Wata matace ke 'kokarin shigowa asibitin hannunta rike da kati ta kusa yin tuntu'be da Wasila dake durkushe tana rike cikinta......Da sauri tace"A'a ya kuke zaune anan ko ba haihuwa za tayi ba."? Rashida ta goge hawaye tace"Ba haihuwa zatayi ba Daga scanning muke shine ta kasa tafiya cikinta ne ke ciwo." matar tace"To maza kamata muje wancan rumfar ai nan kan hanya ce."Rashida ta kama hannunta ta dora kafadarta matar ta riko kugunta suka mikar da ita tsaye.......Horn din da ake zabgawa ne ya sanya matar juyawa a fusace tace"Mutane babu uziri shikkenan dan kana cikin abin hawa na 'kasa bai da 'yanci sai ai ta zabga masa horn mtsss! ta karashe maganar tana tsaki hade da dan matsawa motar ta kunno kai cikin asibitin.........Hafsa dake draving ta dan juyo tana kallonsu, sai kawai idanunta suka saukan Wasila tana sunkuyar da kai hade da rintse idonta.....Da sauri ta samu guri tayi parking ta fito.....Zeey dake kusa da tace"Ki shiga ki fito ni inanan." Tace"Zeey fito dan Allah Wasila ce matar governor ina tsammanin bata da lafiya fito da sauri." Zeey tai saurin bude motar ta fito......Suna karasa inda suke Hafsa tace"Sannu Wasila baki da lafiya ne."? Jin muryar Hafsa yasa tayi gaggawar dago kanta tana kallonta, a hankali ta lumshe ido bakinta ya bushe 'kamas! ta d'aga mata kai.....Hankali a tashe Hafsa ta kalli Rashida dake share kwalla tace"Kunga likita? kuma meke damunta dan da kagani tana cikin matsala sosai." Rashida tace"Munga likita har yace taje tai scanning to daga dawowarmu ne sai kuma jikin ya rikice." Hafsa tace"Muga scanning din." Ta mika mata da sauri ta bude tana dubawa....Da sauri ta dago tana kallon wasilan Ciki! mamaki takeyi sosai lallai babu yanda Allah baya tsara lamarinshi......Tace"Zeey dan Allah ku kamo ta keda Kanwarta ta muje." Wayarta tayi gaggawar fito dashi ta soma kiran 'kawarta dake asibin mai suna Aliya likita ce ta mata, tace"Aliya ganin nan na shigo asibitin ku amma ina tare da mara lafiya." Aliya tace"Okey ku shigo ofis dinmu ina shirye shiryn tashi ma dan dai kawai kince zaki shigo ne." Tace''Gamunan." Har da ita gurin rirrike Wasilan suka mikar da ita tsaye.......Sai me suna fara tafiya jini ya soma zirarowa daga kafafunta.....Salati suka sa Rashida ta dinga kuka tana rirrike wasilan da fadin"Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un." A gaggauce Aliya ta karaso gurin, a take sukayi gaggawar dora wasila kan wani keke kai tsaye dakin 'yan 'bari Aliya tace a nufa da ita.....Hafsa Rashida hankalinsu yayi masifar tashi.....Hannu na kyarma ta kira wayar Khalifa ta shiga shaida masa halin da ake ciki....Lokacin ma yana hanyar zuwa gidan abokin nashi dan haka kawai sai ya juya akalar motarsho zuwa asibitin
Kasancewar sun tari al'amarin da gaggawa ya sanya suka samu nasarar tsayar da zubar jinin dake barazana ga d'an tayin dake kwance a mahaifarta.....Sistar Aliya ta fito daga room din tana cire safar hannunta, ofis dinta ta nufa nan ta tarar dasu sunyi jugum! ta zauna tare da zare glass din idonta, Hafsa tace"Allah yasa dai cikin nan bai zube ba dan wallahi zubar jinin nan ya tsoratani." Sistar Aliya tace"Ciki nan daram! ammafa Allah ne kawai ya kare wallahi dan saura kadan ya zube dan dai munyi gaggawar tarar abun ne da tuni sai da labari." Hafsa da Rashida suka sauke ajiyar zuciya suna hamdala....Sistar Aliya tace" Ammafa samun kwanciyar hankali shine dole sai anyi mata daurin mahaifa domin mahaifarta na saurin budewa, ko tana aiki karfi ne."? Da sauri Rashida ta girgiza kanta, Sistar Aliya tace"Tun bayan sati uku da suka gabata mahaifarta ta bude sakamakon aiki ko duguwar tafiya mai tsayi Allah ne kawai ya tsare wannan cikin ni nayi mamaki wallahi." Hafsa tace"Naji dadi sosai kawata babu damuwa za'ayi komai indai cikin zai zauna ka kira Abban Afnan yanzu zan shigo.
Aliya tace"Wai ya kuke da itane naga duk kin tashi hankalinki.'' Tace"Matar Abokin Abban Afnan ce muna shiri da ita sosai." Aliya tace"Okey naji kince Khalifa zai zo ina mijinta." Tayi saurin fad'in "Yayi tafiya ai kuma amanarta na hannun khalifa kinga dole ya kula da ita." Aliya tace"Dole kuwa tunda shi aka bawa amanarta....Scanning din take dubawa tana girgiza kanta tace" Gashi cikin yayi kwari wata uku da sati biyu." Hafsa ta shiga tunani, Eh tabbas hakan zata iya faruwa tunda satittikan cikin yayi dai-dai da lokacin auransu.
Khalifa ne ya shigo cikin asibitin, ya kira wayar matarshi, ta fito daga ofis din Aliya ta masa jagora har dakin da Wasila ke kwance ita kadai ce ba a dakin babu kowa tayi zuru zuru da ita sai nadamar rayuwa takeyi lallai 'yaya mata na cikin hadarin rayuwa idan suna da ciki, wahalar da ta shiga dazu ta bata tsoro tayi tunanin ma mutuwa zatayi dan lokacin da taga jini ya soma zuba daga jikinta hankalinta yayi masifar tashi......Shigowar khalifa dakin ya sanya ta sunkuyar da kanta kwalla na taruwa a idonta....Khalifa ya karasa bakin gadon zuciyarsa duk ta karye tausayi kawai yaran suke bashi, A nutse sistar Aliya tayi mishi bayani tace" Tana jiran Dr Alfindiki ya fito zasu shiga da ita teatar room domin ayi mata aiki, bai wani tsaya dogon tunani ba ya sanya hannunshi ya kuma bada umarin a daure mata mahaifar duk domin samun zaman lafiyar cikin dake kokarin zubewa.
Rashida ta tinga share hawaye Hafsa na rarrashinta, Ita kuwa Wasila idanunta bushewa sukayi 'kamas! hausawa sukace da wata wuyar ai gwara wata ita yanzu wace irin wahalace bata sha ba shiyasa sam bata damu ba tana ganin Allah ne mai rayawa da kashewa.
Cikin nasara akayi mata aiki aka fitowa da ita dakin da suke sistar Aliya tace ta zauna ta huta tukkuna sai sai su tafi gida amma kuma ta kafa mata sharad'ai sosai kan dole ta kula da kanta babu aikace akaice da zurga zurga sannan kuma ta daina zama da yunwa ta kuma nemi magunguna na karin jini."
Bayan fitar Aliya daga dakin, Khalifa ya dinga tausarta yana bata hakuri kana yace tunda haka ta kasance cewar tana da cikin Ahamdu to lallai zaiyi mishi bayani domin ya sani....Tace"Ni dai bana so ka fada mishi don Allah ka bari duk ranar da Allah ya saukeni lafiya sai ya sani amma bana so yanzu ya san inda ciki a tare dani.....Khalifa yace."Hujjarki zaki fada min da kike cewa bakya so ya sani? mutum da abinshi, ai ya zama dole ma ya sani idan sanadiyar cikin yasa ya mayar dake dakinki dama haka muke so." Tace"Bana son haka nafi so kowa Allah ya hadashi da dai-dai dashi dama kaddarar wannan cikin ne Allah ya hadani dashi duk sanda na haife shi kuma zai bashi abinshi." Khalifa ya girgiza kanshi yana kallon tsananin wauta da rashin wayo a tare da ita.
Hafsa da kanta ta fita bakin asibiti ta shiga wani kanti da suke siyar da dogwayen riguna da hijab ta siyo mata riga kala biyu da hijab biyu sai pants da audiga.......Zeey sai jin haushi takeyi tana ganin duk 'yar uwar tata ta 'bata musu lokaci gurin wata shashashar da basu da hadi da ita taji zafi sosai dan ganin yanda Hafsan ke ta rawar jiki kan Wasilan.......Jikinta babu kwari suka fito daga dakin....Khalifa ya bude musu motarshi suka shiga, duk gabad'ayansu....Yaja motar suka fita daga asibitin
Har cikin gidan ya shiga da motar, Uwani ta fito ta tsaya dama yini tayi cikin fargaba da tashin hankali ganin 'yayan nata sun fita tun safe amma yanzu gashi har karfe shida na yamma basu dawo ba dalili kenan da ya sanya hankalinta tashi.......Fitowar Wasila daga motar yasa ta fuskanci da akwai matsala, sai dai tayi kokarin kar'bar su khalifa hannu biyu suka shiga cikin gidan
Khalifa ya shaida mata shi din abokin Ahamdu ne ya kuma shaida mata abinda ya faru da Wasilar shine dalilin da ya sanya ma suka dade basu dawo ba, Sai kawai ta tsinci kanta da yi masa godiya har muryarta na rawa, wato ita tanan sake da baki 'yarta zata mutu akan titi lallai akwai mutanan arziki a duniya.......Khalifa ya shaida mata abinda Dr Aliya tace dangane da ita Wasilan dole sai an kiyaye an kuma sa ido, har sai sanda cikin yayi kwari tukkuna....Uwani tace"Insha Allahu za'a kiyaye....Yace."Insha Allahu zan sanar da Abokina abinda ke faruwa mybe ma gobe mu shigo dashi ko da daddare nasan yaji labarin cikin nan zai bukaci sanin abinda ke faruwa....Uwani tace E hakan nada kyau sosai dan muma munyi wannan maganar kuma munje can gidan nashi domin mu shaida masa sai da bamu sami ganinsa haka muka dawo gida." Khalifa yace."In sha Allah zai zo da kafafunshi kar ku damu...Kudi ya basu kimanin dubu ashirin yace su rike a hannunsu tukkuna, kana ya mike Hafsa dw zeey ma suka mike suna musu sallama, Wasila da kyar ta mike tsaye domin rakasu, godiya kawai takeyi dan ta rasa ma da wace kalma za tayi amfani lallai yau taga ranar d'an adam Khalifa da matarshi nada hali irin na mutanan arziki.
Tun a cikin mota Khalifa da Hafsa suke mamaki ikon Allah kenan! Hafsa tace"Shiyasa ba ba'a saurin yin saki komai 'bacin ran da mutum yake ciki kafin ya yanke hukunci ya samu nutsuwa, ko ni anan gurin naga wautar governor wallahi duk dai komai kaga ya faru da mutum kaddara ce amma dai rashin hakuri shike jawo wani abun, yarinya karama da ko 2years bata cika ba take fuskantar kalubale irin wannan Allah Abban Afnan da ba dan zuwana asibitin nan da sai da cikin nan ya zube in ba wani tsananin rabon ba." Khalifa yace."Tun yaushe nake nuna masa gaskiya ya'ki fahinta kin sanshi fa taurin kai gareshi sai abu ya kwabe yazo yana nadama ni wallahi na yarda da tuban yarinyar nan bana haufi a kanta kuma ina masa sha'awar ya mai da dakinta tunda dai har rabo ya shiga tsakaninsu.........Tace"Aikuwa dai amma ina jin idan yaji labarin tana da dauke da cikinsa zai sauko zai kuma so ya dawo da ita duk domin cikin jikinta."
Khalifa da Hafsa har suka isa gida suna zancan Cikin wasila da yanda ta basu tausayi Zeey kam dama tun a hanya ta sauka tace zataje gidansu friend dinta sai suka sauketa ta samu abun hawa ranta a 'bace! sosai take kishin Wasila da ita da abinda ke cikinta.
Duk rashin imani irin na Uwani sai da ta tausayawa 'yar tata ta dinga rarrashinta taci abinci tasha magani sai ta kwanta, Wasila ta dinga mamaki ashe Uwani dama nayi mata irin wannan son, taji kwalla ta taru a idonta, tana so ta faranta ran uwarta da 'yar uwarta amma babu hali Kudi suna suke magana, gashi kuma ita tayi al'kawarin barin harkar dake kawo mata kudin da suke jin dad'i.
Bayan sallah isha'i Khalifa na shirin zuwa gidan Abokin nashi motar shi ta shigo gidan......bayan motar ta tsaya Garba yay gaggawar bude masa motar ya fito....Khalifa ya karasa gurinshi tare da mika masa hannu yana fad'in "Fitowar nan da nayi, nayi ta ne da niyar zuwa gidanka sai gaka kazo.'' Yace." Okey Allah yasa alkairi ne zai kawo ka." Khalifa yace."Idan kaji ana alkairi d'aya kenan muje ciki." Suka jera a tare suna tafiya domin shiga cikin gidan kai kana kallon yanda suke mu'amula kasan abokai ne masu tsananin zumunci da kaunar junansu.
Littafin na kudi ne......!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys
*56*
Hafsa ta gansu sun shigo tare sai ta saki fuskarta sosai tana dariya tace"Sannu da zuwa gwara da Allah bai sa ka bawa mijina wahala ba kazo dama bana so ya fita ya barni ni kaina a gida naji dadin zuwanka." Ya danji wani iri da jin maganar Hafsa!wato shine mara galihu kenan wanda bai da mata mai tattalin sa yana yawo da daddare babu me cewa dan me.''?
Kan kujera ya zauna yana jan kafafun Afnan dake kwance kan kujerar tana kokarin yin barci, jin muryarshi yasa ta bude idonta a hankali ta shige jikinshi tana fadin "Dadyna yaushe kazo ina Aunty Amaryata."? Rungume ta yay yana shafa kanta yace." Baby Afnan iya rigima baki bacci ba."? Kai ta daga mishi tana lumshe idonta....Hafsa tace"Yanzu nan ta gama rigima ai ta gaji ta kwanta tana son yin bacci 'kiriniya da fitina a gurin Afnan sai a hankali."
Dan hararata yay yace."Ke waye yasan abinda kikayi kina yarinya gwara nata me sauki ne." Hafsa tasa dariya tare da wucewa daining tana fad'in "Governor da Afnan kenan ai fada a shirya." Shima dariyar yake yana shafa kan Afanan din yana lallabata tayi bacci.
Khalifa ya zauna kusa dashi yana me cire halar kanshi da fad'in"Yau na sha zurga zurga Wallahi da tun safe ban zauna ba."
Yace."Shiyasa nayi ta tsammanin shigowarka naji shiru kasan dai maganar nan ba zata yiwu ta waya dole sai mun tattuna akai , Alhaji Danliti ya matsa min da kiran waya kan dole sai mun bashi rancen kudi har miliyan saba'in wai zai shigo da kaya, kudinshi sun yanke kasan sam bana son mu'amula dashi saboda bai da dad'in sha'ani."
Khalifa yace."Mu aje maganar Alhji 'Danliti a gefe guda ni muhimiyyar magana ce nake tafe da ita." Ahamdu ya kalleshi a nutse yace."To ina sauraranka."
Khalifa ya dan gyara zamanshi sosai ya mai da hankalin sa kan abokin nashi ya bude bakinsa a nutse yace."Shin kasan matarka da ka saki tana dauka da cikin ka har na tsayin watanni uku da sati biyu."
Yaji wani irin shocking a jikinshi ya zubawa khalifa yana kallonshi yana so yayi mishi 'karin bayani. Khalifa ya gyara fuskarsa sosai alamun maganar da zaiyi mai muhimanci ce Yace."Wasila na da ciki kamar yanda kaji na fada maka da farko, Dazu ina kan hanya ta ta zuwa gidanka Hafsa ta kira ni a waya kan cewa inyi gaggawar zuwa babban asibitin murtala dake cikin gari ga abinda ke faruwa, dalili kenan da ya sanya kaji ni shiru banzo ba............Khalifa ya shiga warware masa abunda ya faru da Wasilan da irin sirad'in da ta tsallake dashi kanshi cikin jikinta da yake cikin wasiwasi da 'kila wa 'kala ya kuma tabbatar masa da cewar mutukar ana so cikin ya inganta a kuma haifeshi cikin salama da nutsuwa da kwanciyar hankali tilas yarinyar ta samu kulawa mai kyau sannan ne za'a samu dukanin abinda ake so."
Tunda Khalifa yake maganar yake jin wani iri a jikinshi, ya shiga lissafin watannin cikin dai dai lokacin auransu ne dan a hasashen sa ma yana zargin haduwarsu da yarinyar ta farko ta same shi...........Jikinsa ne yayi sanyi sosai kafatanin hankalinsa ya karkata kan ingantuwar d'anshi da samun xaman lafiyarsa a cikin uwarshi, gabanshi ya dinga faduwa yana addua da godewa Allah da bai sa cikin ya zube a kan hanya ba! Ji yay wani irin gumi na keto masa, Khalifa ya lura abokin nashi ya shiga rud'u da tashin hankali sai ya dafa kafad'arshi a nutse yace."Yanzu wace shawara ka yanke dangane da yarinyar dashi babyn dake cikin cikinta." ? Ya dan kalli Khalifa cikin yanayi na damuwa yace."Nama rasa me zanyi wallahi Khalifa nagode kwarai da gaske Allah ya bar abota da zumunci mai amfani yanzu idan da babu kai mybe da tuni na rasa gudan jinina, bana haufi kan cikin yarinyar nan nawa ne Khalifa nasan lokacin da nayi abina." Khalifa yace."Haba babu komai wallahi ni da kai yanzu 'yan uwane mun wuce a kira mu abokai duk abinda nayi maka kaina nayi wa, ina tambayar ka matakin da zaka dauka dangane da yarinyar da abinda ke cikinta babu shakka dukaninsu suna bukatar kulawa mai kyau.......Yace."Khalifa kasan dai halina idan nayi magana kan abu ko kuma na yanke hukunci kan abu bana ta'ba barin abu daga baya in waiwayeshi, amma tunda haka ta kasance Zan sakata gida in killace ta sannan in hada mata komai na jin dadin rayuwa ta zauna ta cigaba da kula min da yaro na har sanda Allah zai sa ta haife mun abuna.....Idan ta haihu in taga zata shayar dashi ok idan taga bata da ra'ayin hakan zan nemi mai raino insha Allah amma bana ji sanadiyar wannan yaro ko yarinya na cigaba da zaman aure da ita.
Khalifa bai so jin haka da gareshi ba amma bashi da magana dama kuma yayi al'kawari kancwa ya bar cewa dashi ya mai da yarinyar, yasan duk sanda ya gane mahimancin ta a gurinsa zai dawo yana neman shawararshi, Sai kawai yace."Shikkenan hakan yayi dan gaskiya na fahimci akwai matsatsi da rashin sukuni da rashin abinci mai kyau a tare da ita da Mahaifiyarta da yar uwarta ina ganin idan anyi hakan zasu samu sakewa sosai kai kuma zaka samu lada kuma dan Allah ko bayan ta haihu ka kar'bi d'anka ko 'yarka to ka bar musu gidan da komai na ciki su zauna sada'katuljariya zaka samu lada."
Yace."Khalifa a yanzu yarinyar nan zan iya yi mata komai albarkacin gudan jinana da take dauke dashi kasan ni idan nayi kyauta bana waiwaye saboda haka bayan gida ma ni mai iya mallaka musu wani abun ne kar ka damu da wannan." Khalifa ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Hafsa dake karasowa inda suke......Ta zauna kusa da mijinta a hankali kai da ka gani kasan itama tana cikin damuwa, Wai shin Shi governor wane irin mutum ne? ace ayi ta abu d'aya haba ai yaci ace ya hakura ya dawo da yarinyar nan, ta lura kamar ma ya fiso yayi ta zama a haka babu aure da shekarunsa da komai shiyasa mutane ke masa kallon mara lafiya da sauransu. Irin abinda take ta fad'a kenan cikin ranta........Ya d'an kalli agogon hannunshi shifa da ba dan dare yaja ba da ya dauki khalifa sunje ya gano yarinyar nan ba wai dan ita zaije ba a'a dan abinda ke cikinta cikin fargaba yake sosai yana ganin kafin gari ya wace cikin zai iya zubewa...... Babu zato khalifa yaji yace."Tashi muje nagano yarinyar nan."
Khalifa ya kalleshi cikin mamaki yace."Yanzu da daran nan dubi time fa sha d'aya shaura." Ya d'anja tsaki yana mutsika goshinsa yace."Gabad'aya hankalina ya kasa kwanciya Khalifa ina jin a jikina kafin safiya cikin nan na iya zubewa ko wani abu ya faru, nasan mutukar banje na ganota ba ba zan iya rintsawa ba." Khalifa ya dinga kallonshi yana jijjiga kai yace."Shin wai ita kake son gani ko kuma abinda take dauke dashi."? Da sauri yace."No ni abinda ke cikin cikinta nake son gani ba wai ita ba meye gamina da ita." Khalifa yayi wani murmushin takaici yace."To ina me tabbatar maka da cewar ko kaje yanzu wahalar banza xakayi dan nasan tayi bacci kuma ka'idar masu lalurar ciki ba'a tashinsu daga bacci, kuma kana maganar ba dan ita zakaje ba to shi cikin naka in kaje ganinsa zakayi ido da ido ko kuwa zaka ce ta d'aga maka riga ne ka gani."? Ya shiga kallon Khalifa yana me nazarin maganarshi, Ya akayi kwakwalwarshi ta toshe ne? shifa a tunaninsa idan yaje yace ta bud'e masa riga yaga d'anshi! sai kuma yanzu maganar Khalifa ta sanya ya hango kuskuransa, yanzu dai babu aure a tsakaninsa da yarinyar nan yasan ko yaje bashi da hurumin rike mata koda d'an tsaya ballanta yace ta bud'e masa riga yaga d'ansa
Gumi ya shiga karyo masa ya ciro hankici yana gogewa ranshi sai 'kuna yake yi yarinyar nan tayi bala'in cutarsa yasan kuma yanzu shi da kwanciyar hankali har sai yaga d'anshi a hannunshi tukkuna
Khalifa yace."Hakuri za kayi gobe idan Allah ya kaimu sai mu je da wuri ku gaisa kasan kuma ko kaje babu ruwanka da ita tunda ba muharramarka bace." Sai yaji kamar ya kwad'awa Khalifa mari da jin maganar da ya fad'a Yaja karamin tsaki yana me mikewa tsaye da fad'in "Allah ya kaimu goben zan shigo da wuri muje, kuma a goben nake son sauya musu gurin zama duk domin samun nutsuwa da kwanciyar hankalina inaji a jikina mahaifiyar yarinyar nan zata iya zubar min da ciki koda kuwa ita yarinyar bata so." Khalifa yace."Kai kake wannan hasashen amma a dazu munyi magana da mahaifitar yarinyar ta tabbatar min da cewar kwanaki sunzo har gida domin su shaida maka abinda ke faruwa basu sami ganinka ba kaga kuwa idan hakane to bata da hannu gurin zubewar cikin ka." Yayi shiru yana nazarin khalifan kafin ya kad'a kanshi yana fad'in"Koma dai menene ni bazan ta'ba aminta dasu ba tunda sun shani na warke Allah ya kaimu goben kawai." yana gama maganarshi ya nufi hanyar fita, Khalifan ya mike yabi bayanshi.....Hafsa kam dama tuntuni tayi shigewarta d'akin Governor bai ta'ba 'bata mata rai irin yau ba mutum sai kace fir'auna zuciya kullum babu kyau ace kayi ta ri'kon mutum a ranka.
Yanda yaga dare haka yaga rana ya kwana yana juye juye da zumud'in son gari ya waye duk domin zuwa ganin gudan jininshi dake kwance cikin mahaifar Wasila......Asubar fari ya mike ya shiga toilet wanka ya soma yi kana ya dauro alwala ya fito ya shirya tsaf ya nufi masjid, ya kasance mutum na farko bayan liman da ya fara isa masalacin, sai ya zauna cikin nutsuwa ya fara jan carbi kafin liman ya tada sallah.
Misalin 'karfe takwas sun shirya tsaf! sun fito da jakkunansu, da duk abinda suka san nasu ne a cikin gidan, suka fito tare Uwani da Rashida suke jan akwatinan kayansu yayin da Wasila ke bin bayansu cikin sanyin jikinta, wani irin yanayi mara dad'i takeji a cikin zuciyarta.....Bakin gate suka nufa, Wasila ta fito da keys din gidan ta mi'kawa d'aya daga cikin masu gadi tace"Idan As yazo su bashi. masu gadin gidan kamar zasuyi magana sai kuma sukaja bakinsu sukayi shiru suna kallonsu suka fice daga gidan da akwatinan kayansu.......A jigaje ta 'karisa bakin babban titi dan wannan tafiyar da sukayi ya sanya ta haki! dan har sai da suka samu guri suka zauna ta huta tukkuna kafin su cigaba da tafiya.......Babur din a dai-dai sahu suka samu ya daukeshi zuwa tashar kabuga.
"Wai wannan wane irin wulakanci ne ? na shigo gidanka tun safe ka shanya ni a palo sai kace yaronka ina ta fama zaman jiranka kai kana can kanayin abinda ya dameka, idan ba zaka fito ba zanyi tafiyata ba wai ban san gidan bane."!!! Ahamdu yake waya da khalifa lokacin da yake kai komo a tsakiyar palon nashi......Khalifa ya fito daga bedroom d'insu kunnanshi ma'kale da waya yayin da Hafsa ke biye da bayansa hannunta rike da turare da kuma hularshi tana gyarawa.
Ahamadu ya dinga watsa musu harara kamar idonsa zai fad'o 'kas! Yace." Ga d'an iska kun bari yana muku jiran gida kun shigo ciki wai me yasa bakwa gajiya da abu guda ne."!! A zafafe yake maganar......Hafaa ta gumtse dariya kanta a 'kas tana sanyawa mijin nata links din hannunshi tace"Allah ya huce zuciyar governor ba wai abinda kake tunani muke ba, lokacin da kazo gidan bamu dad'e da tashi ba shiyasa."
Ya maka mata harara yace."Ke kika san wannan ni a gurina karfe shida na safe ba safiya bace lokacin duk wani me himma yake tashi domin gudanar da harkokinsa na yau da gobe ke kuma a lokacin kike sake ma'kalewa wai ke gaki wacce ta iya soyayya."
Khalifa yace."Wai meye laifina nan ne? tayi fa 'kokari sosai kawai kazo mata gida da asuba kuma kace sai kaga yanda kake so ba zai yuwu ba lokacin da kazo ma ni ko tashi banyi ba wayarka ce ta tasheni." Yace." Dan Allah ni muje dubi time kun 'batawa mutane lokaci mtsss!. Duk suka bishi da kallo cikin mamaki masifa yake musu sai kace sune suka sashi ya aikata abinda ya aikata shine kuma zai zo ya d'aga musu hankali basuji ba basu gani ba...
A mota ma sai mita yakewa Khalifa, wanda tun baya ramawa har ya shiga ramawa ya dinga yi masa shagu'be duk domin ya fahimci cewar shifa d'an taimako dan haka ba zai zo ya dinga d'aga mishi hankali ba idan yana so ya cigaba da samun nutsuwa da kwanciyar hankali to yayi gaggawar dawo da iyalinshi gabansa, To
wannan magana da khalifa yayi itace ta kashe masa baki yayi shiru sai dai jefe jefi yakan ja tsaki ya duba agogon dake daure a hannunsa.
Dai-dai gate din gidan khalifa yay parking ya shiga horn da sauri daya da sauri mai gadi ya bude gate din dan duk sun dauka As ne sai bayan motar ta shiga cikin gidan ne suka gane cewar bashi bane..........Shine ya fara fitowa kafin Khalifan ya fito.......Dake masu gadin biyu ne daya sai ya tsaya bakin gate din daya kuma ya nufi in da suke....Gaishesu ya shiga yi yana so yayi magana amma be san me zaice ba yaso dai ya shaida fuskokinsu mussaman Khalifa da shine yayi zuwan karshe cikin gidan.......Shine ya fara yin gaba da nufin shiga cikin gidan sosai Kafin Khalifa yace."Ka d'an dakata na kira wayarsu naji ko." Dan tsayawa yayi yana ya mutsa fuska, Khalifa ya kira numbar wayar Rashida dan itace me waya kuma numbar ta ya kar'ba, Wayar na hannunta tayi saurin d'agawa tana kara wayar a kunnanta lokacin suna tsakiyar tasha suna ciku cikun hawa mota........Tayi ta fadin "hello " hello "hello network da hayaniya sun hanata jin muryar Khalifa inda shi kuma nashi 'bangaran yana jin muryar ta rad'au! sai dai dik inda take tana cikin hayaniyar jama'a da ababen hawa! Fad'i yake " Rashida kina jina? kina jina." Da karshe ma sai wayar ta tsinke yay gaggwar cirota daga kunnanshi yana dubawa.....Mai gadin dake tsaye yace."Yallabai mutanan gidan fa basa nan dan tun sassafe suka fita da akwatinan kayansu da alama sunyi balaguro ne."! Ya wani juyo a sukwane! yana kallon gate man d'in bakinsa na motsi......Mai gadin yace."Amma dai ina kyautata zaton yanzu basu isa tasha ba ko sun isa baici ace sun tashi ba tunda kasan dole kafin mota ta tashi sai tayi lodi sai dai kuma muma bamu san inda suka nufa ba."
Jikinsa ya soma wani irin rawa! yana kyarma! kafafunsa suka shiga kyarma Cikin tsawa da d'aga mirya Yace ."Wane irin wawanta ne wannan!? Wane irin sakarci da hauka ne yasa zaku barsu su fita! meye amfaninku a gidan!? waye ya basu izinin fita da jakkunan kayansu!? ina kuma suka tafi? Ina zasuje! min da gudan jinana? sai muryarshi ta shiga rawa yana wa tsawa masu gadin mugun kallo babu marasa tunani da kwakwalwa kamarsu da har suka barsu suka fita daga gidan sun riga sun cutar dashi mutukar sukayi sanadiyar zubewar cikinsa dama tun jiya yake ji ajikinsa akwai abinda zai faru, Ya kalli khalifa yana tsuma!!! Yace." Ko ina suka nufa sai na lalubosu! dan basu isa su yanke min
wannan hukuncin ba, kawai ka shiga mota muje." Yana maganar ne a sanda yake nufar motar tasu cikin gaggawa da kuma saurin gaske ya bude motar ya shiga
khalifan dake tsaye cikin mamaki! ya rasa ma tunanin da zaiyi ashe wasila bata da hankali dama? tanajin abinda likita tace dangane da lafiyarta da babynta amma zata dauki jiki suyi tafiya mai nisa cikin mota mai kwajab kwagab! babu sakarkaru sai masu gadin gidan da suka barsu suka fita daga gidan........Da saurin gaske yabi bayan abokin nashi ya shiga motar da gaggawa ya mayar da murfin ya rufe Ahamdun yaja motar da karfin gaske, ya nufi kofar fita daga gidan cikin sauri wanda yake bakin gate din ya matsa gefe guda yana zazzare idonsa.
Littafin na kudi ne......!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap Numbar
*07084653262*[14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys
*57*
Zaman motar ne ya isheta ta dinga ya mutse fuskarta tana dan tsartar da yawu ta tagar motar kanta ne ke sarawa tana jin wani irin amai na taso mata, hayaniya ta mutane duk ta cika mata kunne ga warin fetur da tsamin hammatar wata mata dake kusa da ita d'aga rigarta ta fito da nono ko kunya ba taji tana shayar da yaronta alhalin motar da akwai maza a cikinta, haushin matar ya sanya ta dinga dauke kanta tana jan tsaki wasu matan sam babu kintsi da kamun kai cikin motar haya mai dauke da mazan da ba muharraman ta ta fito da nono kowa nagani gashi da ta motsa warin hammatar ta zai buga......Mutum biyu kacal ake jira motar ta tashi Wasila duk ta kosa su tafi ko ta sha'ki iska mai dad'i bayan warin hammatar matar ma mazan dake ciki wasun sy wari sukeyi abinka da wanda rana ta daka....Uwani da rashida kam hira sukeyi suna cin awara da suka siya kafin su shiga motar...Kira ya shigo wayar rashida dake kan cinyarta. Da sauri ta kalli Wasila dake zura kanta tagar motar tana shakar iska tace"Anti Wasila kinga Khalifanan ya sake kira." Tace"Ki daga mana to." Rashida ta d'aga wayar tare da fad'in "Hello." Khalifa dake driving yay sauri mika mishi wayar ya kar'ba da sauri yana kokarin kara wayar a kunnensa ta fad'i 'kasan site sakamakon rawar da hannunsa yake yi....Kasancewar wayar ta bugu da karfi yasa ta mutu ya dauko da sauri ya kunna ta bude, ya lalubi numbar yana sake kira, A dai-dai lokacin ne kuma wasu matasa suka shigo motar direban motar ya Umarci rashida ta gyara sosai domin su samu gurin zama garin gyarawa wayar dake cinyarta ta fad'i kasan motar ba tare da ta sani ba....Aikuwa shi wanda zai zauna kusa da ita ya sanya hannunsa ya dafe ta, a take yay dubarar cire sim din lokacin da Rashidan ta juya suna magana da Wasila ya jefa wayar karkashin kayanshi, Rashida matsatsi da xafin mota ya sanya ta manta da wayarta burinta kawai su tashi saboda zafin ya isa.....Aikuwa sai da direba ya cika motarsa tsaf sannan ya shiga ya zauna maxauninsa ya tashi motar suka fita daga cikin tashar suka dauki hanya
Abin kamar al'mara kiran wayar yake ana ce masa a kashe take, ya kira ya kai sau ashirin maganar dai daya ce wayar a kashe take! Ya d'ago kanshi yana wata irin zufa bakinsa na rawa yace."Khalifa wai meke faruwa ne? Wayar nan fa ta'ki shiga kana ji da kunnanka a kashe take Why! Wad'annan yaran naso su sanya zuciyata ta buga!!!!!!! Khalifa tsorona Allah tsorona Annabi kar cikin nan ya zube, ko a samu wata matsalar nasa raina akanshi."Ya 'kareshe maganar cikin rauni da sarewa da al'amarin.
Sosai ya bawa Khalifa tausayi yace."Ni ina tunanin network ne matsalar Amma kar ka damu abokina insha Allah cikin nan ba zai samu matsala ba muje tashar kabuga insha Allah xamu samesu idan ma motarsu ta tashi ai mun san inda suka nufa kai tsaye sai mu wuce can garkon ni da kaina zanyi wa mai allo bayanin komai."
Hularshi ya cire ya ciro hankici ya goge fuskarshi da saman kanshi, Yana jin wata irin fargaba na kamashi yanzu da wane ido zai kalli mai allo to me ma zaice masa idan sunje? Yace"Khalifa bani da wani bayani da zan iya yiwa mutumin nan saboda ina jin kunya wallahi in ce masa saboda d'ana ko 'yata dake cin Wasilan zan dauketa kasan da akwai nauyi." Khalifa yace."Kar ka damu zanyi mishi bayani."
Ya shiga girgiza kanshi yana fad'in "Kamar nasan abinda zai faru shiyasa jiya nace maka muje inda suke da yanzu duk hakan bata faru." Khalifa yace."Ni nayi mamaki wallahi saboda jiya lafiyar Allah muka rabu dasu ko da wasa basu shaida min cewar zasu tafi wani gurin ba amma basu kyauta ba wallahi kuma Wasila tayi wautar gaske."
Girgixa kanshi kawai yake yana adduar Allah yasa su samesu a tasha don shi kam yana bala'in jin kunyar had'a ido da mai allo.
Khalifa ne kawai ya iya fitowa daga motar bayan shigarsu tashar ya kutsa cikin mutane direbobin motoci yana dube duben motocin mutane, ko kusa ko alama bai hango koda kyallin mayafin wata daga cikinsu ba, haka ya gaji ya nufi inda motar su ke fake.....Shi kuwa uban gayyar tamkar wani zautacce ko kuma mara kunne yana ri'ke da waya a hannunshi sai kiran numbar Rashida yake tamkar mai kunnan 'kashi ko kuma kurma yana jin abinda matar nan ke fad'a masa cewar wayar a kashe take amma ya kasa daina kiran wayar.......Ganin Khalifa ya doso motar tasu cikin sanyi jiki ya sanya shi rarraba ido yana jiran karasowarsa...
Khalifa yace."Babu fa alamun yaran nan cikin tashar nan kawai shiga mota muje." Jiki a mace ya bud'e mota ya shiga duk yayi wani laushi kamar mara lafiya....Khalifa yaja motar suka fita daga tashar duk rayukansu babu dad'i.......Sai da suka hau kwalta sosai kana ya sauke numfashi yana huci! yace."Khalifa Allah banta'ba ganin sukuwar uwa irin uwar wad'annan yaran ba, ni yanzu ma ita nake jin haushi wallahi." Khalifa yace."Gaskiya tayi wauta itama data d'auki yarinyar nan da wannan lalurar suka dauki hanya bayan sai da na fad'a mata dokar da likita ta kafa kan 'yar tata shiyasa wallahi mace komai shekarunta watarana ta tafka maka wani abun haushin sai kaji kamar ka d'ora hannunka akanka.
Yace."Nifa babu ruwana Allah cikina ya samu wata matsala sai na dauki mataki kanta da ita da uwar tata." Khalifa yace."Ai kaji irinta wai kai me yasa kake hakane? Matar nan fa ta tabbatar min da cewar sunzo har gidanka da maganar cikin basu samu damar ganinka ba suka hakura suka koma kan me yasa za kaga laifinta anan bayan tayi kokarin ganin an fita hakkina."
Tsaki! yay yaja bakinsa yayi shiru yana muzurai! da ya tuno wani abu sai gabanshi ya fad'i! gaskiya yana bala'in son cikin nan nashi a yanzu ji yake zai iya hakura da komai na rayuwa mutukar cikinsa zai tsira.
Tafiya suke mota na gwajab gwajab yayinda ciwon ciki da mara ya tsananta a gareta ta! ta dinga sunkuyar da kanta tana zufa da kiran sunan Allah gumi ko ta ina d'iga yake a jikinta, tsabar yanda take jin jiki sunan Allah kawai take kira tana jin wani irin imani na ziryartar ta anya kuwa wannan cikin bashi ne ajalinta ba? abinda take fad'a kenan cikin zuciyarta.
Sun isa garin Garko Lafiya sai da kuma lokacin mai allo ya jima da fita tsangaya, Tanimu ne yay musu jagora har makarantar tashi.....Mai allo na tsakiyar al'majiransa ya hango zuwansu sai ya mike a nutse yana fara'a yana musu barka da zuwa......Cikin wata rumfar kwano da babu kowa a jiki suka nufa. Ma allo da kanshi ya karkade musu tabarma suka zauna sai aka shiga gaishe gaishe, Ahamdu sai sunkuyar da kanshi yake duk kunya ta dabaibayeshi sai yanzu yake jin kunyar dattajon yaga shi kuwa sai fara'a yake yana tambayarsa gida da harkokin yau da kullum. Khalifa yace."Alhamudllhi malam komai na tafiya yanda akeso sai da aita tayamu da addua." Mai allo yace."Addua munanan munayi har sai da numfashin mu ya dauke."
Khalifa ya ja gwaron numfashi kafin ya gyara zamanshi a nutse yace."Allah shi gafarta malam dama mun biyo sahun yaran nan ne wato ina nufin Wasila da 'kanwarta da kuma mahaifiyarsu, domin muji shin sun iso lafiya! sannan kuma muna da tabbacin cewa nan suka nufo dalili basu da wani gurin in ba nan d'in ba, Allah shi gafarta malam babu maganar rufe rufe cikin maganar nan Yarinyar nan Wasila na dauke da ciki har na tsayin watanni uku da satika kuma akwai matsala mai girma tattare da ita da d'an dake jikinta wannan shine babban dalilin ma da ya sanya shi Abokin nawa yace."Lallai ilallah sai munzo domin mu tabbar da zuwan nasu cikin 'koshin lafiya."
Mai allo ya dinga kallon Khalifa cikin mamaki da kad'uwa ya d'an gyara zamanshi kafin yace."To Idan na fahimci inda maganarka ta dosa anan shine kana so ka sanar dani cewar kun biyo sahun su Wasila domin kuna tunani ko nan suka zo kamar yanda ka fad'a hakane ko? Khalifa yace."Hake Malam." Mai allo yace."To a gaskiya ni dai har na fito daga gida banga zuwansu amma ban sani ba ko bayan na fito suka iso bari nasa yaro yaje ya duba a gida." Ya mike ya fita daga inda suke.
Ahamdu ya kalli Khalifa cikin sarewa da tsananin damuwa yace."Anya Khalifa anya yaran nan suna nan kuwa? jikina na bani ba nan suka zo ba." Khalifa yace."Ka dai bari tukkuna mybe bayan ya fito daga gidan suka sauka garin kamar yanda ya fad'a d'in in banda abinka idan ba nan suka zo ina zasuje da yafi nan d'in." Yay shiru yana jin wata irin zufa na karyo masa, mikewa yay ya fito daga rumfar kwanon ya kama kallon hanya sai kace wani zautacce ga rana sai kwalle masa ido take.
****
Misalin 'Karfe biyu da rabi na rana suka sauka garin Fataskum, bayan sun sauka daga mota Uwani ta dinga rarraba ido tana dube dube hanya dan garin gabad'aya ya sauya mata yau kusan shekaru goma sha biyu da rabonta da garin, tin tana goyon Rashida lokacin Yahuza na dan da mutuwa tunda tayi wannan zuwan bata sake waiwayar garin ba, dama mutum hud'u ne suka rage musu a dangi Babban yayansu mahaifiyarta da suke kira da Kawu Madu sai Mai binshi Kawu Isa sai kuma Iya mai waina da Tabawa dama su biyar iyayensu suka haifa mahaifiyarta itace ta uku ita ke bin Kawu Isa sai Iya mai waina sai kuma Tabawa! Mahaifiyarta itace kawai tayi aure a wani gari, amma dukaninsu cikin garin Fatskum suke tare da iyalinsu mutukar sun fita daka garin to sunje wani garin ziyara.....Tun bayan rasuwar mahaifiyar Uwani Kawu yaso daukarta domin su dinga kallonta a matsayin 'yar uwarsu, mahaifinta ya'ki lamince masa haka suka hakura suka bar mishi 'yarshi, gashi bashi da cikakkiyar lafiya shima a lokacin ya hana a tafi da itane domin ya dinga kallonta tana d'ebe masa kewar mahaifiyarta.......Sai da cutar ajali ta kamashi ne 'kaninshi ya daukeshi ya kaishi gidanshi dake akwai shago a wajen gidan nan ya ajeshi yake kula dashi, to shine fa tun daga lokacin Uwani ta soma shan wahalar rayuwa gidan Kawun nata har mahaifinta ya kwanta dama, a lokacin ta 'kara shiga tsaka mai wuya ga wuya ga maraici ga tsananin azabah! Saboda zalinci irin na Kawun ya siyar mata da gidan da ya zama gadonta ya sanya kudin a aljihunsa ya cinye matansa na zugashi da fad'in Ai idan yaci Allah ba zai tuhume shi ba tunda dai shima yana ciyar da ita...........Sai da sukayi aure da Ayuba ya jagorance da kanshi sukaje can Fatsukum din dangin mahaifiyarta da kwatance, to tun daga sannan ta gane hanya........Saboda matsatsi da talauci da kuma rashin kudin mota ya sanya bata zuwa garin a kai a kai, sai ta dauki shekaru masu yawa kafin taje to wannan karon dai shekarun data dauka ba taje ba sun fi na baya.......Da tambaya suka iske gidan Kawu Madu dake shi d'in ba 'boyayyen mutum bane a garin yasa basu sha wahala ba,
Suna zaune kan katuwar tabarma shida abokanansa gabansu katon farantin silba ne jere da kwanuka, da jug jug na ruwa da alama abinci suke shirin ci ya hangosu, Sai ya shiga wasiwasi da tunani to sai da suka iso inda suke ya tabbatar da cewa su d'in ne Yace."Uwani ko ba ita bace."? Tace."Nice Kawu."! Sai ya washe bakinsa yana fad'in "Kece kike tafe da ranar nan babu shakka yau an tuna damu kenan gaki ga zuriarki lallai yau patskum nada manya 'baki sannuku da zuwa." Mi'kewa yay yana 'kwalawa yaran dake wasan langa langa a 'kofar gidanshi kira.....Suka rugu a guje yace."Maza ku kwashi kayan nan ku shida dasu gida.....Yaran suka dinga ihu! suna fad'in "Yeeee! munyi 'baki daga birni da gudu suka runtuma cikin gidan suna jan akwatinan kayan nasu
****
Can ya hango yaron da aka tura gidan ya fito daga wata hanya yaji tamkar yaje ya tareshi ya tambayeshi, sai dai kawai ya daure ya bi yaron da kallo har ya isa inda mai allo yake ya tsuguna yana masa magana." mai allo ya Umarceshi da ya koma gurin zamanshi kana ya mike daga kan kujerarshi Ya nufo inda yake tsaye babu yabo babu fallasa a tare dashi, tun kafin ya karasa inda Ahamdun yake ya hango damuwa da tashin hankali a tare dashi, sosai ya shiga mamaki yana tunanin to bayan rabuwarsu ya mayar da ita ne har ta samu cikin ko kuma bayan ta fito daga gidan cikin ya bayyana ? babu me bashi amsa sai su ya sauke ajiyar zuciya lokacin da ya karasa inda yake a nutse yace."Alhaji mu shiga ciki sai muyi maganar." Ga yanayin yanda mai allo ke masa magana yasa ya fahimci akwai damuwa, jikinsa babu kuzari ya juya yana tafiya me allo ya bi bayanshi.
Mai allo ya zauna kan tabarma yana kallon Ahamdu A nutse ya soma magana kamar haka
"Yau shekaru takwas kenan rabon da Wasila da 'yar uwarta Rashida su tako 'kafarsu garinan! shiyasa nayi mamaki mutuka! a lokacin da kuka zo min da wannan maganar, amma kuma banyi muku musu ba saboda nasan hakan zata iya kasancewa tunda muma kullum cikin tunanin zuwansu muke nasan duk tsiya yarinyar bata da wasu iyaye sai mu, kuma nasan dole watarana zata kawo kanta inda muke duk kuwa da tsananin 'kiyayyar da suke mana ita da 'yar uwarta......Ni da 'Yan uwana da sauran dangi kullum cikin saurare muke da kallon hanya muna jiran tsammanin zuwansu garinan, tun bayan rabuwar auranka da ita muka yanke shawara kancewa mun dauke hannunmu da kansu gabakid'aya wanda har 'Dan uwana Habibu da ya fusata yace. Duk ranar da suka shigo garinan to sai ya koresu ni ne na hanashi nace mutukar sunzo inda muke to zamu kar'be su hannu biyu amma idan basu nemi in da muke ba to zamu kyalesu da halinsu da kuma mahaifiyarsu, to a gaskiya ni nafi gazgata zaton cewar Yaran nan sun bi bayan mahaifiyarsu can garinsu." Mai allo ya 'karashe maganarshi yana so ya tabbatar musu da gaskiyar lamari......Khalifa ne kawai ya iya magana Yace. "Allah shi gafarta malam ko zamu iya sanin garin su mahaifiyar tasu."? Mai allo yayi shiru yana d'an tunani kafin yace." Wallahi sunan garin ya kwanta min a raina, tun da kasan can d'in ba nan ne inda cibiyar mahaifinta yake ba, shi kanshi 'kanina Yahuza a hannun Kawunta ya aureta amma dai na ta'ba ji sau d'aya 'kanin nawa ya ambaci sunan garin har yace watarana zai daukeni ya kaini mu gaisa da danginta to kuma sai Allah ya dauki abinshi.
Khalifa da gogan naku bakinsu ya mutu murus! Saboda dukaninsu sun rasa tudun dafawa sun ma rasa wane tunani zasuyi shin yanzu ina zasu samu yaran nan? Su dun tunaninsu babu inda suka dashi sai nan dan suna tunanin itama Uwanin a nan take ashe ba haka bane! Gashi gurin wanda suke tunanin samun cikkaken bayani shima yace bai ma sannan sunan garin da suka nufa ba........Innalilihi wa'ina ilaihi raji'un!
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys
*58*
Cike da farin ciki da walwala ya shiga gidan nashi yana kwalawa matarshi kira..........Kuluwa ta fito daga wani guri wanda alamu suka nuna cewar madafi ne (khicin) hannunta da wata katuwar mara da alama kwasar towo take, tace"Malam ganin nan Allah yasa lafiya irin wannan kira hak.....Kafin ta rufe bakinta sai idanunta ya sauka kansu Uwani da 'yayanta, lokacin 'kan'kani ta kirne fuska tana fad'in "A'a yau kuma Uwani ce a garin."? Uwani dasu Wasila duk sunga sauyin fuska a tare da ita, lokacin da take maganar da alama dai batayi maraba da zuwan su garin ba.......Kawu Madu yana washe hakoransa yace." Wallahi kau nima nayi mamaki sosai dan baki ji dadin da nakeji ba, abinci zamuci dasu malam tsalha na taso domun in shigo dasu gidan." Kuluwa tace"To sannunku da zuwa ku shigo ciki." Kawu Madu yace."Uwani ku shiga ciki a baku abinci ku huta ai da alama ma kun kwaso rana." Uwani tace"Aikuwa wallahi munsha zaman mota da gajiya." Kawu Madu ya juya ya fita yana fad'in "Bari nasa Ayuba yaje can cikin kasuwa ya siyo muku ruwan sanyi."
Uwani da Rashida suka shiga daukan jakkunansu dake yashe a tsakar gidan suka nufi dakin Kuluwa, suna shiga katuwar rumfa ce sai dai babu shinfida a cikinta sai guntattakin tabarmi da ledoji ko ina kaca kaci da kwari ka 'kananin kyankyasai ga wani uban 'kuda da yake tashi a rumfar da wani kafirin zarnin fitsarin yara......Tun lokacin da suka shiga rumfar Wasila ke yatsine ya tsinen fuska zuciya sai masifar tashi takeyi aikuwa kafin tayi wani yun'kuri amai ya kece mata! a guje! tayi waje ta nemi bakin rariya ta tsuguna ta dinga kelayashi tana kwallah......Rashida ce tsaye a kanta tana mata sannu duk ta shiga damuwa. Bayan ta gama aman ta bata ruwa ta wanke bakinta da fuskarta kana ta mike jiri na d'ibarta......Rashida ta rike hannunta wai su koma cikin d'akin girgiza kanta tayi da kyar tace"Rashida rabu dani don Allah zuciya tashi takeyi idan na koma gurin nan zan iya yin wani aman." Aikuwa karaf a kunnan Kuluwa ta rike baki tana fad'in "Ke ja'ira yarinyar me kike nufi? daga zuwa zaki fara yiwa mutane sanabe da iyayi kina nufin kazama ce ni kome." Rashida tayi saurin girgiza kanta tana fad'in "Ba haka take nufi ba baba." Kuluwa tace"To me take nufi da har zata shiga dakina ta rugu waje da gudu tana kwara amai." Rashida tace "bata da lafiya ne dama tun a mota cikin ta ke ciwo." Kuluwa ta girgiza kanta tana fad'in "Maji ma gani dai idan tusa zata hura wuta, kome kuke tafe dashi dai-dai nake daku to kaji."! Tana gama maganar ta ta shige madafi domin cigaba da aikinta.
Uwani na cikin dakin abin duniya yayi mata yawa, tunani takeyi yanzu wace irin rayuwa zasuyi cikin gidanan! tun da can baya tasan Kuluwa macace mara mutunci da muguwar kaxanta sam bata so kowa yazo inda take tabi ta asirce Kawu Madu sai abinda tace yayi yake ji shima wani lokacin tsoranta yake yi, Ta dinga tunanin irin wuyar da zasu sha ita da 'yayanta a gidan dan ga dukanin alamu Kuluwa ba tayi maraba da zuwansu ba, tunani take ko su tafi gidan Kawu Isa ne? sai ta tuno shi kuma ai bai da gidan kanshi haya yake kuma daki guda ne suke gamutsuwa dashi da matarshi da 'yayanshi.....Iya mai waina kuma ba ita kadai bace a gidanta tana da kishiyoyi kuma babu wadataccen gurin zama, dole dai gidan Kawu Madu din shine gurin zamansu, Kwallace ta taru a kwarmin idanunta tayi saurin gogewa, lokaci guda duniya ta juya musu baya, sun fara d'and'anar jin dadin rayuwa kuma sun koma gidan jiya............Sai a lokacin nadama mara amfani ta kamata ta dinga tunanin abubuwan da suka dinga faruwa a baya da irin kud'ad'en da 'yarta ta rike da samun nasarar auran Ahamdu tayi, Yanzu ne ta gane auran Ahamdu da 'yarta shine rufin asirinsu tasan da Wasilan na gidanshi har yanzu da tuni basu shiga wannan gararanbar ba.
Kuluwa ta shigo dakin hannunta rike da wata katuwar langa tana kallon Uwani tace"Naga kamar kema kina cikin alhini da damuwa to Allah yasa dai ba abin kunya kukayi a can ba kuka gudo nan dan naga alamun ciki a tattare da waccan 'yar taki."
Uwani ta kalleta ranta ya 'baci da maganarta amma saboda sanin halinta yasa tace"Eh kuluwa ki daina shakka ko kokwanto Wasila na da ciki amma kuma da Ubanshi."
Kuluwa ta ta'be bakinta tana fad'in "To yanzu naji zance Allah ya rabasu lafiya sai ki kira su kuci abinci gashinan babu yawa dai aci da hakuri tunda ban san da zuwanku ba." Uwani tace"To mungode." Kuluwa ta fita daga dakin, tana gyara daurin zaninta wanda yayi da'kal! da'kal da daud'a!
Uwani ta le'ko tana kiransu Wasila dake zaune jikin bishiyar darbejiya dake gidan.........Rashida da kyar ta lalla'bata suka koma dakin....suna shiga ta fito da sauri tana fad'in "Rashida ba zan iya ba wallahi mutuwa zanyi zuciyata tashi takeyi." Karaf a kunnan Kuluwa cikin fusata tace"Ke! buhun ubanki nace! Buhun ubanki kaji min shegiyar yarinya ciki haukane da zaki zo min gida kina min iskanci! har ki dinga cewa zuciyarki tashi takeyi to bari malam ya shigo wallahi kinji na rantse ba zaki zauna min a gida ni ba'a kawo min iskanci ehe! dama ai baku bane tilashin mu ita Uwanin itace tilas dinmu dan haka sai ku koma inda kuka fito abin arziki baya zama na tsiya." Takarashe maganar tana kumfar baki kai daka ganinta a fusace take! Uwani ta fito daga daki tana bata hakuri saboda tasan halin ta zata iya cewa su Wasilan baza su zauna a gidan ba kamar yanda ta fad'a, Hakuri take bata tana karyar dai muryarta sai rawa take! Kuluwa ta cigaba da aikinta tana sababi! da zagin Wasila
Uwani ta dauko langar abinci ta dire a gabansu tana fad'in " Ku kiyaye da wannan matar idan kuna son zaman lafiya bana son abinda kikeyi Wasila kinga bamu da gatan da yafi nan, Kuluwa macace mara hakuri zata iya sa Kawu yace ku bar mishi gida kamar yanda ta fad'a saboda haka duk abinda zakiji na tashin zuciya ki dinga daurewa kina hakuri haka take muguwar kazama ce tun tana da kuruciyarta gashi har girmanta......Wasila bata iya magana ba rashida ce mai magana tace"Gaskiya Uwani gidan nan baiyi wallahi duba fa ki gani ko ina kazanta da kashin dabbobi dubi bandaki babu kofa sai buhu kiji warin masai dake tasowa har nan kawai mu zamu tafi Garko ke kiyi zamanki nan tunda kece tasu."
Uwani ta marairaice fuskarta muryarta na rawa tace"Rashida kin san yanda nake son ku kuwa ? bana so kuyi nesa dani shiyasa na'ki aure na 'kare rayuwata tare daku, ina 'kaunarku saboda nasan bani da kowa sama daku, Uwata ta mutu Ubana ya mutu mijina ya mutu sai ku kawai nake kallo naji dadi idan kuka tafi Garko kuka barni wace irin rayuwa kuke tunanin zanyi a cikin garin nan."!?
Tausayin mahaifiyar tasu ne ya kama su, sai suka hau goge hawaye, suna adduar Allah ya kawo musu dauki da gaggawa amma hak'ikanin gaskiya mahaifiyar tasu tasha wuyar rayuwa ta kuma yi wahala dasu bai kamata su guje mata ba,
Zama tayi kusa dasu tana bud'e langar abincin aikuwa sai wani irin towon dawa ba'ki'kikirin yayi musu sallama! towon sai shaining yake ga wata uwar miya kamar fitsarin jaka, sai wake guda guda a cikin miyar tana ta warin daddawa......A guje Wasila ta mike ta nufi bakin rariya ta dinga kakarin amai tana zubar da kwalla! Kuluwa tayi azamar fitowa daga kicin da ludayi a hannunta....Wannan karon Uwani da kanta taje ta rirrik'e 'yar tata tana mata sannu ita kuwa sai rike ciki take tana mur'kususu da kiran sunan Allah! Kuluwa ta dinga kallonsu bakin cikin duniya kamar ya kasheta 'Kwafa tayi ta koma kicin din! Yau ba gobe ba zasu bar mata gidanta dan bata ciki da iskanci da wulakanci......Kawu Madu ya shigo gidan yana sa'be babbar riga sai kawai ya gansu cirko cirko Uwani da Rashida kan Wasila dake durkushe tana kakari......Yace."A'a Uwani meke faruwa ne Me yasa me ta take amai haka."? Kafin Uwani tace wani abu Kuluwa tayi zuruf ta fito daga kicin fuskarta a murtuke tace" 'Kyankyamina takeyi shine take amai tunda suka shigo gidanan basu shiga dakina ba can bakin bishiya suka zauna saboda suna kyankyamina saboda haka yau ba gobe ba zasu bar min gidana dan wallahi ba zan dauki wannan iskancin ba." A take Kawu Madu ya sha kunnu yana kallonsu rai a bace yace."Ashe baku da tarbiya dama? matar tawa kuke 'kyankyami!? to shikkenan dama ai baku ne tilas dina ba Mahaifitarku ce saboda haka zaku bar min gidana tunda baku da mutunci." Uwani ta shiga share hawaye tana fad'in "Kawu ba haka bane wallahi yarinyar nan nada ciki mai laulayi yana bata wuya dama tun a mota take amai har yanzu ba wai suna 'kyankyamin Kuluwa bane."
Yace."Uwani."! ta amsa yace."Shin yaushe kikayi wa yarinyar ki aure babu labari gashi nace tana da ciki."! Kuluwa tace"Nifa malam ban yarda ba wallahi wannan yarinya cikin shege tayi shine suka kwaso jiki suka gudo nan sabida gudun abin kunya dan haka wallahi ba'a gidan nan ba idan kuma kace tilas sai sun zauna to ni zan fice na baku guri."
Hankalin Kawu Madu ya tashi, Yace."A'a ba za'ayi hakaba Kuluwa ai duk wannan magana ma bata taso ba, ke Uwani zo ki zauna kiyi min bayanin abinda ke faruwa."
Uwani ta bishi kan tabarma suka zauna tare Kuluwa ta 'karaso gurin hannunta rike da ludayi ta zauna kujera 'yar tsugo tana fad'in "Eh ai gwara muji bayanin komai domin mu samu kwanciyar hankali." Uwani ta share hawaye a hankali ta soma warwarewa masa abubuwan da suka faru da rayuwarta ita da 'yayanta komai bata rage masa ba sai da ta fad'a mishi......Kuluwa tace"Duniya kenan yanzu ke Uwani bakiji kunya ba, wato lokacin da kuka samu kudi kuka samu dad'in duniya baki tuna damu ba sai da wahala ta taso ki sannan zaki tuna damu ki kwaso jiki ra'be ra'be da 'yaya kizo ki d'ora mana nauyi to ba zata ta sa'bu ba! Mu ba zamu dauki nauyin ki kuma mu d'auki nauyin 'yayanko ba, Dan haka gobe gobe yaran nan zasu bar gidanan suje can dangin mahaifinsu tunda suna raye, kema abinda yasa ba zamu kore ki ba saboda mun san ko kinje can gidan Kawunki ba zai kar'be ki ba saboda haka ke kad'ai zamu ri'ke saboda kece tamu."
Kawu Madu yace."Kwarai kuwa Kuluwa wannan magana taki gaskiya ce, Yaran nan baxa su zauna mana a gida ba sabida bamu da hakki a kansu dan haka kamar yanda kika fada hakane kwana guda zasuyi su bar mana gida suje can cibiyarsu.........Uwani ta dinga kuka tana fad'in "Haba Kawu ku duba al'amarin fa kada kuyi min haka bani da kowa sai 'yayana bani da uwa da uba bani da miji sai 'yayana su nake gani naji sanyi a raina." Kuluwa tace"To ai tunda hukuncin da muka yanke bai miki ba to sai ki bi 'yayan naki haba! wannan 'kulafucin son 'yaya dame yayi kama.'' Ta mike tana jan tsaki ta shiga dakinta.....Kawu Madu ma ya mike yana fad'in "Na fad'a miki Uwani na yanke hukunci Kuluwa ta yanke hukunci saboda haka shawara ta rage gareki." Ya buge babbar rigarsa ya 'kara gaba.
Wasila da Rashida kam! basu ciwo ba dalili dama sunfi son su tafi can garkon shiyasa sukaji dadin hukuncin da Kawu madu ya yanke a kansu amma basu nunawa mahaifiyar tasu ba, sai suka shiga kwantar mata da hankali da fad'in ko sun tafi insha Allahu zasu dinga zuwa a kai akai suna dubata.....Uwani dai jinsu kawai takeyi abin duniya ya taru yayi mata yawa bata ta'ba nadamar rayuwa ba irin yau.
Kuluwa ta dinga shige da fice a tsakar gidan tana sakin 'ba'kaken maganganu wanda ya sanya jikin Uwani yi sanyi taji a zuciyarta gwara kawai su Wasila su bar gidan dan ba zata iya jurar rashin mutuncin kulawa tana aibata mata yara da kiransu karuwai watarana tana ganin zata iya mayar mata da martani kan maganar da takeyi, ta dinga jin wani irin d'aci! da bakin ciki a raina ashe haka abun yake da ciwo a duk sanda aka danganta d'anka da wannan suna (karuwai) gaskiya ta gode Allah da ya bata 'yaya masu hankali da hange nesa tasan da bada hakan ba da tuni sunanan da kuluwa ke kiransu dashi ya tabbata tunda ita da kanta ta dinga turasu karuwancin, tagode Allah da yasa wannan cikin dake jikin Wasila ta sameshi ta hanyar halak ba haram ba.
Kuluwa na ganin irin tsarabar da suka kawo sai ta hau washe bakinta ta dauki turmin atamfofi irin na leda guda biyu tace wannan ni zan d'inka in sa a jikina wannan yadin kuma na malam ne, sauran kuma Iya mai waina da Tabawa su kasafta a tsakaninsu." Su dai kallonta kawai sukeyi duk tabi ta kwashe kayan ta shige dakinta dasu sai murna takeyi ko Kawun ma bata nunawa ba.
Sai dare suka samu suka sanya abinci a cikinsu shima abincin Inna Tabawa ce ta kawo musu cikin katuwar Samira shinkfa da wake ne da manya da wani uban yaji da yaji gishiri da citta! haka suka cuccusa dan gwarashi kan narkeken towon dawan da Kuluwa ta kawo musu, Wasila dai kad'an taci tasha maganinta ta nemi gefenan tabarma ta kwanta tana mai da nuffashin wahala.............Duhu sosai gidan babu wadatacciyar fitala sauro da kwari ka sukayi sallama! Wasila ta gigice ta dinga soshe soshe kukan sauro duk ya cika mata kunne! Uwani tace "Ku tashi mu koma daki mu kwanta kunga mutanan gidan sun shige sai mu kadai a tsakar gida ga sauro." Rashida tace "Yanzu cikin wannan kazantar zamu mu kwanta ga yara nasan suna fitsarin kwance." Uwani tace"To ya zakuyi ai da zama cikin sauron nan gwara cikin rumfar." Wasila tace"Uwani ku shiga ku ku barni anan Rashida ki dauko min zanin atamfa cikin kayanmu in rufe jikina." Uwani tace"Akwai fa damuwa kwanciyar ki anan." Tagoge kwallah tace"Uwani nan yafi min kan in shiga dakin nan inzo ina kakarin amai da daddare d'an abincin da naci ya dawo, kuma wannan matar tazo tana miki masifa."
A sanyaye Uwani tace"Shikkenan ai." Ta mike a hankali ta shiga dakin rashida tabi bayanta......Nan su kaga yara birjik a rumfar ko wanne ya wargaje kafafunshi wasu sun soma sakin fitsari abinsu sai barci suke.....Uwani ta ra'ba can wata kusurwa ta karkad'e wani buhu ta shimfida ita kuma rashida ta nufi dakin Kuluwa dan jakkunan kayan nasu na cikin dakin........Nan ta tarar da Kuluwa ta bude musu kaya sai bunkice takeyi musu, tana ganin rashida sai ta diriri ce ta hau ya'ke...."Am...dama ai nace bari na gyara muku kayan naku in adana muku su guru guda." abinda tace kenan tana sosa kanta....Rashida bata ce komai ta dauki zannuwa uku na atamfa ta fito daga dakin....Ita kuluwa tana ganin rashida ta fita daga dakin sai ta cigaba da bincika kayan ta dauko manya manyan shaddodin Wasila masu uban stone work ta d'aga 'kasan katifarta ta sanya ta mai da katifar......Da sauri ta gyara jakkunan kayan ta fito daga dakin tana zare ido.
Wasila kudindine jikinta tayi. ita kadai kwal a katon tsakar gidan ko tsoro bataji gari yayi shiru sai kukan tsintsaye kawai ke tashi.......... Cikin ikon Allah bacci mai nauyi ya dauketa ta dalilin magungunan da takesha
Fitowar Kawu Madu daga dakinsa ne ya tayar da ita Sai taji ana kiran sallah da alama asuba tayi, Kawu Madu ya kalleta yana mamaki yace." Ke anan kika kwanta." Sunkuyar da kanta tayi kawai sai ya girgiza kanshi ya nufi bandaki da buta a hannunsa........Yana fitowa ya daura alwala ya nufi masalaci,
Kasa shiga bandakin tayi sai kawai tayi gaggwar tsugunawa a bakin rariyar tayi fitsarinta ta kwara ruwa, kana ta matsa gefe guda ta daura alwala ta bar gurin.
Shimfidar data kwanta ta dauke ta cire dankwalin kanta ta gyara hijab dinta ta tada sallah......Uwani da rashida suka fito a tare suma alwalar suka daura nan tsakar gidan sukayi sallah domin dai cikin rumfar babu guri bayan haka kuma ko ina kasa 'kafarka fitsari ne.
Suna zaune a tsakar gidan gari yayi haske Kuluwa ta fito tayi alwala ta goge bakinta da gawayi kana ta shiga kichin ta kunna wuta ta dora ruwan kunu sannan ta nufi daki domin yin sallah.
ၥYaran dake dakin suka soma fitowa su kusan bakwai wasu jikinsu da fitsari wasu babu ba tare da sunyi alwala ba suka soma wasa a tsakar gidan wasu kuma tuni sun fice waje da abubuwan wasan su......Su Wasila suka dinga mamakin wannan rayuwa....Nan rashida take shaida musu abinda taga kuluwa nayi musu da kayansu....Fitowarta yasa tayi saurin yin shiru to itama Kuluwar a kunyance take dan haka sai tayi saurin fadawa kichin tana sosa kai! Wasila abin dariya ya bata sai ta shiga girgiza kai tana fad'in ''Ni dariya ma take bani wallahi." Rashida tayi dariya kasa kasa tana kallon kicin din.
Wani tsalan kunu ta kawo musu cikin kwanon sha da kufuna guda uku sai 'kullin sikari akai....Uwani ta gaisheta tanayi mata sannu suma suka gaisheta Ita kuwa ta kasa tsayawa a gurin kunyar hada ido da rashida take......Tana shiga kicin Wasila ta saka fuskarta cikin hijab taci dariyarta ta koshi, kai mara gaskiya dai ko a ruwa gumi yake.
Fitowa tayi daga kicin din da katon farantin silba da narkeken d'umamen towo an yanyanka shi sai miya tsululu towon sai iyo yake cikin miyar....Ta kalli rashida tana fad'in 'kawata ga d'umame nan idan kunsha kunun sai kuci kwaji dad'in tafiya da karfinku." Rashida tace"Mungode Kuluwa." Da sauri ta bar gurin tana kwalawa yaranta kira wai suzo su dauki kununsu da duk ta zuba musu a kufuna 'kudaje sai bin bakin kufunan sukeyi.....aikuwa da d'ai- da d'ai yaran suka dinga shigowa suna daukar kufonan kunun suna sha ba tare da sun wanke bakinsu ba.
Kawu Madu ne ya shigo da sauri yana fad'in "Ina Wasila da Rashida." Sukace gamu Kawu Yace." To maza ku fito ga motar abokina ya kawo ice yanzu zai fita cikin gari sai yaje ku a tasha ku shiga mota." Suka mike da sauri Rashida ta shiga dakin domin dauko musu jakar kayansu, dama tasu daya ce ta uwani daya.
Uwani ta mike tana yakar zuciyarta hawaye ne yake so ya 'balle mata tana mayar dashi, suka je bakin kichin din da Kuluwa ke ciki tana zaune dirshan gabanta da karon bokintin da ta dama kunu tana katsewa gefanta kuma tukunyar miya ca bude ga ludayi a kasa....Uwani tace"Zasu tafi." Sai ta hau washe baki tana fadin"Bari na taso inyi rakiya ni kuwa me zan baku. 'Yayan nan."? Fitowa tay ta shiga dakinta da sauri ta dauko wata yar takarda fara ta mikawa rashida tana fad'in 'Kawata ga yariruka kwa sanya ku gaishe da kawunan naku." Rashida ta karba tana godiya tabi bayan Wasila da Uwani da suka riga sukayi gaba.
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*59*
Tun a mota yake jin alamun zazzabi zazzabi a jikinsa yasan kuma ba komai ne ya jawo mishi faruwar hakan ba sai alhini da damuwar da yake ciki idanunsa sun kad'a sunyi jawur! jijiyar kanshi ma ta tashi, yanda le'bunanshi suke a bushe haka ma'kogwaron shi yake dan rabonshi da ruwa ko abinci tun jiya da daddare da yasha coffee kafin ya kwanta, sam ya ma manta da wani abinci saboda tsananin damuwar da yake ciki....Yana kallon khalifa na tu'ki yana kur'bar lemo amma shi sha'awa ma baya bashi bakinsa duk ya bushe yana jin wani irin abu ya tokare masa a ma'kogwaronsa.
Ganin tashin hankali murarar a tartare da abokin nasa yasa ya d'an kalleshi bayan yayi parking din motar cikin gidanshi, Yace."Kayi hakuri abinda zan iya cewa da kai kenan! ka cigaba da addua kawai kan Allah ya tsare maka cikinka da ita kanta yarinyar wannan damuwar duk ba ita mafita ba, tunda dai Allah ya raba ganawa sai ka bar mishi ikonshi, ni munyi magana da ita a jiya ta kuma shaida min cewar mutukar ta haihu to zata kawo ma'ka d'anka har inda kake." Saurin kallonsa yayi yace."Okey ashe da sa hannunka ta gudu kenan." ? Khalifa yay saurin girgiza kanshi yana fad'in" No ka fahimce ni mana! Jiya nake fad'a mata cewa dole sai na sanar maka da maganar cikin ta nuna bata so nace mata ai tilas ka sai ka sani shine tace ko anfad'a maka ko ba a fad'a maka ba in ta haihu zata kawo maka d'anka kaji dalilin da ya sanya nayi maka wannan maganar amma wai maganar da sanya hannuna a cikin guduwarsu bata taso ba."
Girgixa kanshi ya shiga yi yace."Ban san a ina zanga 'kawarta ba mybe a samu wani labari a gurinta." Khalifa yace."Eh to ai kuma inda za'a sameta ne aiki." Yace."Zan duba wayarta baza'a rasa numbar ta ba." Khalifa yace."Yawwa hakan yayi kyau Allah yasa a dace yanzu dai ka kwantar da hankalinka mu shiga ciki kaci abinci ka huta tukkuna insha Allahu komai zaizo da sauki."
Girgiza kai kawai yay yace."Khalifa hankalina ba zai ta'ba kwanciya ba sai naga yarinyar nan, na 'kwallafa raina kan cikin jikinta burina kawai in ganta kuma in tabbatar lafiyar abinda ke cikinta." Khalifa yace." Shine ai nace damuwa da tashin hankali bashi ne mafita ba addua itace mafita kawai ka kwntar da hankalinka ka cigaba da addua.''
Murmushi mai ciwo yay khalifa bai san yanda yake ji a zuciyarsa ba shiyasa yake cewa ya kwantar da hankalinsa a maganar kwanciyar hankali ta 'kare a gurinsa yanzu mutukar ba ganin yarinyar nan yayi ba. A
Tare suka fito daga motar tamkar wanda 'kwai ya fashe musu a ciki suka nufi cikin gidan. ga gajiya ga rashin samun nasara.
****
Dake akwai tafiyar 'kafa tsakanin bakin titi da cikin 'kauye yasa suka samu babur irin na (kafu-kafu) ya shiga dasu ciki har 'kofar gidan Mai allo aka ajesu, kana suka biyasu hakkinsu.....Suna kokarin shiga gidan ya fito da cazbaha a hannunshi, kawai sai yay tozali dasu. Ya bude baki yana kallonsu cike da mamaki.
Idanun Wasila ya kawo ruwa rau-rau! ranar naka sai naka! Wai itace tazo garin Garko da 'kafafunta! Hawaye suka zubo mata a kumatu, kai a 'kasa suka isa inda yake suka zube gwiwa bibbiyu suna kuka! Tausayinsu ya kamashi da sauri yace."Ku tashi mu shiga ciki.'' Jikinsu a sanyaye suka mi'ke rashida taja akwatin kayan nasu suka bi bayansa.
Kamar dai koda yaushe Bitan na zaune a tsakar gida tsaf da ita jikinta sai kyallin mai yake da alama bata jima da yin wanka ba tana sanye da wani leshi ruwan ganye(kore) irin nada ta d'aure kanta tamau! da dankwalin leshin, cinyar ta farantin shinkafa ne tana tsincewa sai kawai ta tsinkayi muryar mijin nata yayi sallama, Da sauri ta d'ago kanta tana kallon bakin 'kofa, Yanzu yanzu ya fita ko mantuwa yay abinda take ayyana cikin ranta, sai kuma taga su Wasila a bayanshi.
Tace"A'a malam su wa nake gani a bayanka yau.''? Yace."Gasunan nima fita ta na hango zuwan su Wasila ce da Rashida." Bitan! ta ri'ke ha'ba babu yabo babu fallasa a fuskarta tace"To masha Allah sannunku kuzo ku zauna ga gurin zama." Mai allo yace."Kuje ku zauna." Sukaje suka zauna kusa da ita sai sunkuyar da kai suke mussaman Wasila dama itace akuyarta tayi kuka a garin.....Mirya na rawa tace"Kawu ina wu
ni mun sameku lafiya." ? Yana daga tsaye yake amsawa yana nazarinsu....Rashida ma ta gaishi ya amsa, kana suka shiga gaishe da bitan itama ta amsa cikin kulawa kafin ta mike a nutse ta nufi kicin....Mai allo ya dinga kallonsu zuciyarsa na karyewa 'yayan Yahuxa tamkar 'yayan cikinsa suke, duk yanayin da ya gansu na dad'i ko na rashin d'ad'i dole ya shiga damuwa, kallon farko da yay musu ya fahimci akwai damuwa da firgici a tartare dasu mussaman Wasilan da tayi firgai firgai da ita kamar ma mara 'koshin lafiya. Bitan ta fito daga kicin hannunta rike da samira mai hannun roba, ta aje a gabansu ta koma kicin din da sauri ta fito hannunta rike da wani farin jug ta bude randa ta debo musu ruwa ta aje a gabansu ta zauna tana fad'in" Kuci abinci kunji ko ku daina kuka da damuwa rayuwar nan kowa hakuri yake da ita."
Malam yay gyara murya yana kallon matar tashi yace."Zan fita kamar yanda na niyyata idan Allah yasa na dawo sai na zauna dasu, Insha Allah." Bitan tace"To malam ubangiji Allah ya tsare a dawo lafiya." ya amsa yana kokarin fita, Wasila da Rashida har rige rige suke gurin yi masa adduar dawowa lafiya ya amsa musu a lokacin da yake kokarin fita daga gidan.
Bitan taga sun kasa cin abincin tace"Ku saki jikinku fa kuci abinci insha Allahu ba zaku samu wata matsala dani ba, ni dama tuntuni ina tausayawa rayuwarku mutukar kun gane gaskiya kuma kun gana mahimacin Kawunan ku a gurin ku , ai magana ta wuce suma kansu Kawunan naku hankalinsu a tashe yake, amma nasan yanzu hankalinsu zai kwanta tunda kun dawo garesu."
Sai suka sake jin kwarin gwiwa a tare dasu, Rashida ta bude samirar abincin dake gabansu, burabusko ne (biski) yayi shar shar dashi sai kamshin man'kuli zuryan yake, ga maggi star guda biyu a gefe da yaji....Wasila taji yawunta ya tsinke sosai taji sha'awar cin burabuskon ta mike a nutse ta wanko hannunta, ta dawo ta zauna Rashida ma mikewa tayi taje ta wanke hannunta sukayi bisimillah tare da fara cin abincin.
Bitan ta mike a nutse ta shiga kicin ta kunna wuta, Girgi zata dora musu na mussaman, sabida yaran sun bata tausayi sosai da sosai sam basuyi sa'ar uwa ba duk wata wahala da suka shiga mahaifiyarsu itace sila shiyasa kwata kwata basa shiri da ita sabida munanan haleyenta gashi tayi ta zagin mijinta a gabanta, duk abinda za tayi wa yaran za tayi musu ne saboda Allah da kuma maraicinsu, ba dan halin Uwarsu ba..
Tas suka cinye burabuskon basu rage komai ba, Wasila tafi rashida ci dan daga karshe ma rashidan cire hannunta tayi ta bar mata ta 'karasa cinye tayi gatsa tana hamdala hankalinta ya kwanta sosai da tsabtar Bitan shiyasa kome ta girka ta bata zata iya ci......Bitan ta fito daga kicin hannunta rike da wani ma dai-dai cin kwando dafaffan 'kwai ne a ciki da yawa ta aje a gabansu tace ku 'kara da wannan yanzu zansa yara sunyi min cefene na sake dafa muku abinci. "Wasila tayi murmushi tana fad'in " Bitan mungode Allah ya saka miki da alkairi." Murmushi kawai tayi ta koma kicin tana cigaba da aike aikenta.
Hajara ce tayi sallama ta shigo gidan tare da d'an autanta Lamir yana biye a bayanta.......Tsayawa tayi bakin kofa tana kallonsu, Sunkuyar da kai sukayi kamar munafukai. Bitan ta fito daga kicin taganta tsaye a bakin kofa tace"Ki shigo mana ai ba abin mamaki bane addua bata fad'uwa 'kasa banza." Hajara tace"Ai dole nayi mamaki Bitan! Yaushe suka zo kuma."? Bitan tace"Ke dai shigo ki zauna." Hajara ta karasa kan tabarmar ta samu guri ta zauna idanunta a kansu Wasila ta dinga tunano rigimarsu da Hajaran tana shan duka a gurinta a duk lokacin da sukazo garin, dan kwata kwata basa shiri sunfi shiri da Rashida......Cikin jin nauyi suka gaisheta ta amsa tana fad'in "Kunga uwar bari kenan."!? Sukayi 'kus! kansu a 'kasa, Hajara zata fara sababi! Bitan ta dakatar da ita da fad'in " Haba Hajara wannan ba kana bane! Kullum fa addua kuke kan Allah ya karkato da hankalin yaran nan gareku Allah kuma ya amsa adduarku sannan kice wani abu, don Allah kar ki fad'i wata mummunar magana kan yaran nan ki kyalesu ma suji da abinda ya damesu.
Hajara ta fashe da kuka tana fad'in "Haba Bitan! al'amarin nan fa akwai dam
uwa da ba'cin rai wallahi yaran nan sun sanya mu a fargaba da tashin hankali mussaman waccan mai 'katon kan tana sunkuyar da kai munafuka kawai Ai dama nace duk sanda kika kwaso kafafunki kika zo sai na ci miki mutunc.......Bitan tace" Ashe bakiji maganata ba kenan haba hajara."? Hajara ta kwance bakin zaninta ta goge hawayen fuskarta tana fad'in "Allah ya ji'kan ka Yahuza." Ai sai Wasila da Rashida suka sa kuka! Suna bata hakuri! Takaicin duniya ya ishi bitan Hajara tazo ta dagula al'amari ta tayarwa da yara hankali sai koke koke sukeyi......To itama hajaran da taga sun ki su daina kukan sai ta shiga rarrashinmu itama ba yin kanta bane tunawa tayi da d'an uwanta....Rashida da Wasila suka dinga bata hakuri da fad'in "Insha Allahu baxa su sake guje musu ba tunda sun gane basu da kowa a duniya da wuce su......Hajara taji dad'in wannan magana tasu sai tace " Komai ya wuce insha Allahu.
Hajara bata koma gidanta ba har sai da malam mai allo ya dawo suka gana da juna sannan tayi musu sallama ta tafi gidanta da al'kwarin dawowa gobe idan Allah ya kaimu.
Bayan sallahr isha'i mai allo ya samu nutsuwa duk suna zaune a tsakar gida bayan sun gama cin abinci, mai allo ya gyara zamanshi kan buzunsa yana kallonsu a nutse yace."Naji da dadi kuma nayi farin ciki da har kuka gane mahimancinmu a gurinku, yanzu kun gane cewar baku da wani gata a duniya da wuce Allah da ma'aiki da kuma ni da 'yan uwana, Mahaifiyarku ta dauke ku ta kai ku can cikin danginta, sun nuna muku cewar su basu da ala'ka daku , kamar yanda kuka fad'a min cewar da kyar ma suka bari kukayi kwana a guda a gurinsu, ni a ganina ba suyi lefi ba kamar yanda kuke tunani sun nuna muku mahimcin danginku ne, me yasa basu kori ita mahaifiyar taku ba? saboda sun san tasu ce kuma bata da wani guri da za taje idan ba gurinsu ba, naji dadi da faruwar hakan, na kuma tabbatar da cewar hakan zai sake sanyawa ku shiga cikin hankalinku ku gane meye rayuwa, alhamdullhi, Allah ne abin godiya a garun mu baki d'aya." Shuru yayi yana sauke numfashi kafin ya cigaba da magana yana me kallon inda Wasila take zaune, Yace."Jiya mijinki yazo garinan cikin tsananin rud'ani da tashin hankali yana shaida min cewar wai kina dauke da cikinsa a jikinki shin hakane ko ba haka bane? tunda dai ni kafin wannan zuwan nashi wattani uku da suka wuce yazo har nan ya shaida min cewar ya sake ki saki d'aya wanda a lokacin mukayi ta tsammanin zuwanki baki zo ba sai yanzu.
Tun lokacin da mai allo ya firta maganar mijinta yazo taji duk wani kuzari nata ya dauke yawun bakinta ya tsinke gabanta ya shiga fad'uwa da 'karfi da 'karfi sai kawai ta soma fad'in kalmar innalilihi cikin zuciyarta, muryar mai allo ce ta dawo da ita hayyacinta yace."Ke nake sauraro Wasila." Ta d'ago kanta idanunta cike da 'kwalla tace"Eh Kawu in da ciki." Yayi jim! kafin yace."To masha Allahu, yanzu akwai aure a tsakaninku kenan? ko ku kuma bayan rabuwarku dashi cikin ya bayyana kanshi."? Ta goge hawayen dake kuncinta tace"Bayan mun rabu cikin ya fito.'' Shiru yayi yana girgiza kanshi kafin yace."Gaskiya mana, yazo nan hankali a tashe a jiyan ni har na soma tunanin ko da akwai aure a tsakaninku ashe shi saboda cikinsa ya biyo bayanki, to babu lefi ai idan Allah yasa Habibu ya dawo daga tafiya, tunda shine yake da numbar wayarshi sai ya kirashi ya shaida masa abinda ke da akwai, amma maganar zai daukeki ya killace ki kiyi mishi rainon ciki duk bata taso ba, anan ma zaki raini ciki ki kuma haife lafiya ba tare da wata matsala ba insha Allahu, wannan dai hakkinsa ne dole a fad'a mishi halin da kike ciki duk saboda jininsa da kike dauke dashi a jikinki." Kuka tasa tana fad'in "Dan Allah Kawu kar a fad'a masa bana so kawai a bari idan na haihu sai a bashi d'anshi Ni bana so yazo inda nake." malam ya shiga kallonta yana mamakin gursheken kukan da take.
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*60*
Mai allo ya dan gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Kiyi shiru ki kwantar da hankalinki ki daina kuma kuka, sanar dashi ba yana nufin cewa zaki koma gidanshi bane, A'a za sanar mishi ne domin fita hakkinshi, ba wai dan muna neman wani abu a gurinshi ba, yana da kyau ya san cewar har yanzu kina nan dauke da cikin nashi, kuma ya samu nutsuwar zuciyarshi, ni ba zanyi miki dole ba kamar yanda nayi a farko, ba zance tilas ki koma domin ki cigaba da zama dashi ba, zaki zauna ki samu nutsuwar zuciyarki ki haihu lafiya kana ki za'bi namijin da yayi dai-dai da rayuwarki ki aura."
Bitan tace"Wannan magana da kayi itace mai kyau, saboda haka ki daina kuka kuma ki samu nutsuwa da kwanciyar hankali ko dan saboda cikin jikinki insha Allah babu wanda zai miki tilas kan ki koma zama gidan shi tunda bakyaso to Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi." Wasila ta shiga goge hawayenta tana sauke ajiyar zuciya, Bitan ta mike ta nufi wani daki minti biyu ta fito daga dakin hannunta rike da fitilar kwai ta gyara a nutse ta gyara fitilar ta kunna ta koma dakin.....Kimanin minti goma tayi a ciki ta fito tana fad'in "Na gyara muku shimfida sai ku kwanta ku huta mussaman ke Wasila naga alamun gajiya a tare dake kiyi bacci sosai sai ki samu sassauci da nutsuwar zuciya." Suka mike a nutse suka shiga dakin..........Bitan ta zauna kusa da mijinta suka cigaba da tattaunawa dangane da al'amarinsu Wasilan.
Dakin na shimfide da lede sabuwa da lalubewa masu dan kauri sai katifa ma dai-dai ciya mai cin mutum biyu jakar kayanu ajiye a gefe, dakin dai ya ishesu su biyu ba tare da wani ya takurawa wani ba.....Wasila ta cire hijab din jikinta, ta janyo akwatin kayansu tana dubawa kaya mara sa nauyi zafi takeji idan da son samu ne ma ta watsa ruwa, saboda zafin da takeji, Da kyar ta samu wasu riga da wando irin marasa nauyi sosai ta saka a jikinta, ta nemi ta gyara tufkar gashinta, Rashida dake kokarin kwanciya kan katifar tace"Anti Wasila ni kuwa zan baki shawara.'' Ta kalleta tana fad'in "Wace irin shawara."? Rashida ta mi'ke zauna a hankali tace" Dan Allah ki koma gidan Ahamdu wallahi shine marufar asirinki yanzu idan kince wani auran zaki sakeyi to ai baki san wanda zaki aura ba, kin san yanzu auranan zamani nan sai a hankali, amma ni ba tun yau ba nake sha'awar auranki dashi wallahi, kuma idan kin duba kinyi tunani fa za kiga bashi da laifi dangane da abinda ya faru a tsakaninku, ke koma yana da laifi to naki laifin yafi nashi, saboda haka nake baki shawara kan dan Allah idan yazo da niyar mai dake gidanshi ki amince kawai ki koma zakiji dadi muma muji dadi."
Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon 'yar uwar tata tace"Wato Rashida har yanzu kwadayi da hange ne cikin ranki ko? Rashida ta girgixa kanta alamun a'a.......Ta cigaba da cewa''Idan ba kwadayi ba me zai sanya kice min in koma gidanshi? Kince nafi shi laifi Eh na yarda na fishi laifi kuma na amsa laifina amma me yasa lokacin da nayi nadama na nemi afuwarshi bai yafe min ba? lokacin da nake kuka nake neman gafarar shi a lokacin ji nakeyi zan iya zama dashi cikin ko wane hali saboda yayi min hallaci ya kuma yi min abinda ba kowa ne zai iya ba, ni ba nufina a kasheshi ba ko a cutar dashi, amma na lura shi abinda yake zargi kenan......Kinga duk mutumin da yake zarginka hankalinsa ba zai ta'ba kwanciya dani ba, Ni nasan koda na koma gidanshi to koma mu 'kan'kare za'ayi sabida yana zargina, sannan kuma ni bana jurar wulakancin da raini sam mutumin nan baya ganin mahaifiyarmu da daraja da mutunci ban san dalili ba ko dan yana da kudi ne oho! , naji ciwo sosai ranar da kuka zauna a gidanshi keda Uwani ya wulakanta ku, yana da kudi yana ganin babu wanda ya isa! sannan kice na koma gidanshi, ai ko zan koma auranshi sai ya mutunta mahaifiyata, ballanta ma bana sanyawa zuciyata cewar watarana zan koma gidanshi in cigaba da zama a matsayin matarshi, kawai Allah ya hada kowa da dai dai shi."
Rashida tace"Wallahi ba Kwadayi bane ni kawai mutumin yake burgeni yana da kirki da tausayin talakawa kinsan dama ance dan adam tara yake bai cika goma ba, kuma ni a ganina ba wai baya ganin girman u
wani bane kawai dai kinsan wasu masu kudin kuma ranar da mukaje ai bai san cewar mune ba shiyasa, ni daina zan cigaba da tayaki addua kan Allah ya karkato da hankalinsa kanki gaki dauke da cikinsa ai dole ma nayi sha'awar ki koma hannunshi kuji dadin rainon danku." Tsaki taja tana fad'in "Ranki zai 'baci mutukar kika sake yi min wannan banzar maganar."! Rashida tayi shiru tana kallonta.....Mikewa tayi taje ta kwanta tare da rufe kafafunta, maganar rashida tasa duk wani bakin cikin dake damunta ya dawo sabo, dal! ta dinga jan tsaki tana juye juye, hawaye ta share tana sake tuno lokacin da take birgima da ihu a gidanshi tana rirrikeshi ya taimaketa ya hakura ya mai da ita yanayi mata wulakanci, ai wallahi ta bar auranshi mutukar ta cika ita d'in 'yar halak ce........Da kyar bacci ya dauketa mai cike da mafarkai marasa dad'i.
Washe gari da safe da rubutu ta fara karyawa malam mai allo ya fara rubuta mata a'lkur'ani ya Umarceta tayi bisimillah tasha kana ta shafe cikinta dashi, sai da ya tabbatar tayi yanda yace din sannan hankalinshi ya kwanta...........Bayan sun karya ne, sai sukayi wanka, rashida ta taya Bitan gyaran gidan ita kuwa Wasila dama tana yin wanka ta kwanta bacci mai nauyi ya dauketa.
****
Ya tashi cike da rashin walwala da rashin kuzari gabakid'aya duniya tayi mishi zafi ya rasa abinda zaiyi ya samu sassauci, da kyar ya samu ya kur'bi tea kofi daya, yayi kwance kan kuje daga shi sai singlet da wando iya gwiwa, wayarshi yake dubawa, ya bude ma'adanar hotonanshi, ya lalube pictures dinsu yana kallo, ji yayi hankalinsa ya tashi ya mike zaune yana rawar jiki, dan wayar har sai da ta kusa faduwa ya riketa da kyau, ya kurawa fuskar wayar......Da sauri ya mike ya nufi dakinshi, drowars ya shiga budewa nan naga ya fito da Pose dinta da sababbin wayoyin da ya siya mata, zama yayi gefan bed ya kunna wayar yana dubawa, numbobin mutum uku ya gani tashi data As sai kuma wacce yaga ansa Hdz Camas! da sauri ya dauki numbar awayarshi dan yana zargin itace numbar yarinyar da yake nema tayi mishi karin bayani......sai da ya kira sau uku kafin A daga wayar, Camas na kokarin shiga sabuwar motarta kira ya shigo wayarta koda ta duba taga sabuwar numbar bata damu ba saboda tasan tana hurd'a da mutane sosai Ta daga wayar da sallama a bakinta.
Ya amsa a nutse yana fad'in "Ina magana da Hadiza ko."? Tace " Eh ko kace Camas! dan haka jamaa ke kirana." Ajiyar zuciya ya sauke, wanda har sai da taji a kunnanta, ya mike ya kunnanshi makale da wayar ya fito palo ya zauna kan kujera a Yace " Nasan Zakiyi mamakin me magana dake, Ni ne Ahamdu Mijin kawarki Wasila."
Camas taji gabanta ya yanke ya fadi har sai da wayar ta kusa faduwa, baki na rawa tace"Yallabai ina wuni." ya amsa a nutse yace."Tambayarki zanyi.' Tace."Allah yasa na sani." jikinta duk yayi sanyi dan tayi tunanin ko zai tambayeta kan kud'adan wasila ne wanda ta riga tayi fata fata dasu mussaman da taji labarin sun bar gari gabad'aya sai ta sake sakin jikinta tana facakarta da kudi.
Yace."Ko kin san ina 'kawarki suka koma da zama."? Shiru tayi tana tunani, Yace."Ke nake sauraro." Tace"Yallabai ban sani ba wallahi dan nima sai labari naji a gari wai sunyi tafiya amma dai nafi tunanin ko can kyauyensu suka nufa Garko."
Yace."Basu nufi can ba domun kawun su ya tabbatar min da cewar basu je mishi ba ya dai ce yana tunanin sunbi mahaifiyarsu, shin ko kin san inane garin su mahaifiyar tasu." Tayi shiru tana tunani kafin tace"Wallahi na san sunan garin amma ya kwanta min bari yanzu in kira mahaifiyata a waya nasan ita bazata rasa sani ba, insha Allah zan kira ka sai na fada maka."
Yace."Okey to ina sauraranki."! Camas! ta kashe waya tana tunani cikin mota, shin me yasa guy nan yake son sanin inda Wasila take, ko dai zai mayar da ita ne a matsayin matarshi, tabdijam idan hakane kuwa wallahi ba zata fad'a mishi ba, key tasa zata tashi mota, kiranshi ya shigo tayi banza da wayar har ta katse....Ta tashi motar ta tanaji wayarta nata famar ringnig amma taki dauka, har sai da ya gaji ya hakura.
Yana zauna rike da waya ya rasa ya zaiyi amma yarinyar nan ta shammace shi gabakidaya ya d'o
ra buri da tunani a kanta yana tunanin koda sunanan garin da suke ya ji ya san mutukar sun shiga garin tunda ba'ki ne nemansu ba zaiyi wuya ba, bai hakura ba ya cigaba da kiran wayar yana ta adduar Allah yasa ta dauka kawai sai yaji ta kashe wayar ma gabad'aya, ya dinga bin wayar tashi da kallo tamkar wani zautacce.
****
Yau kwanansu hud'u a Garko hankalinsu ya kwanta sosai Wasila ta mirmure ta samu lafiya sai abun da ba'a rasa ba, kuma laulayin ya danyi sauki sai dai jefi jefi take amai shima da safe takeyi kafin ta karya......Bata aikin komai Bitan da Rashida suke aikin gidan kullum malam mai allo cikin siyo mata kayan gon yake irinsu d'ata da goba mangwaro da sauransu, sannan kullum sai tasha rubutu da tofi safe da dare, ita kanta yanzu ta soma samun kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya mussaman in ta juya gabas yamma kudu da arewa tana ganin 'yan uwanta da danginta na shige da fice a gidan.....Ita kanta Hajara kullum a tafe take idan bata zo yau ba to gobe zaka ganta tazo kuma bata zuwa gidan hannunta haka kawai sai ta tazo musu da tsarabar kayan kwadayi.................
Malam mai allo da kanshi ya shiga kasuwar garin ya siyo musu abubuwan bukata dai-dai karfinshi yanzu babu wani abun da zasu nema su rasa a gidan dai-dai silafas na yawo a tsakar gida mai allo ya siyo musu ko wanne da nashi.
******
'Bangaran Ahamdu kuwa jinya ya kwanta ta tsayin sati uku har sai da Hajjah tazo gidan tayi jinyarshi wanda sai a lokacin ma ita ta san abinda ke faruwa, aikuwa ta shiga yi mishi fada tamkar ta ari baki, taji ciwon abinda ya aikata shi ba yaro karami ba, an samu yayi auran kuma baije ko ina ba ya fara saki, ai mutane ma sai su daukeshi karamin mutum......Ahamdu baya so ya fada mata dalilin da ya sanya hakan ta faru kawai dai yace mata tsautsayi ne da kaddara, ita kuma tace lallai sai ya kaita gidansu yarinyar tayi bikonta, nan yake shaida mata shima yanzu halin da ake ciki bai san inda yarinyar take ba, Hajjah ta dinga mamaki Yace."Naje can garin nasu gurun waliyyinta shine ya tabbatar min da cewar bata gurinshi amma yafi tunanin tabi mahaifiyarta garinsu, to inda aka samu matsala shine shima bai san wane gari ne ba."Hajja dai ta dauki laifin kacokan ta dora a kanshi ta kuma ce idan haka zai dinga auran yaran mutane yana saki to babu ubanda zai bashi auran 'yarshi mutukar ba kwad'ayayyan abin duniya bane......Tace kuma lallai idan ya samu sauki ya dauketa ya kaita can gurin mai allon a bashi hakuri a bisa abinda akayi mishi, bai musa mata ya amince da maganarta saboda dama can baya tsallake umarinta
****
Bayan Sati biyar.......Cikin Wasila ya fito sosai dan har ya hud'a zani yayi kurcici dashi kamar an kifa 'kwarya yanzu yana matakin wata biyar da kwanaki, tayi kyau sosai ta murje ta daina laulayi yanzu komai tana ci ta zauna lafiya ta daina amai da sauransu, sai dai kuma yanda cikin ke mata motsi a cikinta ne yake damunta, ga wani uban cin abinci da takeyi mutakar tana jin yunwa idan bataci abinci ba sai jikinta yay ta kyarma shiyasa kullum bitan cikin d'orawa da saukewa takeyi bata bari abinci ya yanke mata, sabida Wasila ta zama rumbu.
*****
Sun shirya tsaf tsaf! shida Hajja suka fito harbar gidan nashi, ya fito da wayarshi yana neman numbar Khalifa sai kiranshi ya shigo da sauri ya kara a kunnanshi Khalifa yace "Anya kuwa tafiyar nan dani za'ayi kuwa! Wallahi Hafsa ce ta tashi da zazzabi me zafi yanzu yanzu zan kaita a dubata muna zargin dai ko an samu 'karuwa ne."
Yace."Ayya! Allah ya sawa'ke! babu matsala bari mu tafi kawai insha Allahu zamu shigo nida Hajjah sai mu dubata." Khalifa yace."Okey babu damuwa A mika min gaisuwa gurin aramma." Yace."Zaiji insha Allahu." Yana kokarin kashe wayar ne Khalifa yace."Allah yasa idan kaje kawai ga mutuniyar taka tana cire kafa da kyar! dan cikin nan yanzu nasan yayi kwari." Ya d'anyi ya'ke wanda hausawa suke fad'in yafi kuka ciwo "Khalifa bana tunanin akwai cikin nan fa." Khalifa yace."Kar ka cire tsammani abokina." Yace."To Allah ya amshi adduarka." Khalifa yace."ameen ya rabbi sai kun dawo kenan."? Yace."Insha Allah." Kashe wayar yayi ya mayar aljihu kana ya nufi
parking spece lokacin Garba nata 'kokarin karkad'e mota Hajjah na gidan baya a zaune, kawai shima sai ya bude ya shiga ya zauna kusa da ita, Garba ya shiga ya zauna maxauninshi ya kunna motor a nutse suka fita daga gidan, Yayin da ma'aikatan shi ke faman yi mishi fatan alkairi da dawowa gida lafiya.
Littafin na kudine......!
Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biyaba kema keda Allah! Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*'Yr Bngr Sys
*61*
'Katuwar tabarma ce shimfid'e a tsakar gidan, Wasila na kwance hannunta rike da mafici tana fifita zafi ake sosai a garin ga dukanin alamu ruwan sama na dab da sauka mai allo yana gefe kan buzunsa da wani ma dai-dai cin allo a hannunshi yana rubutu, Bitan da Rashida suna daga can gefe suna aikin gyara zabbi wanda malam ya sanya d'anshi Tanimu ya yanka su saboda Wasila wai ta dinga samun kuzari da karin jini da lafiya shiyasa ba'a daukar lokaci ake soya mata kaji da dafaffan kwai duk sanda ya fita kasuwar cikin gari kuwa sai ya siyo mata manya manya kifi masu kyau da kara lafiya.........Ya d'an kalleta tana kwance tana aikin fifita sai gumi take Yace."Da alama dai yau garin ruwa ne zai sauka shiyasa zafin ya tsananta da yawa." mikewa tayi zaune tana gyara daurin dankwalinta tace" Kawu malam Allah zafin nan duk ya gigitani na rasa yanda zanyi." Murmushi yay yace."Bake kad'ai ba wasila nima Allah Allah nake in gama miki rubutunan in fita insha iska a waje duba dai dik girman gidanan babu iska ga rana ta game ko'ina." Bitan dake sauraron hirar tasu tace"Ai idan kaga irin wannan ranar to tabbata ta ruwa ce dan haskenta yayi yawa, dubi gabas ka gani hadari ne sosai shiyasa nake sauri in gama ayyukana kafin ruwa ya sauka." Wasila tace"Allah gwara ayi ruwan ko a samu sassauci ni akwana ma anayi.'' Mai allo yasa dariya yana fad'in "Wato ke kanki kika sani ko? idan anyi an kwana ana ruwa 'yan kasuwa suce me? wani fa sai ya fita zai samo abinda zai kaiwa iyali." Tace"Allah Kawu malam zafin ne ya isa Allah na tuba." Bitan tace"Aike Wasila dole ne kiji zafi saboda lalurar dake jikinki dama haka masu ciki suke da jin zafi." Tace"Aikam dubi wuyana kuraje duk sun fito, ni ruwan sanyi ma nake so." Mai allo yace."Wannan ne kuma baki isa ba! za'ayi miki komai wanda kike so amma banda shan 'kankanra." Marairaicewa tayi tace"Kawu malam ba 'kankanra zansha ba ruwan sanyi fa nace don Allah a taimaka asiyo min." Shiru yay yana cigaba da rubutunsa, ta dinga magiya tana karyar da kai! Yace."Bari Tanimu ya shigo." Da sauri tace''Kawu ka bawa rashida kud'in ai tasan gurin." Yace."Bana son aiken rashida gurin nan akwai maza." Shiru tayi tana had'iyar miyau da kyar ma'kogwaronta duk ya bushe! Kallonta yay ta bashi tausayi kwata kwata yanzu baya so yaga abinda zai 'bata mata rai ko ya sata a damuwa, ya kalli Rashida dake wanke hannunta bayan sun gama aikin, yace."Zo kar'bi maza jeki bakin gada gurin masu siyar da ruwan sanyi ki siyo mata kar a bada mai 'kankara." Rashida tace "To ta karaso da sauri ta 'karbi kudin, hijab tasa ta kama hanya ta fita bayan ta dauki wani jug mai dan girma.
Tana fita dalleliyar motarshi ta karyo kwana zata shigo cikin layin......Yara yaran dake wasa a bakin hanya suka watse suna ihu da bin motar da kallo, Rashida na tsaye a bakin kofar gidan motar tayi parking a wani fili dake gefen gidan.....Wucewa take kokarin yi yay gaggawar bud'e motar ya fito gabanshi na wani irin fad'uwa, babu abinda yake fad'i cikin zuciyarshi sai alhamdullihi."!!! Rashida tayi saurin dafe kirjinta tana kallonshi Sai kuma ta washe baki wanda kana ganinta kasan tana cikin farin ciki.......Garba ne ya bud'ewa Hajja mota ta fito tana mita da fad'in " Zaman mota ai sai ya saka ciwo tafiya ba tafiya ba 'kafafuna duk sunyi tsami.'' Hannunta ya d'an ri'ke kana ta gyara sa takalminta da lullubin mayafin ta da ya sauka kafadarta........Rashida ta karaso gurin cike da nauyi da jin kunya take musu barka da zuwa! Ya dinga amsawa da sakakkiyar fuska kamar bashi ba sai wani dariya yake yana godewa Allah lallai Khalifa Waliyi ne ashe dai da gaske a maganarshi , ya tabbata tunda yaga 'yar uwarta itama tana ciki........Ya kalleta a nutse yace."Ina fata mai allo na nan." Tace."Eh yana nan yau bai fita da wuri ba ya tsaya yiwa anti Wasila rubuta." Da jin maganarta sai yaji tamkar an tsiyaya mishi ruwan sanyi mai madara a ranshi yaji duk wani kunci da tashin hankalinsa ya kau! sai ya dinga zumud'in shiga gidan, yana fad'in "To kije ki shaida mishi cewar mune muke tafe." Da sauri Rashida ta nufi cikin gidan cikin murna da farin ciki sai kace wacce akace ga mahaifinta ya dawo duniya......... Lokacin da shiga gidan Wasila ta tashi hakanan Bitan ma tana kicin tana gyara tukunya, ta zube a gabanshi da walwala a fuskarta tace"Kawu ga Alhaji Ahamdu mijin anti Wasila nan shida mahaifiyarshi yace a sanar maka da zuwansu." Mai allo ya jinge allon dake hannunshi yana kallonta Yace."To Masha Allah sune suke tafe cikin wannan ranar? maza karkade tabarmar nan ki gyara musu guri bari na shigo dasu Allah yasa ma ban fita ba da munyi sa'bani." Rashida ta shiga karkad"e tabarma tana sake share gurin da marmatsar da abubuwan dake kan hanya.....Mai allo ya sanya takalmansa a nutse ya fita daga gidan.........Tana 'kokarin fitowa daga band'akin ne hancinta ya sha'ko mata masifaffen 'kamshin turaransa da ba zata ta'ba mancewa dashi ba......Gabanta ya yanke ya fad'i lokacin da ta tsinkayi muryarshi yana sallama a gidan ta kuma tsinkayi muryar mai allo yana fad'in "Sannunku da zuwa Alhaji sannu kun d'auko rana Hajiya sannu da hanya, ku shigo ciki......'Kyauran band'akin ta ri'ke gam! jikinta na kyarma! ta dinga fad'in innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! me ya kawo shi? me yazo yayi mana? me yake nema kuma? babu wanda zai bata amsa, ta cigaba da rike kyaure tana rawar jiki tana kuma juyo muryoyinsu a lokacin da suke gaisawa da juna. Jikinta ta duba daga ita sai zanin atamfa dan da zafi ya isheta bayan fitar rashida ruwa ta cika a bokiti taje ta kwara a jikinta wai ko ta samu sassauci babu abinda ke jikinta sai zanin atamfar da dankwalinshi, kamar za tayi kuka yanzu ni ya zanyi na fito ga mutane gashi ba suttura a jikina? tunanin da take kenan ta juyo muryar Mai allo na fad'in " Rashida shiga ki kira 'yar uwarki mana ni kaina a 'kasa ina rubutu ban san sanda ta tashi daga gurin nan da tana kwance a gurin nan da kake zaune." Yafad'a yana nuna masa inda yake zaune, sai ya shiga bin gurin da kallo kamar zai ganta a gurin......Rashida ta duba dakin bata ciki, Bitan dake kokarin fitowa daga d'aki tace"Ai inajin tana band'aki wanka take kasan dama yini take watsa ruwa bata son zafi ai." Mai allo yace."To to koda naji." Ahmadu kuwa jin abinda Bitan tace sai kawai ya shiga rarraba idanunsa a cikin gidan yana laluben ta ina zata fito......Aikuwa sai yaji motsin 'kyaure a wani 'bangare da sauri ya mai da idanunshi gurin......Ta fito a hankali kamar wacce 'kwai ya fashewa a ciki take tafiya, zanin jikinta ya d'angale saboda daurin kirji da tayi sai tayi amfani da dankwalin gurin kare kirjinta da fuskarta.......Gogon ya wani susuce a gurin ya dinga kallonta tin daga kafafunta har zuwa kanta, jikinsa yay wani bala'in sanyi lokacin da ya hango tudun cikinsa dake jikinta, rintse idonsa yayi yana tasbihi ga Allah ya sauke wata gawurtacciyar ajiyar zuciya, Ya bud'e idanunsa da sauri a dai-dai lokacin da take 'kokarin shiga d'akinsu santsin takalmin dake kafarta ya kusa kayar da ita, tayi axamar rike kyauran d'akin tana salati zubewa tayi bakin kofar lokaci guda zanin jikinta ya kusa sa'bulewa dankwalin da ta rufe kanta da kirjinta tuni yayi nashi guri, wani irin 'kullewa marar tayi tana murd'a mata.........kawai ganinsa tayi tsaye a kanta ya wani gigice yana sa'be babbar riga dama manyan kaya ya saka tunda duk sanda zaije gurin mai allo baya zuwa da tazarce na shadda ko yadi riga da wando da malin malin yake sanya........Shine yay bake bake a gurin yana fad'in "Subahanallahi! Kafin ta juyo miryar Bitan na fad'in " Haba Wasila sai da fa na hanaki saka takalmin nan saboda santsin sa sau nawa yana kokarin kayar dake dan dai kawai Allah na kiyayewa ne, kinga ni dai yau ga abinda ya ja miki." Bitan ta 'karashe maganar tana kokarin mikar da ita! Rintse idonta tayi tana fad'in "Wayyo cikina mara ta ciwo Bitan Ya Allah."!!!! Da sauri yay nufi shiga dakin zufa na karyo mishi Hajjah ta dakatar dashi tana hararshi, ita ta shiga dakin suka kama Wasilan suka janye ta daga bakin kofa! Shi kuma ya cire hularshi yana fifita da ita! Wannan wane irin tsautsayi ne? daga zuwanshi yana murna Allah dai ka taimake ni."! Abinda yake fad'a kenan ya koma ya zauna yana cigaba da fifita da hularshi fargaba duk ta cika masa zuciya......Mai allo ya kalleshi cikin naxari sai kawai ya girgiza kanshi yana murmushi a cikin zuciyarshi ya cigaba da d'auraye rubutun dake jikin allon hannunshi, Yace." Tuntuni naji Bitan nayi mata magana kan ta daina saka takalmin nan saboda rashin ji ta'ki dainawa, gashi yana so ya cutar da ita, tunda abin ya kasance da haka da kaina zan dauke takalman na fita dashi.''
Ya aje hular dake hannunshi a gefe yana fuskantar mai allon sosai, Yace."Shine babban damuwar dama, akwai kuruciya da rashin sanin ciwon kai a tare da ita shiyasa take aikata komai yanzu daba dan Allah ya takaita ba da mummunar faduwa za tayi." Mai allo yace."Allah dai ya kikeye." Mikewa yay hannunshi rike da rubutun ya nufi dakin......Binsa yay da kallo yana ji kamar yabi bayanshi sai dai kallon da Hajjah tayi mishi a d'azu yake tunawa.
Mai allo ya tsaya bakin 'kofar dakin yana mikawa Bitan rubutun hannunshi da fad'in "Bata tasha kana kuma ki shafe mata jikinta dashi, za taji sassauci rashin jin magana ne irin na mutan yau, takalma zan daukesu yanzu in fita dasu idan ya kasance ta shiga bandakin babu takalmi sai ta shiga haka ai lalurace tunda shi takalmin na baraxana da lafiyarta" Hajjah babah tace"Kwarai kuwa malam ka kwashe takalman a fita dasu tunda suna neman cutar da ita kuma mutukar tana ganinsu to ba zata daina sakawa ba."
Mai allo ya sunkuya bakin kofar ya kwashe sabbin takalman 'yan madina ya samu leda ya zuba a ciki ya daure ya rataye jikin wata kusa dake bangon gidan yana fad'in "Anjima idan zan fita zan fita dasu in bawa yara sayi amfani dashi."
Yana zaune yana kallon mai allon duk ya rasa abinda ke damunshi hankalinshi na cikin dakin burinshi ya sake tozali da ita da cikin jikinta, jikinsa ne yay sanyi ganin babu wata sakewa irin tada a tare da mai allon yasan dai sun gaisa cikin girma da mutunci amma duk wannan rawar jikin da mai allon keyi masa ya daina magana ma ba sosai sukeyi ba......Hajjah babbah da Bitan suka fito daga dakin, Hajja na fad'in "Ciki fari dama ai kyaga wauta iri iri Allah dai ya rabasu lafiya.'' Duk suka amsa da " ameen." Har dashi gogan da yabi ya zubawa hajja ido yana so yayi magana sai dai yayi shiru ya sunkuyar da kanshi 'kasa, tunda khalifa baya gurin to yanzu hajja itace garkuwa a gurinshi amma shi kanshi yanzu ya gane ya tafka babban kuskure sosai mugun kunyar mai allon ne ma ya rufeshi yanzu da wane ido xai kalleshi yayi mishi bayani dangane da abinda yake tafe dashi.
Hajjah ta gyara zamanta a nutse tace"Malam gurinka nazo domin magana mai muhimanci nake tafe da ita.'' mai allo ya gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Hajiya ina sauraranki." Hajja tace"Malam da farko dai ina me baka hakuri a bisa abinda ya faru, nasan dole rayukan ku su 'baci saboda duk mutumin da akece an saki d'anshi dole ne ranshi ya 'baci mussaman idan anyi bunkice an duba anga babu 'kwakkwaran dalilin da ya sanya aka aikata sakin kamar dai yanda al'amarin nan faru, yarinyar nan wasila an saketa ba tare da wani dalili me karfi ba, tabbas an shiga hakkinta mutuka!! kuma irin wannan sakin shine ubangji baya so.....To amma nasan dai kai mai ilimi ne kuma kasan kaddara dai- dai gwargwado kasan cewar duk abinda Allah ya kaddara sai ya faru a kan bawanshi to sai ya faru, saboda haka ina so dukaninmu mu dauki wannan abun a matsayin kaddara wacce ta riga fata......Kuma hakika naji dad'i sosai da ya kasance cewa sakin an aikata irin wanda musulunci yake so, akwai sauran dama a halin yanzu, dan haka muke ro'ko ayi hakuri yarinyar nan ta koma d'akinta."
Mai allo ya sauke ajiyar zuciya mai 'karfi! yana kallon matar.....Hakika matar nada mutunci da kima da kuma sanin ya kamata ko ga yanayin kalamanta, baya jin zai iya wani ja'inja kan maganarta mutukar shi Ahmadu da yarjewarsa take masa bikon matarshi, zai amince da maganarta, sam baya so a zo ayi abu irin na baya ma'ana a koma gidan jiya, Ahamdu ne me aure ba Hajjah ba kuma shi ake so ya furta da bakinshi kan cewar ni wane na janye sakin da nayi wa mata wance na mayar da ita dakinta yanzu tana matsayin matata kamar yanda addinin musulunci ya tanada, to mutukar yaji wad'annan kalmomi daga bakinshi, bashi da tace addini ya riga ya halasta masa matarshi tunda dama ba tayi iddah ba." Yace."To masha Allah Hajiya, ai dukanin abinda kikaga ya faru dama da sanin Allah duniya babu wanda ya isa ya tsarawa kanshi rayuwa face wacce Allah ya tsara masa, auran Ahamdu da Wasila ya 'kare a lokacin da Allah yake so, kuma a sanda yake so zai iya sanyawa su koma su cigaba da zama mutukar rabo bai 'kare a tsakaninsu ba, Ni bani da tacewa anan gurin hakanan itama yarinya bata da magana, tunda a yanzu addinin musulunci ya bashi dama a hannunshi, zai iya yankewa kanshi hukunci, ina nufin ya d'auki aniya a zuciyarshi kancewa ya mayar da matarshi ko kuma akasin hakan duk wannan damar yanzu a hannunsa take, Yanzu ni shi nake jira ya furta min da bakinshi cewar ya amince yarinyar nan ta cigaba da zama matarshi ko A'a."? Mai allo ya 'kare maganarshi hankalinshi a kwance.
Hajjah babba tace"Eh gaskiya ne malam maganar ka na kan hanya a yanxu magana na bakinsa dani da kai duka 'yan fatan alkairi ne domin dukaninmu ba zamu haramanta abinda ya halasta ba saboda haka magana yanzu tana gurunka kai muke sauraro." Hajja ta'kare maganarta tana me zuba masa idanunta.........A nutse ya d'ago kanshi zaiyi magana kenan, Ta fito daga dakinsu, sai duk suka zuba mata ido har ta tattako a hankali ta 'karaso inda suke zaune! gaban mai allo ta dur'kusa tana hawaye da rike masa hannuwa tace"Kawu kaine fa kace ba zaka sake takurani ba! Kawu ashe ka manta al'kawarin da kayi min ranar da muka zo garinan kace ba zaka sake yi min tilas ba, zaka barni da kaina na za'bi miji wanda yayi dai-dai da rayuwata na aura." Da sauri! ya d'ago kanshi yana kallonta jin abinda take fad'a! da cikinsa za take tunanin yin aure? Kafin ya gama tunani ya juyo muryarta na shashshe'ka tana fad'in "Kawu ni daina bana son na koma gidanshi, sabida ba zan iya rayuwar da nayi dashi a baya ba, Zargina yakeyi Kawu nasan kasan aure da zargi a musulunci ya haramta ni kawai a kyaleni na haifu lafiya sai a bashi d'anshi." Cikin kuka da yanayi na damuwa take maganar gashi ta ruk'e hannun Kawunta katamau!
Dukaninsu suka bita da kallo mussaman gogon da duk jikinsa yayi sanyi ya dinga kallonta yana hango tsabagen 'kiyaysrshi a cikin kwayar idanunta......Sai yaji wani irin ba'kin ciki da takaici ya turnu'keshi! wato har wani kuka take tana nadama da fad'in ba zata koma gidanshi ba, to me yake mata da za tace ba zata koma gidanshi ta cigaba da yin rayuwar da tayi a baya ba? shin tun da suke yaushe yayi zarginta? shine zai fad'awa kowa cewa ita d'in kamila ce kuma nitsatstsiya tunda ta kawo mishi burducinta! bai ta'ba zarginta ba sai sanda wannan al'amarin ya faru!!!! 'Kwafa yay cikin ranshi, ai magana a hannunshi take ba'a hannun wani ba, malam mai allo na shirin yayi magana, Ya rigashi da gyaran murya kafin yace."Ai maganar saki tuntuni na janyeta malam yarinyar yanzu haka a matsayin matata take, wannan dalilin ne ma ya sanya ni dauko Hajja domin tazo ta baka hakuri a bisa abinda ya faru tsautsayi ne da kaddara amma insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba." Mai allo ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace."To madallah Alhaji naji dad'in wannan kalmar taka kuma Wasila zata koma gidanka insha Allahu amma ina so in baka shawara ko kuma in tunasar dakai duk da cewar ka sani, Allah da kanshi ya hallata saki amma kuma baya so a akaita shi, kayi kuskure a lokacin daka yanke hukunci, bance yarinyar ba tayi maka laifi ba tabbas tayi laifi wanda ya dace ka dauki ko wane irin mataki a kanta, amma banda saki, ni a ganina ba tayi abinda za'a saketa ba, saboda ita mace komai girmanta da shekarunta abar tausayi ce ballanta yarinya 'karama irin wannan!? Ka saketa tana da ciki, abinda ba'aso sannan ta amshi laifinta ta nemi afuwarka ka koreta daga gidanka, bazan 'boye maka Alhaji yarinyar nan ta wuya da wannan cikin na jiki kafin su zo nan kenan, sai bayan zuwansu, dana tsananta gurin yi mata tofi da rubutu sannan ta samu lafiya har kazo ka ganta haka, ina fad'a maka da can kwanakin baya kazo da sai ka tausaya mata mutuka dan abincin kirki bata iyaci sai yame yame irin nasu, to Alhamdullhi yanzu lafiya ta samu tana iya cin komai ta zauna lafiya, saboda haka nake baka shawara da kuma tunasarwa kan cewar duk wani abu da matarka za tayi maka na kuskure to ka dinga sanya hankali da nutsuwa kafin ka yanke hukunci akai dan saurin saki bashi ne hukunci ba, wallahi Alhaji da kazo bayan yarinyar nan ta haihu to banga dalilin da zai sanya in tilas ta mata cewar sai ta cigaba da zama da kai ba, zan dai baka dama ka shiga cikin zawarawanta idan har kana da muradin hakan."
Ya dinga kallon mai allo cike da d'umbin mamaki! wato shine ma zaibi layin zawarawa sai kace wani shashasha! tsaki yaja cikin ranshi mai allo bai ta'ba 'bata masa rai ba irin yau! amma sai ya shanye ya dake! ya hakura tunda dai magana ta'kare ai shikkenan........A nutse yace."Arrama insha Allahu hakan ba zata sake faruwa dukanin abinda ka fad'a gaskiya ne tsautsayi da 'kaddara basa wuce kan kowa, saboda haka insha Allahu magana ta wuce a gurina zan rike yarinyar nan tsakani da Allah da manzonsa, Saboda haka yanzu sai su shirya kayansu ita da 'yar uwar tata mu tafi in yaso sai ta dinga d'an d'ebe mata kewa har Allah ya sauketa lafiya"...............Da jin maganar dake fitowa daga bakinshi yasa ta mike da sauri ta shige d'akinsu tana wani irin kuka mai cin rai!!? Ta sanya hannuwanta duka ta dunga dukan katifar dake shimfid'e a tsakar d'akin.
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whsap numbar
*07084653262*alliya:
'Yr Bngr Sys
*62*
Rashida ce ta shiga dakin ta tsaya kanta tana kiran sunanta, "Anti Wasila dan Allah ki daina kuka ni wallahi banga abin kuka da damuwa anan ba,Allah na yarda da nadamar mutumin nan yanzu kuma yana sonki dan da baya sonki ba zai tayar da hankalinshi a kanki ba, kawai ki hakura ki koma dakin ki shine mutuncinki damu gabakid'aya." Idanunta jaga-jaga da hawaye ta dago tana kallon 'yar uwar tata dake durkushe kusa da ita, "Rashida nifa bazan koma yanzu ba sai na haihu haka kurrum kai tsaye zaizi yace ya mai dani sai kuma na kwashi jiki na bishi babu wani shiri da da yanxu ba d'aya bane yanzu nasan ciwon kaina." Rashida tace"Eh gaskiya kuma hakane to da zai bari ki haihu shikkenan yafi sauki hakan amma yanzu ku kin koma nasan hankalinsu mai allo ba zai kwanta ba.
To a can tsakar gida kuma sai fafatawa ake tsakanin mai allo da Ahamdu da kuma Hajjah inda mai allo ya kafe kai da fata yace Wasila ba zata koma ba sai ta haihu sannan Ahamdu da Hajjah sai rarrashinsa suke da kawo masa misalai wanda suke nuni da cewar in ta koma d'in ai babu matsala insha Allah zasu kula da ita da kyau dan har hajja tayi al'kawarin zama tare da ita har sai ta haihu tayi ar'bain tukkuna sannan ta tafi gidanta, Malam mai allo yayi shiru yana nazarin maganarsu, shi dai hankalinsa yafi kwanciya da zaman yarinyar a gabanshi to amma bashi da yanda zaiyi dole ya hakura ya basu tinda yanzu suke iko da ita, Yana mutukar ganin girman hajja sabida matar tasan abinda takeyi sosai.....Yace."To shikkenan ai tunda kun rinjayeni na bar muku amma kuyi hakuri ku barmin rashida dan naji kana cewa tare zaku tafi da ita." Ahmadu ya marairaice sosai yana rarrashin mai allo kan yay hakuri ya basu har rashidan zamanta tare da 'yar uwarta zai d'ebe mata kewa sosai mai allo dai sun gama kashe mata jiki sai kawai ya amince musu amma kam zai sha kewa dan d'an zaman da sukayi dasu na watanni uku sun saba da juna sun sha'ku sosai.
Bitan na kicin ta kwalawa rashida kira ta fito da sauri ta nufi kicin......Bitan ta kammala abinci tsat tsaf ta jera kwanukan silba kan wani katon faranti shima na silba sai she'ki yake kwanuka uku ne akai d'aya lafiyayyan towon farar shinkafa ne tas dashi a nad'e cikin leda d'aya miyar taushe ce da taji gyada da alayyahu da yakuwa, d'aya kwanon kuma farfesun naman zabbi ne sai kamshi yake yayi shar shar dashi, tace"Dauki ki kai musu sai kizo ki dauki wancan jug din ki kai musu ruwa." Rashida ta dauki abincin ta fita.
Mai allo ya mi'ke ya bar gurin domin su samu sakewa suci abincin a nutse Ahamdu ya saki jikinshi yaci abincin sosai irin wanda ya Jima baici irinshi ba, hakika ya yarda da kula da tsabtar matar shiyasa ya zage sosai ya cika cikinshi
Rashida kam na daki na rarrashin Wasila suci abinci ta'ki hawaye kawai take! tarasa abinda yake damunta, mai allo ya d'aga labulen dakin yana fad'in "Ina Wasila."? Da sauri ta goge hawayen ta tace" Gani Kawu, Yace."Kiyi hakuri kinji ko kiyi hakuri ki kyautata hakuri a karo na biyu na umarce ki da kiyi biyayya kibi abinda nace miki insha Allah zaki samu alkairi a gaba, bani na fad'a ba Allah ne ya hukunta hakan! duk macen da mijinta ya saketa saki d'aya kafin ta 'kare iddah mijinta ya dawo yace ya janye sakin ma'ana ya mayar da ita ko bata so dole ta koma ta cigaba da zama dashi a matsayin mijinta, dan haka nake sake baki hakuri nake kuma ro'konki da kibi mijinki ki koma d'akin ki insha Allahu za kiji dad'i kuma kiyi alfahari anan gaba." Mai allo ya gama kashe mata jikinta da maganganunsa shiru tayi tana tsiyayar da hawaye mai allo ya saki labulen dakin zai tafi tace"Kawu ina da magana." Ya dawo da baya yana kallonta......Tace"Kafin na koma to ina so muje can pataskum gurin Uwani kaga tunda muka zo ba muje saboda yanayin rashin lafiyana ba kuma musan halin da take ciki ba."
Mai allo yayi shiru yana nazarin maganarta ta Yace.''To babu laifi sai kuje domun ki shaida mata abinda yake faruwa, yana da kyau a fita hakkinta a matsayinta na mahaifiyarki tasan halin da ake ciki, bari na sanar da Alhajin abinda ke faruwa." Labulen dakin ya saki ya nufi inda suke zaune Sun gama cin abinc
i suna hira mutumin ya saki jikinsa sosai dan har ya kira Khalifa a waya ya shaida masa abinda ke faruwa.....Mai allo ya dan jingina jikin bango a nutse yace."Anya Alhaji tafiyar nan zata yiwu yau kuwa."? Yayi saurin kallonshi yana so yaji dalilin da zai hana yiwuwar tafiyar......Mai allo yace."Yarinyar nan na bukatar ganawa da mahaifiyarta hakan nada kyau sosai mahaifiyarta tasan halin da ake ciki ta kuma sanya mata albarka, a zamantakewar auranta, dan haka nace ko zamu bari rana ita yau! insha Allah sai kadawo ka d'aukesu kafin sannan sunje sun dawo ta sake nutsuwa tukkuna.
'Dan 'bata fuska yayi yace."A'a malam ina ganin rana d'aya ma zamu iya zuwa mu dawo
Ba tare da anja dogon lokaci ba, ni da kaina zan kai su su dubata insha Allah gobe zamu dawo tare da khalifa sai su shirya muje daga can sai mu wuce kawai.'' Mai allo yace."Babu laifi hakan Allah ya kaimu lafiya." Hajjah tace "Amin amin ya rabbi mungode malam Ubangiji Allah ya kara girma da dattako." Mai allo yace."Babu komai hajiya mudai fatan anan shine Allah yasa anyi kenan Allah ya d'orar da zaman lafiya."
Ya d'an gyara zamanshi as'usel kamar ko da yaushe dai ya ciro kudi masu yawa a jikinshi ya dora saman buzun mai allo yace."Malam zamu koma Allah ya saka da alkairi." mai allo yace."Alhaji Ahmadu baka gajiya kullum cikin hidima kudin nan sunyi yawa." Yace."Babu komai malam Allah ya bamu mu bayar meye amfaninsu in ba'a badasu ba." Mai allo yace." To maddalah mungode kwarai Allah ya kara arziki da wadata." Ya amsa da "ameen." yana gyara babbar rigarshi.
Hajja ta le'ka d'akin su Wasila tana gyara lullu'binta tace"To Ina kuke zamu tafi Wasila kina ina.''? Wasila dake kwance kan kafita ta fara kokarin mikewa zaune Hajja ta shiga dakin tana fad'in "A'a yi kwanciyarki kinji ko sannu! Dan Allah kiyi hakuri karki sa damuwa cikin ranki insha Allahu abinda ya faru a baya bazai faru ba yanzu ki kwantar da hankalinki ki daina damuwa kuma ki daina kuka." Kanta a kasa tace"Insha Allah Hajja nagode ki gaida gida." Tace"Gida zaiji insha Allahu gobe inanan ina jiran zuwanku." Shiru tayi tana mayar da 'kwallar dake kokarin zubo mata......Hajja ta fito daga d'akin kawai sai ta ganshi ya 'kurawa kofar dakin ido kamar zai shiga, kai kana kallonsa kasan a dame yake daurewa kawai yake yana kokarin dauke abin daga ranshi duk dan kar girmanshi ya zube a idon yarinyar da mutanan gida.....Hajja tace"To ko zakuyi sallama ne naga kanata kallon dakin....Girgiza kanshi yace "Tunda kunyi sallama babu damuwa ai gobe zamu had'u insha Allah." Tace"To babu lefi." Bitan ce ta fito daga daki hannunta rike da wata roba mai murfi mai kamar kwanon sha robar da fulani ke zuba nono a ciki, daya hannun nata kuma ledar fura ce a cure tace"Hajjah ga wannan babu yawa, tun zuwanku naso in dama muku ayyuka sunyi yawa." Hajja ta kar'ba da walwala a tare da ita tace"To godiya muke Bitan Ubangiji Allah ya saka da alkairi kwarai naji dadin yanda kika kar'bemu hannun biyu mungode sosai." Bitan tayi murmushi kawai tana fad'in "Babu komai hajiya mune da godiya ai ku gaishe da gida Allah sauke ku lafiya." Hajja ta amsa da ameen kana tabi bayan Ahmadu da ya riga yayi gaba." Suna tsaye da mai allo suna sallama, Garba dake zaune cikin mota ya fito suka gaisa da mai allon kana ya koma ya jingina jikin motar yana ganin tawowarshi ya hude mishi mota ya shiga Hajja ma shiga ta zauna da sauri ya zauna a maxauninshi , Ahmadu ya shiga dagawa mai allo shima yana daga mishi hannu gami da yi musu fatan sauka lafiya.
Bitan ta le'ka dakin nasu sai ta tarda rashida ita kadai a zaune Wasila tayi bacci Tace"Au bacci tayi kenan."? Rashida tace"Eh tun dazu nayi nayi taci abinci ta'ki ci." Bitan tace"Kyaleta na fad'a miki tana tashi daga wannan bacci xata nemi abinci da kanta." Rashida tayi dariya tana fad'in "Aikuwa yanzu ma kawai dan tana cikin 'bacin rai ne amma anti Wasila da abinci ba dama." Bitan tasa dariya tare da fitowa daga dakin.
Aikuwa hakane ya kasance da wata masifaffiyar yunwa ta tashi da kyar taje ta wanke bakinta ta nufi kicin Bitan tace"A'a kar ki fara da abinci d'azu malam yace." Kafin kici komai kisha wann
an rubutun." Dakin bitan din ta nufa ta kar'bi rubutun ta tsuguna da bisimillah a bakinta tasha ragowar ta shafe cikinta dashi kamar yanda ta saba.....Bitan ta mike da kanta taje ta dauko mata abincin ta gyara zama sosai zauna kana tayi bisimillah ta fara cin abincin........ Sai bayan da ta kammala cin abincin ne tace "Bitan ina Rashida."? Tace" Bata jima da tafiya gidan Innar ku ba, malam yace taje ta fad'a mata abinda ke faruwa.
Ta sunkuyar da kanta kasa a hankali tace"Yanzu Bitan sai na koma gidan mutumin nan."? Bitan tace"To ya zakiyi Wasila shine alkairi don Allah kiyi hakuri ki daina wasiwasi insha Allahu babu wani abunda zai sake biyowa baya kuma insha Allahu zaki haihu lafiya." Shiru tayi tana tunanin shin idan ta koma gidan ko wane irin zama zasuyi dashi, ita yanzu ta daina jin sonsa a ranta, kawai zata koma ne ta zauna tare dashi saboda an rinjayeta.
Bayan magariba da mai allo ya shigo ya sake tabbatar mata da maganar ya kuma umarcesu da su had'a kayansu su kuma shirya da wuri don kar yazo yana jiransu.........mai allo kwana yayi yana karatun al'kurani mai girma sai da ya had'a izifi sittin kana ya tofa cikin tsabtattaccen ruwan sama, ya samu jarka mai kyau ya zuba ya rufe da murfinta ya aje a guri guda, kana ya mike a nutse ya fito ya d'aura alwala ya wuce massalaci.
Karfe tara shaura na safe sun shirya duk suna zaune a tsakar gidan har da Inna Hajara data dako sammako tazo gidan, ita da mai allo sun tasa Wasila a gaba sai fada suke mata mai tafe da nasiha irin fadan da iyaye kan yiwa 'yayansu a lokacin da za'a kaisu dakin mazajensu, Gatan da bata samu ba a farko, sosai take share hawaye tana jin wani iri a jikinta tabbas duk wanda yayi rashi iyaye nagari yayi babbar asara, Ada babu mai nuna mata ga yanda za tayi itace ke zartar da hukunci kan mahaifiyarta da 'yar uwarta dan sai abinda tace sannan Uwani da Rashida keyi, shiyasa takejin wani irin a jikinta, gaskiya babu abinda za tacewa mai allo da Hajara da ita kanta Bitan din dan sun nuna mata kauna da so da kulawa, duk mutumin zai fad'a gaskiya yayi maka fad'a kan wani kuskure naka to babu shakka masoyinka, dan haka sai ta dauki aniyar zama lafiya gidan Ahamdu kamar yanda suke bukata ta kuma yi musu alkawari kan insha Allah za tayi mishi biyayya iya iyawarta."albarka suka shiga sanya mata suna cike da farin ciki mara misaltuwa
Wannan karon cikin babbar mota (Sieana) sukaje garin wacce ke dauke da kayan abinci dana masarufi, Ahmadu yayi niyar farantawa mai allo kamar yanda shima ya faranta mishi saboda ya fahimci tsayuwar shi kan Wasilan da abinda ke cikinta yasan bashi da abinda zai biyashi a bisa abinda yayi mishi, sai dai hausawa nacewa yaba kyauta tukwici.....Almajirin malam ne ya hangi zuwansu lokacin da yake kokarin shiga gidan malam din, dan haka koda ya shiga gidan sai yake shaidawa malam din zuwansu, Wasila taji gabanta ya fadi har sai da ta rasa miyau a bakinta, tayi shiru tana kokarin maida kwalla ita har ta gaji da zubda hawaye..........Mai allo ya shigo dasu, cikin gidan yana musu barka da zuwa, Garba da Hadi sune suka shiga shigo da kayan abincin cikin gidan malam ya cika da mamaki yana so yayi magana Khalifa yayi saurin tareshi da fadin malam kada kace komai don Allah ba wai munyi hakan bane domin mu biyaka mun san bamu da abinda zamu biya dashi wannan ihisani ne kawai mukayi maka saboda karamcinka." Mai allo ya girgixa kanshi yana fadin anya abun baiyi yawa ba kuwa? Khalifa yace."Beyi yawa ba malam ka sanya albarka kawai." Yace."To nagode kwarai Allah ya sanya alkairi ya kara arziki da wadata." Khalifa ya amsa da ameen ya rabbi."
Inna Hajara kuwa mamaki take sosai ita bata ta'ba 'karewa mijin Wasilan kallo ba sai yau! sai take ganin kamar ma yafi karfin wasilan dama haka Allah ke tsara lamarinshi Addua ta shigayi kan Allah ya xaunar da ita lafiya a dakinta.
Malam ya sanya Tanimu ya dauki jakar kayansu ya kai motar, kana dukaninsu suka fito daga cikin gidan......Ita dashi aka bari a baya, sai ta dinga ra'bewa tana so yayi gaba shi kuma ya'ki tafiya da sauri yana tafiya sannu sannu yana kallonta ta gefan ido sai 'boye fuskarta take ci
kin mayafi, tana kauda kanta, tuntu'be tayi da bakin 'kofa yayi gaggawar rike mata hannunta yana d'an janyota jikinsa, da sauri ta bude fuskarta tana zumbura bakinta, jikinta ta janye daga nashi, ya danyi gyaran murya a hankali yace."Meye amfanin rufe fuskar da ki keyi ke ba amarya ba."? Shiru tayi mishi ta dan 'kara sauri gabanta na fad'uwa bata so wani ya juyo ya gansu suna jerawa, ganin yanda take tafiya da sauri da sauri yasa shima ya 'kara sauri har suka iske inda motar take......Khalifa da kanshi ya bude mata bayan mota ta shiga, Rashida na kokarin ta shiga ta zauna kusa da ita yace."kanwata zo ki zauna nan." Sai ta zauna inda ya nuna mata,Inna Hajara kuwa hawaye ta fara sharewa ta kasa daurewa, ganin hakan ya sanya su Wasila suka fara kuka mai allo yace."Wannan shirme ne hajara Alhaji ku tafi kawai idan ba haka yanzu xata sanya yaran nan koke koke."! aikuwa yana ganin Wasilan na kuka yayi saurin shiga motar ya zauna kusa da ita, yana d'aga musu hannu mai allo ya mi'ka mishi ma dai-dai ciyar jarkar rubutun dake hannunsa yace."Kullum ta dinga tsiyaya tana sha safe da dare tana kuma shafe cikinta dashi." Ahmadu ya kar'bi rubutun yana godiya da fad'in "Insha Allah malam Allah ya biya bukata."
Mai allo ya d'aga masa hannu yana fad'in "Ku sauka lafiya Allah ya tsare Alhaji Allah ya saka da alkairi." Shi da khalifa suka amsa da "Ameen malam Allah ya saka da alkairi." sai da motar ta 'bace daga gurin sannan suka koma gida duk jikinsu a sanyaye mussaman Bitan da Inna Hajara, to shima dai mai allon daurewa kawai yake yi saboda yayi mutukar sha'kuwa da yaran kuma yana jinsu cikin ranshi.
Hawaye take sharewa tana d'an kauda kanta tare da kare fuskarta da mayafinta, 'kamshin turaranshi da hucin numfashinsa duk ya isheta ta rasa ya za tayi gabanta sai fad'uwa yake, sai kawai taji hannunshi a jikinta ya kamo hannunta dake cikin mayafinta ya ri'ke cikin nashi a hankali ya soma murxawa yana kallonta ta gefan idonshi.......Kokarin cire hannun nata ta shigayi ya rike tam! ya had'e 'yan yatsunsa da nata guri guda ya rintse gam gam! kamar wanda yake bata amana ko kuma yake d'aukar mata al'kawari!!! Ajiyar zuciya ta shiga saukewa ta kauda kanta tana kallon hanya, a hankali taji hucin numfashinsa dai dai fuskarta, a razane ta juyo sai kawai fuskarsu ta had'u guri guda! bakinshi ya sauka kan nata bai jira komai ba, ya sanya harshensa ya lashi le'bunanta yana sakin ajiyar zuciya! ya d'auke fuskarshi ya gyara zamanshi kamar bashi ba,
Ta dinga jin wata irin fargaba da fad'uwar gaba sai kawai ta shiga rarraba idanunta cikin motar tana kici kicin kwace hannunta dake rintse da nasa.........