Maman Maama
Episode Fifty: The Utterance 2
Assalamu alaikum my dear fans. Baki ba zai iya bayyana muku irin godiya ta a gare ku ba a bisa karbuwar da littafi na ya samu a zukatan ku. Nagode Nagode sosai kuma nima ina sonku a duk inda kuke.
A duk lokacin da marubuciya ta dauki biron ta dan rubutu, to tabbas da akwai wani topic a ranta da take son yin rubutu a kansa. Dan haka duk abinda zata rubuta will be akan wannan topic din. Sanda nayi niyya kuma na fara rubuta Diyam abinda yake raina guda biyu ne, na farko shine illolin auren dole na biyu kuma karfin soyayya ta gaskiya. Dan haka duk abinda nake rubutawa akan wadannan abubuwan ne.
So aim din bawai na koyawa mata yanda zasu gyara aurensu bane ba, aim din na nunawa iyaye da sauran al'umma illar auren dole ne. Allah yasa za'a fahimci manufa ta, ba wai ina nufin rayuwar da Diyam tayi a gidan Saghir itace dai dai ba, a'a, ina nuna akwai possibility na samun irin wannan rayuwar a auren da aka gina shi da tubalin kiyayya.
A kodayaushe rubutu na is open for corrections, criticism and suggestions. Duk abinda ka gani wanda kake ganin ba dai dai bane ba zaka iya tuntubata ka nuna min ko kayi dropping comment yadda zamu hadu mu tattauna har a samu fahimta. Amma kuma, ita fahimta hausawa sunce fuska ce kowa da irin tasa.
Godiya ga wata baiwar Allah data yi min wani gyara a last episode, akan maganar da nayi ta cewa "nothing gives a man the right to hit his wife" what I should have said a gurin shine "nothing gives a man the right to hit his wife the way Saghir did" saboda munsan cewa an bawa maza damar horon disobedient wife da bakin sutturar su, shima kuma sai akace kar su taba fuska. Nagode baiwar Allah duk da bansan sunan ki ba. Lol
Kar in cika ku da surutu, ga Diyam...........
Na tsaya a gurin tamkar wadda aka dasa ni, ina kallon bayan motarsa, ina nan tsaye su Alhaji Babba suka fito suka shiga motar Kawu Isa suka tafi ba tare da sun ko kalli inda nake tsaye ina kukan rabani da yata ba. Asma'u ta fito da tazo ta kamani "Adda kiyi hakuri kizomu koma gida, ki rabu dashi yayi ta tafiya da ita din, Allah zai baki wadansu kuma ita din ma da kafafuwanta zata dawo gurinki" ta kama ni muka shiga ciki. Muka tarar da Inna ta zabga ragumi idonta yayi ja, Asma'u tace "dan Allah Inna kar ki wani tayar da hankalin ki, ance musu in babu su ba zamu iya rayuwa ba ne ba? Ai mu kwallon mangwaro muka yar muka huta da kuda wallahi. Da auren Saghir ba gwara babu ba?" Inna tace "hmmm. Asma'u ke yarinya ce. Ba zaki gane ba".
Ni dai sai na wuce su na shiga daki na zauna a bakin gado. All I have ever wanted tun da aka daura aurena da Saghir shine inji sanda zai furta da bakinsa yace ya sake ni. To gashi na samu amma kuma yanayin da sakin yazo min sai yasa naji sam banji dadinsa yadda nayi tunanin zanji ba. Hakan kuma yana da dangantaka da abubuwa da dama. Na farko zargin da Saghir ya sake ni saboda shi, wanda kuma ba gaskiya bane ba, na biyu zumunci daya karasa lalacewa tsakanin mu da yan uwanmu, na uku Subay'a I can't even imagine yadda rayuwar Subay'a zata zamo a gidan Saghir ba tare dani ba. In banda mutuwa menene yake raba uwa da yar karamar yarta? Amma ni gani a raye amma an raba ni da tawa yar. And I asked myself then, shin Saghir yana da wannan damar?
Ranar haka na karasa wuni raina babu dadi. Da nazo sallah kuwa ina dora goshina a kasa sai kuka, zuciyata ta cunkushe gabaki daya, na idar na daga hannuna da niyyar yin addu'a amma sai na rasa me zan roka kuma. Sai kawai na roki Allah daya dubi zuciyata tunda ya fini ni kaina sanin abinda yake cikin ta, na roke shi ya daidaita min lamurana zuwa ga abinda yake shine dai-dai bawai abinda ita zuciyar tawa take so ba, ya saka rabuwar nan da mukayi da Saghir ta zamanto mafi alkhairi a gare mu baki daya, sannan ya bayyana gaskiya ya goge zargi ya kawo daidaito tsakanin mu da yan uwan mu. Na kuma roke shi daya kasance tare da Subay'a a duk inda take.
My life had been full of challenges so far, na fuskanci kaddarori iri iri wadansu naji dadin yadda na dauke su wasu kuma I have made a total mess of them. Amma a cikin regrets dina babu rabuwa da Saghir, na daiyi regretting irin zaman da mukayi amma banyi regretting kuma bana jin zanyi regretting zama na dashi. For more than eight years muna tare dashi amma dai dai da rana daya ban taba jin zuciyata tana sonshi ba, ko da kuwa a cikin ranakun da yake kyautata min ne sai dai inni kiyayyar sa ta dan kwanta min amma ba dai ta tafi ba ballantana sonsa ya shiga. Nayi addu'ar kuma kullum, kullum nayi sallah sai nayi addu'ar idan zamana da Saghir ne mafi alkhairi Allah ya rage min kiyayyar sa a zuciya ta. Dan haka da akayi rabuwar sai nayi taking that as shine zabin Allah kuma ma roke shi ya cigaba da zaba mini.
Na fara zaman iddah a nan gaban inna, ba inda nake zuwa sai kewayen maman iman sometimes inyi kallo musamman in Asma'u ta tafi makaranta, sometimes kuma in zauna anan dakin Inna inyi ta karatu wanda shine yake kara nitsar min da zuciyata ina jina ina zama at ease. Inna ta gayawa Mama abinda ya faru, kuma tazo har gida ta ganni ta kuma yi min nasihohi sosai akan karbar kaddara da kuma shirin facing rayuwar da zata zo min. Tace "in kin gama iddah Diyam makaranta zaki koma. Kar ma kiyi tunanin aure gwara kiyi karatu ki huta kema jini ya dawo jikinki sosai. Sannan ki samu exposure. Kuma ki koma islamiyya ki karasa saukar ki dama kin kusa ko?" Na daga mata kai, tace "sai ki karasa kuma ki fara hadda, ki cigaba da bin sauran littattafan addini suma kina kara buda kwakwalwar ki" nace "insha Allah Mama". Washegari sai ga Rumaisa amarya tazo gurina. Muka wuni tare muna ta hirarrakin mu sai naji hankalina ya kwanta sosai.
Monday Sadauki yazo kamar yadda ya saba zuwa. Last Monday bai zoba ya kira Inna yace wani issue ne ya rike shi a Maiduguri amma tayi hakuri. Wannan Monday din kuwa tun safe naga tana ta ha蓷a masa kunun aya wai taga yana so, ta dama masa fura itama ta saka a fridge ni dai ina ta kallonta. Yamma tana yi, dama nasan da yamma yake zuwa sai na saka hijab dina na tafi gurin Maman iman muka kafa hirar mu. Bana son ganinsa yanzu kuma nasan kona zauna a cikin daki in yazo sai Inna tace in fito in gaishe shi. Amma muna zaune kawai sai ga baban iman da baki sunzo, dan haka dole nayi musu sallama na fita na koma gurin Inna. Ina shiga naga takalmin namiji a kofar palo, sai na jawo farar kujera na zauna a tsakar gida amma ina zama inna ta kira ni, na bata rai kamar zanyi kuka na tashi na shiga. Yana zaune a kasa, Asma'u kusa dashi da wata takarda a hannun ta tana nuna masa wani abu suna magana a nutse. Ga kunun ayansa nan a cup a hannunsa yana sha. Na zauna a gaban Inna nace "sannu da zuwa" ya dago ya min kallo daya ya mayar da kansa yace "sannu maman Subay'a" sai ya cigaba da yiwa Asma'u bayanin wanda na fahimci kamar takardar jamb ce take kokarin cikewa. Na mike na shiga daki nayi kwanciya ta. Sai naji Inna tace masa "Diyam fa sun rabu da Saghir" naji yace "rabuwa Inna" cikin mamaki, Inna tace "rabuwa fa, ya sake ta" yayi dan shiru sannan yace "ya Salam. Subhanallah. Abu baiyi kyau ba. Allah yasa hakan shi ya fi musu alkhairi" Inna tace "ameen" Asma'u tace "ai rabuwar ma itace alkhairi hamma, wannan auren na Adda ai dashi gwara babu" Inna tace "rufe min baki sarkin magana. Waye ya tambaye ki? Tashi ki fita" ta tashi ta fita. Sadauki yace "na dauka ai ko ganin ku tazo yi" Inna tace "uhm uhm, ai satinta biyu kenan anan. Tun sanda nayi maka wayar nan ai bata koma ba dama. Nan yazo har gabana ya sake ta yasa hannu ya dauki yarsa" yace "Subay'a? Ita ta bashi ita ko kuma shine kawai ya dauke ta?" Inna tace "ina kuwa zata bashi ita? Gata nan tunda ya dauki yarinyar nan kullum sai na ganta tana kuka kuma nasan kukan yarta take yi amma ya zanyi?" Yace "a'a in dai ba ita ta bashi ita ba to zata iya karbar yarta. Ai both islamically da constitutionally bashi da right din daukar yarinyar" Inna tace "to ta yaya za'a karbo ta kenan?" Yace "ba wahala ai. Ko hisba akaje akayi reporting zasu karbo yarinyar a hannunsa su kawo mata" Inna ta jinjina kai tace "mutanen nan sunyi mana ba dai dai ba daga ni har yaran nan, amma yanuwan mune. Bana son cigaba da rigima dasu so nakeyi a samu fahimta a tsakanin mu. Amma zabin Diyam ne" sai ta saka baki ta kira ni. Na gyara hijab dina na fita, sai na ganshi a zaune yana daddanna waya kamar ba shine yanzu suke magana rai rai da Inna ba, na zauna a gabanta nace gani, tace "Sadauki yace za'a iya karbar Subay'a a hannun Saghir in aka gayawa hisba. Kina so a karbo miki ita?" Na juya na kalle shi busy with his phone, at least a matsayin da yake dashi na yayana da muka tashi tare kuma Inna ta bashi wannan labarin ai ya kamata ko magana mai dadi ce yayi min, sai na dauke kaina nace "ina son karbar Subay'a Inna, kuma zan karbo ta insha Allah amma bana bukatar taimakon sa. I can do it on my own" sai naga yayi sauri ya dago kai yana kallona. Yace "how?" Nace "ba kace hisba ba? Ai nasan hanyar hisba din kuma ina da bakin da zanyi musu bayani in naje" Na daga kafada na mike na komawa ta daki.
Daga nan babu wanda ya sake maganar karbar Subay'a ni kuma kullum yarinyar tana raina, kullum zan kwanta bacci sai nayi tunanin ko tayi bacci? In ina cin abinci sai na tunanin ko taci in na tashi da safe sai nayi tunanin ko an tashe ta an shirya ta zuwa makaranta? Kullum kuma a kowacce Sallah sai nayi mata addu'a amma kuma kamar yadda Inna ta fada bana son cigaba da rigima dasu Alhaji Babba, so nake a samu daidaito. Amma daidaiton da baiyi involving komawa ta gidan Saghir ba.
Lokaci ya cigaba da tafiya, har nayi wata biyu a gida. Duk sati ranar Monday sai Sadauki yazo gidan da yamma, in kuma ba zai samu zuwa ba to zai kira Asma'u ko Inna yace musu ba zai zo ba amma ni ko zuwa yayi gaisuwa ce kawai a tsakanin mu, sai sometimes ya kan tambayeni ko da abinda nake so to which I always reply "babu komai. Nagode".
Su Alhaji basu sake kallon inda muke ba ballantana Saghir. Ni kuma sosai na kwantar da hankali na babu abinda yake damuna sai kewar Subay'a. Har yar kiba ta nayi na kara haske.
Ranar nan na hada kayan Subay'a da muka taho dasu gidan, nima kuma ina bukatar kayan amfani dan wadanda nazo dasu sunyi min kadan ga kuma har phone dita tana gidan Saghir. Amma sam bana son zuwa gidan Saghir, duk kuwa da cewa ina son ganin Subay'a amma bana jin zan iya taka gidan dan haka sai na bawa Asma'u ta kai mata sannan na lissafa mata abubuwan da zata dauko min kafin a debo kayana. Tunda akayi sakin inna take cewa za'a debo kaya amma jin su maman iman suna shirin tashi saboda sun kammala ginin su yasa Inna tace a bari sai sun tashi tukunna saboda a samu gurin ajiye kayan.
Asma'u ta shirya taje ta dauko min duk kayan da nake bukata, amma sai tace min Subay'a bata gidan, daga alama gurin Hajiya Babba ya kaita. Sai na fara tunanin to chanza mata school yayi ko kuma dai tana gida kawai? Sai kuma tace min Fauziyya tace in na kunna waya ta zata kirani. Kuma ta bani labarin cewa "kinga gidan nan kuwa Adda? Gaba ki daya ya lalace har wani karni yake marar dadi. Kayanki kuwa in ba'a je an debo su ba to kuwa sai dai a wuce dasu bola. Na tarar da Saghir a gidan ma, yana kwance a palo ni ko kallon sa banyi ba na shiga na dauko abinda zan dauko na fito".
Da yamma nayi charging wayata da daddare kuma na kunna. Fauziyya ta kirani few minutes after na kunna. Muka gaisa tace "Halima yanzu wai da gaske ba zaki dawo ba?" Nayi dariya nace "my fight is over Fauziyya. Na gama. Bai gaya miki ya sake ni ba?" tace "ya gaya min amma ai saki daya ne dan haka akwai chance na zaki dawo din. Ya gaya min komai bayan kin tafi, kuma ni zanji dadi in kika dawo gidan nan. He loves you da gaske, in ma da baya sonki yanzu gaskiya yana sonki. Ya gaya min dalilin da yasa ya aure ni. Ni kuma na aure shine saboda ina son inyi settling down sai yazo da maganar aure ni kuma na karba. But a yanzu halin da yake ciki bayan tafiyarki I don't think Saghir is the right person to settle down with. Sun daura abota shi da shaye shaye. Most of the time ma baya kwana gida, kullum masifa kullum zage zage. Shi ne na kira in gaya miki, for the sake of your only daughter ki dawo maybe zai dawo hankalinsa in kina nan".
Nace "kiyi hakuri Fauziyya, but kamar yadda na fada miki. Na gama. For more than eight years nake tare da Saghir amma babu abinda muka tsinta a ciki auren mu daga ni har shi in banda wahala. Rabuwar insha Allah itace alkhairi. And kar kice baya sonki, tunda har ya zabeki a cikin sauran mata ya aure ki to kuwa tabbas yana sonki. Ki ci gaba da kokarin ki, it will be okay with you insha Allah".
And then one day, lokacin har nayi period biyu ina jiran daya. Monday, ranar da Sadauki yake zuwa sai Rufaida tayi rashin lafiya dan haka Mama ta tafi dubata ta barmu gida ni da Asma'u. Ni nama manta ranar Sadauki yake zuwa dan haka ina zaune a palo ina kallon wani film din hausa da na aro a gurin maman iman kawai sai jin sallamar sa nayi. Na tashi zaune sosai na gyara hijab dina sai gasu sun shigo shida Asma'u tana ta zuba masa surutu shi kuma yana mata dariya. Ya zauna ta gaishe shi ya tambaye ta ina Inna ta gaya masa bata nan. Sai ya dafe kai "kash, yau kice bani da kunun aya kenan" Asma'u tace "lah, sai da tayi maka ai kafin ta fita" sai ta tashi ta dauko masa ta zuba masa yana sha sannan na gaishe shi "sannu da zuwa. Ya office?" Ya kalle ni yace "yauwa. Lafiya lau" and that was all. Naji wani makokon takaici ya tokare ni. It really does hurt to be ignored, especially by someone da kuka saba sosai.
Sai kawai na kara volume din kallo na a raina ina fatan karar zata dame shi ya tashi ya fita amma sai ma naga sun dauko takardu shida Asma'u suna dubawa suna ta magana, kallo nake amma hankali na yana kansu sai na fahimci maganar ssce suke yi tana cewa "ni dai dan Allah hamma ka cire ni daga makarantar mu ka saka ni a government school in yi exams dina a can, wallahi government anfi ci, private basa bayarda da amsa" yarike baki "au kenan amsa kike so a baki? Maimakon kiyi karatu kici da kanki?" Tace "chaf, wadanda ma suka fini kokari basa ci ballantana ni? Yanzu kuma kaga in banci ssce din nan ba jamb dina ta tashi a banza kenan fa sai na sake wata" yayi dariya yace "kinsan kuwa sau nawa na zana jamb? Kuma a karshen karshe dai ban samu admission din dana ke nema ba" sai ta juyo ta kalle ni tace "Adda kema da kin sani kin cike form din jamb din. Kinga sai muyi tare in ba haka ba sai next year kuma" nayi kamar ban jita ba sai naji yace "in kina so sai a kawo miki gobe" na juyo na kalle shi naga yana kallona sai na kalli sides dina kamar me neman wani abu sannan na nuna kaina nace "are you talking to me?"
Sai yayi kamar zaiyi dariya amma ya wani maxe ya dauke kai yace "kina so ko ba kya so?" Nace "ina so, amma karka wahalar da kanka gurin kawo min, zan kira yaya Mukhtar ince ya siyo ya kawo min" ya daga kafada yace "duk daya. Tunda kinci waec dinki ba sai kin sake ba" sai na kalle shi da mamaki, I don't remember telling him cewa nayi waec ballantana zancen naci, nace "ya akayi kasan naci waec?". Sai kawai ya zauna yana kallona. And then all of a sudden sai ganin Saghir mukayi ya shigo palon hannunsa rike da Subay'a. He looked at me then at Sadauki and then at me again. Subay'a ta saki hannunsa ta taho gurina da gudu na bude hannuna na rungume ta ina jin dadi har cikin raina.
Saghir yace "what the f....." Sai nayi sauri na mike nace "Asma'u dauki Subay'a ku fita" dan nasan halin Saghir zai iya fadin komai ko yin komai a gaban Subay'a shi babu ruwansa. Ai kuwa tun kafin su fita ya fara "wato na matsa na baku dama ko? Shine wato zaku cigaba daga inda kuka tsaya? Ba kwajin kunyar duniya ba kuma kwajin ta Allah ko?" Sai Sadauki ya gyara zamansa ya dora kafa daya akan daya yayi folding hannunsa yana kallon Saghir. Ni kuma sai na mike, gabaki dayan su basa gabana dan haka baxan tsaya su bata min raina a banza ba. Nazo zan wuce Saghir ya kamo hannuna "ina zaki je? Munafuka kina wani saka hijabi kamar mumina" nayi kokarin kwace hannuna nace "don't touch me" ya maimaita "don't touch me, don't touch me kullum don't touch me." Sai ya juya yana kallon Sadauki yace "but I did touched her. Dan haka gwanjo nace. Duk inda zaka shiga babu inda ban shiga na fita ba and I left my foot print there" raina ya kai kololuwar baci, ban ma san me zance ba sai ji nayi Sadauki ya danyi dariya yace "are you sure about that?" Na kama kokawar kwace hannuna daga rikon Saghir zuciyata tana tafasa, zan so ace na fisu karfi in hada su duk su biyun inyi ta duka, how dare they talked about me like that.
Saghir yace "of cause am sure kasan a ledarta na bare ta. Sabuwa fil aka kawo min ita and I took her virginity" I froze. What? Ba zan ma iya kallon side din da Sadauki yake ba amma sai naji yace "ita nake so, not her virginity so...." Na kwace hannuna da sauri nayi bakin kofa hawaye yana bin fuskata, kafin in fita Saghir ya finciko hijab dina ya dawo dani cikin palon, ya hada ni da jikinsa muna facing Sadauki, Sadauki ya mike tsaye, Saghir yace "me yasa zaki gudu ne? Dan ke fa ake wannan taron ai ya kamata ki tsaya ki saurara kema ki tofa albarkacin bakinki a ciki. For example, tell him about our first night, tunda yace bai damu ba tell him how I did it maybe zai damu" na fara girgiza kaina da sauri. It is either Saghir is drunk ko kuma kwakwalwar sa ta fara tabuwa. And he said it. "I raped her" and then I saw a flash of fire a idon Sadauki. Saghir ya sake maimaita wa "I raped her the first night da aka kai min ita gida na. That was how she got pregnant for me har ta haifa min twins".
Sadauki took one step sai nayi saurin kwace jikina daga Saghir na tari gaban Sadauki na daga masa hannu "don't. Kar kace wani abu kar kayi wani abu just go" Saghir yace "yeah. Just go. But before you go, listen to this. Na mayar da ita dakinta." Na juyo da sauri ina kallonsa zuciyata tana bugawa kamar zata bar kirjina nace "no, no" yace "yes. Na mayar dake tunda dama saki daya nayi miki kuma shima bada son raina ba. Na mayar dake saboda ina son ki sannan kuma saboda I want him to think of you every night of every day when laying on his empty bed har zuwa ranar da zaki bar duniya ko kuma shi zai bar duniya. Sai inga karshen soyayya".
Inna ce ta shigo dakin da sauri, daga alama taga motocinsu a waje kuma tayi sensing something is wrong. Tana zuwa bata ce komai ba sai ta kama hannun Sadauki ta ja shi da sauri ta fitar dashi daga palon. Kafin su fita ya juyo ya kalleni and I saw a look on his face similar to wanda na gani ranar da zamu rabu a gidan Alhaji Babba. Na juya da gudu na shige bedroom din Inna na rufe kofa.
[2/23, 9:26 PM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Fifty One : The Will
A jikin kofar na zame na zauna ina jin zuciyata tana wani irin bugawa, ji nake yi kamar zan mutu, kaina yayi wani irin zafi kuma hawaye ya tsaya a ido na. Ban taba tunanin it's possible ka tsani mutum kamar yadda naji na tsani Saghir a lokacin ba. Na fara girgiza kaina ina cewa "no no no" kamar mahaukaciya. I can't even imagine komawa gidan Saghir a matsayin mijina, I can't imagine him touching me again. I would rather die. Ina jiyo maganganu a palo kamar muryar inna amma bana gane me take cewa, sai naji ta taba kofar amma da yake ina jikin kofar sai ta kasa bude wa sai naji tana kiran Asma'u. Sai kuma naji ana knocking kofar. Da kyar na bude idona na matsa daga jikin kofar sai suka bude suka shigo su biyu sannan Subay'a ta shigo itama tana kallo na sai naga Asma'u tayi sauri ta dauke ta sun sake fita.
Inna ta durkusa gabana tana taba wuyana tana magana a hankali amma ni bana jin ma me take cewa. Sai kuma naga ta kama ni ta mayar dani kan gado ta kwantar dani ta juya na riko rigarta sannan cikin muryar da naji kamar ba tawa ba nace "Inna bazan koma ba. In na koma mutuwa zanyi" ta juyo tana kallona sai ta zauna tace "komawa ina?" Sai kawai na bita da kallo, wato Saghir saboda bai daraja ta ba bai ma gaya mata cewa ya mayar dani ba? Sai ta gane me nake nufi tace "cewa yayi ya mayar dake?" Ban iya bata amsa ba sai kuka, sai ta mike tsaye "wannan wanne irin abu ne? Wanne irin ya mayar dake kuma? Suzo nan su kare mana cin mutumci sannan kuma ya mayar dake bayan babu wani mataki da aka dauka? To babu inda zaki koma. Yanzu fa Hafsa take bani labarin wai kawun ku Isa ya bashi Suwaiba" Suwaiba yar kawu Isa ce itama kuma kusan set din mu ce, mun dan girme ta kadan. Lokacin muna yara ita da Rumaisa ne suke crushing on hamma Saghir, murja tana yawan gayamin cewa har yanzu suwaiba tana son Saghir amma ni ban taba ko saka abin a raina ba.
Inna tace "wato su suna can suna kokarin yi masa huce haushi shine shi kuma zai zo nan yace ya mayar dake? To ku biyu yake so ya hada a gida daya ko kuma ya yake so ayi? Ai indai kinga kin koma gidansa to ki tabbatar an zauna ne an hada ku anyi muku fada kowa an bashi laifin sa bawai kullum ace kece da laifi ba" tayi ta fadanta ni dai ina jinta kawai. Amma ni a raina nasan ko anyi mana fadan bana jin zan iya sake zama da Saghir, not after what he did today, not after what he said a gaban Sadauki.
Tuni da Sadauki da nayi sai naji wata irin fargaba ta shige ni. Tsoro nake ji sosai, tsoron abinda Sadauki zai iya yi akan furucin da Saghir yayi a gaban sa. Ina tsoron zuciyar Sadauki, ina tsoron zafin sa, ina tsoron rashin tafiyar sa, considering abinda yaji da kuma yanayin da ya fita a ciki, bansan hukuncin da zai dauka ba. Sai na samu kaina dayi masa addu'ar Allah ya taushi zuciyarsa Allah ya hane shi ga aikata abinda zaizo yayi nadama.
Sai magrib na tashi. Nayi alwala nayi sallah nayi kuka sosai a cikin sujjada ta na roki Allah ya kawo haske a cikin al'amura na. A lokacin ne Asma'u suka dawo ita da Subay'a. Subay'a ta taho gurina da gudu ta fada jikina tana kallona tace "Mommy kin daina kukan? Dazu naga kina kuka" nace mata "na daina subis" sai tayi dariya tace "Daddy ya tafi ko? Dama cewa yayi zai kawo ni gurinki in kwana biyu sai mu koma gidan mu tare" bance komai da akan wannan sai tace "Mommy kullum sai nayi kuka nace da Hajiya ta kawo ni gurinki ita kuma taki. Mommy dan Allah ni kar a mayar dani can gidan gwara in zauna a gurin ko kuma mj koma gidan Daddy na tare" sai na daga ta nace taje tayo alwala tayi sallah.
Na lura ta rame, ta fada sosai tayi baki. Kamar ba'a kula da tsaftarta sosai sannan idonta ya nuna alamar damuwa. Sai na yanke wata shawarar, bawai ni kadai ce bazan koma gidan Saghir ba har da Subay'a ma ba zata koma ba, tazo kenan.
Da dare ina jin Inna tana cewa Asma'u ta kira mata Sadauki, kamar tasan ina son in tabbayda lafiyar sa. Asma'u ta kira switched off, a raina nace nasan za'a rina, amma ban furta komai ba nayi shiru kawai. Nan fa hankalin Inna ya tashi tace "wai me ya faru ne mai zafi a tsakanin su? Ni sam banji dadin yadda naga Sadauki ba tunda kuma ya fita hankalina yana kansa wallahi" ta juyo tana kallona tace "me Saghir din ya gaya masa me zafi haka?" Na sunkuyar da kaina kawai, ni ba zan iya gaya mata kalaman Saghir ba. Jin nayi shiru sai tayi ajjiyar zuciya tace "Allah ya kyauta".
Washegari babu kunya babu tsoron Allah sai ga Aunty Fatima nan da Hajiya Yalwati da kanwar Hajiya Babba wai Alhaji Babba ya turo su su gaya wa Inna cewa Saghir ya mayar dani, a gaya min in shirya sai mu saka rana ni da Saghir din sai yazo ya dauke ni. Ni kawai kallon su na tsaya ina yi cike da mamaki. Inna tace "yanzu Fatima har da ke? Har dake za'a ci amanar marigayi dan bashi da rai?" Aunty Fatima tace "me akayi Amina? Yanzu mayar da auren shine cin amana?" Inna tace "ba mayar da aure ne cin amana ba, rashin kulawa da nuna son kai shine cin amana" sai ta lissafa musu dukkan laifuffukan Saghir wanda ni na gaya mata tace "ni ba wai goyon bayan Diyam nake yi ba ko kuma bana so ta koma dakinta ba, a'a, so nake a zaunar da Saghir shima ta fadi laifin Diyam din sai a hada su kowa ayi masa fada a bashi laifin sa. A ja masa kunne akan dukanta dan ni abinda yafi komai daga min hankali kenan" sai Aunty Fatima ta nuna itama bata ji dadin abin ba tace "ni duk fa bansan wannan ba, ni cemin sukayi Diyam tana kula Sadauki shi kuma Saghir yaji haushi ya saketa. Kema yadda muke dake ai kamata yayi duk abinda ya faru ki kira ni ki gaya min. Da Diyam da Saghir duk yayana ne ai". Amma ita kanwar Hajiya sai ta kama fada, ita wai lallai nayi wa Saghir sharri "babu wani shayeshaye da yake yi balle neman mata" sukayi ta bugawa da inna har tayi zuciya ta tashi ta tafi Aunty Fatima ma ta tafi sai Hajiya Yalwati ta zauna tace sai anjima zata taho. Daga jin haka nasan tsegumi ta zauna yi.
Tace "wallahi Amina karki mayar da yarinyar nan. Yaron nan fa bawai gyaruwa yayi ba. To yaron da baiji kan iyayensa ba ina zaiji kan wani. Shaye shayen nan fa munsan yanayi amma sai a rufe ido ace bayayi. Neman matan nan kuwa yinsa yake yi kamar babu gobe. Ita kanta Fatima da take wannan maganar rannan a gaba na naji tanayiwa Minal yarta fadan kar ta kuma kula shi. Dama Suwaiba ce tasa kuma yanzu sunce sun bashi dan haka ku rabu dasu, in dai abinda Diyam ta fadi gaskiya ne in ya auri Suwaiban ai zasu gani" Inna tace "za kuwa su gani. Ai ni zanso ayi auren nan ma ko dan gaskiya ta bayyana" Hajiya Yalwati tace "gaskiya kam zata bayyana. Tun yanzu ba gashi nan muna gani yana zuwa yana daukan ta a mota ba? Ahau, lokaci kadai muke jira".
Har tana shirin tafiya kuma sai cewa tayi "ni Diyam kuma ta wani zubin banji dadin tahowar nan taki ba. Dama ke ce mai dan saka shi yana dan kawo mana abinci gidan. Yanzu kuwa shiru. Rannan har ya fara zancen aurar dasu murja yanzu kuwa yadda yake a rikicen nan nasan ba lallai ne yayi ba". Inna ta dauki yan kudade ta bata tace ta siyawa yara sabulu.
Da dare sai ga wayar Saghir. Na kalli wayar kawai na dauke kai. Yayi ta kira sai na saka a silent sai ya turo min message "ki shirya. Rana ita yau zan zo mu tafi". Sai na kashe wayar gaba-daya na ajiye.
Washegari wai dan rashin kunya sai ga Hajiya Babba da kanta. Ina ganin ta nayi wa Asma'u text. "Ki dauki Subay'a ku bar gidan nan, sai na kira ki zaku dawo". Ina kallon su suka fice. Tazo ta saka inna a gaba "yanzu ya za'ayi ace kince ba zata koma gidan taba? Yanzu zumuncin kenan? Koma menene ya faru a tsakanin su shi ya hakura ita me yasa ba zata hakura ba?" Inna tace "tace ba zata koma ba. Ni kuma baxan matsa mata ba, matsantawar da nayi mata a wancan karon ma da ace zan iya dawo da hannun agogo baya da banyi ba".
Sai ta kama hannuna ta jani daki muka zauna a bakin gado tace "yanzu Diyam ke kinsan halin Saghir. Kinsan cewa ya chanja sosai saboda ke kuma ya chanja din. Yanzu da kika barshi Diyam Saghir duk ya koma yadda yake da koma fiye da haka. Me yasa ba zaki je ki karasa abinda kika fara ba? Ko dan saboda Subay'a" nace "Hajiya Saghir fa ba wai chanzawa yayi ba. Indai har da gaske ya chanza bai kamata ya koma ruwa ba dan bana tare da shi. Hakan yana nufin saboda ni ya chanza kenan ba wai saboda kansa ya chanza ba. To yanzu kuma in mutuwa nayi fa?" Tace "a hankali ai yake gyaruwar, in kin koma zai cigaba da gyaruwa ne" nace "Hajiya tun farko ba kwa ganin kamar akwai son zuciya da zalunci a cikin dora mim alhakin gyaran Saghir? Ku da kuka haife shi baku gyara shi ba tun yana danyensa ta yaya zaku bani shi bayan ya bushe kuma ku saka ran in kare rayuwata gurin gyaransa?" Tace "saboda munsan zaki iya. Kin fara kuma zaki iya karasawa" na girgiza kaina nace "bazan koma ba Hajiya" tace "saboda me?" Nace "saboda bana son shi Hajiya" sai ta tsaya tana kallona. Sai na tuno da ranar da Saghir yazo gaban inna yace baya son aure na. Hajiya tace "ba kya son sa fa kika ce min Diyam. Yanzu har idonki yayi budewar da zaki kalle ni kice ba kya son Saghir? Koma dai menene Saghir din nan, koma da gaske ne maganganun da kike fada still Saghir dai danuwan ki ne kuma duk kin da kike masa ba zaki taba cire jinin ki daga nasa ba. Mijinki ne kuma, tunda dai yace ya mayar dake Sannan uban yarki ne, ba zaki taba chanja mata uba ba" nace "Allah zai raya ta ko ba a gidan sa ba" sai ta mike da fushi ta fita, ina jinta tana cewa da Inna ina Subay'a zata tafi da ita, sai inna tace "Diyam tace Subay'a ba zata koma ba. Zata rike yarta" nan tayi ta bala'i "wallahi bata isa ba, ita tace ba zata koma ba sannan yar tasa ma ta hana shi?
Da dare inna ta kuma saka Asma'u ta gwada number din Sadauki but still bata shiga. Inna ta kalleni tace "ke baki san inda yake zaune ba?" Na girgiza kai nace "ban sani ba Inna. Sai dai office dinsa na sani" Asma'u tace "ni dai nasan kamar a hotel yake zaune. Amma bansan wanne hotel din ba" Inna tace "to ko Asma'u zan tura office din nasa gobe ta gani? Ni duk zuciyata bata min dadi wallahi".
Washegari Asma'u tana dawowa daga school sai gashi ya kirata. Tace "Inna ga hamma yana kira" Inna tace "to kiyi sauri ki dauka mana kar ta katse kuma? Alhamdulillahi" Asma'u ta dauka tana gaishe shi sai naga ta kalleni tace "tana nan" sai kuma ta mike zata fita, Inna tace "ina kuma zaki je?" Sai Asma'u ta daga mata hannu ta fita kawai.
Shiru shiru, ni dai ina zaune a kan kujera staring into nothingness har Asma'u ta dawo after like two hours. Ta zauna tace da Inna "yace ince miki yana lafiya kuma gobe zai shigo" Inna tace "shikenan? Duk wannan dadewar kuna waya shikenan abinda yace?" Asma'u tace "tambayoyi yayi ta yi min kawai. Akan Adda. Yanayin zamanta a gidan Saghir" Inna tace "ke kuma me kika ce masa?" Asma'u tace "everything. Duk abinda na sani na gaya masa sai dai kuma wanda ban sani ba. Abinda na fahimta shine duk shekarun nan shi ya dauka Adda lafiya take zaune a gidan mijinta" na dauke kai ina lissafin wanne ne abinda Asma'u ta sani wanne ne kuma wanda bata sani ba?
Washegari da safe muna breakfast yazo. Fuskarsa babu annuri ko digo a cikinta ya gaishe da Inna muma muka gaishe shi. Ya kalli Subay'a yace da inna "an dauko tane?" Inna tace "tunda uban ya kawo ta Diyam tace ba zata koma ba" yace "good. Ba zata koma ba. Ita ma kuma Diyam din ba zata koma ba sai dai in har ita ce take son komawar" ya juyo ya kalle ni yace "kina son komawa gidan Saghir?" Na sunkuyar da kaina ina girgiza kaina da sauri, yace "good. Then ki dauki wayarki ki kira shi. Ki gaya masa ba kya sonsa ba zaki koma gidansa ba. In yana son rabuwa ta arziki to ya kawo miki takardar ki within the next three days, in kuma ba haka ba kice masa zaki kaishi kara in yaso alkali ya raba ku".
Ya juyo yana kallon Inna yace "Baffa uba ne a gurina. Dan yadda nake jinsa a zuciyata har yafi yadda nake jin shi kansa wanda ya haife ni saboda Baffa ya bani abinda shi din bai bani ba. Baffa ya bani soyayya, ya bani kulawa, ya bani tarbiyya. And he used his last breath a duniya to tell me in kula daku, and that's what I have been trying to do, and that's what I will continue to do sai inda karfi na ya kare".
[2/24, 8:22 PM] Ummy Gugah LING: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Fifty Two : A Little Game
Inna ta fara sharar hawaye, ita dama kwana biyun nan komai sai kaga ta fara hawaye. "Allah ya ji kan baffan ku. Babu abinda bai gaya min ba sai kace yasan abinda zai faru bayan babu shi. Abinda na wulakanta shine yanzu gatana ni da yayana, wadanda kuma na daukaka fiye da komai sune muka zama abin wulakanta wa a gurin su." Sai Asma'u ta tashi ta koma kusa da ita tana rarrashinta, Sadauki ya mike tsaye yana kallona yace "ki kira shi yau. Gobe ki gaya min yadda kuka yi dashi". Na gyada kaina sai ya juya ya fice.
Ina kallonsu suka gama kukansu amma ni ko hawaye banji a idona ba, maybe ko kukan ya kare ne oho, nidai abu daya da na sani shine baxan koma gidan Saghir ba and that's final.
Sai yamma na samu courage din kiransa. Bugu daya ya dauka yace "ha! Finally. Kin shirya inzo mu tafi?" Na lumshe ido na na bude, ina bitar abinda Sadauki yace min nace "ba wannan dalilin da yasa na kira ka ba. Na kira ne in tabbatar maka da abinda na gayawa Hajiya sanda tazo. Aure na dakai ya kare Saghir. Ba zan koma gidan ka ba saboda rabuwa a tsakanin mu tafi alkhairi akan zaman. Ina neman ka sawwake min. Ka kawo ko kuma ka aiko min da takarda ta nan da kwana uku in kuma ba haka I will have no other choice than in kai karar ka alkali ya raba auren mu" ya yi shiru amma nasan bai ajiye ba, sai yace "are you threatening me Diyam?" Nace "ba threat bane ba, option ne na baka kamar yadda nima Allah ya bani option na ko in hakura in zauna da kai ko kuma in kai karar ka in baka kudin yin wani auren kai kuma ka sawake min" yace "ohh, abinda ya tsara miki kenan ko? Abinda yace ki gaya min kenan? To ki bude kunnen ki kiji sosai nima nawa sakon zuwa gurinsa. Kice masa nace bazan sake ki dinba, idan akwai abinda yafi court ya kai ni can. Amma kafin ku tafi court din bara in fara gaya muku abinda zai fari a can din. Muna zuwa zan zayyana wa alkalin cewa shi wanda ya taimaka miki kika kawo karar tawa tsohon manemin ki ne, na kama ku na hana ku harka shine kuka yi deciding kawo kara ta saboda in sakar masa ke. How about that?" Nace "kai kanka da kake fadar maganar kasan cewa ba gaskiya bane ba. Kuma duk inda alkali yake ai mutum ne mai ilimi wanda zai zai saurari kowa. Ni fa 拼a ce Saghir ba baiwa ba, tunda nace bana sonka set me free please" yace "in nayi haka Diyam ai na bashi abinda yake so kenan, na baku abinda kuke so. Ni kuma nayi alkawarin tunda kuka making fool of me for years sai na dauki fansa. Plus wulakancin da yasa police suka yi min. So here is another message to him. Tell him nace I want my job back, I am kind of out of money yanzu. In ba haka ba kuma zan fara spreading rumors a cikin ma'aikatan sa, and this time around I won't be drunk yadda zanyi passing clear message har su fahimci wanene real Mr Abatcha, suma su fara boye matansu. Kuma harda gishiri zan kara wa maganar" ya karashe maganar yana dariya.
Na cire wayar daga kunne na saboda yadda maganganun sa da dariyar sa suke kara huta ga already wutar da take ci a kirjina. Shin anya kuwa Saghir yana tsoron Allah? Shi karya bata yi masa wuya. Sanda ya dake ni a gida ya nuna yana zargina da Sadauki banji haushin sa ba kamar wanda naji akan maganganun da ya fada ranar nan akaina a gaban Sadauki, it shows cewa abinda yayi din ma bashi da remorse akan sa tunda har fada yake yi proudly a gaban third party. Yanzu kuma maganganun sa sun nuna min cewa ba wai ya mayar dani bane ba saboda yana son aurena ba, ya mayar dani ne to get back at Sadauki. Am not a toy, am a person with zuciya a kirjinta da kuma jini a jikinta. Am not going back.
Da dare na gwada wayar Sadauki dan in gaya masa abinda Saghir yace amma naji har yanzu bata shiga. Haushi ya ishe ni na ajiye ta kawai. Amma sai na gayawa Inna duk abinda Saghir yace akan maganar Sadauki. Ta juya kai tace "wannan yaron baya kyautawa. Shi bai san hukuncin wanda yayi wa wani irin wannan sharrin ba? In kotun za'a je fa shine a kasa dan bashi da wata shaida" sai kuma tace "ni bana son zuwa kotun nan wallahi, zuciyata bata so, yan'uwan mu ne mutanen nan, so nake ayi sulhu a tsakani ba sai kowa yaji ba. Ba ga Suwaiba nan ba an bashi, kuma yana da wata matar a gida me yake nema kuma. In kudin yake so sai a bashi shima in dai za'a rabu lafiya. Ni kotun ce bana so, kuma bana so ya bata wa yaron nan suna a gurin mutanen da suke ganin girmansa".
Nima kuma bana son court din, amma kuma bana son komawa gidan Saghir kuma bana son in watsawa Sadauki kasa a ido ince bazan je ba. Dan haka ranar sai naki bacci na kwana ina gayawa Allah. Kuma na tabbatar ya jini kuma na yarda da cewa zaiyi hukuncin da ya dace.
Washegari da safe Asma'u ta tafi school ni kuma na koma na kwanta in danyi bacci sai naji karar wayata. Na dauka ina kallon number din Sadauki. Sai na jujjuya wayar a hannuna dan in tabbatar da cewa tawa ce bata Asma'u ba. Sai data kusa katsewa sannan na dauka da sallama na gaishe shi yace "ya kuka yi?" Sai da bashi labarin duk abinda Saghir ya fada. Sai kawai naji yayi dariya, yace "that man is so predictable. Ya fadi exactly abinda nake so ya fada. Tell him, na tsorata na tuba nace yayi hakuri kar ya zubar min da mutunci a gurin mutane, kice nace ya dawo ya cigaba da aikinsa ai dama ni ban kore shi ba shine ya daina zuwa. Sannan kice masa kema kin hakura ba kya son zuwa court dashi dan haka zaki koma gidan sa amma kina so please ya baki wata biyu saboda kina so ki shirya sosai" nayi saurin cewa "bazan koma ba" yace "I know. But just tell him that" nace "saboda me?" Yayi shiru sannan yace "do you trust me?" Nayi shiru nima ina lissafa lamarin sannan nace "yes, amma ina bukatar bayani" yace "okay, let me break it down for you. Bana son ke ko Inna ku shiga court dashi saboda kamar yadda Inna ta fada yan uwanku ne babu yadda zakuyi dasu. Sannan kuma ko an kaishi court din karshe kawai raba auren za'ayi and to get even that sai anyi ta faman cecekuce ana saka ki kina bayar da labari kina kara maimaita wa. I don't want to put you through that emotional trauma. You have had enough of your share of emotions. Still kuma in nace zamuyi sueing dinsa for abinda ya fada a kunnena yayi, ba lallai ya samu wani sentence mai kyau ba saboda a lokacin da yayi din akwai aure a tsakanin ku dan haka iyayenki za'a jawo cikin case din for marrying you off that young. Bana son insa Inna cikin wannan maganar. So option dina shine ya zama tsakani na dashi ne kawai ku kuna gefe. And I promise you ba zaki koma ba but for that I need you to call him ki gaya masa abinda nace".
Nace "okay, zan gaya masa" yace "thank you. But please kar ki gayawa Inna. Let it be our little secret".
Ban gayawa Inna din ba kuma ban kira Saghir ba sai washegari. Ji nayi bana son kiran nasa dan haka sai na tura masa text message na fada masa abinda Sadauki yace in fada. Sai kuwa gashi nan ya kira ni na dauka da kyar, yace "it wasn't so hard now was it? Dama nasan zamewa zaiyi ya barki. Ai mutane irin su babu abinda suke so irin su gyara public picture dinsu, ina komawa kuma zanyi requesting karin albashi kuma sai inga in zaiyi denying" yayi ta maganganun sa ni dai bance komai ba har ya gama sannan yace "and you? Mai zakiyi da wata biyu?" Nace "shiryawa nake so inyi sosai" yace "wacce irin shiryawa kuma? Ba kayanki kawai zaki zuba a akwati ba?" Nace "ina so in shirya emotionally, bayan abubuwan da ka fada ranar nan a gaban Sadauki ai you should be greatful da nace zan dawo din ma" sai na katse wayar kamar nayi fushi na kashe ta ma gaba daya.
Daga nan komai ya lafa a bangaren mu. Two weeks after that Sadauki yazo yayi wa inna sallama yace zaiyi tafiya zuwa Canada. Yana shigowa Subay'a ta zagayo ta dawo bayan kujerar da nake zaune. Muka gaishe shi ya amsa sai ya mika mata hannu "Subis come here" sai ta makale. Yayi dariya yace "inna na kawo karar Subay'a, bata gaishe ni" Inna tace "ke! Ba zaki zo ki gaishe shi ba?" Still taki zuwa, zanyi mata fada yace in rabu da ita, yayi wa Inna bayani "dama family na na Maiduguri kusan duk suna Canada, zan danje in yi musu kwana biyu. In naje zan kira ku da number din da za ku same ni da ita should in case ko wani abun zai tashi" Sai Inna ta nuna irin bata ji dadin tafiyar tasa ba, Asma'u harda matsar kwalla yace "ko wata daya fa ba zanyi ba. Just hutawa nake so inyi saboda ina aiyuka da yawa a nan".
Yana fita Subay'a ta zagayo cinyata tace "Mommy bana son mutumin nan" Inna ta kwade ta da muhuci tace "kar in sake jin kince ba kya sonsa, kuma in na sake ganin yazo kin ki gaishe shi ni dake ne. Babanki ne shi, tunda yayan babarki ne".
Sai bayan tafiyar sa Inna ta tambayeni "wai ya kuke ciki ne maganar Saghir? Ni baki ce min komai ba" nace "na gaya masa abinda Sadauki yace in fada masa, shi kuma yace ba zai sake ni din ba sai dai aje court din. Shi kuma Sadauki yace vaya son muje court dasu" inna tace "nima bana so, to amma ai ba zaki yi ta zama da aure aka ba. Dole dai cikin biyu za'ayi daga. Bara ya dawo daga canadan muji".
Sati daya da tafiyar Sadauki muka je gidan Mama gabaki dayan mu. Anan ne muke samun labarin ashe rigima ake tayi a sharada tsakanin Alhaji Babba da kawu Isa. Kawu Isa yayi wa Saghir huce haushi na da suwaiba, har Saghir ya karba ya an fara shirye shirye sai kuma yaxo yace ya fasa ni zai mayar sai kawu Isa ya nuna cewa ba'a kyautawa yarinyar ba, amma as usual, Alhaji Babba ya goyi bayan dansa.
Mama tace "ni tsoro nake ma Allah yasa bai lalata musu yarinya ba, dan labaran da muke ji basu da dadi".
Bayan dawowar mune nayi bakuwa. Fauziyya. Ni ban san ma tasan gidan mu ba sai yau. Na karbe ta sosai muka shiga daki nayi serving dinta abinci da drinks. Sannan tace "muna ta jira kuma har yanzu shiru" nayi dariya kawai, sai tace "ko sai za'a koma sabon gida sannan zaki dawo?" Nace "sabon gida kuma?" Tace "eh mana, ko bai gaya miki ba ya siya mana sabon gida? Sai ta fara yi min bayanin girma da kyan gidan "kowa da part dinshi, part din kowa yayi girman gidan da muke ciki. Yayi order komai na gidan next week za'a kawo su" sai ta nuna min key din mota "kinga ya siya min mota, kema ina jin kina komawa za'a siya miki taki. Shima ya sake wata" na gyara zama ina nazarin ta nace "why are you here Fauziyya?" Tace "ziyara na kawo miki mana. Kuma in gaya miki alkhairin da ya samu mijin mu dan in kwadaita miki komawa gidan. Hausawa sunce the devil you know is better than the angel you don't know. Na zauna dake lafiya, gwara ko dawo akan a kawo min wata wadda ban sani ba".
Bayan tafiyar ta na zauna tunani. Kudi? Lokaci daya? Saghir? Ina ya samu kudi? And I remembered lokacin daya samu aiki yazo yake bani labari yace "financial secretary aka ce miki. Ni nake kula da duk harkokin shige da ficen kudi a companyn".[3/7, 9:06 AM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Fifty Three : Check up
Sai naji tunani na ya tsaya. I just want to make a sense of wannan abin but na kasa believing abinda nake thinking. Is Saghir helping himself out of Sadauki's money? Ko kuma yana blackmailing Sadauki ne akan wannan maganar? But anya Sadauki zaiyi paying Saghir irin wannan kudin saboda empty threats dinsa? Tun sanda yayi threat din ni ban ji ko alamar tsoro a voice din Sadauki ba. Menene ma kuma dalilin da yasa Sadauki ya mayar wa da Saghir aikinsa? In dai kuwa har Saghir kudin Sadauki yake dauka then he is dumber than I thought.
Koma dai menene ni abinda na sani shine ya kamata inyi warning Sadauki akan ya kula da kudinsa tun kafin Saghir ya debi wanda zai kassara Sadauki ko kuma shi wanda ba zai iya biya ba. Kamar yadda na tabbatar zan mutu haka na tabbatar Sadauki ba zai bar masa ba.
Wayar Asma'u na nemo na dauki number din da naga Sadauki ya kira ta rannan na saka a tawa wayar nayi dialing amma sai taki shiga, naji kamar in jefar da wayar saboda bakin ciki, wato a wannan number din ma sai da yayi blocking dina? Wai me yake tunanin kansa ne? Ni ma na damu, sai sune suyi tayi ai daga shi har Saghir din.
Washegari Saghir yazo gidan. Ya ci kwalliya fiye da yadda yake da sai sheki yake yi kamar tarwada. Sai naga rashin kunyarsa da har zai iya shigowa palon Inna bayan duk abinda yayi mata da kuma sakinna da yayi a gabanta. Subay'a ta tafi da gudu ta rungume shi ya daga ta sama yana juya ta kamar yadda yake yi mata sanda muna gidansa. Asma'u tayi tsaki ta fita. Sai ya dan rissina ya gaida Inna ta amsa masa ba yabo ba fallasa. Sai ta dauki mayafinta tace min zata je unguwa. Ya zauna yana kallona yace "babu gaisuwa gimbiya" na kalle shi nace "yaushe babana ya zama sarki ballantana ni in zama gimbiya?" Yace "ai ba gimbiyar gari bace ba, gimbiya tace ni kadai. Kinsan cewa an bani kyautar budurwa naki karba saboda ke? Ke kinsan wanne irin so nake miki kuwa Diyam?" Nayi shiru ina tunanin irin maganganun daya fada a nan palon a gaban Sadauki, is that his version of love?
Yace "wata biyun nan yayi min yawa please. Ki rage. Ko kuma ince na rage miki da kaina. Na sayi sabon gida, you are going to like it. Zanyi tafiya zanyi two weeks kafin nan komai na gidan ya kammala ina dawowa zamu tare. So, I want you to get ready kafin nan kafin lokacin dan har dake din zamu tare a lokaci daya. Kinga da kin koma ma da dake zamuyi tafiyar nan. Am taking Fauziyya to the honeymoon I promised her, but in kin koma kema sai muyi fixing time ki zabi kasar da kike so mu tafi" na gyada masa kai kawai a raina ina jin haushin Sadauki da yace ince da Saghir zan koma. I don't like this idea at all.
Ya fara duba kayan jikin Subay'a "wannan kayan duk sun tsufa a zubar dasu Diyam. Ga kaya nan na taho mata dasu suna mota sai ta cigaba da amfani dasu" sai ya dora ta akan cinyarta tana ta zuba masa surutu yana dariya, ina jinsu ya fada mata zaiyi tafiya ita kuma ta fara lissafo masa kayan da zai siyo mata. Sannan tace "Daddy dan Allah ka dawo da wuri mu koma gidan mu ni nafi son zama tarr da kai da Mommy" yayi pecking dinta a cheeks yace "ina dawowa zamu koma kinji princess? It is going to be sabuwar rayuwa for us".
Sai naji a raina cewa tunda har yanzu ni matarsa ce then it is my responsibility inji source din kudinsa. Sai nace "kudi ka samu ne masu yawa haka? A ina?" Sai ya watso min wani mugun kallo yace "matse ni sai in gaya miki, kinsan dai tunda kika sanni da arziki na kika san ni ko? Ko kin taba gani na ina gyaran matattun motoci? Wanda ya samu dukiya sama ta ka shi ake yiwa tambayar inda ya samu dan zata iya yiwuwa yankan kai ko fashi da makami yake yi".
Sai da yasa na raka shi har bakin kofa, ya fito da kayan Subay'a jaka guda ya mika min sannan yace "I will be seeing you soon, sweet pie".
Washegari jirginsu ya daga shi da Fauziyya, I didn't even know ina suka tafi sai ya suka sauka ya kira ni yace min sun sauka a Miami, yace in ajiye number din saboda zai ke kira na da ita.
Bayan tafiyar Saghir ne Asma'u ta kammala jarabawarta, tayi candy, sannan kuma hakan yazo dai dai dayin saukar Alqur'anin ta. Wannan yasa ta shirya walima a nan gidan mu ita da kawayenta. Inna ta aika wa duk yan'uwa aka gayyato su kuma ga mamakin mu sai gasu sunzo, sai dai abinda muka lura dashi shine babu jituwa tsakanin iyalin Alhaji Babba da kawu Isa. Aka gabatar musu da abinci iri iri wanda su kansu sai da sukayi mamaki, daga abincin da aka ci har zuwa sutturar da muka saka daga mu har Inna duk sun nuna cewa ba a cikin kunci muke ba. Su Murja sai tambayata suke yi "yaushe zaki koma gidan hamma?" Murja ta jani gefe "dan Allah Diyam in baki koma bama kiyi masa magana ko zaiji maganar ki. Kinga maganar auren nan fa ta tsaya duk uban kudin da yake samu kwanan nan amma yace ba zaiyi ba. Shi kuma kawu isa da muke tunanin tura masa samarin mu shi kuma gashi yanzu ko magana basa yi da Alhaji" nace "wai me ya hadasu ne?" Ta rufe baki tace "ba za'aji a baki na ba".
Kwana biyu da yin walimar Asma'u sai ga Kawu Isa a gidan mu. Mamaki ya ishe ni na tuna ranar da yace sun cire mu a cikin zuri'a ranar da sagjir ya sake ni a gabansu amma yanzu gashi few months after ya dawo da kafafuwansa. Muka gaishe shi ni da Asma'u muka fita muka basu guri da inna. Sun jima suna maganganu kafin muji ya fita sannan muka dawo dakin. Asma'u ta saka Inna a gaba da tambaya "me yace? Me ya faru" Inna tace "ina ruwanki? Suda mai bakin magana"
Sai da Asma'u ta tafi islamiyya sannan inna ta bani labari. "Zuwa yayi yace min wai dan Allah duk yadda za'ayi kar mu mayar dake gidan Saghir. Ashe abinda Yalwati take fada min rannan gaskiya ne, Suwaiba dai har da cikin Saghir a jikinta. Alhaji Babba yace shi lallai sharri aka yiwa dansa, shi ma kuma Saghir din yace ba nashi vane ba kuma yama fasa aurenta ke zai mayar. Shine shi kuma hamma Isa yazo yace kar mu mayar masa da ke in yaso yayi biyu babu kenan. Su yanzu likitan da zai cire cikin suke nema". Nayi shiru ina jin hawaye yana bin fuskata. Na tuno zafin da naji sanda Saghir yayi min sharri a gaban yan'uwan mahaifina amma duk babu wanda yayi komai a kai. Ga zina nan ta kare a gabansu, yanzu sai su ware ni da Saghir waye mazinaci.
Bayan sati ya kuma zagayowa sai ga malam iliya maigadin gidan Saghir ya kirani hankali a tashe. Na tambayeshi sai yace "yan NDLE ne suka zo gidan, sun yi filla filla da komai na gidan wai suna neman kayan maye" cikin tashin hankali na tambayeshi sun samu sai yace "sun samu, a dakin mai gidan sukayi ta fitowa dasu sannan suka samu wasu kuma a motarsa. Yanzu tafiyarsu kenan nima guduwa nayi da ina jin dani zasu hada. Shine na kira ki tunda su basa nan in gaya miki halin da ake ciki" nayi masa godiya na kashe wayar, ina kokarin bawa inna labari sai ga kira ya shigo wayarta daga Hajiya Yalwati tana ta kuka "Amina mun shiga uku. Wai yan drugs ne suka zo zasu tafi da Alhaji. Alhaji Babba fa? Me ya hada shi da shaye shaye?". Nan take Inna ta rikirkice ta saka mu muka shirya muka tafi gidan gaba daya, muna zuwa muka tarar har an tafi dashi ga yan gidan nan sun fito sunyi chirko cirko masu kuka nayi masu salati nayi, yan unguwa kuma ana tsaye ana kallo. Mukayi ta basu baki muna mayar dasu cikin gida har muka samu suka koma ciki sannan aka fara tunanin ta inda za'a bullowa lamarin. Ni dai na fada musu abinda mai gadin gidan Saghir ya fada, dan haka sai muka fahimci cewa neman Saghir suke yi shi yasa suka kama Alhaji. Aka kira Kawu Isa aka gaya masa amma yace shi babu ruwansa "tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka".
Dan abin kunya sai surukan gidan aka nema, ciki harda wanda yake neman auren Murja, su sukayi ta zirga zirga Inna kuma ta saka Asma'u taje ta ciro kudi a account a bawa wancan cin hanci a bawa wancan amma sai da Alhaji Babba ya kwana biyu a garkame sannan suka sake shi da yarjejeniyar Saghir yana shigowa kasar zai danka musu shi a hannun su.
Ranar da Alhaji ya dawo gida haka ya zauna yana ta kuka kamar karamin yaro "ban taba ganin cin mutumci irin wannan ba, wannan yaro mai ya janyo min haka ni Muhammadu. Ankwa hannu da kafa haka aka saka min ana jana a titi kamar wanda yayi kisan kai" sai kuma ya fara yiwa Inna godiya a kan kokarin ta da karfin ta da kudinta gurin ganin an fito dashi. Yana ta kuka har ciwonsa yana kokarin tashi dan haka akayi masa allurar bacci mu kuma muka tafi gida.
What remains a mystery shine yadda akayi yan drugs suka yi suspecting Saghir yana ta'ammali da kayan maye har suka kaiwa gidansa ziyara.
Two weeks after tafiyar Saghir sadauki ya dawo. A gurin Asma'u naji zancen dawowar tasa sai kuwa gashi nan yazo gidan. Ina jin shigowarsa na shige cikin daki na lulluba kamar mai bacci. Ina jin su suna ta hirar su a palo, ya kawowa Asma'u graduation gift na wata desighner handbag da takalmi, ya kawo wa Subay'a yar karamar computer ta yara mai kyau. Ta shigo da murna tana nuna min "Mommy kinga abinda wannan yayan naki ya kawo min, amma ke yace bai siyo miki komai ba" na karba ina dubawa nace "to kije kice kin gode madallah" ta fita na koma na kwanta.
Ina ta so dai inyi masa maganar kudin companyn sa, amma bana son ganinsa dan haka bayan ya bar gidan sai na kara dauko waya ta ban kirashi ba dan nasan ba shiga zata yi ba amma sai na rubuta masa message. "Ka sa ido a kudaden kamfanin ka. I might be wrong. Just taking precautions". Na tura masa. Na zauna da wayar a hannu ina jiran reply, shiru shiru babu. Har na gaji na ajiye ta na tashi na cigaba da harkoki na. Aka jima na sake dubawa babu reply, nayi tsaki a raina nace "ku kuka sani" Sai kuma nake jin haushin kaina for caring a inda ni ba'a damu dani ba.
Saghir yakan kira ni sometimes, in ya kira sai in bawa Subay'a suyi magana. Ko da wasa ban bashi labarin case din drugs ba dan nasan ba karamin aikinsa bane ba yaki dawowa dan ba damuwa yayi da abinda za'ayiwa Alhaji in bai dawo din ba. Ranar nan ya kira na bawa Subay'a suka gama maganganun su sai yace ta bani, na karba yace min "jibi zamu dawo. Ina son ki kawo Subay'a airport ta tare mu. Tace tana son zuwa" nace "okay Allah ya kaimu jibin. Allah ya kawo ku lfy" yace "ameen. Hope kin gama shiryawa dan daga airport sabon gidazamu zarce" na sake cewa "Allah ya kaimu" na kashe. I didn't have the energy or the patient to argue.
Muna gama wayar sai naga Asma'u ta dauki tata wayar tayi kira sannan tace "jibi zai dawo" ta kashe. Ta kalleta nace "what was that?" Tace "Hamma yace in gaya masa ranar da Saghir zai dawo" na saki baki kawai ina kallonta. What was that about?
Ranar dawowarsu na shirya Subay'a tana ta murna muka tafi malam Aminu Kano international airport. Muka tsaya a gurin da aka tanada dan taryar matafiya. Subay'a tana ta tsalle ta kasa tsayawa a guri daya yayin da ni kuma nake ta lissafe lissafen halin da nake ciki. Ni har yanzu ban gama fahimtar kudurin Sadauki na mayar da Saghir aiki sannan da kuma hanani gaya masa cewa ni ba zan koma gidansa ba. Na fahimci kamar yana buying time ne but for what? Me yasa kuma yake son jin lokacin dawowar Saghir?
Muna tsaye akayi announcing saukar jirgin su Saghir, muna tsaye kuma har suka gama checking out suka fito. Na hango shi, as handsome as ever, hannunsa cikin na Fauziyya suna fitowa daga revolving door din gurin. Subay'a ta fara murna "Daddy, Daddy" ya dago mata hannu yana murmushi.
And then as he steps his feet out of the door, police surrounded him. Police, not NDLE officers. Fauziyya ta matsa baya da sauri tana ihu, Subay'a ma ta fara ihun kiran Daddy yayinda shi kuma ya fara demanding dalilin kamashi. Na daga Subay'a na rungume ta a kirjina, muna kallo daga inda muke tsaye aka garkamawa Saghir ankwa a hannayensa aka wuce dashi police car da take gefe tana jira.
Subay'a ta fara jera min tambayoyi "me yasa yan sanda suka tafi da Daddy na? Ina zasu kai shi?" A lokacin naji karar shigowar text cikin wayata. Na dauko ta na duba naga number din Sadauki. Sai yanzu yayi replying message dina. Na karanta "check up" it said.
[3/7, 9:06 AM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Fifty Four & Five : The Games We Play
"Check up" na maimaita a fili. Nasan wannan kalmar amma a ina? Sai mind dina ta koma baya, back in time lokacin muna yara a gida muna playing game of cards ni da Sadauki a incomplete benen Baffa a lokacin da nake gudun islamiyya ya rama min duka ance in na koma sai an zane ni. A cikin game din ana cewa check up. And it means game over.
Amma wanne game din ne over bayan ni bansan sanda game din ya fara ba? Ya akayi ya turo min wannan text din a dai dai wannan lokacin? Ko dai Sadauki yana da hannu ne gurin kama Saghir?
Kamar ance min in juya baya sai na juya. And I saw him. Yana tsaye ya jingina da jikin motarsa with dark glasses a idonsa and a broad smile on his face yana kallon motar police din da aka saka Saghir a ciki, sai da yaga sun ja sun tafi sannan ya bude motarsa shima ya shiga shima ya tafi.
Da sauri na koma taxi din da nayo shutter nace masa mubi bayan police car din data fita. A hanya drivern yake ta surutai "ai haka police suke yiwa irin wadannan bata garin, in sunyi abu sai su gudu su bar kasar sai a shammace su ranar da zasu dawo azo ayi gaba dasu. Ai wannan commissioner din baya wasa" jin ban kula shiba sai yayi shiru kuma muka cigaba da bin su a baya har na tabbatar cewa bompai zasu tafi dashi sannan nace da drivern ya kaini badawa layout, gidan Mama, muna zuwa na ajiye Subay'a na gayawa Mama briefly abinda ya faru, naci sa'a yaya Sadiq yana gida sai ta hadani dashi muka koma police station din dan muji takamaiman abinda ya faru, for what charges aka kama Saghir.
But ni already jiki na ya gama bani charges din ina dai so ne in tabbatar da zargi na. Ina kuma bukatar wasu amsoshin daga Saghir. Da kyar muka samu desk officer din ya kula mu, amma da muka nemi ganin Saghir Muhammad da aka shigo dashi yanzu sai kawai yayi mana dariya irin mun ma bashi dariya din nan, yace "wannan ai ko uwarsa ce take son ganinsa sai dai ta hakura. Ku koma gida kuyi taja masa charbi dan yau ne za'ayi masa tambayar kabari ta duniya" ya fada yana dariyar mugunta.
Nace "to zamu iya sanin dalilin da yasa aka kama shi?" Yace "ke wacece a gurinsa?" Nace "matarsa" yace "kinsan inda yake aiki?" Na hadiye wani abu a kirjina Nace "eh. Abatcha Motors" yace "to can zaki je ki tambayi abinda yayi, zasu yi miki bayani dalla dalla".
Haka muka hakura muka fito. Yaya Sadiq yana jan motar mama ni kuma ina gaba nayi shiru ina juta lamarin a raina. My deepest fear have come true, wannan case din bana drugs bane ba kuma wani ne daban, case din Sadauki ne, Saghir ya debi kudin companyn Sadauki yayi facaka dasu Sadauki kuma ya saka an kama shi. But what was Saghir thinking?
Gidan Alhaji Babba nace Yaya Sadiq ya kaini, dole inje in fada musu halin da dansu yake ciki in yaso a hadu a san yadda za'ayi tackling lamarin. Ga kuma wancan case din NDLEA da yake jiran Saghir. Sai kawai naji ina jin tausayin iyaye da yan uwan Saghir.
I also needed to talk with Sadauki. Bana ko raba daya da biyu nasan tarko ne Sadauki ya dana wa Saghir shi kuma ya fada head over heels. Wato wannan shine time din daya nema in yi masa buying kenan. Sai kuma na sake tambayar kaina "menene hadin Sadauki da case din NDLEA? I really do hope bashi da hannu a ciki.
Da muka je gidan kuma sai na kasa gaya musu, musamman ganin da nayi suna ta fama da kansu, an dafa wake da shinkafa ana ta lissafin yadda za'a samu kudin mai, sai da naje na bayar aka siyo musu. Sai na ja Hajiya Yalwati gefe na labarta mata. Ta rike baki tana salati tace "gurin aikin sa kuma? Ba companyn Sadauki bane yake aikin ji nake ya kore shi?" Nace "bai kore shi ba, ga kuma abinda ya faru. Yanzu yana bompai. Naje an ma hanani ganinsa" haka na tafi na barta da jimami nace ta gayawa Alhaji da Hajiya. Ni ba zan iya ganin wannan heart break din ba.
Daga nan gida yaya Sadiq ya kaini, na bar Subay'a gidan Mama in yaso gobe in na koma station din sai in biya in taho da ita saboda nasan yanzu in muka he gida ta saka ni a gaba kenan da tambayar ina daddyn ta? Ina police suka kai shi?. Ina shiga gidan Inna tana sallamar wani yaro da yazo siyan kankara ta gane something is wrong, sai data sallame shi tace min "lafiya? Ina Subay'a? Rigima kuka sake yi da Saghir?" na zauna ina cire hijab dina nace "inna Saghir yana bompai" ta saka salati tana tafa hannu tace "masu neman nasa ne suka kama shi? Dama sun san yau zai dawo?" Nace "basu bane ba Inna. Wani case din ne daban, basu gaya min menene ba amma sunce case ne daga gurin aikinsa" na fada ina kallonta cikin ido, nan da nan sai naga ta fahimta tace "Sadauki? Me ya kuma hada su kuma?" Na daga kafada nace "ban sani ba. Sai gobe zan sake komawa inji ko zasu yi min bayani" tace "to ki kira Sadaukin mana ki tambayeshi shi?" Na kwanta a kujera ina cewa "ba zai dauka ba Inna. Dama can baya daukar waya ta ballantana yanzu".
Na jima kwance da idanuna a rufe har aka fara kiran magrib. Ni dai va bacci nake ba kawai ina ta lissafe lissafe ne, Sadauki should have just let me take Saghir to court shikenan a wuce gurin. In na rabu dashi ba dai shikenan ba?
Ina ji da dare Inna ta saka Asma'u tana ta bugawa Sadauki waya amma yaki dauka, daga baya ma sai ya kashe wayar gabaki daya. A raina nace dai dai kenan.
Washegari tun da wuri na tashi na shirya inna ma ta shirya tace gwara muje tare, muka bar Asma'u a gida muka tafi bompai amma muna zuwa muka tarar Hajiya Babba ta riga mu zuwa ita da wani kaninta. Idanunta sun kumbura alamar tayi kuka harta gode wa Allah. Muna shiga ta taho gurina da sauri "Diyam sharri yake masa wallahi, wallahi sharri yake yi masa ina yaron nan zai kai wadannan uban kudade?" Inna ta rike ta tana lallashinta ni kuma na karasa gurin desk officer din da yake on duty. Ya miko min wata takarda wacce take dauke da case statement na case din Saghir, a jiki naga bayanin cewa ya yi transfer din kudi ne daga account din company zuwa private account dinsa. Amount din dana gani sai daya saka kaina ya sara naji kamar zan fadi, mai Saghir yake tunani ne wai? A jiki kuma naga cewa Saghir din ya karbi laifinsa tun a jiyan da aka kawo shi dan haka har an fara shirin tura shi court. Na ajiye takardar nace da officer din "can I see him please" ya kalle ni da mamaki yace "are you sure? He went through some questioning so an dan sassama shi kadan" ya karasa yana grinning. Na juya na kalli inda Hajiya har yanzu take zaune tana kuka Inna tana rarrashinta. Nace "zan ganshi, amma ni kadai" sai ya miko min wani form yace in cike. Na karba na tafi gurin su Hajiya nace musu "sun hana ganinsa, gwara ku tafi gida kawai. Ni zan zauna in cike wasu takardu yanzu zan biyo ku" kamar ba zasu tafi ba sai kanin Hajiya wanda dama tunda muka zo naga yana ta nuna alamar ya gaji yace "in mun zauna ma babu abinda zasuyi mana fa, zasu iya wulakanta mu gwara mu koma gida sai asan yadda za'a bullowa lamarin" sai naci sa'a suka bishi suka tafi ni kuma na koma ciki na cike form din da aka bani, aka kaini wani daki na zauna ina jira, shiru shiru tun ina kallon agogo gar na fara zama frustrated ina jin tamkar na shekara a dakin sai aka bude kofa aka shigo.
Saghir ne, amma kamar ba Saghir ba. Daga shi sai singlet da gajeren wando, fuskarsa babu inda bai kumbura ba dan idanuwansa da kyar suke budewa. Sai kawai naji zuciyata ta karye na rufe baki na kama kuka. Officer din daya shigo dashi yace "na gaya miki ai" sai ya zaunar da Saghir akan benchi ya juya ya fita. Na tsaya kawai muna kallon kallo. Sai can yace cikin wata irin murya "kinzo ne dan ki sakani a gaba kiyi ta kallo kina cewa Allah ya kara ko kuma kinzo ki karasa aikin da tsohon saurayinki ya fara?"
Na zauna ina facing dinsa nace "Saghir me yasa ka daukar masa kudi? Why? In zaka dauki kudin kowa a duniya me yasa zaka taba na Sadauki bayan kasan abinda yake tsakanin ku?" Yace "menene a tsakanin mu din? Ke? Dan ke akayi min wannan abin na sani kuma yayi da dan halak. Sai na rama duk ranar da na bar gurin nan sai na chanja masa kamanni kamar yadda yasa aka chanja min nawa" na girgiza kai cike da takaici, he is still being arrogant, nace "ni so nake in tabbatar, ka daukar masa kudi ko ba ka daukar masa ba? Ina so insan gaskiyar maganar nan saboda in san ta inda zan bullo mata" ya dauke kai yace "I don't need your help. Kiyi tafiyar ki kawai. Ki je ki gaya masa cewa tarkon daya kafa ya kama shaho" na girgiza kaina a raina nace 'he have no idea how much trouble yake ciki' sai na bashi labarin case dinsa da yan drugs. And that broke him down.
Hannu biyu yasa ya dafe kansa, ya jima a haka sannan ya dago yana kallona yace "wannan duk yana cikin irin kiyayyar da kike yi min Diyam? Me yasa baki fada min ba kika barni na dawo kasar? Me yasa kika barni na fada tarkon da makiyana suka kafa min" naji tausayinsa har cikin raina, nace "Saghir, ko daya ba naki gaya maka ne saboda bana sonka ba, naki gaya maka ne saboda nasan in na gaya maka ba zaka dawo ba and that means trouble for Alhaji, wanda babanka ne shi mahaifi dan haka dawowarka yafi maka alkhairi akan kin dawowarka" yace "really? To case din Sadauki fa? Shima kamanin da yayi yafi min alkhairi akan rashin kamani? Waye ya gaya masa zan dawo da har yasa aka tare ni a airport?" Nace "duk abinda zan gaya maka ba lallai ka yarda ba. Amma duk da haka zan gaya maka. Bani da idea akan abinda ya faru tsakanin ka da Sadauki. Na san dai yana buying time for something but bansan menene ba. Kuma ina so kasan cewa zanyi iya kacin kokari na na ganin ka fita daga gurin nan but for that ina bukatar ka gaya min gaskiya. Ka dauki kudin Sadauki ko baka dauka ba? Drugs din da aka samu a dakin ka da motar ka, naka ne ko ba naka ne ba?"
Ya jima shiru kamar ba zaiyi magana ba sannan kuma sai ya danyi murmushi yace "that former boyfriend of yours is smart, na bashi credit anan. Tunda yaron nan ya dauke ni aiki, ina jin ma ai na taba gaya miki, babu aikin da nake yi. Sai ya dauki wani a matsayin assistant dina to duk aikin da ya taso shi ake bawa yake yi and I tot 'huta roro' tunda dai ana bani salary na mai kyau ai bani da problem. Shekara da shekaru, ko banje gurin aiki ba bani da matsala, I should have known tun a lokacin that something is off but ni ta constant monthly income dina nake yi. And then lokacin da na koma aiki, suddenly it was all work for me. A lokacin ne nasan ma how much money ne a cikin account din Company and it was a huge money. Kullum kudi suna shigowa wadansu suna fita, kudi masu yawa. Shi yayi tafiyar sa, and duk takardar da aka kawo zaiyi signing sai a kawo min ace yace inyi a maimakon sa. Duk kudin da za'a fitar ni za'a saka in fitar dasu haka duk kudin da za'a shigar. It was like cewa ake yi Saghir dauki kudin nan. And I saw my chance. Mutumin nan yaci amana ta yayi making fool of me for years, dan haka dole ce ta saka ni na cigaba da aiki under him saboda babu inda zanje in samu din. Dan haka sai na dauka as a revenge for what he did to me kuma dan in kafa kaina nima in daina aiki under him. Nasan zai gani amma kuma nasan yana tsoron kar in bata masa image dinsa with that scandal so I expected him to keep quiet. Da kudin na sayi gidan dana gaya miki na kuma saya mana motoci ni da ke da Fauziyya and I gave some part of the money to Kabir da niyyar zamu hada share muyi business tare. Sauran kuma dasu nayi wannan tafiyar wadansu kuma suna account dina da niyyar su zasu rike mu kafin business din da zan fara ya kankama".
A gyada kai, my mind already thinking ta yadda za'a harhado kan wadannan kudade. Ya cigaba:
"Drugs kuma, wadanda aka samu a daki na, a kasan gadona, ba nawa bane ba. You know I don't do drugs. Na Kabir ne ya bani ajjiya saboda yana da iyali karsu taba masa ni kuma tunda zanyi tafiya shine yace in ajiye masa, a mota ta kuma alcohol zasu samu".
Na gyada kai nace "so, where is Kabir now?" Ya daga kafada yace "ta yaya zan sani tunda ina nan a rufe?" Nace "but ta yaya akayi suka kai mamaye gidan ka?" Yace "I have no idea. Ask that smart boyfriend of yours maybe shi yana da idea".
Na mike tsaye nace "thanks for telling me the truth. Zan je gidan Alhaji zamu zauna muga ta yadda za'a bullowa lamarin. Insha Allah, you are getting out of here. Zamuyi reporting cewa stuffs din Kabir ne ba naka ba." Na juya zan fita sai yace "why?" Na juyo ina kallonsa nace "why?" Yace "why are you trying to help me bayan duk abinda nayi miki? I tot ke celebrating zakiyi ma cewa you are finally getting rid of me" nace "kamar yadda Hajiya ta gaya min rannan. Kai dan'uwa na ne, mijina, kuma uban yata".
Daga bompai gidan Alhaji Babba na koma, a can na same su harda inna duk sunyi jigum jigum har aunty Fatima itama tazo. Na zauna na lissafa musu tas abinda ya faru. Saghir dai ya dauki kudi ba sharri ne akayi masa ba, ya kuma admitting to ajiye drugs a gidan sa amma yace ba nasa bane ba na Kabir abokin sa ne.
Nan take Alhaji Babba ya dauko waya ya kira Alhaji Murtala mahaifin Kabir yana tambayarsa in yasan inda Kabir din yake amma sai yace shima nemansa yake yi bai san inda yake ba, ya dauka ma tare suka fita da Saghir, da yake duk halin daya ne. Nan fa hankalin Alhaji ya sake tashi. In ba'a samu Kabir ba Saghir ne a ruwa.
Out of the confusion na fita waje na zauna a compound. Sai na dauko wayata nakira Fauziyya. Tunda na ganta a airport sanda aka kama Saghir ban kuma waiwatarta ba kuma babu wanda ya kuma kiranta. Bugu biyu ta dauka. "Halima ya ake ciki?" Naji haushin da bata kirani taji ya ake ciki ba sai yanzu? Amma sai nayi mata bayanin duk abinda na fahimta da kuma halin da ake ciki a yanzu. Sai ta tabbatar min da cewa tabbas taga sanda ya ajiye drugs din a day to tafiyarsu yace ajjiya aka bashi but bata san menene ba a lokacin kuma bata san waye ya bashi ajjiyar ba. Sai na ce mata ta shirya ta taho gidan Alhaji itama ayi komai da ita.
Sai can yamma ta zo, tana ta dari dari dan duk yan gidan ba sonta suke yi ba kar ma Hajiya taji labari, tace tsohuwar karuwa ce. Ita ta sake tabbatar musu da cewa Saghir shi ya ajiye drugs din da hannunsa, ta kuma gaya musu zancen gidan daya siya wanda su sam sam basu san da zancensa ba. Tace gidan yana unguwar rijiyar zaki dan haka muka yi shirin gobe zamuje a ga gidan sai kuma a nemi mai siya. Za'a karbi motarta da tasa a hada da wadda yace ya saya da sunana duk a siyar, sai a hada kudin da sauran kudin da yake account dinsa aga abinda za'a tayar kafin a nemi inda Kabir yake a dankashi a hannun NDLEA a kuma karbi kudin Saghir na hannunsa. Sauran kudaden kuma da Saghir ya riga ya kashe bansan inda za'a same su ba. Da Fauziyya zata tafi tace min "Mr Abatcha, ai yana jin maganar ki ko? Zaki iya sakawa ya saki Saghir ko?" And I didn't answer her.
Muna komawa gida na kira shi da wayar Asma'u tunda ba zai dauki tawa ba amma still sai yaki dauka, I guess yayi tunanin Inna ce take nemansa da gaske. Amma ita inna tunda taji zancen cewa Saghir ya dauki kudin Sadauki da gaske sai tayi shiru bata kuma cewa komai ba. But like I told Saghir, zanyi iyakacin kokari na gurin fito dashi so I decided to see Sadauki the next morning.
Da safe muka sake komawa gidan Alhaji Babba, Fauziyya ma tazo za'a tafi sabon gidan Saghir sai nace musu suje kawai, na gaya musu inda zanje. Abatcha Motors.
Na tarar da gurin kamar wancan zuwan nawa ana ta hada hada, sai dai yau kamar gurin yafi cika kuma motocin gurin sunfi nada yawa har bazan iya kirgasu ba, na samu receptionist din nace masa "ina son ganin ogan ku" sai ya tsaya yana kallona yadda na hade rai ya dauki waya yayi magana a ciki sai kuma ya kalle ni yace "ya ga shigowar ki ta CCTV. Yace kije office dinsa. In kika bi nan...." Na daga masa hannu nace "nasan inda office dinsa yake thank you" sai kuma na tafi inajin haushin kaina for being rude ga wanda bashi yayi min laifi ba.
Na ga wannan kyakykyawar secretary din nasa, ta yi min sannu da zuwa sannan tazo ta bude min kofa kamar ranar nan na shiga but sai na bar kofar a bude na tsaya ina kallonsa a zaune yana kallona shima.
Nace "let him go" sai ya taso ba tare daya ce min komai ba yawuce ni majestically ya rufe kofar dana bari a bude. Ya juyo ya samu kujera ya zauna yace "he took, or rather stole my money" nace "kudi, kudi, kudi dai? Shikenan abinda yake da muhimmanci a gurin ka kudi? Look at what you have, lokacin da naga amount din kudin da Saghir ya dauka I tot ya kassara ka but ni banga alamar anyiwa companyn nan ko da scratch ba" yayi murmushi yace "you are right. Amma dai ya dauka. So, dole zai biya in kuma ba zai iya biya ba sai ya tafi gidan maza har zuwa ranar da iyayensa zasu samu kudin da zasu biya masa" na tako nazo gaban table dinsa na tsaya, ina jin kamar in rufe shi da duka. Nace "me yasa? Tarko ne ka dana masa na sani but why? Me yasa? You could have just let me take him to court kamar yadda nayi niyya ya sake ni and that'll be all. Zumuncin dama ai a lalace yake menene saura. Why do you feel the need to lock him up?" Yace "kamar yadda kika ce in kika kai shi court ya sake ki that will be all. Meaning duk abinda yayi miki yayi a banza kenan? What he did to you and said to my face shikenan yayi a banza kenan?" Ya fada with bitterness in his voice, ya cigaba "wannan abinda yayi, kuma ya gaya min yayi, shine greatest mistake dinsa a rayuwa kuma shine abinda zai paying for in prison for as long as possible" na zauna a kujerar da take facing dinsa nace "ni yayi wa, ba kai ba...." Yace "da ni yayi wa da sai abin yafi zuwa masa da sauki" naji zuciyata ta karye nace "Sadauki.....komai ya faru fa ya wuce. Ni duk na yafe kowa saboda a yanzu kowa yayi paying price dinsa. Tun daga ranar da aka kaini gidan Saghir nake addu'a cewa Allah ya saka min akan duk wanda ya zalinceni, kuma a yanzu bayan shekaru duk wadanda suka zalinceni din babu wanda bai karbi hukuncinsa ba. Inna, tun ranar da aka kaini gidan Saghir har yau Inna cikin regret take, har yau bata samu peace of mind ba saboda bana jin akwai abinda yafi ciwo irin ace uwa tayi destroying rayuwar yarta da kanta. Alhaji Babba a yanzu fa bashi da komai, ka tuna dukiya da izza irin ta Alhaji Babba amma yanzu rigar da zai saka ma sai in na debo na Saghir da baya sakawa na aika masa saboda shi ba zai bashi din ba. And Saghir, Saghir fa ta kare masa, ko da bakayi trapping dinsa ya daukar maka kudi ba Saghir already yana da case, NDLEA sun samu drugs a dakinsa dan haka suna nemansa. So you see? You don't have to do anything Allah yana planning komai accordingly" yace "na yarda, kamar yadda na yarda cewa Allah yana using people to furnish other people. Alhaji Babba da kike magana fa har yanzu baiyi regret ba, ko ya taba kiranki ya baki hakuri akan abinda yayi? Har yau da zaki tambayeshi cewa zaiyi taimaka miki yayi ya aura miki Saghir, dukiyarsa kuma cewa zaiyi makiyane suka saka masa hannu. So dole ya cigaba da zama gida daya da kaji da raguna ya cigaba da having sleepless nights for as long as I had, which will be like forever tunda har yau ba baccin nake yi ba"
Na mike tsaye ina jin haushinsa nace "how thick is your skull? In kana furnishing Alhaji su kuma iyalansa fa? Me sukayi maka? Makota fa? Me sukayi maka? Gidan gona tunda ka bawa Asma'u zan saka ta ta chanja masa guri. Batun Saghir kuma za'a biya ka kudinka, za'a siyar da duk abinda ya siya da kudaden sannan a nemo sauran a cika maka a baka kayanka ba shikenan ba?" Ya mike tsaye yana murmushi yace "me da me za'a siyar, gida da motoci? You are kind of late because I already bought the house and one car about two weeks ago" na juyo da sauri nace "what?" Ya gyada kai yace "bayan ya debi kudina I asked someone to track duk abinda zaiyi da kudin, naji ya sayi gida da motoci and I became worried cos zai iya siyar dasu ya biya ni. Luckily for me, sai ga report cewa one of his friends..." Ya duba wata takarda a gefe yace "Kabir, ya saka gidan da mota daya a kasuwa zai siyar, he was in a kind of hurry sai na taimaka masa na siya, yanzu har na zuba yan haya a gidan. Shi abokin daya siyar din yanzu ance min ya gudu ya bar kasar" ya sake murmushi "hard luck for him".
Na dafa kujera na zauna ina kallonsa. Na fahimci lissafin sa tsaf kuma na gane mai ya faru. Saghir ya saci kudi, Kabir set him up with the drugs sai ya siyar da gidan ya hada da sauran kudaden ya gudu. Meaning yanzu Saghir bashi da abinda zai biya ga kuma case din drugs a kansa. Sai na mike ba tare dana sake cewa komai ba har nayi hanyar waje kuma sai na tuna abinda ya faru rannan dan haka na juyo nace masa "open the door" yace "Please Diyam, stay out of it. Let him take the fall. He more than deserve it" na dawo gabansa nace "tell me something. Me yasa ka yafe wa Inna? Inna tafi kowa musguna maka a duniya amma ita mai yasa ka yafe mata?"
Ya dago kai yana kallona yace "she gave birth to you".
[3/7, 9:06 AM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Fifty Six : A Walk To Freedom
"She gave birth to you"
Maganar ta daki kunnuwana sannan ta wuce har cikin zuciyata, sai naji tamkar ta kunno min emotions din dana ke ta kokarin dannewa a cikin zuciyata, sai hawaye yazo idanuna ya fara zuba kan kuncina a hankali na fara rera kuka sai ya taho inda nake da sauri yace "Diyam....." sai kuma ya dakata ya juya ya koma bayan table dinsa ya danna button din bude kofa yace ba tare daya kalleni ba "good bye Halima".
Na juya nima da sauri na fita ina kokarin goge hawayen fuskata. Na sauka daga stairs din cikin sauri na fita daga building din. So nake kawai in samu seclusion din da zanyi kuka na son raina har in gode Allah. Na tsaya a bakin kenan naga mota tayi packing a gaba na sai driver din ya fito ya zagayo inda nake ya bude min kofar baya yace "oga yace ki shigo a kaiki gida" har nayi tunanin kin shiga sai kuma nayi lissafin gwara inyi kukana a cikin mota ni kadai da ac akan inyi a cikin napep mutane suna kallona.
Na shiga ya rufe kofar ya zagayo gurin driver sannan na masa kwatancen gidan Alhaji Babba muka tafi. Na jawo hijab dina na rufe fuskata nayi kuka na na koshi amma ni kaina bansan kukan menene ba, kukan tausayin kaina ne ko na Sadauki? Kukan abinda ya faru da ne ko kuma wanda zai faru nan gaba? Ko kuma kukan abinda yake faruwa yanzu ne?
Nayi bitar maganganun Sadauki ina son inyi placing dinsa a scale din dai dai da rashin dai dai. A iyakacin fahimta ta tun muna yara nasan kafiya da zuciya sune manyan flaws din Sadauki. And he seemed to be harder yanzu. Ya nutse sosai a cikin kogin revenge yadda har yana kokarin yayi loosing kansa, and I won't allow that.
Nasan duk abinda yayi akan gaskiyar sa yake, babu inda ya kaushe wa shari'a but still Allah da kansa yace yana son bayinsa masu hakuri ni kuma ina so Sadauki ya kasance a cikin jerin mutanen da Allah yake so.
Muna zuwa gidan Alhaji Babba na sauka, drivern ya tambayeni in shikenan inda zai kaini na amsa masa da eh. A dakin Alhaji na same sun yi tsuru tsuru har da Fauziyya. Ina shiga Alhaji ya mike yana tambayata "ya kuka yi Diyam?" Na girgiza kaina kawai na zauna a raina ina cewa 'you are in for a bad news' duk da daga yanayin su na fahimci sunje gidan Saghir sun tarar da yan haya a ciki. Alhaji ya zauna shima, yanayinsa kawai ya isa ya saka mai raunanniyar zuciya kuka, yana cewa "wannan wacce irin mummunar kaddara ce ta afkawa yaron nan? Wallahi ni ko da wasa bai gaya min ya dauki wadannan kudade ba, ballantana ya gaya min ya karbi wannan ajiya. Ba wanda yake neman shawara a gurinsa shi kadai yake al'amarinsa shida abokansa. Yanzu gashi gidan munje mun tarar da mutane sunce su haya suke yi a hannun wani agent suka karba" sai na basu labarin duk abinda na fahimta da maganar, a lokacin da Saghir yake can yana honeymoon dinsa shi kuma babban abokinsa Kabir ya saka gidan da kuma motar da Saghir din ya siya da sunana a kasuwa, ya karbe kudaden ya hada dana wajensa ya gudu ya bar kasar bayan ya bawa Saghir ajjiyar drugs kuma yayi masa chunen NDLEA.
Kowa yayi shiru a dakin har na gama bayani na, sannan na kara da cewa Sadauki yana kan bakansa na cewa sai an biya shi kudinsa. Har na gama babu wanda ya samu damar bani amsa. Sai dana gama sannan Hajiya Babba tace "Allah, Allah mun tuba. Allah in laifi muka yi maka ka dube mu ka yafe mana ka kawo mana sassaci a lamarin nan. Allah ka dubi yaron nan ka fitar dashi daga wannan matsala" ni dai nace "ameen" amma a raina nasan a inda matsalar take. Alhaji ne yayi deciding cewa zai je yaga Saghir kuma zai gaya masa halin da ake ciki. Sai naji dadi dan ni kam I wasn't looking forward to breaking the news to Saghir cewa best friend dinsa ne yayi framing dinsa dan ya cinye masa kudi.
Daga gidan Alhaji gidan Mama na tafi. Ina shiga Subay'a ta taho da gudu ta tarye ni tana cewa "Mommy ina daddy? Kin dauko shi daga gurin yan sandan?" Na jawo ta na rike fuskarta a hannuna nace "Daddy ya sake yin wata tafiyar, amma zai dawo very soon" sai ta saka kuka ita gurin Daddy zata je ita in kira mata shi a waya. Sai da Mama tayi barazanar dukanta sannan na samu tayi shiru.
Muka zauna na bawa Mama labarin duk abinda ake ciki tace "ki fita cikin maganar nan Diyam. Ki barshi shi da iyayen sa suyi ta fama ai tsuntsun daya ja ruwa hausawa suka ce shi ruwa kan doka. Duk halin da Saghir yake ciki iyayen sa ne suka jawo masa dan haka ki barsu su girbi abinda suka shuka da hannun su" sai nayi shiru ina kallon Subay'a tana wasa ina tunanin ko zata daina tambayata daddyn ta?
Sai yamma sosai na shirya Subay'a muka koma gida, muna zuwa na tarar Inna itama dawowar ta kenan sai Asma'u take bamu labarin Sadauki yazo yiwa Inna sallama zai tafi 'business trip'. Na kwanta kawai na rufe idona amma nasan babu wani business guduwa yayi dan kar inyi breaking dinsa.
An saka ranar shari'a Saghir sati biyu bayan kama shi, na shirya na koma bompai gurinsa amma sai yaki yarda ya ganni, officer din yace "ya zama very emotional kwana biyun nan yace baya son ganin kowa" sai na fahimci cewa Alhaji yazo ya bashi labarin cin amanae da Kabir yayi masa, and it broke him, finally.
Tun da aka saka ranar shari'ar Saghir ban zauna ba, nice gidan Alhaji, nice bompai, nice NDLEA, kuma nice kiran Sadauki. Kullum sai na kira shi da yawar Asma'u amma itama sai ya daina dagawa. Sai in zauna in tsara masa message, duk abinda nasan zai saka ya sauko in tura masa amma ko reply daya ban taba samu ba.
During one of my visits to NDLEA ne na samu rannan suka saurare ni, nayi musu bayanin abinda ya faru nayi mentioning sunan Kabir and that cought their attention, ashe dama suna suspecting dinsa amma basu da hujjar kama shi dan haka sun yarda zai iya framing Saghir din but still there is a case, kuma dole someone has to take the fall, Saghir kenan, dole zasuyi convicting Saghir suyi sentencing dinsa har sai an kama Kabir ya kuma karbi laifinsa. I felt relieved, duk da ba wani important improvement bane ba but at least it was a step further.
An siyar da gidan Saghir inda muka zauna, an siyar da tsohuwa da sabuwar motarsa sannan an siyar da motar daya siyawa Fauziyya itama. Sai aka hada da kudaden daya bari account din sa but all that only raised one third of kudin da ake binsa. A lokacin ne na kuma fahimtar cewa Saghir bashi da kowa, bashi da brother dama, cousins din kuma da brother in laws din duk babu wanda yayi zaman arziki dasu ballantana su tsaya masa, uncle din kuma yayi wa yarsa ciki dan haka ko sau daya bai taba shiga maganar ba, daga ni sai Hajiya da Alhaji, ga Alhaji babu isasshiyar lafiya ga kuma tsufa daya kara saukar masa. Yan uwan Hajiya ma duk sun zare hannayensu sunce wannan abin kunyar ba da su ba.
Nima rannan na dawo gida a gajiye Inna ta kalleni tace "daga yau babu inda zaki kuma fita akan maganar nan. In dake ce wani abu irin wannan ya same ki da daga Saghir din har iyayensa babu wanda zai daga ko dan yatsa ne ya taimaka miki, dariya ma zasu yi miki" na zauna kawai nayi shiru, sai tace "ko kin chanja shawara kuma Saghir din zaki komawa?" Nayi saurin girgiza kaina. Bana son Saghir kuma na gama aurensa, that's a fact, but still har yanzu mijina ne, nayi kurakurai da dama a rayuwar auren mu bab sani ba ko wannan kokarin da nake masa zai taimaka min wajen goge wadancan laifukan. Sannan kuma, Subay'a, bata da wani uban daya wuce Saghir duk wani wanda zai rike ta sai dai ya zama uban kara amma ba mahaifi ba, and I am not looking forward to telling her that babanta yana prison, what will happen kuma inta fahimci cewa Sadauki yayi playing role a saka babanta a prison din?
Another dalilina kuma shine Sadauki. Sadauki loves me, for that bani da dobt, wannan kusan shine dalilin da yasa ya gudu saboda kar yaga na damu ya kasa abinda yayi niyya. And I love him, shima bani da dobt a kan wannan dan haka nake so in chanja ra'ayinsa zuwa forgiveness, for his sake, saboda ina gudar masa daukan alhakin wadanda basu da laifi, ina kuma gudar masa dana sani a nan gaba.
Ranar sharia tazo and we all went to the court, na bar Subay'a a gida, wadda a ranar ma sai da tayi min complain din neman daddyn ta. Na samu seat a farko farko na zauna bracing myself for duk outcome din da za'a samu. Muna zaune aka shigo da Saghir, looking very down and defeated, ban taba ganin sa a haka ba. Ya zauna a gurin zaman accused looking down at his fingers.
Sai aka fara gabatar da kara, aka lissafa all charges against him sai lawyers suka fara maganganun su da ba ganewa ake yi ba, nayi ta stressing 茩wa茩walwa ta ina so in gane mai suke cewa amma sam bana fahimta sai dai in sunyi magana inga alkali ya gyada kai har suka gama. Sannan ya juyo yana kallon Saghir ya tambaye shi "how do you plead?" Ba tare daya kalle shi ba yace "guilty" and my heart went out to him.
A take alkali ya yanke masa hukunci, for the crime of kudin Abatcha Motors daya ci, za'a rike shi a prison har sai familyn sa sun biya kudin, for the crime of drugs, shima zai zauna har sai an kama Kabir.
In both cases he is doomed for life.
Aka gama karanta masa sentence dinsa amma bai dago kansa ba, na fara jin koke koke a baya na. Na waiga naga Hajiya tana kuka ita da kanwarta, sai Fauziyya daga can gefe, sai su Murja sun hada kai ita da sauran yan'uwanta suna yin nasu, and then a can karshen room din na hango wadda banyi tunani ba. Suwaiba. Itama tana nata kukan.
Sai aka taho dashi za'a wuce dashi, ya tsaya yana kare mana kallo daya bayan daya, sai muka hada ido and he smiled. Da sauri na mike na tari abin hawa zuwa gida.
Ranar kwana nayi banyi bacci ba. Washegari Mama tazo suka wuni anan ita dasu Rufaida da Muhsina. Bayan sun tafi da yamma sai naga Subay'a ta shigo da banki irin na kasar nan na yara ta saka a kasan gadon Inna. Nace mata "Subay'a? Banki kika siyo mana?" Tace "eh, kudi zan ringa tarawa a ciki in biya wannan yayan naki kudin sa da yake bin Daddy na" I was stoned, nace "Subay'a? A ina kika ji wannan maganar?" Tace "Mama naji suna hirar da Inna, wai Daddy na yana gurin police sai an biya yayanki kudi sannan za'a fito dashi".
The next day na tashi da wuri na shirya, Inna ta tambayeni inda zanje sai nace "prison" sai ta shirya min abinci a basket tace "ki kai masa".
Da yake anan kano central prison yake, dan haka da kafa na tafi tunda babu nisa da gidan mu. Na jima ma'aikatan prison din suna ta ja min aji kafin su yarda zan ganshi. Sai suka kaini wani guri suka ce in zauna. After waiting for like eternity sai gashi sun fito dashi. He looked very different. Older but calmer. Suka zaunar dashi a kujerar gaban table din da nake sannan wanda ya kawo shi ya matsa baya but yana kallon mu.
Na sunkuyar da kaina ina lissafa fingers dina shi kuma yana kallona yace "my God, you really are beautiful" na dago na kalle shi and he smiled. Nace "ga abinci nan inji Inna" yace "thank you. Dama kinga azumi nake yi" nayi shiru ina tunanin ban taba ganin Saghir yana azumi ba in ba Ramadan ba. Sai yace "ya kika ga sabon gida na? Yayi kyau?" Na kalli surrounding din gurin nace "nan ba gidan ka bane ba Saghir. I am going to get you out of here" yayi dariya yace "how? Zaki saka ni a jaka ne mu tafi gida tare?" Nayi shiru. Yace "nasan maybe, just maybe, zaki iya convincing your lover boy ya yafe min kudinsa, but zaki iya kamo Kabir ki danka shi a hannun hukuma ki saka yayi confessing cewa shi yayi framing dina?" Nace "maybe, just maybe, zan iya convincing Sadauki ya yafe maka, sannan in saka shi yayi amfani da power dinsa to get you out. Nigeria ce fa, with few phone calls an gama komai".
Yayi dariya "not even in your dreams. Ba zaiyi ba. Mutumin da yake son ganin baya na ta yaya zai taimaka min?" Nayi shiru, nima kaina bansan ta inda zan bullowa wannan lamari ba but i am going to try.
Yace "I really did mess up ko? Nayi messing up auren mu. It would have been a great one" nace "not 'you' but 'we'. Tare muka hadu muka rusa auren mu. Ina fatan kuma zaka yafe min my part of the mess" yace "oh, you mean the closed doors ko?" Nayi murmushi. Na juya hannunsa yace "na yafe" nace "thank you".
Sai ya saka hannu a aljihu ya fito da takardu guda biyu yana kallona sarcastically yace "ya sunan ki ma? Ke ce Halima ko kece Fauziyya?" Bance komai ba sai ya miko min daya, naga sunana baro baro a jiki na bude na karanta
Ni Saghir Muhammad Kollere na saki matata Halima Usman Kollere saki daya, in ta samu miji tayi aure
Na dago ina kallonsa yace "daya ne ba yawa, in kika hada da wancan sun zama biyu kenan. Ni kuma na rike daya a gurina with hope that maybe, just maybe, zaki zauna ki jira ni" nayi murmushi yace "not even in my weirdest dream ko? I will just have to keep hoping".
Mutumin daya rako shi ya matso yace "time up" na gyada kaina na mike kamar zan tafi sai kuma na dawo na tsaya a gabansa nace
"For raping me, na yafe maka. For the twins, na yafe maka. For everything, na yafe maka. And I am going to get you out of here"
Yayi murmushi yace "thank you. Goodbye Halima".
Sai na juya da sauri na fita daga gurin, na kuma fita daga cikin prison din, hannuna rike da takarda ta.
Na fara tafiya a kafa ina jin iskar yanayin damina tana ratsani. Wani abu naji ya yaye daga 茩wa茩walwa ta. I felt a sense of freedom wanda rabon da inji shi tun ranar da aka aura min Saghir. Hatta hanjin cikina ji nayi yana warwarewa tamkar da a nannade yake a guri daya, wani abu daya tokare a makogwarona naji ya sauka at last ina sha茩ar numfashi freely.
And I decided that I am going to do the right thing.
[3/7, 9:06 AM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Fifty Seven: Moving On
A hankali nake tafiya, enjoying my own company, feeling as free as a bird. Wannan feeling din da banji ba lokacin da Saghir yayi min sakin farko sai yanzu nake jinsa. Nayi murmushin da ya shiga har cikin zuciyata sannan a hankali na fara tariyo rayuwar auren mu da Saghir a kaina.
Shi dai Saghir, babban abinda yayi dooming rayuwar sa har ya kai shi ga stage din da yake ciki a yanzu shine rashin tarbiyya. Makauniyar soyayyar da iyayensa suka nuna masa tun yana jariri ita ce silar komai. Sai ya taso a matsayin sangartacce, mai son kansa kuma marar yawo saboda bai san yadda zaiyi ya kula da kannasa ba kwata kwata ballantana har ya kula wani, that including su kansu iyayen nasa. Rashin yawon sa shine ya bawa Sadauki da kuma Kabir damar kai shi inda yake a yanzu.
Na tuno ranar daya ce min bararoji a palon Hajiya, na tuno sanda ya shigo daki a gaban Inna yace baya sona, na tuno abinda ya faru a first night din mu da kuma abinda ya biyo baya, na tuno haihuwar twins, zama na a gida da kuma komawa ta gidansa. Inda ace zan zauna zan iya lissafa sau nawa muka yi magana ni shi inus our first year of marriage. Har zuwa haihuwar Subay'a bata chanja zani ba. Na tuno da yawan comments din da yake yi akaina cewa bani da body parts din daya ke so a gurin mace, year after year, then suddenly lokaci daya ya chanja after ya gama gasa ni for about seven years sai kuma ya dawo yana bani kulawa always commenting on my beauty and the so called body parts din daya ke so wadanda a lokacin na fara developing dinsu. A duk lokacin da naga yana wannan care da comments din nasan inda maganar zata kare, his bed. I remember yadda yake yawan comment cewa I tasted different than sauran matan da yake sharing bed dinsa dasu. And then he said he loves me.
But that got me thinking, it that really love? I mean zaka iya cutar da wanda kake so? Ka dake shi ka aibatashi a gaban mutane ka aibata iyayensa masu rai da marasa rai sannan kace 'you are really beautiful' ka ja shi zuwa gadonka? It that love or something else?
Duk wanda yace baya sonka, ya wulakanta ka a lokacin da baka da physical appearance din daya ke so, sai daga baya kuma daka samu sannan yazo yake kulaka, to me that is not love, that is lust.
Nasan so kuma I don't think I can hurt wanda nake so intentionally. Ko a gurin da ake aibata shima ba zan iya zama ba ballantana ni inyi da kaina. In na bata masa ransa kuwa to tabbas akan wani abu ne da nasan is for his own good. Kamar abinda na kudurce a raina cewa ina so yayi.
A tsakar gida na tarar da Inna da Asma'u suna ta gyaran gida saboda tashin su Maman Iman shekaran jiya. Na gaida ta sannan na mika mata takardar da Saghir ya bani na shige daki, ina jinta ta saka Asma'u ta karanta mata. Sai na zauna a gaban kujerar da Subay'a take kwance a kai ina kallonta a raina ina lissafin whats next a rayuwar mu ni da ita, Allah ne kadai masani amma ni nasan zanyi duk abinda ya kamata inyi a matsayi na na uwa dan ganin cewa ta samu farin ciki koda kuwa hakan yana nufin yin gibi ga nawa farin cikin. The first thing da zanyi shine in mayar da ita school, already tayi missing term guda gashi har anyi hutu ana shirin komawa sabon session. Dan haka na yanke shawarar nema mata school a arear gidan mu in saka ta wadda nasan Inna zata iya biya dan ni koboless nake a yanzu, hatta kudin recharge card ma bani akeyi.
Inna ta shigo ta zauna tana kallona da takardar a hannunta tace "na kira Hajiya Yalwati na gaya mata, nace ta gaya wa su Alhaji" na gyada kai kawai, sai kuma tace "Allah yasa hakan shi yafi miki alkhairi Allah kuma yasa karshen wahalar ki kenan" nace "ameen Inna. Nagode".
Washegari da wuri Asma'u ta fita saboda tana ta harkar neman admission, ina jinsu suna waya da yayanta da sassafe a raina nace "kaga masu business trip". Bayan ta fita nima na fita naje nayi mana register ni da Subay'a a islamiyyar bayan layin mu wadda ake yi safe da yamma. Sai a lokacin nayi dana sani dana yi jamb din nima maybe da yanzu nima ina neman admission din amma yanzu ya wuce ni sai next year. Bayan na dawo ne na tarar da bakuwa a palo tana jirana. Fauziyya. Sai naga duk ta chanja duk babu gayun nan, ga hijab a jiki, the first time da naga Fauziyya da hijab. Daga yanayin fuskarta na gane itama ta karbo tata takardar sai na maze muka gaisa tana ta yiwa Subay'a wasa, ni kuma sai na kira Subay'a na aike ta gurin Inna dan yanzu sam bana son yin hira a gabanta.
Sai Fauziyya ta miko min wata takarda tace "kinga Halima" na karba na bude a raina ina saka ran ganin irin tawa takardar amma sai naga report ne daga asibiti da yake nuna cewa Fauziyya tana dauke da juna biyu. Na ninke na mika mata ina kokarin kakalo murmushi nace "well congratulations" sai ta fara share hawaye tace "zubar wa zanje inyi Halima. Ya zanyi dashi? Na gaya miki nayi aure ne saboda ina son inyi settling down a gidan miji, wannan cikin would have been a good news da ace abinda ya faru bai faru ba, yanzu ta yaya zanyi inyi raising baby alone babu miji babu mataimaki? Kinsan iyayena basu da rai, kuma yanzu ba kowa ne zai aure ni da baby ba, Saghir kuma...." Sai ta rufe fuskarta tana kuka, na taso na dawo kusa da ita ina rarrashinta tace "jiya da yamma naje ganinsa, ya bani takarda wai ya sake ni saboda bashi da ranar fitowa. Bai ma san da cikin ba ban gaya masa ba saboda so nake in zubar dashi" nace "to yanzu ni me yasa kike gaya min? Ba kya ganin cewa kina gaya min ne saboda deep down ba kya son zubarwar kina so wani ya baki shawara yace kar ki zubar?" Ta dago kai tana kallona sai ta gyada kai tace "haka ne, ina son baby na amma ya zanyi" nace "ni ba gashi yanzu an barni da Subay'a ba? Ke da kinyi karatu, ni fa secondary school kadai na gama da kyar, ba zaki iya ki nemi aiki da takardun ki ba ko dan teaching ne ko da private school ce ki ke yi kina samun kudin da zaki rike kanki da abinda Allah ya baki ba? Ni ina ganin in dai ba gani kikayi zaki takura ba to gwara ki ajiye batun aure a side ki samu abinyi first, in mijin yazo along the way shikenan, who knows? Maybe kiga Saghir ya fito nan bada dadewa ba" sai naga hope yazo fuskarta tace "da gaske? Zaki taimaka masa?" Na gyada kai nace "zanyi iyakacin kokari na, amma babu guarantee. Sai dai ina so kiyi min alkawarin ba zaki zubar da cikin ba" ta gyada kai da sauri tace "na fasa zubarwa insha Allah. Allah kuma ya baki sa'a akan abinda kika saka a gaba". Mun jima muna hira sannan na raka ta bakin hanya ta tafi.
Kwana biyu bayan nan da sassafe ina bacci naji ana ta haya niya a tsakar gida, na leko ta window sai naga ma'aikata ne suke ta shigo da kayan gini, na tashi na fito palo na gaishe da Inna na tambayeta "aikin menene za'ayi a gidan nan?" Sai tace "can dakunan za'a gyara sai a zuba kayanki da aka kwaso" ban wani damu da aikin ba da yamma zan tafi islamiyya na leka naga kusan sabo ake mayar da gurin. Hatta plaster da floor an kankare ana sake wasu, an cire ceiling da electric wiring duk za'a sake sai na dawo gurin Inna nace "wannan aikin Inna a ina aka samu kudin yinsa haka?" Bata kalle ni ba tace "matse bakina sai in gaya miki" ban sake cewa komai ba na juya na fita.
Washegari da safe aka sauke katangar da akayi a tsakiyar gidan mu ya koma kamar yadda yake ada. Kwana biyu ana aikin aka mayar da tsofaffin dakunan inna tamkar brand new dan in ba sanin su kayi ba ba zaka gane suba. Maimakon inga an kawo kayana da aka debo daga gidan Saghir sai naga ana shigo da wadansu kayan wadanda ko a ido ka kalla kasan ba class dinsu daya da wadancan nawan ba. Sai na sake komawa gurin Inna "Inna ina wadancan kayan da aka dauko?" Bata kalle ni va tace "na siyar dasu na kara jari" sai na mayar da bakina na rufe.
Asma'u tana shigowa na jata gefe daya yadda Inna ba zata jiyo ba na fara zazzaga mata masifa "ke ce kika ce da mutumin can ya gyara mana gida?" Ta daga kafada "wanne mutumin kuma?" Nace "kar ki raina min hankali kinsan wanda nake nufi ai" tace "the last time I checked shima gidan su ne. Menene laifi a ciki dan na gaya masa masu haya sun tashi za'a zuba kayanki a ciki shine yace a bari azo a gyara gurin tukunna. Daga nan kuma sai ga kaya ya aiko dasu a zuba" na bita da harara nace "kice masa......" Tace "ince masa an gode? To zan gaya masa" sai na dauki katako kamar zan dake ta ita kuma ta fice da gudu.
Wasa wasa ana gama wa da dakunan inna nada muka koma ciki muka tare. Inna da Asma'u daki daya ni da Subay'a daki daya. Na dauko akwatunan kayan sawar mu da muka debo daga gidan Saghir na jera mana abin mu. Subay'a tana ta murna wai munyi sabon gida. "In Daddy ya dawo anan zamu zauna tare dashi".
Daganan kuma aka fara gyaran dakunan Baffa. Aka gyare su tas suma aka saka sababbin furnitures aka barsu a matsayin gurin saukar baki. Inna tayi ta gayyatar yan uwa su zo suga sabon guri, kowa yazo ya gani yayi ta sam barka. Lokacin ne Adda zubaida itama tazo dai ta jani gefe tace "Alhaji ne ya turo ni gurinki. Yace inyi miki godiya sosai akan irin kokarin da kika yi tayi a lokacin shari'ar Saghir. Allah yayi miki albarka Allah ya bar zumunci kuma Allah yaji kan baffanku" nace "ameen. Shi kuma Allah ya fito dashi" "hmmmm" kawai tace, sannan tace "ki samu lokaci kije ki dubo alhajin" nace "to". Sai kuma na kawo mata shawarar da nake ta sakawa a raina tuntuni nace "Adda, a shawarce ku manyan mu tare da Aunty Fatima dasu Inna ku ya kamata ku shiga cikin maganar Alhaji da Kawu. Ya kamata su daidaita haka nan tunda wanda ake rigimar a kansa ma yana can a rufe" tace "zasu daidaita ne, amma ba nan kusa ba kinsan cikin suwaiba ya ki fita har yau, shegen jika za'a ajiye musu, yarinyar ma an kaita Kollere a can zata haihu" na dafe kaina ina jin babu dadi, ina taisayawa yarinyar nan wallahi Saghir ya shafa mata bakin fenti marar goguwa. Yanzu dai yaya biyu za'a haifawa Saghir kenan. Sai na bata labarin cikin jikin Fauziyya, ta rike baki tace "to ai kuwa bana jin mutan gida sun sani".
Duk wannan abinda ake yi shi oga mai gyaran gida ko keyarsa ban gani ba. Ban san ko ya dawo daga so called tafiyar ba ko kuma bai dawo ba. Amma kusan kullum ina jinsu suna waya shida kanwarsa kuma nasan suna gulmata dan sai inga ana maganar ana kallona ana dariya. In naga haka sai in tashi in bar gurin.
A haka har akayi resuming school. Nayi wa inna maganar Subay'a sai tace in bincika makaranta mai kyau sai na gaya mata har na bincika ma na samu wata anan kusa damu wadda zata iya zuwa da kanta. Sai tace da safe in je inji fee dinsu da sauran abubuwa. Amma da safen ina tashi sai naga Asma'u ta tashi itama tana shiryawa nace ina zata je wai "hamma yace in shirya in shirya Subay'a zai zo da wuri muje a sata a school" cikin fada nace "oh dama yana gari kenan. In shi ya haifar min yar ba sai yazo ya dauke ta ba in gani" sai naga duk sun tsaya suna kallona sannan na fahimci nayi rashin kunya a naganar. Nace "amma inna sai ya fara gaya min ai ko? Kulawa ma ai yabawa ce" Asma'u tace "yace ai fushi kike yi dashi. Wai in yayi miki magana ma ba zaki kula shi ba" nace "ya gwada ya gani? Ni ina na ganshi ma balle inki kula shi?" Sai tace "to ki shirya sai kuje tare ku kaita" na tashi nace "bazanje ba ai bai gayyace ni ba".
Ina kallo suka fita, sun jima sannan suka dawo Subay'a tana ta bata rai amma suna zama sai ta fara bani labarin sabuwar makarantar ta, ta nuna min uniform dinta da books din da already aka riga aka bata. Gobe zata fara zuwa fresh. Sai kuma naji dadin kula Subay'a da yayi har ya tuna cewa sabon session za'a shiga ya kamata sata a school. Daganan kuma sai ya ajire driver wanda kullum yake zuwa ya kaita school sannan in an tashi ya dauko ta.
Asma'u ta samu admission a northwest university ta fara karatu. A lokacin ne nima na gayawa Inna kudirina na shiga computer school kafin shekara ta zagayo in nemi admission, harda karawa da cewa "irin wadda Sadauki yayi lokacin da baici jamb ba" wai duk dan ta bari saboda naga yanzu shine favorite person dinta. Amma sai ta tabe baki tace "wato ke lissafin karatu ma kike yi kenan, auren kuma fa?" Naji kamar zan saka kuka nace "aure kuma Inna? wanne irin aure dan Allah dan Annabi?" Sai tace "au baki san wanne irin aure ba? Ai kin kusa gama idda zaki sani a lokacin" kamar ta fada da bakin mala'iku kuwa a ranar sai ga third period dina tazo. Ina cikin saka pad a daki sai gata ta shigo ta kalleni tace "to alhamdulillah!" sai naji duk kunya ta rufe ni. A raina nace "shin wai Inna auren dole zata sake yi min ne?"
A ranar na shirya nace gidan Mama zan tafi in kwana biyu, amma inna ta hana ni tace "islamiyyar fa?" Haka naja jakata na mayar daki na dawo palo na cigaba da zama.
Two weeks bayan nan, ina zaune zaman kallo zaman kashe wando kamar kullum sai jin muryar Sadauki nayi a tsakar gida yana tsokanar Subay'a da sunan da yake gaya mata "Subis" sai na mike da sauri har da dan guduna na shige daki na rufo kofa. Sound proof ne dan haka bana jiyo mai suke yi a palon sai daga baya Subay'a ta shigo ta turo baki, ta zauna a gefe na tace "wannan yayan naki ne yazo" nace "kin gaishe shi?" Ta gyada kai.
Dan rashin ta ido sai ganin kiran sa nayi a waya ta. Na kalli wayar a raina nace "lallai ma Sadaukin nan" ina kallon wayar wannan kiran ya shigo ya katse wani ma ya shigo har ya gaji ya daina. Sai na dauki wayar ina kallon number din. Finally dai anyi unblocking dina kenan. Ya kamata dai inyi saving number din nan, amma wanne suna zan saka masa? Sadauki? Ko hamma kamar yadda naga Asma'u ta saka?
Sai kawai na bude keyboard dina nayi typing "Aliyu" nayi saving. Asma'u ta budo kofa ta shigo tun kafin tayi magana nasan me zata ce "ki zo inji Inna" na dauki hijab dina na saka na fita. Yana zaune can carpet a gefen kujerar da Inna take zaune, an cika masa gabansa da kayan ciye ciye, yayi kwalliyarsa cikin normal kananan kayansa. Nayi saurin dauke kaina daga kansa saboda zuciyata da naji tana kokarin barin kirjina. Na zagaya naje na zauna can nesa dasu nace "Inna gani" tace "baki ji Sadauki yazo ba? Ai dai kya fito ki gaishe shi ko?" Na kalleshi muka hada ido, har da wani langwabar da kai kamar wani abin tausayi. Na dauke kaina nace "sannu da zuwa" yace "yauwa. Ya gida ya makarantar?" Asma'u ta fara bashi labarin school dinsu, yana ta tsokanar ta wai jambite ni dai sai na mike zan bar musu gurin sai yayi sauri ya tashi yace "Inna zan wuce, Allah ya bamu alkhairi" tace "ameen, Allah yayi albarka" sai da ya je bakin kofa sai ya juyo yana shafa kai "ammm, Diyam. Akwai sakon Subay'a a mota ko zaki zo ki karba" nace "Asma'u, bi shi ki karbo mata" sai ta mike tayi hanyar daki tana waka "you know I love it when you call me senorita" ta shige daki ta rufo kofa. Na cigaba da zama na shi kuma yana tsaye a bakin kofa yana kallona sai kawai gani nayi Inna da dauko mafici tayo kaina dashi sai na tashi da sauri na fita.
A garage na same shi a tsaye yana dariya. Na hade rai nace "ina sakon?" Yace "yanzu ke baiwar Allah sai Inna ta biyo ki da mafici sannan zaki zo gurina?" Nace "akwai sakon da zan karba ko babu?" Ya jingina a bango ya rungume hannayensa yace "babu, just want to see you, that's all" nayi shiru, trying so hard not to look at him, yace "ba kya son gani na yanzu ko?"
[3/7, 9:06 AM] Zuraiyah Zuzu 馃専: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episode Fifty Eight : Murjanatu
Na dauke kaina gefe nace "tunda babu sakon da zaka bani, Allah ya bamu alkhairi" na juya zan tafi sai ya zagayo ta gabana ya tsaya yace "look into my eyes and tell me ba kya son ganina and I promise you I will leave you alone" na daga ido na kalle shi amma muna hada ido sai nayi saurin sunkuyar da nawa idon kasa saboda wani zazzafan sako daya iso gare ni daga cikin idanunsa, sai na jawo fuskar hijab dina na rufe fuskata dashi, amma ina ganin duhunsa, sai naga ya sunkuyo dai dai fuskata yace murya can kasa "open your eyes and look into my eyes kice 'sadauki bana son in sake ganin ka" sai na juya fuskata daya side din nace "ka bani hanya in wuce, ko ka manta na baro 拼ata a daki ita kadai? And she needs me saboda babanta bayanan yana prison" sai ya gyara tsayuwar sa yace "hmmm. Gori zaki yi min kenan ko? Wai '拼ata'" ya fada yana kwaikwayon magana ta. Bance komai ba sai kuma yace "Subay'a will be fine, nayi miki wannan alkawarin. Na san ba zan taba replacing mahaifinta ba, amma zanyi duk iya kacin kokari na inga na bata duk abinda ya kamata uba ya bawa yarsa. Kar ki manta ina da training din rikon 蓷an wani. Ban tashi da ubana ba duk kuwa da cewa yana raye, and still I have gotten the best fatherly care and love"
Na fahimci zancen Baffa yake, sai na bude fuskata ina kallonsa nace "hakane, amma banbancin ka da Subay'a shine shi Baffa bai rufe mahaifinka a prison ba sannan bai yi gidan gona a cikin gidan grandfather dinka ba. No child will ever forget that". Ba tare dana kalleshi ba na wuce shi na koma ciki.
Ina shiga na wuce Inna a palo na shiga daki ina jin zuciyata tana yi min zafi, haushin Sadauki nake ji kuma haushin kaina nake ji. Ji nake kamar wani dan karamin yaki akeyi tsakanin zuciyata da 茩wa茩walwa ta ko wanne yana gaya min abinda zanyi. Sai na sake jawo jakata na kuma hada kayana kamar rannan na fita na samu Inna a dakinta tana sallah sai na zauna na jira ta sai data idar sannan ta juyo tana kallona, daga yanayin zaman da nayi tasan magana ce a bakina dan haka tace "ya akayi?" Nace "Inna, alfarma nake nema a gurin ki. Dan Allah Inna ina so ki fita daga maganar Sadauki" ta kalle ni da mamaki tace "ban gane ba? In fita daga maganar sa kamar yaya? Wacce maganar kenan?" Sai nayi shiru na kasa bata amsa sai tace "ba kya sonsa ne yanzu kuma?" Na girgiza kaina nace "kawai dai Inna ina son ajiye maganar sa a gefe sai zuwa lokacin da muka sake fahimtar juna tukunna. Kinga shekaru da yawa, abubuwa da yawa sun chanja. Ba lallai ne halayyar sa ta da ita ce a yanzu ba. Ni so nake ki bar mu ni da shi kiyi ta mana addu'a in Allah yasa muka fahimci juna sai mu sanar muku ku saka mana albarka" a juya kanta gefe tace "fushi kike dashi akan maganar Saghir ko?" Nayi shiru, sai ta cigaba "ruwansa ne in yaga dama ya yafe masa, ruwansa ne kuma in bai ga dama ba kuma yaki. Ni ba wai ina matsa miki ki kula shi ko ki aure shiba, ina kokarin gyara abinda na bata ne a baya, ina kokarin bashi abinda na hana shine a baya tare da fatan ko hakan zai rage min laifuffuka na a gurinsa da kuma a gurin ubangiji. Dan haka ni dai shi nake so ki aura, amma zabi yana gurinki in kince a'a bazan ji dadi ba amma ba zan matsa miki ba".
Nace "Nagode Inna" sai kuma na gabatar mata da bukata ta tason zuwa gidan Mama. "Kwana biyu" ta ce min, naso ta barni inyi sati ko ma sati biyu amma taki, haka na hakura na dauki kaya set biyu da safe na tafi tunda ina son zuwan saboda ina so muyi shawara.
Ina zuwa na tarar Rumaisa tazo, na saka ta a gaba da tsokana mai ciki mai ciki ita kuma tana ta jin kunyar Mama, sai da muka kebe tace "wai dama haka ake ji in ana da ciki?" Hmmm kawai nace mata a raina ina cewa wannan kukan dadi take yi, na tuna cikin twins ina 14 years, babu abinda na sani, ga babu miji babu iyaye. Na tuna cikin Subay'a yadda na sha wahalar laulayi, da gorin da Saghir yayi min wai daga an taba ni sai ciki.
Sai da muka samu zama sannan na bawa Mama labarin cewa Sadauki fa ya dawo, bai dai furta direct ba amma ya nuna. Ta daga kafada tace "so? Ji nake murna zakiyi kuma naga kin bata rai" sai na gaya mata kuduri na akansa.
"Ba wai bana son aurensa bane ba Mama, so nake ya kunce kullin da yayi da kansa, saboda jin dadin kansa kuma Subay'a" tace "so kike ya yafewa Saghir kudin da yake binsa?" Na girgiza kai nace "ba wannan kadai ba, so nake ya taimaka masa yayi solving drug case dinsa. Sadauki yana da power, zai iya jan wasu strings ayi closing case din Saghir na drugs, ko kuma ayi tracking Kabir a kama shi asaka shi ya amsa laifinsa. Bayan ya fito dashi kuma ina so ya bashi aikin yi, saboda nasan with that reputation babu ma'aikatar da zasu dauki Saghir aiki ballantana ya samu abinda zai rike yayansa". Mama tace "anya kuwa Diyam wadannan sharadan naki basuyi tsauri ba? Wane ne zai je neman auren mace kuma tace masa sai ya fito da tsohon mijinta daga prison kuma ya bashi aiki? Anya kuwa kina ganin zai amsa?" Na girgiza kaina nace "ban sani ba Mama, shine kuma shawarar da nake so ki bani yadda zan saka Sadauki ya karbi wannan maganar. Ni dai abinda na sani shine zuciyar Sadauki tayi tauri da yawa, ya kasa yafewa wadanda yake ganin sun cutar dani da shi. Kuma nasan gurin Sadauki Saghir yafi kowa ba茩i, shi yasa nake so ya yafe masa kuma ya taimaka masa. Nasan in dai har ya iya yafewa Saghir to babu wanda ba zai yafewa ba, in dai har ya taimaka wa Saghir to babu wanda ba zai taimaka wa ba".
Mama tayi shiru tana kallona sannan tace "zuciyarsa tana da tauri tabbas, ke ai kinsan haka tun kuna yara haka yake kuma sai rayuwa ta kara taurara shi. To ni a shawara ta ba juya masa baya zaki yi ba jawo shi kijinki zakiyi. Ki nuna masa irin son da kike masa ki bashi dama ya nuna miki nasa, to shi kansa ba zai san sanda zuciyar tasa zata rissina ba, abinda zaiyi ke kanki sai ya baki mamaki".
Kwana na biyu gidan Mama na shirya zan koma gida Inna ta kirani. "Sadauki yazo dazu, na gaya masa kina nan gidan yau zaki dawo sai yace zai zo ya dauko ki" nace "to" a raina ina jin haushin mai yasa ba zai kira ni ya gaya min ba.
Sai bayan magrib sannan yazo, har na gaji da jira na kwanta a palo ina game a wayata sai ga kiransa "Aliyu" nayi tsaki sai kuma nayi murmushi na daga nayi sallama, ya amsa yace "na dauka ba zaki dauki wayar bama ai. Kin san ni yanzu tsoran ki nake ji fa" nace "naga alama kam. Amma ai ba yanzu ne ka fara tsoran nawa ba dama ka dade kana yi" sai yayi dariya, and I couldn't remember the last time da yayi dariya irin haka. Nima sai nayi murmushi. Yace "ina waje, Please kar kice da Mama ni nazo dan kunyarta nake ji" na tashi na shiga dakin Mama zan mata sallama tace "da daren nan" sai na sunkuyar da kaina nace "Sadauki ne yazo zamu tafi tare" tace "kuma babu gaisuwa? Ki ce masa ya shigo mana" na dauki waya na kira na gaya masa yace "ke ba'a sirri dake? Ban taba zuwa na gaishe ta ba sai kuma in zo in fitar mata da 拼a? Ni kunyar ta nake ji" nace "to ai in bance kai ne ba ba zata barni ba cewa zata yi dare yayi" a dolen sa ya shigo, yana ta sunkuyar da kai yana shafa keya, and I asked myself "wai me yasa maza in suna jin kunya suke shafa keyar su?".
Bayan ya fita nayi wa Mama sallama na bishi a baya. A cikin mota na same shi a zaune a seat din driver. Sai ya bude min kofar gaba yayi min alamar in shigo da hannunsa. Na shiga na rufo kofar sai ya juyo yana kallo na, na sunkuyar da kaina kasa ina feeling uncomfortable. Motar naga kamar tayi mana kadan, space din tsakanin mu yayi kadan, ga motar ta cika da kamshinsa mai shiga har cikin ruhi. Sannan kuma gashi yana min murmushi.
Naji kamar in bude motar in fice. Bai kunna motar ba ya juyo yana kallona Yace "wai ke duk fushin ne haka? Me zanyi ne wai ayi min murmushi ko guda daya ne" sai na kara bata rai na turo baki yace "okay rashin kunyar tana nan ashe kenan. Na dauka an barwa Subay'a" sai ya tayar da motar muka bar gidan.
A hanya yace "kinsa naji kunyar Mama fa, banzo na gaishe ta ba sai da nazo zance" na kalle shi nace "zance? Gurin wa kaje zancen? A kano muke fa ba'a Maiduguri ba" ya dan bata rai kamar mai tunani sai kuma yayi dariya yace "ohhh okay, yanzu na gane wannan fushin na menene. Ai na gaya mata zan zo gurinki dama kuma tace in gaishe ki" nace "kar ma kayi tunanin da nake tunanin kana yi. It is not what you are thinking" yace "yes it is. Hausawa sunyi karin magana suka ce kishi kumallon mata, amma ke naki kishin aman gaskiya yake saka ki. Daga jin muna magana da Inna sai ki kama amai?" Na gane maganar da yake yi nayi saurin cewa "ba fa abinda kake tunani bane ba, bani da lafiya dama a lokacin. To ni ina ma ruwa na da aurenka" yace "okay idan rashin lafiya ta saki amai ita ce kuma ta saka daga nayi miki sannu kika rufe ni da fada?" Nace "kaga nifa bana son ake juya min magana ta" yace "shikenan, an daina" muka cigaba da tafiya sannan yace "na bata labarin ki. I told her ina son aurenki first and she agreed" ya fada yana kallona, nayi kamar ban jishi ba ina jin bacin raina yana karuwa, amma sai ya sake cewa "tana sonki sosai. Tace zata zo Nigeria karshen week din nan purposely saboda ta ganki" na saka hannuna na toshe kunnuwa na ina jin zaman motar duk ya ishe ni. Nace "stop the car" yace "why?" Nace "ko dai ka daina wannan maganar ko kuma ka tsayar da motar nan in fita in karasa a kafa" sai ya kama dariya yace "an daina your highness".
Muna zuwa gida nayi masa godiya, kafin in bude kofar ya kira suna na "Diyam" na juyo ina kallonsa yace "Please in na kira ki ki dauka kinji. Say whatever you want to say in kin dauka din but please kar ki 茩i dauka".
Ranar na jima banyi bacci ba ina juyi. Feeling a familiar warmth a cikin zuriya ta wanda a da naje tunanin ko ba gushe yanzu baya nan. Zuciyata da 茩wa茩walwa ta suka cigaba da battle dinsa ni kuma na zama confused dan bansan wanne daga cikin su zan bi ba. My heart was telling me in kira Sadauki a waya, in bude masa zuciyata in gaya masa irin zurfin da soyayyar sa tayi a ruhina, while my mind was asking me to hold on, reminding me cewa ba lallai ne in Sadauki ya samu abinda yake so ni kuma ya bani abinda nake so ba.
Washegari da safe bayan na dawo daga islamiyya ya kirani, daga alama a office yake "kinci abinci? Me kika ci?" Nace "kosai Asma'u ta soya mana" yace "yan gayu. Ni kuma kinga yunwa nake ji babu wanda ya damu yace Sadauki ga abinci" nace "Sadauki ko Mr Abatcha?" Yayi dariya yace "all the same" nace "ni banga same ba. Sadaukin dana sani is different from this rich Mr Abatcha" yace "really? To fada min menene bambancin" nace "da farko dai Sadauki baya taba yin abinda zai bata ran Ummah ko Baffa. Ita kuwa Ummah a cikin masu hakuri ma ita daban Allah yayi ta, bata taba fada ballantana har ta kasa yafewa wadanda suka bata mata. Na tabbatar kuma zata so ace yayanta, ni da kai, munyi koyi da ita, ko da bamu zama irin ta ba sai mu kwatanta ko yaya ne"
Ya jima shiru sannan yace "she was a good woman. The best. Bata bata wa kowa, in mutum ya bata mata ma sai tayi kamar bata gani ba duk kuwa da cewa ta gani 蓷in. Har gida har daki za'a zo aci mutuncin ta ba tare data yi laifin komai ba and she will always looked at me and said "kar kayi magana, kar kace komai" and I will keep quiet. Amma ranar data mutu kinsan me Alhaji Babba yace? Cewa yayi ba za'a shigar da gawarta gidan mijinta ba as if she were some kind of trash" na goge hawayen daya taru a idona ina tuno wa da abinda ya faru a ranar data chanja gabaki dayan rayuwata.
Nace "sai menene kuma? Hakan ai bai rage ta da komai ba a wajen ubangijin ta, kuma muna saka mata ran cewa yanzu tana gurin da yafi gidan nan kyau da daraja. Kuma nasan da ace zata kalle ka a yanzu zata ce "kar kayi magana, kar kace komai" saboda tana son ka zama mai hakuri mai yafiya irin wanda Allah yake so, Annabi kuma yake alfahari dasu" yace "nasan abinda kike so ki ce, so kike yi kice in yafe musu gabaki dayan su, amma abinda kika manta shine, su fa basu yi nadama ba har yau. Yes, Alhaji ya bani hakuri ranar nan amma daga ni har ke har shi munsan cewa tuban muzuru yayi, na saka shine a corner babu yadda zaiyi shi yasa ya bani hakuri amma a lokacin da yana da dama da ina juya bayana zai da蓳a min wuka"
Nace "na sani, amma wannan shi da ubangijin sa, ni da kai na damu ba dasu ba, zuciyarka nake fatan gyarawa and maybe a kokarin haka kaga tasu itama ta gyaru. Kasan abinda na fahimta? Babu abinda yafi saukarwa da mutum nadama irin idan wanda akayi wa sharri yayi sakayya da alkhairi. Take Inna as an example. Ba karamar nadama ce Inna tayi ba kuma a yanzu babu wanda take kaunar farantawa sama da kai" ya ajiye numfashi yace "kina so in yafe musu?" Nace "yes, amma badan ni zaka yafe ba. Dan Allah zaka yafe. Take your time and think over it. Kai da kanka zaka yanke shawarar yin abinda ya dace". Sai ya chanja maganar "yanzu ya za'ayi a kawo min kosan nan zuwa office?"
Kamar wasa few days bayan nan da daddare ina shirin kwanciya ya kira ni "me kike shirya wa bakuwar ki ne?" Nace "wacce bakuwar kuma?" Yace "kin manta nace akwai wadda zata zi gurinki?" Naji duk nishadin dana ke ji ya kau, nayi shiru yace "gobe zata sauka. Jirgin safe. Ni ina da meeting about that time. Ki shirya sai in turo miki da mota kije ki dauko ra a airport" nace "ni kuma? To ni da bansan ta ba ta yaya zan gane ta?" Yace "ki saka bakar doguwar riga ita kuma zata saka milk. You will know her when you see her" na hadiye abinda ya tsaya a kirjina nace "ya sunanta?" Yace "Murjanatu".
Not edited. Sorry for the typos.[3/4, 8:20 PM] +234 703 589 5826: 鉂わ笍 DIYAM 鉂わ笍
By
Maman Maama
Episodes Fifty Nine & Sixty : The Answers
Da safe na gayawa Inna sakon Sadauki. Tace "to fa! Sai kije ki dauko ta din. Anan zata sauka ne ko kuma a wani gurin daban?" Nace "nima ban sani ba inna" sai tace "to ki kira shi ki tambayeshi mana, in nan zata sauka ai gwara mu sani dan ayi mata abinci ko?" Na kasa kiransa saboda ji nayi duk haushinsa nake ji, sai na tura masa text "a nan zata sauka?" Sai da na fito daga wanka naga reply dinsa, "bakuwar ki ce ba tawa ba. Besides, ni gwauro ne bani da gurin da zan sauke ta".
Karfe goma da rabi yace min jirgin su zai sauka. Karfe goma driver yazo yana jirana. Asma'u tana school Subay'a ma haka, dan haka dole na shirya ni kadai na fita ina ta bace bacen rai. Sai 10:30 muka je airport din a raina ina cewa 'in sun sauka ma ta jira, da waye ya gayyace ta zuwa wajena?" Sai kuma nayi rashin sa'a jirginsu yayi delay dan haka sai da muka jira ma sannan suka sauka. Ina tsaye da bakar rigata da ya umarce ni in saka idona akan kofa ina ganin masu fitowa, mostly turawa ne maza da mata, sai few blacks suma kuma yawanci maza ne sai kuma wasu family da suka fito tare. Sannan na hango ta ta taho, tun daga nema na ganeta saboda kalar rigar jikinta. Waya a makale a kunnenta tana magana tana murmushin da yake bayyana hakoranta, naji kirjina ya buga da karfi a lokacin da zuciyata ta ayyana min wanda suke wayar dashi.
Ta fito waje sosai tana dan dube dube, idonta ya sauka a kaina sai naga ta sake fadada murmushin ta ta katse kiran sannan ta taho inda nake. I was suppose to like nima in tafi inda take sai mu hadu a hanya amma sai nayi tsayuwata pretending as if ban gane taba har ta karaso gaba na tana murmushi tace "Diyam?" Sai kuma na kirkiro murmushi nayi mata ina studying dinta. Baka ce, mai matsakaicin jiki kyakykyawar gaske and every part of her was screaming "I am rich" dan kallo daya zaka yi mata kasan cewa bata san wata kalma wai ita wahala ba. And something caught my attention, kalar skin dinta, manyan fararen idanuwanta, shape din fuskarta da kuma yanayin murmushin ta irin na Sadauki ne. Na tambayi kaina "are they related? Ko hadin gida za'ayi musu?"
Na kirkiro murmushi nace "Murjanatu?" Sai tayi dariya, ta saka phone dinta a cikin karamar jakar da take rataye a kafadarta sannan sai kawai naga ta rungume ni, ta sake ni tana kara kallona tace "wow, you are even more beautiful in person than yadda aka kwatanta min ke" na danyi dariya ina tunanin tsaurin ido na Sadauki da zai zauna yayi wa budurwarsa description dina. Nace "welcome to kano, fatan dai baki sha wahala sosai ba" ta yarfe hannu tace "zafi, haka kullum in muka je Maiduguri nake fama. Kamar ace an ciro mutum daga cikin freezer ne an saka shi a cikin oven. Na kan tambayi Adama, wai haka kaji sukeji in ana gasa su? irin frozen chicken din nan kuma a saka su a oven" nayi dariya a raina ina cewa wannan surutu ne da ita.
Drivern da muka zo dashi ya zo ya fara jan akwatin ta ni kuma sai na mika hannu da niyyar in karbi jakar hannunta amma sai taki bani tace "rufa min asiri, so kike yaya ya gasa ni kamar gyada?" Na maimaita kalmar yaya a raina. So they are related da gaske.
Muna tafiya veil din kanta ya fado kafadarta ya bayyana gyararren gashin kanta, but sai naga bata damu data gyara ba har sai da ni da kaina na gyara mata. She just thank me casually muka cigaba da tafiya.
A hanya muka dan taba hira, duk da dai da yawa daga hirar ita takeyi, a lokacin take gaya min cewa wannan ne zuwan ta kano na farko "in munzo Nigeria gida muke zuwa, Maiduguri, sai Abuja sometimes, mun dai taba zuwa Kaduna once" jin haka sai na fara yi mata bayanin guraren da muke wucewa a hanya, and she looked very interested.
Da muka je gida ina kallonta ina jiran inga tayi wa gidan mu wani kallo haka, ko kuma in an bata abinci inji tayi wani comment marar kyau amma sai naga sam babu abinda ya dame ta, she is the most down to earth person I have ever met. Ta zauna ta harde kafa tana ta cin tarin abincin da Inna ta jera mata tana kuma yiwa Inna hira. Sai tace "ina 'yar Asama? Kullum sai an bamu labarin Yar Asama da Diyam, Diyam this Diyam that. Ko kaya muka saka sai yace "ku kun mayar da kanku turawa, kuyi ta saka kananan kaya, why can't you dress like Diyam?" Ta fada tana kwaikwayon yadda Sadauki yake maganar sa.
Na kai mata kayanta dakina sannan na hada mata ruwan wanka a toilet nace tayi wanka ta huta. Bata tashi ba sai da Asma'u ta dawo daga school, ina jin Inna tana yi mata bayanin bakuwar da akayi sai kuwa naga ta tura baki tana kunkuni, Inna tayi mata warning kar ta sake tayi mata wata magana marar dadi.
Na shiga daki na tarar ta tashi daga bacci tana sallah, na zauna ina jira har ta idar sannan na tambayeta ko da akwai abinda take so. Kafin ta bani amsa Asma'u ta shigo tace "nazo gaishe da matar yayana" sai naga Murjanatu ta kalle ni sai ta cigaba da nineke abin sallah. Asma'u ta sake cewa "matar yaya barka da zuwa" sai Murjanatu ta kalle ni tace "ana miki magana" nace "ke take gaisarwa fa" sai tace "matar yaya naji tace, wanne yayan?" Na gyara zamana ina so inyi confirming suspicio dina Nace "Sadauki mana" ta dan bata fuska tace "waye Sadauki?" Na sunkuyar da kai nace "Aliyu, mu anan Sadauki muke ce masa" cikin mamaki tace "yaya Aliyu? Nice matar tasa kuma?" Nace "well, not legally yet, yace dai an bashi ke an kusa biki" sai ta zauna a bakin gado ta dafe kanta tana dariya tana kallona tace "tsokanar ki yake, he is my brother, my half brother, baban mu daya".
Har dare Murjanatu tana ta tsokana ta. Ina jinsu suna waya da Sadauki tana bashi labari suna dariya sai na harare ta daga ita har wayar tata, ina jinta ta gaya masa wai ina hararar ta sai naga ta saito ni da wayar kamar zata min hoto sai na rufe fuskata ita kuma tayi ta min hotuna a haka.
Sosai Murjanatu ta sake a gidan mu, nan take muka kulla kawance mai kyau a tsakanin mu. Tana ta yimin hirar gidan su, Papa, Mama, Adama, Sa'adatu, Yani. Amma ban taba yi mata tambaya a kansu ba, na saka a raina cewa Sadauki ne ya kamata ya bani labarin su. Na fahimci kuma tana tsoron Sadauki, duk da kuwa na kanga suna yin waya suyi hira amma kamar bata taba ketare maganar sa, bata yi masa musu, kuma tana bani girma sosai saboda shi.
Ranar nan bayan Murjanatu ta kwana uku da zuwa muna waya dashi tace gobe mu shirya gabaki daya zai zo mu fita yawo "mu zagaya da Fanna taga garin Kano" nace "Fanna?" Yace "yes, Murjanatu. We call her that a gida".
Ina gaya musu sai murna, nan da nan Asma'u ta fara making list na guraren da zamuje, aka fara ware kayan da za'a saka da irin kwalliyar da za'ayi. Murjanatu ta kalleni ina yi musu dariya tace "gobe sai na yi miki kwalliya. Asma'u zata rike min ke in kinki tsayawa".
Na dauka wasa suke sai washegarin na fito daga wanka sai gasu da make up kit, nace bana so amma haka suka tilasta min suka yi min kwalliya. Na dauko abaya ta na saka sai Murjanatu ta tsaya tana kallo na tace "wannan rigar is too loose, bai fitar da duk abinda ya kamata ya fitar ba bayan kuma akwai abin" sai ta dauko wani belt a kayanta ta daura min, na kalli kaina a mirror naga yadda hips dina suka fito sosai, ni kaina bansan ina dasu har haka ba, sai na girgiza kaina nace "bazan iya fita haka ba. Mutane zasu ke kallona fa" sai ta dan dake ni a kafada tace "dalla in sun kalle kin sai me kuma? Ke wallahi halin ku daya da yaya Aliyu yanzu zaku fara wa'azi" nayi dariya kawai amma na hakura ne kawai dan bana so in gwale ta amma ni nasan bazan iya sakewa ba sam.
Muna gamawa yazo, muka fita ni dai ina ta rabe rabe a bayansu. Muna fita muka hango motarsa duk da bama ganinsa but I felt his eyes on me sai na kara buya a bayan Murjanatu ina jin kamar zan gurde in fadi har muka karaso inda yake, Murjanatu ta bude min kofar gaba tace "entere" nayi murmushi na shiga ina jin still idanuwansa a kaina amma na kasa kallon side din da yake, sai naji yayi gyaran murya yace da Murjanatu "koma ciki ki samo mata hijab" sai ta kama bubbuga kafa a kasa kamar mai shirin kuka sai yayi mata tsawa "are you still there?" Da sauri ta koma cikin gida.
Nayi kasa da idona ina wasa da fingers dina, still feeling his eyes on me. Sai yace "kinyi kyau sosai Halima. But I can't let people see you like this. Ina da kishi da yawa I might end up fasa wa wani hanci akan hanya. In son samu nane ma bayan hijab har nikab zaki saka ki rufe fuskarki" tunda ya fara magana nake murmushi, ina jin feeling mai dadi a raina cewa nima ina da value. Sai na tuno da ranar da Saghir yake fito min da gashina "let's show them abinda matansu basu dashi".
Ta kawo min hijab din na saka ya saka hannu ya gyara min fuskar hijab din sannan yace "that's much better" sai kuma ya leka waje yace da Asma'u da Murjanatu "duk wadda bata shigo ba zamu tafi mu barta" da sauri suka bude baya suka shigo suna dariya.
Yawo mukayi sosai a garin kano, har gidan sarki sai da muka je muka shiga ta kofar gudu muka fito ta kofar arewa muka ga grand central mosque. Muka je gidan mesium muka je gidan makama da gidan mutan da. Muka hau badala, muka hau dutsen dala da gwauron dutse. Muka je har government house muka yi zagaye a ciki muka fito sannan muka tafi Abatcha Motors.
Murjanatu tace "yau dai finally zanga wannan precious Abatcha Motors din da yake rike yayana a Nigeria. Ko da yake ban sani ba ko ba shi kadai bane yake rike shi ba" ta fada tana mintsini na ta baya. Na juya na harare ta shi kuma yana mana dariya muka shiga building din.
Da yake weekend ne duk babu ma'aikata sai security kamar zasu ci mutum. Muna zuwa suka taso kamar zasu durkusa mana ni dai duk sai naji inajin nauyin su. Ya saka su bude ko'ina a gurin sannan yace dasu Murjanatu su zagaya duk inda suke so mu kuma sai ya saka aka kawo mana kujeru gaban wani fountain muka zauna.
Sannan ya dauko waya yayi kira, da alama abinci yayi mana order. Sai kuma yace min "ranar nan, you asked me some questions. Are you ready for the answers?" Na tuno tambayoyin da nayi masa farkon zuwa na office dinsa. Sai nace "eh. Ina son sani please". Yace "okay. Let's start from the beginning".
"Tun farko na san cewa Alhaji Bukar ne ya hada auren Ummah da mahaifina, amma bamu taba maganar dashi ba saboda ganin kamar umman bata so".
"Sunan mahaifina Alhaji Umar Mustapha Abatcha" nayi saurin cewa "Alhaji Umar Mustapha dai wanda muke jin labarin sa?" Ya gyada kai yace "shifa. Family din Mustapha Abatcha family ne da yayi suna ba'a Maiduguri ba kadai har ma da sauran Nigeriya. Suna da kudi tun asalinsu but kudin Umar Mustapha daban ne dana sauran. Tun yana saurayi ya mallaki kudin da shi kansa mahaifinsa a lokacin bashi da su. Harkar man fetur yakeyi yi, tun yana yin gidajen man fetur a gari gari har ta kai shi ga fara siyan rijiyoyin man fetur din gabaki 蓷aya. Bashi da lokacin aure, dan haka ya jima baiyi ba, wannan yasa yan'uwansa, musamman da yake duk yan uba yake dasu dan shi kadai ne a gurin mahaifiyarsa, suka sako shi a gaba, suna saka ran in ya mutu suci kudi. A lokacin ne Alhaji Bukar, tsohon amininsa da sukayi secondary school tare yayi masa tayin auren bafulatanar yarinya Zainab. Shi kuma sai ya karba yana ganin tunda ba auren soyayya bane ba ba zata ke demanding time dinsa ba. Ta gaya masa labarin wanda take so aka raba su and he was sympathetic, yana nuna mata kulawa sosai ita kuma ta kwantar da hankalin ta sukayi zamansu lafiya a nan family house dinsu dake Maiduguri. A haka har ta samu ciki. A lokacin ne kuna ya fara business da Canada yana exporting crude oil daga Nigeria zuwa Canada wanda har yanzu shine sana'arsa, a yanzu yana daya daga cikin manyan dealers na crude oil a kasar Canada.
Tunda zainabu ta samu ciki shikenan kuma sai al'amurra suka cabe mata, gashi lokacin baya zama a kasar ita kuma taji duk duniya babu inda ta tsana irin gidan aurenta, babu wanda bata son gani kamar mijinta, babu kuma abinda take son rabuwa dashi irin cikin jikinta. Ta zama kamar mahaukaciya, sai ta fita da gudu sai an bita ana kamota ana dawo da ita gida, wani lokacin kuma sai ta zauna tayi ta dukan cikin wai sai ta kashe abinda yake ciki. Alhaji Umar yana zuwa ya ganta a wannan halin yasan asiri ne dan haka ya hada malamai aka zauna addu'a da magungunan karya sihiri akayi tayi mata, in abun ya lafa kwana biyu sai ya dawo. Ta sha wahala sosai. Ranar nan cikin dare suna bacci ta tashi tafita ko dan kwali babu ta kama doguwar katangar gidan da aka zagaye da waya da kwalabe amma a haka ta haura ta var gidan cikin jinin ciwuwwukan da taji, Alhaji Umar yana tashi yaga bata nan ya fito yayi ta nema babu wanda ya ganta sai ya dauki mota ya fita hankali a tashe. Cikin ikon Allah sai ya samo ta tana ta tafiya kamar zautacciya a kamata da kyar ya saka a mota daga nan sai airport. A can ya samu yayi mata adduoin ta dawo hankalinta ya sako ta a jirgi ta taho Kano ya kira Alhaji Bukar ya gaya masa, shi kuma sai ya koma ya nuna cewa bai same ta ba. Akayi ta nema har da cigiya a gidajen radio daga baya aka hakura.
Ita kuma ta dawo gurin yaya ladi ta zauna a kano. Har ta samu lafiya sosai aka tabbatar duk sihirin dake jikinta ya fita. Anan ta haife ni, Alhaji Umar yazo da kansa yayi min huduba da suna Aliyu "saboda ka zama jarumi ya sa na saka maka Aliyu" daga nan sai ya datse igiyar aurensa da zainabu, ya kuma roki Alhaji Bukar cewa ya nemo wannan wanda take so din yayi kokarin hada su aure, bayan an samo Baffa kuma Alhaji Umar da kansa ya bashi amana ta. "Dan Allah ka rike shi tamkar kai ka haife shi. 茒a na kowa ne ai, wata kila ma kai zaiyiwa rana bani ba. Ni dai kawai ina son shi da mahaifiyarsa su kasance safe". Through all those years da nake gurin Baffa ashe duk Alhaji Umar yana biye da rayuwata, kuma yace ko da sau daya Baffa bai taba neman wani taimako daga gare shi ba.
To bayan rasuwar Umma da Baffa, bayan na koma gidan Alhaji Bukar, sai yake gaya min cewa ya gaya wa mahaifina zancen rasuwar, amma baya kasar a lokacin yasan da zaizo gaisuwa ma amma yace a gayamin in saka rana da kaina sanda na ke ganin am ready in gaya masa zaizo Nigeria sai mu hadu a Maiduguri. I fixed the date, sai muka tafi. But cikin rashin sa'a sai ya zamanto shi din wani abu yarike shi a can kasar da yake zaune, Canada, dan haka bai samu tahowa da wuri ba. Ban sami kowa a Maiduguri ba sai step grandmother dina a uncles dina. A lokacin ne kuma kika kirani da maganar za'a hada aurenki da Saghir. Nan take naso in yi musu dan karamin hauka a gidan na dage akan lallai sai an taho anzo Kano an nema min auren ki. Duk kallona suke kamar tababbe, irin suna ganin ban isa aure ba ai. Aka kira Papa aka gaya masa yace a rabu dani, wanne irin aure kuma? Sai na karbi wayar na gaya masa ko dai ya ajiye koma me takeyi yazo ya nema min aurenki ko kuma in kama gabana kuma babu wanda zai kuma jin labari na. Sai na gaya masa ko wa cece ke da dangantakar mu. Wannan ne ya ja hankalinsa. Sai ya bani hakuri akan cewa ba zai iya zuwa ba sai dai mu taho tare da Alhaji Babagana, daya daga cikin uncles dina. Muka taho din kuwa and you know what happened a gidan Alhaji Babba. Sanda muka fita I was beyond broken. Sai nace bazan koma Maiduguri ba, a gidan Alhaji Bukar zan zauna. Na zauna gidan Alhaji Bukar trying to find a solution amma na rasa ko daya, babu irin tunanin da banyi ba ciki kuwa har da in shirya mana visa tare zuwa Canada sai in dauke ki mu tafi can mu cigaba da rayuwar mu. But sai na tuno da kalaman Baffa da yake cewa ba yaso ya bani aurenki in dai babu amincewar Inna a ciki, nasan kuma yadda Inna bata sona in na dauke ki zata hada daga ni har ke ne ta tsine mana kuma ba zamu taba ganin dai dai ba a rayuwa. And I didn't want to put you through that. Sai na fara bincike ta karkashin kasa, Alhaji Babagana ya bani kudi sosai kafin ya koma Maiduguri dan haka bani da matsalar kudi, I followed Alhaji Babba, I watched him a lokacin da ya siyar da garejin Baffa, I also watched him lokacin da ya siyar da filina, I watched him lokacin daya siya wa dansa gida na bishi har gidan na gani. But bayan ya tafi sai na tsaya ina studying gidan, bai yi min ba kwata kwata. Unguwar was deserted dan haka babu security kenan, ko menene zai samu mutum a gidan babu wanda zai sani. Na haura na shiga har cikin gidan sai naga locks din kofofin ba masu kyau bane sosai sai naje na siyo wasu na dawo na cire wadancan na saka sababbin da kaina. But still ban gamsu ba dan nasan wannan mijin naki ba lallai yake zama a gida bake kadai zai ke bari so I hired a gate man for you. Malam Iliyasu" na kalle shi da sauri nace "Malam Iliyasu dai maigadin gidan Saghir?" Yace "yes. Tsohon soja ne yana gadi anan kusa da gidan Alhaji Bukar to sai wanda yake yi wa gadin ya rasu. So I took him zuwa unguwar na nuna masa gidan, mukayi sa'a Saghir din yazo sai na nuna masa shi nace yaje ya nuna masa cewa gurin zama yake nema, yana son zaiyi masa gadi free of charge abinda yake so kawai a bashi dakin mai gadi ya zauna anan. And he took the bait. Nace yace masa free ne dan na fahimci babu yaren da Saghir yake ganewa sosai irin na kudi. So, Malam iliyasu yayi muku gadi, ni nake biyansa duk wata, in return shi kuma yana supplying dina with information musamman abinda ya shafi lafiyar ki"
Ban bar kano ba sai da nayi attending daurin aurenku da Saghir. Daga nan airport na wuce straight na tafi Maiduguri ina zuwa kuma na tarar takarduna sun gama haduwa zuwa Canada dan haka kwana na daya a Maiduguri na tafi Ottawa, capital din Canada inda anan ne mahaifina yake zaune da iyalinsa.
I had been holding on, ina ta gayawa kaina cewa ba gaskiya bane ba, cewa ban rasa ki da gaske ba, but sai a jirgin nayi loosing din sauran hope dina. Gani nake yi na rabu dake kenan har abada and I couldn't picture my life without you, gani nake babu wani sauran meaning a rayuwata. Daga airport maimakon gida sai asibiti aka wuce dani, ji nake kamar tsaga kirjina akeyi da wuka ana yankar zuciyata sala sala. Mahaifin da naci burin gani sai a asibiti na ganshi and the first thing da ya fada min shine "are you this weak? Do you really want to die saboda mace?" Nace "she is not just any woman. She is mine and they took her from me" yace "to me zakayi akai? Zaka kwanta ka mutu ne while tana can tana sabuwar rayuwa da wani ko kuma zaka tashi ka rayu and show them that abinda sukayi is wrong?" And I decided, maybe gwara in rayu din, maybe one day I will be able to see you again, and get you justice from whoever wrong you.
But it was easier said than done. A watannin farko na aurenki I spent more time in hospital than at home. In ina gidan ma kuma ina daki a rufe. Bana kula kowa bana yi wa kowa magana. All I kept thinking about was you, you and you. Kullum tunani na a wanne hali kike ciki? Kinyi missing dina ko kuma kinyi accepting auren ki kin cigaba da rayuwarki da mijinki. Na kira Malam Iliyasu sai yake gaya min cewa Saghir yayi tafiya sai ke kadai a gidan tare da wata mata. And the agonizing months suka wuce, the most terrible times of my life. Ranar nan ina gida da rana kawai sai ga wayar Malam Iliyasu, nayi mamaki dan nasan cewa dare ne ku a wajenku na dauka sai naji cikin tashin hankali ya na gaya min wai baki da lafiya, shi yana ganin ma kamar kin mutu dan yaga maigidan ya dauko ki cikin jini ya saka ki a mota ya fita dake. Papa yana office dan haka message kawai na tura masa na dauki kudi da passport na tafi airport. Ban samu jirgi zuwa kano ba sai Abuja. Sai dana shiga Abuja sannan na samu wani zuwa kano ina shiga kano na kira Malam Iliyasu yace min shi bashi da wani labari tunda kuka fita shiru, sai na wuce gidan Alhaji Babba, na shiga har compound din gidan saboda yadda nake jin raina I was beyond caring akan me zai faru in aka ganni. Amma sai na tarar da gidan a hargitse, hankali na ya tashi and I asked wani mai kula da flowers sai yace min ai gobara ce Alhaji yayi duk shagunan sana'arsa sun kone kurmus babu abinda ya tsira dashi. Sai na tambayeshi game da matar Saghir, sai yace haihuwa ce kika yi amma yaran sun mutu, ke kuma an kaiki asibiti amma baisan wanne asibitin ba. Muna cikin magana Inna ta shigo gidan, ta wuce mu ba tare da ta ganni ba kuma na lura hankalinta a tashe yake, ta shiga cikin gidan ta sake fitowa sai na tura wanda muke tare nace yaje ya tambaye ta ya mai jiki? Anan naji sunan asibitin da kike, ana bukatar jini kuma ita ta rasa kowa duk gidan suna gurin Alhaji da yake asibiti shima. Sai na fice ba tare data ganni ba, na je asibitin da kike na nemo dakin da kike na shiga har ciki na ganki. You were sleeping, kamar allurar bacci aka yi miki. Kin kumbura sosai kinyi fari tas. I stayed a dakin for a while ina ganin kamar in na fita bazan dawo in tarar dake da rai ba but i knew dole inyi wani abu sai na tafi nace Inna ce ta turo ni in biya kudi kuma a dauki jini na, akwai wadda a gurin ta tambayeni ko nine mijinki and it pained me to say no. Aka gwada jini na and luckily sai yayi matching da naki"
Na katse shi "wait, wai kai ka bani jini ranar nan a asibiti?" Yayi murmushi "naki fadar kaina ne saboda nasan yadda Inna bata sona zata iya cewa ba za'a karba ba dan kar in shafa miki maita or something like that"
Kullum ina zuwa in duba ki. Na tabbatar kina samun sauki sosai, ranar nan saura kadan Mama ta ganni na buya duk I doubt ko ta ganni ma zata gane ni saboda ni kaina nasan I looked terrible. Ranar nan nazo sai akace min a ranar za'a sallame ki. Sai na tsaya and I saw you sanda kuka fito, ke da Inna da Saghir da wadansu mata. Kuka shiga motar Saghir ke da Inna kuka tafi and I kept following you a kafa sai danja ta tsayar daku har na karaso inda kuke and I did what I shouldn't have done, nayi miki magana"
Da sauri nace "I knew it. Nasan kai na gani amma inna tace wai aljanu ne suka bude min ido". Yayi murmushi. Ban kyauta ba na sani bai kamata inyi wa matar wani magana ba but I did it.
A ranar na koma Abuja daga nan kuma na koma Canada. A cikin jirgin nayi making decision cewa it is time to move on, tunda ke gashi har kin haihu, seven months after the wedding har kin haihu. Dan haka ina zuwa gida na samu Papa nace "am ready to move on yanzu" yace "good. Sai ka tafi makaranta kayi mechanical engineering dinka" sai nace "ina son karatu amma nafi son business, in yaso sai in hada da karatun da business din duka" yace zai saka ni a harkar Mai, but sai nace masa bana son aiki under him, I want something of my own, yadda zan making name for myself ba wai in jingina dashi ba. Na dauka zaiji babu dadi but sai naga yayi murna, yace wannan ya nuna masa how strong I am. Sai yayi signing check ya bani yace in cike kudin da nake ganin zasu ishe ni in kafa kaina. Na rubuta na mika masa sai ya yaga check din yace "wannan kudin da zan bawa wani ne in tazo neman taimako gurina. Ba kudin da zan bawa tilon dana ya kafa business ba. Sai ya sake signing wani ya miko min yace "multiply that by hundred, ka rubuta kaje ka karba. Allah yasa albarka a ciki".
That was the beginning of Abatcha Motors. I chose Kano saboda in samu damar keeping eyes on you. Cikin few months aka gama komai na fara hiring ma'aikata. A lokacin ne Malam iliyasu yake gaya min cewa kuna cikin matsalar kudi dan yaga aba ta fitar da kayan gidan ana siyarwa. So, I talked to someone who talked to someone har aka gayawa Alhaji Babba cewa ga sabon company nan ana daukan ma'aikata and luckily shi kuma Saghir ya dauko takardunsa ya fito neman aiki a lokacin sai aka turo min shi. A gurin interview din dana yi masa ne na tabbatar cewa bai sanni ba. I gave him a job. Amma ba job bane ba dan baya ma cikin list of staff dina. Salary dinsa daban nake bashi and his salary was just like me giving you money. Ina bashi kudin dana san ya isa ya kula dake.
Ina gab da komawa Canada ne sai yazo office dina yana ta complain wai matarsa ce zata haihu kuma doctors sunce ba zata iya haihuwa ba sai dai ayi mata aiki, gashi sunyo masa bill na kudi da yawa. I was scared kar yazo yaki biyan kudin ki zo ki samu matsala so I paid the money. Har na kara masa da kudin ragon suna da sauran hidima, ranar da za'ayi aikin na kwana ina miki addu'ar nasara, I wanted to go and see you but nasan hakan ba dai dai bane ba sai na hakura nace ya kirani in anyi and I asked him ya sakawa yarinyar Subay'a hoping hakan zai faranta miki ranki.
Daga nan na koma school. Carleton University of Canada. Anan nayi karatu tsahon shekaru biyar na fita da matsayin mechanical engineer. A wannan shekarun ne muka yi bonding sosai da yan uwana. My four sisters, Sa'adatu, Yani, Fanna da auta Adama, wadanda Papa ya bani task din koya musu hankali dan zaman kasar turawa ya saka duk sun koma suma kamar turawan. Yanayin shigarsu da yanayin mu'amalar su. I treated them with fire, but sometimes kuma sai inyi musu sanyi muyi ta wasa da dariya. Maman su kuma ta bani goyon baya sosai gurin koya musu hankali dan dama yanayin nasu duk yana damunta itama turancin ne yasa bata iya tsawatar musu.
All those years, nayi iyakacin kokari na dan ganin na cire ki a zuciya ta amma abin ya faskara. Nayi addu'a, nayi azumi nayi sadaka duk da wannan niyar, daga baya sai na saka a raina cewa wannan shine kaddara ta, zan rayu da sanki a zuciyata amma bazan rayu dake ba. Ban dauka cewa babu abinda ya ragu na sonki a zuciyata ba sai dana dawo, ranar da staff dina sukayi surprising dina da party, I saw you there, I tried pretending but then I saw him holding your hand and I couldn't take it, nasan in ban bar gurin ba zan iya rufe shi da duka dan haka na gudu"
Then one day ina dakina na hotel ana ruwan sama, har na fara shirin bacci sai ga wayar Malam Iliyasu yace min mamanki da kanwarki sunzo gidan Saghir ya kore su, ga dare gashi ana ruwa yana jin tsoron kar wani abu ya faru dasu. I left everything na hau mota na taho unguwar ina tafiya ina dubawa, hankalina a tashe ina tsoron kar in zama too late, sai gasu nan kuwa na gansu already har sun fada hannun mugaye. I couldn't imagine me zai faru da Asma'u idan da Allah bai sa Malam Iliyasu ya kirawo ni ba. That was when I decided to sue Alhaji Babba for garejin Baffa da filina. Tunda rashin mutumci suke ji I decided to show them rashin mutunci".
"Wannan shi yayi stating chain of events din da har suka kai ga rufe Saghir"
"Ina so ki fahimci cewa ban rufe Saghir dan in aure ki ba. Yes, I loved you, I love you and I will take your love with me to my grave but da ace zaman lafiya kuke yi da Saghir da babu abinda bazanyi ba dan ganin cewa zamanku ya dore a tare. I would have given everything in dai zakiyi farin ciki. But after na fahimci irin zaman da kuke yi, after what he said a gaba na ba tare dako digon nadama a muryarsa ba, after ke da kanki kin gaya min cewa ba kya son komawa gidansa then I won't let you. Yes, na barwa Saghir kudina intentionally saboda ina so ya dauka, saboda ina son in samu hujjar rufe shi yayi paying for abinda ya aikata. But I didn't force his hands. Shi yayi making decision din dauka da kansa. And that's what took him to prison bani ba".
"Yanzu na dawo gurinki Diyam. Ina neman aurenki bisa yardarki. Yes, nasan shekaru sunja ba lallai ne kina da feelings for me a yanzu ba. Amma ina so ki fada min abinda yake ranki, in kika karbi offer ta ta aure I will surely be the happiest man on earth, in kuma kika ki karba I will be heart broken maybe fiye ma da wancan karon but I will respect your wish. Bazan matsa miki ba ba kuma zan bari a matsa miki ba".
Ina jiran amsar ki.