*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Barka da sallah 'yan uwa. Fatan ansha ruwa lafiya. Allah ya amshi ibadunmu ya kuma kawo ma na ƙarshen wannan annoba ta covid 19. Amin*
*Free page*
0️⃣0️⃣1️⃣
Idon sa ya rintse, lokaci guda kuma ya daka tsawa "get the hell out of here!" Gigicewa yarinyar ta yi, jikin ta na rawa.
Sai da ya sake ma ta magana cikin tsawa " out of my office!" Sannan ta fita daga office ɗin a bircike, yai tsaki tareda jawo wayar landline ya danna kira, cikin muryar shi mai ɗauke da amo ya ce " Anas, i need another secretary"
Bai saurari mai zai ce ba ya ajiye phone ɗin. Ya ja tsaki sannan ya fara latsa laptop da ke gaban shi...
"Ene what happened?" Matashin saurayin ya tambayi yarinyar da ke harhaɗa files ta na yi ta na share ƙwalla.
Ta ɗago jajayen idanun ta ta kalleshi ba tareda ta ce komai ba sannan ta cigaba da abinda ta ke yi.
A hankali ya ce " please stop crying, i'll talk to him" ya wuce cikin katafaren ofishin da ya fi kowanne girma acikin kamfanin.
Har yanzu aiki ya ke yi, shi ya sa ko da ya ji alamar buɗe ƙofa bai ma ɗago ya ga waye ba. Ya san sarai mutum ɗaya ne zai iya shiga ma sa office karangatsau haka.
" what exactly is your problem, wai kai for once ba za ka iya haƙuri da juriya da zama da mutane ba. Yanzu mi ta ma ka dan Allah?"
Ya fi minti biyu bai ce komai ba kuma bai ɗago ba.
"Najeeb magana fa na ke yi"
Sai a lokacin ya ɗago kykykyawar fiskar shi ya ce " Oh na ɗauka ƙara ka kawo ai"
Ya ja kujera ya zauna sannan ya kalli Najeeb ya ce " wannan kuma mi ye matsalarta?"
Kamar abin da Najeeb ɗin ke jira kenan ya fara kwarwa " the girl is so dumb, imagine jiya na ba ta report ba ta yi ba, wai ta manta. Yau kuma na ba ta wani, ta je ta yi min shirme....."
" ya isa haka ba sai ka kai ƙarshe ba, na san ƙarshen labarin. Yanzu ya ka ke so ayi?"
"Change her, May be wannan karon ka kawo namiji"
" kamar da gaske, Secretary biyu kafin wannan ba maza ba ne, su ma ba korar su ka yi ba"
Najeeb ya ɗan haɗa rai yace " look dude, ka san yanda na ke son aiki na, you either work perfectly or you leave. Ba na son shirme"
"Na ji za a nemo wani, but gaskiya Najeeb this time around ka yi haƙuri da koma wanene"
"Yallaɓai Anas na ji na amince. Sai me kuma?"
Anas yai dariya ya ce " duk yadda ka ce Engineer"
...............................................
Waya ce ɗare a kunnen ta lokacin da ta tsaida mai keken. Sai da ta zauna sannan ta ce Muda-Lawal ta ci gaba da waya wanda duk rabi masifa ta ke yi.
Ta na ajiye wayar ta kalli ƙeyar mai keken ta ce " nawa ne?"
"Ɗari da hamsin" ya faɗi hankalin sa na tuƙin da ya ke.
" hala ka fara fashi da makami ko?"
Mai keke ya tunzura ya ce" ban gane maganar ki ba"
"Idan na baka tamanin ka sa makami ka ƙwaci sauran kuɗin"
" gaskiya 'yan mata idan ba za ki ba da ɗari da ishirin ba ki sauka" ya na magana ya na rage gudun keken.
" sai ka zo ka fitar da ni ai"
Mai keke ya ja keken sa ya tsaya "sauka dan ba zanje a naira tamanin ba"
" duniya da 'ya'yan ta. Idan na sauka a keken nan na zama turmi" ta daka ma sa tsawa "za ka ja keken ka mu tafi ko dai!"
Mutumin da ke gefen ta ya ce " mai keke mu je zan biya kuɗin"
Sai a lokacin ta kalli mutumin. Saurayi ne dan a ƙalla ba zai wuce shekara ishirin da tara zuwa talatin ba. Ta ce "yawwa shishshigi. An gaya ma ka ban da ɗari da hamsin ɗin biyan sa ne?"
"Allah ya ba ki haƙuri" ya faɗi ya na kauda kai gefe saboda yadda ta tsare shi da manyan idanun ta.
"Ba zan gaya ma ka sunana ba hakanan ba zan ba ka numbata ba dan na san dalilin shishshigin kenan"
Murmushi yai ba tareda ya kalleta ba. Mai keke ya cigaba da tafiya, a hankali mutumin ke satan kallon ta sai dai ita hankalin ta ya karkata ne kan wayan ta. Chan ta lura ya zuba ma ta ido. Ta ɗago idon ta da sauri ta ce "Malam kallon yai yawa, idan idon ka bai faɗo ba zan ƙwaƙwaleshi da kai na"
Mai keke ya fashe da dariya a zuciyar shi ya na mamakin masifar budurwan nan.
Har aka iso inda za ta sauka ba wanda ya tanka ma ta. Ta na sauka ta fito da naira ɗari biyu ta miƙawa mai keke ta ce ban ɗari da Ishirin. Mai keke ya ce "Oga ya biya mi ki duka kuɗin"
" chan ta matse mu ku " ta faɗi tareda maida kuɗin ta cikin purse.
Ta ƙarasa wajen park ɗin ta na tafiya ta na waya. Yayinda hayaniyar masu mota ke tashi a tashar.
"Dan Allah baiwar Allah ki saurare ni" ta ji an faɗi a bayan ta, ta juyo a tsanake.
"Sai aka yi ya?"
Yadda ta yi maganar da faɗa-faɗa ya sa ta ƙara burgeshi. Yai Murmushi ya ce "suna na Rayyan, kar ki min fassara amma idan ba za ki damu ba ko zan iya sanin sunan ki? Please" yai maganar yana haɗa hannun sa alamar roƙo.
"Ai da ma na san dalilin biya min kuɗin kenan. To ba zan faɗi sunan....."
Chak ta tsaya lokacin da aka ƙwala sunan ta
*'Aisha mai gwanjo'*
ta juya ba ta ga mai kiran ba, ta yi tsaki.
Wani saurayi ne ya ƙaraso akan machine ɗin sa ya na murmushi
" Allah ya ja zamanin ki 'yar kasuwa"
Sai a lokacin ta gane shi.
"Sabi'u Inuwa Manzo" ta faɗi ta na maida hankalin ta gareshi.
"Aka ce kina Yola, ya na ganki a Bauchi"
"Wallahi na je gida biki ne yanzu ma na ke son komawa Yolan. Kai fa ina aka turaka?"
"Sun turani Ilorin amma na relocating na dawo Bauchi, kin san mutum mai iyali sai a hankali"
'Yola...Yola..Yola mutum ɗaya' ake kira ta yi saurin sallama da Sabi'u Inuwa Manzo ta wuce wajen motar.
Har Sabi'u zai wuce Rayyan ya tambayeshi sunan Aisha da numbarta. Sai da Sabi'u ya sha dariya kafin ya bashi numbar bayan da Rayyan ɗin yai ma sa bayanin masifar da ya sha shi da mai keke. Sabi'u ya ce ai indai Aisha Farida Salihu ne to kaɗan ka gani.
................................
Tana shiga makarantar aka ce principal na neman ta ta sani saboda tafiyar da tayi ne dan haka hankali kwance ta wuce office ɗin sa. Da mamakin ta sai taga ashe neman saboda wasu 'yan mata 'yan aji shida da ta daka ne kafin ta tafi.
Ba ta bashi haƙuri ba balle ta nuna ta yi nadamar abinda ta yi sai da ta bari ya gama masifar shi ta ce " Mr principal dududu saura sati uku na bar makarantar nan. Yara kuma na dake su ne saboda raini da izgilanci da su ke min, ko gobe su ka sake zan dake su dan ni ba sa'ar su ba ce"
"Idan ba dan Yasir ba ai da tuni mun rabu da ke. Aisha tunda ki ka fara bautar ƙasa a makarantar nan koyaushe ana complain ɗin ki"
"Zan iya tafiya?"
Principal ya girgiza kai "kai kai kai, wannan mijin ki ya shiga uku wallahi"
Lokacin da aka tashi break ta haɗu da Yasir a staff room.
"Tawan ya ki ke, gida ya ƙarɓe ki fa sai wani ƙyalli ki ke"
"To miya fi raina"
Kujera ya ja zuwa kusa da ita kamar kullum ya na ƙoƙarin shawo kan ta. Sai dai kamar kullum ɗin zancen ta ɗaya ne.
"Mun kusa gama bautar ƙasan nan fa Farida ki taimakeni ki amince da ni" ya faɗa haɗe da haɗa hannunwan sa biyu alamar magiya.
"Yasir kenan, soyayyar talaka da maikuɗi a Nigeria its a nonono option for me. Wahala kawai zan sha ni kuma ban shirya ba. Balle kai da ka ke ɗan bare-barin nan ina zaman zama na iyayenka su turomin Yasin mai walƙiya na bi duniya"
Yasir ya sa dariya sai da ya yi mai isar sa ya ce "wallahi shiyasa na ke ƙara son ki, ba kya rabuwa da abin dariya. Yanzu miye kuma Yasin mai walƙiya"
"ka fini sani sarai"
Yasir ya cigaba da dariya.
......................
*Wacece Aisha Farida Salihu?*
Malam Salihu ɗan ƙaramar hukumar Wase ne da ke jahar Plateau. Sai dai tun yana ɗan shekara sha takwas da ya ƙare sakandare ya dawo cikin Jos da zama. Sana'ar sai da kayan gwari ya fara kuma Alhamdulillah yana samu. Su biyar ne a wajen mahaifin su wanda ya jima da rasuwa tun yana shekara bakwai a duniya, shi ne na huɗu a gidan kuma su biyu ne maza. Babban yayansu Musa shi yana Kano inda yake kasuwancin sa acan sai yayun sa mata Halimah, Asma'u da ƙanwar sa Fatima, wanda a lokacin duka sun yi aure Shekarar sa biyar a Jos yai aure.
Aminah 'yar Jos ce domin iyayen ta anan su ke da zama tun shekara da shekaru sai dai asalin su Fulanin Dukku ne da ke Jihar Gombe.
Shekarar Aminah shabiyar aka yi auren wanda a lokacin JSCE kawai ta kammala. Suna zaune da Salihu lafiya cikin so da ƙauna har wata takwas kafin mummunan ala'amari ya faru. Tana zaune ta shirya abincin rana ta tsara kwalliya tana jiran sa, saboda ko yaushe Salihu a gida ya ke cin abincin rana, taji sallamar mutane daga waje. Ta sa mayafi ta fita inda taga Alhaji Nuhu ne wanda su ke haya a gidan sa da kuma Yusufu wanda rumfar sa ke kusa da na Salihu a kasuwa. Yanayin su kaɗai ya tabbatar ma ta akwai matsala. A hankali Alhaji Nuhu ya sanar ma ta Salihu ke asibiti ya yi hatsari. Cike da tashin hankali ta bisu asibitin inda Salihu ke kwance rai a hannun Allah. Da asuba Salihu ya cika wanda sanadiyyar haka ya sa Aminah suma. Da ta farfaɗo ma dai rikicewa ta yi wanda da ƙyar Nanna wato mahaifiyar Aminan ta shawo kan ta. Sai da aka yi bakwai ɗin Salihu Nanna ta fahimci Amina ciki gareta wanda ko Aminan ba ta san da shi ba. A hankali Aminah ta dinga renon cikin ta wanda Inna mahaifiyar Salihu ta ke matuƙar farin ciki da cikin. Tsakar daren ranan Alhamis Amina ta tashi da naƙuda,aka kira wata nurse da ta ke ƙasan layin su, zuwa asuba ta haihu, ta samu ɗiya mace. Aisha Farida aka sa ma ta saboda sunan da Salihu ke cewa zai sawa 'yar sa ta fari kenan saboda sunan innar sa Aisha ya ce zai haɗa da inkiyar Faridah.
Amina ta cigaba da renon Aisha Farida a gidan su. Tana son ɗiyar ta sosai, ko kaɗan ba ta ma ta karan 'ya'yan fari irin na fulani. Shekarar Aisha Farida biyu da rabi Baba ya fara yiwa Amina maganar aure saboda a lokacin akwai manema dayawa da suke son ta. Duk ciki ba ta da zaɓi dan ita tun Salihu ba ta kuma sa soyayyar wani namiji a ranta ba. Cikin maneman ta Baba ya zaɓa ma ta Malam Haruna wanda shima mutumin Dukku ne yana ɗin ki a Terminos. Matar sa ɗaya da yara shida. Lokacin da Amina za ta tare Inna ta so a bar ma ta takwarar ta sai dai Amina ta nuna batason hakan dan a ganinta Farida ta yi ƙaranci a raba ta da uwarta. Ba laifi Haruna na ƙoƙarin nuna adalci tsakanin matansa sai dai Laraba sam ba ta da haƙuri kullum cikin tsangwaman Amina da 'yarta ta ke yi. Amina za ta lamunci komai amma idan akan Farida ce to ba za ta bari ba. Watarana Amina ta dawo daga unguwa lokacin watan ta takwas a gidan ta samu Laraba na dukan Farida tsabar wahala sai da yarinyar ta suma amma haka Laraba ta cigaba da jibgar ta. Da gudu Amina ta yi kan 'yar ta tana ihu. Daga asibiti dai Amina gidan su ta wuce ta yi yaji. A ranan Haruna ya zo biko sai dai ta nuna ma sa matuƙar za ta zauna da shi to dole ne ya raba mu su gida. Yai-yai da ita ta ƙi chanja ra'ayinta, daga baya ya yarda da hakan. Har ya kama ma ta haya ɗaki ɗaya a wani gidan haya a tudun Fera. Ana saura kwana ɗaya tak ta tare saboda har an je an jera ma ta kayanta sai ga Haruna ya zo neman ta da yamma, ta fita ta sameshi a ƙofar gida. Bai amsa gaisuwarta ba ya damƙa ma ta takardar saki ɗaya. Ba dalili ba komai. Ƙarshe dai yadda aka je aka jera kayanta haka aka dawo da su gida. Ta ƙare iddar ta ta cigaba da zaman gida. Da tanada hali ma makaranta za ta koma sai dai iyayenta ma su ƙaramin ƙarfi ne. Kuɗin makarantar Farida. Baffanta Musa ke aikowa tareda kuɗin buƙatunta duk wata, ya so ya ɗauketa sai dai Amina ta ƙi musamman da ya maida Inna zuwa gidan sa a Kano.
Ganin zaman gidan shiru ya sa ta fara yin su kunun zaƙi da zoɓo tana siyarwa. Shekararta ɗaya tana zawarci Ibrahim ya fito neman ta shima dai yanada mata, ba ta bashi dama ba sai dai ganin Haruna ya dawo yana son maida auren su ya sa ta yi saurin amincewa da Ibrahim. Haruna yai nadamar sakin ta acewar sa bai san ya akayi ya saketa ba.
A Saminaka Ibrahim ya ke da zama da shi da matarsa da yaran su uku. Watannin farko an tafi lafiya-lafiya sai daga baya Matar sa Kubura ta fara nuna halin muguntar ta, ƙarshe sai raba mu su gida Ibrahim yai Lokacin Amina na laulayin ciki. Sai da su ka raba zama Amina ta samu sakewa ita da 'yar ta. Da cikin ya cika wata tara Amina ta haifi ɗa namiji. Hakan ya farantawa Ibrahim rai saboda yaran Kubura duka mata ne. Wannan haihuwar ya jawo Kubura ta sake jin tsanar Amina. Da daɗi dai ba daɗi su na zaune har Faruƙ ya shekara biyu. Kasancewa abubuwa sun fara ja baya wa Ibrahim ya sa su ka bar gidan haya su ka koma gidan sa. Zama tareda Kubura dai sai ma abin da ya ƙaru.
Watarana Farida da Safiya 'yar Kubura su ka yi faɗa. Kubura na kitchen ta ji kukan Safiya aikuwa ta fito da gudu, ba tareda bin bahasi ba ta kama jibgar Farida daga ƙarshe ta kaita kitchen ta sa wuƙa a cikin wuta sai da ta yi jaa sannan ta cire ta manna a bayan Farida. Farida ta calla ihu wanda Amina da akewa kitso a makwabta sai da ta ji kukan 'yarta. Da gudu ta sa hijab ta taho gida inda ta samu har lokacin Kubura ba ta cire wuƙan da ya ke kwance a bayan Farida ba har wajen yai rami, tsabar wuya tuni Faridan ta suma. Amina ta yi kan Kubura ta kama ta da faɗa wanda a sanadiyyar kokawa da sukayi Amina ta rasa cikin ta. Wannan ya sa Amina ta nemi saki a wajen Ibrahim. Duk wani magiya da roƙo ya yi amma ta ƙi yarda ƙarshe cewa ta yi idan bai saketa ba da shi da matar sa za ta shigar da su ƙara a kotu na zubewar cikin ta da kuma ƙunar da Kubura ta yiwa Farida. Dole haka Ibrahim ya saketa ba tareda ya so ba. Ba ta bar ma sa Umar Faruƙ ba ta ce idan ya cika shekara uku za ta bawa ƙanwar sa Sadiya da ba ta jima da aure ba. Hakan kuwa aka yi dan Amina da kanta ta kai Faruƙ wajen Sadiya da ke aure a Kaduna. Ta ce ma ta madamar Ibrahim yana tareda Kubura bata yarda ta mayar da Faruƙ Saminaka ba.
Aikin cleaner Amina ta fara a wata private school da ke anguwar su. Inda anan ta saka Farida. Dalilin Farida ta haɗa Amina da Alhaji Kabir mai makarantar. Wata rana ta yiwa wata 'yar ajin su duka iyayen yarinyar su ka kawo complain makaranta. Da komai ya lafa Alhaji KB ya kira Amina ya fara ma ta faɗa akan rashin ƙwaɓar Farida da ta ke wanda hakan ya jawo Farida ta zama ba ta jin magana. Amina ta sa kuka tareda cewa tunda kallon da ake yiwa 'yarta kenan za ta cire Farida a makarantar. Alhaji KB da ya ke da tausayi ya fara bata haƙuri. Daga ranan su ka fara mutunci, watarana da ya ji tarihin rayuwarta ya ce ma ta mi zai hana ta koma makaranta. Ta ce za ta so hakan amma yanzu kam ba hali sai dai gaba. Alhaji KB ya ce ma ta idan ta samu mai taimaka ma ta zata koma? Amsar da ta bashi ya sa zuwa sati biyu ya samo ma ta form ɗin SS1 a wani makarantar gomnati. Da farko ta ƙi sai dai daga baya data yi shawara ta amince. Ta dena aikin cleaning ta koma makaranta. Bayan shekara biyu lokacin tana SS2 Alhaji KB ya bayyana manufar sa. Da farko ta ƙi shi daga baya ta amince amma da sharaɗin ba za ta zauna da matarsa ba. Sai a lokacin ya tabbatar ma ta shekara huɗu da rasuwar matar sa kuma basu taɓa haihuwa da Ita ba har ta rasu.
Auren Alhaji KB Amina ta samu kwanciyar hankalin aure wanda rabonta da shi tun aurenta da Salihu. Bayan da result na Waec ɗin ta ya fito Alhaji KB ya nema ma ta admission a UJ ba ta samu ba dan haka kawai ya nema ma ta ADR CLIS (AD Rufa'i College for Legal and Islamic studies) da ke Misau inda ta fara karantar Law. Da ta gama diploma lokacin ɗan su ɗaya Hamza, ta fara koyarwa a makarantar sa kafin ta cigaba da karatu. Sai dai samun wani cikin ya sa ta ajiye batun karatu a gefe tukunna. Ta cigaba da renon cikin ta.
Zaman Amina da Alhaji KB zamane na amana yana son Farida tamkar shi ya haifeta har lokacin da ta haifi Hamza bai taɓa nuna wa Farida banbanci ba. Alhaji KB ɗan asalin Jahar zamfara ne yanada 'yan uba amma a wajen mahaifiyar sa su biyu ne shi da ƙanwar sa Hannatu. Mahaifiyarsa ta rasu tun yana shekara shida. Uƙuba na matan uba ya sa ya koma wajen ƙanwar Mamansa da ke aure a Jos lokacin yana shekara sha ɗaya. Anan yai karatu ya zauna har ya kai matsayin da ya ke yanzu. Hannatu ta jima da rasuwa. Ta rasu jim kaɗan da barinsa Zamfara. Raliya ɗiyar Hajiya Aina'u mariƙiyar sa ya aura. Sai dai har Allah ya ma ta rasuwa ba su taɓa haihuwa ba. Haka nan bai ƙara aureba sai akan Amina. Sau biyu tak ya kai Amina Zamfara inda anan ta gane 'yan uwan Alhaji KB ba sa ƙaunar ta, shi ɗin ma abin hannunsa ya sa su ke ɗan girmamashi.
Abdul na da shekara biyu Alhaji KB ya rasu. Mutuwar da ta gigita Amina da Hajiya Aina'u. Lafiya-lafiya ya tafi Zamfara kawai sai yayan sa Ubaidu ya kira wai Kabiru ya rasu zazzaɓi ya sashi a gaba da dare kafin safiya ya cika.
Amina ba ta shiga tashin hankali ba sai da kwana ishirin kacal da rasuwan Alhaji KB 'yan uwan sa su ka zo su ka koreta a gidan sa. Ƙarshe a gidan su ta ƙare takaba. Kafin wata uku da rasuwar sa su ka saida makarantar sa da gidan sa da mafi yawancin kadarorin sa. Hajiya Aina'u da Amina sun yi ƙoƙarin shigar da ƙara Kotu sai dai tun farko da su ka yi yunkurin hakan aka rufe bakin su. Haka nan Amina wadda 'ya'yanta ke kira da Ummi ta koma gidan jiya sai dai wannan karan tana da ilimi daidai gwargwado da kuma wayewa. Wata makarantar ta nema aiki kuma ta samu da wannan ta ke yin hidimar yaranta da shi. Tsohon mijinta Ibrahim ya nemi ta yi kome saboda yanzu ya rabu da Kubura kuma Alhamdullillah matar sa Hafsatu tanada kirki. Ummi ta ƙi tace ita da aure har abada. Ba yadda Babanta bai yi ba amma ta ƙi ta ce aure huɗu da tayi a baya sun isheta. Yaranta uku na gabanta Farida, Hamza da AbdulMalik. Shi ma Faruƙ ya kan zo hutu wajen Ummin sa lokaci zuwa lokaci har lokacin a Kaduna ya ke. Hajiya Aina'u na ƙoƙarin taimakawa Amina da ɗawainiyar yara daidai gwargwado sai dai fa har yau 'yan uwan KB ba su waiwayeta ba balle su nemi taimakawa yaran marigayi. Gado da ya bari kuma babu batunsa dan tuni sunyi wasan kura da dukiyar sa.
Aisha Farida Salihu yarinya da ta taso da ƙiriniya ga surutu. Ba dai ka faɗa ta yi shiru ba. Kwata-kwata ba ta da tsoro, tana son umminta sosai gashi ba ƙaramin shaƙuwa su ka yi ba, idan ka ga suna hira tamkar wa su ƙawaye. Sau tari ma akan ɗauka ya da ƙanwa ne su. Tunda su ka koma gidan su Ummi, Farida ta dena zaman banza ganin dai yanzu ba da bane. Ta koyi kitso da lalle tana yi, ga saida kayan ƙwalama da ta ke yi a school. A haka har ta ƙare secondary school ɗin ta. Jamb ɗin ta na farko ba ta ci ba dan haka ta fara zuwa koyon computer a shagon ƙanin Umminta Ahmad. Ta koyi abubuwa da dama dan Alhamdulillah Allah ya bata ƙwaƙwalwa. Da ta sake Jamb ta tafi Federal polytechnic da ke Bauchi saboda UJ da ba ta samu ba. Business Administration ta karanta a ND da ta zo HND ta koma Marketing. Aisha Farida 'yar kasuwa ce tuƙuru. Dan tana makaranta ba ta zauna haka ba ita ce saida turare, takalma da jakukkuna. Ga shi duk hutu idan ta je Jos za ta saro gwanjuna ma su kyau ta zo tana sayarwa students. Wannan ya sa 'yan ajin su ke kiranta Aisha mai gwanjo.
Yanzu shekarar ta ashirin da uku, tana service a Yola. Tun a camp su ka haɗu da Yasir Sa'ad ɗa ga senator Sa'ad Babagana. A UK Yasir yai karatu. Da farko su na fita daga camp zai relocating zuwa Abuja Inda iyayen sa su ke sai dai soyayyar Farida da ya shigeshi farat ɗaya ya sa ya fasa. Hakan ya sa a Inda aka turata primary assignment ɗin ta shi ma ya je. Duk iya watannin da su ka yi tare Farida ba ta bashi dama ba. Tausayin sa ta ke ji ta girme shi da shekara ɗaya ita kuma tana ganin tsayawa soyayya da shi ɓata lokaci ne. Ga uwa uba kiran da Hajiyar sa ta mata akan ko da wasa kar ta amince da soyayyar Yasir saboda karatu zai yi hakanan akwai alƙawarin aure tsakanin sa da wata. Ita dai Farida ba dan tsoro ta ke baya-baya da shi ba ko kuma ta ƙi son sa ba sai dai bazata bawa kanta ciwon kai a kan Yasir ba. "Yaushe ma ka girma?" Abinda ta ke yawan gaya ma sa kenan.
*ga mai son cigaban labarin zai biya #200 kacal ta wannan account ɗin 3099546325 Azizat Hamza, firstbank. Idan kuma credit card ne to MTN card na 200 za a turo wa wannan numbar 08137311900. Sannan za a turo shaidar biya (screenshot) na kuɗin zuwa numbar nan still 08137311900. Ko kuma ka biya #300 ka samu labarai biyu*
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Barka da sallah 'yan uwa. Fatan ansha ruwa lafiya. Allah ya amshi ibadunmu ya kuma kawo ma na ƙarshen wannan annoba ta covid 19. Amin*
*Free page*
0️⃣0️⃣2️⃣
Da dare baƙuwar number ya kirata, da ta ɗauka sai ga muryan Rayyan.
"Ɗankwassi! a ina ka samu number ta?"
"My Farida kenan, abinda ka ke so ai duk wuya duk rintsi sai ka samu"
"Chan ta matse ma ka" ta faɗi tareda kashe wayar.
Ya sake kira ba ta ɗauka ba. A hankali a hankali Rayyan ya cigaba da kiran Farida, tun tana ƙin ɗauka har ta koma idan ta ɗauka za ta surfa ma sa masifa, shi kam da gaske ya ke dan haka bai damuba duk abinda za ta ce ma sa shanyewa ya ke. Cikin sati uku sai da ya san yadda ya ja hankalin Farida har tana ɗan kulashi ta dena ma sa faɗa idan ya kira.
Ranan da su ka yi passing out ɗin su sai ga shi a Yola. Ta ji mamaki hakanan kuma ya ɗan samu matsayi a zuciyarta. Saboda Yasir ya haƙura da ita ya sa ta introducing Rayyan a matsayin saurayin ta. Yasir kamar ya haɗiyi ran sa saboda baƙin ciki haka su ka rabu da shi baran- baran. Ko sallama babu.
Rayyan Abdullahi ɗan Kano ne kuma ma'aikaci a Zenith bank. Ya je Bauchi ta'aziyar 'yar yayarsa da ta rasu su ka haɗu da Farida. Sosai ya ke jin Farida a ransa, tsiwarta da masifarta yana burgeshi matuƙa. Ya ɗau ɗamaran koyawa Farida son sa musamman da ya gane ba ta da wani tsayayyen saurayi. To ina za ta yi saurayi bayan masifarta kaɗai ya isa ya sa samarin su dinga gudun ta.
..................................
Isowar sa kenan cikin gidan a gajiye. Kai tsaye ɗakin sa ya wuce dan ya san Daddy ba ya nan balle ya je ya gaida shi. Ya na shiga ya danna SHS zuwa Main kitchen "lemon tea in 10minutes" ya faɗi tareda zama ya fara cire socks na shi daga nan ya cire gaba ɗaya kayan jikin sa sannan ya shiga toilet.
Adama ta zo haurawa ɗauke da tea ɗin Najeeb ta haɗu da Afrah da ke shirin haurawa saman. Ta duƙar da kai ta gaisheta, Afrah ta amsa a gatsine.
"A Ya Najeeb za ki kai wa?"
Adama ta amsa da "eh"
"Kawo zan kai masa" ta ƙarɓi tray ɗin daga hannun Adaman.
Ta cigaba da hawa stairs ɗin tana tafiya ƙarar takalminta na ba da sautin ƙas- ƙas- ƙas...
Tana jin ƙaran ruwa a banɗaki lokacin da ta ajiye ma sa tea ɗin a ɗakin, kamar za ta fita sai kuma ta samu kujera ta zauna tana jiran sa. Kusan minti biyar sai ga shi ya fito ɗaure da towel. Ya na faman goge gashin sa da ɗan ƙaramin towel ya ganta ta ƙura ma sa ido.
"What the fuck! Mi ki ke yi a ɗaki na" Ya daka ma ta tsawa
Daburcewa ta yi ta fara kame-kame.
"Get out" ya daka ma ta tsawa ba shiri ta fita da gudu dan ta san halin sa sarai.
Sai da ya shirya cikin farar riga da wando baƙi three quater sannan ya buɗe laptop ɗin sa ya na duba wani aiki da Joseph sabon sakatarin sa ya turo ma sa. Yana dubawa yana sipping tea ɗin sa a hankali. Ba laifi Joseph yai ƙoƙari, da alama ya san aikin sa dan tunda ya fara ma sa aiki bai samu kuskure ɗaya cikin ayyukan da ya ke sa shi ba, sai dai da saura tunda dududu sati biyu da Joseph ɗin ya fara ma sa aiki kenan.
..........................
A hankali soyayyar Rayyan da Aisha Farida ta fara nisa, domin har ya je Jos ya gaida Ummi...
"Farida ba magana na ke mi ki ba"
"Ummi dan Allah ki haƙura da wannan zancen, zan dai dinga zuwa mu su akai-akai yanzu tunda na gama bautar ƙasa"
"Kin sani sarai har yau Alhaji Musa ni yake ɗaurawa laifi akan na raba ki da dangin Baban ki. Sun fi ni iko da ke Farida"
"Ni kan Ummi ki yi haƙuri, ba zan je ba, albarkacin Inna na ke zuwa mu su dama, kuma ta rasu shikenan"
"Ki yi yadda ki ke so Farida" Ummi ta faɗi tareda barin ɗakin.
Ita ta rasa dalilin da zai sa sai yanzu Baffa Musa zai takura wai ta koma wajen sa da zama. Ita yaushe ma za ta juri zafin Kano balle uwa uba rashin kunyar yaran sa. Dama dalilin Inna ke kaita Kano kuma tunda ba ta nan kowa ya riƙe kan sa. Da wannan tunani ta janyo purse ɗin ta tana irga kuɗin da ke ciki a karo na biyar kenan tun safiyar yau.
Sosai Ummi ta nuna ɓacin ranta akan ƙin zuwa Kano da ta yi, ko gaisuwarta yau da safe ba ta amsa ba.
"Nanna dan Allah ki cewa Ummi ta bar ni na yi zamana anan. Wallahi ba jin daɗin zaman Kano na ke yi ba"
Nanna da ke shan kunu da ƙosai ta ce " kin dai san da daɗewa Ummin ki tai alƙawarin za ki koma Kano da zaran kin gama makarantar ki. Alhaji Musa da kan shi ya kirata jiya ya ke cewa ya ji shiru. Ke idan ba ke bama ba saurayin ki ɗan Kano bane, idan ki ka je chan sai ku saita kan ku, kinga ba sai an sha wahala ba daga nan sai dai mu je bikin ki chan Kanon"
Ta turo baki tana faɗin "Allah dama kun gaji dani. Ni dai ba zan je Kano ba"
"Ah to, sai ki kira Baffan na ki ki gaya ma sa ai"
Farida ta zumbura ba ki ta fice a ɗakin....
Cikin kwana biyar ta gama shirin ta tsaf, ba wai tana son zuwa Kano bane, sai dai tunda abinda Ummi ke so kenan dole ta yi shi. Ranan asabat ta wuce Kanon tsabar haushi ko kiran Baffa Musan ba ta yi ba balle ta sanar ma sa da zuwan ta.
A ƙofar gida ta haɗu da su Kamal yaran Baffan su na wasa, da gudu su ka zo su ka tareta sannan su ka tayata ɗaukan kayan ta.
Da sallama ta shigo tana ƙarewa cikin gidan kallo wanda ya sha sabon fenti da alama dai saboda bikin Hajara da Salima da za a yi ne.
Baaba Sabuwa ta fara gani wanda ihun yara ya sa ta fito daga kitchen. Duk cikin matan Baffa Musa ita Farida ke ɗan gani da mutunci saboda itace uwargida kuma ba laifi tana da kirki.
"Oyoyo mutanen Jos. Sannu da zuwa"
Gyalenta ta saƙala ajikin igiyar shanya tana faɗin "fatan mun sameku lafiya"
"Lafiya lau, ya su Ummin na ku?"
Daga kitchen ta ke amsa ma ta da lafiya. Sai faman buɗe tukwane ta ke yi tana neman abin da za ta sa a baka.
"Baaba Sabuwa ni kam har yanzu ba ku bar baƙar al'adar ku ba, ace abincin rana sai ƙarfe uku"
"Lah yanzu na ke son ɗaurawa ai"
Farida ta dubi wayar ta tana faɗin " a ƙarfe ɗayan!"...
Sai da dare Baffa ya sa aka kirata. A falon shi ta sameshi yana cin abincin dare. Bayan ya ma ta ya hanya sannan ya fara bayani " Aminah ta ce ba ki fara aiki ba dan haka zan sa Yakubu ya nema mi ki aiki a kamfanin da ya ke aiki ko za a dace kema ki samu. Kafin nan kuma ki cewa yaron da ke neman ki ya turo saboda mu san da gaske ya ke yi. Kin dai ga yanzu shirin auren ƙannen ki a ke yi, zuwa ƙarshen shekara ke ma ayi na ki"
"Ni dama na san dalilin cewa in dawo Kano kenan, ni Baffa ban san mi na tare ma ka ba. Kanata wani ƙannena-ƙannena, na ga su suka ƙi karatu su ka ce aure za su yi. Ni dana zaɓi karatu na yi kuma na gama ai sai a bar ni na ɗan sha iska kafin a fara maganar aure na"
Ya ma ta daƙuwa ya ce "Uban ki Farida, na ce kin ci ƙaniyar ki. Wato har yanzu ba ki bar rashin kunyar ki ba ko" .
"To Baffa ina zaman zamana a Jos, ka takura Ummi wai ta turoni Kano. Duk abinda na yi ai kai ka ji za ka iya..."
Marfin kwanon silver ya wurga ma ta ta kauce ba shiri. " ki kiyaye ni Farida wallahi zan mummunan saɓa mi ki. Tashi ki bani ware! Ja'ira kawai"
Sum-sum ta tashi ta fice a falon dan ta san ƙarshe zai iya marin ta ko ma ya daketa. Dan Baffa Musa akwai saurin hannu.
..........................
Ba ƙaramin kyau yai ba cikin shirin sa na riga da wando baƙi sai kuma blazer kalar navy blue. Ɗauke da briefcase ɗin sa ya sauko daga stairs ɗin cikin takunsa na girma da ƙasaita.
Ƙai tsaye wajen dining ya je inda iyalen gidan ke cin abinci. Ya sunkuya yaiwa wata budurwa peck a kumatu yana faɗin " good morning baby"
"Morning Big B" ta amsa tana ma sa murmushi
Itama Afrah da ke gefe ta ce " Good morning Yaya"
"Morning" ya faɗa a taƙaice.
Tea ɗin da ke gaban Baby ya ɗan ƙurɓa ya ce " sai na dawo ko"
Wata haɗaɗɗiyar mata da ke zaune opposite da Baby wanda tun saukowar shi idon ta ke kan sa ta ce "have breakfast with us, please"
A dararance ya kalleta ya ce "na gode Justice Nabilah"
Har ya bar falon ba ta dena kallon sa ba, zuciyar ta na ƙuna. Sai yaushe ne ɗan ta zai kira ta da sunan uwa? Sai yaushe alaƙar su zai dawo dai-dai kamar kowace uwa da ɗan ta? Shekaru sun ja amma har yau babu wata chanji tsakanin su.
Baby ta ce"Sorry Mom"
Justice Nabilah ta girgiza kai ta ce " kar ki damu Najdah" ta ƙaƙaro murmushin dole dan jaddada maganar da ta yi.
Ita dai Najdah jikin ta ne yai sanyi, har yau ta kasa gano dalilin ƙiyayyar Yaya Najeeb da Mom, wanda tun tasowar ta haka ta same su.
Tambayar duniyar nan ta yiwa Big B da Mom amma duka babu wanda ya bata gamsashshiyar amsa. Harta Daddy bai san dalilin wannan gabar ba. Tun yana faɗa akan wannan ƙiyayyar ta su har ya haƙura ya zuba mu su ido...
Tunda ya fita daga gidan kai tsaye wajen motar sa ya wuce. Wanda tuni aka fito ma sa da ita daga parking lot. Sau ɗari zai ɗau driver sau ɗari zai koresu. Shi ya sa yanzu kusan wata uku kenan rabon da ya sake ɗaukan driver. Shi ya ke tuƙa kan sa, ran da yake son yin aiki a cikin mota kafin ya ƙarasa office to zai sa drivern Daddy ya kai shi office.
*Najeeb Adam Jibo*
matashin da ya ke ji da kyau,kuɗi,ilimi da kuma gata. Ɗa namiji guda ga tsohon Ambassador kuma Professor Adam Jibo da Justice Nabilah Al-Jabir.
Adam Usman Jibo ɗan asalin ƙaramar hukumar Kumo ne da ke jahar Gombe, sai dai kasancewar tun rasuwan mahaifinshi ya dawo wajen ƙanin Baban sa da ke Kano da zama ya saka zamansa ya koma Kano. Alhaji Mustafah Jibo babban ɗan kasuwa ne da ya ke da arziƙo tun a wancan lokacin.
lokacin da Adam ke da shekara bakwai a duniya mahaifin sa ya rasu, dan haka zaman sa da shi da ƙannen sa mata biyu su ka dawo hannun Alhaji Mustafah , lokacin Mustafah da matar sa shekarar su takwas da aure amma basu taɓa haihuwa ba. Sun riƙe Adam da ƙannen sa Ruƙayya da Fatima tamkar 'ya'yan da su ka haifa. Sai da su ka shekara goma sha biyar da aure ba haihuwa sannan Hajiya Mama wanda haka su Adam ke kiranta ta dage akan lallai Alhaji Mustafah ya ƙara aure ko za a dace.
Wata ƙanwar maƙocinsa kuma amininsa ya aura. Budurwace dan a lokacin da aka yi auren su shekararta shashida. Cikin ikon Allah watan Halima goma ta haifi ɗan ta namiji ya ci suna Sulaiman. Murna wajen Alhaji Mustafah ba a magana. Bayan Sulaiman ta haifi Abubakar sai da ta shekara huɗu kafin ta haifi Aisha wanda lokacin haihuwanta ta wahala sosai, tun lokacin haihuwar kuma ta ke jinya bayan sati uku ta rasu. Mutuwar da ta girgiza iyalen Alhaji Mustafah gaba ɗaya.
Hajiya Mama ba ta haifa ba amma ta ɗauki duka yaran tamkar ita ta haifesu, wanda ko kaɗan ba za ka taɓa ganin abu ɗaya da zai nuna ma ka ba ita ɗin ta haife su ba. Ba ma kamar Aisha wanda ita ta shayar da ita. Haka yaran su ka taso ba su da wata uwa da ta wuce Hajiya Mama. Kuma har lokacin da Alhaji da Hajiya Maman ba wanda ya banbanta tsakanin yaran marigayi Usman Jibo da kuma ainihin yaran Alhajin. Sai dai a hankali su ka fahimci Aisha ba ta magana, kurmiya ce. Anyita magani amma shiru, tana ji amma ba ta iya magana. Wannan lalura ta sa da Alhaji da Hajiya Mama su ka maida hankalin su wajen kula da Aisha sosai.
Da Adam ya gama primary school na shi Alhaji Mustafah ya kaishi Lagos karatu. Bayan kammala secondary school na shi a kings college da ke Lagos ya wuce Harvard yai degree ɗin sa a fannin International relation,daga nan ya wuce London Business school yai wani degree ɗin a fannin Business sannan yai masters na shi da Phd a Yale University. Ya fara koyarwa a Yale kafin Nigeria ta tura shi Canada a matsayin Ambassador daga nan aka maida shi USA daga USA sai Belgium daga nan sai South korea wanda daga south korea ɗin ne yai retire ya dawo Nigeria inda yai zaman shekara ɗaya yana hutawa, gomnati ta mi shi chaaa akan ya shigo siyasa a dama da shi sai dai shi ya fi son koyarwa saboda ya amfanar da mutane ilimin da ya tara. An awarding na shi professor kuma yana visitin lecturer a jami'o'i da dama a ƙasar, musamman ABU, BUK, UJ, UI da sauran su.
Adam Jibo ya haɗu da Nabilah Aljabir ne a Yale University lokacin yana masters na shi. 'Ya ce ga wani hamshaƙin mai kuɗi Aljabir Al Mukhtarr ɗan asalin ƙasar Bahrain. Soyayya ce mai ƙarfi ta shiga tsakanin su tun haɗuwar su a library. Ba ƙaramin sa'insa aka samu ba kafin aka amince da auren su musamman da ya ke tana balarabiya shi yana bafulatanin Nigeria. Sai dai Nabilah ita kaɗai ce 'ya mace a wajen mahaifinta kuma mahaifinta na son ta sosai.
Bayan auren su da shekara ɗaya ta haifi Najma wanda sunyi niyyar sawa yaransu sunayen da su ka fara da harafin N da A da J. Harafin N saboda Nabilah, harafin A da J kuma na Adam Jibo. Bayan shekara uku ta haifi Najeeb wanda daga shi sai da shekaru su ka ja kafin Najdah ta zo duniya, kusan shekara sha uku Najeeb ya bata. Dawowar su Nigeria Nabilah ta yi Pre Law school na wata shida kasancewar a ƙasar waje ta yi karatu kafin ta yi regular Law school. Ta yi aiki a kotuna da dama kafin daga bisani ta kai matsayin Justice.
Najma ɓangaren likitanci ta karanta tana aiki a National hospital Abuja a matsayin gyneacologist. Tana auren wani hamshaƙin mai kuɗi ɗan kasuwa kuma likita Dr Mujahid, yanzu haka yaran su uku.
Tun kafin Adam Jibo ya dawo Nigeria dama ya riga ya gina wani ƙaton gida a Kano. Anan iyalen sa ke sauka idan sun zo hutu Nigeria. Ƙannen sa sun yi aure suma da nasu iyalin Fatima na aure a Kano yayinda Ruƙayya ke aure a Katsina. Suma ƙannen sa 'ya'yan Alhaji Mustafah sun yi aure da iyalen su. Sulaiman yana Kano yayinda Abubakar ke Abuja. Duk wata su kan haɗu ayi meeting a gidan tsohuwa wato Hajiya Mama. Alhaji Mustafah ya jima da rasuwa tun kafin rasuwan Aisha. Hajiya Mama tana nan a gidan Alhajin sai fama da jikoki. A gefen gidan Alhajin duka Sulaiman da Abubakar su ka yi gininsu. Shi Adam ne gidan sa yai nisa da su. Sai dai shima indai yana gari to kullum sai ya je ya gaida Hajiya Mama wannan ya zamo ma sa al'ada. Hajiya Mama ita ya sani a matsayin uwa. Goggon su ta jima da rasuwa bayan rasuwar Mahaifin su ta sake wani auren a Ashaka inda wajen haihuwa ta rasu. Haƙiƙa Hajiya Mama uwa ce ta gari. Ba ta haifi nata ba amma ta riƙe yaran mijinta tsakani da Allah wanda har yau suna darajata. Inda ace ta ha'ince su da tuni sun watsar da kashinta musamman bayan da Alhaji Mustafah ya rasu.
Duka karatun Najeeb a ƙasar waje ya yi su. To dama a ƙasar wajen aka haife shi. Yai degree na shi na farko a MIT (Messacheusettes Institute of Technology ) inda ya karanchi Engineering and Technology daga nan ya sake wani degree ɗin a ɓangaren Architecture. A London yai Masters na shi kafin ya tafi Korea yai Phd na shi.
Ya fara aiki a Korea da wani construction company kafin ya ajiye aikin ya je yai wani course a India, lokacin Mahaifinsa Professor Adam Jibo ya dawo Nigeria da zama. Bayan ya ƙare course ɗin ne ya dawo Nigeria ya buɗe Kamfanin sa mai suna *Najeeb constructions* shekaru bakwai da su ka wuce kenan.
Ya taso cikin kuɗi kuma ya nemi kuɗi ya samu. A shekarun sa talatin da huɗu, ba abinda ke gaban sa da ya wuce kamfanin sa. Zai iyayin komai saboda samun ɗaukakar kamfanin sa.
Anas shi ne babban aminin sa, jinin su ya haɗu sosai duk da kuwa Najeeb ya girmeshi da shekara uku, amintar su ta sa lokacin da ya buɗe kafanin sa ya jawo shi gefen sa su ka haɗu su ka ɗaukaka kamfanin saboda shima Architect ne. Bayan Daddy da Najdah wanda ya ke kira Baby to Anas shi ne mutum mafi kusa gareshi idan ka ɗauke Hajiya Mama. Sun jima da baran-baran da yayarsa Najma a kan ƙin Mahaifiyar su daya ke yi wanda har yau babu wanda ya san dalili abu kusan shekaru ishirin kenan.
*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣0️⃣3️⃣
Kamar kowani lokaci idan ta zo Kano ɗakin Inna ta ke kwana, wannan karan ma hakan ce ta faru, sai dai yanzu Maijiddah da Zainab ke kwana a ɗakin bayan rasuwar Inna. Daga zuwan Farida ta kori Zainab a ɗakin tace ba za su kwana su uku ba. Zainab ta fice daga ɗakin tana ƙuƙuni.
Maijiddah 'yar Baaba Sabuwa ce, kuma duk cikin yaran gidan tafi su hankali, kasancewa anyi auren ƙannenta biyu gashi za'ayi wasu biyun ya sa ake goranta mata rashin miji, kullum a takure take, dududu shekarar ta ishirin amma yadda ake mata gori a gidan ka ɗauka ta shekara talatin ne ba tayi aureba. Wai har 'yar Zainab da ke shekara shahuɗu tanada samari ita ba ta da kowa. Duk masu zuwa wajenta ba sa jimawa su ke guduwa. Islamiyya kaɗai ta ke zuwa yanzu, sai kuma takan taɓa ɗinki a keken Baabarta sannan tana sana'ar kitso. Dan wani lokaci har gida ake zuwa a kirata ta je ta yi kitso, domin gaskiya Allah ya bata baiwar iya kitso.
Shekarar ta uku da gama secondary, dokar Baffa Musa ce, sai dai mace ta yi karatun gaba da secondary a gidan mijinta amma ba a gidan shi ba, shi ya sa Maijiddah ba ta yi wani hoɓɓasa domin ta cigaba da karatu ba, saidai cikin ran ta tana ƙwaɗayin hakan. Ba wai muni gareta ba tana da kyau dai-dai gwargwado sai dai gaskiya guntuwa ce. Dan harta Zainab da bata gama tsayinta ba, ta fita tsayi.
Maijiddah tafi ganin gajartar da Allah ya mata a dalilan da ya sa ta rasa manema...
Suna sallar Asuba Maijiddah ta gaida Farida sannan ta fara gyara ɗakin su har lokacin Farida na yin azkar. Da ta gama ta fita dan ta fara hidiman cikin gida. Lokacin da Farida ta fito daga ɗaki Maijiddah kaɗai ta samu a tsakar gida tana shara. Cikin isa ta riƙe ƙugu tace " Jiddah ina batun dokokin dana sa a gidan nan wancan zuwana Kano?"
"Anty Farida kin san yau Lahdi ne ba a tashi da wuri"
Murya sama-sama ta fara magana. " Tab! wato dan bana gidan shine aka watsar da dokokina ko. To ku sani Wallahi duk wanda ya san yau ranan aikinsa ne bai fito ba ganinan zuwa har ɗakin uwarsa in dakeshi kuma ba abinda zai faru. Zan irga uku ɗaya....biyu...." sai ga yaran suna fitowa daga ɗakunan su da gudu. Da ke sun manta tsarin da ta musu, kowa sai ya fito dan kar ya zama ranar sa ce kuma bai fito ba ta bishi ɗaki ta zane. Ba yau Farida ta fara zane yaran gidan ba, yanzu haka yadda su ke tsoronta ko su Yaya Yakubu iya kaci.
Maijiddah ta ɗan yi murmushi lokacin da ta ga ƙannen nata na fitowa da gudu.
...............................
Ba tareda ya ɗago ya kalli Joseph ba ya ce " three days" Joseph ya haɗiyi yawu moƙot saboda ba shi da ta cewa, amma taya kwana uku zai ishesa ya je Enugu burial na Maman sa ya dawo a kwana uku, bayan Enugun ma chan cikin wani ƙauye mai nisa su ke.
"Anything else?" Muryar Najeeb ta dawo da shi daga tunanin da ya ke. Joseph ya girgiza kai da sauri ya ce "no sir". Da hannu Najeeb ya ma sa nuni da yai waje. Joseph ya bar office ɗin da sauri...
Tare su ka fita da Anas, sunje sun duba wani site da kamfanin su ke ginawa. A hanyar su ta dawowa Anas ya nuna yunwa ya ke ji dan haka dole su ka tsaya a wani restaurant da ke kusa.
Fiskar san nan tamau ta ke kamar bai taɓa dariya ba a tarihin rayuwar sa. A haka su ka shiga wajen cin abincin, shi idan ba dan Anas ba ba abinda zai sa ya tsaya a irin wannan waje. The restaurant is not even classy.
Sai da su ka zauna waiter ya zo dan ya ƙarɓi order ɗin su. Da sanin Najeeb ya faɗi wani kalar girki wanda baya cikin menu ɗin su. Saurayin ya ɗan tausasa murya ya ce "sorry sir, we dont have that in our menu"
Najeeb ya smirking ya ce " then, water will be fine"
Har zai tafi Anas ya tsayar da shi ya ce ya kawo wa Najeeb irin abinda ya ordering.
"Seriously!" Najeeb ya faɗi yana ɗan girgiza kai.
"Mutumina kai fa ba engine ba ne, tun safe fa ba abinda ka ci. Gara ni naci ɗumame na ƙoshi kafin na fito, amma kai na san bayan tea ba abinda ka sa a baki"
"Did i complain?"
"Idan kai ba za kula da kan ka ba, i'll help you do that"
Kafin a kawo abincin wayar Anas ta yi ringing ganin mai kiran ya sa ya ce da Najeeb yana zuwa. Fita yai daga wajen don ya samu daman magana sosai.
Wata budurwa da saurayi su ka shigo wajen cin abincin . Hankalin Najeeb na kan wayar sa dan haka bai lura da su ba, sai dai table ɗin da ke kusa da na su su ka zauna, da ke budurwar ce ta bashi baya dan haka bai ga fiskarta ba sai dai ya ga na saurayin lokacin da ya ɗago zai ɗau ruwan da waiter ya ajiye mishi.
Surutun da budurwar ke yi ya sa ya ƙara tsanar wajen saboda hayaniya da ta cika shi. Tukunnama, ta ya mace za ta dinga surutu haka in a public place kamar wannan. Tun da su ka shigo siririn muryanta ya gauraye wajen. Kafin saurayin da su ka shigo tare yai magana ɗaya budurwar ta yi ɗari. A haka Anas ya shigo ya same shi, su na fara cin abincin Najeeb yai tsaki ya aje fork da sokali sannan ya ɗau tissue ya goge bakin sa.
"Abincin bai ma ka ba ko?" Anas ya tambaya yana kallon sa. Najeeb ya ɗau ruwa ya kora batareda ya bawa Anas amsa ba. Tsakani da Allah ba wai abincinne bai ma sa ba, ba kuma yunwanne ba ya ji ba. Sai dai surutun wannan budurwane ya cika ma sa kunne. A rayuwarsa ya tsani hayaniya balle kuma yawar magana.
Kamar Anas ya gane damuwarsa ya ce a hankali "wannan yarinya ba dai surutu ba. Kamar radio"
Najeeb ya cigaba da danna wayarsa ba tareda ya ce komai ba...
..........
"Ka san Allah, idan na yi wata ɗaya a garinkun nan toyewa zan yi. Irin wannan zafi haka!. Da wayona Ray ban taɓa fin sati uku a Kano ba, ina ma zan iya"
Farida ta faɗi tana kora ruwa amaƙoshinta saboda tunda su ka zauna ta ke ta zuba surutu.
Rayyan ya ce "gashi ɗan Kano za ki aura ba"
"Ai ka ji inda matsalar ta ke, ina ga fa sai dai kai ka dinga zuwa Jos, dan ba zan tare a Kano ba. Tukunna Ray, wai a garin nan ka taso cikin wannan zafin?"
Rayyan ya langwaɓe kai dan wannan tambayar kusan karo na uku kenan da za ta yi shi a ɗan zaman su a wajen nan.
" My Farida mu ci abincin nan, zai yi sanyi fa"
A hankali ta fara tauna jollof rice ɗin wanda ko loma uku ba ta kai ba ta ajiye cokali. Ta yiwa wani waiter hannu akan ya zo.
Rayyan ya ma ta kallon mi ke faruwa amma ta kauda kan ta ta yi kamar ba ta gani ba.
"Waye ya girka abincin nan?" Tambayar da ta yiwa waiter kenan.
"Any problem ma'am?" Ya tambaya with politeness.
Farida ta kalli abincin ta kalle shi sannan ta ce "abincin ku shine problem ɗin ai. Na san wadda ta girka abincin nan ko tantama babu Bayarabiya ce. Idan ba haka ba taya za'a yi jollof rice a restaurant kuma a cika ma sa yaji. An gaya mu ku kowa ne ke son yaji? ko kuma dai so ku ke mutum ya ci ya koma gida yana gudawa. Da a garin da ba zafi ne sai ace ya yi dai-dai amma wannan Kanon na ku da shegen zafi kuma ku dafa abinci mai yaji kuna ba wa mutane. Mi ku ke nufi?"
Waiter ɗin bai gama fahimtar maganar Farida ba, saboda ba wani hausan kirki ya iya ba. Shekaran sa na uku kenan a Kano. Ya dai gane kalmar 'Yaji' dan haka ya ce " ma'am with due respect, i dont think the food is pepperish"
Farida ta hangame baki " Yo ƙarya na ke yi kenan?"
"Sorry ma'am"
Rayyan ya girgiza kai ransa a ɗan ɓace ya ce " Farida dan Allah ki barshi haka, bari a kawo mi ki fried rice"
"A'a Ray, sai ya taɓa abincin nan ya ji dan ya tabbatar da magana ta"
Wani matashi wanda tun shigowar su Farida ya ke ankare da yadda ta cika wajen da surutu ya taso ganin dramar da ake yi.
"Haba Madam. Tun ɗazu ki ke damun mutane da surutu fa, kar ki manta nan public place ne"
Kallon sama da ƙasa ta ma sa sannan ta ce " Malam sa'ido,gulma da munafurci. Kunnen ka bai jiyo surutun da ke fitowa daga TV ba sai nawa. Tsabar ha'inci ka bar matarka da cin garau-garau , ka zo ka tisa tumbinka a gaba kana cin fried rice da chicken, Allah wadai"
Kunyar da Rayyan ya ji ko wanda aka yiwa maganar bai ji ta ba. A ƙalla mutumin nan zai kai shekara Arba'in, amma Farida ba ta ga girman sa ba ta ke yaɓa ma sa magana.
Mutumin ya zuba ido yana kallon ta kawai tsabar mamaki.
"Kalleni da kyau Malam na fi ƙarfin ka, inma kana ƙungiyar mafiya ne to jinina fau-fau ya fi ƙarfin ka"
Mutumin ya kalli Rayyan ya ce "ɗan uwa gaskiya kana ƙoƙari. This girl is fire" sannan ya koma table ɗin sa.
Ta ce "Ba fire ba Volcano. Mtsww"
Ta kalli waiter ta ce "taste this food before i loose my temper"
Da sauri ya ɗau sokali ya ɗeba abincin ya taɓa. Irin masifan da ta yiwa mutumin nan wai ta ce ba ta loosing temper ba to idan ta yi ya za ta zama kenan.
Tabbas abincin ya ɗan fito da taste ɗin yaji amma bai kai har yadda Farida ta kururuta ba.
"Sorry ma'am, i apologise on behalf of our kitchen...."
Lokaci guda Najeeb ya miƙe tsaye hakan ya bashi damar ganin fiskar budurwar wanda alokacin ke yiwa waiter bayanin abinda zai kawo ma ta a madadin jollof rice mai yaji da su ka kawo. A yadda ta ke masifa ya ɗauka zai ganta gabjejiya sai ya ganta 'yar mitsila bai fi mutum ya mangajeta ba amma sai shegen baki. Kallo ɗaya ya ma ta ya ɗauke idon sa ya fice daga restaurant ɗin.
A mota ya jira Anas wanda shi kam sai da ya ci yai naƙ sannan ya fito.
"Mutumina ka san yarinyar nan ta bi waiter har kitchen ɗin su. Na ji tausayin saurayinta wallahi, haka yai wani lafau da shi abin tausayi"
Najeeb ya ce " its his fault ai, ta ya zai dating lousy girl kamar wannan"
"Yarinyar tana da kyau ba laifi, sai dai surutu kam Tabarakallah ko gidan radio iya ka ci" ...
Rayyan da Farida kuwa ba su suka bar restaurant ɗin ba sai da Farida ta sauke masifar ta ta huce. Shi Rayyan abincin ma kasa ci yai, ita kuwa aka kawo ma ta fried rice ta naɗa harda take away ta yi.
....................
"Gaskiya Yaks idan na ce ma ka akwai vacancy a ƙasa na yi ƙarya, sai dai ka bani lokaci nan zuwa next week zan bincika, idan ma ba ta samu anan ba zan iya nema ma ta a wani wajen. Ai ƙanwar mu ba za ta rasa aiki ba Insha Allah"
Yakubu yai ma sa godiya sannan ya fice daga office ɗin.
Anas kenan, yana da sauƙin kai ba kaman Oga kwata-kwata ba, wanda mulki da girman kai ya hanashi sakewa da mutane. A shekarun sa na uku da fara aiki a Najeeb constructions sun saba da Anas sosai, tamkar yayansa haka ya ɗauke shi...
Anas na tattara wa su files kiran Najeeb ya shigo wayar sa, dama files ɗin wajen Najeeb zai kai su dan haka ya amsa wayan da sauri dan ya san abokin na sa da gajen haƙuri.
"Mr Man yanzu na ke shirin kawo ma ka files ɗin"
Cikin huci Najeeb ya ce " Anas ka san that stupid boy bai zo ba, and numbar sa ba ta shiga. Find a replacement, ba zan iya da shi ba"
"Calm down Yallaɓai, barin zo office ɗin sai mu yi maganar...
Duk yadda Anas ya so Najeeb ya ƙarawa Joseph lokaci hakan bai yiwu ba, ƙarshe dai cewa yai ya nemo ma sa wani ko wata.
"Gaskiya you need to change abokina, this guy is good, and kai ma tsakani da Allah ka san kwana ukun da ka bashi ya yi ma sa kaɗan"
"I dont bloody care. Zaman shi a chan ba zai dawo da wanda ya mutu ba neither will it profit him in anyway. So why will he risk his job for that"
"It's his mother's burial, kuma kasan al'adun su da namu ba ɗaya bane"
"And so freeking what?. Just ka nemo wani kawai"
Anas ya kalli abokin na sa cike da takaici ya ce " ba kowa ke da mummunan ra'ayi irin taka ba Najeeb, just because ba ka ɗauki mahaifiyar ka a bakin komai ba doesnt mean kowa ma haka ya ke. Joseph yana son mahaifiyar sa, shiya sa ya tsaya yaiwa mahaifiyar sa proper burial kaman yadda al'adar su ta tanada. I hope you understand that"
"Oh please Anas! Not this talk again"
"Ka na so, ba ka so, gaskiya ce dole na faɗa ma ka duk min ɗacin ta kuwa"
"Find another secretary for me Arch Anas Ali Almustafah"
Kallon-kallo su ka yiwa junan su kafin Anas ya fice daga office ɗin.
*💮SAKATARIYA TA💮*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣0️⃣4️⃣
Ranan Tuesday sai ga Joseph ya zo office, ya sani sarai Najeeb zai yi fushi da shi amma bai ɗauka abin zai kai ga kora ba. Infact, irin koran walaƙancin da Najeeb ya ma sa sai da yai dana sanin fara aiki da Najeeb. Tun farkon zuwan sa kamfanin ya samu labarin halin maigidan na sa a wajen sauran ma'aikata, sai dai bai ɗauka abin na sa ya kai yadda ake faɗi ba sai da ya gani muraratan.
Anas dai ba yadda ya iya ne amma ran sa ya sosu da abinda Najeeb yai wa Joseph.
"Sir, he gave me 3 days, only 3days. I left Kano on tuesday morning, i reached my village on wednesday. My mother was buried on saturday and i make sure i squeezed myself and came back to Kano on Monday night. But he wont listen"
Joseph ya faɗi yana goge hawaye. Shi takaicin sa ma bai wuci yadda Najeeb ya nuna halin ko in kula da mutuwar mahaifiyar sa ba.
Anas ya kalle shi ya ce "please dont take it personal, Najeeb doesnt even respect his own mother. I'm sorry about your loss Joseph, i lost my mother when i was only 7yrs so i know how you feel"
Kalaman Anas su suka kwantarwa Joseph hankali har ya ƙarɓi check ɗin da Anas ya bashi sannan ya tafi...
.....................
Ido Yakubu ya zaro lokacin da Anas ya gaya ma sa akwai vacancy na ɓangaren secretary ɗin Najeeb.
Indai kana aiki da Najeeb Constructions to dole ne ka san halin Najeeb balle kuma jiya-jiya Najeeb ya gama koran Joseph wanda harda kira ma sa security su fita da shi, ba dan Anas ya sa baki ba Allah kaɗai ya san halin da Joseph zai shiga.
"Kana tsoron kar a walaƙanta ƙanwarka ko?" Anas ya jefa ma sa tambaya
"Na ma ka alkawari zan yi ƙoƙari na ga ƙanwarka ba ta walaƙanta ba, za tai aiki da Najeeb na lokaci kaɗan ne ana samun wani vacancy ɗin zan chanja ma ta aiki"
Yakubu ya sauke ajiyar zuciya ya ce " Aikin Farida da Sir Najeeb ba mai yiwuwa bane, idan Farida ba ta ƙona shi ba to shi zai murɗe ma ta wuya ya kasheta. Ka san Farida kuwa? Ai Najeeb da Farida su ka haɗu anan kamfanin inaga ƙonewa kawai zai yi dan wuta da wuta ne"
Dariya Anas yai ya ce " har akwai yarinyar da za ta iya karawa da Najeeb? Gaskiya zan so ganin wannan Faridan"
"Hmm, na san halin Sir Najeeb na kuma san 'yar uwata Farida, amma wallahi duk inda Sir Najeeb ya kai da jin kai da miskilanci to Farida ta taka shi. Maganar ta zama Sakatariyar sa ma bai taso ba. Farida Farida Hmm..."
"Wallahi ni kuma da ka yi bayanin nan sai na ga sun dace gara a samu wacce za ta iya taka ma sa birki ko zamu huta da halin san nan"
"Allah akwai matsala idan Farida ta yi aiki da Sir Najeeb, yaƙi za'ayi fa a kamfanin nan"
"Kar ka damu mutumina, ka turo ta kawai na ma ta interview"
...........................
Ɓangaren turaruka ya nufa a Mall ɗin saboda favourite perfume na shi ya kusa ƙarewa. Kamar daga sama ya fara jin muryan ta, kamar ranan da ya fara ji yau ma masifa ta ke yi. Zuciyar sa ce ta raya ma sa ba ita bace amma kunnensa ya ƙaryata hakan, domin kuwa muryar sak da wadda ya ji ranan a restaurant. Yana so ya maida hankalinsa kan abinda ya ke dubawa amma kuma idanuwan sa na ƙwaɗayin gaskata abinda ya ke ji, shin yarinyar ranan ce? ko kuwa wata ce mai irin muryarta.
Kasa daurewa yai sai daya juya ya maida dubansa ga inda ya ke jiyo muryan. Ita ɗince dai, 'yar mitsilar yarinya mai shegen surutun nan. Ya kai duban sa ga wanda ta ke wa masifan ya ga ba saurayin ranan bane wani ne daban, haka kawai ya ji tsanar yarinyar dama ma su irin halinta kam ina za su iya kama kai.
He couldn't believe it, garin kallonta sai ga shi har turaren da ya ɗauka yana shirin faɗuwa daga hannunsa. Yai saurin taro turaren tareda sake murmushi saboda wautar da yai, garin gulma. Abin haushin ma ba wai ya san yarinyar bane amma kuma gashi halayyarta ya dameshi. Ya saurin kauda kan sa lokacin da su ka zo za su wuce shi, tana tafiya tana surutu, kafaɗarta ya ɗan gogi bayansa kaɗan, yai saurin juyowa ya bi bayanta da kallo amma she's too busy talking to even notice what happened.
"Lousy girl" ya faɗi a fili sannan ya ɗau turaren ya bar wajen...
"Ni wallahi da na san ɗan abinda za mu saya kenan da ban biyoka ba Yaya Faruƙ. Duk abinda mu ka ɗauka ka ce yai tsada. Dama ai abu mai kyau shi ake siya da tsada"
"Wallahi mijin ki ya shiga uku Farida, ke fa ki ka ce mu zo nan ba ni ba. In ba dan ke ba mi zai sa na zo siyayya a nan"
"Amma Yaya ai ba ka cemin ba ka da kuɗi ba ko!"
"Allah ya shiryeki dai"
Har su ka bar Mall ɗin ba ta dena complain ba, dama wasu kaya ne Yaya Faruƙ zai siya na bikin ƙannen sa. Ƙarshe dai daga Mall ɗin kasuwa su ka wuce...
......................
Ana zaune ana duba kayan da su Faridan su ka siyo Maijiddah ta shigo tsakar gidan da sallama, dawowarta kenan daga yiwa Hajiya Yelwa kitso. Kai tsaye ɗaki ta nufa bayan ta gaishe su.
"Ke Jiddah zo nan" Farida ta kirata.
Ba mu su ta dawo ta tsugunna gefen Faridan ta ce "gani Anty"
"Kina gani kowa yana duba kaya yana sa albarka ke za ki tsallake ki shige ciki"
"Lah Anty zan cire hijabi ne na wanke hannuna sai na fito"
Zainab ta ce " ba wani, baƙin ciki ta ke ba nata kayan bane"
Farida ta wurga mata wani awarwaro wanda ya doki hancinta maimakon bakinta da Faridan ta yi niyya.
"Zan ci Ubanki agidan nan, sa'arki ce da zaki dinga yaɓa ma ta magana son ran ki. Na ce sa'arki ce!" Ta daka ma ta tsawa.
Anty Hanne wanda ita ce ta biyu a matan Baffa Musa kuma Umman Zainab ta ce " Yo ba gaskiya ta faɗa ba. Anyi auren ƙannenta biyu yanzu za a sake wasu biyun. Ai abin kunya ne ace ko mashinshini ba ta da shi"
"Da kyau, dama Zainab ai daga nono ta sha. To barin gaya mu ku, tafi ƙarfin tayi baƙin ciki da bikin ƙannenta saboda duk cikin su ba wanda yake auren mijinta. Na ta mijin na nan zuwa, za ku ganshi handsome gentleman da shi"
Hajara ta ce " waya ga handsome mijin shortie" gaba ɗaya sai aka sa dariya banda 'yan ɗakin su Maijiddan wanda su ke tausayinta. Maijiddah ta fashe da kuka ta tashi za ta bar wajen Farida ta riƙe hannunta ta ce " ba inda za ki je. Ki tsaya ki kalli kowacce ido cikin ido ki maida mata martani daidai da ita"
"Anty Farida gaskiya su ka faɗa, na yi kwantai"
"Ji mim shirme, inba dan ke da su ɗin duk 'yan ƙauye bane dan kina 20yrs ba ki yi aure ba shine kin yi kwantai. Tukunnama ke za ki aurar da kan ki ne? Ko mijin ya zo kin ce bakya so"
Ta kalli Hajara da ke dariya ta ce " ke kuma fantsararriya, za ai aurenki at 16yrs ba abinda ki ke hangowa sai kwanciyar aure saboda abinda ki ka sani kenan. Gaya min me ki ka iya? Wacce sana'ar ki ka iya? Jakar banza kawai, yanzu haka wankar tsarki mai kyau ba ki iyaba, tun tasowar ki ke daƙiƙiya ce, shiyasa ko jarrabawar WAEC ma ki ka ce ba za ki rubuta ba. Har mijin da za ki aura abin alfahari ne, ina shi ma wani tunkuzan ne kamar ki, ba ilimin Arabi bare boko"
"A hakan dai auren za ta yi, ta fi wasu da maneman ma ba ta da su" Anty Hanne ta faɗi tana hararan Farida
"Wallahi Jiddah ta fi ƙarfin ta auri miji kaman Haladu, mi za tai da irin su Haladu ai shi kam sai jaka irin Hajara. Mijin Jiddah ɗan gayu kuma mai ilimi ne Insha Allah"
Tuni wajen ya kaure da hayaniya, Baaba Sabuwa dama tuni ta shige ɗaki saboda takaici, ita ɗin kanta ba daɗin ganin Maijiddah ta ke agidan ba. Anyi auren ƙanwarta Murja duk da kuwa tsakaninta da Murjan shekara ɗaya ne to yanzu ga Salima ma za ayi na ta amma ita shiru. Tana jin hayaniyar su amma ko leƙowa ba ta yi ba.
Farida kam duk ta inda aka ɓullo kare Maijiddah ta ke ta hanata tafiya kuma ta hanata kuka. Ƙarshe dai sai gajiya su ka yi su ka barta dan indai wajen ɗasa magana ne to Farida ta kere su...
Da dare da za su kwanta Farida ta sa Maijiddah a gaba da masifa.
"Ke sai ana magana ki fara kuka, ba dole su raina ki ba. Ai su na magana ki na magana, wanda ya gaji ya bari. Tukunna ma ke idan za ki fita sai ki dinga saka dogin hijabai kamar matan Malam, a haka kam ai ko mutum zai tsaida ke a hanya ma zai ɗauka ke matar aure ce ya fasa"
" Lah na saba ne ai"
"A wannan zafin, to kul, kisa ɗan dai-dai amma banda dogin nan, idan ba haka ba zan sa almakashi na rage mi ki tsayin su"
"Kai Anty"
"I'm serious"
Maijiddah ta sa dariya...
Washe gari da sassafe Farida ta shirya za ta bi Yakubu wajen aiki saboda interview da ya ce za a ma ta yau. Sai da za ta fito daga ɗaki taga Maijiddah na shiryawa itama da alama fitan za tai,
" 'Yan mata ina zuwa da sassafe haka"
" Hajiya Yelwa ce ta kirani wai dan Allah na zo na yiwa jikokinta kitso yau za su tafi"
"Ba za dai ki gyara ba ko"
"Mi na yi Anty?"
"Jiya mi na gaya mi ki?"
"Kayya Anty"
Farida ta je ta binciko ma ta wani hijabi cikin kayanta wanda bai da tsayi ta miƙa ma ta. "Sa ka wannan"
"Anty da kin barshi, skirt ɗin da na sa fa ya ɗan kama ni"
"Saka!"
Ba mu su ta amsa hijabin ta saka, da ke ita ɗin guntuwa ce ya kusa kai ma ta gwiwa.
Haka su ka jero su ka fito, ɗakin Baaba Sabuwa kawai su ka shiga su ka gaisheta sannan su ka fita...
..............................
A office ɗin su Yakubu ta zauna wanda shi da colleage ɗin sa Engr Mathew su ke sharing. Tun a office ɗin ta dinga sa Mathew dariya da surutunta. Ƙarfe tara da rabi Yakubu ya dawo office ɗin ya ce Farida ta biyoshi. Kai tsaye office ɗin Anas su ka je. Da sallama su ka shiga office ɗin lokacin Anas na duba wasu takardu. Ɗagowar da zai yi ya ga yarinyar ranan, ta ke murmushi ya suɓuce ma sa cikin ransa yana ayyana abubuwa dayawa.
"Bismillah zauna" ya faɗi yana nuna ma ta kujera.
Yakubu ya ce " sir ni zan wuce office"
" Ok Yaks"
Sai da Yakubu ya fita sannan ya kalli Farida ya ce " Aisha Farida Salihu right?"
"No" ta faɗi tana kallon cikin idon sa.
"No kuma, ba sunan ki kenan ba" ya faɗi da mamaki
"To yallaɓai ka ga takarduna ka ga sunan da ke jiki kuma sai ka sake tambaya"
"Hmmm. Well na ga takardun ki kuma ba laifi i'm impressed. Sai dai aikin da za ki yi babban aiki ne kuma aiki ne da sai kin yi haƙuri sosai"
"Rayuwar duniya kanta sai da hakuri, balle aiki a ƙarƙashin wani" ta amsa tana kallon laptop ɗin da ke gaban Anas
"Da alama dai Yaks bai yi ƙarya ba gameda yarinyar nan, tabbas za a sha kallo tsakaninta da Najeeb" abinda Anas ya faɗi a zuciyarsa kenan. A fili kuma ya ce
"Malama Aisha, kasancewa muna buƙatan Secretary da sauri so gobe za ki fara aiki. Kafin nan zamuje ki ga office ɗin ki sannan zan nuna mi ki yadda za ki dinga gudanar da ayyukan ki"
"Abin da sauri-sauri haka?" Ta tambaya
"Ko ba za ki iya ba ne?"
"Kana ganin Ogan ka zai iya korana ne? Dan ance mini abu ƙiris mutum zai yi ya koreshi"
" I see, ashe kinada labarin wanda za ki yi aiki a ƙarƙashinsa. Kin san ba ya ɗaukan raini, Malama Aisha"
Farida ta ɗan yi murmushi ta ce "ni kuma banda mutunci ba, ga rashin haƙuri kamar zawo"
Anas yai murmushi sannan ya miƙe ya ce " welcome to Najeeb constructions miss Aisha Farida"
"Thank you" ta faɗi tareda miƙewa itama...
Ta yi mamakin ganin girman wajen da aka nuna ma ta a matsayin office ɗinta, cikin ranta tana ayyana irin shagalin da za ta yi a wannan waje, ga ƙaramar fridge ga AC, kai aiki cikin jin daɗi haka.
"Ehmm, Ogan ki bai ƙaraso ba tukunna so zuwa gobe idan kin fito za ki ganshi. Ba sai an nuna mi ki shi ba kina ganin sa za ki ganeshi" maganar Anas ya dawo da ita daga tunanin da takeyi.
"Ba matsala Sir Anas"
Anas ya ce " Kira ni da Anas ɗin kawai ai ke ƙanwar mu ce"
"Rufa min asiri, rashin kunyata ba ta kai nan ba. Kai fa sa'an Yaya Faruƙ ɗin mu ne"
"To kirani da Yaya kawai kinga dama ba ni da ƙanwa mace"
"Na gode Ya Anas"...
Ba su shiga office ɗin Najeeb ba haka su ka fito. Ya ƙara ma ta wasu bayanai gameda aikin, sannan ya ba ta takardar shaidar ɗaukanta aiki. Sai da ta biya office ɗin Yakubu sannan ta wuce gida.
Anas kuwa Farida na fita daga office ɗin sa ya ɗau waya ya kira Najeeb. A take ya sanar ma sa an samu sakatariya kuma gobe za ta fara aiki.
"she better be good" abinda Najeeb ya faɗa kenan.
Anas ya ce " ai mutumina sai ka ganta kawai. Wannan karan kai da chanja Secretary sai dai in ita ce ta ajiye aikin"...
Sai da Najeeb ya tsaya har Hajiya Mama ta gama ganin likita sannan ya maida ta gida. Da zai tafi kamar kullum sai da ta tsokale shi
"A dawo lafiya tuzuru"
"Ke fa tsohuwar nan kinada matsala" ya faɗi yana ɗan hararanta
"Matsala ta ɗaya ce, kai aure ka ajiye iyali kamar kowa. Ko sai ka gama tsohewa kafin kai auren"
"Ke zan aura ai, zan ɗau ragowar Alhaji Mustafah"
"Allah ya jiƙan rai, ai shi bai fi rabin shekarunka ba ya ajiyeni a gidan sa"
"Tsohuwa na tafi, kar ki riƙeni da surutu"
"Allah ya bada sa'a tuzuru"
Girgiza kai kawai yai sannan ya fice daga falon. Idan da sabo ya saba da tsokalar kakar ta sa, wanda da ita ya ke sakewa yai walwala kamar mahaifiyar sa. Kulawar da bai nunawa mahaifiyar sa ba a Hajiya Mama ya ke ba wa...
*💮SAKATARIYA TA💮*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣0️⃣5️⃣
Daga Najeeb constructions kai tsaye gida Farida ta wuce, ba ta samu Maijiddah a gida ba dan haka kaya ta chanja su ka wuce kasuwa da ƙanwar Maijiddan, amarya Salima. Da ke ita ɗin tafi Hajara mutunci shiyasa ta su ta ɗan zo ɗaya da Farida, duk da ba ta kai Maijiddah kirki ba inji Faridan.
Ɓangaren Maijiddah kuwa da ta je ta samu jikokin Hajiya Yelwa suna karyawa dan haka sai da ta jira su ka gama sannan ta mu su kitson, da ke ba wannan ne karan farko da ta ke mu su kitso ba, su na yi su na hira. Yawanci in sun zo hutu wajen Hajiya Yelwa to ita ke mu su kitso.
Ta tsantsara mu su kitso mai kyau harda adon beads. Dama ga yaran 'yan gayu da su. A Lagos su ke da zama ko hausan kirki ba sa ji. Maryam da su ke kira da Baby saboda sunan Hajiya Yelwa da ta ci 'yar shekara bakwai ce, sai ƙaramar Alizah 'yar shekara huɗu.
Maijiddah ta na zaune a ɗakin Hajiya Yelwa tana jiran ta, ta riga ta gama yiwa yaran kitso tun ɗazu amma Hajiyar ba ta nan, ta ce kuma ta jira ta har ta dawo.
Tana zaune kan carpet tana danna ƙaramar wayarta ƙirar Tecno wanda ya ji jiki ya tsufa. Tun wanda Yaya Faruƙ ya siya ma ta ne lokacin da ta yi sauka shekara huɗu da su ka wuce.
Ba ta ankara ba ta ji shigowar Alizah ɗakin da gudu. Ɗago idon da za ta yi ta ga ƙatuwar kyanwa ta yo kanta, ƙwalla ƙara ta yi ta hau gadon Hajiya Yelwa da sauri, ai kuwa kyanwar ma kawai sai ta hau gadon da alama kyanwar gudun Alizah ta ke. Maijiddah ba shiri ta dira a gadon ta nufi ƙofa da gudu. Ɗaga labulen da zai yi yai karo da ita, da ke guntuwa ce kanta ya tsaya ma sa iya ƙirjinsa. Ƙoƙarin tureshi ta ke ta wuce dai dai nan kyanwar ta shuri ƙafarta ta fice daga ɗakin. Laushin jikin kyanwar da ya taɓa ƙafarta ya sa Maijiddah ta yi suman tsaye a wajen.
Alizah ta fara cewa " Daddy, please catch the cat for me"
Bai saurari yarinyar ba, ya ɗauki Maijiddah cak yai kan gadon Hajiya Yelwa da ita. Miƙar da ita yai sosai sannan ya cire ma ta hijabi dan ta samu iska ya shigeta sosai, Ƙaramin fridge da ke ɗakin ya buɗe ya ɗau goran ruwa mai sanyi. Ya zuba ruwan a hannunsa ya shafa ma ta a goshinta da wuyanta amma still ba ta farfaɗoba. Ya sake yin haka a karo na biyu wanda yana shafa wuyanta da ruwan sanyin ta jaa dogon numfashi ta buɗe ido, ta fara ƙoƙarin tashi dan ta zauna, ya sa hannu ya tallafa ma ta tareda faɗin "relax"
Sai alokacin ta fara wuri-wuri da ido saboda ganin ba hijabi ajikinta ɗankwalin kanta ma ya zame.
"Duk a dalilin kyanwa ki ke son hallaka kan ki. Miye abin gudu a jikin kyanwa?"
Ba ta bashi amsa ba sai ma ta sunne kanta cikin cinyoyinta. Ƙananun ƙitson kalaba (braids) da ta yi su ka zubo.
Ganin yadda gashin ke da tsantsi ya sa shi taɓawa dan ya tabbatar gashin kanta ne ba na aro ba (wig). Yana son mace mai gashi, haka nan ya tsani mace ta ƙara gashi abinda har yau matarsa Aneesah ba ta dena sawa ba kenan tun yana faɗan har ya gaji.
Tabbas gashin ta ne ya faɗi a ransa. Ga shi baƙi ga tsawo ga tsantsi.
Shigowar Hajiya Yelwa ya sa yai saurin cire hannunsa.
"Alhamdulillah!, ka ga yadda na tsorata da Alizah ta ce wai Hauwa'u ta mutu"
Yai saurin miƙewa ya ce " ai Hajiya ba dan ina wajen ba ƙila mutuwar za ta yi. Kin ga yadda ta firgita kuwa, sumewa fa ta yi"
"Ai Hauwa'u kam sai dai Allah shi albarka kawai. Tukunna ma waya fito da kuliyar ne?"
Alizah ta ɓuya bayan Daddynta dan ta san ita ce ta tafka aika-aikar nan. Tun kafin Maijiddah ta zo Hajiya Yelwa ta sa aka rufe kuliyar kuma ta mu su kashedin kar su yadda su buɗe ta.
Hajiya ta kama hannun Maijiddah ta ce " dan Allah ki yi haƙuri kin san sha'anin yara. Fatan ba ki ji ciwo ba?"
Maijiddah ta girgiza kai sannan ta lalumo hijabinta ta saka.
Yana tsaye ƙikam yana jira ta ɗago yaga fiskarta da kyau, ɗazu cikin ruɗu ya ke bai tsaya ya kalleta sosai ba. Sai da ya ƙare ma ta kallo sannan ya ce "Hajiya an gama haɗa kayan ne?"
"Angama Yaya, na ce da Faty ma ta kai su cikin mota"
"Barinje in gani kar su yi mantuwa"
Har ya kai bakin ƙofa sannan ya sake juyowa ya kalleta, har a lokacin bata gama nitsuwa ba jikinta na ɗan kakkarwa, yai murmushi sannan ya fita...
Hajiya Yelwa sai da ta tabbatar Maijiddah ta nitsu sannan ta sa autarta Faty ta raka ta har bakin gate duk da kuwa Fatyn ta tabbatar da an sake kulle kuliyar.
Hannunta riƙe da ledar da Hajiya Yelwa ta bata su ka fito da Faty.
Yana gindin mota ya ga fitowar su dan haka yai saurin ɗaga wa Faty hannu alamar ta zo.
"Kinga barinje Yaya na kira na" Faty ta gayawa Maijiddah.
" Lah ba komai, sai anjima" Maijiddah ta faɗi ta yi hanyar gate ɗinsu. Ba ta yi wasu taku mai yawa ba Faty ta ƙwala ma ta kira.
Da ta juyo ta ma ta hannu alamar ta zo. Tsayawa ta yi ta rasa mi za ta yi. Ga Daddyn su Alizah ya ƙura ma ta ido.
"Ki zo inji Yaya" Faty ta faɗi da ɗan ƙarfi. Ba yadda za ta yi haka ta fara taku a hankali har ta kai wajen motar, gefen Faty ta tsaya tana kallon ƙasa a hankali ta furta " ina kwana"
"Ki shiga ya kai ki a mota" Faty ta faɗi tana ɗan murmushi ƙasa-ƙasa.
A hankali ta ce " Lah Faty sai ka ce ba ki san gidan mu ba, ƙasan layi ne ba nisa"
"Wato dai ladar ne ba kya so na samu" Ya katse ta
"A'a Yaya, Allah ba nisa. Na gode"
" ki shiga mota ko na sa akawo kyanwar ɗazu"
Ai cikin firgici ta kama handle ɗin ƙofa tana kokawa da shi. Faty ta fara ma ta dariya.
Shi ma murmushin yai sannan ya danne key ɗin hannunsa ƙofar ta buɗu...
Sai da su ka fita daga cikin gidan ya ɗan kalleta ya ga ta takure gefe ya ce " ki na tsoron kar na sayar da ke ne?"
Ta girgiza kai
"Ko nima ina da kamannin kyanwa ne"
"A'a"
"To ya kika takure, kin ƙi ki sake jiki haka nan ba ɗan hira"
Shiru ta yi dan ba ta san mi za ta ce ba. " ashe ke ce me yiwa Hajiyata kitso. Kin san yadda ta ke yabonki kuwa. Ga ki 'yar ƙarama da ke, anya kin kai shashida kuwa?" Yai tambayar ne dan samun damar gabatar da ƙudirinsa, yanayin tsayinta da ƙaramin fiskarta ya ke ganin kamar ba za ta kai 18yrs ba shi kuma a gaskiya ba zai iya auren under 18 ba.
"Na wuce mana" ta faɗa a hankali
"Faɗamin gaskiya, shekarun ki nawa?. Idan ki ka min ƙarya ma zan gane"
"20"
"Ishirin! Kai yarinya ba ki kai ba"
"Yaya kawai ƙaramin jiki ne dani fah, amma anyi auren ƙannena har biyu yanzu ma an kusa wasu biyun" sai da ta yi maganar sai kuma taji haushin maganar da ta yi.
Cikin zuciyar sa ya ke jimami sai dai bai bayyana ba ya ce " ke mi ya hanaki auren? Karatu ki ke?"
Shiru ta yi ta juyar da kanta wajen glashi tana kallon waje.
Bai sake tambayarta ba yana dai sake karantar yanayinta. Sai da su ka iso ƙofar gidan su sannan ya miƙa ma ta wayarsa ya ce " sa min numbar ki anan"
Kwarjininsa da girmansa shi ya hana ta mishi musu. Ta ƙarɓa wayar ta saka nambobin ta.
Miƙa ma ta kuɗi yai ta ƙi ƙarɓa.
"Kuɗin ƙitson da ki ka yiwa su Baby ne"
"Hajiya ta bani ai"
"Hajiya daban ni daban. Ki ƙarɓa ko na sa a kawo kyanwar gidanmu na ɗaure mi ki ita a ƙafa"
Ta ƙarɓi kuɗin ta ce " na gode Allah ya saka da alkhairi" ya amsa da amin. Sai da za ta fita ya ce " a samu a addu'a, Insha Allah anjima zamu hau hanya"
"Allah ya kaiku lafiya ya tsare mu ku hanya"
"Amin"
...........................
Su Faridah ba su dawo ba sai yamma lis, da su ka dawonma hidimar gida ya sa ba su zanta da mutuniyarta ba. Sai da ƙarfe goma ta gota na dare bayan ta gama goge doguwar rigar da za ta saka gobe sannan Maijiddah ta fara ma ta bayani.
"Anty Farida barin nuna mi ki wani abu"
Ta miƙa ma ta wayarta. Farida ta amsa wayar tana faɗin " wannan tsohuwar wayar ta ki ma ya kamata ki chanja ta"
*Alhamdulillah! ni da yara na mun sauka lafiya. Na gode da addu'arki gare ni*
*AbdulWahab Bello Hassan*
"Weeeeeehuhu. Waye wannan dan Allah? ki ce addu'ar mu ta kusa karɓuwa"
"Kayya Anty, ɗan Hajiya Yelwa ne fa"
"Sai aka yi me. Abeg gist me, ya akayi ya samu numbar ki?"
Maijiddah ta labarta ma ta duk abinda ya faru.
"Ai Insha Allah mun sameshi 'yar uwa ki dai cigaba da tashin dare da kikeyi. Allah ya kusa amsar addu'ar mu. Tukunna ke da me ki ka ma sa reply?"
"Ban ma sa ba"
" amma anyi 'yar ƙauye anan"
"To Anty mi zan rubuta?"
"Mtsssw, give me the phone jooor"...
.........................
Doguwar riga ta atamfa ta saka kalar atamfar ja ce da ratsin fari dan haka ta saka ƙaramin gyale fari. 'Yar powder ta murza sannan ta goga jan janbaki kaɗan wanda ya ke ƙara haska fiskanta.
A karo na biyu Yakubu ya aiko ta fito shi zai tafi.
"Jiddah wannan yayan na kun ko"
Maijiddah dai sai dariya ta ke ma ta...
Su na tafiya Yakubu na ta yiwa Farida faɗa akan indai haka za ta dinga makarar da su to zai dena tafiya da ita kowa yai hanyar sa. "Haba Ɗan Musa, sai kace wanda mu ke aikin asibiti. Ban isa na fito ban karya ba, Allah na gani"
"Lallai kuwa, Sir Najeeb zai samu dalilin koran ki cikin sauƙi kenan"
"Ba Sir Najeeb ba Allah ya sa Sir Salihu ne"...
Office ɗin Anas ta fara zuwa dan ta gaishe shi ta samu cleaner tana shara.
Ta juya za ta fita sai ga Anas ɗin ma ya shigo.
"A'a ƙanwar mu ce da wurwuri haka, ashe da dai ba za kuyi faɗan latti da Ogan ki ba"
"Ina kwana Ya Anas"
"Lafiya Aisha Farida"
Bayan sun gaisa sannan ta wuce na ta office ɗin.
Nan ma ɗin ana kan gogewa ne hakan ya tabbatar ma ta Ogan na ta bai ƙaraso ba, ta zauna tana danna wayarta...
Cikin takunsa na ƙasaita wanda ke ƙara ma sa kyau da kwarjini ya shigo kamfanin na sa. Duk inda ya wuce gaishe shi ake yi sai dai fuskarsar nan mur ta ke balle ma asa ran zai amsa gaisuwar. Dama idan da sabo to sun saba. Sir Najeeb ba ya amsa gaisuwa.
Yana shiga lifter ya danna 3rd floor wanda nan ne za ta sada shi da office ɗin sa.
Ya ma manta batun yau sabuwar sakatariyar sa za ta fara aiki dan haka kai tsaye ya shiga office ɗin, sai dai tundaga bakin ƙofa muryarta ya fara dokan kunnensa.
"No it cant be her" ya faɗi lokacin da ya tako cikin office ɗin. Sai dai itan ɗin ce dai ya gani, ba ta san ya shigo ba saboda hankalinta na kan wayar da ta ke yi.
Ƙanshin turarensa da ya cikata ne ya sa ta ɗago da idon ta.
"And who are you?" Ya faɗi yana ƙare ma ta kallo.
" The new secretary" ta amsa ma sa
" This is bullshit" abinda ya iya faɗi kenan ya nufi hanyar office ɗin sa.
Tunaninta baƙon Oga ne dan haka ta yi saurin tsaida shi. Cikin bayanin da Anas ya ma ta. Bai kamata wani ya shiga office ɗin Oga ba tareda izininta ba.
" Mr Arab you cant enter the office, my boss is not around" ta faɗi da ƙarfi.
Tsayawa yai da buɗe ƙofar Office ɗin ya juyo ya kalleta, lokacin ta baro wajen kujeran ta ta nufo shi.
" you can seat and wait for him there" ta nuna ma sa kujeran da baƙi za su zauna Idan sun zo.
Ƙura ma ta ido yai, itama idon ta na cikin na sa. Hazel eyes na shi ta ke kallo wanda ya sa ta ji wani kasala nan da nan ta yi saurin ɗauke na ta idon. Ta yi gyaran murya sannan ta ce
" please go and wait for him"
Girgiza kai yai ya sa hannu zai buɗe ƙofar Farida ta yi saurin buge hannun sa ta shiga gaban sa ta stretching hannayenta tana tare ƙofar da su. "Dan Uban ka, dan kana balarabe sai ka ce ba za ka bi doka ba, to ba ka isa ba"
Idonsa ne su ka firfito lokacin da ya ji abinda ta faɗi.
Ta kalleshi ta ce " you will not enter this office. Anta La adkul.....a'a ba haka bane, Anta La Tadkulul Bab.... mtsww, yau ga ranan zuwa Islamiyya nan, ni Aisha ɗan Larabcin ma ta gagareni"
Hannu ya sa a aljihu ya zaro waya ya kira wata number, ana ɗaga kiran ya ce da kakkausar murya "Come to my office now"
Mamaki ne ya mamaye fiskan Farida lokacin da taji abinda ya ce sai dai ta dake a wajen ba ta matsa ba.
Suna tsaye a haka Anas ya shigo. Ganin yadda Farida ta yi kane-kane a bakin ƙofar office ɗin Najeeb ya sa shi fashewa da dariya.
"Tell this crazy girl to get out of my way" Najeeb ya faɗi cikin tsawa.
Anas ya dubi Farida wanda jin abinda Najeeb ya ce ya sa jikinta yai sanyi, ta sauke hannayenta amma ba ta matsa a bakin ƙofar ba.
Ya ce " Aisha ya ki ka hana Ogan na ki shiga office? ko salon na ki aikin kenan?"
"Ya Anas ni ban san shi bane ai. Akace sunan Oga na Najeeb Jibo, kuma na ga wannan balarabe ne. Suna *Jibo* kan ba na fulani ba ne?"
Anas ya fashe da dariya ya ce " kuma da gaskiyan ki fa. Sai dai wannan bafulatanin ruwa biyu gareshi, ruwan fulani kuma ruwan larabawa"
"Ya Anas ina dai ba ya jin Hausa?"
"Hausa kai, hausa kamar Jakar Kano ma"
"Shikenan ni Aishatu, daga fara aiki har na tafka katoɓara"
"Fatan dai ba ki zage shi ba?"
A sanyaye ta ce " sai dai gobe kar a ƙara"...
"Barin ji mi Ogan zai ce" Anas ya faɗi tareda shigewa office ɗin Najeeb. Dama tuni Najeeb ya shige ya barsu su.
Yana zaune kan kujerar sa ya na kallon ƙofa lokacin da Anas ya shigo.
" lokacin da na ce ka nemo min secretary, ban ce ka nemo mahaukaciya ba. She's fired, find another one" abinda ya faɗi kenan lokacin da Anas ya ƙaraso wajen sa
Maimakon Anas ya bashi amsa sai ya sa dariya har da riƙe ciki.
"This not funny, da na yi aiki da wannan gara na dawo da Joseph"
Har lokacin Anas bai bar dariya ba, sai da yai mai isar sa sannan ya zauna ya kalli Najeeb da ya cika yai fam.
"First of all Aisha ba mahaukaciya ba ce, secondly, a iya sanina da Najeeb na san girman kan sa ba zai taɓa bari ya dawo da Joseph ba. Thirdly idan ka kori Aisha, kai za ka ɗau nauyin neman wata ko wani da kan ka. Aisha ƙanwar Architect Yakubu Musa Wase ne, and as far as i know Yakubu is like a brother to me dan haka ƙanwarsa ƙanwata ce"
"Wow! Ban san ka fara kalen dangi ba ai"
"Ni ma kuma ban san ka fara tsoron mata ba"
"What do you mean?" Najeeb ya faɗa a fusace
"Na san ka gane Aisha ita ce yarinyar da ta tada hayaniya a restaurant ranan. Shi ya sa ka ke tsoron aiki da ita"
"Tsoro?" Ya furzar da iska daga bakin shi sannan ya ce " i'll give her a chance, idan ba ta iya aiki ba zan koreta. And i dont care who's sister she is"
"Ko kai fa mutumina" Anas ya faɗi tareda tashi tsaye. Har ya fara tafiya ya juyo ya ce " Dan Allah, ya ka ji da ta hanaka shiga office ɗin ka?"
Najeeb ya jefe shi da biro, Anas ya goce yana dariya...
Yana fita ya samu Farida tana zaune hankalinta kwance kamar ba laifin da ta yi.
" ƙanwata na roƙa miki shi, dan haka ba wata matsala amma ki bishi a hankali"
"Na gode Ya Anas"...
Ta so jin maganarsu, amma bangon office ɗin sa soundproof ne ba abinda ta ji shiyasa ta haƙura da laɓen da ta yi ta je ta zauna...
Fitan Anas ke da wuya telephone ɗin office ɗinta ya fara ƙara. Ta san shine, dan ta nan Anas ya ce za ta fi comminicating da Ogan ta.
Ba tareda wani tsoro ko fargaba ba ta amsa kiran.
"In my office now" abinda ta ji ya faɗa kenan da kakkausan murya..........
*still on the free pages*
*💮SAKATARIYA TA💮*
.......(My Secretary).......
*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Free page*
0️⃣0️⃣6️⃣
Ta fi Minti biyar a tsaye bai ce ma ta komai ba, aiki ya ke yi ma a system na shi.
"Sir kai ka kirani kuma ka shanya ni kamar kayan wanki, idan ba abinda zan yi zan koma dan bana iya juran tsayuwa"
Ɗago ido yai yana kallonta. Lallai ma yarinyar nan, shi a tunaninsa da ta shigo office ɗin sa za ta bashi haƙuri sai ta yi ƙum da bakinta ko gaishe shi ba tayiba.
"Let me make this clear to you..."
"Sir Najeeb ka yi Hausa kawai zan fi ganewa, turancinkan nan ban faye ganeta ba. Lanƙwashe harshe ka ke kamar bature"
Bai ji mamakin maganarta ba duba da yadda ya san halinta.
" i will say this only once Miss Salihu. I do not tolerate laziness. This is an office, you should learn to behave yourself according to this company's rules. Is that clear?"
Kallon sa kawai ta ke yi ba ko kiftawa
"Miss Salihu is that clear!" Ya daka ma ta tsawa.
"Yes...yes Sir"
"Good, now get out of my office"...
Tafi minti goma ta rasa yadda za ta arranging files ɗin da ya bata, kamar da gayya aka hargitsa files su ka zama haka. Tana cikin yi kira ya shigo, ta yi tsaki kafin ta ɗauka.
"In my office now"
Doguwar tsaki ta ja sannan ta tashi ta wuce office ɗin sa.
Ce ma ta yai yana da meeting ƙarfe shabiyu. Baƙin ciki ya zo ma ta har wuya. Maimakon ya gaya ma ta da ya kira sai da ya bari ta sha wahala ta zo har office ɗin sa.
"Why are you still standing, get out?"
"Sir, na san kai Oga na ne kuma zan ba ka girman ka amma kuma wallahi ba zan ɗau walaƙanci ba. Sir daga zuwa na na yi jelen tsakanin office ɗinka ya fi sau goma. Haba dan Allah, indai saƙon magana ne idan ka kirani sai ka gaya min ba wai sai na zo har nan ba. Wannan ai salon mutum ya samu ciwon baya ne"
Ganin ya miƙe ya sa tai shiru. Har gabanta ya tako ya tsaya. " Miss Salihu, i know you are a lousy crazy girl but that should stop outside this company. Here, you are just a secretary, so work like one" yana gama faɗin haka ya fice daga office ɗin ya bar Farida baki buɗe.
"Allah ya isa na, mugu kawai. Daga ranan farko a addabi mutum da aiki kaman Jaki" ta yi tsaki sannan ta fice daga office ɗin...
...........................
Ƙarfe sha biyu saura minti biyu ya fito daga office biye da shi kuma sakatariyar sa Farida, tana ɗauke da wasu files a hannunta. Lifter su ka shiga saboda a second floor za a yi meeting ɗin. Ƙanshinsa ne duk ya bi ya cikata, ta rasa wannan ƙanshin na shi, its so inviting, so cool.
Kiiiinnnnn. lifter ta tsaya su ka fito yana gaba tana bin bayan sa har su ka shiga hall ɗin.
Kowa ya hallara a wajen dama shi ake jira. Dokar Najeeb ne lateness is a punishable offence.
Ta samu kujera kusa da mace ɗaya da ke wajen ta zauna bayan ta ajiye files a gaban Najeeb.
Duk yawancin bayanan su ba ganewa ta ke yi ba, ko dan maganar ta fi karkata zuwa ga ayyukan gine-gine da kamfanin ke yi ne...
Ƙarfe ɗaya saura minti biyar aka rufe meeting,su ka fito.
Yanzu ma bayanshi ta bi su ka haura. Sai dai ta yi laushi sosai tana ajiye files akan table ta kwantar da kanta.
Rufe ƙofar da yai ya sa ta ɗago idon ta. Ya cire suit ɗin sa, farar shirt ɗin ne kawai ajikinsa yana warware hannun rigar da alama dai alwala yai. Su na haɗa ido ya ƙara haɗa rai...
Sai da ya tafi ta fara ƙoƙarin neman banɗaki dan ta yi tsarki ta yi alwala. Office ɗin ta dai babu, ƙoƙarin fita ta ke matar ɗazu ta shigo office ɗinta.
"Assalamu Alaikum sister"
"Wa'alaikissalam, 'yar uwa sannu da zuwa"
"Suna na Munibat AbdulHamid, i'm an Engineer. Office ɗina na second floor"
"Masha Allahu. Suna na Aisha Farida, sabuwar sakatariyar Sir Najeeb"
"Na ce dama ko zamu sauka mu je sallah. Akwai masallaci a ƙasa"
"Wallahi na gode, kamar kin san abinda ke raina kenan , dama banɗaki na ke nema"...
Fita su ka yi Sister Munibat ta nuna ma ta inda banɗakin mata ya ke, sannan su ka sauko su ka wuce masallaci. Anan Farida ta ga wa su ma'aikata matan duk wanda tacewa ita sakatariyar Sir Najeeb ce sai su ce "Hmmm, Allah ya sa ki iya dan Sir Najeeb Sai a hankali"
Ita kam ba ta ce komai ba dan tun kafin su faɗi haka ta ji a wajen Yakubu da Anas.
Daga masallaci canteen ɗin kamfanin su ka wuce, su na shiga Farida ta hango Yakubu da wasu su na cin abinci dan haka ta yi saurin ƙarasawa wajen table ɗin su.
"Yaya Yakubu ka siya min abinci yunwa na ke ji"
Yakubu ya harareta ya ce " idan ba ki da kuɗin siya ki je ki karɓi ruwa, ruwa is free for all the workers here"
"Haba dan Allah, na ce ma Yayan ma ba za siya mun ba"
"Yayan ai ba na Allah Annabi bane. Na cin hanci ne"
Engr Mathew da ke gefe ya ce " sister ki zauna za'a siya miki abinci. You are our beautiful sister ai"
Farida ta je ta jawo kujera ta zauna. Yakubu ya ce "Matt, wannan yarinyar ci ta ke kamar gara ga ta da shegen son bati. Idan za ka bi shawarata ka barta ta siya da kanta idan ba haka ba kullum kai za ta maƙalewa"
"No problem, this beauty deserve to be serve like a Queen"
Farida ta yiwa Yakubu gwalo...
Su na cin abinci Najeeb da Anas su ka shigo, nan wajen yai tsit. Kai tsaye wani gefe su ka je su ka zauna inda wajene da aka tanada ɗan gefe da sauran mutane. Kujerun wajen da table ɗin ya fi sauran ƙayatuwa. Wajen cin abincin Sir Najeeb kenan, da ke Anas shi ne na hannun daman sa sai ya zamana tare su ke zama su ci a wajen.
Jin wajen yai shiru ba kamar yadda ta fara shigowa ba ya sa Farida cewa " ni kam mutuwa ce ta wuce ne? Na ga kowa yai shiru sai ƙaran sokala da fork kawai"
Yakubu ya taƙaleta ya mata nuni da ido. Sir Najeeb da Anas ta hango su na cin abinci.
Ta gane saboda Sir Najeeb ne kowa ya nitsu a wajen. Sakamakon da da ake cin abincin ana hira yanzu kam kowa abincin ya ke ci baki gum.
"Ya Anas...Ya Anas" muryarta ya karaɗe wajen.
Anas da ya ke kurɓan juice ya ajiye glass ɗin ya juyo da sauri. "A'a 'yar uwa ke ce, ya aiki"
"Lafiya yayana. Yaya wai ni an saka dokan hana magana ne anan? na ga anyi shiru"
Anas ya ce " ni ma ban sani ba amma ki tambayi Ogan ki"
Farida ta maida kallonta wajen Najeeb da ya cika ya kumbura kamar zai fashe. Ta ce " Sir Najeeb ka hana magana a nan ne??" Tambayar ta fi kama da gatse ko shaƙiyanci kuma da gangan ta yi hakan. Tashi Najeeb yai ya bar wajen. Yana fita daga canteen ɗin aka sa ihu. Wasu sai a lokacin su ka san miye aikin Farida, ta burge kowa, sai dai dayawa sun ji tausayinta dan a tunaninsu ƙarshen aikinta ya zo kenan. Harta Anas sai da yai dariya, shi kam sai da ya cinye abincinsa kafin ya tafi.
Suna fitowa a canteen ɗin Yakubu ya ce " tunda aikin ne bakyaso shikenan. Idan ya koreki za ki san zafin neman aiki ai"
"Haba Yakubu, mutumin nan fa mutum ne amma yadda ku ke zuzuta shi ku ke tsoronsa sai ka ce wani ifritun Aljani"
"Ni dai na gaya mi ki"
Wai da su ka taho da Sister Munibat ma harda ba ta addua'ar da za ta yi idan ta shiga office, ita kan dariya kawai ta yi ta wuce.
..........................
Tana zama a kujerar ta aka kira, as usual dai cewa yai ta zo.
"Sir gani"
Kallon walaƙanci ya ma ta sannan ya jefa ma ta takardar da ke hannunsa.
"Read it"
Tsugunnawa ta yi ta ɗauko takardar ta fara karantawa a zuciyarta.
"Read it loud" ya daka ma ta tsawa
Haka ta fara karanta ma sa daga farko har ƙarshe. Sai da ta tsaya sannan ya ce " i'm sure lokacin da aka baki takardar ɗaukan aiki an haɗa mi ki da wannan takardar, but you are so dumb to not have read it. Now, daga gobe ki fara shiga irin yadda aka tsara a dress code ɗin nan. This is a construction company not a fashion show"
"Sir, ni banda kuɗin siyan kaya irin wannan, kuma dai yau na fara aiki balle ace zan samu albashi dan haka sai ka yi hakuri har na karɓa albashi tukunna"
"Miss Salihu you are stepping beyond your limits, dont you dare talk back to me again" ya nuna ta da yatsa
"I gave you a week to find cooperate clothes. A week Miss Salihu"
"Ok Sir"
Hannu ya ɗaga ma ta ta juya ta tafi.
Ta ɗauka zai ma ta maganar abinda ya faru a wajen canteen sai ga shi bai yi ba. Ita kan bonus ɗin ta dama ta riga ta tanadi amsar da za ta bashi idan ya ma ta magana...
Aiki dai ta aikatu dan da gayya ma ya ke sata wasu ayyukan. Sai dai tunda ranar farko ce haka ta haƙura ta dinga binshi a hankali kar ya ce ma ta lazy.
A haka su ka ƙare aikin ranan, ƙarfe huɗu za su dinga tashi dan haka ƙarfe huɗu saura kwata ta fara haɗa kayanta. Kiririnkiririn sai ga telephone na ƙara.
"Mtsww sarkin naci" ta ɗauka fiska ɗaure kamar tana gaban Sir Najeeb ɗin.
Ajiye wayar ta yi ta shiga office ɗin sa. A ranta tana ayyana abin da za ta ce idan wani aikin zai ba ta.
Tana shigowa ya nuna ma ta wata laptop ya ce ta ɗauka ta tafi da shi gida wanda za ta dinga ƙarasa aiki da shi a gida kenan.
"O'o ni Aisha, wato agidan ma ba hutu za kai ba"
"What do you say?"
"Babu, na ce Thank you Sir"
Sai da ta juya za ta fita ya ce "Miss Salihu"
Haɗiye miyau ta yi tareda dunkule hannunta ɗaya ta juyo.
"Fix a meeting with the Sudanese tomorrow"
Wa su Sudanese kuma? Ta faɗi a zuciyarta a fili kuma ta ce "Ok sir"
Ta san ko ta tambaye shi ma ba gaya ma ta zai yi ba dan haka ta bari akan za ta samu Anas ya ma ta bayani...
......................
Gaba ɗaya a gajiye ta isa gida, Yakubu sai dariya ya ke ma ta wai indai a haka za ta ci gaba ba za ta jima da Sir Najeeb ba dan shi kam aiki ya ke so a mishi tuƙuru.
Bayan Maghrib ta kira numbar da Anas ya bata na wasu Sudanese da ke son haɗa hannun jari da Najeeb. Ta faɗa mu su meeting ɗin su da Najeeb gobe ƙarfe goma.
Su na cin abincin dare Baffa Musa ya aiko a kirata. A falonsa ta sameshi yana aikin lissafi a takarda. Ɗan nesa da shi ta zauna a ƙasa ta gaishe shi.
"Ya aikin dai"
"Alhamdulillah Baffa"
"Allah ya taimaka, iyayen yaron nan sun sameni kuma mun tattauna da su. Na ce su bani lokaci na yi bincike saboda kar a samu matsala irin na baya"
Farida ta rintse ido tana tuno abinda ya faru a baya. Ta ya za ta manta wannan babban al'amari daya faru a rayuwarta.
Maganar Baffa ya dawo da ita.
"Sun ce Asalin su 'yan Wudil ne amma kuma tunda Kakansa ya dawo cikin Kano da zama ya zamana 'yan uwan su sunfi yawa anan. Ina so idan komai ya daidaita da yardar Allah da ke da Maijiddah ƙarshen shekara ayi bikin ku tare. Tunda Allah ya sa Saminu ya amince. Na huta da yawan maganganu da ake akanta"
"Baffa wani Saminu kuma?"
"Yaron shagona"
"Baffa auren sadaka za ka yiwa Maijiddah, haba dan Allah sai ka ce wanda ta ke da wani aibu"
"Bance tanada aibu ba. Amma tunda har yanzu shiru ba wanda ya zo neman aurenta kinsan dai ba zan zuba ido ina ganinta haka har a gama auren ƙannenta ba"
"Wallahi Baffa kai bagidaje ne. Wai za ka aurar da ita wa yaron shagonka, irin ta yi kwantai ɗin nan,cab ɗi"
"Tashi ki bani waje. Ba shawararki na nema ba"
"Baffa dan Allah ka saurareni, Wallahi indai ka aurar da ita wa Saminu Jiddah ba za ta taɓa samun kwanciyar hankali ba. Walaƙantata zai yi dan ya san sadaka aka bashi ita"
"Ban nemi shawaranki ba. Tashi ki tafi "
"Baffa akwai wanda ya ke sonta fa"
"Waye?"
"AbdulWahab sunan shi, ɗan gidan Hajiya Yelwa wanda Jiddah ke wa kitso"
"Hajiya Yelwa?"
"Cikakken sunan sa AbdulWahab Bello Hassan"
Baffa ya ajiye biro ya kalli Farida da kyau ya ce " na san ki da yawar magana amma ban sanki da sharri ba. Yaushe ɗan gidan Alhaji Bello Kachako ya ce yana son Maijiddah"
"Allah Baffa da gaske na ke, ka tambayi Jiddah"
"Shi kenan, kiramun ita"
Ko da ta shiga ɗaki Maijiddan ta samu tana waya. "Ki je inji Baffa"...
Farida na shirin kwanciya ta jiyo muryan Baffa yana faɗa. Da sauri ta zari hijabi ta fita saboda ƙaramar riga ce a jikinta.
" kin san ko waye shi kuwa?, babban ma'aikacin custom ne fa. Ba na son sharri Maijiddah ki riƙe matsayin ki"
Duka matan sun hallara a falon dan suma faɗan Baffa ya tado su daga matsugunninsu. Maijiddah kam ta kifa kai tana kuka dan ta tsorata da masifar Baban na ta.
"Ikon Allah! Yanzu dan ba ki da mashanshani sai ki yiwa bawan Allah sharri. Ba ki tsaya ma kusa ba sai chan nesa da ke ki ke hangowa. Ni dama na san yawan zuwa gidan Hajiya Yelwan nan kwaɗayi zai sa miki" Anty Hanne ta faɗi tana tafa hannu.
"Munafukai anzo gulma. To ta Allah ba taku ba" ta kalli Baffa ta ce "Baffa ina ni na ce ma ka AbdulWahab na son ta, to ka manta da na yi maganar. Idan gaskiya ce ai ba za ta ɓuya ba idan ma ƙarya ne za a gani. Jiddah ta shi mu tafi"
Jiddah kam tana tsugunne a wajen ko motsawa ta kasa yi. Haka Farida ta zo ta ja ta su ka bar falon...
"Dan Allah ki bar kukan nan, tukunna kukan mi ki ke yi? Saboda Baffa bai yarda da ke ba? Shareshi idan AbdulWahab ya turo ai za su ga zahiri"
Cikin kuka ta ce "Anty Farida wai Baba cewa yai idan ma asiri na ke son yi akan shi gara na bari. Allah ya bani miji Saminu, ta ya mahaifina zai min wannan zargin. Har rashin miji zai sa na koma asiri"
" Jiddah ki godewa Allah, domin addu'arki ta ƙarbu Insha Allah. Ba ga ni ba, ko kin manta abinda ya faru da ni shekaru uku da su ka wuce, i was exactly your age lokacin. Wani surutu ne ba ayi ba, an zage ni an zagi Ummi, hatta Abbana da ke kabari sai da ya samu kason shi. Dan haka ki cigaba da addu'a kuma ki yi ƙum da bakin ki. Duk lokacin da AbdulWahab ya turo su za su ji kunya ai"
"Na gode Anty"
Ta gode Allah da Anty Farida ta yadda da ita lokacin da ta ji record ɗin hiran da su ka yi a waya. Ta rintse ido tana tuno abinda ya faru tsakaninsu duk da kuwa alokacin ba ta cikin hayyacinta saboda firgicewa da ta yi da ganin kyanwa.
Hiran su ta tuno wanda ya sa duk wani baƙin ciki ya kau daga zuciyarta.
*" Hauwerh za ki iya auran tsoho?"*
*"Mi zai hana?"*
*"wannan tsohon fa shekarunsa ɗai-ɗai har arba'in da ɗaya, ga yaran sa har biyu"*
*"ai ba tsoho ba kenan"*
*" haka ki dai ki ka ce gimbiya Hauwerh"*
*"zan samu amsata anjima ko?"*
*"sai bayan kwana uku"*
*"wai-wai har 3days. To, Allah ya kaimu"*
*amin*
Gaskiyarsa ya fi komai birgeta. *" ina son matata sosai Hauwerh, sai dai umurnin Hajiyata ne akan lallai in ƙara aure kafin shekara ta ƙare. Kuma kallo ɗaya na mi ki na ji kin birgeni"*
Ta sha ji ana hiran sa idan ta je yiwa Hajiya Yelwa kitso. A yadda ta fahimta matarsa na aiki a Abuja shi kuma da yara su na Lagos, sai ƙarshen wata ta ke zuwa mu su. Wannan ne dalilin da ya sa Hajiya Yelwa ta sa shi ƙara aure.
Kamar yadda Anty Farida ta ce za ta yi shiru har sai ya aiko gidan su. A da tunanin da ta yi shine gobe da safe ta playing record ɗin hiran su wa Baabar ta ta ji saboda ta yadda da maganarta ta kuma yiwa Baba bayani...
........................
Washe gari ma shigar atamfa ta yi duk da kuwa a dresscode ranar Jumua'a ne kawai aka amince asa kaya native.
Yana shigowa ta bi bayan sa da sauri.
"Sir kana da meeting da Sudanese ƙarfe goma. Sannan akwai wani Mr Habib Olalekan da ya kira ya ce yana buƙatar ganinka na ce ya zo ƙarfe tara"
"What about the files that i asked you to arrange?"
" na gama Sir"
"Bring them here"...
.........
Sati ɗaya kenan da fara zuwa aiki. Duk wani kafa da Sir Najeeb ya ɓullo da shi dan ya muzguna ma ta tana shanyewa, acewarta dole ta jure kar ya ɗauka ta gaza aikinta ne. Tsawa da masifa kam tana shan shi kullum.
A ɓangaren Maijiddah kam tunda sauran 'yan gidan su su ka ji labarin abinda ya faru sai su ka koma tsokanarta da habaici da Matar custom. Abin yana sosa ma ta rai sai dai ba yadda za ta yi tunda dama sun saba tsokanarta. Bisa umurnin Farida ta amince da AbdulWahab. A yadda ya tsara immediately zai tura iyayensa ayi maganar sai dai ta ce ya bari a gama bikin ƙannenta tukunna.
Da sati ta zagayo ta je yiwa Hajiya Yelwa kitso, kunya duk ya cikata lokacin da Hajiyar ta kira ta da 'surkuwa ta' da kyar ta iya ƙarasa kitson saboda yadda ƙannen AbdulWahab su ka sa ta agaba da tsokana.
Shirye-shiryen biki ake ba kama hannun yaro. Dan asabat za a ɗaura aure...
Kallon rainin hankali ya ma ta sannan ya ce "repeat what you just said"
"Sir Najeeb ina son ɗaukan leave na kwana uku. Ba zan zo aiki ba ranan Laraba Alhamis da kuma Jumma'a"
"You are crazy right? Yaushe ki ka fara aiki da za ki ɗau 3days leave?"
Ta yi shiru
"Answer me!" Ya daka ma ta tsawa.
"Sir, bikin ƙannena za ayi kuma..."
"And so?"
"Sir...."
"Get out of my office"....
Washe gari laraba ya ɗauka ba za ta zo ba sai ya ganta. A zuciyarsa ya ce ashe ta san mi ta ke yi. Sai dai ƙarfe ɗaya na yi da aka fita sallah ta yi tafiyarta.
Da ya dawo daga masallaci ya shiga office ya ga takarda akan desk ɗin sa.
*Sir na tafi, sai Monday zan dawo. Ka yi haƙuri wannan hidimar ta gida ce dole ayi komai da ni*
Duƙunƙuna takardar yai sannan ya cillar " crazy bitch"
Ya ɗau waya ya kira Anas.
"Hello mutumina ya aka yi?"