Typing
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce
Assalamu alaikum, barkanku da wannan lokaci, barkanmu da sake dawowa filin daga, insha ALLAHU zan cigaba da littafin ƘWAI CIKIN ƘAYA kamar yanda na fara, inafatan haɗin kai daga gareku, haɗin kan kuwa shine tsaftataccen Comments da zai iya zaburar dani akan abinda nake rubutawa, masu ɗaukar littafi su ɗaura a youtobe wlhy wlhy na rantse duk wanda ya ɗauramin ƙwai cikin ƙaya a youtobe kar yay kuka dani akan matakin da zan ɗauka yay kuka da kansa. Masu cewa kuma na maida littafin na kuɗi kudaina yimin ƙarya, inda naso hakan da tun a 1 zance na kuɗine. Masoya kumuje zuwa, yanzu za'a fara wasan .
BOOK TWO
(1)
............Kowa yana cike da murnar dawowar aunty Shahudah a gidan amma banda ni, ba komai ya jawo hakanba kuwa sai irin tarbar dana samu daga gareta bayan dawowata aiki a randa ta dawo.
Cikin ɗokin ganinta da kewa na nufeta, amma saita kalleni cikin wani yanayi na wulaƙanci da ƙyama kamar yanda ta sabamin a baya, daga ƙarshe ta koma dariyar aikina. Hakan ba ƙaramin ciwo yayminba, musamman yanda naga harsu Mom sun biye mata suma suna tayata dariyar. Daurewa nai nima na tayasu, dan na ɗaukama kaina alƙawarin insha ALLAHU sun daina ganin raunina a yanzu. Sai da muka gama dariyar sannan na nufi ɗakina nabarsu, su Aunty Aamilah na bata labarin yanda akai nazama dss a yanzu.
Ina shiga ɗakina na faɗa saman gado na fashe da kuka, tabbas wulaƙanci bashida ƙyau sam a rayuwa, ƙasƙanci ga mutum abune mai muni, amma a wannan duniyar babu abinda mutane suke alfahari dashi kamar ƙasƙanta ɗan uwansu musulmi.
“Sai kaga mai dukiya yana ƙasƙanta talaka koda da magana ne, mai ilimi na ƙasƙanta marashi, mai mulki na ƙasƙanta mabiyansa, miji na ƙasƙanta iyalansa, ɗan uwa na ƙasƙanta na ƙasa dashi. koyaya mutum yafi wani saikaga yana hura hanci wajen ganin yayi tozarci ga wanda bai kaisaba, kaicon mutane da wannan ɗabi'a, kamanta ALLAHN daya baka shima bai manta da shiba, sannan badan ka fisaba ya baka shi ya hanashi, ikonsane wannan yabama wani ilimi yayi wani jahili, ya bama wani dukiya yayi wani talaka, ya bama wani haihuwa yayi wani babu ɗa, ya bama wani mulki yayi wani mabiyi, ya bama wani lafiya yayi wani mara lafiya, kowa a rayuwa akwai jarabawarsa, kaine wane bashike nuna kafi kowa ba, kai ka samu kaza ko kake da kaza bashike nuna ALLAH yafi sonka ba, nima ALLAH yana sona, kuma ina sake gode masa da yanda yayini aunty Shahudah.......”
Tun daga wannan ranar na sake jabaya ga kowa da komai na gidan, Dad dama bai dawoba, hakama Yah Qaseem yayi tafiya tun washe garin dawowar aunty Shahudah gidan. ko a wajen aiki bani da wata walwala, Ummie da wasu abokan aikina sai suka danganta rashin walwalar tawa da kewar Yah Qaseem da bayanan, dan zuwa yanzun mutane da yawa sun san alaƙar dake a tsakanina dashi.
Ni kuma a ɓangarena ba damuwar rashin yah Qaseem bane da lamarin gidanmu kawai kecin raina, akwai wani abu daban danaketa ƙoƙarin tureshi a raina, dan bana fatan gaskata zancen zuciyata koda da wasa kuwa.
★★★★★★★★
Yau data kasance juma'a dai-dai da dawowar aunty Shahudah da kwanaki huɗu Dad shima ya dawo, kowa yay murnar dawowarsa tamkar yanda muka saba, ya kuma samu tarba daga matarsa harma da Aunty Shahudah dake ganin wannan dawowar tatace. Nidai ina daga baya-baya dukda jana a jiki da Dad keyi, dan motsi kaɗan ya sako sunana a cikin zancensa, hakan na kula baƙaramin sosa zuciyar Aunty Shahudah ya keyi ba, hakama Mom. Dana kula abin zaiyi tsamari saina zare jikina na gudu ɗaki, dama dai muna zaune ne muna cin abincin dare.
Ban sake yunƙurin fitowaba kuwa har safiyar washe gari domin nima naji a raina yakamata na basu waje su gana da mahaifansu. duk da kasancewar asabar ce babu aiki ban iya komawa barci ba, dan narigada na saba yanzu da yanayin tashin sassafe. Ina zaune akan abin sallah tun bayan idar da sallar asubahi ban tashiba, na lazimci azkar nai karatun Qur'ani, rashin abunyi ya sakani tashi nahau gyaran ɗakina, hakan sai ya jani tsayin lokaci har kusan tara da wasu mintuna.
Sama-sama nake jiyo hayaniya kamar na kuka, kukan kuma yaymin kama da muryar Mom. Nai azamar ajiye tawul ɗin dana ɗauka zan shiga wanka na fita. Sosai gabana ya faɗi saboda cin karo da Mom dake kuka iyakar ƙarfinta, Dad na riƙeta, daƙyar na iya haɗa maganganunsu, daga ƙarshe na fahimci ƙanin Mom ɗine ALLAH yayma rasuwa mai suna Usman, tabbas naji suna yawan faɗar sunan Uncle Usman, sai dai ban sanshiba, ban taɓa ganinsaba, dan duk zamana a gidan ban taɓa zuwa gidansu mom ɗinba, bankuma cika ganin ƴan uwanta suna zuwaba, kowa dai yasan halin wasu ƴan bokon nan da aƙidar rashin son takura.
Nima dai tausayin Mom ya sakani bin sahun masu sharar hawaye, nan dai Dad ya cigaba da lallaɓata, kafin yajata sama, muma yace duk mu shirya domin tafiya can gidan. Hakanne ya saka kowa nufar ɗakinsa mu duka.
______________________________
A daren jiya juma'a misalin ƙarfe sha biyu da wasu mintuna mummunan labari ya iso gidansu Jawaad, cewar Uncle Usman ya samu haɗarin mota a hanyarsa ta dawowa daga tafiyar da yayi ta kwanaki biyu.
Lallai wannan gida sun fuskanci tashin hankali na bazata, dan bayan mahaifin Jawaad basu ƙara rasa ko ɗaya a cikinsuba, kaf ƴaƴan malam Yusif Abdul-aziz ne kawai ALLAH yayma rasuwa. Saiko shi malam Yusif ɗin da matarsa ɗaya sai mama maryam, idan ka cire waɗanan huɗun sauran duk sunada ransu, saima yaɗuwa da suka sake yi saboda haihuwar jikoki harma da tattaɓa kunne.
Ruɗanin da mama Atika ta shigane ya sakata yanke jiki ta faɗi, dan abune da tunaninsu bai taɓa kawo musuba anan kusa duk da sunsan mutuwa tabbacice ga duk mai rai, ba Uncle Usman ba ko ita kanta data tsufa sosai bata tuna mutuwar zata iya ɗaukarta a yanzu balle shi da ayanzune ake ƙara shiryama duniyar filin zama.
Lokacin da gidansu Jawaad ke cikin wannan ruɗanin shi yanacan suna gumurzu da wasu gungun ƴan ta'adda da suke fako tun kusan sati uku da suka shige, sai a yaune ALLAH ya basu nasarar yin fito na fito dasu, sun sami nasarar kama wasu a cikinsu, yayinda wasu suka gudu.
Kusan ƙarfe huɗu na dare suka iso station ɗinsu da waɗanda suka cafko, sunyi tiɓis da gajiya, ga yunwa dake cin hanjinsu ta bala'i ma kuwa, sai dai jarumtarsu da juriya mai haɗe da trianing ɗin da suka gogu a ciki duk ya ɓoye gazawarsu. Rose cema dai kawai ta kasa juriyar kasancewar ƙarfin zuciyar mace dana namiji ba ɗayaba, dukda itama ta cancanci a kirata jarumar kuwa, Jawaad ma baiso akai aikin da itaba, amma ta matsa akan sai taje, badan yasoba ya barta ta bisu.
A station ɗin suka ƙarasa kwanan, washe gari safiyar asabar ana idar da sallar asuba Jawaad ya kira gimba akan yazo ya ɗaukesa. Yanda yaji muryan gimban ne ya bashi mamaki, cikin yanayin gizagonsa yake jefa masa tambayar lafiya?.
Sanin halinsa baya son ɓoye-ɓoye a magana ya saka Gimba faɗa masa gaskiyar tashin hankalin da ake ciki a gidan nasu.
Dukda halin da yake ciki da matsalolin dangin mahaifin nasa hakan bai hanashi shiga ƙololuwar tashin hankaliba, a take ya birkicema su Jabeer, waɗanda suma jin rasuwar tai bala'in sakasu a ruɗani. Basu wani ɓata lokaciba suka nufi gidansu Jawaad ɗin kai tsaye, duk da halin gajiya da buƙatar hutun da suke a ciki. Sun iso gidan ƙarfe kusan bakwai da wasu ƴan mintuna, hankalin Jawaad ya sake tashi sosai ganin halin da ahalinsa ke a ciki, tuni ya manta da gajiyar dake tattare dashi.
Bai zaunaba su Uncle Nasir suka jashi zuwa asibitin da gawar Uncle Usman take domin su amso, abinda yasa ba'aje tun jiyaba saboda ba'a nan cikin gari bane, inda ya baro yafi kusa da inda yay haɗarin, shiyyasa aka maidashi asibitin can garin.
★★★★★★★
Ƙarfe goma da wasu mintuna muka iso gidansu Mom, katafaren gida na alfarma da ƙawa, dukda cikin tashin hankalin mutuwa mukazo hakan bai hanani mamaki da jinjina dukiya irinta wannan ahaliba, lallai dolene su aunty Shahudah suyi wulaƙanci yanda sukeso, kaga gida tamkar ba hannune ya ginashiba, harabar gidan kawai naganimafa kenan, sai mutanen gidan da zakaima kallo ɗaya ka fahinci ƴan bokone na haƙiƙa tun zamanin da boko keda tsada da daraja kuwa......
Ina cikin wannan tunanin ne nafara jiyo ƙarfin koke-koke na ƙaruwa, babu shiri na dawo hayyacina, a sannanne na lura ashe an iso da gawar mamacinne.
Har ciki sosai Ambulance ɗin dake ɗauke da gawar ta shigo, ta tsaya dai-dai sashen danaji wasu na ambata da sashen mama Atika mahaifiyarsu Mom. Zuciyata tai masifar harbawa saboda ganin wanda ya fito daga Ambulance ɗin.
Cikin tsagwaron mamaki na furta “Boss kuma anan?” akan laɓɓana, kamar yanda nakejin zuciyata aduk sanda ta samu kusanci dashi yanzunma bata canja zaniba, dole na shiga karanto addu'a gudun kar nayi abinda zai jawo hankalin mutane a kaina.
Nayi nisa a tunanin da har aka fidda gawar ban saniba, saida suna gab da shiga sashin ne nakai idanuna kansu tare da sauraren koke-koken mutane, su biyune kawai ke ɗauke da gawar a mankara, tana lulluɓe da farin ƙyalle da yay face-face da jini, alamar dai mamacin ya bugu sakamakon Accident ɗin da yayi, nantake sai zuciyata tai rauni saboda tunowa da mutuwar nawa mahaifin, sai kawai na durƙushe a wajen na fashe da kuka mai cin rai da zuciya.
Isowar gawarce ta saka gidan ya kuma cika sosai, koke-koken da akeyi ya sake ƙaruwa, ban kuma ganinsaba kuma har aka sake fitowa da gawar kusan sha biyu na safe, da alama dai yanzu an masa sutura za'a miƙashi gidansa na gaskiyane. Wani da nake ƙyautata zaton ɗansane ya rugo da gudu ya riƙe mankarar da aka ɗakko yana kuka da roƙon su ajiye masa Dadynsa, yarone da bazai gaza shekaru sha uku ba a duniya, sai ƴanmata guda biyu da zasu iya kawai 23 da 20 suma sukazo suka riƙe. Hakan ya kuma tada hankalin jama'a, ni kaina sunyi masifar bani tausayi, suma kenan da suke da gatan dangi dana jin daɗin rayuwa, na tuna sanda baba ya tafi ya barni, har aka binnesa ma ni bansan ina nawa hankalin ya keba.
Na share ƙwallar dake gudu bisa kumatuna, dai-dai isowarsa, wajen da alama yanzune ya fito, shine ya janye yaron ya rungumesa a jikinsa yana bubbuga bayansa, hakan ya saka ƴan matanma sakin mankarar suka durƙushe a wajen suna kuka. Bai saki yaronba har saida aka fita da gawar, ya shafa kansa yana ɗago fuskarsa, babu wanda yasan miya faɗama yaron, amma kowa ya kula magana yay masa kafin ya sakesa ya fice shima zuwa waje inda za'a sallacesa.
Tashin hankalin da ake cikine yasa ban samu damar tunanin alaƙar gidan da boss ba sam, bankuma sake ganinsaba, sai dai ganin nasa da nayi yana nan daram a zuciyata, dan kwanaki kusan shida kenan ban gansaba ko'a office, tun fitar da sukai ranar sai yaune na ganshi. A mamakina sai naji raina sakayau, bakamar yanda na tsinci kaina cikin ƙunci ba a kwanakinan.
★★★★★★
Tun bayan zuwanmu gidan ban sake sanya ƴan gidanmu a idonaba, har zuwa yanzu da aketa hada-hadar sallar azhar da cin abinci, garama dad bayan sun dawo daga binne gawar ya shigo cikin gidan shi da wasu manyan mutane sunyi gaisuwa, daga haka ban sake saka ko ɗaya a cikinsu a idanunaba.
Mutane nata shiga sassan gidan domin gabatar da salla, sai dai ni narasa ina zan dosa koda na tashi, waɗanda nazo dominsu ban sake ganinsuba, ina zan shiga nikan nace zanyi salla? Tunda babu wanda ya sanni babu kuma wanda na sani.
Ina nan zaune ina saƙa mai fishsheni a zuciya budurwar dake zaune a kusa dani ta miƙomin jakkarta da waya akan na riƙe mata tana zuwa, kamar zanyi magana sai kuma na amsa ina maida mata murtanin murmushin da takemin, ina zaune a wajen ban motsaba nai uban tagumi harta dawo.
Na miƙa mata kayanta, ta amsa tana min godiya, harta tafi sai kuma ta dawo da baya idonta a kaina.
“Ƴar uwa kozaki taso muje muyi sallane? Naga kowa na harama amma ke koma motsi bakiyba, ko dai kina hutune?”.
Murmushin yaƙe naimata, sai dai ban motsaba, nace, “Karki damu zan nema waɗanda mukazo tare sai nayi a wajensu”.
Tai ɗan shiru tana kallona, kamar bazata tankaba, dan harna fara murnar ta barni, sai na tsinkayi muryarta tana faɗin, “Yanda mutane ke cike a gidannan kafin ki ganosun ai kin wahala, sannan duk inda zakiy salla a gidannan yau bazai kai nutsuwar inda zamujeba, dan sashen yaya ne kawai nasan babu mutane, indai ba kina tsoron karna saidaki bane”.
Ta bani dariya, amma sai banyiba saboda yanayin da ake ciki, sai kawai na miƙe batare danace komaiba, dan na lura akwaita da surutu.
Tun shigowarmu sashen na yarda da zancenta, dankuwa tsit yake babu wata hayaniya anan, tamjar ba cikin gidan yakeba. Sai wani daddaɗan ƙamshi daya shige mini hanci, batare dana shiryaba na shaƙa na haɗiyeshi cikin maƙoshina, karon farko a rayuwata da naga falon da yafi na gidan Dad ƙyau da tsari, ada tunanina yana bani babu gidan da yakai na Dad haɗuwa da tsaruwar kayan alatu, dan dukkan gidajen iyayen su Ummie basu kai na Dad ba, amma a yau dana tsinci kaina cikin wannan aljannar duniyar duk sai na raina wancan alfaharin nawa, yanda aka ƙawata matattakalar benen dake falon kawai abar kalloce ga mai kallo duk wayewarsa kuwa. Ban gama bama idona abinciba budurwar taja hannuna zuwa wani ɗaki, mun iske mutum uku suna salla, sai ɗaya data fito daga bayi da alama alwalar itama tayo, sai wata kwance a kan gadon dake ɗakin da yara biyu suna kallon waya. Duk suka zubomin ido na rashin sani, wadda ta fito daga bayice tace, “Wai ina kikajene haka Nabeelah? an aika Ammar ya kiraki amma yace bai gankiba”.
Hannuna ta saki tana saɓule jakkarta dake a kafaɗa, “Babu inda najefa Aunty Hanifah, ina can jikin sashen Uncle Sulaiman zaune, nima yanzu saida na leƙo naga kuna nan sannan ai na taho”.
Batace mata komaiba, hakanne ya sakani gaisheta dan naga babbace ta girmeni, na juya ga wadda ke a saman gadon tare da yara itama zan gaisheta sai tai saurin gaisheni. Murmushi kawai nayi, dan ita zan iya girmarta, suma yaran sai suka gaidani, na amsa musu da kulawa ina tambayar sunayensu. Namijin yace Ammar, macen kuma Islam. Yaran sun birgeni, gasu masu ƙyau. Wadda muka shigo tare da aka kira da Nabeelah ce tace min na shiga bayin nayo alwala, cikin tsokana take faɗin “Karnayi abin kunya gashi bansan sunan ƙawar tawabama”.
Ƴar dariya nai babu shiri, ina ƙoƙarin shigewa nace mata sunana Bilkisu. A tare naga duk sun kalleni suna ɗora hannu a bakunansu, hakama biyu a masu sallar da suka idar suma suka juyo suna kallona. Yanda naɗanyi diri-diri na alamar shakkune ya saka ɗaya a cikin waɗanda suka idar da sallar babbar mace tai murmushi da cewa “Mai babban sunace ashe”. Numfashi na sauke a hankali kafin na gaisheta cikin risinawa, ta amsamin tana sake faɗaɗa dara'ar fuskarta, kafin tace naje nai alwalar kar lokaci ya ƙure. Shigewa nayi bayin nima da tunanin ko sunan waye nasu Bilkisun? Daga gani kam dai suna girmama mai sunan sosai.
Ina fitowa Nabeelah ta shiga, suma duk sun tashi daga abin sallar alamar sun bamu waje, sai wadda muka iske tayo alwala kawaice ke salla a wajen, na gaida sauran biyun da bamu gaisaba suma sannan na kabbara sallata.
Bayan mun idar da sallar a cikinsu babu wanda ya tambayeni game dani, sai dai sunata ƙoƙarin sakoni cikin hirarsu wadda duk ta karkata ga mai irin sunana danaji manyan na ambata da Yaya Bilki, yaran kuma na kiranta Mah-mah Yanda suke hira akanta cikin damuwa da kewane ya sakani tunanin ko bata da raine? Bani da mai bani wannan amsar, dan haka na haɗiye abina cikin rai ina cigaba da saurarensu....
Kusan mintuna talatin ina sauraren hirarsu mai cike da birgewar kasancewarsu ahali ɗaya, kafin na miƙe domin tafiya, dan ya kamata naje na binciki inda su Mom suke koda su basu damu da nemanaba.
Duk kallona sukai cike da alamar tambaya.
Murmushi nayi, nace, “Zanjene kar abokan tafiyata suyita nemana”.
Suma duk murmushin sukaimin, Nabeelah ta miƙomin wayarta tana faɗin, “To sakamin Number ki muke zuminci, danni dai nayi ƙawa daga yau”. Ban musaba na amsa wayar tata fuskata har lokacin da murmushi, na saka mata Number ta ina miƙa mata wayar, wadda naji suna kira Aunty Batool tace, “Lallai kin jajubarma kanki kuma Ummien mu, dan shegen surutun Nabeelah takai a guji ƙawance da ita, gaki keman daga gani bakida yawan magana”.
Sanin dani take yasani faɗin, “Aunty ai sunfi daɗin ƙawance irinsu Nabeelah”.
Atake kowa ya shiga faɗin a'a-a'a, yayinda Nabeelah keta ƙoƙarin kare kanta, niko ina musu dariya. Godiya na sake musu kafin nai musu sallama.
Zuciyata tai wani irin harbawa lokacin da akai knocking ƙofar ɗakin tare da sallama cikin wata irin sassanyar murya dake nuna mai ita yana a matuƙar gajiye, tattare da tsagwaron damuwa. Akusan tare suka amsa, nikuma na janye hannuna dana ɗora akan mariƙin ƙofar cike da fargaba, ban gama tattara fahimtata waje gudaba aka turo ƙofar aka shigo, kaɗan ya rage ya bugeni, nai saurin ja baya kaɗan dan na bashi hanya sosai.
Idanunane suka fara sauka akan ƙyaƙyƙyawar ƙafar da baƙin wandon jeans ya sake haskawa, jijjigar da zuciyata keyine ya dasamin tsoron yarda da hasashena, dan haka na kasa ɗago idona naga wanene? Dukda ƙamshin turarensa ya nema saka zuciyata faso ƙirjina ta fito......
Ganin yaƙi shigewa ya bani hanyane ya sakani ɗago idanuna a hankali nakai dubana gareshi, a lokaci ɗaya idanunmu suka shige na juna saboda shima dai-dai ya kalleni. Naɗan sake ja da baya na alamun mamakin sake ganinsa anan, amma shi a mamakina sai naga ya janye nasa idanun babu wani alamar mamakin ganina da ya nuna.
Yanda naji su Nabeelah na rige-rigen gaishesane ya sakani aro jarumta nima nabi layinsu na gaidashi, sau ɗaya ya amsa mana tare da amsa ta'azziyar da mukai masa ya ƙarasa ga iyayensu Nabeelah, hakanne ni kuma ya bani damar saurin ficewa cike da sassarfa daga ɗakin..........
ALLAH ka gafartama iyayenmu .
4 hrs · Public
Save · More
36
Bilqeesa Ibraheem Bilyn Abdull Ce:
Alhmdllh inama kowa fatan alkairi, nakumaji daɗin wannan tarba, naso ace zan iya jurewa na biku ɗai-ɗai na amsama kowa Comments ɗinsa, sai dai nace kuyi haƙuri, kamar yanda matsalan ido ta dakatar dani da typing dolene yanzuma na ringa lallaɓawa saboda kunada ɗunbin yawa, akwai group insha ALLAHU da aka buɗe a shafin manhajar Telegram, masu amfani da wannan shafi su maza su garzaya idan suna buƙata, domin canne zai zama dandalin tattaunawa akan littfin ƙwai cikin ƙaya da sada zuminci, duk mai karatu yana buƙatar dandali na tattaunawa akan littafi, dan da yawanmu hakan na bamu nishaɗi da sake fahimtar da mu abinda bamu fahimtaba, kuma yana ƙarama writer ƙarfin gwiwar typing koda batai niyyar hakanba, ku maza kar a baku labari. Zakuna samuna koda yaushe a can domin ku tabbatar ina tare daku, masoyan bily kuma na isar da saƙonku gareta akan ta daina tsoron jay😂, masoyan Shahudah tana miƙo muku gaisuwa itama🤓.
https://t.me/joinchat/TIsXYRvhtri2kQ9E4x7w6g
Wannan shine link ɗin group namu mai suna MASARAUTAR BILYN ABDULL A manhajar Telegram😘😘.
2
..............Koda na fito daga ɗakin saida na huta a falon saboda yanda zuciyata ke mutsu-mutsu a cikin ƙirjina, ina matuƙar mamakin wannan al'amari dake yawan faruwa tsakanina da mutumin nan, na kuma rasa wazan tunkara da maganar halin da nake tsintar kaina akansa kozan samu fashin baƙin saɓanin wanda zuciyata ke kissima min, nidai nasan ba tsoronsa nakeba, to minene dalili? Wannan amsar nake neman mai bani.
Gwiwa a sage naja ƙafafuna na fice daga sashen zuwa harabar gidan. Yanzunma dai ban sami ko ɗaya daga cikin su aunty Aamilah ba, gashi banida Number kowa a cikinsu. Dole na sake nemar guri na zauna inda babu yawan hayaniyar mutane, sai jefi-jefi nakan ɗanga sun gittani.
★★★★★
Yanda Jawaad ya nuna halin ko in kula da ganin na Bilkisu bazaka taɓa tunanin yama santaba, sai dai harta fice daga ɗakin yana kallontane ta wutsiyar ido, acan ƙasan zuciyarsa na raya masa “Ita kuma miya kawota nan?” sai dai a fili bazaka taɓa fahimtar komaiba.
Zama yay a saman ƴar dirowar dake farkon shigowa ɗakin, cikin girmamawa ya gaisa da iyayensa, sukai masa gaisuwar ta'aziyyah tare da jero addu'ar neman gafara ga mamacin, har suka cigaba da ɗan tattaunawa akan rasuwar wadda ta jasu tunowa da rasuwar mahaifin Jawaad ɗin shima da ɓatan mahaifiyarsa.
Haɗiyar zuciya kawai Jawaad yake famanyi, amma bakinsa ya kasa furta komai, daga ƙarshema saiya miƙe yana faɗa musu zaije ya ɗan kwanta, gimba zai kawo musu abincin da zasu ci.
Basu hanashi tafiyaba, dan yanayinsa ya nuna yana buƙatar hutun sosai.
★..::..★
Sai kusan ƙarfe biyar na hangi Mom suna gaisawa da wasu gungun baƙi da sukazo musu gaisuwa, da sauri na miƙe na nufeta karta sake ɓacemin, dan matuƙar gajiya na gaji da zaman ni kaɗai, danma naɗanyi cheating dasu Rebecca ne a group ɗin da muka buɗe iya mu biyar kawai na rage kaɗaici. Daga gefe na tsaya harta gama gaisuwa da mutanen suka tafi kafin na ƙaraso gareta, gaidata na farayi a ɗarare, tunda nasan bani da wata fawa a gareta, amma a mamakina sai naji ta amsa harda tambayata ina na shiga tun ɗazun bata ganniba? wani sanyi ya ratsa zuciyata, kasancewata marainiya ina matuƙar buƙatar kulawar mahaifiya koda kaɗanne, rashin samu kuma na sakani a ƙunci sosai, sai dai ina ƙoƙarin shanyewa ba kowa ke fahimtar hakanba. Cikin girmamawa na bata amsar tambayarta, saita bani umarni akan muje ciki naci abinci.
Ban sake sakashi a idonaba har zuwa dare bayan sallar isha'i da muka fito domin tafiya gida, ƙiri da muzu Aamilah da aunty Shahudah suketa ƙoƙarin zamewa haɗa tafiya dani, duk da basu fito fili sun faɗaba na fahimci haka da kaina, dan kafin nagama kimtsawa harsun fice daga sashen na Mama Atika, sai tare muka fito da Mom, sai muka iske harsun tafi wai tare da Yah Salman.
Banji haushiba, saima murmushi da nayi kawai, driver ne zai tafi da Mom, dan haka nima su zanbi dole. Mom ta tsaya gaisuwa da wasu mata da suma zasu tafi, ƴan gayune sosai da kallo ɗaya zakai musu ka fahimci naira ta zauna musu, nidai bayan na gaishesu jikin mota na koma na
jingina kawai ina kallonsu da mamakin yanda naga Mom ta sake dasu sosai, yanda na santa da wulaƙanci, koda yake masu iya magana kance wata gaban tafi gaban raini ai.
Zuciyata ta motsa da ƙarfi a cikin ƙirjina, hakan ya saka tsoro ziyartar raina, koban faɗaba nasan hakan na nufin Dodona ya kusanto wajen koma yana wajen, zuwa yanzu nafara sabawa da wannan SABON AL'AMARIN namu.
Ilai kuwa ina ɗago idanu akansa na sauke, tsaye yake ɗan nesa damu kaɗan, hannunsa ɗaya cikin aljihun wando, ɗayan kuma ya riƙe waya dake kunnensa, wadda ke nuna alamar yana magana da wanine, ɗan taku yake ɗaya biyu cike da nutsuwa da cikar haiba, ba kayan ɗazun bane a jikinsa, daga wando har rigar jikinsa na yanzu duk fararene tas, gefe wando na duka ƙafar biyu akwai ratsin dogon zare jaa daga sama har ƙasa, sai agaban rigar shima anyi rubutu da ja, hasken dake ƙwanyar a tsakar gidanne ya sani ganin abinda aka rubuta, sai silifas fari shima, sosai kayan sukai masa ƙyau, har na iya kasa janye idona a kansa dukda wutsilniyar da zuciyata keyi kuwa.
Haka kawai Jawaad dake waya da Jabeer yaji a jikinsa kallonsa akeyi, kallon kuma irinna wanda keda kaifin gani da baiwar ƙarfin kwarjinin idanu, duk yanda yaso basarwa tamkar yanda ya saba hakan sai ya gagara, dole ya fara wulƙita nasa fararen idanun kozai samu nasarar cafko wannan mayen idon dake neman saukar masa da gajiya. Karaf kuwa idanunsa suka sauka akanta, shima ƙirjinsa ya motsa alamar harbawar zuciyarsa. Tabbas yaji a ransa itace ke kallonsa, amma a mamakinsa sam idanunta da hankalinta basa kansa, karon farko da miskilancin yarinyarnan ya motsa zuciyarsa, tun ganinsa da ita na farko a airport ya fahimci miskilace ta bugawa a jarida, kasancewar ALLAH ya azurtashi da ilimin karantar hallayyar ɗan adam cikin lokaci ƙanƙani, zuwa yanzu mamakin ganinta yabar ransa, dan ya kula akwai alaƙa tsakaninta da Qaseem.......
“Hello...hello...” Da Jabeer keta ambatane ya sakashi dawowa hayyacinsa, dan tuni ya saki wayar da suke ya kama sabgar bilkisu, abinda bayayi sam a rayuwarsa (wato shiga abinda bai shafesa ba), yaja siririn tsaki yana murza goshinsa da hannunsa daya ciro daga cikin aljihu.
Dai-dai lokacin da Bilkisu ta buɗe gaban mota ta shiga ta zauna, dan Mom harta shige baya itama.
Wani irin harɗaɗɗen numfashi ya sauke har Jabeer na tambayarsa “ko lafiya?”.
Gutun tsaki yaja yana yanke wayar batare daya bashi amsaba, yakuma jan wani tsakin har sau biyu yana takaicin kansa da shiga hurumin da ba nasaba.
___________________________
Washe gari ban biyosuba, dan inama barci suka fice, babu wanda yace a tasoni, nima koda na tashi kuku ke sanarmin sun tafi banji komaiba a raina saima daɗi, tunda nasan zuwana bazai ƙara komaiba koya hana, hasalima banason gamuwa da Dodona.
Bayan na karya ɗaki na koma nai wanka, nai shiri cikin doguwar riga ta atanfa data samu zaunannen ɗinki, bawata kwalliya naiba, nasaka turare sama-sama na fito bayan na yafa ƙarmin gyale.
Kai tsaye gate na nufa wajen baba maigadi dake zaune shida mai bayin filawar gidan suna hira, suna ganina suka shiga gaisheni cikin girmamawa, sam banason hakan da sukemin, dan kuwa niba kowa bace a gidan face maicin alfarma, sannan duk sun girmeni, baba maigadi ma a haife ya haifeni, shima mai bayin fulawar kobai haifi kamata ba nasan yanada manyan ƴaƴa.....
“Hajiya fita zakiyine?”.
Baba mai gadi ya katsemin tunanina, kaina na girgiza masa ina murmushi. “A'a baba ba fita zanyiba, hasalima wajenka nazo muyi magana idan ban takura makaba dan ALLAH”.
Da sauri yace, “Haba wace takura kuma” yay maganar yana miƙewa da sauri, babu jimawa sai gashi da farar kujera, ajiyemin yay gefensu alamar na zauna, mai bayin fulawa kuwa yay mana sallama akan zaije gida yakai cefane.
Sake gaisawa mukai da baba maigadi, yay min ta'aziyyar rasuwar da akayi, nako amsa masa tare da tambayar lafiyar iyalansa, bayan amsamin da yay muka ɗanyi shiru, tunani nake ta ina zan fara abinda ya kawoni garesa?. Zuwa wasu ƴan mintuna sai dabara ta faɗomin, nai murmushi ina sake maida hankalina ga
reshi da kunna voice recorder dan na samu damar kwashe dukkan abinda zamu tattauna nayi nazari a tsanake a kansu.
“Uhm... Baba dan ALLAH niko wata tambayace dani?”.
Fuskarsa faɗaɗe da murmushi yace, “ALLAH Yasa na sani hajiya”.
Murmushi naɗan masa, nace, “Insha ALLAHU inada tabbacin kama sani ɗin”.
Baice komaiba sai hankalinsa daya maido kaina baki ɗaya, nima sai na sake nutsuwa sosai.
“Baba dan ALLAH ko zaka iya tuna ranar da abinnan ya faru da Amina a gidannan da wanda ba'asan ko waneneba?”.
A bazata maganar tazo masa, dan haka kawai saiya hau tari babu shiri. A rikice na shiga masa sannu, na jawo ruwan dana fito dashi daga ciki na miƙa masa da sauri bayan na ɓalle murfin, amsa yay har hannunsa na rawa ya kafa goran a baki ya ɓaɓɓaka, saida yasha kusan rabi kafin ya sauke, idanunsa harsun kaɗa sunyi jajur, sai naji tausayinsa ya kamani, koda ya dawo dai-dai shiru nai ban sake masa tambayarba har tsawon wasu mintuna.
Na sake jeho masa tambayar a karo na biyu, yanzunkam a mamakinawa shiru yay bai tanka minba, sai dai yanata ƴan kalle-kalle tamkar mai tsoron a ganmu ko wani ya jimu. Jin bashi da niyyar bani amsa ya sakani kallonsa, a karo na uku na sake maimaita masa tambayar da sigar kwantar da kai.........
“Ɗi!! Ɗi!!! Ɗi!!...” mukaji horn ɗin mota daga waje, hakanne ya sakashi tashi da sauri ya nufi gate ɗin, na tabbatar dama hanyar da zai gudu yake nema, sai kawai na samu kaina da ƙura masa idanu ganin yanda har yanzu jikinsa ke mazarin rawa.
Hancin motar Dad ne ya danno kai cikin gidan, na sauke ajiyar zuciya ina miƙewa tsaye, saboda tsayawar da driver yayi a saitin da nake zaune, shi kuma Dad ya sauke glass ɗin ɓangarensa yana mani murmushi.
Nima murmushin nake masa ina miƙewa na nufesa, da hannu yaymin nuni nazo, dole nabi motar da direba yaja zuwa ciki inda zaiyi fakin.
Tare da Dad muka shige cikin falo yana tambayata miyyasa banbi su Mom ba can gida?, cikin girmamawa na bashi amsa akan sun wucene ina barci lokacin. Nayi zaton zaiyi faɗa, amma sai naji kawai yay ƙaramar dariya. Mun yada zango a falon ƙasa, ya bani Umarnin naje nasa kuku ya haɗa masa abinci mara nauyi yunwa ya keji, ya fita bai karyabane.
Koda naje kicin ɗin sai ban fitoba na zauna mukayi abu mai sauƙi wa Dad ɗin ni da kuku, dan zuwa yanzunkam Alhmdllh hannuna yay masifar faɗawa akan girki kala-kala na zamani, na gargajiya kuwa dama bani da matsala a kansa, innata tarigada tayi min wannan horon tun ban gama fahimtar muhimmancin girki ga ɗiya mace ba.
Bayan mun kammala nice da kaina na kawoma Dad, lokacin yana waya, na ɗora tiren bisa tebir ɗin tsakkiyar falon na jasa gabansa, buɗe masa komai nayi tare da tsiyaya masa ruwa a kofi sannan na koma gefe na zauna, a haka ya faracin abincin yana cigaba da wayarsa data jashi tsayin lokaci, sai yazam yanacin abincinne kawai a shiririce. Dan harya kammala wayar baici ko kashi ɗayaba bisa uku, ya ajiye wayar yana maido hankalinsa gareni, “Taso muci mana ɗiyata”.
“Lah Dad nakane, ni ban daɗema da karyawaba fa”.
Cike da kulawa yacemin, “Da gaske?”.
Na langaɓe kai gefe ina ɗagawa alamar eh. Murmushi yayi ya cigaba dacin abincinasa yana mani hirar data bani mamaki, dan kuwa akan kasuwancinsane ya ɗakkomin hira, yana faɗamin alkairi da kullum kamfaninsa ke samu da yanda kuɗaɗe ke shigo masa babu ƙaƙƙautawa. Banda masha ALLAH da ALLAH ya ƙara sanya albarka babu abinda nake iya cewa, danni kam dai ban fahimci dalilin mani labarinba, tunda a ganina ai sirrinsane wannan, ko a cikin ƴaƴa kuwa a ganina sai wanda ka aminta da amanarsa.
Kamar kuwa ya karanci mike raina, sai cewa yay, “Kinji inata baki labarin abinda bai shafekiba ko?”.
Murmushin yaƙe naɗanyi ina gyaɗa kaina, shima ya murmusa yana mai kai cokalin romon farfesun daya ɗobo a bakinsa.
“Karkiji komai a ranki Bilkisu, na yarda da kene kawai shiyyasa, dan na fahimci keɗin yarinyace mai hankali da tarin nutsuwa, sannan sam baki da yawan surutu, waɗanan halayyar taki na ƙaramin ƙaunarki sosai”.
Murmushi yanzunkam nayi har haƙorana na bayyana
, nace, “Nagode Daddy”.
Ƙaramar dariya yay yana miƙewa bayan ya ajiye kofin da yasha ruwa, “Kinga bara naje naɗan kwanta na huta, zuwa yamma saimu tafi gidan rasuwar muma”.
Kaina na jinjina masa kawai, dan nima tuni nake buƙatar keɓancewa, inason yin nazari akan halinda mai gadi ya shiga akan tambayar danai masa ɗazun kafin zuwansu Dad daya gaza amsa mani.
Koda Yammar bamuje ko inaba, dan banga Dad ba sai bayan la'asar lokacin da yah Salim ke dawowa gidan. Harare-hararen da yaketayine ya sakani tashi na barmusu falon na koma ɗaki.
★..★...:::::...★..★
Washe gari litinin kowa yasan tushen aiki, hakanne ya sakani shiri tun a farar safiya, lokacin dana fito babu wanda ya fito a mutanen gidan, tea kawai nasha driver ya ɗaukeni zuwa station ɗinmu kamar yanda a yanzu da Yah Qaseem bayanan kullum shine ke kaini.
Nayi mamakin rashin ganinsa yauma a office, bayan nasan ya dawo, daga baya sai nayi tunanin kodan dai rasuwarcan ne da bansan minene alaƙarsa da mamacinba, dan har yanzu ina mamakin ganinsa a gidan su Mom ɗin, dukda wani sashe na zuciyata na rayamin shima ɗan uwansune ƙila sunje gaisuwane.
Daga haka ban daɗaba ban ragaba har lokacin tashi yayi muka tashi.
Tare muka tafi a motar Ummie, dan ita Dadyn ta ya bata mota ƴar ƙarama tun fara aikinmu, tun tafiyar Yah Qaseem sai yazam direba na kawoni da safe, ita kuma mutafi tare idan mun tashi sai ta ajiyeni gida ta wuce nasu gidan.
Kiran da Nazifa tai minne a waya muke amsawa tare da Ummie dake tuƙi, dan a amsa kuwwa (Hans free)na saka wayar yanda itama zataji, munzo dai-dai shataletalen (roundabout) ɗin da zamu ɗauki hanyar gida danja (traffic light) ta tsaidamu, sai kwasar dariyar labarin da Nazifa ke bamu mukeyi.
Kusan minti goma muna a haka, saina fahimci sam motocin basa motsawa ma, buɗe motar nai na leƙa, hayaniyar mutane sosai ke tashi, dan motocin dake tahowa a dukkannin titinan huɗune suka cure waje guda, watama ta mugun bugama wata, sun saka jami'i mai bada hannu a tsakkiya sunata zabga masa masifa. Mamaki ya sake kamani, nadai dawo na zauna, mun cigaba da hira kusan ta minti ɗaya nadai sake jin abin bai zaunamin a raiba, dan wannan go slow ɗin yafi kama da wanda aka haɗa da gangan, gashi motoci sai sake taruwa sukeyi titin na sake cinkushewa. Ummie na bama Nazifa amsa ni kuma na maida kallona ga mirror ɗin waje, har yanzu dai babu alamar motsin motocin a dukkanin titinan huɗu da suka raba kansu, sai naɗan kalli Ummie ina yamutsa fuska, dan na lura har yanzu ita bama ta fahimci halin da ake cikiba.
“Ummie akwai matsalafa, tabbas wannan cinkosan haɗashi akayi akan sani”.
Da sauri ta katse wayar tana cema Nazifa muna zuwa.
Kashe motar tai duk muka fita a hanzarce, tabbas an haɗashine da gayya, hakkanne ya sakamu fara ƴan dube-dube muna kutsawa tsakanin motoci domin san isa ainahin wajen da danjar take.
Gaba ɗaya wajen ya hargitse, sai hayaniya ke sake tashi, duk yanda mai bada hannun keson dai-daita komai hakan ya gagara, ga waɗanda motarsu ta gogi junama sun fara faɗa na shirin danbe. babu yanda za'ai muyi magana muma wani ya sauraremu, dan abin yafi karfinmu.
Kalle-kalle na maida hankalina wajenyi sosai kozan samo bakin zaren,
Idona ya kasa barin wata baƙar mota mai baƙin gilashi {tinted glass}, na wuceta yafi sau uku ina sake dawowa gareta, dan sai buga azababben horn mai motar yake nason a bashi hanya ya wuce tamkar shi kaɗaine yafi kowa buƙatar titin kosan tafiya.
Glass ɗin na ƙwanƙwasa, dan na tabbata koma wanene a ciki shi yana kallon na waje ai, ba'a saukeba na sake bugawa, dan haka kawai nakejin wata irin jarumta da ƙarfin zuciya da bansan daga ina tazo minba........
A fusace aka bugo mirfin motar ya bugeni, kafin na dawo daga jin zafin da nayi kawai naji ƙarar harbin bindiga har sau biyu.
Take wajen ya hargitse da ihu, nima na toshe kunnena ina mai duƙewa ƙasa, mutane sai fita suke daga mota suna gudu, masu dabara kuma na kwanciya a ƙasa, tuni jama'ar dasuka taru suna hayaniya kowa ya kama gabansa, wasu sai son jan ababen hawansu baya suke suna k
omawa da baya-baya domin ƙoƙarin barin wajen.
Cikin tunanin da yazomin daga UBANGIJINA ya sani fahimtar akwai matsala.
Murfin motar da bai gama buɗuwaba aka ziro hannu ahaka aka ƙara wani harbin na kalla, da ƙafa na turashi ya bigi motar, hakan yasaka hannun da yay harbin ya matse sosai, ƙara ya saki yana sakin bindigar itama ta faɗi ƙasa.
Jan motar sukai da wani irin ƙarfi, dukda motsocin dake gabansu bila adadin, tuni wajen ya sake ruɗewa, jikake garraaam!! Kaccaam!! Na haɗewar motoci, wata na bugar wata, gilasai sai fashewa suke famanyi, waɗanda suke a motocin basu fitaba sunata ihu na firgita.
Saura kaɗan su takemin ƙafa, nai azamar sunkuyawa na ɗauki bindigarsa data faɗi, banyi zato ko tsammanin zan iya abinda nake yunƙuriba, amma cikin amincin UBANGIJI koda na harba sai harsashin ya sauka akan tayar motar ta baya.
Tangal-tangal motar ta fara, hakan kuma ya sake hargitse wajen da ihun mutane. Kuma harbin ɗayar tayar nayi, hakan ya saka motocin dake gefenta, sukuma suka bigi fitilar dake a tsakkiyar titi ta tsaya cak.
Gaba ɗayansu suka fito kuma lokaci ɗaya, dukansu sanye cikin baƙaƙen kaya, gaba ɗayansu bindigace a hannayensu, hatta da wanda na bugama hannu da ƙofa na ɗauka tashi yana tare da wata, hannunsa dana buga sai faman jale-jale yake tabbacin na jimasa ciwo.......
Da ƙarfi naji an fisgi hannuna, dai-dai shigar ihun Ummie cikin kunnena tana faɗin “Bily!!! harsashi!!”..................✍🏻
Typing📲
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce🤙🏻
BOOK TWO
Page 3
...............Shuuuu yazo ya wuce sai jikin glass ɗin wata motar bus.
Saurin kallon wanda ke riƙe da hannuna nayi, gabana yay masifar faɗuwa saboda cin karo da nai da fuskar da ban taɓa tunanin gani a wajenba ko tsammani, ya sake fisgar min hannu muka duƙe bayan wata mota saboda tahowar wasu harsasan huɗu kanmu.
Cikin matuƙar fusata ya girgizamin hannu yana faɗin, “K shashasha ki dawo hankalinki!!”.
Yanda yay maganar da wata firgitacciyar muryace ta dawo dani duniyar mutane, amma hatta da kunnuwana da sun doɗe baki ɗaya ko ƙarar harbin banaji.
Ya jefamin wata bindigar a jiki, cikin zafin nama na cafeta.
Sosai Jawaad yaji mamakin salon na bilkisu, sai dai babu wannan lokacin a garesa yanzun, dan haka ya maida hankalinsa akan abinda ke gabasu.
Wajen ya sake hargitsewa da musayar wutar harbe-harbe, kowa burinsa ya kare kansa, mutane kam bamuda tabbacin halin da suke ciki a yanzu.
Bazan iya tantance muku halin dana tsinci kainaba a ciki a wannan lokacin, amma ni kaina nasan na zama jaruma mai ban al'ajabi..
Kowa ya jigatu a wajennan. Bagamu jami'an tsaronba baga ƴan ta'addaba, balle kuma jama'ar gari da suka fimu shiga ruɗani da tashin hankali. Sai dai abin farin cikin shine mutum biyune suka haɗu da tsautsayin harbi a farar hula, ɗaya a ƙafa ɗaya a hannu, amma Alhmdllh babu wanda ya rasa ransa sai a cikin ƴan ta'addar da aka harba a ƙirji. Mun sami nasarar cafkesu baki ɗaya, su biyarne, ɗaya ya mutu, ɗaya naji masa ciwo a hannu, sai raunika da sauran suka samu da wasu a cikinmu harda ni da gilashin wata mota ya yanka a hannu.
Wannan shine karon farko dana taɓajin mummunan rauni makamancin haka a rayuwata, sai dai lokacin dana jisa ruɗani baisa na maida hankaliba dukda inajin wani masifaffen zafi da raɗaɗi na ratsani, a cikin ƴan uwana kuma babu wanda ya lura sai da ƙura ta lafa, zuwa sannan na zubar da jini sosai, harma takai ina ganin jiri a idanuna, dama gashi inajin yunwa sosai. Rose da hankalinta ya fara kaiwa kainace ta iso gareni da hanzari, dan tuni hayaniyar mutane data ababen hawa data cika wajen ta fara yima kunnuwana nisa, duhu ya fara mamaye idanuna, hakama numfashina sai tattarewa yake waje guda yana dunƙulewa a cikin ƙirjina, abinda kawai zan iya tunawa shine taroni da tai na faɗa jikinta, daga haka ban sake fahimtar komaiba daga duniyar mutane.
★★..::..★..::..★..::..★★
A hankali nake buɗe idanuna da sukaimin masifar nauyi, naɗan motsa kaɗan ina cije leɓe kafin na samu nasarar buɗe ido da ƙyau. ‘Asibiti kuma?’ na ambata a hankali ina waige-waige da kallon ɗakin dana buɗe ido na ganni cikin bazata. A saman hannuna dake naɗe da bandegi na sauke ganina, sai yanzune abinda ya faru yake ƙoƙarin dawomin a zuciya, a hasashena zan iya cewa jiya kenan abin ya faru, dan yanzu dai ranace ƙwanyar na fahimta, idan kuma ban mantaba ƙurar jiya ta tashine da yammaci har zuwa duhun mangariba, kenan a cikin asibiti na kwana?.
Bani da amsar tambayar tawa, kamar yanda babu alamun akwai mai amsa mani ita a kusa, dan babu kowa a ɗakin sai ni kaɗai.
Na ɗauki tsawon wasu mintuna da bazan iya ƙididdige yawansuba sallamar Ummie ta riski kunnuwana, nakai dubana gareta yayinda take ajiye madaidaicin kwandon data shigo dashi a hannu,
“Bily ashe kin tashi ma?”
Tai maganar tana matsowa daf dani. tare da taɓa hannuna da naji ciwon. murmushi nai mata, kafin na buɗe baki a hankali ina bata amsa da “eh”. Zama tai a kujerar gaban gadon, tana murmushi, tace, “Kai Alhmdllh, bily kin bala'in rikitamu jiya, wlhy mun zata bazaki sake buɗe ido ki ganmu ba”. Da tsagwaron mamaki nace, “Miyasa?”. Tai ƙaramar dariya tana miƙewa, “karki damu zan baki labarin komai, yanzu dai bara na kira Doctor danya dubaki, daganan kici abinci ko, dan tun kiran sallar farko na tashi domin na haɗa miki shi”. Kaina kawai na iya rausayarwa gefe ina binta da murmushi, tare da tarin ƙaunar da nake jinmu tamkar jini guda.
Ba'a ɗauki wani dogon lokaciba Doctor yazo, yaymin tanbayoyi kafin ya bama Ummie Umarni akan ta taimakamin nayi wanka ga bayi nan, idan na kammala naci abinci nasha magani, zuwa yamma ƙilama su sallameni tunda sunga komai normal.
Da taimakon Ummie na sakko a gadon, sai yanzune na kuma fahimtar a ɗaki na musamman nake, kuma ni kaɗaice a ciki, na kalli ledar jini dake rataye a ƙarfe cikin mamaki, Ummie data lura saita bani amsa da faɗin, “Ke aka ƙaramawa, dan sanda muka iso jininki ya zuba da yawa, amma Doctor yace babu wata damuwa a hakan, idan an ƙara miki zai amfaneki, idan kuma ba'a ƙaraba bazaki cutuba, sai dai boss ya dage akan a ƙara miki jinin dole, anbuƙaci gwada su oga Hafiz koza'a samu na ɗaya a cikinsu yay dai-dai da naki, amma sai boss ya hana a gwada kowa, a cewarsa jininsa yana rukunin da zai iya bama kowa, dan haka a ɗeba nashi, kowa yasha mamakin furucinsa, amma bawan ALLAHN nan ya fuske abinsa, babu ma wanda ya samu ƙofar kawo masa wargin tambayar dalilin hakan, daga ƙarshe dai jininsa aka ɗiba aka saka miki.......”
Lokaci ɗaya nai masifar zabura da zaro idanuna waje, har ina bige hannuna mai ciwo, hakan ya sakani cije lip ɗina na ƙasa kafin nace, “Jininsa fa kikace?”.
Sosai ta ƙyalƙyale da dariya, “Wlhy karkiji wasa, jinin Boss ne ke gauraye da naki suna aiki a kowacce kafar jijiyarki a halin yanzu”.
“Na shiga uku ni Bilkisu” nai maganar ciki yanayin ta ƙaremin. Dariya Ummie ta cigaba dayi, dan na lura sam bata fahimci tashin hankalin da nake a cikiba da gaske, ban sake iya maganaba har taimin rakkiya cikin toilet ɗin ɗakin dake tsaf babu datti, ga ruwan ɗumi ta haɗa mani kuma.
A cikin dabaru nake wankan gudun karna jiƙa hannun dake naɗe da bandeji, sai dai zuciyata sam bata tare da hankalina, sai faman juya maganar sakamin jinin Boss da Ummie tace anyi nakeyi, haka kawai naji hawaye masu ɗumi suna sauka bisa kumatuna, bansan na mineneba, sannan bansan dalilin zubar tasuba, sai dai wani gefe na zuciyata na danganta saukarsu da ganin kamar bankai matsayin da za'ace jinin wannan bawa ya gaurayu da nawaba, da kuma zaka tambayeni dalilin faɗar haka a lokacin bazan iya cewa komaiba balle yin fashin baƙi. Haka dai na kammala na fito, da taimakon Ummie na kimtsa cikin kayan da tazomin dasu, ta shafa min mai harda ƴar hoda fara ta sakamin dan karna zauna fuska na ƙyalli, na zauna a saman gadon jingine da filo ita kuma ta haɗamin tea, tare da zubamin farfesun kan rago daketa ƙamshin kayan yaji.
“Ummie ƴan gidanmu kuwa sun sani?”.
Sai da ta miƙamin tea ɗin kafin tace, “Eh, tun jiya da daddare sukazo ai, Daddy, Mom sai Aamilah da Shahudah da Salim, lokacin bakisan inda hankalinki yakeba, anama ƙara miki jinin ne”.
Kaina na gyaɗa mata sannan na amshi kofin, cikin suɓucewar harshe nace, “Sanda sukazo Boss na nan?”.
Tsareni tai da kallon tuhuma, ni kuma na basar cikin kauda mata shakkun dake neman yin ƙutse a ranta, fahimtar hakanne ya sakata daidaita yanayinta itama, tace, “A'a sun tafi lokaci harsu Oga Aliyu, ni kaɗaice kawai, saboda nima Daddy ne yace na jirashi shida Mami zasuzo su dubaki saisu tafi dani, tunda Doctor yace basa buƙatar kowa ya zauna dake”.
Bansan miyasaba sai kawai naji zuciyata tamin daɗi da rashin haɗuwar tasu, na cigaba da shan tea ɗin a hankali, Ummie ce ta kuma maido hankalina gareta da faɗin,
“Ammafa kin bala'in burgeni jiya wlhy Bily, wai dama baki da tsoro ashe?”.
Murmushi nayi kaɗan ina lumshe idanuna tare da muskuta zamana yanda zanji daɗi sosai, “Ummie ba tsorone banda shiba, wani lokacin tsoro da kansa yana jin tsoron mai tsoronsa, sai dai ba kowacce ƙwarin gwiwa ke fahimtar da hakanba, a duk lokacin da kikejin tsoron abu to kawai ki tunkareshi koda kina tunanin zaki halaka ne, ina mai tabbatar miki shi wannan abin tsoron shine zai koma tsoronki, da gaske daga jiya na ƙarajin ƙarfin gwiwar yima ƙasata aiki bakin rai bakin fama , alƙawarin danai da izinin ALLAH bazata tashi a banzaba, daga yanzu zan cigaba da tunkarar kowanne irin abin tsoro daka iya tsoratar da al'ummar ƙasata koda zai sakani fuskantar ƙalubale, bani da kowa sai kaina Ummie, akwai irina da yawa a faɗin duniya, waɗanda sukafini shiga gararin rayuwa da buƙatar jin ɗumin duniya a dalilin rashin majingina ta iyaye, wadda mutuwa ta nisantasu, kokuma iyayen na raye ƙaddara ta nisantasu, sai dai ita duniyar ta juya musu nata bayan saboda bata buƙatar nasu ɗumin, waɗanda kuma keda kusanci da duniyar suna hantararsu saboda basu da buƙatar taimakonsu koda da nuna tausayawane, irina da sukasan wannan zafinne kawai yakamata ace suna iya tunawa dasu da waiwayensu a lokacin da suka sami damar ƙutsawa jikin duniya ta ƙarfin tsiya. Na shiga aikinnan ne domin ALLAH, zanyi hidima wa ƙasata domin ita ƙasata ce, zan rungumi marayu irina domin ƴan uwanane, zan kare haƙƙin ƴan ƙasata domin suɗin ahalinane, nabar kallon allon tsoro a gabana a yanzun, allon jajircewa kawai nake burin cinmawa insha ALLAHU, abokan tafiya kawai nake buƙata, waɗanda basai naje farautarsuba, da kansu nakeso suzo gareni, hakkane kawai zaisa na tabbatar da sun cika sharuɗɗan abokan gwagwarmaya dai-dai da yaƙar tsorona, jiya ta wuce, yanzu a yau muke, abi mafi muhimmanci shine mu fiskanci gobanmu idan muna cikin masu rabon gani”.
Sosai Ummie keta faman jinjina kai da dogon bayanina da bani da tabbacin zai zama abin fahimta ga kowa har ita kanta, wani zai iya kallonsa ta fuskar ƙuruciya, wani yace rashin hankali na mata, wani yace wauta ta mara gata, wani yace zaƙewa ta ƴaƴa mata masu san nuna daidaita kafaɗunsu da maza, hakan bazai dameniba a duk yanda fahimtarka ta baka, abinda na sani kawai zuciya sirrin mai ita kawai takeji, duk bin diddigin ma'abocin kusanci koya kasa kunnuwa bazaiji komaiba sai bugawarta, idan kuwa har mun yarda gaibu sunanta gaibu, to yazama tilas muyi imani da hankali koda bama ganinsa a zahiri saita yaƙini kawai.
“Maganganunki irin na mutanene masu himma bilkisu, sannan masu duba gabansu mizatazo dashi, bawai yau ɗinsu kawaiba, da jiyansu data shuɗe ta zama tarihi, tun haɗuwata dake ta farko na fahimci kinada wata baiwa ɓoyayya da bakowa ALLAH ya bama ilhamar hasasotaba, daga lokacin kuma da muka kasance ma'abota kusanci na tabbatar da zamu ribantu da junanmu, sai dai taki ribar da zamu samu saita ɗara tamu muhimmanci da amfani a garemu, k.......”
“Sam ban gamsu da bayanankiba Ummie” na faɗa cikin ɗaga mata hannu saboda yanda ta kwararo zance.
“Miyasa kikace haka Bily?”.
“Banason faɗa kice na maida hannun agogo baya, mubar zancen kawai watarana ma ƙarasa, mizai hana kije wajen Doctor kimasa maganar ya sallamemu haka, banason zaman asibiti a rayuwata”.
kafin Ummie ta samu damar yin magana aka turo ƙofar aka shigo da sallama, Dad ne, hakanne ya sakani faɗaɗa murmushi akan fuskata, saurin tashi tsaye Ummie tayi ta bashi kujerar da take zaune akai, kafin ta gaidashi cikin girmamawa. Nima gaidashi nai, ya tambayeni jikina cike da kulawa. Naji daɗin ganinsa sosai, nakumaji daɗin alhinin daya nuna akan halin dana tsinci kaina, sai dai nayi ƙoƙarin daƙile alwashinsa na buƙatar nabar aikin, danshi kam ya fara tsorata dajin cewa wannan aikin namu da gaske bai dace da ɗiya mace ba, musamman ma irina da nake yarinya ƙarama.
Cikin murmushi da girmamawa a garesa nace, “Dad addu'arku kawai muke buƙata, idan har zamu cigaba da sakawa a ranmu mata basu dace da irin kowanne aikiba saboda matsalolin cikinsa, to lallai yankinmu bazai daina fuskantar koma bayaba, hakama sauran mata masu tasowa bazasu daina fuskantar ƙalubale na daƙile burinsu akan kansu da ƙasarsuba”.
Sosai Dad yay murmushi, ya shafa kaina da cewar, “ALLAH yay miki albarka kinji, lallai tunaninki ƙyaƙyƙyawane Bilkisu, ALLAH ya kiyaye gaba to, nabiya ta wajen likita, ya baki sallama yanzu haka, sai dai ya tabbatarmin daga office ɗinku an turo ɗaukarki, ɗan aiken na hanya kuma, dan haka ni zan wuce, dama daga nan airport na dosa”.
“Dad badai har zaka sake wata tafiyar ba?”.
Murmushi yaymin mai ƙayatarwa yana jinjina kansa, “Hakane bilkisu, masu iya magana nacewa na kwance baiga gariba, muma addu'arku muke buƙata tamkar yanda kuke buƙatar tamu kinji, wannan karon kuma bazan jimaba, dan sati ɗaya kacal zanyi, idan na wuce hakan kuwa bazan zarta gomaba”.
“To Dad ALLAH ya tsare hanya, ya kuma bada nasarar abinda za'a fita nema mai albarka”.
“Amin ɗiyata, nagode sosai”.
Itama Ummie tai masa addu'a, ya amsa mata da kulawa kafin ya ajiye mana kuɗaɗe masu kauri ya fice daga ɗakin”.
Koda Dad ya fice fuskarsa ɗauke take da murmushi tare da ɗunbin tausayin yarinyar a ransa, shidai haka kawai ALLAH ya dasa masa ƙaunarta a zuciya, yaɗan juya ya kalli ɗakin yay murmushi kafin ya cigaba da tafiya........
Gaff sukaci karo da mutum, Gimba yay saurin fara jero kalamun ban haƙuri a gareshi. Batare da Dad yay masa wani kallon arziƙiba yace babu damuwa, yay wucewarsa. Binsa da kallo Gimba yay cikin wani tsagwaron mamaki da juya abinda ya gani a cikin zuciyarsa, sarai ya gane mahaifin matar Boss ɗinsace ta da, kuma mijin Gwaggonsa, afili yace, “To mikenan? Mi yazo yi nan? Minene ma'anar wannan kallon da yayma ɗakin nan? Minenema haɗinsa da ɗakin?”. Bashi da mai amsa masa wannan tambayoyin, dan haka yaja bakinsa ya tsuke dan bai dace ya shiga abinda babu ruwansaba, Boss na yawan masa nasiha da kiyaye abinda ba huruminsaba koda a inane, kuma koda akan minene.
A ɗaki kuwa bayan fitar Dad yabo Ummie ta shiga jero masa, yayinda Bilkisu ke tayata tare da ƙara buɗe ƙyawawan halaye na Dad waɗanda Ummie batasan da suba. A haka gimba yay sallama a ƙofar ɗakin, sai da na suturta jikinna kafin mu bashi damar shigowa, dukda bamusan shiɗin waneneba.
Mun gaisa da juna cikin girmamawa, sannan ya kora mana bayani akan cewar Boss ɗinsa Jawaad ne ya bada umarnin yazo yakaimu gida dan an bani sallama.
Kallon juna mukai ni da Ummie, kowanne baki a hangame, sai dai bamu da damar bin ba'asi akan wannan umarnin, dan kuwa dai yana sama damu, mizaisa mu tuhumesa da abinda bamu da bakin zarensa. Haka muka shiga kimtsawa har Doctor ya shigo, ya ƙara mana bayani akan yanda zan kula da cuwon saboda gudun karya zarta haka, tare da kwanakin da zan ringa zuwa asibitin domin tabbatar da ingancin kulawar da nake bashi.
___________________________
JAWAAD
___________________________________
Zaune suke a office ɗinsa su huɗu, aminan juna kenan da sukejin kansu jini guda, sannan abokan amanar juna masu taruwa wajen magance matsalolin juna da ƙarfin zuciya dana aljihu.
Sunyi nisa cikin tattauna abinda ya faru a yammacin jiya ne, domin dai da gaske Jabeer ne ya haɗa cinkoson jiya da gangan saboda son cimma burin kama tsagerun da suka biyo, amma sai suka ɓace musu, ganin zasu rasa wannan damarne Jawaad ya bama Jabeer umarnin nuna ƙwarewarsa kasancewarsa masani sosai ta ɓangaren na'ura mai ƙwaƙwalwa.
A take kuwa ya nuna gwarzantakar tashi, ya haɗa cinkoson da su Bilkisu suka riska saboda tabbacin nan kaɗaice hanyar da masu laifin zasubi su tsira da wuri, ita kuma Bilkisu tayi tarar aradu daka akan abinda bata da tabbaci.
Aliyu ne ya fara faɗin, “Maganar gaskiya na daɗe banga jarumar mace mai ƙarancin shekaru irin yarinyarnanba, a yanda labari ke fitowa da ga bakunan mutane na yanda ta tari motar mutanen da suka fara ganin farkon al'amari da yanda ta tunkari mutanen zai baka tabbacin da gaske tanada kaifin zuciya akan aikinta”.
Cikin jin jina kai na tabbaci Jabeer yace, “Lallai maganarka tana akan gaskiya wlhy Aliyu, nifa abindama ya sake birgeni da ita shine, dukda mugun ciwon da taji, amma saita dake dan tabbatarma da duniya lallai ita ma'aikaciyar tsaroce ta gaske ba ƴar burgaba”.
Fuska shimfiɗe da murmushi Hafiz yace, “Sosaima kuwa Jabeer, dolene ƙaimin yarinyar ya burge kowa, dan kuwa da ƙwaƙwalwa tai amfani wajen fahimtar motar tana da alaƙa da rashin gaskiya, ta kuma nuna himmarta na sadaukarwa koda hakan na nufin zata cutu a wajensu, ta cancanci kowanne irin jinjina ga hukumarnan tamu, musamman idan akai la'akari da shigowarta cikin aiki jiya-jiya kawai, bana tunanin kuma an taɓama fita da ita wani aiki makamancin haka koda sau ɗaya”.
Duk wannan zance da suke faman zubawa akan yabon Bilkisu da jinjina himmarta Jawaad na zaune shima a cikinsu, yana sanye cikin baƙaƙen suit kamar sauran da a kullum suke ƙara masa kwarjinin kasancewarsa ma'aikaci, sai dai ya cire rigar sama, yana zaune ne kawai da baƙin dogon wandon da rigar ciki mai dogon hannu kalar kore mai haske, maɓallan rigar uku a buɗe, hakanne ya bayyana singlet ɗinsa kaɗan fara tas, yaci zanzaro, ya tsuke ƙugunsa da belt kalar shirt ɗinsa.
Abinda zai baka mamaki ko tari bai yiba akan maganar, baima nuna ya fahimci mi suke tattaunawarba sam, yana zaune ne ƙafa ɗaya kan ɗaya tamkar wani basarake, kansa sunkuye yanata faman danne-danne a cikin tab... ɗinsa ta kamfanin Apple, sam fuskarsa babu wata walwala, kuma ba'a tsuke take sosaiba.
Aliyu ne yakai dubansa garesa, tare da faɗin, “Ka fuskanci abinda muke tattaunawa game da yarinyarnan kuwa Jay?”...............✍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
Typing📲
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce🤙🏻
BOOK TWO
Page 4
...............Shiru tamkar bazai tankaba, kusan sakanni sha biyar kafin yay magana batare daya bar danne-dannen tab... Ɗinba balle ya kallesu, “Wace yarinya kenan?”. Yay tambayar cikin nuna halin ko'in kula balle su sami ƙwarin gwiwa akan ya jisun.
Duk kallonsa sukai da mamaki saboda yanda sukasanshi dason mutum mai himma, amma yanda ya amshi maganar ya matuƙar basu mamaki a yanzun.
Jabeer ne yace, “Yarinyar jiya daka bama jini mana Jay”.
“Humm” yace kawai ya sharesu bai sake tankawa ba, tsawon mintuna duk sun zura masa idanu suna jiran ƙarin bayani, dan sunyi tsammanin fara jin yabon yarinyar da ga bakinsa ma kafin su su furta, amma ya share kamar ya manta dasu ma a office ɗin.
“Wai boss lafiya kuwa?” Hafiz yay tambayar a wani yanayi.
Sai yanzune ya ɗago ya kallesu su duka, kallo irin a taƙaice ɗinan ya janye mayatattun idanunsa masu cikar gashi da haske tamkar madara, ya taɓe baki kaɗan kafin ya miƙe daga wajen ya nufin kujerarsa ta zama, dan da suna zaunene a rukunin kujeru da'aka shirya a office ɗin domin hutawa ko ganawa da baƙi na musamman.
Sai da ya zauna sosai ya juya kujerarsa tana fuskantarsu kafin yace, “Abun harinmu a yanzu shine mutuwar jami'inmu da sir Ahmad yamin bayani, minene shawararku akan hakan?”.
Aliyu ne ya samu damar faɗin, “Bincike akan shi ɗin wanene? Tunkan fara aiki a wannan hukumar har zuwa farawar tashi, tare da sanin masu bashi gudunmawa akan aikin da yazama sanadinsa, da kuma sanin a ƙarƙashin wa ya samu umarnin”.
“shawara mai ƙyau” Jawaad ya faɗa yana lumshe idanu da kwantar da bayansa jikin kujerar yana lilawa a hankali fuskarsa ɗauke da murmushi, kusan sakanni biyar kafin ya sake ɗagowa yana kallonsu da nazartarsu. Ya ɗauke idanunsa tare da sake komawa jikin kujerar ya kwanta, “Idan an sallamota daga asibiti zatayi bincike akan dukan bayanan Aliyu”.
Cikin matuƙar mamaki suka kallesa, cikin harɗewar harshe Jabeer yace, “wai kana nufin yarinyar?”.
Kallonsa kawai yay ya janye idanu, sai dai baice komaiba. Sun fahimci amsar kenan, dan haka Aliyu yace, “Amma boss baka ganin aikin zai mata girma? Musamman idan mukai dubi akan shine na farko?”.
Cikin halin ko in kula ya taɓe baki, ba tare daya kallesu ba yaja wasu takardu dake saman tebir ɗin nasa yana faɗin, “Maybe hakan, maybe kuma ba hakan baneba, naga kuma da kanku kun yarda da ƙwazonta, to miye kuma na kokwanto yanzun?”.
Babu wanda ya sake cewa komai. sai dai a ƙasan ransu duk sai suka kasance cikin nadamar kwarzanta ƙwazon yarinyar da yawa irin haka, dan a ganinsu bata kai ƙwarin da za'a sakata a irin wannan babban aikin hakaba mai haɗari, musamman idan sukai dubi da ko rose data daɗe a cikinsu baya bata irin wannan damar.
Takardar da ya maida hankali a kanta ya ɗago saitin Hafiz, “Hafiz wanene da wannan bayanan haka?”.
Tasowa Hafiz yay ya dawo gabansa, ya zauna a ɗaya daga kujerun gaban tebirin yana mai amsar takardar, nazarin mintuna biyu ya ɗago kai yana kallonsa, “Akan case ɗin yaron nan da aka samu makamai a shagonsu ne, Aliyu ne akan binciken kuma”.
Jawaad ya maida kallonsa ga Aliyu, hakan ne ya saka Aliyun tasowa ya nufosu shima.
__________★★__________
BILKEESU
_________________________________
Wani irin mayataccen ƙamshi ya shiga rige-rigen zirarawa cikin ƙofofin hancinanmu yayinda muke shiga motar da boss ya turo ɗaukarmu, batare da kowannenmu ya fargaba muka tsinci kawunanmu da lumshe idanu muna sake buɗe hancunan namu sosai. A haka yaja motar muka bar asibitin, tabbas wannan ƙamshine daya cancanci ajiyeshi a ma'ajin zuciya da ƙwaƙwalwa saboda ya kasance na musamman, bansan miyasa na kirashi na musammanba, sai dai kawai zan iya fassara hakan da kasancewarsa na musamman a duk lokacin da hanci ya shaƙa koda ba namuba. Naji tamkarma kar motar ta tsaya ace na daina shaƙar wannan ƙamshin, sai dai babu yanda zanyi dan hakan tilasne. A wannan yanayin muka isa gida, ya ajiyemu a gate ya juya, mukuma muka shiga ciki bayan mun masa godiya.
Mun iske gidan babu kowa, suna gidan rasuwa su duka, dan haka mukai zamanmu dagani sai Ummie da tace boss ya bata umarnin ta zauna dani harna warke tun a jiya. Ban tambayeta daliliba, kamar yanda itama bata kawo komai a rantaba game da hakan, sai dan tana ganin ya fahimci bani da wadda nakeda kusanci da shi sama da ita a station ɗin namu.
__★.:.★__________★.:.★__
JAWAAD
_____★.:.★__________★.:.★_____
Suna tsaka da cigaba da magana shi da su Aliyu kira ya riskesa daga office ɗin B.G, duk da kiran ya bashi mamaki daga shi harsu Jabeer ɗin hakan bai hanashi fita domin cika umarni ba.
Galala nai da baki ina kallon haɗuwa da tsari na office ɗin da Jawaad ya shiga, komai yaji babu algus. Banma kaina buƙuluba nabi ko'ina daki-daki da kallo a office ɗin, kafin na sauke idanu ga mai ikon faɗa aji na hukumar tasu. Danƙari, na ambata a zuciyata dan kuwa munzo ƙarshen zance, sam babu alamun fara'a balle sassauci tattare dashi, Jay ya miƙa gaisuwa cikin girmamawa kafin ya samu izinin zama daga gareshi.
“Sir Ance kana kirana” Jawaad ya faɗa cike da girmamawa.
A cikin maƙoshi ya bashi amsa da cewar, “Uhhm” daga haka yaja bakinsa yay tsit. Gani nai shima Jawaad ɗin ya sake kame kansa ba tare daya sake tankawa ba, kusan mintuna huɗu suna a haka kafin ya ɗago kai tare da juyama Jawaad fuskar lap-top ɗin dake gabansa, hotone mai motsi (video), Bilkisu ta bayyana tana harbi da bindiga har guda biyu a rikicin jiya, gaba ɗaya bidiyon bai wuce na minti ɗaya da wasu sakanni ba, saboda iya itaɗin kawai aka nuna, ƙarewarsa ce ta saka Jawaad kallonsa cikin rashin fahimta.
Cikin zafin rai da fusata ya zazzaroma Jawaad ɗin idanunsa jajaye, “Wannan yarinyar tanada izinin yin harbi ne kamar haka dama?”.
Jawaad da ya tsuke fuska shima ya girgiza kansa kawai.
“Ya akai tayi kuma?”.
Sai da Jay ya furzar da huci kaɗan kafin yace, “Sir bamu da wani zaɓine bayan hakan, domin musayar wutace, idan kuma bata da makamin kare kanta a hannu rayuwarta na cikin haɗari, musamman daya kasance da taimakonta muka riski masu laifin”.
“Hakan yana nufin shine matakin ƙarshe da kuke da mafita kawai?”.
Shiru Jawaad yay bai motsaba, sai maƙogwaronsa ne keta kai kawo a cikin wuyansa, yayi kicin-kicin da fuska.
“Da kai nake magana Captain!”.
“Sir nasan munyi kuskure, amma a duba uzirinmu muma, musamman na isa wajen a ƙurarren lokaci, sannan a duba irin rawar da yarinyar ta taka, duk da kasancewarta ƙaramar ma'aikaciya, wadda ta shigo jiya-jiya cikin wannan hukumar tamu, ta nuna ƙwazon da ya kamata a jinjinama ƙoƙarinta ba ƙalubalantar taba, domin kuwa ita bata da laifi, nine mai laifi dana bata bindigar”.
“Uhyim, kana nufin yanzu dai ka kareta?, sannan dukkan hukuncin da zai biyo baya zaka ɗauka kuma?”.
Shiru tamkar bazai amsaba, sai kuma ya ɗago idanunsa harsun kaɗa da ɓacin rai, a kasaushe yace, “Aimin duk hukuncin da za'ai matan babu damuwa”.
Shiru B.G yay kawai yana kallon Jawaad ɗin, yasan yaron dama akwai taurin kai, dan tun shigowarsa hukumar ƴan sanda ma da tsaurin ido ya shigo, kasancewar wanene mahaifinsa yasa aka hana kowa nuna masa yatsa, himmarsa da zafin nama ne ya saka aka maidoshi cikin hukuma DSS, shi kuma har cikin ransa yaron bai masaba, sanin dalilin kuwa wannan sirrinsane....
“Kaje zamu nemeka” B.G ya faɗa a daƙile.
Uffan Jawaad baice ba, ya miƙe kawai tare da yin salute nashi ya fice abinsa yana haɗiyar zuciya, duk wanda zai iya ganinsa a wannan lokacin dolene ya fahimci ransa a matuƙar ɓace yake, mai makon ya wuce office ɗinsa sai ya nufi office ɗin L.C, wato sir Ahmad barewa, canne kawai zai kai damuwarsa ya samo mafitar da yake buƙata.
Bayan yay knocking ƙofar aka bashi izinin shiga, ya riga da yasan ya gansa ta cctv, tunda ya turo ƙofar ya shigo sir Ahmad ya fahimci akwai damuwa, ya kafeshi da idanu kuwa, yayinda shi kuma Jawaad ɗin yaƙi yarda su haɗa idanu.
Sai da ya miƙa gaisuwa Sir Ahmad yay masa nuni da kujera alamar ya zauna.
Koda Jay ya zauna sai baice uffanba, sai ajiyar zuciya kawai yake faman yi, sir Ahmad yay murmushi irin nasu na manya masu kaifin tunani, kafin ya miƙe daga mazauninsa ya nufi firij ɗin dake a office ɗin, goran ruwa ya ɗakko ya miƙa masa batare da yayi magana ba, babu musu ya amsa, ya ɓalle murfin yana kai goran bakinsa, sai da ya shanye fin rabi sannan ya ajiye yana sauke numfashi a jajjere.
Wani murmushin Sir Ahmad ya kumayi, sannan ya zauna a kujerar dake kusa da Jawaad ɗin suna kallon juna “Captain! Lafiya kuwa? Waya zinguro mazajene?”.
Idanu Jay ya ɗago ya kalli Sir Ahmad, sai kuma ya janye yana shaƙar numfashi da zafi.....
“Jay!”
Sir Ahmad ya kirayi sunansa yana ɗora hannunsa bisa kafaɗarsa.
A karo na Biyu Jawaad ya sake kallon Sir Ahmad barewa, ya cije leɓensa da ƙarfi yana faɗin, “Daga office ɗin B.G nake Sir”.
“Na sani ai” cewar sir Ahmad yana murmushi.
Cikin sauri da tsagwaron mamaki Jawaad ya kalli Sir Ahmad, kallo irin na tuhuma.
Ƴar dariya sir Ahmad yayi, ya kuma kai hannu ya bubbuga kafaɗar Jawaad ɗin a hankali, “Kar kai fushi yarona, karkuma ka shiga ruɗani, banason ka manta kanka a cikin mutane masu kaifin basira, za'ai amfani da yarinyarne kawai ai wasa da hankalinka, kaga kenan an samo lagwonka da damar bama maƙiyanka yin wasoso a saman mutuncinka, kar kaga laifin B.G, shima sashi akayi, domin bana tantama umarni ya samu daga sama, sai dai wanene? Akan minene? Shine ban saniba”.
“Zuutt!” wani abu dake tsaye a maƙoshin Jawaad ya faɗa cikin cikinsa, ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, saboda dai Sir Ahmad ya dawo dashi a hayyacinsa da wuri...
Sir Ahmad ya miƙe yana murmushinsa na kamilallun mutane, ainahin kujerar zamansa ya koma ya zauna..
“Abin bai baka mamakiba ace iya inda take harbin kawai aka kawo masa, sannan kuma ita kaɗai, bayan kuma batakashin da kuka gwabza a wajen ku kusan goma ne”.
“Sir ai abinda ya matuƙar ɓatamin rai kenan, taya za'ai ace itace kawai za'a ɗauka?....”
“Saboda ita kaɗai tazo da salon da ya ajiye ruɗani a zukatan masu fargaba akan jajircewarka”.
“Salo kuma sir?!”.
“Yes! Jawaad, salo mai ƙayatarwama kuwa, andaɗe ba'a samu mai ƙaracin shekaru irinta da wannan ƙwazonba, abin ƙarin mamakin kuma gata mace, yarinyar da alama zata ajiye tarihi a wannan hukumar, dan alamomin hakan sun farane daga jiya”.
“Sir! to amma su wanene ke ganin hakan matsayin ƙalubale garesu? Miyasa kuma....?”.
“Nima ban saniba Jay”.
Shiru Jawaad yay na wasu sakanni kafin yace, “Saboda mi suka zaɓi hukuntata bayan karramawa ta cancanta dashi sir?”.
Sir Ahmad yay gajeruwar dariya idonsa akan Jay, yace, “Saboda ƙwazonta abin dubawane ga mai hankali, sannan abin tunani ga irin waɗanda basa buƙatarta, wannan shine aiki na farko da yarinyar tayi, kuma ba sakata akayiba, sai dai ƙwazonta ya girmi matsayinta da gogewarta a aikin, hakanne ya sakasu saka maka alamar tambaya (?), musamman daya kasance tare da kai aka fara ganin baiwar ta ta”.
Karan farko da Jawaad ya ƙyalƙyale da dariya harda dukan tebir ɗin gabansu, Sir Ahmad dake kallonsa shima murmushinsa ya faɗaɗa, ya juyo sosai yana fuskantarsa, har yanzu kuma fuskar tasa da sauran dariyarsa irin wadda kafin yayita akan kai ruwa rana,
“Sir kasan minene kuwa?”.
“Saika faɗa Jawaad”.
“Sun bani dariya ALLAH, danni Ko sunanta ban saniba fa”.
Dariya shima sir Ahmad ya shiga ƙyalƙyalawa, kafin yace, “Cakwakiya kenan, to tabbas kuwa daga masu wannan ƙullin abun ba haka bane ba Jawaad, kallon ƘWAI CIKIN ƘAYA sukema lamarin”.
“Nima na fahimci hakan a yanzu sir”.
“Yayi ƙyau. Miya faru jiya?”.
Tun daga farkon zuwansu inda abun ya faru har ƙarshe Jawaad ya bama Sir Ahmad labarin komai bai ɓoye masaba.
Kai kawai Sir Ahmad yake jinjinawa har Jawaad yakai ƙarshen jawabinsa, ya sauke numfashi kaɗan yana faɗin, “Zamu shiga meeting anjima, kuma nasan akan wannan maganarne, shawara ɗaya dazan baka yanzu shine, kai ƙoƙarin gano wanda ya ɗauki wannan bidiyon, sannan kayi gaggawar samo bidiyon da yafi wannan na wajensu tsaho, ka kumayi saurin rubuta bayanai akan komai ka tura office ɗin L.G tare da bidiyo ɗin daka samo ɗin”.
Kamar Jawaad zaice wani abu, sai kuma yay shiru yana miƙewa da faɗin, “Okey sir, zanyi ƙoƙari insha ALLAH”.
★★★★
Gaba ɗaya kan Jawaad ya kulle da wannan lamari, ya rasama ta yaya zai fassara al'amarin, maganganunsa da Sir Ahmad kawai ke masa kai kawo a cikin zuciya, tare da zuwansa office ɗin B.G, ya rasa ina zai kama ma shikam? Yana buƙatar ganin su Jabeer tare dashi yanzunan, sai dai tabbas bazai yuwu a station ɗinanba, dan yanzu dukkanin motsinsa abin bibiyane.
Ƙaramar wayarsa ya ɗauka ya turama Hafiz saƙo, kafin ya tura wayar aljihu bayan ya kasheta gaba ɗaya ma, wasu takardu ya ɗiba ya fito a hanzarce, hana kowa ya bisa yayi, ya shiga mota shi da Gimba kawai suka fice daga station ɗin.
Danne-danne yaketa famanyi a lap-top, hakan ya saka gimba kallonsa ta cikin madubi, “Boss! Ina zamuje?”.
Ba tare da ya ɗagoba yace, “A.Y Street”.
Cikin girmamawa Gimba ya amsa, tare da juya kan motar suka nufi hanyar gidan Jawaad ɗin dake anguwar A.Y street.
Sunyi wajen mintuna talatin da zuwa kafin su Aliyu su iso. A falo suka iskeshi har yanzu yanata faman danne-danne a lap-top, a haka ya amsa sallamarsu ko ɗagowa baiyiba ma. Sai da suka zauna da kusan mintuna biyu sannan ya ɗago ya kallesu, kallo ɗaya yayma Rose ya ɗauke kansa, hakan yay bala'in sosa ranta, dan akwai kwallin data shafa, an kuma tabbatar mata idan suka haɗa ido da shi zai haukace mata, yabar kallon kowacce mace da gashin arziƙi sai ita, amma ɗan rainin wayon tun'a station takeson su haɗa ido da shi hakan ya gagara...
“Boss! Lafiya dai ko?”.
Aliyu da ya kafeshi da idanu ya faɗa.
Lap-top ɗin ya ajiye yana faɗin, “Da dai sauƙi Aliyu, an yanka ne ta tashi”.
“Kamar ya?;” suka faɗa cikin haɗa baki su uku, rose ce kawai da bata fahimci hausarba batace komaiba.
Cikin takaici Jawaad yace, “Ƴan uwana wasan jiya ya koma yaƙi, kukan tsuntsuwa mai zanen kanari ya zame mana abin magana”.
Sun fahimci zaurancensa, saboda wannan yana ɗaya daga cikin salonsu, musamman akan aikin da suka samu gamayya da waɗanda basa cikinsu, sai dai basu fahimci dalilin zaurancenba a yanzu, saboda duk sune a wajen babu baƙon ido.
Jabeer yace, “Jay bansan miyasa ka zaɓi ƙin buɗe zancenba, bayan kuma duk mune babu wani bare a cikinmu?”.
Jawaad yace “Nima bansan miyasa harshena ya zaɓi hakanba Jabeer, sai dai saƙon kamar tun daga zuciyane”.
“Idan na fahimta, kamar zuciyarka na ɗarsa maka akwai ɗan baya ga dangi kenan a cikin tafiyar?”. Hafiz yay maganar cikin taraddadi.
Cikin sauke nannauyan numfashi Jawaad yace, “Bani da tabbas, sai dai zuciyata na rayamin akwai idon mikiya a bayanmu”...............✍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
Bilyn Abdull 📚:
Typing📲
Page 5
.............Duk Kasa cewa komai sukai, sai idanu da suka zubama Jawaad tamkar wani bakonsu.
Rose da zuciyarta ke tafasa akan rashin kallonta da jawaad baiyiba ta kasa daurewa, ta dubesu baki ɗaya a wani yanayi, “Boss wai mike fauwane? tai maganar cikin harshen turanci da tsare Jawaad da idanu tana fatan ta dace yanzun.
A mamakinta yanzunma dai ƙin kallonta yayi, sai Lap-top ɗinsa ya miƙa mata kawai, ya koma ya zauna tare da ɗaukar tab.. Ɗinsa ya shiga tafa saƙo da hanzari.
Gani nai Aliyu ya ɗago ya kallesa, yay masa wani salo da ido tare da cije baki, murmushi Aliyu yayi kawai ya maida kansa, kafin ya miƙe yabar falon, hakama Jabeer da Hafiz duk ya tura musu suma, Hafiz shima tashi yay ya fita, Jabeer kuma ya koma kusa da Rose dan kawai ya ɗauke hankalinta da aikin da Jay ya bata itama.
Bayan fitar su Aliyu da kusan mintuna tara ya miƙe yabar falon ya nufi bedroom ɗinsa. Sai da ya kulle ƙofar kafin ya ciro ƙaramar wayarsa yay kiran Hafiz.
“Hafiz yaya? An dace kuwa?”.
“Ba'a daceba Boss, amma ga shawara mana?”.
“Micece shawarar taka?”.
“Mu bincika kowanne manhajar yanar gizo ko zamu dace wani ya ɗauka, kasan yanzu ba'a raba mutane da ƴan ɗauke-ɗauke a waya, maganar gano wanda ya kaima su B.G kuma ba abune mai sauƙiba ace yanzu da gaggawa, sai dai mu canja shawara ta wannan gaɓar”.
“Na fahimceka Hafiz, yanzu kayi duk yanda ya dace, amma inaji a raina koma wanene yakai wannan bayanan yana da kusanci damu Hafiz, amma banason zargin kowa”.
“Boss zargi dolene, kuma koma wanene ya daɗe a jikinmu, a sannu zamu cinmasa da ƙarfin ƙudirar UBANGIJI, dan shine ke haska mana hanya a dukkan lamuranmu”.
“Insha ALLAHU Hafiz, yanzu dai sai na jika”.
Yana yankewa yay kiran Aliyu shima, sai dai daga ɓangaren Aliyun an dace, dan ya turo masa dukkan bayanai akan Bilkisu da abinda ya shafi shigowarta hukumar tasu, da horon data samu, da ƙwazon data nuna tun a wajen horaswa, alaƙarta da Qaseem, sai dai babu wani bayani kafin zuwanta gidansu Qaseem ɗin, hakkanne yaɗan tsayama Jawaad a zuciya, har yakejin dolene ya sake binciken, dan karfa nan gaba ta zame masa ƘWAI CIKIN ƘAYA kuma kamar yanda ƴan bayan fage ke hasashe.
Daga ɓangaren Hafiz ma an dace daga baya, dan kuwa cikin amincin ALLAH ya samo bidiyon faruwar komai tun daga lokacin da Bilkisu ta kaima motar masu laifin caffa kafin zuwansu, har zuwa sanda abubuwa suka lafa.
Yaci karo da Bidiyon ne a wani chennal na youtobe, bayan ya shiga manhajar Google yay Searching, sai dai abinda ya bashi mamaki yana kammala sauke video'n akan manhajar ta youtobe wanda ya ɗora ɗin ya saukeshi daga accaunt ɗin, hakan sai yay bala'in ɗarsa mamaki a zuciyar Hafiz, harya kasa haƙuri ya kira Jawaad ya shaida masa.
Murmushi Jay yayi yana shafa kansa, “Ba abin mamaki bane Jabeer, musamman idan mukai la'akari da babu wata kafar yaɗa labarai da dama ta saki bidiyon mai tsawon hakan, sai wasu ɓangarori da dukansu iya inda muke musayar wutane kawai”.
Hafiz yace “Hankalina sam bai kaiba sai yanzu kam, koma miye yake a ɓoye ALLAH zai bayyanashi ai, mudai domin ALLAH mukema ƙasarmu aiki, duk mai yunƙurin daƙilemu kuma ALLAH zai mana maganinsa”.
“Insha ALLAHU kuwa Hafiz” Cewar Jay cike da takaici.
Kafin dare duk sun haɗa bayanan da ya kamata akan maganar, sun tura iya waɗanda Sir Ahmad ya umarcesu zuwa Office ɗin, L.G, sauran kuma sun adana a wajensu domin ya zame musu hujjar kare kai, hatta da bidiyon suma gutsira sukai suka tura, sauran kuma suka adana a wajensu.
_______★__________
SHAHUDAH
_____________________________
Tunda suka fara zuwa gidan rasuwarnan sau ɗaya taga Jawaad, harga ALLAH ita kuma dominsa take zuwa, a tunaninta idan suka haɗu zai matuƙar rikicewa da ganinta, musamman ma yanda ta sake canjawa da ƙyau mai ƙayatarwa, sosai ta gama shirya shika-shikan rama dukkan abubuwan da yay mata kafin ta yarda da buƙatarsa ta komawa gidansa.
Sai dai abin mamaki da al'aj
abi dukkan tunaninta sai bai zama gaskiyaba, dan kuwa ko a randa suka haɗu kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa, komai kuma a kan idanun Mom ya faru, dan suna a falon mama Atika ne a washe garin rasuwar ya shigo da baƙi su Sir Ahmad da sukazo gaisuwa. Sarai idanunsa sun gane masa Shahudah, amma sai ya ɗauke idanu cikin nuna halinsa na ko'in kula da abu.
Abin ya sosa mata rai sosai, amma saita danne da yaƙinin ƙila yayi hakane saboda ganin suna cikin jama'a. Koda suka koma gida sai basuyi maganar da Mom ba, saboda kowa ya dawo a gajiye wajen bacci yafi buƙata. Washe gari kuwa kwalliya tayi ta musamman dan Jawaad nanma babu sa'a, dan har dare da suka baro gidan bata sakashi a cikin idanunta ba, washe gari kuma suna isowa gate ɗin gidanne motar Jawaad ɗin ke fita da alama ya nufi office ne. Waɗanan akasin da akaita samune suka jefata a cikin damuwa har yau ta kasa daurewa.
“Mom kinga abinda Bb ya kemin kuwa? Bayan ya kamata ace ya nuna zalamarsa da kewata na shekarun da muka kwashe bama tare”.
“Huhm” Mom ta faɗa tana shafa kan Shahudah dake saman cinyarta, dan kuwa suna cikin bedroom ɗin Mama Atika ne ita da Shahudahn kawai, dan ta fahimci ɗiyar tata na tare da damuwa, yau tunda sukazo gidan ta shigo ɗakin Mama Atika bata sake fitaba, shiyyasa ta biyota, sai ta isketa cikin damuwa, hakanne ya sakata zama ta dora kan Shahudah a cinyarta tana shafawa, itakuma take bata labarin ruɗanin data shiga akan tarbar data samu daga wanda batai tsammaniba daga Bb ɗinta (Jawaad).
Mom ta haɗiye abinda ya tsaya mata a maƙoshi tana sake yamutsa sumar Shahudah'n, “Kar taurin kan yaron nan ya ɗaga hankalinki fiye da haka Shahudah, ki barsa, ni da kaina zan sauke masa wutar dake ci a kansa, bara dai a gama hidimar rasuwarnan kinji”.
Kai Shahudah ta ɗaga mata cike da shagwaɓa, har ƙwalla na sakko mata a kan kumatu tace, “Amma Mom wane mataki zaki ɗauka to?”..
Mom ta share mata hawaye tana murmushi, “Karki damu Shahudah zaki gani, kedai sonake kicigaba da kwantarmin da hankalinki, nan kusa kaɗan zaki dawo ɗakin mijinki”.
Kai Shahudah ta ɗaga mata tana murmushi da rungume mom. Murmushi mom tayi taci gaba da lallashinta cikin so da ƙauna.
Nikam nace, “Mai uwa a gindin murhu baya cin tuwonsa gaya ai Shahudah😋😜🤸🏼.
..::..★__________★..::..
BILKEESU
____★..::..★__________★..::..★____
Kwanaki huɗu cir bana zuwa Office ina gida ina jiyyar hannuna, yayinda kullum Ummie ke tare dani, ƴan gidanmu kuwa basa yini suna gidan rasuwa, barci kawai ke kawosu gidan. A kwana na biyar nai shirin komawa aiki, dan naji sauƙi sosai, a kuma daren ranarne Yah Qaseem ya dawo, nayi farin cikin dawowar tasa, dan nikaina nasan idan nace banason Yah Qaseem na yaudari kaina, a ƴan kwanakinan da bayanan sosai nayi kewarsa.
Tun a daren yake jeramin tambayoyi akan hannuna, bai samu amsa ko ɗaya ba daga gareni sai murmushi kawai.
Koda muka tashi da safe ma dai bai fasa sonjin musabbabin ciwonba, da naga ya damu sai kawai nace masa tsautsayine ya gitta mani a wajen aiki, badan ya yardaba ya ƙyaleni kawai, kasancewar yau zan koma aiki nima sai na bisa muka tafi tare kamar yanda muka saba kafin yay tafiyar.
Yah Qaseem na gama daidaita fakin motarsa wani jami'inmu na isowa wajen, ya isarmin da saƙon kira daga office ɗin B.G, maganar da jami'in yazo da itane ya sakamu kallon juna ni da yah Qaseem ɗin.
Idanuna na janye daga cikin na Yah Qaseem daya tsatstsareni da kallon tuhuma, da ƙyar na haɗiye yawun da ya tarumin a baki, dan girman office ɗin mai kiran nawa na kalla da kuma tunanin minene dalilin kiran?.
Yah Qaseem da har yanzu idanusa ke kaina da alamar tambaya na kuma kallo, ya gyara tsaiwarsa yana mai jehomin tambaya,
“Bilkisu mikike ɓoyemin ne?”.
Da sauri na girgiza masa kaina, “Wlhy Yah Qaseem bana ɓoye maka komai, nima bansan minene dalilin kiranba, amma bara naje najiyo”.
Ban jira amsarsaba na bar wajen cikin tafiyar sassarfa, zuciyata sai bugu take da sauri-sauri, dan inaji a raina wannan kiran bana lafiya bane ba, musamman
idan nai dubi da ƙaramin matsayina a hukumar.
Koda na iso sai da na jira aka bani izinin shiga sannan, wannan shine karon farko da zan shiga office ɗin a rayuwata, ba shi kaɗai bane a cikin office ɗin, jinai wani abu ya tsargamin daga saman kaina har zuwa yatsan ƙafata, na aro jarumtar dole na yafama kaina tunda bansan minene dalilin kiranba. Na miƙa musu gaisuwa cikin girmamawa kafin na zauna inda aka nunamin.
Tambayar farko da aka jefamin ta sakani ɗago idanuna na kallesu badan na shiryama hakanba, ba firgici ne ya sakani kallon nasu ba, nutsuwace ta zomin saɓanin yanda na shigo a rikice, dan kuwa a nawa tunanin inhar akan rikicin daya faru kwanaki biyar da suka wucene banga wani abin kuskure dana aikata a cikiba, zamana na gyara na fara amsa musu tambayarsu da iya gaskiyata dana sani.
Yanda Bilkisu ke amsa musu kowacce tambaya kanta tsaye babu ko ɗigon firgici ko rawar harshe ya sakasu kafeta da idanu, su kansu iya zallar gaskiyarta suke gani a saman fuskarta da furucinta.
Sun mata tambayoyi sosai, domin sake tabbatar da gaskiyar tata suka sake maimaito mata dukkan tambayoyin da sukai matan a farko, abinda ta faɗa daga farko shine ta sake maimaitawa saboda hakan shine gaskiyarta.
Kusan awa ɗaya da wasu mintuna suka sallamoni na fito, a raina sai juya wannan al'amari nakeyi...
_____________________________
JAWAAD
Zaune yake a office yanata aikin duba wasu tulin takardun dake gabansa yaji knocking ƙofa, siririn tsaki yaja dan baya buƙatar kowa a irin wannan lokacin, izinin shigowa ya bada batare daya ɗago ba balle kallon wanene?.
Ƙamshin turarenta kawai ya bashi amsar wacece, harta zauna bayan gaisheshi da tayi bai ɗago ɗinba, a haka ya amsa mata.
“Mi kike buƙata?”
Ya faɗa yana cigaba da aikinsa batare da ya ɗago ɗinba.
Duk da taji haushi sai ta danne, abinda ta gani kuma ta jiyo game da kiran Bilkisu da akayi office ɗin B.G ta zayyane masa, karon farko da ya ɗago ƙyawawan idanunsa ya sauke akan rose, sai dai baice komaiba. Duk da tsawon kwanaki kenan tana buri da buƙatar irin wannan kallon daga garesa saboda kwallin da take sakawa na jawo hankalinsa kanta sai ta kasa jurewa, dan wani irin kwarjininsane ya kuma cika mata idanu da gangar jikinta, tai azamar janye idanun nata ƙirjinta na wata irin harbawa.
Har lokacin idon Jawaad na akanta, ya cigaba da ƙare mata kallon nazari har kusan mintuna biyu kafin ya janye ya maida ga aikinsa.
Ɓoyayyen numfashi rose ta sauke, daga can ƙasan ranta kuma wani daɗi na sake mamayeta, dan kuwa dai tasan ta gama da taurin kan Jay kamar yanda bokanta ya sanar mata, inhar suka haɗa ido wannan kwallin na idonta to lallai tagama da mallakarsa har abada, ba kuma zai sake kallon kowacce maceba bayan itaɗin.
Sakanni kusan ashirin bai tankaba, bai kuma sake kallonta ba. Takaici ya sake mamaye zuciyar rose, ta buɗe baki da nufin yin magana ya miƙe tsaye, bindigarsa da wayoyinsa dake saman tebir ya ɗauka ya tura cikin aljihun Blue jeans ɗinsa, tare da ɗaukar tab... ɗinsa a hannu. “muje” ya faɗa batare da ya kalleta ba.
Binsa tai da kallon mamaki, harya buɗe ƙofar office ɗin ya fice, dole itama ta tashi da hanzari ta bisa, a ranta tana ayyana cewar ‘Yau ƴan wulaƙancinne a kansa kenan?’.
Fitowar Jay daga office yay dai-dai da fitowar Bilkisu daga sashen office's ɗin su B.G, kaɗan ya rage suyi karo, kasancewar hanyar data haɗa shataletalen office's ɗin ɗayace kafin su ƙarasa su hau lifter da zata kaisu kasa.
Da sauri naja baya ƙirjinna na motsawa, cikin dakewar harshe da banyi zaton inada shi ba nace, “Kayi haƙuri dan ALLAH , bansan ka taho bane”.
Ƙyawawan fararen idanunsa ya zubamin kansa tsaye, kusan sakan biyar tamkar zai cinyeni dasu sannan ya janye batare da yace dani komaiba. ya raɓani zai wuce, hakan yasa na matsa baya na bashi hanya, tafiya ya fara tare da faɗin, “Biyoni”..............✍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
Billyn Abdul:
😂🤣😂🤣😆😆😆Kunsan miyasa nake dariyarnan? Akan yanda kuke ganin kamar bily tsoron Jay takeyi, dukfa halin da take shiga shiba fahimta yakeba, hasalima kallon miskila idan kun lura yake mata, akwai masu samun kansu a irin yanayin bily akan wani ko wata, sai daga baya suke fahimtar dalilin shigarsu irin wannan halin, itama bily lokaci zai warware mata komai har muma mu sami amsa, ina muku fatan alkairi aduk inda kuke, sosai Comments naku na sakani nishadi da sani typing kodama ban niyyaba.
I love you wujiga-wujiga irin trillions ɗinnan🤸🏼🤸🏼🤸🏼 😍😘😍😘😍😘🤗.
Page 6
Ko kaɗan ban fahimci dani yakeba, musamman dana waiga naga rose data fito daga office ɗinsa a bayanna, wani kallo naga ta watsamin mai kama da takaicin tabi bayansa. Numfashi na sauke mai nauyi na shafa ƙirjinna dai-dai saitin zuciyarta dake harbawa da sauri-sauri, duk da na fahimci kallon da rose tai mani sai hakan bai dameni ba, dan bata ita nakeba. Nima fita nai daga wajen, na fito ainahin harabar station ɗin domin nufar sashenmu.
“Ɗi! Ɗi! Ɗi!!” gimba ya danna mata horn kamar yanda Jay ya bashi umarni.
Duk da naji horn ɗin hakan baisa na fahimci da ni akeba, saboda idan akai dubi da sauran jami'ai irina daketa kaikawo a harabar wajen, kowa da hidimarsa.
“K! Wace irin daƙiƙiyace da baƙya fahimtane? A haka kike tunanin zama jami'ar tsaron al'umma!!?”
Maganar Rose a tsawace ta shiga dodon kunnena ina gab da shiga lungu da zai sadani da office ɗinmu. Da sauri na juyo, idona ya sauka akan rose dake huci da jifana da kallon takaici mai nunin tsana. Duk da naji zafin kalaman datai amfani dasu a gareni sai na danne saboda tana sama da ni, a ladabce nace, “Kiyi haƙuri maa! Bansan dani kike ba”.
Tsaki rose ta buga, tare da juyawa tabarni a wajen, wani jami'i dake tsaye kusa damu ya kalleni da tausayawa, dan shi dai yarinyar tunda tazo station ɗin ɗabi'unta birgesa sukeyi, ganin ban fahimci manufar rose ba sai yay min fassara akan nabi bayanta maybe kirana akeyi.
Godiya nai masa, kafin nabi bayanta cikin nutsuwata, sam ban iya sauri ko rikita kaina a tafiya ba koda kuwa a tsorace nake, a yanzunma duk da zuciyata na cike da tunani da baƙin cikin abinda tamin ban rikita kainaba a yayin bin bayanta, can na hangota jikin wata farar mota mai ƙyau da ɗaukar hankali, na cigaba da takawa a nutse gareta, ina isa jikin motar ita kuma tana buɗe gaba ta shige, hakan sai ya sakani a duhu, dan bansan kuma wajenwa zanje ba. Saitin inda take na ƙarasa, na ɗan risina yanda zata ganni ina faɗin, “Gani maa!”.
Kafin ta bani amsa ƙofar murfin baya naga ta buɗe, ita da drivern naga duk sun kalli bayansu, hakanne ya sakani kallon murfin ta waje nima, muryar drivern ta katse min tunani, “Ki shiga” ya faɗa yana nunamin bayan.
Duk da na shiga ruɗani, ga harbawar da ƙirjina keyi hakan bai hanani bin umarninsaba, koda wasa ban kalli waye a bayanba, na shiga kamar yanda aka umarceni, sai da na zauna ne wani mayen ƙamshi ya samu cikakkiyar damar surɗaɗawa a ƙofofin hancina, da sauri nai ƙoƙarin kallon gefena, gabana ya faɗi dan ganin wanda banyi zatoba, fuskarsa babu alamar wasa kamar yanda na gansa yanzu da mukai karo.....
“Sai kin gama kallona zaki rufe ƙofar ne?” muryarsa ta daki dodon kunnena babu zato, kaina na girgiza da sauri ina tattaro busashen yawun bakina da ƙyar na haɗiye, tare da jawo murfin motar na rufe. Nama rasa yanda zan fassara wannan al'amarin sam, gashi yanayin dana tsinci kaina ya hana mani damar yin nazarin daya dace da hakan.
Ɓangaren Rose da Gimba kuwa mamakine fal a rayukansu, gimba shaidane akan bai taɓa ganin rose ta shiga bayan motaba kusa da boss, baima taɓa bata wannan damarba koda a fuskane, idan har kaga wani ya zauna a kusa da shi to lallai sai dai cikin su Aliyu ne, amma yau abin mamaki sai gashi shi da kansa yasa hannu ya buɗema yarinya ƙarama murfin mota, ya kuma bata lasisin zama a gefensa, ‘Anya kuwa?’ ya ayyana akan laɓɓansa yana mai satar kallonsu ta mirror.
Ita kanta rose a kume take da mamaki, ita duk zatonta wani abun zai saka yarinyar, b
ata kawo a ranta wannan abar zuwan jiya hukumarsu har tanada lasisin shiga cikinsu ba, balle harma ta shiga motar da boss yake ciki, a kusa da shima, shi da kansa ma ya bata lasisin zaman, abinda ita bai taɓa bata fuska a kaiba, ko zaman gaban motar da yakema sai ya gadama yake barintayi koda taso hakan kuwa, idan ko bata mantaba wannan itace shekara ta bakwai cif tare da shi tana aiki a ƙarƙashin group ɗinsa, ‘To mi hakan ke nufi?’ tayi tambayar a zuciyarta.
Shi kansa Jawaad mamakin kan nasa yake, amma da yake shi kogine babu mai gane gabansa balle bayansa sai bai nuna koda a fuskaba, hasalima tunda suka fice daga station ɗin kansa na duƙene yana danna tab.. Da alama wani abun yakeyi, sai dai ƙamshin turaren bilkisu duk ya addabi hancinsa.
Kowa da abinda yake kissimawa ransa har suka iso inda yake buƙata, gimba ya samu waje yay fakin, babu wanda yay yunƙurin buɗe motar a cikinsu balle ai tunanin fita, duk suna jiran umarni daga garesa. Shiko yay burus tamkar baiji motar ta tsayaba, sai faman danne-dannensa yake cigaba dayi a tab ɗin.
Sosai zaman ya gundureni, ba komai ya jawo hakanba sai matsuwar da zuciyata ta samu saboda kusancin dana samu da shi tare da lokaci mai tsayi da hakan bai taɓa faruwa ba, da gefen ido na saci kallonsa, sanye yake da wandon jeans kalar bulu, sai t-shirt fara, ta kwanta a jikinsa luf, dan yanda ƙirarsa ta bayyana ta cikakken mutum mai motsa jiki kawai ya isa baka amsa, dogon hannu gareta, amma ya tattareshi sama ya koma iyakar gwiwar hannun, sai agogon fata baƙi mai azabar ƙyau a tsintsiyar hannunsa da gashi ke kwance na alamar jin daɗi, na sauke idanuna bisa yatsansa dake cakalar tab ɗin, sanye yake da zoben azurfa mai tambarin stone babba tamkar diamond, da gani kasan zoben zaiyi tsada koda ba'a faɗa makaba........
“Gimba ka tabbatar nanne wajen?”.
Maganarsa ta katse min dogon nazarin dana tafi na babu gaira babu dalili.
“Eh wlhy boss nanne, kuma wannan shine dai-dai lokacin da a kullum yake zuwa cin abincin safe shi da abokin nashi, a yanzu haka kuma inada tabbacin abokin nasa na cikin wajen, nanda mintuna ƙalilan zai iya fitowa”.
Uffan bai ceba, ya kuma cigaba da sabgarsa tamkar bashine yay tambayar aka bashi amsaba, a fuska dai baiyi kama da miskiliba, abinda kawai na fassara halayyar wannan mutumin shine Ɗan wulaƙanci ne lamba ɗaya kuwa, babu wanda ya sake magana tsahon wasu mintuna, bansan mi sauran sukeba, ni dai ina takure ne jikin ƙofa idona a waje ina kallon shiga da fitar mutanen dake fitowa a cikin wajen cin abincin (Restaurant), kasantuwar gilashin motar mai duhune nasan babu mai ganinmu, sai dai mu mu gansa, hakan ya sakani baje idanuna nake kallon komai daki-daki.
“Yauwa boss ga shinan ya fito” gimba ya faɗa da sauri yana nuna ƙofar shiga da fita na gidan abincin. Nidai kallon wajen nayi, shikam ko motsi baiyiba, bai kuma ɗago ya kalli abinda drivern ya nunaba, sai cewa da yay “Rose! Kibi wancan mutumin, duk yanda zakiyi kiyi magana ta shiga tsakaninku, magana kuma irin wadda zata iya zama mai kusanci”.
“Okey boss” ta amsa da sauri tana buɗe motar ta fice, sai lokacinne naga ya ɗago kansa ya kalli wajen, ba tare da ya sauke gilashin motarba, “Gimba ka tabbatar ka ɗaukesu a hoto mai motsi” yay maganar idonsa a kansu.
Saurin amsawa drivern yayi, tare da buɗe motar ya fice da sauri. Gabana ya faɗi dan ganin an barni daga ni sai shi a motar, sai dai nayi ƙoƙarin kamewa gudun karna zubda darajata da akasan ɗiya mace mai tarbiyya da ita, kallonsu na cigaba dayi kamar yanda shima na fahimci hankalinsa na kansu.
Muna kallo rose ta bigi saurayin da ya fito daga wajen cin abincin yana latsa waya, wayar hannunsa ta faɗi, kusan a tare suka duƙa domin ɗauka, bakin rose ɗin na motsawa, sai dai mu bamajin mi take faɗa, saurayinne yay murmushi suka miƙe tare bayan ita ta samu nasarar tattara wayarsa data tarwatse a hannunta, magana yake mata tana bashi amsa da murmushi saman fuskarta, sai dai shima bamajinsa, ta miƙa masa wayar tana faɗaɗa murmushin fuskarta tamkar yanda shima yake faɗaɗa nashi, bai amshi wayarba
sundai cigaba da magana, sai kuma mukaga suna ƙyalƙyata dariya a tare, hanya ya nuna mata alamar suje, babu musu kuwa tabi umarninsa, tana gaba yana biye da ita har wajen wata Blue ɗin mota, shine ya buɗe mata ta shiga ta zauna sannan shima ya buɗe ya shiga sashen mai tuƙi, munata kallonsu har suka bar harabar restaurant ɗin......
Numfashi ya sauke a hankali yana ɗauke idanunsa da ga wajen, hakan ya sakani nima sauke nawa a ɓoye ina gyara zama cikin alamar takura, addu'ata da fatana bai wuce drivern ya dawo cikin motarba kona samu sauƙi, babban fatana kuma yace na koma gaba inda rose ta tashi, sai dai har tsahon mintuna biyar da barin su rose gidan abincin baiko motsaba balle ya kalleni, saima kansa da ya kwantar jikin sit ya lumshe idanu, “Ƙil!-ƙill!!” tab dinsa tai motsi alamar shigowar saƙo, bai motsaba, hakan yasa mamaki ya kamani......
“Ɗauki ki duba mi tace?” ya faɗa ba tare da ya motsaba. Gabana ya faɗi, dan nadai fahimci dani yake, kuma yana nufin tab.. Ɗin tasa zan ɗauka, ganin bai sake maganaba ne ya sakani kallonsa, a ɗarare nace, “Dani kake sir?”.
“A'a da kaina nake” ya faɗa a daƙile......
Kafinma ya rufe baki na kai hannu na ɗauki tab ɗin da ya ajiye a tsakkiyarmu, gabana sai wata irin faɗuwa yake tamkar zan haɗiye zuciyata a cikin bakina, madannin na danna ta kawo haske, wani haɗaɗɗen hotonsa ya bayyana, duk da son kallon hoton da naji ya tsargamin hakan baisa na tsayaba, saima mamakin ganin babu lock a jikin tab din ne ya kamani, naja hoton yay sama kawai, a take apps da yawa suka bayyana, baza ido na shigayi wajen neman messeges app, da ƙyar na tsaida hankalina na ganosa, ina buɗewa kuwa da sunan rose na fara cin karo, na buɗe saƙon nata, abinda ta turo bai shige kalmomi hamsin ba. “boss ya buƙaci nabisa, duk abinda ake ciki zakaji daga gareni”.
Cikin ɗan rawar baki nakaranto masa kamar yanda ta rubuto da harshen turanci, bai motsaba, bai kuma tanka mani ba, hakan yasani ajiye tab ɗin ina mai satar kallonsa, sai da ya ɓata lokaci kafin ya jehomin tambaya.
“Ya sunanki?”.
‘Ikon ALLAH’ na faɗa a raina kafin na bashi amsa da, “Bilkisu Adam makaho”.
Yanda ya buɗe idanu da sauri a kaina ba ƙaramin firgitani yay ba, mayun idanunsa masu saka tsigar jikina tashi ya dasamin, bansan miya bashi mamakiba, sunan nawane? Kokuwa na babana? Kokuwa makahon dana ambata a ƙarshe?. bansan amsarba, bani da ƙwarin gwiwar tambayarsa kuma. Tsahon minti ɗaya da sakanni yana kallona kafin ya janye idanunsa yana motsa baki tamkar mai son cewa wani abu,ni dai ta wutsiyar ido nake kallonsa shi da jin kansa.
Baice dani komaiba ya buɗe motar ya fita, ajiyar zuciya na sauke, dan fitar tasa sai naji kamar ya bani wani ƙaton filin cin karena babu babbaka ne.......
“Ko sai an fiddoki?”. Furucinsa ya daki kunnena, da azama na buɗe murfin na fice nima, gani nai ya wani zubomin idanu, bansan mi yake nazartaba daga gareni, sai jefani a ruɗanin zuciya dana takurar kaifin idanunsa da yayi, hakan yaja nai ƙasa da kaina dan bazan jura kallonba.
Takunsa kawai naji alamar ya matsa daga kusa dani, na saci kallonsa, sai naga yana ƙokarin ciro abu daga cikin but ɗin motar da ya buɗe, nufonin da yayne ya sani saurin ɗauke idona, ya miƙomin farar coat ta mata da tsayinta zai iya kaiwa gwiwa, ban musaba na amsa, sai dai ina buƙatar ƙarin bayani, “Saka” ya faɗa yana wuceni.
Sosai naketa mamaki, na warware rigar na saka a jikina saman Uniform ɗin dana sanya, sai ya zam rigar ta ɓoye bayyanar ni wacece, baƙin wandon kawai ake iya gani ta ƙasa, daga sama kuwa farin baby hijjab ɗinane ya bayyana, sai rigar ta fiddamin da wani tsari daban daya bayyanar da sirrintaccen kwarjinina da wasu ke iya ambata da ƙyawu. Bai cemin komaiba yay gaba na bisa a baya, dan zuwa yanzu kam na fara fahimtar hallayarsa da hanyoyin maganin zama da shi.
Sai da muka gabato shiga ƙofar wajen sannan ya tsaya muka daidaita tafiya, ƙasa-ƙasa na tsinkayi muryarsa yana magana.
“Ki kula sosai, sannan ki tabbatar da yanayinki ya canja tamkar munada dangantaka, idan kikamin shirmen da aikina ya buɗe
lallai sai kinyi nadamar hakan”.
Sosai maganganunsa suka tsirgamin zuciya, dan kuwa ban gama fahimtar ma'anarsu ba balle manufarsu har muka ƙarasa shiga wajen.
Wajen yay bala'in haɗuwa, daga gani kasan masu abokan magana a aljihune kawai keda hurumin shigarsa, dan danan akai mana tarba ta mutuntawa, yanda ya ƙawata fuskarsa da murmushi ne ya ɗauren kai, hakan yasani nima aro irin basajar tasa na yafama kaina ina murmushin, ɗaya daga cikin yaran wajenne ya nuna mana wajen zama, bayan mun zauna yake tambayarmu komi muke buƙata.
Boss ya juyo yana kallona fuskarsa shinfiɗe da wani murmushin da ya kusa zautani, “My princess! Mi kike buƙata?”.
Wata masifar harbawa zuciyata tayi, kaɗan ya rage ban fallasamu ba, nai azamar haɗiye zuciyata dake niyyar fitowa ta baki saboda salon da yay amfani wajen kiran sunana da yanayin fitar sautin, da ƙyar na iya dai-daita kaina nai wani farin da bansan na iyaba da idanu, ina wani narke murya nace, “Duk abinda ka zaɓa mana yayi my king”.
Ɗauke idanunsa yay daga kaina, har zuwa yanzun fuskarsa ɗauke da murmushin da ya fidda lotsar dimples ɗinsa masu ɗaukar hankali, ya duba waiter ɗin yana bashi umarnin ya bashi list ɗin abinda suke da shi ya duba.
Da girmamawa ya amsa yana barin wajen, saurin yin ƙasa nai da idanuna ganin ya maido kallonsa gareni, murya ƙasa-ƙasa yace, “Ina sake gargaɗinki a karo na biyu”.
Kaina na jijjiga masa ina saurin gyara yanayina. Sallama wata matashiyar budurwa taimana saɓanin wanda yazo ɗazun, sanye take da Uniform ɗin wajen itama, cikin girmamawa ta ajiye goran ruwa biyu da kofuna dake saman tire ƙarami, kafin ta miƙa masa ɗan littafi dake a hannunta. Amsa yay yana dubawa, tare da yin alama da pen ɗin data haɗa masa da shi akan duk abinda muke buƙata, baifi sakan sha biyarba ya miƙomin littafin yana fadin, “Duba yayi?”.
Amsa nayi ina kuma matse nutsuwata, nai nazarin duk abinda ya zaɓadin kafin na ɗago ina murmushi, cikin salon da bansan nayiba na ɗaga masa gira ɗaya da juya ƙwayar idona kaɗan alamar yayi.
Idanunsa ya lumshe tare da buɗewa a lokaci ɗaya yana sakin wani lallausan murmushi da yafi na ɗazu.
‘Innalillahi....’ Na iya ambata ina saurin maida fitsarindake neman kufcemin.
Tana barin wajen ya kalleni da sauri, murya ya rage ƙasa sosai, wanda yake nesa damu zai ɗauka soyayya mukeyi, maganar da ya faɗamince ta sakani jinjina masa kai da sauri, ina kuma murmushi, badan tanada alaƙa da murmushin nawa bane, sai dan kawai barin murmushin akan fuskar tawa ya zama tilas saboda kiyaye gargaɗinsa...........✍
🙄saura kuma ai gulmar Jay😏
Barka da juma'a.
Page 7
.................Mintuna kaɗan budurwar ta dawo da tire babba a hannu, wanda aka jero abubuwan da muka buƙata a kansa.
Tana ƙoƙarin ajiyewane Jay ya miƙa hannu zai ɗauki ruwan da aka fara kawo masu, a salon da babu wanda ya isa fahimtasa har bily bata kulaba ya tanƙwaɓi tiren ya suɓuce, jikake “Tarats!!! Tass! Tatass!!” kwanikan da suka zube na fashewa, abinda ke cikinsu gaba ɗaya sun koma jikinsu sun wankesu, duk jikinsu ya ɓaci daga shi har bily da bata san mafari ba, a take duk hankalin mutanen dake kusa dasu ya dawo kansu.
Na ɓata fuska saboda harga ALLAH banji daɗin yanda jikina ya ɓaciba. Cikin langwaɓe kai na kallesa kamar zanyi kuka.
Da ƙyar Jay yay ƙoƙarin haɗiye dariyar dake neman kufce masa saboda yanda Bily tayi fuska kamar zata fasa ihu, ga mai da yay tsalle harkan fuskarta sai naso yake.
A fusace na miƙe saboda ganinma dariya yake neman yimin, dan da gaske haushi naji har raina, maimakon ya mata faɗa amma kuma tsabar wulaƙanci yake neman yimin dariya a cikin mutane, bamma san sanda na fara zazzaga mata masifa akan tayi hakanne da gangan ba, yanda ta rikice ba ƙaramin tausayi ta baniba, amma kuma uwar mi take kallo da zata wankemu haka?, shima jinake kamar na juya na talle masa ƙeya yasin.
Jawaad ya tsaya kawai yana kallon bakin Bily dake masifa, babu shiri murmushi ya suɓuce masa, ganin tamkar abin nata da gaskene shima sai ya miƙe, cikin son maidota hayyacinta ya nema riƙo hannunta, amma sam taƙi yarda, dan danan wasu ma'aikatan nasu sukazo, da alama suɗin manyane, haƙuri suketa bamu amma naƙi saurarensu, daga ƙarshema nai ficewata, shikuma yay azamar biyoni yana faɗin, “princess! Princess! Please ki tsaya mana”.
Ƙo juyowama banyiba na nufi motarmu na buɗe zan shige, saurin riƙe murfin yayi yasha gabana alamar hanani shiga motar, ya wani marairaice yana lallashina, wlhy da kunsan yanda zuciyata ke harbawa sanda muke a wannan yanayin da kun bala'in tausayamin, a haka budurwar da wasu ma'aikatan wajen suka iso suka taddamu, haƙurin suka cigaba da bamu, sai da muka ɗan garasu da kalamun cewar bazamu sake zuwa wajenba tunda basusan kimar Customers ba kafin na nuna na haƙura da ƙyar, dan zuwa yanzu na dawo hankalina akan shirinmu.
Sun buƙaci mu koma wajen a bamu wani abincin amma na tubure akan bazan koma ba, sai dai a haɗo mana takeaway, ba musu suka amince da bukatata, ganin sunbar wajen ne ya sani sauke ajiyar zuciya ina matsawa baya saboda kusancin da muka samu ni da shi neman karya ƙwarin gwiwa da nake bama kaina ya keyi, gashi yay masifar tsareni da idanunsa.
Shima matsawa yayi, ya nuna min mota alamar na shiga yana zubamin harara, “saurin shigewar nayi kuwa, ya rufemin murfin ya zagaya ɗayan ɓangaren, da sauri gimba dake bayanmu tsaye yana kallon dramar tamu ya buɗe masa, hanasa rufewa yayi, saima ya zauna ƙafafunsa duka a waje. A haka budurwar ta dawo ɗauke da takeaway ɗin da muka buƙata, gimba ya amsa ledojin, shi kuma ya miƙa mata atm card ɗinsa tare da wata takarda yana magana ƙasa-ƙasa, “Saboda baƙwason ya tona muku asiri kuka kasheshi?”.
A firgice budurwar ta kalli Jay, sai kuma ta hau waige-waige jikinta sai tsuma yakeyi.
Ya sake faɗin, “Ki daina ɓatama kanki lokaci, akwai address ɗin inda zaki sameta (ya nuna bily) a jikin takardar nan ranar lahadi, yarage naki kizo ko kiƙi zuwa, sauran bayani mahaifinki zanyimawa”.
Sake rikicewa tayi, jikinta sai wata masifar tsuma yakeyi. Yanda taketa kallonsa a firgicene ya sakani tabbatar da maganar bamai daɗi ya faɗa mataba, tabar wajen da sassarfa, yayinda gimba ya take mata baya domin amso atm ɗin idan sun cire kuɗinsu.
Wato dai duk yanda nake tunanin aikin nan namu yafi ƙarfin tunanina, irin wannan makirci haka tamkar wani shirin film.
Gimba bai wani jimaba ya fito da ɗan hanzarinsa, motar shiru tamkar babu mutum mai numfashi, nidai takurace ta hanani yin ƙwaƙwƙwaran motsi, danma ALLAH ya soni yanzu a gaba nake ba kamar yanda muka zoba, shiko bansan mi yakeyiba, dan nakasa kallonsa koda ta mirror ne, abinda ya faru a wajen da
Billyn Abdul:
Page 8
.............Jawaad dake kallonsu daga ciki yay murmushi kawai yana girgiza kai, dan ya fahimci wani abu daga Rose ɗin. hannu ya miƙa ya buɗe murfin ɗayan gefensa, Hafiz dake ta wajen tsaye yace, “Kinga mai sunan Momcy zo tanan”.
Amsa masa nai da “to” na nufi can duk da a raina banso hakanba dai, sai dai haka kawai naji inason bama shegiyar rose ɗinnan haushi yanzun, dan na kula sam bata ƙaunata dai, su mutanen duniya dasun ganka shiru-shiru saisu dinga ɗaukarka sakarai ko bakasan abinda kakeba, indai nice kuwa tasa kanta a ramin damisa wlhy. Ina shiga Hafiz ya rufe murfin, gimba yay ma mota key, bansan yanda aka ƙare da rose ba mukabar gidan bayan oga Jabeer ya shiga gaba bisa umarnin Boss da yay masa magana.
Har muka isa station oga Jabeer da gimba na hira, amma ni dashi kamar mun haɗiyi kwaɗo. Yanda na takurama babu abinda nake buƙata kamar mu iso na sauka nidai. koda gimba ya tsaida motar ban fitaba saida duk suka fita, baiko kalli kowaba a cikinmu yay gaba abinsa zuwa hanyar office ɗinsa, Jabeer ne kawai ya kalleni fuskarsa ɗauke da murmushi yace, “To mai sunan mom sannu da ƙoƙari, ki ƙara ƙaimi da jarumta dan aiki da boss sai jarumi na gaske”.
Duk da ban fahimci zancensaba nai murmushi ina ɗaga masa kai, sannan nace, “ngd” a ƙasan raina kuwa ina tunanin wai sunan wa? gareni suketa wani boyen suna.
Murmushi yay shima, ya nunamin cikin motar yana faɗin, “Karki damu babu godiya a tsakaninmu, ki tattara masa tarkacensa kibisa office dasu, ai kinsan office ɗin ko?”.
Tamkar na fasa ihu haka naji, amma sai na daure nace, “Ban taɓa shigaba dai, amma na sani”. Yace, “To Alhmdllh saiki kaimasa ni na wuce office ”. Kaina na jinjina masa batare da nace komaiba, shima yay murmushi kawai ya wuce abinsa.
Duƙawa nai na tattaro wayoyinsa da tab da wasu takardu daya bari sai bindiga da keys da bansan kona miyeba, sai ƙamshi suke tamkar suma turaren ake fesa musu, ledar takeaway ɗinmu gimba ya bani, ban musaba na amsa, dan duk zatona duk shi zan kaimawa, sallama nai masa na nufi hanyar da zata kaini office ɗin da kaya riƙi-riƙi saikace wata ƴar gudun hijira, danma na barma gimba ledata akan idan na fito zan karɓa dukda yacemin gida zaije. Sai da na hau lifter domin office ɗinsa na hawa na uku ne, sai saƙawa da kwancewa nake ina zancen zuci, na iso shataletalen da ya raba hanyoyi uku na offices ɗinsu, ɗaya nasan hanyar dazata sadaka da offices ɗin su B.G ne, wanda suke a hawa na ƙarshe, sai kuma ɗayar hanyar bansan offices ɗin suwayeba a wajen, sai ɗayar hanyar da naga ya fito ɗazun, nan na nufa kai tsaye, dogon corridor ne da ƙofofi jere kusan goma, hakan yasa na fara bi ina karanta rubutun saman gudun kuskure, sai da naje na bakwai sannan naga an rubuta Captain Jawaad A yusif, inada tabbacin nanne, dan tunda aka gayamin cikakken sunansa bantaɓa mantawaba koda a second ɗaya ne kuwa. Sai da na daidaita kaina da sake ƙarfafa zuciyata da ke neman faso ƙirjina ta fito sannan nai knocking har sau uku, amma banji an amsa maniba, nai jim kusan na minti ɗaya kafin na ƙara yin knocking ɗin kamar mai tsoron a jita, nanma shiru, nakai hannu zan sake aka amsa mani. Ajiyar zuciya na sauke a hankali kafin na tura ƙofar da sallama na shiga, office ne da ya amsa sunansa office, dan kuwa yayi ƙyau, babu wasu tarkace komai kuma tsaf, ga mayen turarensa ya kama office ɗin haɗi da freshener mai daɗin ƙamshi, sai suka bada ƙamshi na musamman, kallo ɗaya naima inda yake zaune a kujerarsa ta office na duƙar da kaina, shima kuma bai kalleniba, baikuma cemin komaiba, yanata rubuce-rubucensa hankali kwance tamkarma baisan wani ya shigoba. Jinai tsayuwar ta isheni, dan haka na gyara kaɗan ina yamutse fuska, batare dana ɗago na kallesa ba nace, “Sir gashi inji oga Jabeer”.
Jay da tun ɗazu ya daina rubutun ya kwantar da bayansa jikin kujerar kawai yana kallonta da jinjina shegen miskilancinta ya lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci ɗaya, sai faman goga ƙasan biron hannunsa yake a jikin laɓɓansa, ko motsi baiyiba ballanta ya amsa mata. Tsabar miskilancin yarinyarne kawai ke bashi mamaki, ya ɗan taɓe baki t
are da maida kallonsa ga Computer ɗin dake kan desk ɗinsa, bironsa ya ajiye yana lafe jikin kujerar ya fara sarrafa keyboard ɗin Computer ɗin.
Ƙaran danna keyboard da najine ya sakani ɗago idanuna nai masa kallon second 2 na janye, karan farko a rayuwata dana sake jinjina wulaƙancin mutuminnan, ‘kenan bazai tanka mani ba komi yake nufi?’ na ambata a zuciyata ina maijin takaicinsa. Satar kallonsa na sake yi sai muka haɗa idanu, da sauri na janye nawa ina tura baki gaba batare dana san nayima hakanba.
Sautin fitar ƙaramin tsakinsa ya sakani saurin sake kallonsa, yako dallamin harara alamun har yanzu idonsa a kaina suke, “Kin zama bodyguard ɗinane shin?” yay maganar a hankali kamar baison yi.
Kaina na girgiza masa, duk da bani da tabbacin kallon nawa yake har yanzu, takawa nai zuwa gaban tebir ɗin na ajiye kayan harda ledar abincin, ban kallesaba bai kuma tankaminba na juya zan fita.
“Zonan”
Na tsinkayi umarninsa. Juyowa nai kaina a ƙasa batare dana kallesa ba, “Zauna” ya sake faɗa a daƙile. ‘Kai nikam na shiga uku da wannan mutumin’ na ambata a zuciyata ina mai jina a matuƙar takure, zuciyata sai faman harbawa take da sauri-sauri. Shiru office ɗin ya sake ɗauka na kusan minti ɗaya, sai ƙarar keyboard da yake dannawa kawai kake ji. Knocking ƙofa akai ya bada izinin shigowa, matashin sauriyi ma'aikacinmune ɗauke da takardu a hannu, kallo ɗaya nai masa na ɗauke idona, duk da shi na lura sai kallon mamakin ganina a nan ɗin ya keyi, har takai boss ya daka masa tsawa.
“Kallon mutane aka turoka yine!?”.
Cikin sauri da ladab yace, “Sorry sir”.
Banji ya tanka masaba, danni kaina a duƙe banma ɗagoba, sai sautin siririn tsakinsa naji kawai, shidai saurayin sai faman nanata kalmar haƙuri ya keyi kusan sau huɗu kafin ya fara masa bayani akan takardun hannunsa, banji ya tankaba, hakan yasani satar kallonsu, gani nai ya miƙa hannu ya amsa takardun yana dubawa, kafin ya ɗago ya kallesa da sake miƙa masa ta kardun yana faɗin, ”Ka kaisu office ɗin Lieut..; Richard, kace ya duba, zuwa anjima sai yazo dasu ina nemansa”. “Okey sir” ya faɗa cike da girmamawa kafin ya amsa ya fita ko sau ɗaya bai sake gigin kallon sashen da nakeba.
Ɓoyayyen numfashi na sauke bayan ficewarsa, saima naji yaɗan bani tausayi........
“Bani malt.. A cikin fridge”. maganarsa ta dawo dani hayyacina, miƙewa nai ina ɗan dube-dube a office ɗin danson gano fridge ɗin, shi kuma yaja ledan abincin ya buɗe, ganin fridge ɗin da nayi bayansa kaɗan ya sakani nufar wajen, kasancewar ƙaramine madaidaici yasa saida na sunkuya, malt ɗin ne kawai a ciki da coc... nidai na ɗakko abinda ya sakani tare da kofin dana gani a saman fridge ɗin kusan guda shidda saƙale jikin wani ƙarfe mai ƙyau, gabansa naje na ajiye ina haɗiye yawu da ƙyar, dai-dai yana buɗe takeaway ɗin gasashen naman kaza daketa ƙamshi, ina ajewa nabar wajen na koma inda na fara zama a ɗaya daga kujeru biyun dake gaban tebir ɗinsa, ganinai kawai ya turo naman gabana, na ɗago na kallesa muka haɗa ido, kuma tamke fuska yay ya nunamin naman. Tamkar zan fasa kuka nace, “Nifa na ƙoshi, azumima nakeyi”. Banza yaymin tamkar baima jiba, ya ɗauki gwangwanin malt ɗinsa ya ɓalle hancin ya kai baki, kafin ya ajiye ya maida hannunsa kan keyboard ɗin Computer ya cigaba da daƙilarsu. Mun kwashi kusan minti uku a haka, bai tankaniba, nikuma banci namanba dukda ƙamshinsa ya addabeni.
kamar daga sama naji yace, “Karki bari na sake miki magana, kiyi ki fitarmin a office”.
Batare dana shiryaba bakina ya suɓuce wajen faɗin, “Toni nacefa azumi nake, sokake na karya azumina ne?”.
Tunda ta fara magana ya dakata daga daƙilar Computer'n ya zubama laɓɓanta idanu da kumatunta da take ɗan kumburawa, sai da takai aya sannan ya janye ya maida ga abinda ya keyi batare da ya nuna yamaji mita faɗaba.
A matuƙar takure nake gaba ɗaya bugun zuciyata da numfashina sun dawo a maƙoshina, kaɗan nake jira na amayota kowama ya huta, yaƙi kulani, sannan yaƙi cemin na tafi, ganinfa yama manta dani saina miƙe abina na nufi hanyar ƙofa, bai tanka maniba har saida na kama ƙofar zan
buɗe sannan yace, “An taɓa karyaki?”. Cak na tsaya, ni ban fitaba, ni ban komaba, bamma iya sakin mariƙin ƙofarba saboda yanda furucinsa ya daki ƙirjina, sai da na shaƙi iska na fesar sannan na juyo a hankali ina kallonsa, kauda kaina nayi saboda ganin shima niɗin yake kallo, ya wani haɗe fuska tamkar hadarin tsakkiyar ogusta.
“Idan kika bari na sake miki magana ki kuka da kanki”.
A yanda yay maganar da tsananin kaushi sai tsoro ya sake tsirgamin, dama dai ƙarfin hali nake kawai, dole na dawo na zauna ina sake haɗe fuska dan nikam gaskiya an sakama rayuwata ido, komawa nai kujerar dana tashi na zauna. Ina zama shikuma yana miƙewa ɗauke da wasu takardu ya fice daga office ɗin abinsa batare da yace dani komaiba. Na sauke nannauyan numfashi ina kallon naman, bani da zaɓinda ya wuce nacin kawai kodan ya barni na tafi, na ɗauki cinya nakai bakina ina ambatar bismilla, ɗanɗanon naman da laushinsa ya sakani lumshe idanuna, ko ba'a faɗaba dama namannan zaiyi ɗankaren daɗi ai, ban ankaraba na laƙume cinyar na sake ɗaukar wata tsoka irin ta haƙarƙarinan, (Damafa inaso shegen gulma ne. Lol) ina gab da cinyeta aka turo ƙofar da azabar ƙarfi aka shigo, a tsananin razane da ganin wanda ya shigo ɗinne ya sakani miƙewa babu shiri ina kallonsa. Shima idanunsa ya zubamin tamkar zai cinyeni da su.
“Ubanmi kikeyi nan Bilkisu?!!”
Idanuna na lumshe saboda tsawar tashi ta rasha kunnuwana, na buɗe a hankali kansa, cike da dakiya na zubasu a kansa nace, “Yah Qaseem miya faru?”.
Wata malalaciyar harara ya zubamin kamar zai juye idanunsa ƙasa, ya fara takowa inda nake, taku baifi ukuba tsakaninmu ya rage aka buɗe ƙofar office ɗin aka shigo. Ni da shi duk kallon ƙofar mukai, sai dai shi a take ya janye nasa idon yana jan uban tsaki. Nikam numfashi na sauke a ɓoye dan koba komai na samu kuɓuta daga wannan yunƙurin na yah Qaseem da bansan mi zuciyarsa ke kissima masa yaminba.
Jay da ya shigo kuwa kallo ɗaya yay musu ya ɗauke kansa ya taka zuwa ga kujerarsa ya zauna.
A mamakina sai naga yama cigaba da daƙilar Keyboard ɗin Computer ɗin hankalinsa kwance kamar baisan damuba. Shima yah Qaseem ɗin bai tanka masaba ya kalleni yace, “Wuce muje”.
Jawaad daketa danne-dannensa batare daya ɗagoba yace, “Kai ka kawotane?”. Dogon tsaki yah Qaseem yaja yana damƙar hannuna da faɗin, “Miye na azarɓaɓi ƙaramin tsagera, ai zan dawo kanka idan na gama da ita”. Ya ƙare maganar da fisgar hannuna muka nufi ƙofa. Jinake tamkar na kurma ihu, ‘Nikuma wannan wace fitinace na shigo ciki haka?’..........
“Wlhy kika fita daga office ɗinan saina saɓa miki kamanninki!”
Muka tsinkayo kakkausan furucin boss yayinda yah Qaseem ya murɗa ƙofar zamu fice. Bani kaɗaiba hatta da yah Qaseem ɗinma tsayawa daga yunƙurin fitar yay, ya juya yana kallonsa, nidai kaina a ƙasa na gaza kallon kowa a cikinsu, addu'ar ALLAH ya kuɓtar dani daga tsakaninsu kawai nakeyi a raina, dan bansan wazan bijiremawaba? Wakuma zanma biyayya ba?. Yarfar da hannuna yah Qaseem yay ya nufesa, zafin da najine ya sakani durƙushewa a wajen ina sakin siririyar ƙarar azaba.
Qaseem daya ƙarisa gaban Jawaad ya bugi tebir ɗin gabansa har wasu abubuwan na faɗuwa, “A matsayinka na ubanwa zaka saɓa mata kamannin?”. Ko motsi Jawaad baiyiba balle ya kalli Qaseem, aikin gabansa kawai ya cigaba dayi hankalinsa kwance. A kausashe Qaseem ya sake maimaita tambayar tamkar zai mari Jay ɗin. Ɗago idanu Jawaad yay ya zubasu akan Qaseem, cike da gadara yace, “Qaseem fitarmin daga office!!”.
“Anƙi a fita, kayi duk abinda kaga zaka iyayi” Qaseem ya maida masa amsa a zafafe shima.
Jawaad bai sake magana ba, ya miƙe ya nufi Bilkisu dake durƙushe tana hawaye saboda hannunta dake zugi.
Tsayuwar mutum kawai naji a kaina, cikin bada umarni yace, “Tashi”. Miƙewa nai babu musu, na saci kallonsa, ganin shima kallon nawa yakene yasa na janye nawa ina goge fuska, kafin ya sake wata magana yah Qaseem yazo ya shiga tsakkiyarmu, ”Wuce muje” ya faɗa yana nunamin hanya, haushin murɗamin hannu da yayne yasa naƙi motsawa. Ganin naƙi motsawarne ya sake hasalashi ya
ɗaga hannu zai saukemin mari.
Rufe idona nai da sauri naja baya saboda masifar firgita da nai da ihun da yaymin akai, na ƙanƙame jikina ganin ya ɗaga hannu zai makeni, shirun da naji yasani ɗago kaina kaɗan naga miya hanashi dukan nawa da yay niyya.. Saurin waro idanu nai waje ganin boss riƙe da hannun Yah Qaseem da ya ƙara kumbura sai hura dogon hancinsa yake.
“kika fita saina karyaki a office ɗinan Miemaa” boss yay magana a dake kamar yanda na fahimci halittarsace yin magana kai tsaye koda a gaban wa yake. Saurin duƙar da kaina nai saboda tsatstsareni da yay da idanu, nai baya daga kusa dasu cike da tashin hankalin sakani tsakkiya da sukai.
yah Qaseem ya fisge hannunsa dake cikin na boss ya kai hannu zai damƙoni ina ƙoƙarin matsawa. Cikin matuƙar zafin nama boss ya fisgi yah Qaseem ɗin gefe, hakan sai ya bani damar mannewa a bango na sake musu kuka kawai, dan zuciyata bazata iya ɗauka ba.
A cikin tsagwaron fushi Qaseem ya damƙi wuyan rigar Jawaad zai shaƙeshi, “Amma kasan zan iya illataka ko?”.
Murmushi Jawaad yayi yasa hannu ya ture hannun Qaseem dake damƙe da wuyansa, cikin halin ko in kula yace, “Ka illatanin mana Qaseem, kai wai wace irin banzar zuciyane da kai haka? Mace zaka ɗaga hannu ka daka?”. A matuƙar masife Qaseem yace, “ina ruwanka? Miye matsalarka?” baki Jawaad ya taɓe yana watsa hannayensa da ɗage kafaɗa yace, “Banda” ya ƙare maganar da juyawa zai koma kujerarsa. Saurin maidoshi baya Qaseem yay, hakan ya saka Jawaad tsayawa sai dai bai juyo ya kalli Qaseem ɗinba, ƙoƙarin danne zuciyarsa yake dan bayaso su raba hali gaban yarinyarnan kamar yanda ya kula Qaseem yana buƙata. Cikin nunashi da ɗanyatsa Qaseem yace, “Wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe da zaka sake saka Bilkisu! cikin lamarinka, itaɗin matar dazan aurace, ya rage naka ka kiyayi ko kaci gaba”.
Rumtse idanu Jawaad yayi saboda jin yanda Qaseem ya ambaci sunan mahaifiyarsa gatsal, ya juyo a hankali yana kallon Qaseem cikin ido, cikin ƙunar zuciya yace, “Ko wacece ita a wajenka baya gabana, sai dai kai kasani baka isa hanani sakata aikin dana gadamaba tunda har tazo station ɗinnan a ƙasana, kasa a ranka yanzu aka fara wasan kuma, ina gargaɗinka Ka kiyayi kai hannu kan mace da nufin duka”. ya ƙare maganar a wani irin yanayin rainin wayo. Hakan sai yay masifar sake fusata Qaseem, a tsawace yace, “Matsayinka na ubanwa?”..............✍
Qaseem team & Jawaad team banda faɗa kuma 🚴🏼🏋🏼🤼🏼😂😖.
Ina Bil-Qas team nidai😜🤫🤸🏼.
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻