabulu da omo ta zo ta ja ruwa sosai ta jika kayan duk abin da take yi akan idon Goggo Marka da Hafsi sai faman bin ta da kallo suke suna faman yatsine fuska kamar sun ga abin kyankyami..
*********
Satin su Mariya biyu da dawo gida izuwa lokacin mutanan unguwa da yawa sun san sun dawo ana ta zuwa musu barka da arzuki da kuma ya mai jiki a nan suke samun labari wajan mutanan gari wai ai Habeeba hauka cewa tayi ta shiga duniya tun da ta haihu cutar hauka ta same ta ba a san in da take ba Mariya da babanta kuma suma sun ba zama duniya ne neman ta tun da suka tafi ba labarin su.
Abin yayi matukar daurewa Umma da Mariya kai sosai suka ji a ransu bisa wannan mugun fata da akayi musu na halaka ko daya ke ba suyi mamaki ba tun da sun san halin wacce ta kulla musu wannan makircin kadan daga aikin ta.
Ba su ce da ita komai ba sai dai suka barta da Allah domin kuwa halinta yafi karfin su.
Kamar ko yaushe yau ma Mariya na goye da Mu'azzam tana dauraye musu kayansu domin tun da suka dawo ko tsinke ba ta bari Umma ta dauke komai ba ita take yi rainon Mu'azzam duk yana wajan ta tun da ba nono yake sha ba sai madara anyi anyi amma ina yaki kamawa ko ya kama ya fara sha sai ya saki dole ta kasance madara ake bashi.
"Mariya".
Ta jiyo muryar Umma ta na kiranta da sauri ta ajje wanki tana amsawa ta doshi dakin.
"Yawwa yar Albarka amshi nan maza ki je gidan kultum ki sayo mani tafarnuwa".
Da mamaki Mariya ta dubeta.
"Umma Tafarnuwa kuma, me zakiyi da ita?".
"Yaa Allah! Mariya kenan. ba fa wani abu bane zan yi da ita kawai kafafuwa na ne naji suna rikewa na san kuma sanyi ne ba wani abu ba shine fa zan yi amfani da ita".
dan tsuke fuska tayi alamun rashin son abin da Umma tace.
"kawai ki bari Yah Dr.Karami ya zo sai a fada masa ƙafarki na ciwo nasan zai baki magani ni kam ban yarda ki yi amfani da tafarnuwar nan ba tun da ba likita bane yace ki yi amfani da ita".
Murmushi tayi ta san halin Mariya sarai tun da ta warke a cutar nan in dai za tayi abu to tabbas sai taji daga bakin Dr.Karami tun da yana zuwa musu lokaci lokaci ya duba jikin Umma.
"Shikenan naji taimaka dai ki sayo mani na ajje in ya zo duk abin da ya ce dashi zan yi amfani".
Fuskar a dan tsuke ta amshi kudin ta ficewarta Umma na bin ta da ido murmushi a fuskarta sosai take jin kaunar 'yar ta ta a ranta sosai yanayin rayuwarta take burgeta da komai na ta godiya take yi wa Allah da ya bata 'ya kamilalliya mai natsuwa da sanin ya kamata duk da karancin shekarun ta hakan bai hana ta sanin ya kamata ba idanuwanta lokaci guda suka kawo kwalla.
"Ina ka shiga ne ina son ganin ka a duniyata ya Allah duk in da wannan bawan naka yake Allah ka tsareshi ka tsare masa rayuwarsa ya Allah ka karkato masa da hankali ya dawo gaban iyalansa suna matukar buƙatarsa".
A bayyane take zancen zuciyarta take ji tana yi mata zafi tun lokacin da ta tsinci labarin tafiyar mijinta shikenan komai ya kara jagule mata ta rasa ina zata sa kanta abubuwa da yawa sun rikita mata rayuwa ita ba dangi ba ita ba iyaye ba sannan gashi yanzu miji ba ta san a halin da yake ba sosai take godewa Allah da irin ƙaddarar da ta samun kan ta a ciki sosai take goɗewa Allah da irin jarabtar da ya jeho mata cikin rayuwarta.
Dauke hawayen ta sake yi tana mai gyaɗa kai ita kadai ta san abin da take ji a zuciyar ta da kasan ruhin ta sosai rayuwar duniyar nan ke tsorata ta sosai take tsorota da komai na duniyar nan baki dayan sa.
*******
Sosai zuciyarta ta buga lokacin da idanuwanta suka hango mata shi zaune saman motarsa ya tallaɓe haba kamar wanda aka aikowa da mutuwa cikin dangin sa runtse idanuwa tayi gani take kamar a mafarki ba gaske ba laɓɓanta ta tura cikin baki tana cizawa a hankali zafin da take ji yana ratsa ta ya tabbatar mata da gaske shi din ne ba wani ba.
Kallon sa take da duk wani yanayi da ta tsinci kanta sosai ta hango sauyin yanayi game dashi sosai ta hango canji a gareshi ba kamar kwanakin baya ba wani abu taji yana mata yawo a zuciya sosai take jin jikinta na sakin wani irin yanayi yana kaiwa ga kafafuwanta kamar ba za su dauki gangar jikin ta ba.
"Yaa Rabbi!".
Ta fadi tana mai kau da kanta tana gargaɗin zuciyarta da ta daina abin da take yi akan Huzaif...
"Mariyaaa!".
Kamar daga sama ta jiyo sautin amon muryarsa mai cike da wani irin yanayi wanda ba ta san yarda zata ce yake ba amma dai da alamun rauni a cikin ta dago kanta tayi ta hango ya sauko daga kan motarsa ya doso in da take da sauri ta juya za ta koma cikin gida domin ba zata iya tsayuwa dashi ba sosai take jin ta a wani mataki wanda ya canza mata komai nata yake yaki da natsuwarta yake haifar mata da abubuwa masu tsoratar mata da zuciya da gangar jiki.
"Don Allah...".
Tsak! ta tsaya ba tare da ta waigo ba jin abin da yace sosai taji wani abu a muryarsa wanda ya kara rikita mata zuciya da kwakwalwa.
"Ban san mai zance miki ba, ban san abin da ya dace na fada miki ba wanda zai canza komai da komai a idanuwanki".
Nisawa yayi yana mai dafe kansa da yaji yana wani irin juya masa kamar zai watsar dashi a kasa bai san abin da zai ce da ita ba bai san abin da ya dace yace da ita ba bai san ya akayi ya zo nan wajan ba bai san akan abin da kawo shi nan ba gashi dai ga Mariya amma shi a karan kan sa bai san mai zai ce mata ba.
Sosai ta gane inda ya dosa sosai ta fahimci akwai abin da ke addabar zuciyarsa.
"Kayi hakuri na san ban kyauta maka ba...".
"Please Mariya mana".
Ya yi saurin katse ta jin abin da take fadi sosai ya ji wani iri a zuciyarsa.
"Ni ya dace na baki hakuri ni ne nayi miki laifi ni ne na aikata miki ba daidai ba afuwarki nake nema ba ban yi zaton kalamai na za su sanya ki ki tsane ni ba...ko da yake komai ya faru ni na jawa kai na don Allah kiyi hakuri".
Wani irin nauyi taji kanta yayi mata sosai taji rashin dacewa sosai taji kunya ta kamata ace mutum kamar Huzaif yake bata hakuri ta ya ya hankali zai dauka anya kuwa ba wata manufa a zuciyarsa anya kuwa zata yarda da maganarsa domin ita tun haduwarsu ta farko ta raina wa a zancin sa sosai ta gane bai iya lafuza ba...
"na san dole ki ji ba dadi a ranki amma duk da hakan ki daure ki yafe mani Mariya sosai da sosai na shiga tashin hankali a rayuwa tun haduwa dake na kasa sukuni komai nawa na rasa gane kan sa na sani kece...kece silar komai ya faru kuma na sani nine ban da gaskiya".
"Na yafe maka Allah ya yafe mana baki daya ni dama ba kayi mani komai ba".
Sosai ta gaji da maganganunsa shiyasa ta katse masa hanzari da amsar bukatarsa.
Wata irin a jiyar zuciya yayi kafun ya dubeta da wani irin kallo.
"Na gode sosai Mariya".
Gyaɗa kai tayi kafun ta dago idanuwanta ta dube shi sosai taji gabanta ya fadi saboda wani irin kallo da taga yana yi mata sosai taji wani iri a ko ina nata da sauri tayi kasa da kai.
"So Fine Boy waye wannan yaro mai kyau dashi".
Ya fadi yana shafar kansa.
"Kanina ne".
Ta fadi a hankali sosai taji dadi da yabon da yayi wa Mu'azzam hakan ya kara rage haushin sa da take ji.
"Don Allah bani shi mana mu gaisa".
Ya fadi yana mai kasa da murya gami da mika mata hannu a hankali ta kwance Mu'azzam ba tare da komai ba ta mika masa wata irin runguma yayi masa gami da manna masa kiss a fuskarsa a daidai lokacin Mu'azzam ya buɗe idanuwansa yana kallon Huzaif murmushi yayi masa shima nan da nan ya wangale masa baki hakan ba karamin burge Huzaif yayi ba sosai ya shagala da kallonsa yana yi masa wasa har ya so mantawa da Mariya ma a wajan.
Sai da tayi gyarar murya sannan ya dago ya dube ta da murmushi a fuskarsa.
"Yana da kyau sosai ina son sa.
Ya sunansa?".
"Ibrahim amma Mu'azzam muke kiran sa".
"Nice Name sunan nashi ya dace dashi sosai, ya fi ki kyau fa".
Ya fadi da sigar zolaya
Dariya tayi kadan kafun ta mika masa hannu.
"kawo sa Umma ce ta aike mu fa?".
Ba musu ya mika mata shi
Kamar daga sama sai ga Hafsi tsaye akan su ta na duban su daya bayan daya a sheke Huzaif ya dube ta sannan ya dubi Mariya kau da kan ta tayi hakan da ta nuna sai ya karanci wani abu game da ita shima sai ya tsuke fuska kamar ba shi bane yake yiwa Mu'azzam wasa yanzu.
Tsaki ta ja ganin sun ba banza ajiyar ta tayi cikin gidan tana kunkuni.
"Sai anjima ma ko nagode".
Ta fadi tana juyawa da sauri ya tsaida ita yana mai sanya hannu cikin aljihunsa kudi ya zaro masu dan dama ya mika mata.
"Gashi ki sai wa Mu'azzam cakulat sannan don Allah in kin shiga ki gaida Umma".
Irin kallon da ya ga ta na yi masa ne mai cike da tuhuma da ban so abin da kayi mani ba duk sai ya tsargu jikin sa yayi sanyi duk sai ya ji ya rikice ya rasa ma mai zai yi.
Girgiza kai tayi kafun ta saki wani murmushi.
"Uhmm rike kudin ka na gode sosai".
Ta na fadin haka ta taka kafa da sauri ta bar wajan kallo ya bita dashi yana faman gyada kai kamar wani kadangare har takule a sabule ya mai da kudin sa aljihu ya jima a tsaye cikin nazari kafun ya ja kafarsa ya isa wajan motarsa ya bar unguwar cike da abubuwa masu girma da suka saka zuciyarsa nauyi.
Duk abin da yake yi Mariya na laɓe a zauren gidan da tashige tana kallonsa sosai taji ya bata tausayi sosai take jin wani irin abu game dashi a zuciyarta musamman yarda ya baiwa Mu'azzam kulawa duk sai taji duk wani kunci da take ji game dashi yana bacewa daga filin zuciyarta gyaɗa kai tayi ta kara sa cikin gidan ta sayo tafarnuwar ta fito a hankali take tafiya zuciyarta na ta kawo mata abubuwa masu yawa suna samun gurbin zama a kofar gida ta ja burki ta tsaya tana gyara goyon Mu'azzam.
Horn taji anyi mata a bayanta da sauri ta juya gabanta na faduwa duk a tunaninta Huzaif ne ya dawo amma sai ta ga akasin hakan Dr.Karami ne zaune cikin motarsa ya zuru kafafuwansa waje ya sauke gilas din yana kafe ta da idanu sai faman murmushi yake yi ita ma murmushi tayi tana mai yin kasa da kai.
A hankali ya mike kan kafafuwansa ya karasa fitowa ya kulle motar yana takowa zuwa gareta har lokacin kanta na kasa
"My Boy ya kake?".
Ya fadi yana taba Mu'azzam shi kuma sai faman zillo yake yi alamun yana so yaje wajan sa sosai suka saba tsakaninsu sosai Dr.karami yake son Mu'azzam in dai ya zo gidan to tabbas Mu'azzam na hannunsa har sai ya tashi tafiya.
"Ina yini".
Ta fadi kanta a kasa bai kula ta ba illa kokarin zare Mu'azzam da yake yi a bayan ta ganin haka ya sanya ta kwance shi.
Daukarsa yayi ya rungume shi yana mai manna masa kiss shikuwa sai faman Dariya yake yi.
"me kika fito yi waje tare dashi da ranar nan?".
"Umma ce ta aike ne sayan tafarnuwa".
Kallon hannunta yayi ba tare da ya ce da ita komai ba ya fara taka kafafuwan sa zuwa cikin gidan domin ba ai masa shamaki ba Umma ta bashi dama ya dinga shigowa duk lokacin da ya zo ya daina tsayawa a waje.
Mariya bin sa tayi a baya har suka isa cikin gidan bakin Kofa suka hango Hafsi baje tana cin awara tayi ɗaiɗai da kafafuwanta sai faman jan hanci take yi tana gumi alamun yaji yayi yawa ko kallon su ba tayi ba su ma ba su bi ta kan ta ba sukayi sallama dakin Umma su ka shiga bayan ta ba su izini.
Bayan sun gaisa nan Mariya ta shiga korawa Dr.karami bayani akan tafarnuwar da ta sayo wa Umma dariya yayi sosai kafun ya numfasa.
"Mariya iyayen tsari to ai ba wani abu bane tafarnuwa tana da amfani sosai a jikin mutum ba ta da illar komai ana so mutane suke amfani da ita sosai ko a cikin abinci ne domin magani ce kamar yarda kika ji Umma ta fadi don haka sai ki kyale tayi amfani da kayanta".
Dariya Umma tayi mata itama dariya tayi tana mikawa Umma tafarnuwar.
Shiru ne ya gifta tsakanin su na yan dakiku kafun Dr.Karami ya ja numfashi ya dubi Mariya sannan ya dubi Umma.
"Umma dama akwai maganar da nake so muyi game da Mariya akan karatun ta ya kamata ace ta koma makaranta zaman ta hakan ba zai yuwuwa ba ya kamata ace a yarda take da kuruciyar ta ace tana makaranta yanzu".
shiru Umma tayi tana gyaɗa kai sosai taji dadin maganar Dr.Karami domin tafi kowa son Mariya tayi karatu domin karatun Mariya abu ne mai muhimmanci a garesu dama al'umma baki daya sai dai WANI HANZARI ba gudu ba ba a nan gizo ke saƙar ba...
"Umma karki damu nasan abin da kike tunani wannan duk ba wani abun da zai gagara ba ne ni aka ran kai na nayi alkawari zan dauki nauyin karatun Mariya tun daga yanzu har zuwa lokacin da zata kammala shi".
Wani irin duban hanzari Umma tayi masa tana girgiza kai ba ta san wani irin mutum bane shi sosai ta fuskanci mutum ne shi mai yaƙana da alheri a rayuwarsa ba abin da ya hada su ba dangin iya babu na baba amma jibi yarda yake dawaniya da su tun daga lokacin da ta shiga matsalar cutar ta har zuwa wannan lokaci bai gajiya ba ga shi yanzu ya dauko wani gagarumin aiki wanda ya kamata ace su iyayenta ya dace ace duk sun yi sa.
rintse idanu tayi wasu hawaye suka zubo mata ganin hakan ya sanya Dr.Karami saurin dubanta.
"Don Allah Ki daina wannan kukan bai dace da ke ba sam! Addu'a ya kamata ace kin yi kawai Allah ya tabbatar da alheri".
"Hisham ban san da bakin da zan gode maka ba kayi mani komai na rayuwa ba tare da kasan su waye mu ba nagode sosai Allah ya saka maka da alheri ya cika maka burukan ka na alheri ya kare maka rayuwa da zuri'a" .
"Ameen Summa Ameen".
Ya fadi yana duban Mariya wacce tayi kasa da kai tana faman hawaye sosai ya ji ba dadi a ransa ba zai iya cigaba da zama yana ganin hawayen su ba don haka ya mike ya na mai ajje Mu'azzam.
"Zan tafi Sai gobe kuma in Allah ya kai mu zan zo domin yin abin da ya dace".
Ya na fadin haka ya fice daga cikin dakin ya bar su Mariya shanye da baki suna duban junansu...
*KAMALA MINNA*😎😎
[8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
BABI NA ASHIRIN.
Dubansa take yi da wani irin yanayi na na raina wayonka da azanicin ka kafun ta kau da kai tana mai sakin guntun tsaki ta nisa cikin yanayi na haushi.
"Ban san mai ya hau kan ba Dr.Erena sosai ka bani mamaki ban taba zaton kalaman nan za su iya fitowa ɗaga bakin ka ba ka dube ni up zuwa down ban yi maka kama da mai karamin tunani irin naka ba aiki na zo yi a wannan company ba zaman zance mara kan gado ba".
Ta karashe tana mikewa kan kafafuwanta fuskar dauke da tsananin bacin rai sai dai kuma acan kasar ruhinta da zuciyarta ba haka bane domin kuwa murna take har da tsalle-tsalle Dr.Erena ya kusan fadowa komarta abin da ta jima tana KUDIRI da muradin tabbatarsa kenan.
"Areef..".
Da sauri ta daga masa hannu kafun ta dauki jakarta dake ajje kan table din Office din nasa.
"Ya isa haka bana bukata ban so ka takura min, in kuma kace takura min zakayi wallahi yanzun nan zan rubuta maka takardar ajje aiki...".
Da sauri ya mike jin abin da take fadi jikinsa har ɓari yake yi ya iso inda take tsaye ya kafeta da idanunsa da suka gama tafiya a duniyar Areefa.
"No Please ba sai mun je wannan matakin ba...But Areefa ya kamata ki fahimce ni mana alkawari nayi miki komai kike so kuma ko me kike so ayi na miki alkawari...".
Da sauri ta watsa masa wani kallo wanda yake kara rikita masa lissafi kafun ta tsume fuska.
"Ban san ta ya zan maka bayani ka fuskanta ba Dr.Erena ban san da wani irin kalami zan yi amfani ka gane abin da nake nufi ba".
Tana gama fadin haka ta fara taka kafafun ta ta doshi kofar fita zuciyarta cike da abubuwa masu matukar yawa.
Shi kuwa shanye baki yayi yana kallonta har ta fice kafun ya ajje wani numfashi mai karfi ya koma ya zube kan daya daga kujerun Office din nasa.
******
*FIRST CLASS INTERNATIONAL SCHOOL GWADA*
Sosai farinciki ke wanzuwa a fuskarta tun lokacin da Dr.Karami ya danko ta daga gida zuwa haɗaɗɗiyar makarantar da ya zaba mata zata cigaba da karatun ta.
Zaune take zuciyarta falla da farinciki mara musaltuwa har da guntayen hawayen na farinciki duban Dr.Karami take cikin wani irin yanayi wanda ita kanta ta kasa tantacce matsayin da take ji ya samu a zuciyarta sosai take jin matsayi mai girma game dashi a filin zuciyarta sosai take jin komai na canzawa a duniyar rayuwarta a yau daya kadai sosai take hango mafarkinta zai tabbata na son karatu da ta jima tana rokon Allah ya bata damar da za tayi shi yau gashi Allah ya jeho mata Dr.Ƙarami mutumin da bata taba zaton za ta gan shi a duniyar mafarkin ta ba balle a zahiri amma gashi Allah ya kawo matashi ta hanyar da bata yi zato ko tsammani ba.
Numfashi ta ja kafun ta dago kai ta na kallon Office din da ta baro shi a ciki shi da shugaban makarantar suna zantawa.
Kamar daga sama taji an dafa mata kafaɗa da sauri ta dawo daga duniyar tunanin da ta fada dago kanta tayi ta sauke kan wata matashiyar yarinya wacce a shekaru za suyi kai daya sai faman murmushi take sakar mata cikin yake ita ma Mariya ta sakar mata da martani.
"Sannu ko sunana Baseera Haruna Sa'eed ni sabuwar daliba ce da Dadyna ya kawoni yau ke ya sunanki".
Mariya da ta saki baki da idanuwa ta na kallon ikon Allah sai yanzu ta kyafta idanu kafun ta sake murmushi tana motsa laɓɓanta cikin mamaki da wannan kanzagi da zalaka na wannan yarinyar sai kace ta tambaye ta saki baki sai ratata zance take yi kamar an kunna rediyo ana sauraron shirin INDA RANKA.
"Karki damu haka nake shi kansa Dadyna aku yake ce mani wai na fiye surutu shiyasa yace kawai nafi dacewa na zama yar jarida".
'Kuma dai!'
Mariya ta fadi a zuciya tana tallaɓe haɓa kafun ta nisa.
"yo ai ni kin hanani ma cewa komai sai zuba kike yi dole dadynki yace dake Aku ke ba ki san ni ba nima ban sanki ba amma kin saki baki sai watso mani zancen ki ke kamar na tambaye ki".
Da sauri ta caɓe.
"Woohh ai na san ke ba mai cutar wa bace daga ganinki kina da kirki da natsuwa sosai da sosai domin dady yace in zan yi abokiya na samu mai natsuwa ba irina mai shegen surutu ba".
Dariya sosai Mariya take yi har tana rufe bakin ta mamaki take yi da halin Baseera sosai da sosai taji lokaci guda taji ta kwanta mata rai.
"to ni dai zancen ya tsaya nan naji abin da Dadynki yace yanzu dai ke a ina kike kuma aji nawa kike...".
yarfar da hannu tayi tana mai yatsine fuska.
"wai fa ss-1 nake daga makarantar da muka baro da yake dadyna ma'aikaci ne sai aƙayi masa canji aka kawo sa nan garin shine zai canza min makaranta wai sai dai a mai dani js-3 ki ji fa don Allah ai wannan ci baya ne kamar ni kuma fa ina da kokari sosai da sosai...".
"Yaa Allah! Baseera wai don Allah bakin ki baya ciwo ne don Allah tsaya ki ja numfashi mana".
Mariya ta tare ta tana mai kama hannunta ta na zaunar wa kan kujerar da take zaune a kai.
"karki damu akan haka nima yanzu placement zan rubutu na tafi ss-1 kin ga kawai sai mu tafi tare...".
Wata irin zabura tayi tana dariya.
"da gaske ki ke don Allah to shikenan ma na hakura da fa balli na tayar nace ban yarda ba amma tun da kin ce haka zan zauna saboda ke my abokiya".
"Yaa Allah Baseera Oh My God wai ke don Allah yaushe zaki yi hankali ne Yaa Allah!".
Wata murya ce suka ji kamar daga sama tana fadin haka da sauri Baseera ta zabura tana dosar mutumin da yake tsaye nesa dasu hannayensa sarke a kirjinsa sai faman kallon su yake yi da yanayi na damuwa a fuskarsa.
"dadyna zo ka ga my new ƙawa wallahi mai kyau da ita ga ta da natsuwa irin ƙawar da kace nayi...".
Janyo ta yayi yana jan kunnan ta wata karamar kara ta saki.
"Dady Please don Allah ba zan sake ba".
"Ban san yaushe zaki girma ba Baseera ke ko gajiya ba kya yi da surutu haba mana! a ko ina sai kin nuna halin ki nikam zan ce ma na fasa saka ki a makarantar ba zan iya da rawar kan ki ba...".
"wayyo Allah dadyna Please for give me I'll never do that again".
Yanayin da ta marare ce taka langwashe murya ya sanya shi dungure mata kai yana murmushi halin Baseera sai ita duk yarda ta san zai sanya ka ki daukar hukunci akan ta ta sani.
"Zo mije ka ga my New Ƙawa please dadyna".
ta fadi tana jan hannunsa shi kuwa sai fizgewa yake yu amma taki dai nawa har sai da ya bi ta sannan ta daina magiya har zuwa lokaci Mariya na zaune idanuwanta akan su duk abin da suke yi tana kallo wani burgewa da sha'awa suke mata sosai da sosai taji Baseera da mahaifinta sun burgeta yarda suke kulawa da juna da nuna soyayya tausayin kanta take tana tuno nata mahaifin in da yana nan da shi ma haka zai nuna mata soyayya fiye ma da ta Baseera amma ina! hakan ya gagara ƙaddara ta rabata dashi rabuwar da ba ta san a wani hali yake ba ba ta san yaushe ne zai dawo duniyarsu ba su cigaba da rayuwa a tare a inuwa daya.
Tsiwar Baseera ce ta dawo da ita duniyar zahirin ta daga ta tunani nisawa tayi taja murmushi kafun ta dubi mahaifin Baseera da yake tsaya yana dubanta.
"Ina yini dady".
Mariya ta fadi cikin muryarta mai sanyi da girmamawa a ciki.
Sosai yaji ta burgeshi sosai yaji yana so su kulla ƙawance da yarsa ya lura akwai natsuwa da hankali a tattare da ita.
"lafiya yau ya hakuri da aku mai bakin magana".
Murmushi ta saki don ta fahimci in da ya dosa da maganar sa kasa tayi da kai tana mai amsa masa.
"Dadyna ka ga ba ta fada min sunanta ba amma ni na fada mata".
Baseera ta fadi tana mai duban Mariya da take kallonta fuskarta dauke da murmushi.
"Yaa Allah! ta ya ya za ta fada miki bayan kin cika mata kunne da surutu Allah yasa ma tace ba za tayi kawancen ba...".
"Dadyyy!".
Baseera ta fadi da rigima a muryarta kamar zata fashe da kuka duban Mariya tayi cikin yanayi na mararecewa.
"Please don Allah fada min sunanki kin ji in ba haka ba nace ba zan yi makarantar ba ma".
Yanayin da tayi maganar da gaske take hakan ya baiwa Mariya dariya ganin da gaske take.
"sunana Mariya Bello Gwada".
"woohh so Fastastic Nice Name".
Baseera ta fadi tana mai kambama sunan Mariya.
Ya tsine fuska Mariya tayi kamar wacce aka tsikarawa allura da sauri Baseera ta ware idanu alamun tsoro tashiga tambayar ta lafiya mai ke damunta?.
Girgiza kai tayi alamun bakomai amma ita kadai ta san abin da take ji tun da ta tashi yau take jin wani iri a jikinta kamar bata da lafiya lokaci-lokaci take jin cikin ta da mararta na murɗa mata sai taji kamar numfashinta zai dauke amma ba wanda ta fadawa haka sai dauriya da take yi taki bari kowa ya gane sai dai in ya motsa mata take cizon laɓɓanta har ya lafa.
Miƙewa tayi jin mararta ta daure sosai tana faman cizon laɓɓanta sosai Baseera ta lura da haka da sauri tayi wa mahaifinta nuni da abin da Mariya take yi da sauri shima ya ware idanuwansa sosai akan ta kafun ya dafa kafadarta.
"lafiya Mariya me ke damun ki ko baki da lafiya ne?".
haɗe jikinta tayi waje daya ji take yi kamar kayan cikin ta za su zubo kasa da sauri ta durkushe kasa tana mai sakin numfashi da sauri-sauri hakan da Alhaji Haruna ya gani ya sanya shi firgita kadan da sauri ya kamo ta sosai yana mai duddubata Baseera dake tsaye kuwa jikinta sai faman ɓari yake yi idanuwanta lokaci guda suka kaɗa sukayi jajir.
"Dady what is wrong?".
Muryarta a raunane kamar mai son fashewa da kuka.
"Mariyaaa!".
Muryar Dr.Karami da karaɗe wajan lokacin da ya fito daga office idanuwansa suka gane masa abin da ya sanya shi faduwar gaba idanuwansa a warwaje da sauri yayi jifa da ledar dake hannunsa ya tako cikin sassarfa kamo ta yayi sosai izuwa lokacin har ta fara ficewa daga hayyacinta hakan da ya gani ya kara tsora tashi da sauri ya dubi su Baseera da Mahaifinta cikin yanayi na tuhuma kafun ya kau da kansa cak! ya dauke ta yayi hanyar ficewa da ita daga wajan hakan da suka gani su ma sai suka rufa masa baya wajan da yayi Parking ya isa ya buɗe gidan baya ya sakata ya rufe kafun ya dawo gaba ya shige duk abin da yake yi cikin yanayi na tsoro da fargabar abin da zai je ya dawo key yayi mata kafun ya fizgeta ya bar harabar wajan suma Su Baseera motarsu suka hau suka rufa masa baya.
Wani clinic ya nufa da ita dake kusa da makarantar cikin sauri yayi parking ya zo ya sungume ta yayi ciki da ita ba wani bata lokaci aka amshe ta kayi emergency da ita sosai Dr.Karami ya shiga tashin hankali ba abin da yake tsoro illa wani abu ya samu Mariya bai san abin da zai ce da iyayenta ba bai san da wani ido zai kalle su ba bai san a me za su dauke shi ba fata yake yi Allah ya saukaka lamarin Allah yasa ba wani abu ne ya same ta ba.
Kafadarsa yaji an dafa hakan ya san yashi tsayawa cak! daga Safah da Marwa da yake faman yi a kofar dakin da aka shigar da Mariya da sauri ya juye ya dube shi shima shi yake kallo kafun ya kau da kai bai san shi ba bai ma taba ganinsa ba amma sosai zuciyarsa ke nazarin mutumin domin kuwa abun da yafaru da Mariya a wajan su ne yana zargin su komai ya faru da ita su ne sila numfashi yaja kafun ya sake dubansa.
"Mene ne hadinku da Mariya mai kuka mata?".
Abin da ya fadi kenan muryarsa da zurfi a cikinta yana faman haɗe fuska waje daya.
Sosai Alhaji Haruna yayi murmushi kafun ya bugi kafadar Dr.karami kadan.
"Haba mana abokina karka zarge mu da komai a kan yar uwarka ba abin da muka yi mata...".
"Ta ya kake so na yarda da maganarka...".
Kafun ya dire ya jiyo muryar Baseera cikin kuka tana cewa 'Ina Mariya?'.
Mamaki ne sosai ya cika sa ya shiga duban Baseera da alamun tambayoyi masu yawo sosai yake kallonta ko zai gane fuskarta amma ina bai ga alamun sanayya ba a tattare da ita kuma bai san taba balle yace yar uwar Mariya ce.
"ya kamata ka fahimci wani abu a kan Baseera ba mu da niyyar cutar da ita kamar yarda ka ganmu a yau mu ma haka a yau mu ka fara ganin ka Baseera Da Mariya cikin wannan lokaci suka hadu na kawo Baseera zan saka ta a wannan makarantar to a nan ta gano Mariya har take cewa dani tayi ƙawa shine fa na zo ganinta har mun gaisa ma sai naga ta shiga wannan halin Dan'uwa karka zargemu da komai wallahi zuciya daya muke tare da ku ba mu da niyyar cutarwa gareku don nasan illar haka".
Tun da ya fara magana Dr.Karami ke dubansa da idanunsa sosai ya fuskanci gaskiya a cikin kalaman sa sosai ya gane mutum ne mai kamal da hankali gami da natsuwa lokaci guda yaji kunyar abin da yayi domin kuwa Alhaji Haruna zai girme masa nesa ba kusa ba.
Murmushi yayi yana sosa keya kafun ya dubi Alhaji Haruna.
"Afuwan na tuhume ku akan abin da ban san ya yake ba kuyi hakuri Mariya amana ce a waje na dole in shiga yanayi in na ganta cikin wani hali".
"kana da gaskiya hakan yayi daidai yanzu dai wani hali take ciki".
Gƴaɗa kai yayi kafun ya nisa.
"sun shigar da ita ciki domin dubata...".
Bai kai ga karasawa ba likitan da ya shiga duba Mariya ya fito yana duban su kafun ya ba su hannun suyi musabaha yana mai duban su daya bayan daya har ya dire kallon sa ga Alhaji Haruna.
"Kai ne mahaifinta ko?".
Ya tambaya kafun ya dora.
"karka damu tana lafiya lokacin ta ne yayi nasu na mata kuma bata saba ba shiyasa ta shiga wannan hali amma Alhamdulillah muyi settling din komai yanzu haka ta samu barci nan da 30mint komai zai zama normal".
Hamdala sukayi su duka kafun Alhaji Haruna ya nisa.
"Muna godiya Doctor sosai da sosai Allah ya bata lafiya".
"Ameen.Yanzu dai zan muku last na magungunar da za a sai mata tana amfani dashi".
Gyaɗa kai sukayi Dr.Karami shi dai shiru yayi yana mamaki yarda Alhaji Haruna ya zage yana nuna shine Mahaifi gareta ba tare da nuna eh da gaske ba 'yar sa ba ne hakan yayi masa dadi a rai lokaci guda yaji mutumin na burgeshi sosai da sosai.
Ko da ya dawo daga duniyar tunani mamaki ne ya sake kashe shi ganin Alhaji Haruna yabi likita Office din sa sakato yayi da baki ya duban hanya kafun ya dawo da kallon sa wajan Baseera da ta zauna ta zabga tagumi hannu bibbiyu kamar wacce aka aikowa da mutuwar wani a dangin su duk bakin surutu ya mutu kamar ba ita ba ce aku a dazu.
"Ya sunanki?".
Dr.Karami ya fadi yana mai duban ta cikin yanayi na mamakin yanayin da ya ganta aciki kuma ya san duk a dalilin Mariya ne.
Ba ta an sashi ba illa kallo da ta yi masa tana mai sauke numfashi mai kwari sosai.
"C'mon Baby girl tell me your name...ko ba kya so ƙawancen da Mariya ne".
Ba tayi niyyar ansa shi ba amma jin abin da yace ya sanya ta sauri dubansa da murmushin yake.
"Please don Allah karka hana Mariya ƙawance dani sosai nake son ta a raina a lokaci guda naji ta burgeni kuma Dadyna ya na son ta ya yaba da hankalinta sosai da sosai".
"Oya C'mon tell Now".
Murmushi ta saki ganin yarda yayi mata cikin yanayi na wasa.
"Baseera Haruna Sa'eed".
Sosai yake dubanta yana tunanin in da ya san sunan mahaifinta sosai yake zaton ya san sunan amma ya manta a ina ne ya san haka gyaɗa kai yayi kafun ya nisa fuskarsa da murmushi.
"Masha Allah to naji na amince kuyi ƙawance But...akwai sharaɗi kafun amincewar...".
"Na yarda wallahi tell me".
Ta fadi cikin yanayi na zagwadi dubanta yake yi sosai, sosai ya lura i Baseera irin mutanan nan ne masu barkwanci da wasa da dariya a ko ina suke.
"ban da wasa in an fara karatu ina so ku hada kan ku waje gudu sosai nake so naji ana alfahari da ku a cikin makarantar nan".
"Promise".
Ta fadi tana mai dariya burin ta ya cika na samun ƙawa a lokaci daya daga zuwa makaranta.
"hala tana nan tana yi maka halin nata na surutu kamar aku".
Muryar Alhaji Haruna ta yanke musu hirar tasu Murmushi Dr.Karami yayi kafun ya dubi Baseera da ta cuno baki gaba alamun ba ta so abin da dady yayi mata ba.
"Yaa Allah! Ai ba za tayi ba tayi mani alkawari dainawa in kuma ta cigaba ba zan barta ta cigaba da ƙawance da Mariya ba".
"yawwa kayi mani daidai".
"kai dady".
Baseera ta fadi fuska a shagwaɓe har sai da ta basu dariya su duka.
"ku tashi mu shiga mu duba ta ko?".
Ya fadi yana mai dubansu ai kamar jira take cikin hanzari ta mike tayi hanyar shiga dakin har tana kokarin buge Dr.Ƙarami shi kam dariya abin ya bashi shikuwa dady dafe kai yayi kawai yana mai duban Dr.Karami yana mai masa nuna da ido yayi hakuri ba ta da hankali murmushi kawai ya yi yayi gaba.
Kwance suka tadda ita sai faman sharar barci take yi kallo daya zakayi mata ka gane ta ji jiki a dan lokacin don har fuskarta ta fada sosai Dr.karami yaji wani iri a ransa ganin yanayin da Mariya take ciki ji yake yi kamar ciwon da yake jikinta ya dauko ya mai doshi nashi jikin bai son abin da zai sake taba mata rayuwa bai son abu ko ya yake ya rikita Mariya sosai yake jin tausayin ta sosai yake jin wani iri game da ita duk lokacin da take cikin hali na damuwa sosai yayi KUDIRI a zuciyarsa da ruhinsa da izinin Allah sai ya canza mata rayuwa sai ta ji dadin rayuwa sai taji dadin yan uwa sai ya zame mata yan uwan da take kwadayi a rayuwarta sai yayi iya kokarin sa don ganin ta fuskanci rayuwar 'yanci duk wani kunci da damuwa sun bar duniyar ta sai dai bai san ta yaya zai yi wannan aikin ba bai san wacce hanya bace da zai bi amma dai zai yi iya bakin kokarin sa don ganin rayuwar Mariya ta zama normal like others.
Sai da suka shafe awa daya kafun Mariya ta farko sosai da sosai take duban su da idanuwanta da suke bude runtse idanu tayi ta shiga tunano abin da ya faru da ita wasu hawaye suka zubo mata a hankali ta ja numfashi kafun ta buɗe idanunwanta Baseera ta gani kusa da ita ta mai sakin mata murmushi ta sanya hannu ta dauke mata hawayen da suke zubo mata.
"Sannu ƙawata".
Ta fadi cikin yanayi na taushin murya da jajantawa.
Ba ta ansa ba sai duban Dr.karami da tayi da ya tallaɓe haɓa ya zuba mata manyan idanuwansa masu firgita mata tunani gyaɗa kai tayi tana masa kallon tambayar me ke faruwa mai ya kawo ni nan?.
Sosai ya gane abin da take nufi amma sai ya kau da kai domin bashi da bakin da zai iya cewa ga abin da ke faruwa da ita so yake yi sai sun koma gida komai a natse sannan sai suyi magana sosai da sosai.
"ina ke miki ciwo Mariya?".
Alhaji Haruna ya fadi cikin yanayi na tausayawa gyaɗa kai tayi alamun babu.
"Masha Allah haka ake so Allah ya kara lafiya ko Mariya"
Gyaɗa kai ta yi kawai sosai take hango karamin ci irin na wadannan mutanan daga haduwa amma sun yi mata abun da wasu nata suka gagara yi mata sun bata kulawa da duk lokacin su sun tausaya mata da halin da ta shiga sosai taji sun samu matsayi mai girma a zuciyarta sosai take hango martaba da karamci tattare da su bata da bakin da zata ce da su komai sai fatan alheri.
Ba su jima cikin asibitin ba bayan dube dube da likita ya sake yi mata ya tabbatar da ba komai ya ba su sallama domin tafiya gida a tare suka fita Baseera da Dady su ka hau mota daya ba don ta so ba don cewa tayi sai dai ta bi Mariya gidan su amma Dady yace tayi hakuri zai kai ta da kan sa zuwa da yamma suna cikin wannan yanayin ne Mariya dake tsaye jingine da motar Dr.karami tana kallon diramar da ake yi da Baseera sosai taji wani abu a kafarta yana bin ta da sauri ta duba.
"Yaa Allah! Jini".
Ta fadi muryarta da karamin sauti da sauri ta dubi wajan da suke tsaye tana duban su a daidai lokacin Baseera ta dubeta ganin yarda tayi da ido ya sanya tambayar ta ko lafiya nuni tayi mata da kafarta da sauri ta iso gareta tana dubawa to da yake zata girmewa Mariya a shekaru sai ya kasance ta gane abin da ke faruwa kuma dama dazu taji abin da likita ya fadi da sauri ta dubi Dady da Dr.karami.
"Dady muje da ita gida don Allah She need help please dady".
Yanayin da tayi maganar sai ya sanya su duban Mariya da sauri don ba su gane akan me take magana ba.
Da idanu tayi musu nuni tsaf! Su ka gane ita dai Mariya kanta na kasa cikin hanzari suka shiga motar su suka dauki hanya da yake ba nisa gidansu Baseera tafiya kadan sukayi suka isa Babban gida ne kallo daya zaka yi masa ka gane mai shi yana da rufin asiri sosai da sosai get ne babba mai ruwan blue sai ratsin gold da kayi masa Horn daya sukayi aka buɗe musu gabadaya suka shige ciki bayan sun yi Parking duk suka firfito ita dai Mariya duk a tsora ce take sai faman haɗe jikinta waje daya take yi da sauri Baseera ta kama ta sukayi cikin gidan a falo su ka tadda Hajiya Abida mahaifiyar Baseera babbar mace ce mai cikar kamala da mutunci sosai ta dubi Baseera fuskarta da tuhuma.
"ba dai har kun dawo ba ina dadyn naki yake?".
Tana magana ta na duban Mariya da take haɗe jikinta kanta a kasa duban Baseera tayi da kallon karin bayani.
"later please Momy".
Ta fadi tana zarcewa da Mariya in da dakin ta yake suna shiga ta zarce da ita Toilet duk wani abun bukata sai da ta tadanar mata kafun ta nuna mata duk yarda zata yi sannan ta fito ta bar ta a Toilet din ma'ajiyar kayan ta ta nufa ta buɗe wata doguwar riga ta fiddo gami da wani hijabi mai kalar pink da ratsin kalloli daban daban wanda suka karawa hijabin kyau sosai bakin kafcecen gadon ta ta ajje su sanna ta zauna ta na mai zabga tagumi mintina goma Mariya ta shafe a toilat kafun ta fito tana raɓe-raɓe kamar mara gaskiya da sauri Baseera ta mike ta isa wajanta.
"dafatan kin yi yarda nace ko?".
Gyaɗa mata kai tayi domin wata irin kunya ce taji ta lullubet sai sunne kai take yi kasa.
"Uhmm Karki damu kin ji ko Mariya ba abin da zai sa me ki in Allah ya yarda".
Kai kawai take gyaɗa mata a haka har ta taimaka mata ta kara gyara jikinta bata kayan da ta dauko mata ta saka da kanta ta gyara mata fuska ta baɗe mata jiki da wani lafiyayyan turare mai sanyin kamshi.
Suna cikin kwalliyar ne Hajiya Abida ta shigo fuskarta dauke da murmushi tana duban Baseera.
"dakyau Auta ta kin kyauta da wannan taimakon da kikayi dadyn ku ya fada min komai dake faruwa".
Murmushi Baseera tayi ita kuma Mariya kasa tayi da kai don kunya.
"'Yawwa Mariya kisan mi yanzu lokaci ne da ya kamata ki kula da kan ki sosai ban da wasan banza ko kule-kule kuma don Allah karki sake ki kasance mai yawan zama cikin maza ke 'ya mace yanzu girma ya kamaki dole kiyi taka tsantsan da rayuwarki domin abu kalilan zai ruguza miki rayuwa ba fata ake ba amma tunatarwa na da dadi in Allah ya yarda Allah zai kare muku rayuwa da sauran 'ya'ya mata masu wannan lokacin Allah ya tsare muku rayuwa ku duka kin ji 'ya ta Mariya".
Sosai Mami tayi mata nasiha da tsoratarwa akan abin da zai rugaza mata rayuwa ba karamin dadi Mariya taji ba ta shiga mata godiya nan aka kawo mata abinci Mami ta saka ta gaba sai da ta ci sannan suka hada mata goma ta arzuki su ka rakota har falo in da Dr.Karami yake zaune da Alhaji Haruna ba karamin bugawa gaban Dr.karami yayi ba ganin Mariya ta sauya lokaci daya kamar ba ita ba ya shiga cizon laɓɓansa don tabbatar da Mariya ce ba wata ba wani murmushi ya sakar mata kafun ya mike bayan yayi wa su Alhaji Haruna godiya da karamci da sukayi musu har wajan mota suka rakosu nan Baseera ta sanar da Mariya anjima da yamma in sun taso islamiyya zata zo gidan su a haka sukayi sallama suka tafi zuciyoyin su fal da farin ciki mara musaltuwa.
Tun da suka baro gidansu Baseera ba wanda yayi magana a tsakaninsu Mariya sosai ta haɗe jikinta waje daya kirjinta taji yana bugawa a hankali ba abin da ke yi mata yawo akai sai abin da ya faru da ita da kuma irin maganganun da taji Mami na fada mata wanda ta tabbatar haka abin yake rintse idanu tayi ganin abin take yi kamar almara kamar cikin mafarki ba gaske.
A bangaren Dr.karami shima mamaki ne ya cika shi ko da yake in yayi duba da yanayin ta lokacin ta yayi a matsayin sa na likita zan iya gane haka wanda ma ba su kai shekarunta ba ma sun yi balle ita da yake zaton za tayi 16years.
Da wannan tunanin da zuciyoyin su suke suka isa gida daidai kofar Gidan yayi Parking tsayuwar motar ne ya dawo da Mariya duniyarta da sauri ta dago kai dubi bangaren Dr.Karami da sauri tayi kasa da kai domin ita yake kallo a hankali ta sanya hannu ta buɗe kofar ta fice kamar daga sama idanuwanta suka hango mata abin da ya kusan sanyata sakin fitsari Huzaif ta hango zaune saman motarsa ya haɗe kansa da gwuiwarsa bisa alamu ya jima a wajan zaune da sauri ta juya ta dubi Dr.karami wani irin kallo ta ga yanayi mata mai cike da tuhuma sosai ta hango wani irin yanayi mai kama da bacin rai a fuskarsa kasa tayi da kai da sauri ta fara taka kafafunta wanda take jin su kamar za su narke sosai take jin kanta na wani irin juyawa kamar zai dare gida biyu duk taku daya in tayi sai ta ja numfashin ta da taji yana barazanar daukewa ba ta kai ga shig gida ba taji kugin tsayuwar mota da sauri ta juyo Dr.Aqeel ta hango yana fitowa daga ciki motarsa idanuwansa akan ta sosai ta firgita ganin wani kallo da shima yake yi mata wanda bata san da me zata fassara shi ba a ranta ta furta.
"Yaa Allah! me ke shirin faruwa da ni ne?".
Ai ba ta san lokacin da ta ja kafa tayi cikin gida ba sai faman haki take yi ba ta tsaya ko ina ba sai cikin dakin Umma ta baje kan katifar dake yashe cikin dakin sai faman sakin hirji take yi gabanta na faman bugu kamar zai tarwatse komai taji yana juya mata Umma da ke zaune ta shiga dubanta da mamaki da farko ba tayi zaton Mariya ba ce sai da ta kalleta sosai domin kayan da ke jikinta ba ta san ta da su ba tana kokarin yin magana ta tsinkayi sallamar Dr.Karami da sauri Mariya ta kara dunkulewa waje daya tana cusa kanta cikin hijabin dake jikinta gabanta na kara tsananta bugawa.
Ko ta kan ta bai bi ba Umma kawai yayi wa bayani abin da ya faru mamaki sosai taji nan ta shiga yi masa godiya amma shi ina hankalinsa na kan Mariya wani kallo yake watsa mata ta gefen ido kafun ya dubi Umma muryarsa da sanyi.
"Umma na mance shaf! in Allah ya kai mu gobe zan koma can wajan aikina domin hutun da na dauka ya kare ina muka fatan alheri sai na dawo".
yana gama fadin haka ya mike saman kafafuwansa Umma kuwa sai faman sheka masa addu'a take yi da neman tsari.
A haka ya fita ba tare da ya dubi Mariya ba baya ya ajje wa Umma bandir din kudi masu yawan gaske duk da zuciyarsa sai a zalzalar sa take yi
ita kam Mariya ba a maganarta domin lokacin da taji abin da ya fadi ba ta san lokacin da hawaye suka wanke mata fuska ba wasu katangun tashin hankali suka rikito mata akai lokaci guda taji wani zazzabi na shirin rufe ta gabadaya ta kasa motsi jikinta gabadaya taji ya canza kamar ba na ta ba komai taji ya sauya mata a kankani lokaci tsoronta daya Allah yasa ba fushi yayi da ita ba ya yanke mata wannan danyen hukuncin mai barazanar tafiya da numfashim ta kuka take yi na zuciya idanuwanta sai zubda hawaye suke yi sosai take hango tashin hankalin da za ta shiga in ba Dr.karami ta dade a wannan yanayin kafun wani mugun barci yayi awon gaba da ita ya je fata wata duniya mai dauke da Dr.Karami wanda ta kasa tantace ta mene ne sannan ta kasa gane wata irin rayuwa ce suke yi sosai ta hango tashin hankali mutane uku take hangowa ko wanne kuma ita ya dosa da abu mai girma wanda ta kasa gane mene ne?