Ruwa ya kuna, jin ruwan heater din ba zafi sosai yasa yasan yau ba'a kawo wuta ba.
Wanka yai a toilet din ya fito yasa jallabiya,yasa turare spray na turarensa Lynx sannan ya fito ya nufi waje yana jin mostinta a kitchen, kokarin zuba man daya taho da shi yai ya fara duba wayar gen din.
Karar dayaji ya fito daga ciki ne ya sashi shiga ciki da gudu, kitchen ya shiga, tuwon da take tukawa ne ya zubo mata a hannu ta kone, dagowa tai ta kalleshi idanunta sun ciciko, da sauri ya karaso ya rike hannun fitilar wayarsa ya kara haskawa bayan hasken fitilar kitchen din, ganin yanda gun yai ja yasa ya jata jikin sink ya fara zuba ruwa, kwace hannunta tai sannan ta juya zata koma gun tukin tuwon.
Hannu yasa ya kara riko saman hannunta, ya dawo da ita jikin fanfo hannun ta ta shiga kwacewa, tace "sakeni" tai maganar cikin rawar murya.
Bai kulata ba ya cigaba da zuban ruwan, yana gamawa ya fara mata addu'a a gun ganin ba zuma a gidan dan yaga haka umma keyi, sai yaga inta kone sai ta shafa zuma.
Kara fizge hannunta tai ta fara kokarin komawa gun tuwon.
Kafadarta ya kamo da karfi yace "ki bari mana, so kike ta tashi?"
Wani kallo tamai hawaye suka zubo mata tace "ta tashi din, ba dai tuwo kake so ba?"
Hannu yasa ya rage gas din sosai sannan yasa hannu ya jaa ta zuwa falo, suna zuwa ta kwace hannunta tana neman komawa, kara kamota yai, kallansa tai ta ce "sakeni" tai maganar cikin wani irin rauni.
Naki
Sakeni please ta fada hawaye na gangaro mata, naki nace
Karfi ta fara sawa tana kokarin kwace kanta hakan yasa ya ja ta jikinsa ya rungume, hannu tasa tana kokarin toreshi sai kuma kawai ta fashe da kuka.
Har cikin ransa yake jin kukanta, kuka take sosai hakan yasa gidan ba abinda kake ji sai kukanta da alama ta dade tana tarashi.
Sai datai mai isarta sannan ta dago ta kalleshi idanunsa sunyi jaaa sosai, tace “Bazan iya zaman nan ba Allah.”
Kallanta yai yace "ke yarinyace haryanzu? Shekararki nawa? Har sai yaushe zakisan aure ba wasan yara bane? Haka kikaga iyayenmu na yi?”
Hawaye ne ya gangaro mata tace "haka ake auren? Tunda nazo gidan nan banda aiki me kake sani? Tun asuba in ka fita sai rana sannan kana dawowa abinci kawai kake ci ka fita sai dare, ni kadai a gida kamar mayya? Kwana biyu zuwa uku jinsa nake kamar na shekara, bazan iya ba wlh, gashi kai kullum fada bafa fadan ke ban haushi ba ni da nake yin duk abinda ka sani haushin kaina nakeji, maidani gida dan Allah, na hakura da komai ma.”
Ta karasa maganar tare da kara zubo da hawaye, na tsawalla ne? Nasan bazata gyaru lokaci daya ba, na zafafa mata ne? Daga zuwa? Tambayar da zuciyrsa tamai kenan, amma ita ba yarinya bace sai yaushe zata daidaita kanta?
Dago fuskarta yai yasa hannu yana share mata kwallar.
Hannu tasa ta ture hannunsa tace "nasan ba damuwa kai dani ba ban kuma nemi hakan ba amma a kalla ka dinga........"
Bakinshi da taji cikin nata ne yasata yin shiru, lab'an bakinta ya tsotsa sannan ya kalleta, idanunta ne suka rarage girma tana kallansa cikin wani yanayi, a hankali ta bude baki zata sake magana ya kara sa bakinshi cikin nata, yanzu kam harshenta ya kamo, samun kanta tai da maida mai murtani, jin yanda yake mata salo ne yasa taji kafafunta na neman kasa daukanta, ganin yanda tad'an murguda kafa kad'an ne yasa ya dan turata jikin kujera, har a lokacin bakinsa na cikin nata suna sumbatar juna cikin wani yanayi yoo abinka da me aikin karfi balle an kai lokacin ba a d’ana ba🙊
A hankali ya dago ta ya bude idanunsa da sukai jaaa, itama idanunta ta bude a hankali tana kallansa, a hankali cikin magana mai kamar ta rad'a muryarsa a dan daushashe yace "bakyasan na dinga barinki ke kadai?" Yai tambayar yana kokarin ce mata zan yi kokarin ganin na baki lokaci na.
kallansa tai kawai sai jiyai tace "Ka dauko mana gen din........"
Duk da yasan abinda ke ranta kenan amma a wannan yanayi da yake kokarin fitarda hakkinsa bai kawo zaiji haka ba.
Kallanta yai yace "shine matsalarki kadai?"Yai tambayar cikin wani yanayi da duk wanda yaji zai san yayitane ta rashin jin dadi kalamanta.
Eh ta fad'a kai tsaye.
Wani murmushin takaici yai sannan ya daga ta yace "kiyi aiki har illa masha Allah."
Ya juya ya fita ya koma waje? da kallo ta bishi dan ya tado mata da sha'awar data manta da ita, me ya sameshi? Ko dayake shi me zai saneshi kullum ransa dama a bace yake.
Khalid kam a waje zuciyarshi takai matuka gun baci, hada gen din yai ya sa socket din ya tada, tana jin karar gen ta fito waje cikin jin dadi, ganin wuta ta bayyana yasata kallansa cikin jin dadi matuka.
Ko kallanta baiba ya wuce ciki, biyoshi tai tare da rufe kofa, tace "ashe ka siyo?"
Bai tanka taba ya wuce dakin.
Ganin yanda ya shiga yasa ta juya kitchen, da kyar ta kwashe tuwon saboda hannunta daga ta sashi gun zafi sai taji gun na zafi.
Haka taita duba kitchen din ganin kubewa bushashiya yasa ta kada ta kawo falo.
Daki ta shiga yayi sallar isha'i ya hau kan gado rigingine, ya riga ya taso da abinda bazai iya maidashi ba, na kai ma abincin, ta fada tana saurin matsawa gun laptop tana kokarin zama, ganin yaki motsawa yasa ta matso tace "na kai"
Ta fada tana dan tabashi dan ta dauka ko bacci yake.
Ganin bai motsa ba yasa a ranta tace “ya gaji ne?”
Juyawa tai har zata xauna sai kuma ta kalleshi ganin alamar bacci yake yasa ta cire kaya ta wuce toilet, dan taji duk kanshi abin girki takeyi.
Wanka tai ta daura zani tare da rufa mayafi a saman kanta, bude kofar tai ganin haryanzu yana nan a yanda yake yasa ta fito.
Taku biyu ya dago ganin yana bukatar fita waje, kallanta yai, itama ta kalleshi, sam ta manta yanayin da take tace “ka tashi?”
Wani abu ya hadiya, yana kallanta, ganin yanda idanunsa sukai ne yasa tace “bakajin dadi ne? Ko gajiyaya?”
Baisan tanka ta dan kalamanta na d’azu ba karamin bata mai rai sukai ba, neman dauke idanunsa yai daga kanta.
Mikewa yai rai a bace yana kokarin barin daki, hannu tasa ta riko hannunsa ba tare da tayi shawara da zuciyar ta ba, tace “bakajin dadi ne?”
Kallanta yai kawai ya kwace hannunsa ta dauka fita zai kawai taga an kashe wutar dakin.
Hannu yasa bayan ya dawo ya jawo nata hannun, a hankali ya karasa da ita kan gado yana jin wani abu na kara taso mai.
Mikewa tai kafin tai wani yunkuri ya maidata, Kh.......
Jin bakinsa cikin nata ne yasata yin shiru, wani irin salo yake da shi kansa baisan ya sani ba, a hankali ya kai bakinsa kan wuyanta, wani irin yanayi ta tsinci kanta a ciki wanda tunda tazo duniya bata taba ji ba, hannu yasa a kan zaninta, cikin wani yanayi na rashin karfi ta sa hannu saman hannunsa, idanunta a lumshe.
Hannu yasa ya ture hanun nata ya zare mahafin xanin, sam Khalid ya gama fita hayyacinsa, balle su Zainab wacce aka tsinci kai a wata duniyar da ba’a taba zata ba, bakinsa yakai...........nai fito a guji, ai takalmi nama sai daga baya na dawo na dauka.
********
Sai da ya kammala sannan nutsuwa ta zo mai, a hankali ya mirgina tare da lumshe idanunsa, Zainab kam bata taba kawo wannan yanayi ba sai dai gaba daya kwakwalwarta ta tafi dan ta manta meya faru a dan lokacin nan, bata san a wani yanayin ta tsinci kanta ba, shekararta 4 da Adam ya akai take jin kamar yau ta fara?
Dagowa yai ya kalleta, ganin idanunta a kansa yasa suka hada ido, da sauri ta dauke nata idon, Khalid duk da hankalinsa ya kwanta amma haushin rashin hakurinsa yake, yaso ya barta da aikinta data aura.
Mikewa yai ya shiga toilet, ya kara yin wani wankan, yana fitowa ya zubama inda take ido, juyowa tai jin motsin ya fito kuma taji shiru, ganin yana kallanta, yasa itama ta zuba mai nata idan, tana san sanin tunani me yake?
Dan hasken dake fitowa daga toilet ne yake dan haske dakin kadan, ganin yaki dauke idanunsa yasa tace “akwai ruwan zafin?”
“Kadan” ya fada tare da wucewa jikin wardrobe, mikewa tai bayan ta gyara zaninta sannan ta fara kokarin saukowa daga kan gado, ta sako kafa daya zata sako dayan tai baya da sauri ya rikota, mikar da ita yai, kallansa ta sakeyi a hankali sannan ta juya.
Hartaje bakin toilet ta juyo ta kalleshi, meya sameshi? Ta tabbatar da dane sai yayi magana, kunya yakeji? Abinka da saurayi tai maganar a ranta gana wanka.
Shiru tai tana tunanin abinda ya faru a d’an lokacin nan.
Murmushi tai ita kadai sannan ta karasa ta fito.
Ganin baya dakin yasa ta fito falo, a kwance ta ganshi baiko ci abincin ba, kuma da alama yayi bacci.
Kallansa tai cikin mamaki, kusa dashi ta matso tace “Abincin fa?” Ta tabashi tana tambayarsa.
“Naci dumame, banaji zan iya cin wani abu ynzu.”
Ido ta zubamai, danta a bace wato ya sata tai abinci sannan yace “bazaici ba?”
A kufule tai ciki, yanajin rufe kofarta, ido ya rufe.
Tana aiki tana masifa haushi ma ya isheta ta rufe laptop din, fitowa tai waje ta shiga duba yanda ake kashe gen din tana kashewa ta wuce ciki kallansa tai a falo a kwance cikin jin haushi tace “inyasan a falo zai kwanta ai ya dauko bargo da pillow.”
Ta wuce ciki harta kwanta taji ta kasa bacci ta dauko ta fito dashi, kusa dashi taje ta samai bargon ta ajiye pillow din ta juya.
Hartai bacci ranta a bace yake.
*******
Ina kudin da Rahinatu tace ta aikon dashi jiya? Naira hamsin?
Goggo ta kalleta tace “Hanne wai dan Allah ni ba yyar mijinki bace zaki sani a gaba da fad’a? Akan ma naira Hamsin?”
Yo ko shi mai gidan ne yacimin hamsin ai naji dalili bare ke kece kika min sirfen? Billahi lazi sai kin biyani hamsin dita.
Goggo tace “zan baki hamsin sau hudu ma amma ki bari Adam yazo.”
Kan bala’i to wlh yau ko za’a mutu sai kin biyan.
Akan tsinanita hamsin kike min masifa?
Tsinaniya? Inyi sirfen in sameta kice tsinaniya?
Yo me akai akai hamsin banda talauci?
Ran Hanne ya kara baci tace “to wlh sai kin biyani in ba haka ba kuma wlh daga yau har kwana biyu bake bacin abinci a gidan nan.”
Sadiya zo ki ban Hamsin naba matarnan.
Sadiya dake sirfe waken alalen siyarwa tace “badai nawa ba kam wlh, kina gani abin aurena nake hadawa.”
Ta juya tana aikinta.
Hanne tace “to wlh ki shirya dakon yunwa.”
Yo a wani abincin? Dumamen tuwo ko saban tuwo?
Koma menene.....
Ta fada tai ciki.
********
Sau uku kenan tana kiran Adam bai dauka ba, kwafa tai tace “zaka san nika wulakanta wlh.”
Adam kam daga yaga kiran Afreey sai yaji hanjin cikinsa na kadawa, gaba daya ya rasa yanda zaiyi, dan ma y saida katin dari takwas a wanda ta turomai aka bashi dari bakwau yaci indomi, da yau kam tsoro da yunwa sai sun halakashi.
Ya zaiyi ya sanar da Afreey wannan labarin?
**********
Ayusher🏌🏻♀
**********
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
“The best and most beautiful things in the world cannot be seen or even touched. They must be felt with the heart”
Helen Keller
{56}
Wajen karfe biyu ya bude idanunsa, jin ba karar gen ga kuma haske kwan wuta ta waje yasa yasan nepa ne, kafafunsa ya sauko dasu daga kan kujerar, gaba daya jikinsa ciwo yake yi.
Daki ya nufa a hankli ya bude dakin, tare da dan haska wayarsa, tana kwance tana bacci, murmushi ne na wani yanayi da yake tausayin kanshi da ita ya bayyana a fuskarsa kafin ya nufi cikin dakin, a hankali ya isa kusa da ita, ya zauna a ta gefenta tare da zubawa fuskarta ido, bacci take kadai ko tana mafarki? Murmushi yai tare da cewa mafarki tana aiki? Yanayin fuskarsa ne ya canza yadan sukunyo yana kallanta cikin wani yanayi da shi kadai yasan me zuciyarsa ke ciki, a hankali ya kai bakinsa kan goshinta ya sumbata tare da dan lumshe idanunsa, sannan ya kalleta ya yace “what should i do with you?” Yai maganar cikin wani irin sanyi murya mai kamar ta rad’a mai ratsa zuciya.
Mikewa yai ya gyara mata bargon sannan yai alwala ya kunna heater ya fito daga dakin, nafiloli yai yasa pillow yai bacci a nan kasan.
Yau kam ya d’an makara dan sai biyar da rabi ma ya farka daga bacci, da sauri ya mike ya shiga toilet din dake falo yai wanka sannan ya nufi daki, tana kwance tana bacci har ya sa kaya, d’an motsi tai bai kalleta ba ya cigaba da shiryawarsa, idanunta ta bude ganin hasken fitila.
Yana gaban madubi yana sa turare, wayarta ta jawo ta duba agoggo sannan tace “yauma da wuri zaka fita?”
“Gaisuwar ki kenan?” Yai tambayar tare da kallanta yana sa agoggo, tace “wai wani irin aiki ne tun safe bai karewa? Kuma irin wannan aikin karfin Allah ni nasan ba wani abu ake baku ba.”
Juyawa yai bai tanka mata ba ya sa mabalen rigarsa sannan ya dau wayarsa, kallanta yai yace “ba saikinyi abinci saboda ni ba, kiyi yanda kikeso.”
Ya juya ya fita, shiru tai, a ranta tace “tausayi na yake?”
Ba tare da wani dogon nazari ba tai sallah sannan ta kwanta, dan baccin awa biyu tai sannan ta mike cikin jin dadin bazatai abinci ba ta gyara dakin tai wanka ta had’o tea ta dauko dubulan tana ci tana aikinta, charge na karewa ta kuna gen ta cigaba da hidimarta, yau ta shirya yin website na gidan Tv dinta da logi, shiyasa ta dukufa sosai a falo tana ta hidima, sai karfe hudu taji gen ya mutu, fitowa waje tai tana dubawa, ganin ba mai yasa ta juye ragowar na jarkar wanda bashi da yawa ta kara kunnawa ta koma ciki.
Tana zama harta dau mouse sai taji yunwa ta kamata, ta mike tai kitchen, ganin tuwon jiya yasa tai shiru ita kadai a kitchen tana tuno abubuwan da suka faru a daren jiya, samun kanta tai da rufe fuskarta tana murmushi, dan ta tabbatar kila kunyarta yake shi yasa ya kasa dawowa cin abinci.
Shiru tai kafin tace “to me zaici?” Ginin kitchen ta kalla haka kawai taji zuciyarta duk ba dadi, jitai bata ma jin cin abincin hakan yasa ta fito daga kitchen din, zama tai a falo, duk yanda taso yanzu tai aikin ta kasa, daga ta tuno yana ta gini sai taji ranta ya baci.
Rufewa tai sannan ta kunna tv bayan tai sallah, abinda ta ganine yasata mikewa ta zauna sosai, ganin masu aikin gini tai ana lafta musu kasa suna dauka, wasu na shafa sumunti, wasu na kankare kasa suna ta faman gyara, jitai gaba daya hankalinta ya tashi abinda Khalid yakeyi kenan?
Waya ta dauko da sauri ta dubo sunansa tana neman kiranshi kawai wayar Aunty ta shigo mata, idanu ta rufe sannan ta dauka.
Aunty daga can tace “Zainab sam baki da kirki, wlh badan ke ‘yar yaya bace ko kallan inda kike bazan karayi ba a rayuwata.”
Zainab tace “me kuma nai?”
Tace “ai ko kudin mahaifinki ne ya turo na miki kayan daki da jere da kuma kayan gara a kalla kya kirani kice sunyi kyau ko basuyi kyau ba, in har bazaki kirani akan gajiyarmu ba.”
Shiru tai Aunty tace “shikenan, Allah ya bada zaman lfy.”
“Ba haka bane banyi tunanin kiran bane, amma komai yayi kyau.”
Kai ta daga kawai tace “shikenan sai anjima” kafin Zainab tai wani abu ta kashe wayar, shiru tai, tana mamakin wannan abu kawai dan bata kira ba sai taji haushi?
******
Karfe biyar da rabi ya dawo, dan ya ajiye aikin zaman shagon, yanzu daga gun gini garaje yake wucewa, yayi sa’a dama store ne ba shi kadai bane ke aiki agun.
Tsayawa yai ya siyo kayan miya, bread da kwai sannan ya taho gida.
Tana zaune a falo yunwa ta isheta yasa ta dumama tuwon tana ci, kallanshi tai bayan ta amsa sallama, tace “yau da wuri haka?”
Harzai mata magana kawai ya fasa ya wuce ciki, kitchen yakai kayan ya ajiye sannan ya wuce daki, da kallo ta bishi tana tunanin gajiyar aiki ce hala? Karar rashin mai gen din ya fara, kafin ya mutu, dan ajiyar zuciya tai bayan ta gama cin abincin ta wuce kitchen ta wanke hannu ta ajiye kwanan ta duba abinda ya siyo sannan tai daki ta sanar mai ba mai.
Jin karar ruwa yasa ta fahimci wanka yake, zama tai a bakin gado, fitowarsa ne yasa ta kalleshi, tana ganin sa daure da towel ga gaba daya saman jikinsa a waje, Khalid irin mazan nan ne masu fadi sannan jikinshi a dan murde yake, wankan dayai yasa gashin kirjinsa sun kwanta, da sauri ta mike ta juya bayanta gabanta na faduwa.
Baiko bi ta kanta ba ya goge jikinsa da karamin towel din da ke hannunsa sannan ya sa jallabiya ya sa turare.
Kokarin fita daga dakin yake tace “naga ka dawo da wuri.”
“Eh da wani abin ne?”
Dan takowa inda yake tai tace “zakaci tuwon?”
Kallanta yai yace “A’a indai kinci shikenan.”
Ya fada tare da fitowa daga dakin, wannan wannan ta fada tana nuna kofa kafin ta daure fuska ta fito.
Yana zaune a falo taje gefe ta zauna ganin wayarsa yake dadanawa yasa ta zauna a kasa inda laptop dinta yake, a kan centre table ta fara duba aikinta, ganin shirun yayi yawa yasa tace “ko zaka kaini gidan?”
“Inkin shirya muje na kaiki.” Ya amsa hankalinsa na kan waya, shiru tai tana tunanin me yake a wayar da ko kallanta baiyi ba?
Mikewa tai ta shiga daki, ta gyara fuskarta ta dauko mayafi da key ta fito.
Haushi ne ya kara kamata ganin har ta isa kusa dashi baiko kalleta ba, sai datace “muje?”
Kallanta yai sannan ya mike yai waje.
Da harara ta bishi sannan tabi bayanshi suka isa gaban mota.
Key ta mikamai ya amsa ya shiga itama ta zagaya ta shiga, shiru tai tana kallanshi samun kanta tai da tuno abubuwan da suka faru a baya a cikin motar, wani murmushi ne ya bayyana a fuskarta, ta kalleshi tana tuno sanda zai tambayeta kwatancen gidanta sai wani left da right yake ce mata, ya wani ce mata excuse me? In zai mata magana, Murmushi tai ita kadai, har suka isa gidan bai tanka ba.
Bala na ganin motarta ya bude cikin hanzari, suna shiga ya taho da gudu yana kwasar gaisuwa.
Bayan sun gaisa ne tai hanyar ciki, ganin Khalid tai a ciki mota bashi ko da alamar fitowa, dawowa tai tace “Muje mana.”
“No jeki fito.”
Ido ta kuramai cikin kuluwa yau tunda ya tashi ko maganar arziki bai mata ba, abinda ya faru daren jiya fa? A banza yake? Kenan duk yanda ya nunamin karya ne? Abinda kawai take rayawa a ranta kenan, yawon bakinta ta had’iya tace “abinda zan dauko nada nauyin bazan iya dauka ba.”
Kallanta yai sannan ya mike, suna shiga tai ciki.
Kallan gidan yai jiyai jikinsa duk yai sanyi, ganin tafkeken falo, da gun dinning a gefe, wanda yake hade da kitchen.
Zama yai akan kujera ta wuce daki ta bar kofar dakin a bude, ganin ta kasa jawo akwatin dake saman wardrobe din ne yasa ta tura kujerar jikin madubi ta hau, ganin ta jawo amma ta kasa dagoshi ta sauko dashi yasa ta sauko ta fito falo.
Kallan Khalid tai tace “dan taimakamin.”
Kallanta yai bai amsa ba kuma bashi da alamar mikewa, kallansa tace “magana nake ma.”
Tambaya ma bata iya ba, abinda zuciyarsa ta fadamai kenan yai ajiyar zuciya.
Kallanta ya sake sannan ya kara dauke kai, wani abu ne ya tokare a mokoshinta a kufule ta juya, karfi tasa ta jawo akwatin, da kyar ta shiga kokarin neman saukewa kawai taji an dageshi daga hannunta, kallan juna sukai kafin ya ajiye a kasa, kallansa take har ya ajiye ya dago tace “kasan zaka tayani meye bazaka amsamin ba?”
Bai kula ta ba ya fara neman juyawa, ranta ne ya kara baci tace “Kayi nadamar aure nane?”
Tsayawa yai ya juyo ya kalleta, idanunta ne suka fara cicikowa tace “akan me yau kwata kwata kaki min maganar kirki? Abu na maka? In haka ne ka fad’amin mana, ai kai ba mai ajiye magana a ransa bane.”
Kallanta yai yadan yi wani mosti da bakinsa, wanda baikai murmushi ba yace “me kikeso in ce miki? Bakya ganin na baki dama ki zauna da aikin da kika aura ne?”
Me yasa taji zafin kalamansa? Bayan hakan take so? Tambayar data wa zuciyarta kenan.
Kallanta yai yace “damar ce bakya san na baki?”
Da gaske kake?
Eh, Na dauka abinda kikeso kenan?
Yai tambayar yana kallanta, murmushi tai tace “ban dauka zaka bani dama haka bane shiyasa, nagode sosai.”
Kai ya daga alamar to sannan yace “karki damu” ya juya ya fita.
Shiru tai a gun meyasa bata farin ciki? Bayan abinda takeso kenan?
Fitowa tai ta nufi kitchen, zare cylinder din jiki tai sannan ta shiga fito da abubuwan abinci wanda ke ciki, yana zaune a falo harta gama.
Kallanshi tai tace “dan tayani.”
Baice komai ba ya dau akwatin ya fita dashi, kallan cylinder din yai yace “do you really need that?”
Tace “eh bansan ya akai Aunty bata sa a ciki ba.”
Bai ce komai ba ya dauka, kallan kayan abincin yai yace “wannan fa?”
Kamar tace Mu tafi dasu sai kuma kawai jikin ta ya bata zaiji haushi, tace “tunanin ba Bala nake.”
Murmushi yai ya dauka ya fito, kallan dayar motar da Dady ya sai mata tai ta kalleshi tace “motar can.”
Kallan motar yai sannan ya kalleta, kamar zata sake magana sai tace “bakomai.”
Wucewa yai ya shiga motar, ta sallami Bala sannan suka fito yana ta godiya.
********
Sai da sukai dan tafiya tace “ko zaka kaini Jifatu? Akwai abinda nake san siya.”
Batama san ya ake tambayar abu ba?
Baice komai ba ya wuce da ita, shiga sukai tare ta dauko mai da take shafawa da abin wanka na shower gel, suna zuwa gun biyan kudi aka buga akace 3000, tana kokarin bada katinta Khalid ya mika nashi, nan aka zara wayarsa ce tai kara akan alert da akai, yana dubawa yaga 1000 ne kadai ya rage a ciki, ajiye wayar yai sannan suka fito.
Haka kawai ta ke jin abin banbarakwai, tunda take bata taba siyan abu an biya mata ba, sai dai ta biya duk abinda ta siya ta kuma biya na wanda sukaje tare, ita ko da Dady ba yawo suke tare ba bale har suje siyayya.”
Suna kokarin shiga mota yaji ance “Kwaro?”
Juyowa yai ya kalleta, Zainab wacce taji muryr mace itama ta juya.
Kallan kallo sukai, yanayin fuskar Zainab ne ya canza tana ma budurwar wani irin kallo.
Ta kusa da ita ta wuce taje kusa da Khalid tace “Ashe zan ganeka?”
Khalid ne ya saki murmushi mai sanyi yace “Safeenah? I never expect to see you here.”
Dariya tai cikin jin dadi tai ajiyar zuciya tace “inalilahi shekaru nawa?”
Shima dariya yai yace “tun a skul.”
Tace “wa?” Tai tambayar tana nuna Zainab da kanta.
My wife, ya fada yana murmushi.
Idanunta zaro tace “me?”
Fuska ya hade yace “ban isa yi bane?”
Dariya tasa tace “bawai baka isa bane, Afreey ta sani?”
Fuska ya hade yace “Zaki fara ko?”
Tace “shekaranjiya muka hadu da ita kuma tana ta zancenka kaga ina zan kawo wannan yanayin?”
Zainab dake tsaye ta ciga ta gama batsewa ta bude mota ta shiga ta zauna tana harararsu, ganin Khalid ma dariya yasa ta karajin wani irin mugun bacin rai.
Safeena ce tace “kuma kun dace amma kamar na santa.”
Murmushi yai yace “na san wannan basai kin fada ba.”
“Oh ni Kwaro ban taba tunanin zakaso wata har kai aure ba, na dauka karatu zaka aura.”
Murmushi yai yace “kefa?”
Horn din motar ne yasa ta kasa magana, kallanta yai yace “Madam ta gaji da jira.”
Oh ni, yau Afreey tazo taga abu, wato Madam ta gaji? Oh ni wannan abu sai kara ban mamaki yake, oh ni Kwaro.
Dariya Khalid yai yace “bye.”
Ya karasa tare da shiga motar, Zainab ya kalla wacce ta cika ta batse, ta murtuke fuska tamau.
Yace “mu tafi?”
Wani banzan kallo tamai ta juya kai, shima ya ja suka tafi, tsayawa yai a gun ‘yan cuwa cuwa yaduba wallet dinsa ganin 300 yasa yasai musu mai suka wuce gida.
Suna isa ta fito daga motar rai a bace tai ciki, tsayawa yai ya zuba mai sannan ya wuce ciki, yana jin cikinsa na karar yunwa, sai dai yasa a ransa dole koma menene ya jure.
Kitchen ya wuce ya gutsiri bread din daya siyo ya dau ruwa ya fito falo yaci ya sha ruwa.
*******
Safeena kam suna rabuwa ta shiga kiran kawayensu na skul tana fada musu Khalid yayi aure, kowa Afreey ya shiga hangowa suna tunanin yanda zasu fada mata.
*******
Nusaiba bazaki tashi kici abinci ba? Wai meke damunki ne?
Kallan Basma tai tace “ni wlh Mumy Uncle nakeso”
Basma tace “banace karki kara maganar nan ba? So kike ran Dadynki ya baci?”
Hawayenta ta share tace “to ni Allah bazan iya hakura ba.”
Idanun Basma ne suka ciko, ta tuno abinda tama Mahaifiyar Zainab da ita kanta Zainab daga koyarwa, share kwallarta tai tace “to sai dai kuwa ki mutu wlh na sake jin maganar nan dukan tsiya zan miki a dakin nan.”
Nusaiba ce ta kalleta tace “Dady zan fadawa tun.......”
Marin da Basma ta wanka mata ne yasata yin shiru, in sake jin maganar banzan nan.
Ta juya ta fita, ba shakka alhakin Ummy dashi zan mutu, tunda ban nemi yafiyarta ba, banama jin tasan nice na kwace mata mijin harta rasu.
Hawayenta ta share cikin wani yanayi......
*********
Yau kam tana tashi taga baya gida, samun kanta tai da jin haushi, kwanciya tai ko dakin ta ki fitowa.
Lalai ma Khalid din nan? Ta fada cikin jin haushi.
Bargo taja ta rufe kanta dashi ta dauko wayarta, gun sako ta bude, me zata ce mai?
Haushi ne ya kamata ta ajiye wayar, ta kara jan bargo tare da yin kwafa.
********
Afreey me kike gani? Ai nasan Babanki dan Albarka ne ba shakka zai dubemu.
Kallan Director Kabir tai tace “badai da gaske kake bako?”
“Haba Afreey kema kinsan ba wasa nake ba, in babanki ya taimakemu wannan karan ba abinda bazan miki ba.”
Wata dariya tai tace “na taba neman abu a gunka? Duk duniya ina da komai danake so abu daya ne ya gagaren wanda shima dole ko da menene sai na mallakeshi, banaji ya shafeka bare ka taimaken.
Ran Director Kabir ne ya baci amma ya ya iya? Daurewa yai yace “ki taimaka ko baki to ya sa a taimakemu dan Allah.”
Zan duba, abinda tace kenan ta fito, tare da hararan kofarsa, wayarta ta dako ta kara kiran Adam, amma sai Kamalu ne ya daga yace mata wai bashi da lafiya.
Kwafa tai ta kashe wayar dole ta je inda yake taji uban me yake boye mata.
Nace Um um dai da dai kin hakura🤪
******
Ayusher🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
{57}
Yau kam sam takaici ma ya hanata yin aiki dan in ta tuna wai ya bata dama tai aikinta sai taji ranta ya kara baci, yanzu ma a karo na ba adadi ta mike tsaye a kufule tace "da cewa nai bansan aikina? Kasan haka meyasa ka....." sai kuma ta kasa karasawa ta zauna akan gado cikin takaici, tun dazu take jin yunwa amma bakin ciki ya hanata ma cin abincin sannan dama ita mace ce mai wahalar da cikinta, tana jin yunwa amma in abu na gabanta to ajiyeshi take.
Mikewa tai ganin azahar har tayi tai wanka ta sa turarukanta masu kamshi ta shafa hoda kanta ba dankwali ta nufi kitchen, bread din da aka gutsira ta kalla ta duba taga ba alamar anyi amfani da cup, kenan bread kawai yaci ko me?
Dankali ta fere ta fara soyawa shiru tai tana tunani, are you okay? Abinda kunuwanta suka jiyo mata kenan, tai shiru tana tunani ai Khalid tun kafin ma su fara wata doguwar magana in har tana cikin wani yanayi yake tambayarta hakan, wanda har take mamakin yanda Adam baya gane halin da take ciki amma shi yake ganewa, kenan ya san abin nan da yake mata yana bata mata rai amma ya cigaba? Tana tunani har dankalin ya kone, haushi ne ya kamata kawai ta hada tea tasha a kitchen din, ji tai idanunta sun ciciko, maida kwallarta tai tana tunanin tunda ta taba auran Adam ta taba zama tunani da har xataji tana shirin kuka?
Fitowa tai daga kitchen din kawai ta dau wayarta ta kira Nabila, waya suka shiga yi Nabila na tsokanarta ina Yaya Ango.
Zainab cikin kuluwa tace "ina na sanmasa."
Nabila tai dariya tace "Wai yaushe a gari Aunty ake bari a gida ba ita take bari ba."
Fuska ta daure tace "karki batan rai, dan na gaji da zaman nan wlh, ga rashin wuta, ga mutum sai zafin rai."
Wata irin dariya Nabila tasa wanda tasa Zainab jin haushi tace "dariya kike?"
Nabila ta tsagaita tace "Aunty mamaki nake ban taba ji kina complain akan wani ba shiyasa"
Zainab tai tsaki tace "wannan in na fara zubo miki complain a kansa ai yasin sai muyi awa biyu a waya."
Nabila ta sake dariya tace "da alama Aunty na san Ya Khalid sosai."
Fuska Zainab ta daure tamau kamar tana ganinta tace "abinda yafi so, ce miki akai banda aikinyi?"
"Kinada aikin yi kike samun dama da lokaci na jin haushinsa?"
Zainab tace "ke kika san wannan, Nusaiba fa?"
"Hmm ni ina na san mata, sai wani hade min rai take kamar ni na kar zomon."
Shiru Zainab tai kafin tace "ke kuma uwar rashin hakuri, kiyi hakuri ki dan lalabata harta saki ranta."
Ajiyar zuciya tai kafin tace "zan gwada amma Allah ta kawon wargi zanyi gaba kin sani."
Na sani kiyi hakuri dai, haka suka danyi hira kafin ta kashe, shiru tai tana tunanin abinyi ganin tanata tunani kawai ta mike ta dauko laptop dinta ta fara aiki, sai la'asar tai sallah sannan ta dafa indomie ta zauna tana ci.
Tana gamawa ko kwanan bata dauke ba ta cigaba da abinda take, sallamar Khalid ce yasa ta dago ta kalleshi tare da amsawa.
Ido ta zubamai ji take kamar ta dade bata ganshi ba, shima kallanta yake yanda tabar kanta a bude da yanda tai zaman nata har jikinsa yaji abin, murmushi tamai shima samun kansa yai da mata sannan ya shiga ciki, daki ya wuce ta bishi da kallo yau ma bashi da niyyar kulatan?
Daki ya wuce ya watsa ruwa saboda gajiyar dayai sannan ya dan zauna akan gadan yana shafa aboniki a bayansa, dan sosai bayansa ke mai zafi, ganin bai fito ba ga charge dinta ya kare yasa ta mike tai dakin.
Ganin sa sanye da wando da farar vest wanda ya daga ta sama yasa ta jawo kofar, shiru tai tana tunani kamar abu taga yanayi, me yake? A hankali tadan tura kofar tadan sa idanta.
Jitai yace "leken me kike?"
Bude kofar tai tace "a ina nai leken?"
Kallanta yai ya rufe man, jin kanshin man zafi yasa tace "me kake?"
Bakomai.
Yai maganar yana maidashi kan madubi.
Haushi ne ya kara kamata dataga yana neman barin dakin, haka ya wuce ta gabanta ranta a matukar baci ta bishi da harara.
Yana kokarin fita daga kofar ta rike rigar sa tace "nice bakasan zama guri daya dani?"
Juyowa yai ya kalleta, tace "ka bar falo ka dawo daki yanzu na shigo dakin ka fita, me kake nufi?"
Kallanta yai ya kalli hannunta data rikeshi, yace "haka kike gani?"
Tace "ba hakan bane?"
Abinda zuciyarki ta raya miki shine daidai a gareki?
Fad'amin ba hakan bane?
"Ba haka bane."
Yai maganar yana kallanta, to menene? Dama ka bani nai aiki?
Hmmm bakyaso?
Ba wai banaso ba amma at least ka dawo yanda na sanka, wannan halin daka faramin yasa ina tunanin abubuwa dayawa.
Zaiyi magana yaji ana buga kofa, kallanta yai yace "bari na duba."
Sakeshi tai zuciyarta na kara hasala, harta juya taji karar text a wayarsa, dauka tai da niyar fitomai da ita, abinda ta gani akan screen din wayar ne yasa yanayinta canzawa.
Idanunta ne suka ciciko, hankali a tashe ta bude wayr ta duba sakon dakyau, bata taba tunanin daukar wayar wani ba bare tunanin bude ta, alert ne na katin dari da aka saka suka turo balance na 900, sam ta kasa dauke idanunta daga kan screen din wayar, jikinta ne ya shiga rawa, tana maimaita 900 a ranta, idanunta ne suka ciciko hawaye suka zubo daga cikinsu ba tare da ta sani ba, jin motsinsa yasa ta ajiye wayar hankalinta a matukar tashe.
Shigowa yai yace "makocinmu ne, bamu kyauta bamu shiga ba yazo mun gaisa yace matarshi za........"
Ganin yanayinta yasa yace "menene?"
Kallansa tai, matsowa kusa da ita yai ya dago fuskarta yace "menene?"
Kwacewa tai da sauri ta shiga cikin toilet, tana shiga ta rufe, shiru yai yana kallan kofar, yana san suyi magana dan kalamanta sun sa jikinsa yin sanyi, da alama abinda yake mata ya mata tsauri ganin lokaci daya komai ya canza mata, samun kansa yai da jin haushin kansa, sai dai baisan meyasa yake hakan ba.
Ganin taki fitowa yasa ya fito falo, Zainab kam tana shiga ta tsaya a jikin kofar ta jingina bayanta gaba daya ta kasa tabbatar da abinda idanunta suka gani, tabbas zero biyu ta gani, kanta ta shiga bugawa a jikin kofar.
Har yai alwala a falo yana jiran ta fito suyi sallah baiga ta fito ba, massalaci ya fita har ya dawo bata fito ba dakin ya shiga sannan ya mike ya kalli toilet din ba alamar fitila ga duhu, buga kofar yai yace “Zainab?”
Jin shiru ya sake cewa “Zainab?”
Nan ma yaji shiru hannu yasa yana kokarin budewa jinshi a kulle ta ciki yasa ya shiga murdawa yana cewa “Zainab! Zainab?”
Bude kofar tai da sauri ya kalleta yace “lafiya?”
Yai tambayar yana duba jikinta, hannunsa tadan ture ta wuce ciki, hijab ta dauka, ta tada sallah ba tare da tace komai ba, shiru yai yana kallanta kafin ya juya ya fita, waje yaje ya kuna gen ya zauna a falo, sai dai gaba daya hankalinsa baya falan yana dakin balle dayaga har a lokacin bata kunna wutar dakin ba.
Ganin ya kasa daurewa ya mike ya nufi cikin daki, kallanta yai wanda hasken waje ya dan haska dakin, tana zaune a inda tai sallah ta sa kanta cikin kafafunta, hawaye kawai ke zubo mata ta rasa dalilinsu, gaba daya haushin kanta takeji ta ko wani bangare.
A hankali ya taka zuwa inda take ya zauna tare da sa hannu ya dago kanta, kallansa tai idanunsa na kanta yace “bakida lafiya ne?” Yai maganar cikin sanyin murya.
Ummy me nakeyi? Ummy na, Ummy! Abinda zuciyarta ke fada kenan, Kuka kawai ta fashe dashi hankalin Khalid ne ya tashi, kallanta yai yace “menene?”
Baki da lafiya ne? Yai maganar cikin tsananin damuwa.
Kuka kawai take tana tuno a yanzu haka tana da kudi saman da miliyan biyu a account dinta wanda Dady ke sa mata, ga dubu dari tana da shi a cikin dakin nan na kudin gaisuwa daya kawo, tana da gida babba, tana da motoci, tana da fili me take a rayuwarta da har.........
Dagatan da yai ne yasa ta kalleshi, zaunar da ita yai a kan gado, hannayensa yasa akan fuskarta yace “ menene?”
A hankali ta girgiza kanta alamar ba komai
ni ne?
Kallansa tai jikinsa ne yai sanyi yace “ am sorry, am really sorry”
Kai ta shiga girgizawa tana hawaye, goshinsu ya hada hannayensa na kan fuskarta a hankali yace “na sani laifi nane”
tace “laifinka name?” Tai maganar hawaye na zubo mata.
“Na komai”
Tunowa tai da abinda tai jiya gen yini yai a kunne, taje jifatu ta kashe mai 3000, ya siyo abubuwan gida na bukata, hawaye ne ya sake zubo mata.
Hannu yasa ya share mata sannan ya jawota jikinsa ya rungume, yace “ya isa haka nan, yaushe kika zama mai raki?”
Dagowa tai ta kalleshu tace “ban sani ba, bansan ya akai na zama mai raki ba.”
Murmushi ya mata mai sanyi a dan jawota cikin sanyi yace “kin zama mai raki but i like it.”
Kallansa tai tace “shiyasa kake shareni?”
Haka kika gani?
Ba hakan bane?
Dam........
Hannu tasa ta rufe bakinsa tace “ya isheni ba sai ka tisa min ba.”
Murmushi yai, itama tai murmushin karfin hali, cikinshi ne yai kara, kallansa tai tace “bakaci abinci ba?”
In ba’a ban a gidana ba a ina za’a bani?
Shiru tai tana maimaita kalaman a ranta, indomie naci in dafa ma? Karkace nama tuwo plz.
Kin manta nace kiyi duk abinda kikaga shine daidai.
Mikewa tai ta fito dan so take ta kadaice, tana shiga kitchen tai shiru, hawayen da ta rasa dalilin zubarsu ne suke gangaro mata.
Idanunta ta rufe haka ta dafa indomie din, ta fitomai dashi falo, kallansa tai tace “kai na ke ciwo zanyi sallah na kwanta.”
Kallan mamaki ya mata, gani yai kafin yai magana harta wuce ciki.
Laptop da takardunta ya kalla, meke damunta??
Tana sallah ta kwanta, shima harya kwanta a falo ya samu kanshi da mikewa yai ciki, haryai bacci idanta biyu, tayi shiru tana tunanin rayuwa, sai wajen asuba ta samu bacci ya dauketa.
*********
Suna zaune a cikin office din taro, shugaban gidan tv din ne ya kallesu ranshi a matukar bace yace “kuna san cemin haka zan cigaba da sa kudina yanzu ba riba?”
Kabir yace “Ranka ya dade kadan kara ha......”
Desk din daya daka ne ya sashi yin shiru, kallanshi yai yace “kana tunani kai ba dan kanina bane zan barka ka cigaba da aiki anan? Wlh kaji na fadama bazan dauki wannan asarar ba, da ka san bazaka iya ba uban waye yace ka kori Zainab?”
Fuska ya hade baice komai ba, to Allah kaji na fadama ficikata bazan sa ba, ace gidan tv yanzu banda asara ba abinda nake samu? Kudin biyan ma’aikata ma neman gagarata yake, duk wadanda suka dau nauyin talluka sun ajiye, ka je ka saka mutanen dakaga dama suna shiri yanzu sam ba wanda ma yake kallan tashar to Allah bazan dauka ba kaji na fada ma, inhar naga bazan iya ba saida gidan tv din zan, yana kaiwa nan ya mike yai waje.
Da kallo suka bishi sannan suka kalli Kabir wanda ya cika fam
*******
Adam ne ya kira Goggo, tana zaune tasa dumamen tuwo a gaba ta kasa ci saboda bakin ciki wulakancin da aka mata kafin a bata dan Hanne sai data kare mata cin mutunci.
Ganin kiran Adam yasa ta dauka da sauri tace “Adam ya ya? An dace?”
Yace “ina fa aka dace Goggo bayan muna cikin tashin hankali, Khalid da takeso yai aure.”
Goggo hankali a tashe tace “uban wa yace yai aure? Wannan d’a anyi an banza, garin ya ya ka bari yai aure?”
Ni kya tambayen garin ya ya? Nine babansa? Ni wlh yanzu bansan me zan ce mata bane.
Ka nuna mata baka sani ba, kai maza kasa ta nemarma aiki kafin ta sani.
Cikin jin dadi yace “haka ne Goggona, nagode”
Nan ta kashe wayar tana fatan dacewa.
******
Wajen karfe 10 ta farka, mamaki ne ya kamata dataga tayi bacci dayawa haka, wayarta ta ajiye tana kokarin saukowa taji tayi ringing, d’auka tai da sauri tace “Umma”
Bayan sun gaisa cikin farin ciki Umma tace “na kira Khalid bai dauka ba dama cewa zanyi gobe zamuzo da Asiya.”
Cikin tsananin murna Zainab tace “Allah ya kaimu Umma, karki manta da...”
Umma ce ta katseta tana dariya tace “ina zan manta da wainar geron ki? Kina san wani abin bayan shi?”
A’a Umma.
Umma tace “sai munzo goben.”
Cikin jin dadi sukai sallama.
Murmushi tai na dadi.
*******
Khalid kam a rana yana duba wayarsa yafi sau ashirin yana fatan ganin sako daga Zenith bank, duk da yasan abin na jan dan lokaci amma zuciyarshi ta kasa hakura
Haka ya hau mota ya taho gida.
********
Ayusher🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
{58}
Wayarsa ya dauko a cikin mota, yasa hannu zai danna kira akan sunanta kawai yaga kiranta ya shigo, shiru yai yana kallan number murmushi bayyane akan fuskarsa, dagawa yai.
Daga can tace “Umma ta sameka?”
Kai ya girgiza tare da cewa “sallamu Alaikum.”
Kunyar kanta taji dan zumudi yasa ta manta, a hankali ta amsa, yace “yanzu zan kirata.”
Tace “okay dama cema zatai gobe zasuzo.”
Shiyasa zumudi ya sa kika kira?
Har ka gano?
Murmusbi yai yace “akwai abinda kikeso?”
Shiru tai tana tuno kudin da ke account dinsa, yanayinta ne ya canza cikin sanyi tace “a’a”
Ba abinda kike so?
Hmmm ta fada tare da daga kai kamar yana ganinta.
Shikenan sai na dawo.
To tace ta kashe wayar, shiru tai tana tunanin kenan in nashi da kudi ta ina zai ci abinci? Mikewa tai ta wuce kitchen, ganin ba nama yasa tai shiru, sai dai bata zafafa tunani ba ta hau yin jellof din macaroni, dan in ta tuna 00 biyu kacal sai taji idanunta na neman kawo ruwa.
Tana kitchen tana kwashe talliyar, sam bataji alamun shigowarsa ba, shikuma ganin bata falan yasa ya taho kitchen da ajiye nama da kayan miyan daya karo dan yasan dole zata bukata saboda zuwan su Umma.
Ganinta a kitchen tana kwashe abinci yasa shi yin murmushi, ajiye wa yan a hankali sannan ya karasa inda take, hannunsa yasa a ta ratsin cikinta, a tsorace ta juyo dan sam bataji motsi ba, gabanta yayi wani irin faduwa.
Tana juyowa kansu na gwaruwa da juna, wata yar kara ta saki, ya saketa kawai baisan sanda yasa dariya ba.
Zubamai ido tai yana dariya yauce rana ta farko data taba gani yana dariya haka a kusa da ita, fuska ya canza ganin yanda take kallansa.
Yace “menene?”
Harararsa tai tace “bansan ka iya dariya haka bane.”
Murmushi yai sannan ya matso ya kara kai hannunsa matsen cikinta ya zagayo dasu, wani irin yanayi ne ya ratsata, kansa ya sako ta kan kafadarta yace “me kike?”
Dan juyowa tai tana san bashi amsa sai dai ganinshi daf da ita yasa ta kasa, sumbatar bakinta yai yace “kin gama aikinki ne?”
Juyawa tai ta karasa tana neman daidaita numfashinta sannan tace “ina zanyi raina yana bace?”
Yar ajiyar zuciya yai yace “fadamin nikam menene baya bata miki rai?”
Kallansa tai kadan tace “ni zan fadi hakan.”
Murmushi yai yasa hannu ya juyo da ita sannan ya kara matsewa yace “haka nake?”
Sai na fada?
Ta tambaya tana kallansa, saketa yai sannan yace “bari na watsa ruwa.”
Juyawa yai da sauri tace “inka fito kazo ka ci abinci.”
Da sauri ya juyo ya kalleta, yace “ni kikawa?”
“Wa ya fadama? Abinci ne nima ban ci ba.”
Duk da haka samun kansa yai da kallanta sannan ya juya ya fita.
Yana fita tai ajiyar zuciya ta hau fifita da hannunta, sannan ta dan yi murmushin da bata san dalilinsa ba.
******
Wanka yai ya zauna a kan gado yana dan mike bayansa tare da daukan maganin zafi.
Zainab kam ganin baifito ba yasa ta leka daki, ganinshi yauma kamar jiya yasa ta juya, jitai yace “bakya gajiya da leke?”
Kofar ta bude ta shiga tana dan kallan dakin tace “wai ni nacema leke nake?”
Kanki fa? Ya daina ciwon?
Kallansa tai sannan ta daga kai, kallanta yai shima ya mika mata man zafin dake hannunsa yace “can you help?”
Me kake?
Ta fada tana takowa inda yake, mika mata yai yace “shafan a tsakiyar nan.”
Kallan jikinsa tai da sauri tace “hannunka fa?”
Baya kaiwa.
Hannu yasa ya jawota ta zauna a kusa dashi, juyawa yai ya kwanta akan gadan yana nuna mata.
Kallan bayansa tai sannan ta lakuto a hankali ta fara shafamai, yanda yake dan motsa bayan inta taba gun ne yasa ta fahimci zafi gun yake mai, idanunta ne suka canza, tsananin tausayinsa ne ya shiga ratsa sassan jikinta, cikin yanayi na tsananin tausayi tace “ciwo yake ma?”
Dan juyowa yai yana daga kwance yace “kadan.”
Shiru tai ta kasa ci gaba da shafawa sai idanunta data rufe, hangoshi take yana aiki tukuro a idanunta, jin bata shafawa yasa ya kara dan jiyo da kansa.
Ganin idanunta lumshe tana tunani yasa ya mike zaune, kusa da kunnenta ya matso yace “Do you need me that much?”
Ido ta bude ta ganshi daf da ita, hannu tasa ta hankadashi kan gado tace “wannan fassarar fa?”
Yace “kin tabbatar?”
Da sauri ta mike tace “in ka so ka fito.”
Ta juya falo da sauri, shiru yai sannan ya kalli laptop dinta wanda da alama tadan tabata amma ba sosai ba, charge ne ya kare? Ba mai ne?
Kitchen ta shiga ta bude ledar da ya siyo nama da kayan miya, shiru tai a ranta tana tambayar wannan nawa suke? Kenan 900 din ta ragu kenan? Hankalinta ne ya kara tashi, haka ta kawo abincinsa falo ta koma kitchen dauko nata.
Kaya yasa sannan ya fito, ta ajiye mai abincin a falo, yana kokarin zama ya ga tana neman wucewa da plate dinta wanda ta zuba abinci itama.
Ina zaki?
Ya tambaya yana kallanta, kallansa tai ta kalli abincin, matsowa tai ta dau serving spoon tana neman zubamai, hannunta ya rike, kallansa tai abincinta ya ajiye a kusa dashi sannan yace “zauna.”
Ba musu ta zauna tana kallanshi, yace “me ya sameki jiya?”
Kallansa tai tace “namanta?”
Kin manta?
Hmmm ta fada tare da kallan gefe.
Fork dinta ya sa a plate din sannan ya kalleta.
Kallansa tai tace “badai baka kake san kace nai ba ko?”
In na fadi haka laifi ne?”
Murshi tai zatai magana taga yasa fork dinsa a ciki bai ce mata komai ba.
Kallansa tai yana ci bai ce mata komai ba.
Tsayawa tai kawai tana kallanshi, ganin taki ci yasa ya kalleta yace “sun kawo wuta?”
A’a
“Me kikai yau to?”
“Ka damu ka sani ne?”
“Banaji”
Haushi ya kamata ta harareshi sannan ta janye plate dinta tace “ai wannan abinci nane, kaci naka.”
Kallanta yai kawai baice komai ba, harta mike kuma ta koma ta zauna tace “ai ma ka cinyen nawa sai kaban naka.”
Murmushi yai yace “nawa da naki ba daya bane?”
Kallansa tai cikin wani yanayi, sai kuma tai shiru, mikewa tai ta shiga daki, kudin nan ta dauko dubu 100 ta zuba musu ido tana kallo, mikewa tai ta fito falo.
Ya gama cin nata yana shan ruwa yaga ta dawo, kallanta yai har ta zauna kusa dashi kadan.
Ajiye kudin tai a kusa dashi.
Kallan bakar ledar yai sannan ya kalleta, tace “kudin ka ne daka kawo.”
Kudina?
Ya fada yana kallanta, tace “hmm nina ce muyi aure dan haka bai kamata na amshi kudinka ba.”
Yanayin fuskarsa ne ya canza, bacin rai ne karara ya bayyana a fuskarsa, Zainab tace “ka amsa nagode da ka kawomin a kalla nasan........”
Yanda taga idanunsa sunyi jaaa sosai ne yasa ta kasa cigaba da maganar, mikewa yai kawai taga ya fita waje, shiru tai tasan bazai amsa haka kawai ba amma itakam zuciyarta bazata iya nustuwa ba in ta tuno kudin nan.
Khalid kam ransa yakai kololuwa gun baci, shikadai yasa yanda zuciyarsa ke tafasa, wayarsa dake kara ya daga.
Salmanu
Bayan sun gaisa yace “dan Allah ka dan kaima Umma dubu daya da dari biyar, zan bata gobe in tazo ta baka, nasan kudin hannunta dasu zatai mota.
To shikenan.
Salmanu zai sake magana Khalid ya kashe dan baisan yai magana mai tsayi kar a gane bacin ransa.
Jin ana kiran sallah yasa ya duba gen din ganin akwai dan mai kadan yasa ya tada.
Shigowa yai tana zaune tana cin abincinta gefe kuma ga kudin nan, baiko ce komai ba ya wuce yai alwala.
Fitowa yai ya kalleta yace “in kin gama kiyi alwala muyi sallah.”
Kallansa tai fuskarsa a daure, ruwa tasha ta dauke kwanukan sannan tai alwala, sallah sukai, bayan sunyi addu’oi tace “Kh......”
Kallan daya mata ne yasata yin shiru, mikewa yai ya shiga daki, ya zauna akan gado tare da daga kansa yana neman kwantar da ransa.
Zainab kam tasan bazai amsa da wuri ba amma dalilin fishin ne bata sani ba, har sukai bacci ba wanda ya sake maganac daga zata mai intaga yanayinsa sai tai shiru, haka tai aikinta sunyi sa’a 8 aka kawo wuta, nan ta cigaba , shikam 9 ya kwanta.
Yauma a daki ya kwanta dan kukan datai jiya ya tabashi.
Karfe 4 ya farka, kallanta yai ta matso kusa dashi tana ta baccinta, bargo ya gyara mata sannan ya mike yai wanka yai alwala yasa kaya.
Zama yai kusa da ita, ya sa hannu yadan tabata kadan.
“Tashi kiyi sallah zan wuce.”
Idanunta ta bude, ta kalleshi.
Haryanzu ranka a bace yake?
Kallansa tai tace “okay”
Yai dan shiru kafin yace “ki gyara gidan kafin suzo, sannan ki yi musu abinci.”
Bata amsa ba sai dai ta kalleshi, yace “wajen azahar zan dawo nima”
Kai ta daga kawai batace komai ba.
Kallanta ya sakeyi yace “insunzo ki tabbatar kin musu sannu da zuwa kin kuma gaisheta kafin ku fara magana.”
Idanunta ne kawai a kanshi, yace “sannan kisa mayafi.”
Ajiyar zuciya tai tace “duk ni kadai?”
Hmm sirikarki ce.
Kai ta daga sannan tace “to.”
Mikewa zaiyi ta riko rigarshj, kallanta yai tace “bazaka.......”
Katseta yai yace “na wuce.”
Shiru tai tana kallansa har ya fita.
*******
Haka ta mike tai gyaran gida, dan tunda tazo yaune ta gyara ko ina ta share, bayanta ne taji ya amsa, tab yaushe raban datai shara? Dan dama ita ba gwanar aiki bace.
Haka ta shiga kitchen tasa shinkafa da miya.
Kallan kudin tai a falo, ajiyar zuciya tai sannan ta dauke ta maidashi kan madubi a daki.
Wajen karfe sha biyu da rabi ta gama abinci tai wanka tana shafa mai taji buga kofa.
Da sauri tasa kaya ta dan shafa hoda tasa turare ta fito, hartazo kofa ta koma da gudu ta yafa mayafi.
Sannan ta fito.
Umma ce ta kalli Asiya tace “nan ne kin tabbatar?”
Asiya tai dariya tace “nan ne wlh Umma zuwana biyu fa da Yaya.”
Umma tai murmushi zatai magana sukaji an bude.
Zainab cikin tsananin jin dadi ta tarbi su Umma.
Haka suka shiga ciki tana mata sannu da zuwa.
Umma kam baki yaki rufuwa, sai jin dadi take.
Ciki suka shiga ta tuna kalaman Khalid hakan yasa ta tsuguna ta gaisheta, Umma ta kalleta cikin jin dadi tace “Zainab”
Zainab cikin jin dadi itama tace “Umma sannunku da hanya.”
Hira ce ta barke Umma nata tambayarta zaman kadaici da sauransu, sunyi sallah Asiya ta taimaka mata suka kawo abinci.
Umma ta kalli Zainab tace “kin fadamai munzo?”
Yace “wajen azahar zai taho.”
Umma tai murmushi tace “sai ki kirashi kiji ko ya taho.”
Cikin kunya ta dau waya tadan matsa.
Khalid na ta gyaran wata mota wacce yake sauri ya gama ya taho yaji kiranta ya daga.
Tace “Su Umma sun iso.”
“Okay ganinan zuwa.”
Nan suka kashe wayar, hankalin Umma nakanta, Zainab ta dawo ta zauna tace “Ya jikin Abba?”
Umma tace “da sauki.”
Suna dan hira wanda duk kalamanta Umma na kula dasu, tundaga yanda take kawo abinci, mantawa datai da spoons sai da Asiya ta dauko, ta kawo ruwa ta manta da cup da sauransu.
Khalid sai biyu da kwata ya samu ya iso, Umma tana kallan ba sannu da zuwa ba komai, har ya gaida Umma basu yi magana ba, Umma ta kalleta tace “Ki kawo wa mijinki nashi abincin.”
Kallan Umma tai dan gaba daya ta juye, tace “ai duka na juye Asiya dan dauko plate ya diba.”
Khalid ne yai saurin cewa “ni nace ta hada gaba daya naga haka muka saba a gida.”
Umma ta fahimci kareta yai sai dai batace komai ba, Zainab ya kalla yace “bani plate.”
Mikewa tai ta daukomai, ta ajiye tana neman tashi ya dan maida ita a wayance, baisan Umma duk ta gani ba.
Kodaga yanayin yanda suke magana Umma tasan da matsala, kallan Asiya tai tace “Asiya kwashe kwanukan ki wanke.”
Asiya ta mike ta kwashe tai kitchen dasu.
Umma ta kalli Zainab sannan ta kalli Khalid ta gyara zamanta, harxatai magana tace “Khalid bamu guri.”
Yace “Umma.....”
Sai kuma ya mike yana kallan Zainab yana fatan kar tai baran barama a gaban Umma, dan duk yanda Umma ke santa in taji yanda ta dauki aure da d’anta lalai da matsala.
Jiki a sanyaye yai hanyr daki Umma tace “ka jira zanyi magana dakai, dan dama babbar maganar a kanka ne.”
Baice komaj ba yai ciki.
Kallanta Umma tai tace “ba auren soyayya kukai ba?”
Kallan Umma tai sai dai batace komai ba, Umma tai jinjina kai tace “Koma auren me kukai bashida tasori a wannan lokacin tunda an riga anyi, ke matarsa ce shi kuma mijinki ne, sai dai wani irin zama ne haka Zainab? Ba girmama juna? Ba ganin mutuncin miji? Sannan da alama ma fada kukai daga aure.”
Kallanta Zainab tai idanunta suka dan ciko tace “Umma!”
Umma tace “na sani nasan duk laifin na Khalid ne sai dai a matsayinki na mace ya kamata ki ja mijinki, Khalid dama tun kafin yai aure ni nasan matarsa sai tayi hakuri da halayensa, sam namiji ne mai wani irin ra’ayi da akida da kuma zafin rai.
Sai dai mu da muke iyayensa mu munsan dalilinsa na yin hakan, duk da hali ne nashi amma ya fara wannan halin ne daga sanda ya shiga jami’a.
Khalid ganin yanda mahaifinsa ke fita tun asuba aikin tuki baya dawowa sai can dare wani sa’in ma baya dawowa sai bayan kwana biyu yasa ya slakanta wahalar mahaifinsa da shi, gani yake mahaifinsa na wannan wahalar ne saboda yai karatu hankali a kwance, wanda kuma a zahiri hakan ne, mun daura burin mu akan Khalid.
Tun daga nan baisan komai ba sai karatu gani yake karatu kawai zaiyiya faranta mana, karatu kawai ya sani, baya ko shiga cikin gida gun mu a lokacin ko a makaranta bai taba cemana gashi da wani abokinsa suna hira ko sunje yawo ba, hankalinmu ya fara tashi ganin dan mu na neman tattare duk rayuwarsa akan karatu, lokacin ne muka sa dokar cin abinci tare, sannan dole in yana gida ya fito a yi hira dashi.
Alhamdulila wannan doka da muka sa itace ta maido da zumunci da kaunar junanmu.
Hatsatin mahaifinsa ya sa daga karatu ya koma aiki, dan a lokacin da abin ya faru ya gama karatu, sai kuma gaba daya rayuwarsa ta koma aiki, bashi can bashi can yana ta faman had’a mana kudin da zamuyi rayuwa, komai na rayuwarmu na kansa, shine cinmu shine suturarmu, shine maganin mahaifinsa, karatun kannensa da sauransu.
Umma ta kalli Zainab wacce tai shiru sai kwalla dake zubo mata.....
***
Ayusher🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
{59}
Zainab ta kalla ta kamo hannunta wanda hakan yasa ta dago ta kalleta.
Kinsan meyasa nake fada miki hakan?
Shiru Zainab tai sai maida kai kasa datai.
“Ke da shi kun taso rayuwa daban daban, akwai abubuwa dayawa da zakiga basu miki ba a zaman takewarku dashi, Khalid ko bashida lafiya baya taba fadamana, duk kuwa yanda yake jin wahalar ciwo baya taba fadamana, saboda bayasan mu damu, in dai har zai zauna da mutum to baya san ya zama ila ko takura ga wanda yake tare dashi.”
Dan dakatawa tai saboda idanunta dasuka dan ciko, tace “ shi da kanshi bazai taba iya fada ba, wanda hakan zaisa a koda yaushe cikin ko wani hali yake zai cigaba da boyewa.”
Murmushi tai tace “Zainab kuyi hakuri da junanku, shi aure tunda ibada ne dole sai an jure, akwai lokacin sabawa akwai lokacin shiryawa, sai dai kada ya zama in ya hade rai kema zaki hade, ko in yana fishi kema zaki dau fishi, Khalid d’ana ne, sai dai bazan fifita shi saboda ke ba tawa bace, ina fatan zaku kula da junanku ku dau junanku a matsayin abu guda d’aya.”
Kai Zainab ta daga cikin wani yanayin, Umma ta kalleta ta kalli agoggo tace “yima Khalid magana yazo zamu wuce, nabar Abbansu a gida ba babba.”
Zainab na mikewa tace “Asiya.”
Asiya dake tsaye a hanyar kitchen tana jira su gama ne ta shigo.
Umma ta kalleta tace “kingama?”
Eh Umma.
Zainab ce ta tura kofar, yana zaune akan gado hankalinsa na waje, haka kawai hankalinsa yaki kwanciya, mikewa yai ya zo bakin kofa ya tsaya yana tunani.
Tana bude kofa ya sa hannu ya jawota ya maida kofar ya rufe, kallansa tai fuskarta dauke da mamaki.
Shima kallanta yai, hannunta da ya rike da karfi ta kalla sannan tadan murza hannun alamar zafi.
Sassauta rikon yai yace “oh sry, me Umma tace miki?”
Idanunsa ta kalla tace “me kake sanji?”
“Ke nake tsoro kar ki fadi ba daidai ba.”
Harararsa tai tace “Umma na jiranka.”
kai ya dan kauda yace “badai kiyi baran barama ba ko?”
Tace “Umma tace ka fito zasu wuce.”
Kallanta yai sannan ya saketa ya juya zai fita, da sauri tace “ka kaisu a mota.”
Juyowa yai ya kalleta a hankali tace “please.”
Kallanta yai fuskarsa a sake jiyai tace “Kaji?”
Murmushi yai sannan ya kalleta yace “muje tare?”
Kai ta girgiza alamar a’a tace “kaje ka dawo”
Okay yace sannam ya dau key yasa a aljihunsa ya fito.
Da kallo ta bishi wani irin tausayinsa ne ke ratsata gaba daya jikinta, daurewa tai ta fito hannunta dauke da leda data sa ma Asiya atamfa a kayan data dauko a gidanta, da dubu biyu a ciki.
Haka sukai sallama harta cema Umma dan Allah wani hutun Asiya tazo.
Umma tace “shikenan, tunda naga akwai wani dakin ta zo insha Allah.”
Har jikin mota ta rakasu, ta ba Asiya ledar da wayau ta juya bayan taga fitarsu.
Suna fita Umma ta kalli Khalid tace “Khalid!”
Yace “Naam Umma.”
Kallansa tai tace “yaushe mahaifiyarta ta rasu?”
Shiru yai Umma tace “da alama ta dade ba tare da ita ba, dan Allah ka kula da ita, ina tausayinta, duk inda kaga aure yayi kargo to lalai miji ne, in har kaga aure ya tabarbare to miji ne, na san halinka sarai sai dainina fatan zaka canza saboda ita, ka ba rayuwarta mahimmanci, ka bata kulawa wanda ta dace dashi, na tabbatar kana santa, to ka jata a jiki ka fahimtar da ita hakan.”
To Umma abinda yace kenan yana tuno kukan datai ranan.
Umma ta kalleshi tace “ko abinda mijinta ya mata ya isa ta samu farinciki, ina tausayin ta matuka, ina fatan ku ba juna kulawar da kuke bukata, tana bukatar lokacinka, ko yaya ne ka kokarta ka bata.”
Shiru yai haka Umma tai ta dan sanar dashi lamura da hakuri har ya kaisu tasha, dan yaso kaisu ma ta hanashi dubu biyu ya ciro a wallet dinsa ya mika mata yace “kiba Salmanu 1500 daya baki jiya, ya sa hannu a aljuhu, dari biyar ya ciro yace ki kara wannan dubu daya kenan sai kudan lalaba kafin karshen satin nan zan turo kudi.”
Murmushin karfin hali tai tace “Allah ya kawo sanda zaka huta Khalid”
Tai maganar tare da share kwallarta. Murmushi yai yace “bakomai Umma muyi fatan Allah ya sa musu albarka dai.”
Umma tai murmushi tace “haka ne Allah ya musu albarka.”
Kallan Asiya yai yace “yar Umma ba’a baki na yin iloka ba.”
Kallansa tai ta dago leda tace “Aunty!” Tai maganar cikin kama kai na mai laifi.
Umma ta kalleta sannan ta kalleshi.
Asiya tai tsuru tana jiran fada sai jitai yace “kinyi godiya?”
Da sauri ta kalleshi tace “bansan ta ajiye ba sai da ka tada mota.
Inkinje gida ki kira a wayar Umma kiyi godiya.
“Nadauka zaka min fada”
“Auntynki ce yanzu da barece zan miki.”
Murmushi sukai dukansu, nan suka sauka yana ce mata zaizo dan zuwa asibiti karshen wata saboda lokacin Abba ne da zai ga likita.
Nan suka tafi ya juyo, har ya isa gida zuciyarshi sam ba dadi, inya tuna ko sanda mahaifiyarta ta rasu bai sani ba wani haushin kansa ne yake damunsa.
Yana shiga duhun magrib na kawo kai, hannu yasa a aljihu ya tuna ashe bashi da kudi, ga mai jiya ya kare, shiru yai a waje idanunsa sunyi jaa yana tausayin ta, inya tuno gidan mahaifinta da gidanta sai yaji duk ya raina kansa.
Jin ana kiran sallar magrib yasa kawai ya fita ya gangara masallaci.
Zainab kam tunda suka tafi ta shiga daki ta zauna a kasa a lungun gado, kanta ta kwantar a kan gwiwowinta, bazata taba yafema su Kabir ba taji zata yafe musu na abinda suka mata amma Allah bazata yafe musu na korar Khalid ba, jin yanda ya taso cikin karatu da aiki ace aikin daya samu an koreshi saboda ita bazata taba yafe musu ba, dan itakam gani take duk saboda ita ne.
Sam bata damu da daren daya kawo kai ba, waya ta dauka ta duba site din gidan tv din su, ganin yanda abubuwansu ke tafiya ba wani ci gaba sai ma ci baya yasa ta cigaba da karantawa tana duduba shirye shiryensu.
Jin bude kofar dakin ne yasa tadan juyo.
A hankali ya karasa inda take, ya zauna a kasa kusa da ita yai zama irin wanda tai yana kallanta.
Murmushi tai tace “ka dawo?”
Sannu da zuwa!
Au sannu da zuwa, ka kaikus?
Ummm sun wuce, kinyi sallah?
Kallansa tai sannan tadan sa hannu a kafadarta, yace “kinyi?”
Nayi la’asar.
Magrib nake tambaya.
Kai ta dan girgiza tace “ina fashi ko shima sai na fito dala dalla?”
Murmushi ya sa ya matso kusa da kunnenta yace “me yasa baki fadan yau bane?”
Kallansa tai tace “oh ni yaushe ka koma haka wai?”
Dariya yai yace “dazu? Yanzu? Jiya?”
Hannu tasa tadan turashi tace “da alama haka kake tun da”
Hannun data turashi dashi ya rike, yanayin kallan da take mai yake mata ne ya canxa, yanzu kam tausayin junansu suke.
Murmushi mai sanyi ya mata yace “kina shekara nawa Ummy ta rasu?”
Idanunta ne suka ciciko da kwalla tace “da alama bamu san komai game da junan mu ba.” Tai maganar hawaye na gangaro mata tana kokarin yin murmushi.
Hannunsa ya sakalo cikin nata ya sako kansa kan nata kan yace “i am a bad person.”
Idanu ta rufe tace “a’a i am the bad person here.”
Wani abu ya had’iya yace “fadamin yaushe ta rasu?”
Kanta ta zame ta kwantar da kanta akan kafadarsa tace “ina 9 years, sanda ta haifi Nabila.” Tai maganar cikin rauni.
Hannunsa dayan ya zagayo dashi ya shafi fuskarta yace “bansan tun kina yarinya bane.” Yai maganar cikin rawar murya.
Hannun dake kan fuskarta ta daura nata hannun akai tace “matar Dady teacher dina ce a skul”
Teacher?
Ya tambaya cikin yanayi na mamaki, dagowa tai ta kalleshi cikin duhun dakin tace “hmm nice na kawowa Ummy abinda zai lalata rayuwarta, na kawowa Dady wacce zata shiga rayuwarsa data iyalinsa, na ba Adam damar tarwatsa rayuwarsa, kaima gashi na shiga taka rayuwar ina neman hanaka..........”
Bakinsa dataji cikin nata ne ya sa ta kasa ci gaba da magana sai hawaye dake gudu akan kuncinta, hawaye me yaji ya zubo a fuskarsa, raban dayai hawaye harya manta, saboda sam duk abinda yazo gabansa mutum ne mai jajircewa.
A hankali ya dago bayan sun gama sumbatar juna, hannayensa yasa akan fuskarta ya dago da fuskarta yace “bake bace dalilin dayasa hakan ya faru da Ummy, sannan Adam zuciyarsa ce ta lalatashi ba ke ba, ni kuma nine na shiga rayuwarki ba ke kika shiga tawa ba.”
Hawaye ne ya zubo mata tace “koba ni nai komai ba akanka kam nasan nice” tai maganar hawaye na sake zubo mata.
Jawota jikinsa yai ya rungume tsam cikin wani yanayi, sai data huce sosai sannan ta dago, wayarsa ya kunna, yace “am sorry gobe zan siyo mai.”
Kai ta daga tace “bakomai”
Yace “sannan kudin dana baki na gaisuwa nine nai ra’ayin baki sannan abune daga cikin al’adarmu ta hausa, na kuma yine dan karan kaina, karki kara neman bani abinda na bada a auranki, ki barni naji da.” A ransa ya karasa da rashin lefen da ban miki ba.
Murmushi tai tace “okay”
Fadamin ya Ummy take? Kamarku daya? Yai tambayar yana kwantar da ita akan cinyarsa.
Kallansa tai tace “kamarmu daya, ai kaga bana kama da Dady.”
Inji wa?
Injini.
Ta fada tana dariya, ido ya zuba mata baice komai ba.
Shiru tadanyi harya dauka bazatai magana ba sai kuma tace “Lokacin Ummy da Dady ni kadai ce a gunsu, yanzu abubuwa dayawa bazan iya tunawa ba a abinda ya faru a lokacin, sai dai a kwakwalwata nasan suna tsananin so na, ina kuma jin dadin yanda rayuwata take a wannan lokacin, kafin a kawo Basma sabuwar Aunty skul din mu..............”
Abinda ya faru a baya ta sanar dashi, hawayen dataji na diga akan fuskarta ne yasa ta runtse idanunta zuciyarta na wani irin bugawa da karfi? Hannu tasa akan fuskarsa.
Jin hawayen daga idanunsa yake yasa zuciyarta ta kara rauni, mikewa tai ya jawota jikinsa, ya matseta sosaj, haushin kansa ne ya kamashi, taya zai kira kansa miji bayan baisan komai game da ita ba? Yana mata kallan dan ta taso cikin kudi, tana komai da kanta yasa take ganin komai dole ya tafi yanda take so?
Jin yanda take kuka tana cewa “Kayi hakuri.”
Ya karasa zuciyarshi yin rauni, meyasa take bashi hakuri? Bayan shine zai bata?
Khalid me kake yi????
Wata ajiyar zuciya hai wacce kana jinta kasan wanda yake cikin yanayi na karayar zuciya ne yake yinta.
Zainab ce tace “shiyasa bansan komai ba sai aikina, gani nake shine zai kwatomin darajata, kayi hakuri nayi amfani dakai bansan halin da kake ciki ba kenan.”
Dago da ita yai ya kalleta sosai yace “why me?”
Idanunsa ta kalla, yace “sanda kike neman wanda zaki aura, why me?”
“I don’t know i just feel like in har dakai ne i can do much better”
Gani tai yayi murmushi, sannan ya kalleta yana shafa gefen fuskarta yace “shiyasa bakya san yanda da mutane?”
Ummm gani nake kowa na amince dashi haka zaimun yanda Adam da Dady sukai akan mace.
Nifa?
Dan kanta tadan kwantar kan hannunsa tadan lumshe ido ta bude tace “bansani ba.”
Murmushi yai yace “Umma gulmata ta miki ko?”
Ummm tasan bazaka min da kanka ba.
Murmushi yai yana kallanta, itama murmushi tai tare da kai kanta kasa, hannu yasa ya jata kan cinyarsa yace “kin yadda dani?”
Kallansa tai tace “bansani ba”
Hannayensa yasa ya zagayota yace “in sanar dake?”
Murmushi tai tace “bana sal......”
Iskar daya farzar ne yasata yin dariya, dagata yai ya mike tace “ina zaka?”
Wanka zanyi na tafi masallaci.
Murmushi tai har ya dau towel sai ji tai yace “ko zaki taimaka da......”
Ai bai karasa ba ta mike cikin hanzari ta fita daga dakin garin sauri har kafarta ta buge amma bata nuna ba, murmushi yai sannan ya zauna a bakin gado.
Shiru yai yana tunani, kenan ba dan Umma ta nunamai ba haka zaita daukanta ayanda yaso? Itama haka?
Taya tai rayuwa da abubuwa biyu? Gana uba ga rashin uwa? Sannan miji yazo daga baya? Sannan aikinta?
*********
Duk yanda taso tai bacci ta kasa, screen din wayarta ta bude, hoton Khalid wanda ya dauka ranar graduation dinsu ne akan alan wayar, ajiyr zuciya tai sannan ta kira number Adam.
Adam dake zaune ransa a bace yana kallan su Kamal nacin shinkafa yaje ci yace mai wai gaskiya a’a bazai bashi gun kwana abinci ma ya dinga bashi ba, haushi duk yabi ya isheshi.
Ganin kiran Afreey yasa ya daga ba tare da ya sani ba.
Tace “Adam ka nemo?”
Jin muryarta yasa ya mike tsaye da sauri, yace “naam?”
Tace “dama dubu goma zan baka tunda baka nemo inda Khalid yake ba shi.......”
Wallahi na nemo.
Wani wulakantacen murmushi tai tace “ina ne?”
Ban san ina bane amma tunda munyi waya dashi in na tambayeshi zai fadamin.
In ka nemo ka fadamin sai na tabbatar zan turoma kudin.
Da sauri yace “zuwa zakiyi?”
Wannan ba damuwarka bane.
Me kike gani in na kirashi kikazo inda zamu hadu?
Yai tambayar yana neman sa’ar amincewarta.
Me yake a kano?
Bansani ba nima in mun hadu ma tambayeshi ko?
Shiru tai dan bata yarda da Adam ba amma tace “to ka mai magana sai na jika.”
Ta kashe wayar tare da zubawa hotonsa ido cikin shagwaba tace “Khalid!”
Nace hmmmmm🤢🤢
*******
Bayan yayi sallah ne sukai sa’a nepa suka kawo wuta, cikin jin dadi ta kalleshi sai kuma tasa yar dariya.
Yace “aikin ya tashi ne?”
Tace “Me kake gani zaifi batawa su Kabir rai?”
Akan me?
Kawai da in bude gun aikina daban da kuma in bude in kwashe masu kwazan aikinsu wannan kake gani?
Murmushi yai yace “gashi kin fada.”
Cikin jin dadi ta kalleshi, yau ne ya fara amsa mata akan tambayar aiki da take mai.
Harta dauko laptop suka dauke wuta, kallan Khalid tai kamar zatai kuka.
Yce “sorry zasu dawo dashi.”
Haka ta maida laptop din, tara nayi ya fara hamma.
Kallansa tai ba dole ba yanata uban aiki kullum ba hutu.
******
Ayusher🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
{60}
Yau harya shirya tana bacci, kusa da ita ya nufa ya sunkuyo ya sumbaci goshinta, sannan ya fita, yana tafe yana addu’ar dacewa da aiki dan bai taba jin haushin fita da sassafe da yake ba irjn yau.
Haka ya wuce gun aikin ginin da suka ci karfi dan an kusa kammalashima.
Zainab kam tana ta bacci, wani irin bacci take wanda take jin dadinsa matuka, kamar a mafarki takejin buga gate, idanunta ta bude sannan ta kalli agoggo, a zabure ta mike zaune ta kara kallan wayarta da gaske 11? Wani irin bacci ne hakan?
Jin bugun kofa yasa ta mike toilet take san shiga amma ganin kar wanda ke bugawa yaji haushi yasa ta zura hijab ta fito.
Tana budewa taga matar na kokarin juyawa, jin karar budewa ne yasa ta juyo ta kalleta tace “oh ashe kina nan.”
Zainab ta kalleta cikin rashin fahimta, dariya matar tai tace “Maman Al’amin ce daga nan gidan.” Ta nuna mata makotanta.
Zainab tace “oh Allah sarki.”
Ta fada tana kallanta, Maman Al’amin tace “bari na shigo mu gaisa dan inata sa rana bansamu na zo ba.”
Jin haka yasa Zainab ta fahimci ciki take san shiga hakan yasa tai gaba da sauri, shigowa tai tana cewa “ba dai bacci kike na tasheki ba?”
Zainab ta kalleta tace “taimako kikai ai.”
Dan dariya tai suka shiga falo, ta zauna sannan suka gaisa cikin mutunci.
“Ina tacewa zanzo gun Amarya mu gaisa amma inata famar hidimar aiki.”
“Masha Allah, a kalla yafi zaman haka.”
Dariya tai tace “duk da agida nakeyi amma sosai nake samu.”
Zainab tadan jinjina kai.
Murmushi tai ta kalli Zainab tace “a kano kike?”
“Eh rabi.” Ta fada tana murmushi.
Maman Al’amin tai dan dariya tace “Allah sarki, ni anan kano nake.”
Bata jira Zainab tace wani abu ba tace “ga wannan, nasan ku amare ba a rabaku da ‘yan abubuwan ku, zan shigo na rasa mai zan kawo miki shine na dauko abinda nake saidawa.”
Ta fada tare da mika mata ledar.
Bude ledar Zainab tai cikin rashin fahimtar menene a ciki ta kara daga robar ruwa wanda aka cika ta da wani abu dark brown, sannan sai kulin garin abu kamar kuka a leda fara, dayan kuma abu ne a dunkule a cikin ledar.
Kallanta tai tace “menene?”
Dariya Maman Al’amin tai tace “haba haba, Amarya kodaga shekarunki ai nasan lokacin auren ne dai baizo da wuri ba, kar kisani dariya taya zaki nuna baki san menene ba?”
Cikin mamaki Zainab tace “na menene? Allah ban sani ba.”
Baki ta bude tace “shekararki nawa?”
Nan da wata biyu zanyi 29, baki ta sake budewa tace “amma baki san wannan ba?”
Eh, abin mahimmanci ne?
Gaba daya kallan mamaki take mata tace “ikon Allah, yanzu yara yan 16 ma sun san kayan mata balle ke?”
Kallanta tai sannan ta kalli cikin ledar, ko irinshi maman Basma ta bata? Amma ita kazace sai su ruwan kankana, wannan kuma daban.
Maman Al’amin ganin da gaske Zainab bata sani ba tace “kiyi kokari ki shanye na ruwan, wannan kuma ki dinga diba kina sawa a nono ko yoghurt kina sha, in kika sha kikaji amfaninsu na miki bayani.
Zainab ta jinjina kai cikin gamsuwa tace “insha Allah, nagode sosai.”
Mikewa tai ta kawo mata ruwa da dubulan dasu alkaki, kadan taci sannan tace zata wuce saboda tana da gyaran Amarya da zatayi.
Zainab ta zuba mata su a leda ta rakota har kofa sannan sukai sallama, komawa ciki tai ta wuce tai wanka ta sa kaya sannan ta shiga kitchen ta daura indomie, wayarta ta dauko sakon Khalid ta gani da alama dazu ya mata.
Kin tashi?
Murmushi tai kamar yana ganinta tace “bayan makara nai, sai fa 11 na tashi.”
11? Dama agoggo ta iya bacci haka?
Nice agoggo?
Murmushi yai sannan ya maida wayar ba tare da ya maida mata ba, Hello?
Nice agoggon?
Haushi ne ya kamata ta ajiye wayar, indomie dinta ga juye ta fito falo tana kallan wayar, har ta cinye baiyi reply ba.
Haushi ya kamata ta juya wayar ta rufeta, kitchen ta shiga ta wanke kwanukan sannan ta kalli ledar, a hankali ta bude robar ruwan ta dan lashi kadan.
Meye wannan?
Ta tambaya tana dan kara kai bakinta kadan ta dan kurba.
Ajiye wa tai ta rufe robar tana cewa “aikam ban iya sha.”
Fitowa tai falo ta dau wayarta, ganin missed call din Khalid yasa ta kirashi da sauri.
Harta katse bai daga ba, ajiyar zuciya tai tace “me kuma nai?”
Jin karar wayar ne yasa ta kalleta, hannu takai zata daga sai kuma ta hau dan kwantar da zuciyarta sai da ta bari tai ringing uku sannan ta daga.
Kina san wani abu ne?
A’a
Okay sai na.......
Kashewa zakai?
Eh da wani abin ne?
A kufule tace “bakomai” kafin ma ya kashe ta kashe.
Fuska ta bata sannan ta tambayi kanta, me nake san ji?
Koma menene a kalla ba kawai ya tambayen ya kashe ba.
Kwan wuta ta kalla suma wadan nan nepan banda rashin mutunci sai yaushe zasu kawo wuta?
Waya ta daga ta kira Nabila suka fara hira, wacce rabin hirar mita take mata akan Khalid ya kira wai kawai ya tambayeta abu yace zai kashe.
Dariya kam Nabila tayishi harsai da cikinta ya kulle, tace “Aunty ni wlh girki nake karkisa na kone.”
Girki? Ta maimaita sannan tace “nabila sai anjima.”
Da sauri ta kashe ta kalli agoggo, karfe 3?
Mikewa tai ta wuce kitchen kamar wacce aka mintsina kawai ta hau yin abinci.
Khalid kam dadi yaji dan yauma da wuri yabar garage gida ya nufo hannunsa dauke da bread, da mai na gen.
Harya shiga falan baiji mostinta ba, hakan yasa ya nufi daki, bata daki sai dai jin karar ruwan flushing daya ji ne yasa yasan tana toilet, murmushi yai sannan ya zauna a bakin gado ya zubawa kofar toilet ido yana jiran ta fita.
Bude kofa tai, sam batasan zata ganshi ba hakan yasa gabanta faduwa, ganin yanda ta tsorata ne yasa ya taso da sauri, tsoro kikaji?
Kallansa tai sannan ta harareshi tace “ba tsoron kaso bani ba?”
Kallanta ya sake yin ya rike hannunta yana kallan fuskarta.
Samun kanta tai da yin kasa da idanunta, murmushi yai yace “dazu kinji haushi ne?”
Dagowa tai ta kalleshi ta bata fuska tace “ba haushin kaso bani ba?”
Murmushi yai yace “haka ne?”
Ba hakan bane?
Sun kawo miki wuta? Ya tambaya yana zama akan gado.
Kh......
Sai kuma tai shiru, yace “Khalid zaki ce?”
Shiru tai tare da kauda kai, yace “fada gani.”
Kallansa tai tace “Khalid wai me yasa kake san cemin agoggo?”
Ta fada cikin dakewa.
Khalid?
Kallansa tai sai kuma tai shiru, Khalid? Khalid? Ya maimaita sannan ya mike ya shiga toilet.
Shiru tai tare da binshi da kallo, ko banza na rama, ta maimaita tare da yar dariya.
Kitchen ta wuce ta juye abincin sannan ta dawo falo.
Fitowa yai sanye da yar karamar riga da wando.
Kallan ta yai, ta kalleshi taga ya daure fuska, dariyarta ga guntse har yazo inda take, gani tai ya zauna a kasa inda take ya mika mata man zafin hannunsa.
Kallansa tai ya dago kansa yana kallanta, amsa tai jikinta a sanyaye.
Rigarsa ya daga yace na shafa anan, ya nuna mata kafadarsa.
A hankali ta lakuto tana shafamai gaba daya jikinta yai sanyi, jin yanda take shafawa a hankali yasashi lumshe idanunsa.
A hankali yace “me kike cewa wancan Mutumin?”
Wani mutumin?
Wancan mutumin dai, sunanshi kike kira?
Yanzu kam ta fahimta hakan yasata cewa “meyasa kake sanji?”
Kansa ya sake dagowa yana kallanta yace “in fadamiki?”
Eh!
Hannunta ya riko ya ya juyo tare da dan mikowa yana kallanta, yanayinta ne ya canza, tana kallansa, in fada miki?
Da sauri ta dago man zafin saitin fuskarta tace “ka manta?”
Wani abu ya had’iya yace “ina dai tausayinki amma ai ba dole.....” sai kuma yai shiru tare da yin murmushi.
Zama yai kusa da ita yace “Allah karki kara cemin Khalid.”
To me kake so na cema?
Shima sai na fada miki?
Ahh to zan ce ma K? Tai fadi yanda ake kiran K
Ke? Kin manta keke, ko dayake ki fada nima sai na ce miki Z, ya fadi Zet yana kallanta.
Z? Eh ba K kika ce ba?
Allah bazan yadda kacemin Z ba.
Dariya yai sannan yace “Auntyn ki dake garin nan a wace unguwa take?”
Sharada menene?
Ko zaki kirata ki fada mata zamu je?
Ido ta zaro tace “muje ina?”
Kallanta yai yace “gaisheta, ki kirata kiji in gobe tana nan.”
Baki ta bude tana kallanshi, sai dai samun kanta tai da jin dadi a kasan ranta, tunda take da Adam bai taba ce mata ko Auntynta ta gaida ba, ita dama zumuncin bai dameta ba balle taje, in har taje gidan to lalai haihuwa ce ko biki, bata taba kawo yau ya kamata taje su gaisa ba.
Kallan Khalid tai fuskarta dauke da murmushi ta sauko ta ja plate ta fara zubamai abinci, hannunta dake komarin suba miya ya rike, a hankali ta dago ta kalleshi yace “kinci abinci ne?”
Zanci anjima.
Hannunta ya sake ta suba miyar, zata mike ya sa hannu ya kara riketa, kallansa tai, spoon ya juya mata saitinta ya kalleta ya nuna mata bakinshi.
Tace “dan Allah kaci abincinka.”
Fuska ya daure yace “ashe yau zan kwana da yunwa.”
Cikinka ne fa?
Eh cikin nawa ne zan gani ko an damu shi.
Khalid hooo abinda ta fada a ranta kenan, spoon din ta dauko ta debo ta nufi bakinshi jin abin take wani banbarakwai.
Baki ya bude ta samai, amsa yai yana ci yana kallanta, sai dayaci sosai, ruwa ta dauka ta zuba takai bakinta ta kurba zata sha, amsar cup din yai ya sa hannu a kugunta ya matso da ita dad dashi, ruwan ya sa a bakinsa sannan ya jawota jikinsa ya sa bakinshi cikin nata ya zuba mata ruwan, tana hadiyewa ya shiga yin salo da bakinta.
Gaba daya jitai jikinta ya mutu, yau kam ta dage sai kokarin biyema bakinsa takeyi, jitai wani abu na tsirga mata, kallansa tai da idanunta da suka shanye?
A hankali ya kai bakinsa kusa da kunnenta yace “zan iya jira?”
Hannu tasa ta turashi baya ya dan yi baya jikin kujera.
Mikewa tai da sauri tai kitchen.
Kallan maganin nan tai kawai ta samu kanta da dauka ta dauke numfashi tana sha, sai datasha kusan rabi sannan ta ajiye tana maida numfashi.
Waya ta dauka ta kira Aunty ta sanar da ita sakon Khalid.
Ba karamin mamaki Aunty tai ba dan kasa bata amsa tai sai da Zainab tace “Aunty kina ji?”
Da sauri tace “ina nan sai kunzo.”
********
Washegari.
Karfe hudu ya dawo ta shirya tsaf cikin lace peach anyi ratsin marron da light brown a jiki, dinkin ya amshi jikinta sosai, tayi kyau matuka, tana zaune tana waya da Nazifi akan list da take so ya turo mata, Khalid ne ya gama shiryawa a daki ya fito falo.
Sanye yake cikin shadda sky blue yasa hula dark blue yayi kyau sosai shima, kallansa ta shiga yi tana murmushi.
Muje?
Ya fada yana kallanta, wayarta ta kashe bayan sunyi sallama sannan ta kalleshi tare da mikewa ta yafa mayafinta a kasan kafadarta, kusa da ita ya tako a hankali, yaja mayafin ya maida shi saman kanta.
Idanunsa tadan dago ta kalleshi sannan tai murmushi.
Hannu ya mika maga kallansa tai sannan tasa nata hannun cikin nashi suka fito.
Mota suka shiga ya kalleta yace “me zamu kai?”
Shiru tai kafin tace “basai munkai wani abu ba, ai ta gida ce.”
Bai ce komai ba ya ja motar, sai daya fita sannan ya fito ya rufe gate, shiru tai tana kallanshi harya dawo.
Kallanta yai yace “musai fruit?”
Kamar tace “akwai halin hakan? Sai kuma tai shiru.
Sai da sukai tafiya sosai suna tafe tana bashi labarin yanda ta zauna a gidan, kan titi ya gangara yai parking ganin mai fruit.
Yace “bari na siyo.”
Shiru tai tare da daga kai.
Harta wuce ta dawo baya tana san kara tabbatar da idanunta.
Parking tai kusa da motar dake gun, sannan ta nufeshi.
Mika dari biyar yai ana zubamai fruit din yana tunanin ya isa?
Jiyai ance Khalid?
Kallanta yai sannan ya dauke kai ya maidashi gun lemo da ayaba.
Kusa dashi taje cikin wani irin shauki take kallanshi kallan shigar dayai da yanda yai kyau yasa takeji kamar ya rungume shi.
Kusa dashi taje tace “kasan ina zani?”
Kallanta yai, tace “gunfa Adam zani yanzu ina san jin inda kake.”
Kai ya girgiza cikin kufula sannan yace “hala baki da abinyi ne shiyasa.”
Murmushi tai cikin farin ciki tace “Ka dawo gidan Tv din nan zan musu magana....”
Baiko bi ta kanta ba ya amshi ledar ya juya, kallan Zainab yai ta glass wacce ta cika tai fam, ko daga cikin glass yana ganin tsantsan kishi dake bayyane a fuskarta.
Kallan Afreey yai yace “wuce kije inda zaki please”
Yai maganar sannan ya juya, rigarsa ta kamo wanda hakan yasa Zainab zaro ido, bude kofa tai da sauri tace “Sweet muje in ka gama.”
Ta fada cikin faduwar gaba dan ita kanta batasan me take fada ba.
Afreey ce ta kalleta, cikin rashin fahimta take kallan Khalid, kallanta yai sannan ya nufi inda Zainab take cikin sanyanyan murmushi.
Juyowa yai ya kalli Afreey yace “zo ku agaisa, she is my wifey”
Jakar hannunta ce ta fadi jitai kanta na wani irin juyawa, Khalid ya kalli Zainab sannan ya kalli Afreey yace “Safiya zo ku gaisa.”
Kallansa tai idanunta ne suka fara canzawa, yasan ba zuwa zatai ba hakan yasa ya kalli Zainab yace “muje?”
Kai ta daga da kanshi ya taimaka mata ta shiga motar sannan ya rufe mata motar ya juya ya nufi inda Afreey take, jakar data yar ya dauka ya mika mata yace “da alama tsayuwar ta miki dadi, mu mun wuce”
Ya juya yashiga yaja suka tafi.
Gaba daya kanta ke juyawa, wayarta daje ta zabga kara wanda Adam ke kiranta ya mata karya akan bayannan.
Wani irin ihu ta saki jin da gaske ba mafarki take ba.
Nikam jin ihun nan bansan sanda na arta a guje ba🏃🏻♀
*****
Ayusher🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
{61}
Gaba daya ji tai numfashinta na sarkewa, mai lemo ne ya matso yace “baiwar Allah lafiya?”
Khalid wanda ya shiga mota yaja ya fara tafiya a hankali yana kallan glass din madubinsa ta baya, Zainab a kufule tace “in kasan bakasan barinta meyasa ka taho?”
Kallanta yai yace “am sorry amma sai na dan duba halin da take ciki, kar wani abu ya faru.”
Baki Zainab ta bude cikin mamaki tace “badai fadamin kake zaka koma inda take ba?”
Eh, ya fada tare da dan yin baya da motar, Zainab kam wani mugun kishi ne ya turnuketa, Khalid ne yai parking ya juya yana kallan bayan motar inda Afree take a tsaye mai lemo na mata magana.
Zainab ce ta juya tana kallanta, sanye take da riga english wears rigar takai mata gwiwa, sai wando jeans pencil, ta yane kanta da mayafi.
Wani irin kishi ne ya kara rufeta, Khalid ta kalla wanda ke kallanta sanda ta wuce ta shiga mota ji take kamar zatai hauka.
Juyowa yai sannan yace “kina ganin ba matsala?”
Wata uwar harara ta watsamai tace “in da matsala ka je ka kaita gida mana.”
Okay to ko zaki fara zuwa sai na biyoki?
Tace “mene?”
Gani tai yana neman fita cikin hanzari ta rikoshi tace “da gaske zuwa zakai?”
Eh na dauka mun gama maganar? Ya fada yana kallanta.
Idanunsa ta kalla tace “ka ajiyeni ni matarka ka tafi gun wata?”
Bakya ganin halin da yake ciki? Sannan waye yace min duk sanda naso nai aure?
“Halin da take ciki?ni halin da nake ciki fa?”
Ido ya kura mata hana kallanta, ta kauda kai tace “maganar aure ai ba auranta kai ba.”
“Bari na je gidansu daga can na gabatar da kaina.”
Ya fada tare da juyawa yana neman fita, da sauri ta kara rikeshi tace “wai da gaske kake?”
Kinga alamar wasa a nan?
Tace “maidani gida.” Ta fada cikin raunin murya.
Yace “ke dai kikace naje gidansu yanzu.”
Yaushe na fada?
To meye na hanani?
“Bansani ba amma nidai.......”
Sai kuma tai shiru, murmushi yai ya matso saitin kunenta wanda hakan yasata dan dagowa, yace “fadamin sunana.”
Sunanka?
“Eh, in ba haka ba yanzu na fita na maidata gida.”
Kai ta dauke tace “meyasa ka taho guna kasan hankalinka yana gunta?”
Fadi kona koma gunta ki fada.
Dan baki ta motsa yace “banji ba.”
Ta kara motsa baki, shikenan tunda bazaki fada ba, ya koma ya zauna.
Kai ta juya tana kallan waje ta glass tace “Sweet.”
Murmushi ya saki, ya juya yaga ba motar Afreey agun, ajiyar zuciya yai yana fatan Allah yasa ta cireshi a ranta.
Zainab ya kalla yace “Ur sweet is here.”
Samun kanta tai da jin kunya, murmushi yai sannan yaja suka tafi.
Hade rai tai, hannu yasa ya kamo hannunta, kallansa tai tace “meyasa baka bitan ba?”
Ina zan bita bayan naga bakya so?
Shiru tai tana tunanin shigar da Afreey tai da yanda tai kwalliya, maza irin haka suke so? Meye damuwata da abinda suke so?
Sake sake tai tayi har suka isa.
********
Cikin gidan aka bude musu gate sukai parking ba wai katan gida bane sai dai kana ganinshi kaga gidan dake da rufin asirinsu, a gun talaka kuwa gida ne na masu kudi.
Ledar hannunsa daya dauko ta kalla kallanta yai sannan ya kalli ledar da take kallo, mika mata ledar yai yace “ki rike.”
Amsa tai ta rike.
Bangarenta suka wuce Zainab tai knocking din kofar, daga ciki wata yarinya wacce batakai Asiya ba tazo ta bude.
Cikin tsananin murna tace “oyoyo Aunty.”
Zainab ta kalleta tace “Amira kece kika girma haka?”
Amira ta basu guri suka shiga,
Falo suka shiga, Zainab tace “ina yaran gidan?
Suna islamiyya
Kefa?
“Bana jin dadi ne, Umma na sallah ne”
Zama Khalid yai a kasa, Zainab ta kalleshi tace “ka hau kujera mana.”
Kai Yadan girgiza mata zatai magana Aunty ta fito sanye da hijab tace “ikon Allah, wallahi ban dauka ds gaske kike ba.”
Zainab ta kalleta tace “kai Aunty.”
Zama tai akan kujera tana kallan Khalid tace “lale lale, Ango godiya nake dan nasan Allah Zainab haka kawai bazatacs zatazo ba.”
Gaisheta yai, ta amsa cikin girmamawa yanda taji ya gaisheta cikin girmamawa.
Cikin jin dadi take kallansa sannan ta kalli Zainab wacce ta rasa ina zata zauna, ganin Khalid a kasa.
Tace “Amarya.”
Zainab ta dake ta zauna a saman kujera tana amsa gaisuwar Amira.
Amira dake tsugune ce ta gaida Khalid ya amsa yana tambayar ta makaranta.
Zainab ta mika mata ledar sannan tace “Ajinta nawa yanzu?”
Aunty ta kalleta tace “ko kunya ma tambaya kike?”
Dan dariya tai tace “Rabona da ita na dade.”
Aunty ce ta mike tai kitchen, sai data shiga sannan ta sa Amira ta kira Zainab.
Nan suka hada kayan da aka shirya dominsu, wanda tayi ne tana san ganin ko da gaske take.
Khalid kam zubo yasha yaci samosa guda daya, wayarsa ya dauka ya mata text, ko na barki na dawo da daddare?
Da sauri ta mai reply tace “a’a”
Murmushi yai sannan ya mike, Amira data fito ya kalla yace “Auntynki zata tsaya anan wai sai dare, ko zakima Umma magana zan wuce sai na dawo?”
Juyawa tai ta sanar da Mamanta, Zainab dake zaune mamaki ya kamata yaushe tacemai zata zauna?
Mikewa tai ta fito falo, kallan Aunty yai yace “Aunty na dawo daddare tace tana nan ita.”
Cikin farinciki ta kalli Zainab tace “masha Allah nagode sosai Zainab.”
Zainab tai yake kawai, haka ya fito tabi bayanshi, suna fita waje tace “yaushe nace zan zauna?”
Dazu ko kin manta?
Cikin mamaki tace “A’a fa nace.”
Au haba? Nikam eh na gani.
Tace “ni Allah bansan doguwar hira, ki daure kanwar Ummy ce ita kanta tanasan kadaicewa dake.
Dan baki ta turo yai murmushi yace “sai na dawo.”
Haka tana gani ya shiga mota, ya kalleta yace “ko na kawo miki laptop dinki? Naga suna da wuta.”
Kallansa tai tace “Lalai ma.”
Murmushi ya yace “ki fadi sunan.”
Tace “naki.” Ta juya tai hanyar ciki, jitai yace “bazaki fada ba?”
Da sauri ta wuce ciki tana murmushi.
********
Marin data xuba maine yasashi gigicewa, hankali a tashi ya kalleta yace “Afreey yadaga zuwana zaki wankeni da mari?” Ya fada tare da rike gun.
Cikin hucci take kallansa tace “ni zaka maida yar iska?”
Kamar ya? Haryanzu hannunsa na kan fuskarsa dan yaji abin.
Hannu ta daga tana neman kara mai wani yai baya da sauri yace “Afreey lafiya?”
Cikin tsananin masifa da tashin hankali tace “ta ina? Taya Khalid zai aureta?”
Adam ya kalleta wato taji yayi aure kenan?
Kallan Adam tai tace “uban me kake har hakan ta kasance?”
“Ni kuma? Wai ya kikeso nai da Khalid ne?”
“Fadamin inane gidansa?”
“Ina na sani?”
Haushi ya tuketa tace “ai kasan inda gidan matarka yake, ina ne?”
Adam cikin rashin fahimta yace “gidan matata suke?”
Jakar hannunta ta cillo inda yake ta sameshi kuwa, kallanta yai yace “Afreey lafiya?”
Cikin masifa tace “kana haukar ina Zainab ta auri Khalid?”
Kallanta yai kawai kuma ya bushe da dariya yace “Afreey yunwa kike ji? Wace Zainab din?”
Wani kallo tamai hawaye na zubo mata tace “bakada hankali amma ko? Tun yaushe nace ma akwai abu a tsakaninsu?”
Jin abin yai sama taka kamar irin an mai duka din nan.
Kusa da ita ya matso yace “kina san cemin Honey ce matar Khalid ko me?”
Sai yaushe zaka fahimta? Sau kuma nawa kake san na fada? Da idona fa na gansu.
Baya baya ya fara yi yana girgiza kai alamar a’a, wayarsa ya dauko da sauri ya kira number Goggo.
Goggo kam acan tun jiya take kwance ba lafiya, ita kadai a dan tsukukun dakin da take, yunwa ta gama cinta harta gaji, gayan tuwon dake gefe ta dauka ta hauci, wallahi yau zata bar kauyen nan ko menene sai dai ya faru amma bazata zauna ta mutu ba, dole ya samu ko hamsin ne tasa a waya ta kira Hajiya Bilki ko aikatau ne ta samar mata amma bazata zauna awannam gidan ba.
****
Adam kam duk yanda ya kirata rashin service yasa taki shiga.
Haka ya hakura yana dagowa yaga Afreey bata gun, hankalinshi a tashe ya dannawa Khalid kira.
Khalid na ganin kiran bai daga ba dan yasan dalili shikuma bai san suyi magana ta waya, dan yanasan sashi yaje gidansu Razy abubuwane suka hadarmai yasa ya manta.
******
Acan gidan Aunty kuwa, Zainab batasan sanda ta sake ake ta hira ba, yayin Amira ne suka dawo su Samira.
Kaya suka cire, Samira tasa riga da wando ta fito.
Zainab ce ta kalleta sannan ta shiga daki ta kirata.
Samira ta shigo tana cewa “Aunty gani”
Zainab ta kalli Kayan tana tuno Afreey, sannan tace “kayan jikinki ina ake saida irinsu? Nabila ce take so.”
Samira tace “gasu nan a ko ina, akwai a stores akwai a kasuwani irinsu saban gari.”
Shiru tai dan batasa saban gari ba, amma ta dake tace “zan fadamata”
Haka suka dawo ana hira itadai sai duba waya take.
Khalid kam sai 8 na dare ya taho, wayarsa daya kashe saboda kiran da Afreey keta mai ya kunna.
Texts ne suka fara shigowa.
Kansa yadan dafa sannan yaa Zainab text akan yana hanya.
*****
Ayusher 🏌🏻♀
🍀A GIDANA🍀
.........................
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*Masoyan Kwaro da Agoggo suna godiya🥰*
{62}
Aunty ce ta shigo daki inda Zainab ta idar da sallar isha’i.
A bakin gado ta zauna ta kalli Zainab cikin jin dadi wanda fuskarta ta kasa boye hakan tace “nagode sosai Zainab, yau bakisan irin farincikin da kika sani ba.”
Zainab dake kallanta tace “kiyi hakuri Aunty yau ma badan Khalid ya sani zuwa ba da haka zan ta cigaba da zama kamar banda kowa.”
Dan ajiyar zuciya tai tace “Da alama kinyi dacen miji na gari, Allah ya baku zaman lafiya mai dorewa.”
Samun kanta tai da cewa Ameen, wanda hakan yasa Aunty murmushi tace “da alama ana san wannan mijin.”
Kallanta tai tana murmushi tace “bansani ba Aunty, bansan ya akw gane ana san mutum ba, na dai san kawai yanzu rayuwata ba daya take dana da ba, inaji kamar bazan iya yini ba tare da shi ba.”
Ta karasa maganar tana sauke kanta kasa, Aunty ta dafa kafadarta tace “Kiyi kokarin faran tamai rai da janshi a jiki, mazajen yanzu ka ja su a jiki ma ya aka kare bare, na tabbatar shi zai nuna miki me nene a ranki.”
Zainab tadan kalleta, Aunty ta dan dafa kafadarta tace “Allah ya kareku dwga sharrin masu sharri, amma anan gidan zaku cigaba da zama?”
Zainab tace “Eh nan yake so.”
“Haka ne, kin kyauta Allah ya kara muku fahimtar Juna.”
Ameen tace sannan ta kalleta tace “Aunty har yanzu baban Amira?”
Murmushi tai na yake tace “yana leko nan sanda ya ga dama kawai dai baya zama ne.”
Shiru Zainab tai tana mata kallan tausayi, Aunty tadan harareta tace “har mun saba ki daina min kallan tausayi.”
Wayar Zainab ce tai kara Aunty ta miko mata ita, ganin Khalid ne yasa tadan juya baya ta dauka “Ur sweet ya iso.”
Kana waje?
Eh
Okay ganinan zuwa.
Kashe wayar tai ta kalleta tace “zamu wuce.”
Kinasan wani abu?
A’a ta fada tana gyara dankwalinta.
“Dama ke kam ta yaushe zakice ma kina san abu? In dai akwai abinda kikeso ki fadamin ko Samira sai na aiko ta kawo miki.”
Zainab ta daga kai sannan ta dau mayafinta ta yafa.
“Dan Abin matan nan na bar ajiyarsu saboda kinga yanda muke zaune da shi, amma in kinaso zansa a kawo miki.”
Tana jinta amma sai tai kamar bataji ba tana kiran Amira, haka suka fito yaran suka rakata har mota.
Suna fita daga gidan ta tsuke fuska, baiko kalleta ba shima ya dauke kai haushi ne ya kamata ganin suna ta tafiya baice komai ba tace “ina kaje da ka gudu?”
Ina kike san naje?
Kallansa tai tace “tambaya da tambaya?”
Amsa da amsa?
Juyowa gaba dayanta tai tace “ba dai....”
Jin ya kamo hannunta ne yasata yin shiru, hannunta ya rike yace “ba dai me?”
Murmushi tadanyi tace “sakeni dare yayi kana tuki da hannu daya.”
Sai kin kira sunana tukun.
Kallansa tai tace “nifa Allah bansan ya akai na samo sunan nan ba.”
Koma ya akai kika samo ni sunan yamin.
Murmushi sukai dukansu, har suka isa gida.
*********
Washegari
A hankali ya bude idanunsa ganinta kwance kusa dashi ne yasashi sakin wani sanyanyan murmushi, hannunsa yasa a gefen fuskarta yana dan shafawa, mostin dayaga tayi ne yasa shi zare hannunsa.
Wayarsa ya dauko yana duba time, yana kokarin sauka yaji ta rikeshi.
Juyowa yai ya kwanta yana kallanta, idanunta ta bude tace “shiri?”
Eh.
Inka tafi sai dare?
Bakya san na fita na dade?
Shiru tadanyi, hannunta ya kamo ya daura akan fuskarsa.
A hankali yace “zan dawo da wuri”
Murmushi tai tace “kadan taimaka min da printing din wasu takardu.”
Okay.
Ya fada kallan juna sukai a hankalu ya matso ya sumbaci bakinta, sannan ya zame gefen kunnenta yace “sai yaushe?”
Murmushi tai tace “kwana 9 nake.”
A zabure ya dago yace “ta me?”
Ta hade rai tace “tara”
Kallanta yai yace “tara? Da gaske kike?”
Eh ya zanyi?
Wani abu ya hadiya kawai ya mike ya nufi toilet, dariya tadanyi sannan taja bargo ta rufe fuskarta, wai Khalid baida kunya dama?
Sako ne ya shigo wayarsa, bata kalli wayarba bare tasa ran dauka tana kwance tana murmushi ita kadai, jiya kwata kwata bata bude laptop dinta ba, anya lafiyar ta kalau kuwa? Kwanan nan aikin ma ba sosai take ba batasan meyasa in tana tare da Khalid mantawa ma take da maganar aiki.”
Kunyar kanta da kanta ne ya kamata ta kara shigewa bargo.
Khalid ne ya fito bayan yai wanka yai alwala.
Kallanta yai yace “kin koma?”
Dan idanun ta ta leko ta kalleshi, zama yai a bakin gado yana shafa mai yace “inata san tambayarki izinki nawa a karatu?”
Karkamin dariya.
Yadan kalleta yace “ba’ai abin arziki ba kenan?”
Tace “tunda na gama primary na daina zuwa.”
( Magana ta gaskiya wannan matsalar tana addabarmu, iya kacin karatunmu na islamiya daga primary ne, da zaran an fara secondary an girma shikenan an daina zuwa islamiya, ana ganin an girmi zuwa islamiya amma bamu girmi karatun boko ba, dan Allah ko ba a je islamiya ba mu dinga kokarin yin tilawa a gida, dan Allah dayawan mu sai mifi wata ko qur’ani bamu bude ba.
Ke da ni da shi da ita dan Allah mu dinga tunawa da Al-Qura’ani muna karantashi ko ya ya ne, in karatu kullum bazai yiwo ba a kalla duk bayan kwana biyu ka karanta.
Allah yasa mu dace Ameen)
Vest dinsa yasa sannan ya fara sa kaya yace “biyar?”
Tace “a’a”
Kallanta yai yace “badai biyu ba?”
Dan dariya tai tace “goma, biyar kass biyar sama.”
Agoggo yasa ya dau wayarsa ya matso kusa da ita ya nuna mata kuncinsa, dan shiru tai tana kallansa.
Kallanta yai ganin yanda ya kalleta yasa ta fahimci yaji haushi, neman dagawa yai da sauri ta riko wuyan rigarsa ta sumbaceshi a kan labansa.
Tana neman sakeshi ya sa hannu ya kara riketa ya kai bakinshi cikin nata, dagowa yai a hankali yace “Allah kwana tara yamin yawa.”
Jan bargo tai ta rufe fuskarta juyawa yai ya fita.
Sam bai ciro wayarsa ba saboda ganin yadanyi late yana fitowa daga masallaci ya wuce gun aiki.
Yana ta aikin wayarsa tai kara, zarota yai ya duba ganin Abba ne yai saurin dauka suka fara hira.
Sai da sukai sallama sannan yaga sako, budewa yai idanunsa ya zaro yana kara kallan sakon, cikin tsananin farin ciki ya tura sakon wayar Zainab.
Zainab kam bacci kadan tai ta tashi tai wanka sannan ta fara aiki, turamai takardun da zai mata printing tai ta email.
Mikewa tai ta hada tea tana sha tana aiki, shiru tai tana kallan screen samun kanta tai da murmushi.
Ya xaiyi in nace nai wanka?
Fuska ta rufe ita kadai kamar wanda yake gabanta sai murmushi take kai kace albishir aka mata.
Jin sako ya shigo wayarta ne yasa ta dau wayar tana fatan Khalid ne.
Ganin shidin ne yasa ta bude sakon da sauri.
Cikin hanzari ta kira wayarsa, Khalid wanda yai murmushi ganin kiranta ne ya mike yai gefe ya daga wayar.
Zainab cikin farin ciki tace “Yanzu naga text.”
Bari na zo gida.
Yanzu?
Eh
Ya fada batace wani abunba ya kashe wayar ya kalli shugabansu yace “zaije gida sannan daga yau bazai sake zuwa ba dan ya samu aiki.”
Sosai ya tayashi murna dan ya san kwazon Khalid.
Jin Khalid zaizo yasa Zainab ta mike da sauri tai kitchen kawai ta hau shan robar hadin nan da aka bata.
Kunyar kanta ne ya kamata tasa dariya ita kadai tana mamakin me take yi,
Mai zaici?
Indomie ta fara kokarin sawa.
Khalid kam gida ya wuce direct yana bude kofar falo tana fitowa daga kitchen.
Wani murmushi ya mata sannan ya bude hannayensa.
Murmushi tai itama hakoranta suka fito tace “badai nufinka in ruga in rungumeta ba?”
Hade fuska yai yace “idan bakiyi ba kuwa komawa zan.”
Kaifa kace zaka dawo bani nace ka dawo ba.
Ina cikin farin cikin ma bazaki min ba?
Kallansa tai shima idanunsa na kanta, takowa ta fara yi a hankali har tazo inda yake.
Hannu yasa ya jawo ta jikinta ya rungume kawai sai jitai ya dan dagata.
Dariya tasa tana dan dukan bayansa tace “ajiyeni dan Allah.”
Ajiyeta yai ya kalleta kallansa tai tace “Congratulation.”
Thanks dear.
Ya fada yana kallanta, idanu ta dan zubamai, sannan ta kamo hannunsa ta bude tafin hannunsa.
Murmushi yai yace “menene?”
Wad’annan hannaye sunsha wahala
Kallanta yai yana murmushi.
Idanunta ne suka ciciko ta dago tana kallanta cikin magana mai shirin kuka tace “yanzu ka daina aikin ginin.”
Kai ya daga mata fuskarsa a sake, ta kara cewa “ka daina aikin mota?”
Murmushi yai ya daga mata kai.
Sakeshi tai jin zuciyarta na rauni tai kitchen da sauri.
Kallanta yai kafin ya bi bayanta, shiga tai tana sa indomie.
Kusa da ita yazo ya sa hannu ya rungumeta ta baya yace “menene?”
Bata juyo ba tace “bakomai, ya Umma tai?”
Kansa yadan tukufo ya kwantar a bayanta yace “kuka kikai?”
Bata juyo ba tace “bansan meke damuna ba wlh, nifa ina dadewa kafin nai kuka amma yanzu komai sai naji inaaa...”
Sai kuma tai shiru, murmushi yai sannan ya kalli kusa da ita ganin bottle a bude yasa ya kalleta yace “na meye?” Yai maganar yana dauka.
Kwacewa tai da sauri tace “Makociyar mu ce ta bani.”
“Menene? Kikasha kuma?”
Kallansa tai tace “ba sai kaji ba”
Tai maganar tana boyewa a batanta.
Dariya yadanyi yace “kawai daga zuwa ta baki abu sai ki hau sha? Sannan harda kin fadamin?”
Jeka jeka falo ka zauna.
Ta fada tana turashi.
Murmushi yai ya fita.
Falo ya zauna ya dau waya ajiyar zuciya yai ganin uban kiran da Afreey da Adam suke mai.
Number Adam ya kira, ringing daya Adam ya dauka, yace “dan gidanku kana ina? Kana ina nace?”
Yai tambayar cikin zafi da fada kamar wanda ke shirin dukansa.
Khalid yace “kaje Naibawan?”
Uban Naibawa zani ba Naibawa ba, ka yaudareni ka cuceni sannan kace wani nace Naibawa, kana ina?
Khalid yace “mu hadu an jima, a Naibawar daka tsana.”
Bai jira yace wani abu ba ya cigaba “zan turoma da Address din dan nasan ka manta gidan, in mun hadu acan naji me kake san cewa.”
Wayarsa ya kashe sannan ya kalli sakon Afreey kala kala data mai, kansa yadan dafa yana cikin tsananin farnciki amma ana neman sashi tunani.
Kiran Abba ne ya sake shigowa, nan Abba ya kara tayashi murna yace “yaushe zaka fara?”
“Bansani basai gobe suka ce naje.”
Khalid dadi ya hanani rufe baki.
Kace Umma taci abinci kar dadi ya hanata.
Shigowar Zainab falan ne yasa ya kalleta, tare da yin sallama da Abba.
Batai auni ba taji ya jawota kan cinyarsa.
Plate din hannunta ta rike sosai tace “zaka sani bari.”
Kallanta yai yace “tunda Allah yayi yanzu na bar wancan aiki, haka zan zauna na saki a gaba ina kalli har sai kin cika 9 days?”
Tace “to ya kake so nayi? Ka dai san ba’ayi.”
Na sani amma kwana 9 tsakani da Allah?anya Sweet din nan naki zai iya jira?”
Dariyarta ta guntse tace “wai sai wani kiran kanka Sweet kake.”
“In baza’a kirani da hakan ba ni ba sai na kira kaina dashi ba?”
Murmushi tai ta ajiye plate din sannan ta mike yace “Dady na gaidake.”
Kunyi waya ne?
Eh na fadamai an samu aiki.
Murmushi tai, plates din indomie din ya dauka ya kalleta yace “thanks.”
Murmushi tai tana kallansa yana ci, meyasa kwanan nan take jinta kamar wata yar mitsilar yarinya?
Bai kalleta ba sai jitai yace “ni adaina kallo na, abarni da takaici kwana 9.”
Mikewa tai tsam ta dau wayarta tai daki, tana shirin shiga tace “na gama”
Ta shige daki, na gama? Ya maimaita cikin rashin fahimta, da sauri ya kalli kofar dan ya gane.
Jiyai ya koshi da abinci ya mike tsam yai hanyar daki.
*********
Zazzabin daya rufeta ne yasa Mumy saukowa gun mahaifinta tana sanar dashi halin da Afreey ke ciki, kallanta yai sannan yace “garin ya ya?”
Wlh bansani ba yanzu na shiga naga bata je aiki ba na ganta a kwance.
Mikewa yai ya hau sama inda tafkeken dakinta yake, tana kwance cikin bargo sai kallan wayarta takeyi.
Abbi ne ya zauna tare da yaye mata bargo, kallansa tai tana hawaye.
Yace “Baby na menene?”
Mikewa tai ta rungumeshi tasa kuka.
Hankalinsa ne ya tashi ya na tambayar menene.
Tace “Abbi bazan iya hakura dashi ba dan Allah ka kwatomin shi.”
Wanene?
Kallanss tai tace “Khalid.”
Ajiyar zuciya yai yace “sau nawa ina miki magana akan wannan talakan yaran? Na dauka tun a makaranta na hanaki?”
Kallansa tai tace “Abbi please.”
Mikewa yai rai a bace ya bar dakin.
Haushi ne ya kamata kawai ta zubo da duk kayan dake kan madubinta.
Abbi na jinta, Mumy na kokarin shiga yace “batta.”
*******
Takardun da aka watsomai ne yasa ya kalleshi yace “Kayi hakuri yaya.”
Ni zaka maida dan iska? Ce maka skai banda abinyi ko me? Ko kuwa ce ma akai kudin da na sa na bude gidan Tv dinan a waje na samosu? Yau zan kira Zainab ta taimaka ta dawo, in kuma har bata yadda ba to zan sai da gidan tv din nan da a gurina yanzu bashida wani amfani.
Kafin Kabir hai magana ya juya ya fita.
Cikin takaici ya ke sakin huci na jin haushi.
Ya zaiyi?
Ya zaiyi?
Nace wa kake tambaya🙄
*******
Da kyar Sadiya ta bata hamsin aka siyo mata kati ta nufi gun network tana komarin kiran Hajiya bilki.
Wayar Adam ce ta shigo dauka tai da sauri tace “Adam an dace?Afir ta samo mana aikin?” Tai tambayar cikin zumudi.
Adam yace “wake zancen aiki rayuwata tana neman karewa an kwacemin mata?”
Mata? A gidan ubanwa kaga mata?
Zaina.....
Kaifa bakada hankali wasa wasa, wato ba neman aiki kake kazo ka daukeni ba can ka cigaba da haukarka.
Goggo Khalid ne fa ya aureta?
Waye Khalid? Inama maganar aiki kana min maganar Zainab.
Khalid fa Goggo abokina driver din nan.
Idanu ta zaro hankali a tashe tace “me?”
Nace mele🙄
******
Ayusher🏌🏻♀