*NAJA'ATU UMAR ABBALE*
~~~~~~~~~~~~~
*1
"Innalillahi wa'ina ilaihi rajiun."! Abinda Baba Talatu tafad'a kenan ta kalli Saddiqa dake gefe a tsaye tana hawaye tace" Yi sauri ki d'ebo ruwa suma tayi." Saddiqa ta futa daga d'akin da sauri, karo suka ci da Baba Malam da Babban d'ansa Alhaji Magaji." Baba Malam yace."
wato dai har yanzu Kuka kuke yi ko da alama dai kuna so ku hana Halima ta kwanta lafiya a kabarin ta." Tana girgiza kai had'e da 'kokarin mayar da hawayen idonta tace"Baba Malam mun daina kuka Yaya Naja'atu ce tafad'i ta suma shine Baba Talatu tace na d'ebo ruwa." Da sauri Baba Malam da Alhaji Magaji suka shiga d'akin. ita kuma ta futa da saurin gaske, ruwa ta d'ebo cikin kofi ta shigo d'akin dashi.
Baba Malam dake tsugune kusa da Naja'atu yana mata addua ya kar'bi ruwa ya shiga yayyafa mata a fuska, Baba Talatu hawaye kawai take sharewa tana girgixa kanta.
Baba malam sai da ya yayyafa mata ruwan sau uku sannan ta saki wata ajiyar zuciya mai kar'fi! idanunta ta shiga kiftawa, sai ta mi'ke zaune da sauri ta shiga rarraba idanunta a kansu.
Baba Talatu ta ri'ke hannunta tana fad'in "Naja'atu kiyi hakuri kada ki jazawa kanki lalura." Ihu! ta zumduma! tasa hannu ta toshe kunnuwanta jikinta na wata iriyar kyarma! tace"Baba Talatu kunnuwa ba zasu iya d'aukar wannanmaganar taki ba! a ina aka ta'ba haka *Uba ya Auri 'Yarsa* ashe dama dake da Baba malam dashi kansa Abban nawa dukkanin ku maguzawa ne ku baku san addin........Kafin ta 'karasa Alhaji Magaji ya kwad'a mata mari! yace."Ke ki nutsu ki shiga hankalin ki bama son shirme da shashanci ki saurara ayi miki bayanin yanda al'amura suke."
A zabure! ta mi'ke tsaye! kamar wacce zata tada iska tace"Baba Magaji ni bazan fuskanci komai ba ba kuma zan nutsu ba, saboda ni ba kafura bace wallahi sai na kashe kaina idan kuka d'aura min aure d Ubana, wai baku ji sunansa bane Abban Naja'atu fa sunansa amma shine zaku daura mun aure dashi! to dukkaninku sai na kaiku *Hizbah!.* Ta'karashe maganar tana wani irin kuka mai cin rai.
Baba Malam ya goge guntin hawayen idonsa ya ri'ke hannunta da fad'in "Auta zauna ni da kaina zan warware miki abunda baki sani ba." Fuzge hannunta tayi tana 'kokarin tsallakeshi ta wuce! Alhaji Magaji yayi sauri tare mata hanya Yace."Naja bakya jin magana ko? To shikkenan idan baki kaimu *Hizbah* bakya 'kaunar Allah." Yafad'a babu wasa a tare dashi.
Hannunsa ta ri'ke jikinta sai mazari yake tace"Abba Magaji ka duba maganar nan da kyau fa! Kayi duba na tsanaki! ya za'ayi dan kawai Mamanmu ta mutu sai suce zasu d'aura min aure da Ubana wace irin rayuwa ce wannan."!!! Tafada cikin wani irin sauti!! Shima a fusace! Yace."Wai ke waye ya fad'a miki Alhaji Abbas Ubanki ne."!? Shuru tayi tana binsa da wani irin kallo! bakinta sai rawa yake yi. da kyar ta iya bud'e bakinta tayi magana....."Baba Magaji bangane maganar ka ba."! murya na rawa tayi maganar, Baba Malam ya zaunar da ita kusa dashi hannunsa cikin nata ya rike sosai yana kallonta, tausayi take bashi sosai, tabbas yasan dole ne ta shiga rud'ani da tashin hankali sakamakon bayyanuwar abinda yake rufe tsayin shekaru goma sha shida! da suka wuce. Wanda ta d'auka a matsayin mahaifinta dashi ake maganar d'aurin aure a tsakaninsu, babu shakka duk wanda ko yaji wannan lamarin dole ya shiga halin d'imuwa da tashin hankali
'Dakin ne yayi shuru na tsayin mintina uku kowa jikinsa yayi sanyi mussaman Naja'atu wacce take jin wata irin fargaba da fad'uwar gaba, tunda Abba Magaji yayi furucin cewar ba Abba Abbas ne mahaifinta ba take wata zabura tana rarraba idonta a kansu bakinta motsi kawai yake tana so tayi magana amma ta rasa me za tace! fashewa tayi da wani kukan tana kallon Baba Malam da kansa yake sunkuye sai zufa yake gogewa, tace"Baba malam kuna so nima na mutu ko? kuna so kamar yanda kuka rasa mamana nima ku rasa ni ko ? zuciyata daf take data daina aiki sakamakon bala'in da kuka jefata a ciki! Baba Magaji yace wai Abbana bashi ne Ubana to shikkenan sai ku fad'a min wanene ya haifeni."? Murya na rawa ta 'karasa maganar.
Baba Malam ya d'ago kansa a nutse yace."Naja'atu Nine Ubanki ni na haife ki Alhaji Abbas Uban ri'kon ki ne kuma miji ga 'yar uwarki Halimatu." wani irin kallo ta shiga yi masa tana girgixa kanta sai hawaye ya wanke mata fuska! murya a sanyaye tace"Baba malam ya akayi haka? ya kuka yi mun wasa da hankalina? ni ban yarda kaine mahaifina ba, Abba Abbas shine Ubana shi na sani tunda na taso shine yaci dani yasha dani ya tufartar dani ya tsaya a kaina nayi karatu kuma shi nake so ya aurar dani ga mijin dana za'bawa kaina."! Ta'karasa maganar cikin yarda da abinda take fad'a.
Abba Magaji ya fusata! sosai ya bud'e baki zaiyi magana Baba malam ya d'aga masa hannu yace."Kada kayi mata tsawa ko ka hantare ta, dole ne dama haka ta kasance da ita damu bakid'aya, ha'kika mutuwa itace ta janyo mana wannan tashin hankalin dan da Halimatu na raye to babu shakka Naja'atu zata cigaba da zama a matsayin 'yar data haifa alhalin kuma 'kanwa take a gareta, Yanzu zamu bari ta nutsu tukkuna zuwa dare sai mu sake wani zaman domin mu sanar da ita abinda ya faru a baya wanda bata sani ba." Abba Magaji ya sauke ajiyar zuciya a nutse yace."Shikeenan Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Baba Malam ya amsa da amin kana ya mi'ke suka futa a tare.
Suna futa, Naja'atu ta kalli Baba Talatu tace"Baba dan Allah dan annabi kada ki bari al'amarin nan ya tabbata, ke macace ce mai hankali da sanin ya kamata kuma kina zuwa isilamiyya kin san dai haramun ne Uba ya auri 'yar sa ko."? A zauce! take maganar.
Baba Talatu tace"Naja'atu Alhaji Abbas ba Ubanki bane an fad'a miki Mijin Yayar ki ne Halimatu Allah ya ji'kanta, Alhaji Abbas kinga wacce ya haifa nan ita da 'yan uwanta su Mussadiq.'' Ta nuna mata Saddiqa dake zaune a kusa da ita.
Wani irin kallo ta shiga binsu dashi tana girgiza kanta, ta rasa a'ina zata ajiye wannan babban al'amari a cikin zuciyarta, *Abbah Abbas* ba shine ya haife ta ba *Baba malam* ya haife ta? anya kuwa da gaske suke wannan maganar ko dai kawai suna so bukatarsu ta biya ne gurin ganin sun d'aura mata aure da *Ubanta* tabbas dole ne ta nemawa kanta mafita dan ita kam bata yarda da wannan maganar da suke ba.
Tana kallon Baba Talatu da Saddiqa suka suka futa daga d'akin, ta shiga girgiza kanta tana masifar mamakin a'lamarin, kwanciya tayi kan tabarmar dake shimfid'e a dakin ta shiga tunano rayuwar ta ta baya tare da mutanan data dauka a matsayin iyayenta.
*🗯️MADADI!!!💍*
_(Ba Haram Bane!!!)_
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi._
~~~~~~~~
~~~~~~~~
*SADAUKARWA GA DUK WANI A HALINA DAKE CIKIN WANNAN UNGUWA♥️*
*2*
*'Kofar Na'isa* Unguwa ce mai cike da d'umbun tarihi, duk wanda ya kwana ya tashi a cikin birnin kano ya san da zaman unguwar. 'kofar na isa unguwa ce ta malamai masana addini da kuma 'yan boko masu aiki da iliminsu, duk wanda yake mu'amula da d'an cikin unguwar zai gane cewar suna da wani irin quality wanda Allah yayi musu, saboda sun iya mu'amula da mutane sosai! akwai masu kudi a unguwar akwai marasa karfi a ciki, dai-dai gwargwado masu rufin asirin dake cikin unguwar suna taimakawa marasa shi mussaman da azimi suna hidima sosai da sosai da wuya kaji ance maka ga wata hatsaniya ta tashi a unguwar irin ta *Daba!* ko kuma *Sace-sace* dai-dai gwargwado suna bawa yaransu tarbiya had'e da ilimin addini dana boko!
Alhaji Sama'ila mai kwano wani attajirin mai kudi ne a cikin unguwar wanda yayi suna sosai dan idan kana neman gidansa daga bakin titi ka ambaci sunansa za'a nuna maka Alhaji Sama'ila mai kwano mutum ne mara ganin 'kyashi mai kaunar dan uwansa da ma'kotansa, Yana da 'yaya Uku kacal wanda matarsa Hajiya Abu ta haifa masa su, Biyu maza mace d'aya, amaryarsa mai suna Hajia Rabi bata ta'ba haihuwa ba tsayin shekarun da sukayi a tare! Yana zaune da ita haka dan shi mutum ne mai mi'ka al'amuransa ga Allah yasan tabbas Allah ne ke bada haihuwa kuma shine yake hanawa.
*Ramlatu* itace babba a cikin 'yayansa sai wanda yake bin ta, Abbas sai Alhasan shine na karshe! tunda su Abbas suka taso a cikin unguwar nan suka ga yanda mahaifinsu ke mu'amula arziki da makotansa sai suma suka fara kwantantawa, hakan yayi wa mahaifin nasu dadi sosai ya kuma 'kara nuna musu cewar hakan da sukeyi shine dai-dai dan cikin jinsin mutunan da Allah ya hallita a duniya babu wanda yafi wani a gurinsa sai wanda yafi bauta masa, kada su nuna sunfi karfin yin mu'amula da wanda suka fi rufin asiri, to babu shakka watarana Allah zai iya 'kwace damar dake hannunsu ya mi'kawa wanda suke ganin bai isa ba......Wannan dalilin ya sanya suka saki jikinsu da kowa suke mu'amula a cikin unguwar tamkar sauran mutane.
'Karamin gida ne madaidaici mai kofa gami da dakalin siminti a kofar gidan, gidan na kallon gate din gidan Alhaji Sama'ila hanya ce kawai ta raba tsakaninsu! Malam Baba shine mai wannan gidan, kamilin mutum nitsatstse mai kamala da dattako, malam baba mutum ne shi mai yawan ibadah da karatun al'kur'ani kusan duk azimin yana zaman tafsiri a kofar gidansa, inda Alhaji Sama'ila ke sawa ana fito da sadaka daga gidansa, akwai jituwa mai kyau a tsakaninsu dan sai nace halinsu ne yazo daya na gudun duniya shiyasa suke zaune lafiya da kowa, Alhaji Sama'ila ya dauki ragamar gidan Malam Baba a hannunsa ba wai dan shi malam din ya gaza ba Malam na futa sana'arsa kuma sa'i da lokaci al'amajiransa na kawo masa abun arziki gidansa babu yunwa ko kad'an! malam nada 'Yaya Uku wanda suka haifa tare da matarsa Baba Talatu Babban cikinsu shine Adamu wanda yaci sunan mahaifinsa sai suke kiransa da Magaji, Halimatu itace ta biyu sai kuma Naja'atu da tazo a karshe! Lokacin da suka haifeta har sun cire tsammani da sake haihuwa sai kuma Allah ya kawo cikinta, lokacin Halimatu na daf da kammala secondary skuul lokacin tana da shekara goma sha shida a duniya.
Tsakanin Abbas da Magaji akwai jituwa sosai suna abota mai kyau da tsabta komai nasu tare sukeyi karatu tare su d'inka kaya iri daya hula iri d'aya takalmi iri daya kai hatta da agogo iri daya suke daurawa! Sai kuma Allah yasa shekarunsu suka zo daya da juna yanzu haka suna matakin shekaru talatin da d'aya koda biyu Lokacin ne kuma iyayensu suka fara yi musu maganar aure dan sun riga sun mallaki hankalin kansu! kuma suna zuwa kasuwa suna harkokinsu, Alhaji Sama'ila yanzu ba ya fita kasuwa sosai su ya d'ora kan harkokinsa na yau da gobe! Alhaji Sama'ila nada shaguna sama da talatin a cikin kasuwar sabon gari kuma dukkanin rumfunan sa harkar siye da siyarwa akeyi a ciki, suna harkar kayan rufin gida da kofofi da ta gogi sannan kuma yana da gidajen bulo suna buga bulo da harhad'a intar lock da ties, mutane da yawa naci da sha a karkashin wannan bawan Allahn, to ganin 'Yayansa sun kai munzali ne yasa ya d'ora su kan harkokinsa na kasuwa kwata-kwata baya nuna bambanci tsakanin Abbas da Magaji Abinda zaiyi wa d'ansa Abbas shi yake wa Magaji, har jama'ar unguwa na surutu kan cewar ba haka kawai Baba Malam ya barshi ba wasu suna gani kamar yayi masa asiri ne domin ya mallake shi shida dukiyarsa, wannan cece kucen da mutane keyi bai dameshi ba, dan saboda yasan Malam baba ba zai ta'ba cutar dashi da zuriarsa ba.
Mama Ramlatu babbar Yaya gasu Abbas tayi aure a cikin unguwar dan gaba dasu kadan cikin unguwar Tudun wuzurci! wanda ta aura yana da rufin asiri dai-dai gwargwado amma tana da kishiya, Ramlatu wata irin mata ce mai izzah da ta'kama! bata da hali mai kyau! Tayi ta wulakanta kishiyarta kasancewar ta yar talaka gorin yau daban na gobe daban! a duk sanda Alhaji Sama'ila zaiyi mata aiken kud'i ko kuma tufafi sai ya had'a da kishiyarta kafin ta bawa kishiyarta sai ta gama yi mata gori sannan! Ita kuwa da yake mai hakuri ce sai dai kawai ta girgiza kai ta kyaleta, gabadaya Ramlatu bata dauko halin mahaifinta da 'yan uwanta ba.
Lokacin data haifi 'Danta na fari! sosai Mahaifinta ya gatantata daki guda aka cika mata da kayan barka, shi kuwa maigidan mota guda ta kayan abinci ya sauke masa, aikuwa Ramtalu ta samu abunda take so shiga take tana fita tana sakin habaici da gori! Cewar da abincin ubanta mutum ke rayuwa sannan kuma da tufafin ubanta mutum ke tun'kaho! Allah Sarki Sakina kishiyarta tasan da ita take, sai ta shiga daki taci kunanta ta koshi kuma ta dauki aniya kan cewar idan mijin nasu ya dawo zata fada masa abinda ke faruwa a gidan dan gaskiya ita ta gaji da wulakancin da matarsa keyi mata, gabadaya ta lura Ramlatu bata san mutunci ba ba kuma tasan mai kyautata mata ba, tunda ta haihu take hidima da ita ta kasa zama ta hutu kullum a tsaye take amma babu sannu bare nagode kullum cikin fada mata bakar magana take to gaskiya ta gaji hakurinta yazo karshe kudi ai ba hauka bane.
Maigidansu na dawowa bayan yaci a binci ya huta sai ta shiga fada masa abubuwan da suke ta faruwa a gidan wanda shi bai san dasu ba, tabbas ransa ya 'baci sosai kuma ya sheda halin matarsa Sakina tana da hakuri sosai da kawaici ba zata takali Ramla da rigima ba duk da cewar itace Uwargida amma ta hakura da komai burinta ta kawo zaman lafiya da daidaito a gidin! Yace."Kiyi hakuri insha Allahu zan sameta nayi mata fad'a amma kada irin haka ta sake faruwa kiyi shuru da bakin ki duk abinda ke faruwa tsakanin ki Ramla ki sameni ki fada mun zanyiwa tufkar hanci." Tace."To insha Allah."
Lokacin da ya shiga dakin Ramlatu tana zaune gefan gado taci uwar kwaliya da less an turo dauri gaban goshi kana kallonta zaka fahimci 'Yar Alaji ce hannunta da kunnata gami da wuyanta duk Gold ne sai walwali take...Zama yayi kusa da ita ya mika hannu ya kar'bi yaron dake hannunta da ta gama bashi nono ya tofa masa addua kana ya kwantar dashi ya fuskanceta.......Babu cikakkiyar walwala a tare dashi yace."Yanzu Ramlatu abinda kikewa Sakina a gidan nan ya dace."!? Wani irin shan kunu tayi ta kumbura fuska tace"Me nayi mata ashe! zaunar da kai tayi tana fad'a maka karya da gaskiya ko."? Yace."Abinda Sakina za tayi nasa ni haka kuma abinda Ramla za tayi nasa ni dukkanin ku nasan halin ko wacce ba wai ina so nace Sakina tafi ki a gurina ba A'a dik matsayin ku d'aya a zuciyata, amma ki sani abinda kikewa abokiyar zamanki bai dace ba! wace iri ce ke mai manta alkairi? menene Sakina ba tayi miki ba, ina cewa gabadaya sai da kika daina girki sai dai ta dafa ta kawo miki har d'aki kuma hakan bai hanaki kwana da miji ba! idan muguwa ce ai zata hanaki ki kwana dani ba tunda itace take girki amma ta dafa ta baki kici kina kwance kuma ki rasa sakayya da zaki mata sai irin wannan."!! Fashewa tayi da kuka tace"Shikkenan to ai ba sai ka futo fili ka nuna kafi kaunarta a kaina ba, amma meye haka daga zuwa babu tambayar ba'asi sai ka kama wasu maganganu ai bani ce nace tayi min girki ba ita taga zata iya ta dauka tayi ni ba burgeni tayi ba, kuma koda ba tayi min girki ba zansa a turo mai aiki daga gidanmu tazo ta kula dani har na haihu."
Yace."Ni dai na fad'a miki wallahi duk sanda kika 'kara ci mata fuska ko kikayi mata gori kan wani abu da aka kawo shi gidan nan sai ranki ya 'baci!! Cikin 'bacin rai tace"To ai shikkenan tunda uwata ce ita sai na kwanta ta takani saboda tana da daurin gindi a gurinka, akan me? kai da ita kuna cin arzikina amma kuma kuce sai nayi muku biyayya wallahi ba zai yuwu ba.""! Takarasa maganar tana buga cinya."! Cikin fusata yace."Zanyi maganin ki ai shashasha mara tunani meye abinci da kike gori a kansa, meye kuma tufafi wanda zasu lalace su barki da mutum! to zanje na samu Alajin da kaina zan fad'a masa bana bukatar k'wayar abincinsa a gidana ko ya aiko dashi na dawo sai an mayar." A fusace ya mike ya futa daga dakin....Shuru tayi tana tunani addua take kada Allah yasa yaje gurin mahaifinta da wannan maganar tabbas tasan idan yaji matsalar daga gurinta ne to babu shakka ranta sai ya 'baci.
Aikuwa misalin karfe biyar da rabi na yamma ta fito daga wanka kenan wani yaro ya shigo gidan yana fadin "Wai Ramlatu tazo soro mahaifinta ne yazo.
Gabanta ya fadi da sauri tasa kayanta ta futa da tabarma a hannunta, tana zuwa soron sai taga Sakina a durkushe suna gaisawa da Alhajin, shuru tayi tana jinsa yana bata hakuri dangane da abubuwan da suke faruwa, koda ta gaishe shi 'kin amsawa yayi ya rufe ta da fad'a sosai yace kuma ta bawa abokiyar zamanta hakuri! tana kuka ta shiga bawa Sakina hakuri! Tace " Babu komai ta mike ta shiga gidan, Alhaji ya kalleta da fad'in "Wallahi Sakina duk sanda mijinki ya sake kai 'karar ki gurina to babu ni babu ke! dama ashe mugun hali ne dake ko? to na kara jin na kawo muku wani abu gidan nan kiyiwa wani gori ranar sai na 'bata miki rai! Hakuri take bashi tana share hawaye, ransa ya a 'bace! ya futa daga soron ya barta a tsaye hannunta ri'ke da tabarma.......To tun daga ranar Sakina ta samu lafiya a gidan Yanzu Ramlatu ta daina yi mata gori da kallon banza amma dai duk da haka idan 'yan wulakancin na kusa tana ta'bawa sai dai kawai ta kau da kanta domin dai a zauna lafiya.
****
Irin kulawar da Abbas keyi kan Halimatu ya sanya iyayensu suka ga kamar sonta yake yi, shi kuma ba haka bane a zuciyarsa kawai yana tausaya mata ne a matsayinta na mace kuma mai nakasa, Halima bata da lafiyar k'afa sosai kafarta ta dama ta samu tawaya tun tana yarinya anyi magani na hausa dana Asibiti tafiyarta bata dai-dai ta ba, sai kawai suka hakura suka bar mata hallitarta da alama haka Ubangiji ya hallice ta, kafarta ta dama itace take da nakasa ta inda in tana tafiya take jefata, Amma a fuska Halima bata da muni kyakkyawa ce sosai mai madaidaicin tsayi! komai nata cikin nutsuwa take gudanar dashi.
Magaji ya fitar da matar aure A lokacin da iyayensu suka bukata, shi kuma Abbas din har yanzu ya rasa wacce zai tsayar a matsayin uwar 'yayansa! Mutum ne mai ruwan idon tsiya ko wace mace ba tayi masa ba! Da kyar da ya tsayar da Halisa a matsayin matar da zai aura gidansu na bayan layi! kuma Halisa kawar Halima ce tare ma suke tafiya makaranta, Allah sarki Halima tunda Taji labarin Abbas zai auri kawarta sai ta rasa nutsuwa komai nata ya tsaya cak! bata san tana sonsa ba sai da taji zaiyi aure! damuwa ta shiga sosai ta rage walwala har sai da iyayenta suka gane!
Da yake Baba Talatu macece mai saurin fahimtar abu nan da nan ta fahimci abinda ke damun 'yar tata! Ta sameta tayi mata fada da nasiha sosai tace"Kada ta janyowa kanta lalura mutum baya ta'ba auran mijin da bana sa ba, dan haka ta cigaba da addua Allah itama ya za'ba mata miji nagari." Duk da wannan nasihar da mahaifiyar ta tayi ma bai sanya ta daina damuwa ba, ita gani take waye zai aureta tana da nakasa (gurguwa) tana ganin watakila ma haka zata 'kare rayuwarta ba tayi aure ba.
Ita kuwa Halisa tunda ta fahimci Halima na shiga damuwa a duk sanda taje mata da maganar Abbas sai ta dauki d'amarar muzguna mata kullum kan hanyarsu ta zuwa isilamiyya sai tayi mata zancensa da irin soyayyar da sukeyi, Halima tayi shuru bata tanka mata, ita kuwa Halisa tai tayi mata dariya...........Akwai lokacin da Abbas yaje zance gurin Halisa ta tsare shi wai dole sai ya fad'a mata tsakaninsa da Halimatu! mamaki sosai ya kamashi Yace."Halimatu kanwata ce amma babu wata soyayya a tsakanina da ita." Halisa tace"To idan kai baka sonta ita tana sonka dan ba kaga halin damuwar da ta shiga ba lokacin da ta samu labarin abinda yake tsakanina da kai, dan haka gaskiya gwara kayi wa tufkar hanci tun kafin tafiyar tayi nisa duk da take kawata bana tunanin zan iya zaman kishi da ita."
Mamaki ya rufe shi da yake mutum ne mai tsare gida sai yace."Okey yanzu kina so ki nuna min ga yanda zanyi kenan? Idan na fahimce ki kina so kice ke ba zaki zauna da Halimatu ba a matsayin kishiya ko me."? Da sauri tace"Kwarai kuwa ai naga kusancin dake tsakanin gidanku da gidansu ne ina tunanin idan iyayenta suka fahimci halin da take ciki a kanka zasu ce ka aure ni kuma bana so gaskiya shiyasa nake so tun kafin tafiya tayi nisa kayi wa tufkar hanci." Ya girgiza kansa yana kallonta yace."Bari kiji Halisa ni ba irin mazan da mata zasu zauna suna tsarawa magana bane! abinda nasa kaina shi nake yi ke baki isa kice ga yanda zanyi ba, bani da ra'ayin zama da mace d'aya ki rubuta wannan ki ajiye bayan na aureki zan sake auran uku mutukar Allah ya bani iko saboda haka sai ki daura d'amarar zama da kishiya Halimatu kuma da kike magana na jawa kunne a kan tana sona to kin sanya ma naji sha'awar auranta zan aureku rana d'aya tunda dama 'kawayen juna ne." Da jin abinda ya fada sai ta mike a fusace! tace"Wallahi sai dai ka za'ba ko ni ko ita dan na rantse da girman Allah ba zanyi kishi da gurguwa ba."!!! Ya bude bakinsa yana kallonta cikin tsananin mamaki! lallai Halisa muguwar jahila ce yanxu me bambamcin muskini da mai lafiya? saboda jahilci da hauka kishi ma sai ta za'bi da wanda za tayi! Ya mike tsaye fuskarsa a murtuke yace." Tunda kin rantse ba zakiyi kishi da Halimatu ba to nima kuma ba zan janye 'kudirin dana dauka a kan auranta ba, saboda haka sai kije ki r'ike duk wani abu da nasa aka kawo miki da niyyar auranki na bar miki, ki samu wani mijin ki aura ni kuma zanje na auri muskiniya sai naga abinda zai cinye ni." Yana 'kare maganarsa ya futa daga soron gidan nasu. durkushewa tayi kasan soron ta fashe da kuka tana data sanin abinda ta aikata, tun farko ta lura Abbas din ba irin lusaran mazan da mace ke tursasawa bane yana da wani irin baud'addan hali tabbas kamar yanda ya fad'a din babu me sashi yayi abinda baiyi niyya ba mutukar ba iyayansa ba.
Tofa al'amarin yayi tsanani dan Abbas yaja tunga ya tsaya kan maganarsa kan cewar ya janye maganar auransa da Halisa saboda wasu dalilai saboda haka Halimatu itace matar da ya za'ba a matsayin uwar 'yayansa, Baba malam da Alhajinsa suka dinga bashi hakuri suna rarrashinsa, kan yayi hakuri ya auresu gabadaya, nan ya futo ya fada musu abunda ke faruwa! Yace."Halisa tayi mummunan furuci ga Halima kuma tayi izgili ga hallitar da Ubangiji yayi mata, dan haka to shi ba zai auri macan da zata dinga kokarin nuna masa yanda zaiyi ba, saboda haka shi ya janye maganar auranta Halimatu yake so. Baba Malam da Alhaji Sama'ila ba suji dadin faruwar al'amarin ba kasancewar mahaifin Halisa din mutumin kirki ne duk tare suke zama bakin titi ranar juma'a da yamma, dan haka sai suka yanke shawarar fada masa halin da ake ciki, suna kuma fatan Allah yasa hakan shi yafi alkairi. Koda mahaifin Halisa yaji yanda al'amarun suka kasance sai hankalinsa ya tashi sosai! babu shakka yarinyarsa tayi wa kanta wauta ba kad'an ba ta cutar da kanta kuma shi sam baiga laifin Abbas ba, da irin hukuncin da ya yanke yana bala'in son yaga jajurtaccen namiji mai tsayuwa kan magana daya.............Halisa tasha fada sosai gurin mahaifinta yace."Tunda ba zata auri mai mata ba to taje ta nemo wanda bashi da mata wanda kuma yayi mata alkawarin da ita kadai zai zauna, mutukar ta kawo masa komai illarsa da rashin nagartarsa to shi kuma zai daura mata aure dashi tunda itace taji ta gani.
Hankalinta a tashe ta nufi gidan Ramlatu, tana kuka ta zayyane mata abinda ke faruwa, a ganinta tinda Itace take gaba da Abbas din zata fada masa yaji tace dan Allah ta bashi hakuri yanzu ta yarda zata zauna da Halimatun a matsayin kishiyarta.......Ramlatu ta fusata ta dinga surutai tana aibata Halimatu da iyayenta a cewarta sam Abbas bai dace da auran muskiniya ba, saurayi dashi mai kyau da kudi da Ilimi yama za'ayi ya auri nakashshiya wacce take ci take sha a 'karkashin alfarmarsa dan haka sai ta shiga bawa Halisa hakuri tace ta kwantar da hankalinta za taje ta same shi, insha Allahu zai aure ta.........Da safe da wurwuri ta sauka a gidan kowa yayi mamakin zuwanta, ko gaisawa ba suyi da mutanan gidan ba ta nufi dakinsa, lokacin yana kokarin fitowa da shirin fita kasuwa! Yace."A'a barka da safiya kece a gidan." Tace."Eh gurinka nazo." Cike da mamaki yace."Gurina."? Tace"Eh yace."To Kinga ni yanzu sauri nake zan fita ki bari na dawo ko kuma ki koma gida da yamma idan na dawo zan shigo gidan naki sai naji abinda yake faruwa.
Cikin d'aga murya kamar wata uwarsa tace"Yanzu kai Abbas ka rasa wacce zaka aura sai Halima muskiniya nakashshiya ashe dama anan ruwan idonka zai 'kare gaskiya ka bani mamaki wallahi! Ga Yarinya mai hankali da nutsuwa 'yar gidan mutunci mai kaunarka amma kace ka fasa auranta ka koma gurin wata banza wacce take ci da sha a 'karkashin mahaifin.......'Daga mata hannunsa yayi fuskarsa a murtuke yace."Wallahi ban san sanda zakiyi hankali ba! kullum kina girma kina cin 'kasa! Yanzu ke ko kunya baki ji ba ki shigo har dakina kina daka min tsawa da nuna min yanda zanyi, haifata kikayi da zaki dinga yi min haka? ina ruwanki da aurena da Halimatu idan ba zaki saka albarka ba to kiyi shuru da bakin ki dan ni wallahi duk abin nan da kuke yi 'kara mun 'karfin gwiwa kukeyi babu gudu babu ja da baya sai na auri Halimatu in yaso ku kasheta saboda 'kiyayyya." Fashewa tayi da kuka tana nuna shi da hannu tace"Ni kake zagi ko Abbas dama ai baka da mutunci baka dauke ni a bakin komai ba kuma kai dama ba'a fada maka magana kaji." Yace."Da kinzo min da lisilama zan fahimce ki amma kinzo kina yi mun hayagaga! a kunne ai kin san halina ni ba'a haka dani." ratse ta yayi ya futa dada dakin, kallo ta bishi dashi tana jijjiga kanta, dama tun yana yaro bata iya lankwasa shi gwara Alhasan shi tana fada masa magana yaji amma banda Abbas futo na futo yake da ita girgiza kanta tayi ta futa daga dakin.
To haka al'amura sukayi ta kasancewa kowa na fadar albarkacin bakinsa kan wannan auran yayin da Abbas ya shafawa idonsa toka ya tsaya kai da fata sai da yaga auransa da Halimatu ya tabbata sannan hankalinsa ya kwanta.
Gida gudu biyu iri d'aya Alhaji Sama'ila ya mallakawa Abbas da Magaji Gidajen nasu na cikin unguwar *Gwangwazo* wajejen gidan Sarki.
kowanne ya tare da matarsa a ciki, Maryam matar Magaji 'yar cikin gari ce dai-dai gwargwado tana da hankali da nutsuwa shiyasa tasu tazo d'aya da Halimatu suke zamansu lafiya, kamar yanda mazajensu ke zaune da juna lafiya suma haka suke mutunta junanmu.
*3*
Halisa hankalinta yayi masifar tashi ganin irin uban gidan da'a kai Halimatu ga uban lefen da Abbas yayi mata atampopi da lesuka masu tsada kuka ta yini tana yi ta rasa nutsuwarta, mahaifiyar ma ba'kin ciki ne fal a cikinta zuciyarta tana aikace-aikacen ta na yau da kullum ta nayi wa 'yar tata fad'an wautar da tayi, in banda rashin tunani da kuma jahilci ina kai ina kushe hallitar Allah alhalin kaima baka wuce Allah ya mayar da kai wata hallitar ba, gashinan lokaci guda Allah ya juya al'amarinsa, tayi kuka tayi nadama gami da dana sani wanda hausawa suke kira da 'keya ce.
Zama mai tsafta ne yake wanzuwa a tsakanin Abbas da Halimatu! tawayarta bata hanata sauke hak'kokin mijinta dake kanta ba, Tana kula dashi sosai dan wani sa'in idan yaga tana hidima dashi har tausayi take bashi dalili yanayin tafiyarta da rashin kuzarinta ma abin tausayi ne, amma abin na bashi mamaki sosai! kafin ya dawo daga kasuwa ta gama komai na gida tayi masa kwalliya mai burgewa. duk sanda ya shigo gidan yayi tozali da ita wani farin ciki ne yake rufeshi, wai shin meye aibunta ne? Halimatu bata da wani abu ko nakasu a gurinsa tinda duk wasu hakkokinsa tana saukewa kwata-kwata nakasarta bata dameshi ba zahirinta yake so ba wani abu na jikinta ba, zaman lafiyar da suke da juna ya sanya yake ji a cikin ransa zai iya zama da ita har'karshen rayuwarsa.
*****
Wata goma cif da auransu Maryam matar Yayanta magaji ta haifi d'a namiji, murna da farin ciki a gurinta tamkar ita ta haihu kullum tana gidan tare da mai jego tayi ta hidima da ita da jinjirin 'Yan uwan Maryam suyi ta tausaya mata idan sunga ta wani abun na wahala sai suce ta zauna, murmushi kawai take musu ta rabu dasu idan kuma sun matsa mata takan ce dasu itafa babu abunda ba zata iya ba saboda haka su daina yi mata kallon mara lafiya da rashin kuzari! To suma ganin ranta ya 'baci yasa suka daina cewa da ita komai! kafin ma suzo ta shiga gidan ta gyara tsaf ta gyara yaron sannan ta had'awa maijego abun kari, sannan ta dawo gidanta tayi wanka ta shirya ta sake komawa, haka ta dinga zurga zurga har sai da akayi suna inda yaron yaci sunan Maigidanta Abbas sai take kiransa da Amir...................KullumAmir a hannunta yake wuni sai dare take mayar dashi ko kuma idan ya bukaci nono sannan, gabadaya dai ita Maryam haihuwar yaron tayi amma raino yana gurin Halimatu, idan ta dauki yaron tun safe to sai dare ita dashi.
Abbas bashi da matsala ta 'bangaran wannan dan shima mutum ne mai son yara duk sanda ya dawo ya tarar da ita tana fama da takwaransa yakan ji dadi yayi ta addua Allah suma ya basu nasu mai albarka.
Shakaru uku da auransu Halima bata ta'ba 'batan wata ba, gashi har anyiwa Amiri 'kanwa Ilham, Abbas tun yana daurewa dai har ya kasa hakuri yace ta shirya suje asibiti a dubasu, koda sukaje likita ya dubaso gabadayansu babu abunda ke damunsu kawai dai lokacin haihuwarsu ne baiyi ba, likita ya rubutu musu magani mai kyau yace suje suyi amfani dashi insha Allahu za'a dace.....Dukkaninsu a sanyaye suka koma gida, kuma ba suyi 'kasa a gwiwa ba suna amfani da maganin kuma suna sake kula da kansu.
Ramlatu kuwa a duk sanda suka had'u da Halimatu a taro sai ta zage ta tayi mata gorin rashin haihuwa, duk taro na family dinsu sai ta tara mata mutane tayi ta nuna ta tana fad'in mugwayen kalamai a kanta, wata irin tsana Ramlatu keyi wa Halima ko ta mece oho! dan akwai ranar da tazo har gida taci mata zarafi da fad'in sun gaji da jiran gawon shanu dan su duk irinsu babu mara haihuwa saboda haka sun gaji da daci da ita idan ba zata haihu ba to zasu kawo wacce zata cika musu gida da 'ya'ya.'
Wannan cin zarafin ya 'bata marai rai sosai ta yini tana kuka dan ki girki ba tayi ba ballanta tayi wanka ta shirya kamar yanda ta saba, koda maigidan ya dawo rasa gane kanta yayi, tambayar duniya tayi masa shuru sai kuka take yi, tsayin shekaru uku da auransu bai ta'ba fuskantar irin wannan matsalar daga gurinta ba, da kyar ya samu yayi wanka ya futo palon tana dai zaune a inda take tana kukan da take, zama yayi kusa da ita yana sake rarrashinta kan ta fada masa abinda ke faruwa, da kyar tayi masa magana tana hawaye gwanin tausayi tace ita taga ji tunda bata haihuwa ya 'kara aure ko kuma ya saketa dan cin zarafin da Yayarsa take mata ya isheta.
Ransa idan yayi dubu ya 'baci! shin wai me yake damun Ramlatu ne? ina ruwanta da matarsa ina kuma ruwanta da rashin haihuwarsa, idan zai mutu bai haihu ba bai dameta ba shine yaga zai iya zama da matarsa a haka, shi kam ya rasa wace irin 'kiyayya Ramla keyi wa Halimatu, hakuri ya bata sosai yace zai same ta yaja mata kunne kan kada ta sake zuwar masa gida.
Jin abinda ya fad'a yasa hankalinta ya tashi sai ta dinga bashi hakuri tana nuna masa illar abinda zai aikata, mutukar ya tunkari Ramlatu da wannan maganar to babu shakka ya sake rura wutar gaba mai zafi a tsakaninsu, kuma ita ba zata so su samu matsala da 'yar uwarsa ba, Nuna mata yayi ya hakura ba zaije gidan Ramlatun ba........Washe garin ranar kafin ya tafi kasuwa sai da ya tsaya gidan Ramlatun sukayi ta babu kyau babu dad'i a tsakaninsu, dan ya nuna mata mahimanci da matsayin Halima a gurinsa kuma ya nuna mata cewar itama ta tsaya a matsayinta na 'yar uwarsa mutukar tasan wata fitina ce zata kaita gidansa to kada ta sake zuwar masa gida, dan tuntuni shi ya riga yasan Allah ne ke bada haihuwa ba wani mahaluki ba! Ramlatu kuka taci ta 'koshi 'dan uwanta da take alfahari dashi shine yazo ya ci kata mutumci a gaban kishiryata lallai babu shakka dole sai ta tashi tsaye kan Halima dan da alama Iyayenta suna tsaye a kanta gurin ganin ta mallake mata d'an uwa.
*Kaji rigima ta Ramlatu ke ba uwar Abbas ba komai ba amma kina kishi da matarsa, Uwar miji aka sani da kishi da matar d'anta Uwar mijin ma irin wacce bata san abinda take ba.*
Abbas zuciyarsa wasai yaje kasuwa yayi harkokinsa......koda suka tashi daga kasuwar kai tsaya 'Kofar Na'isa suka nufa dan ji yake idan bai fad'awa mahaifiyarsu abunda Ramla ke masa ba za'a iya samun matsala nan gana gwara ya fada mata ta kira ta ta ja mata kunne.
Hajiya Abu ranta ya 'baci sosai tace"Ni dik abinda ke faruwa a tsakaninsu ban sani ba wallahi amma Wannan yarinya anyi babbar kwabo wallahi dan taga matar taka mai saukin hali ce shiyasa take mata cin kashi a ko'ina amma kayi hakuri ka kuma bawa Halimatun hakuri insha Allah zan aika yara har gidanta su kira min ita zan mata tsakani da matarka duk sanda ta sake zuwa gidanka domin ta kuntatawa matarka to babu shakka na samu labari da Alhaji maihifinku zan had'ata....
To tun daga wannan rana Halimatu ta samu lafiya Ramlatu ta saurara mata da gorin haihuwa ammafa sa'i da lokaci suka had'u a wata sabgar sai ta yar mata da habaici al'amarin Ramlatu sai addua.
*****
Halisa ce ta shiga kara kaina a gidan, mussaman ranaku guda biyu Juma'a da Lahadi ranakun da ta tabbatar da cewar maigidan nan bai futa sai taci uwar kwalliya ta sanyo turare mai 'kamshi tazo ta yini a gidan! idan sun had'u dashi tana nuna masa kamar babu wani abu a ranta, ta hakura dashi kawai ta zuwa ziyara ne gurin 'kawarta! Sai dai ya girgixa kansa kawai ya shareta dan shi ba yaro bane ballanta ta raina masa hankali.........Ita kuwa Halima zuciyarta ce ta shiga sa'ka mata wani abu! tana ganin tunda dai har yanzu Halisan bata da tsayayye mai zai hana ya aureta ya had'asu tunda ta lura da Halinsa tayi hankali kuma duk wasu alamu da take nunawa a kan mijin nata ta gane sabida shi take zuwa gidan........Koda ta sameshi da maganar cewa yayi zaiyi shawara zai fada mata kome ya yanke!
Kwana biyu ta sake tuntu'barsa da maganar ya dinga kallonta yana mamakinta yace."Ke kina ganin idan na auri Halisa na had'aku babu matsala kuma zaki iya zama da ita."?
Cikin farin ciki tace"Zan zauna da ita tsakani da Allah nasan ko ta nufe ni da sharri zai koma kanta tunda ban cuce ta ba, sannan kuma ina so ka aureta kaga tanan za'a tabbatar da rashin haihuwar mu shin waye yake da matsala tsakanina da kai."! Wannan magana da tayi sai ta sake sa masa 'kwarin gwiwa shima yana so ya tantance waye mara lafiya a cikinsu, kai tsaye ya tunkari Halisa sa maganar, ranar kamar ta zuba ruwa a 'kasa tasha dan farin ciki! ta dinga murna da godewa Allah! Yace."Ina so ki zauna lafiya da Halimatu dan da yawun bakinta nazo nan neman auraki kada ki shiga gidana ki tayar mana da hankali mun gina rayuwarmu cikin mai kyau da inganci" Halisa taji wani irin d'aci a ma'kogwaronta! wato ma ba'a karan kansa yazo neman auranta ba sai da izinin matarsa! 'kwafa tayi a cikin ranta! a zahiri kuwa cewa tayi" Haba Alhajina kada ka damu zan zauna lafiya da ita ai ko lokacin baya ma kuruciya ce ta janyo nayi wannan furucin amma ka daina kokwanto da shakku a kaina."
Yaji farin ciki ya kamashi dama can yana son Halisa halinta ne baya si to tunda dai yanzu tayi hankali zai aureta su zauna tare cikin inuwa daya.
Ba'a wani ja dogon lokaci ba aka d'aura aure Halisa ta tare a dakinta, da yake gidane mai dauke da bangare uku sai kowa ya dauki d'aya, kasancewar babu yara a gidan yasa maigidan ke bin 'Dakunan matayen nasa bai tare a nasa part ba din sai ranar da ya tara iyali tukkuna.
*🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~~~
*Wallahu galibun Ala amrihi👏🏻*
*4*
Sati biyu da shigowar Halisa gidan al'amura suka sauya, Halimatu ta kasa gane kan mijin nata gabad'aya Halisa ta ri'ke masa wuya ko yana kasuwa bashi da nutsuwar kirki mutukar bai dawo gida yayi tozali da ita ba, ranar girkin Halimatu sam bai da wani kuzari da walwala yakan dad'e ma a waje bai shigo ba, idan ma ya shigo d'in babu wani abun arziki da yake tsinana mata ba kwanciyarsa yake yi yai bacci! Halima ta shiga damuwa matsananciya ta rasa wanda zata samu ta fad'awa damuwarta gabakidaya Abbas ya sanja mata baya kula da ita sannan ba ya zama yaci abincinta kamar da idan tayi masa magana sai yace."A koshe yake shine dalili, Ita kuwa Halisa data fahimci rashin jituwa a tsakaninsu sai ta sake zage damtse gurin ganin ta sake mallakarsa, kissar yau daban ta gobe daban, duk abincin da zata bashi sai ta bad'e shi da magani abun mamaki kuma Yayarsa Ramlatu itace ke kawo mata maganin mata dana mallakar zuciyarsa, ita dai burinta Halimatu ta wulakanta a gidan.
Ranar Asabar har ya futa kasuwa da jaraba ta ciwo shi ya dawo gida, a maimakon ya nufi 'bangaran Halimatu tunda Girkinta ne sai kawai ya nufi bangaran Halisa, domin a yanda yake jin kansa yana ganin kamar Halimatu ba zata iya dashi ba, sai yanzu ya gane cewar Halisa ce dai-dai dashi dan tana iyawa da fitinarsa ita kuwa Halimatu rashin kuzarinta a ko'ina ma gwadawa take, ada hakan bai dame shi ba sai da ya auri Halisa ya gane cewar itace zata iya dashi, dan jaraba irin tashi baya tsayawa kan hallitar da Allah yayi masa duk karfi da kuzarinsa sai ya had'a da maganin 'karfin maza, kullum akwai wanda yake kawo musu magani kasuwa suyi ta siya suzo suna gallabar matansu da daddare.
Halisa duk da tasan ba girkinta bane bai hanata nuna masa kulawa ba kar'barsa tayi hannu biyu suka shiga d'aki suka shafe awa kusan hud'u suna abu daya............Halimatu ce ta shiga sashin tana sallama a palon taji shuru idanunta ne ya sauka kan hular maigidan da key dinsa na mota da kuma rigarsa kan kujera.
Tabbas kayan daya sa ya futa dashi ne a dakinta ya shirya kuma asali ma itace ta dauko masa kayan dole kuma tayi mamaki! kafin ta dawo daga tunaninta suka fito daga dakin a tare dashi da halisan daga shi sai gajeran wando, ji tayi yana fad'in "Zo ki bani abinci naci a gurguje na koma kasuwa na bar mutane na jirana." Had'a ido sukayi ita dashi! sai ya wani dake! kamar ba mara gaskiya ba, ya bude baki zaiyi magana kawai sai ta juya ta fita daga palon.
Jikinsa ne yayi sanyi ya zauna kan kujera yana kokarin mayar da kayansa, tabbas yasan wani abun da yake a gidan baya kyautawa sam be san meya sa ba yanzu kwata kwata baya damun cikakken satisfaction da Halimatu! bata da ni'ima kuma bata gamsar dashi kamar yanda Halisa ke gamsar dashi, gashi Halisa ta iya salo-salo shi kuma haki'kanin gaskiya yana so a dinga kula dashi kan shimfida.
Halisa ta fito daga kicin da abinci a hannunta, mikewa yayi da fad'in" Bana jin zan tsaya cin abincin nan zan koma kasuwa yanzu.''
"Haba dai don Allah ka zauna kaci gashi da zafinsa dama ban jima da gamawa ba." Girgiza kansa yayi ya nufi hanyar fita yana kallon agogon hannunsa da fad'in "Biyu da rabi yanzu na fada miki akwai mutanan dake jirana."
Sakin bakinta tayi ta bishi da kallo tana girgiza kai, da sauri kuma ta ajiye plate din abincin taje bakin window ta d'aga labule tana le'kensa, gani tayi ya nufi gurin Halimatu, shi da yace sauri yake yi to mai kuma ya kai shi gurin ta........Takaici kamar ya kasheta ta zauna kan kujera tana cizar yatsa.
Koda ya shiga palon samunta yayi zaune a kan kujera ta tsirawa guri guda ido tana kuka! yaji wani irin tausayinta ya kama shi, yana sonta baya son ganinta cikin damuwa shiyasa yaji wani irin rashin kuzari a jikinsa.
Kafin ya karasa inda take sai da ya tanadi kalaman da zai wanke kansa a gurinta.
Cikin wata mayaudariyar murya ya kira sunanta had'e da kamo hannunta, shuru tayi bata amsa ba, yace."Ki gafarce ni hakika nasan ni mai laifi ne a gurinki, kin san dan adam ajizi ne, ina tausaya miki ne shiyasa bana so na dinga d'ora miki lalurata."
Hannunta ta cire a cikin nasa tace"Wallahi ban ta'ba tsammanin haka daga gurinka ba, ashe dama duk wani abu da kake fad'a a baki ne? Halisa ko wata uku cikakku ba tayi ba ka sauya gabadaya ka daina kula dani baka sauke hakkina dake kanka, yausha rabon daka hada shimfida dani? ina tunanin tunda Halisa ta shigo gidan nan tsayin wata uku sai biyu ka kwanta dani shima sai dana nema sannan kuma abun har ya kai ka dinga satar kwanana kana kai mata, ina hankali da tunaninka suka tafi? idan ni bana ganinku ai Allah yana kallonku kuma kasan sai ya saka mun." Jiki na kyarma yace"Na sani wallahi kiyi hakuri ki dauki hakan a matsayin tsautsayi! na fada miki ajizanci ne irin na d'an adam amma ba zan sake ba kuma inaso kice kin yafe mun."
Tace" Sai ka fad'a mun sau nawa kana satar kwanana kana kai mata." Da sauri yace."Yau ne kawai shima kuma akashi aka samu." Ta goge hawayenta a hankali tace"Na yafe maka amma dan Allah ka dinga kiyayewa kana kokarin sauke hakkina dake kanka.
Yace."Insha Allah ki tayani addua nima cikin 'yan kwanakin nan wani iri nake jina." Tace."Insha Allah zan cigaba dayi maka addua harkarshen numfashina." Mikewa yayi yana fadin." Muje ki rakani ko." Ta mike tana mirmushi tamkar baiyi mata laifi ba suka jera tare suka futa har inda motarsa take.
Halisa har yanzu na tsaye bakin window tana kallonsu suka futo suka tsaya a bakin mota suna magana! gani tayi Halimatun na dariya tana kallonsa shi kuma ya kamo fuskarta ya sumbuta, ya shiga mota hade da daga mata hannu.......Zaman da'baro tayi kan kujera tana hargitsa gashin kanta, kai jama'a!! wai shin Halimatu wace irin macace ne? wacce bata da zuciya bata kishin kanta! ai idan itace mijinta ya saci kwananta ya kaiwa kishiyarta ranar sai ta kusa kashe shi da tashin hankali, amma ita duba dariya ma take harda rakoshi bakin mota.
Wayarta ta dauka ta kira Yaya Ramlatu! ta daga wayar suka gaisa, Murya na rawa tace"Yaya al'amura fa sun dagule wallahi! ban san wane irin so Abbas kewa Halimatu ba! daga aiki ya fara sai kuma ya karye! gashi itama kamar mayya duk abinda za'ayi mata bata fushi, 'karewa ma kwananta ya kawo min a maimakon taji haushi sai ma take dariya harda rakoshi bakin mota." Yaya Ramlatu ta shiga girgiza kanta tace" Nasha fad'a miki Uwarta da Ubanta ba'a zaune suke ba dan ita bata da kuzari da 'kafar yawon gidajen malamai Ubanta 'kasurgumin dan tsubbu ne duk wasu asararai yana dasu, ina kyautata zaton yayi aiki mai zafi akan Abbas din, amma duk yanda zanyi sai nayi na wargatsa shirinsu." Halisa tace"Ni wallahi yanzu babban burina ta fita ta bar min gidana sannan naga na samu ciki na haihu." Ramlatu tace'' Kada ki damu zaki haihu ita kuma zata fita ta bar miki gidanki zaki zauna tare da 'yayanki insha Allah zanyi miki kokari akan wannan lamarin." Tace"Nagode Yaya Ramlatu! Sallama sukayi Ramlatu tace"Yauwa dama inaso kiyi dubara a gurin mijin naki ki samu 'yan kudi masu kauri sai ki kawo min dasu nake so naje a taimaka miki." Tace"Insha Allah zanyi kokari kamar nawa ." Tace"Dubu hamsin ma ta isa."
Ajiyar zuciya ta sauke tace" Zan duba inda yake ajiyar kudinsa idan ya bar key din a jiki zan dauko zan kawo miki anjima dan nafi so ayi komai da zafi-zafi."
Ramlatu tace"A'a kada ki daukar masa kudi ya gane fa." Tace"Ai suna da yawa ba zai gane ba tunda kusan kullum sai ya shigo dasu kafin ya kai banki." Tace"To shikkenan ina sauraranki idan kin kawo min ni kuma nayi miki al'kawari komai yamma zan tafi gidan *Yar Sa'adu."*
Halimatu kuwa zuciyarta fes ta futo daga bangaranta ta nufi na Halisa domin yi mata sallama tana so taje su gaisa da iyayenta sannan kuma ta shiga gidan Dan uwanta su gaisa da matarsa Maryam, abinda yasa Maryam ta rage shigowa gidan saboda zuwan Halisa dan bata so wata hatsaniya ta tashi a tsakaninsu sunanta ya fito, dama kuma ta lura da irin wulakantaccen kallon da Halisa ke mata, shiyasa gabadaya ta dauke kafarta daga gidan, sai dai sa'i da lokaci ita Halimatun ta shiga su gaisa.
Halisa na kokarin zaro kudi cikin drowar taji sallamar Halimatu a palonta, da sauri ta zabura ta futo palon tana kallonta, Halimatu ta fahimci rashin gaskiya a tare da ita, girgiza kanta tayi tace"Halisa zan je gida mu gaisa dasu Baba Malam sai nadawo." Cikin ya'ke tace"To sai kin dawo dan Allah ki mi'ka min gaisuwata gurinsu."
Tace"Zasuji insha Allah." Juyawa tayi ta fita, Halisan ta rakata da wulakantaccan kallo tana cin laya a kanta.....Tsaki taja ta koma dakin ta cigaba da ciku-cikun dauko kudin daga drowar da take a kulle dan ba taga key din ba amma dan jaraba sai da tasan yanda tayi ta zura hannunta ta zaro kudin duk sun ya mutse, da kyar ta samu ta ciro dubu talatin da biyar ta hakura haka, kaya ta sanja ta zuba kudin a jaka tasa kai ta fita daga gidan ba tare da maigidan ya sani ba.
Baba Malam da Baba Talatu sunji dadin zuwan 'yar tasu duk sanda ta kai musu ziyara sukan yi murna da farin ciki ganinta cikin nutsuwa da wadata!
Bayan taci abinci sai suka shiga hira da mahaifiyarta Na'ajatu ce ta shigo gidan hannunta rike da buhun kayan wasanta duk tayi bud'u-bud'u da jikinta, Baba Talatu ta harareta da fadin" Kin gama yawon wasan naki yunwar cikin ki ta koro ki ko."'? Zum'bura bakinta tayi tana kokarin yin kuka. Baba Talatu tace"Ai sai ki nemi me baki abinci dan banyi dake ba dama na fada miki tunda baki zuwa makaranta to zakiyi ta zama da yunwa." Kuka ta fashe dashi ta jefar fa buhun kayan wasan nata tana kallon Yayar tata. Halima ta riko hannunta tana rarrashinta, kwanciya tayi a jikinta tana kuka cikin rashin iya magana sosai tace"Ni ba zani makaranta malam ya dakeni ba kuma sai an bani abincina." Halimatu ta dinga dariya tana kallonsu suna drama Baba Talatu tace"To sai naga wanda zai baki abinci a gidan nan." Kuka take sosai tana fad'in "Ni sai an bani abinci yunwa nake ji."
Halimatu tace"Yi shuru autar Baba Ni da kaina zan baki abinci ki fad'a min ma me kike so na siya miki kici ki kyalewa Baba abincinta."
Hawaye tagoge tana kallonta tace"Zan biki gidanki ki dinga bani shayi da bredi ita Baba Talatu kullum koko da kosai take bani, sannan bata bani na siyo alawa da biscuit. " Baba Talatu ta ri'ke ha'ba! tana fad'in "Ikon Allah! Wato Naja'atu abinda zakiyi mana kenan! kullum fa sai na dafa miki shayi malam ya siyi miki bredi da madara ga kwai amma kice koko da kosai nake baki." ? Halimatu tace"Gaskiya Baba bakya ji da wannan autar taki! dubeta dan Allah yanda kika barta tayi daud'a dubi kitson kanta duk ya tsufa, gashi bakya bata ta siyi sweet da biscuit saboda haka ni zan tafi da ita gidana, zaki bini ko Auta."!? tafada tana kallonta, Da sauri ta daga kanta tana dariya.....Baba Talatu ta gyara zamanta tana ta'be baki tace"Ai sai kuje dama nima na gaji da bari bari yarinya kullum nakan layi tana yawo ta'ki zama a makaranta malam na kaita kafin ya dawo gida ta rigashi, ki tafi da ita ku sata a makaranta tayi karatu watakila idan taga babu idanmu zata zauna a makarantar.
Halima tace"Aikuwa dai bari Baba Malam ya shigo na fada masa.......To koda Baba malam yaji kudirin Halima na tafiya da Naja'atu gidanta, be'ki ba yace dai idan taga da akwai matsala to ta dawo da ita." Baba Talatu ta hada mata kayanta tsaf suka tafi.
*Wannan shine mafarin dawowar Naja'atu hannun 'Yar uwarta, a lokacin tana da shekaru hud'u a duniya dalili kenan da yasa ta girma da tunanin cewar Abba Abbas da Halimatu sune suka haifeta.*
Ita kuwa Halisa koda ta fita kai tsaye tudun wuzurci ta nufa gidan Yaya Ramlatu! basu ja dogon lokaci ba suka dauki hanyar gidan *'Yar Sa'adu* abin mamaki mata ne dan'kam! a gidan! d'aki guda idan waccan ta shiga ta fito sai waccan ma ta shiga ta fito har akazo kansu! koda suka shiga dakin *'Yar Sa'adu* na zaune kan wata kujera katuwar macace mai ki'ba taci uwar kwalliya ga hancinta da wani abu mai kyalli a jiki, hannu da wuyanta duk gold ne! taci ubab bleecig kana ganinta kaga 'yar duniya, suka gaisa da juna, Halisa sai kallon dakin takeyi ganin ko ina manne da hotonan mace da namiji tsirara! sannan ga wasu manya manyan drowars ko wanne kayan mata ne a cike a gurin kala-kala! Yaya Ramlatu ta ciro kudin jakarta dubu talatin da biyar ta zube gaban *'Yar sa'adu* tace" Uwar dakina wannan itace matar 'kanina da nake baki labari gata nan na kawo miki ita don Allah ki san maganin da zaki bata wanda zai sanya ta mallaki mijinta ita kad'ai."
*'Yar Sa'adu* tasa dariya ta bata hannu suka tafa tace"Lallai 'kawata kina ji da matar 'kanin nan naki! Allah yasa idan ta samu duniya ta tuna dake, akwai wata mallaka da zan bata! Amma gaskiya tana da tsada kuma naga kudin da kuka ajiye bashi da yawa! Wannan mallakar tana da sirri dan da yawa mutane sunyi amfani da ita sun tabbatar da gaskiyar maganata, ina zaune ake zuwa anayi min tukwuci da kujerar makka had'e da gida da filaye, dan haka idan kuna da bukatar na baku ita to gaskiya zaku ajiye min dubu dari biyu."
Halisa tayi saurin kallonta tana marairaice fuska tace"Dan Allah ki bani wallahi nayi miki al'kawarin idan bukata tabiya zanzo na kawo miki kudinki har inda kike." Ramlatu tace"Eh kwarai kuwa ni zan zama sheda a tsakaninku tunda dai kin tabbatar da ingantuwar maganinki to ki amince ki bamu insha Allah cikin sati guda za'a kawo miki sauran kudinki."
*'Yar Sa'adu* tayi shuru tana tunani! Wani littafi ta dauko ta mikawa Halisa da biro tace"To na amince zan baki amma kisa hannu! sannan ki rubuta abinda kika bani da farko."
Halisa ta kar'ba da sauri tasa hannu! sannan ta rubuta kudin data bayar dubu talatin da biyar! *'Yar Sa'adu* ta kar'ba ta ajiye, sannan ta mike taje ta dauko mata wata 'yar mitsitsiyar kwalbar fiya-fiya! wani abu mai mai'ko da yau'ki! ne a ciki tace"Gashinan duk sanda zakuyi auratayya da mijinki to sai ki lakata kad'an a d'an yatsan ki! sai ki tofa maliki yaumin dini 'kafa takwas a jiki sai ki lakata maganin a gabanki, kafin kwana biyu zaki bani labari." Halisa ta dinga washe bakinta tana godiya, *'Yar Sa'adu* tace''Mijin ki zai zame miki kaska sannan ba'kin ciki zai kashe kishiyarki wannan shine la'kanin maganin." Wani sanyi ya sauka a zuciyoyinsu jin abinda 'Yar Sa'adu ta fada, godiya sukayi mata sosai tare da al'kawarin insha Allahu cikin satin nan zasu kawo mata kud'inta........
*Ayar Allah da ita ake wasa, wai kuma mutum yace yana so yaga dai-dai a rayuwarsa, Ubangiji Allah ka karemu daga fad'awa halaka.
*🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~~~
*5*
Kamar dai yanda 'Yar Sa'adu tafad'a musu hakane ya kasance, kwana biyu zamantakewar gidan ta samu tangard'a! Abbas hankalinsa ya dauke gabad'aya baya ganin kowa a gabansa sai Halisa! Komai ta tambayeshi baya yi mata musu da gardama, kuma koda ya duba gurin da yake ajiyar kudinsa yaga ba yanda yake ba, da yayi mata magana kai tsaye tace"Ita ta dauka tayi ba'ki ta sallamesu! shuru yayi mata baice komai ba, tana ganin ya shiga toilet ta bude drowr ta dauki dauri d'aya ta mayar ta rufe! Sai da ya fita sannan ta lissafa kudin dubu dari ne, kai tsaye ta yafa mayafinta ta nufi gidan Yaya Ramlatu da kudin, Gidan 'Yar Sa'adu suka nufa, nan Halisa ta zauna tayi ta basu labarin yanda al'amura suka kasance ta dinga basu labarin irin abun da Abbas din yake mata idan suna kwance da daddare! 'Yar Sa'adu da Ramlatu suka dinga dariya suna tafawa! ita kuwa Halisa tace"Ai gaskiya maganin nan karshene kuma yaci kudinsa, dan a tsakanin kwanaki bakwai d'in nan sai da na samu kudi a gurin sa sama da dubu dari! kullum in zai futa sai na tambayeshi kudi kuma sai ya bani! baya tambaya me zanyi na lura yana tsoron kada dare yayi yazo da wata magana nace masa wani abu daban." 'Yar Sa'adu ta gyara zamanta kan kujera tana dariya had'e da 'kas-'kas! da cingum din bakinta, tace"Ke waye ya fad'a miki dama mata na zama yanzu! ai yanzu dama na hannuki kiyi kiyi ki samu abunda kika samu kuma ba zama zakiyi ba idan maganin ya kare ki sake zuwa ki siyi wani."
Halisa tace"Insha Allahu ai na gane hanya kuma." Cike da farin ciki sukayi sallama da 'yar Sa'adu suka nufo gida.
****
Bayan wata uku kullum jiya iya yau a gidan, Halisa ta k'wace miji gabadaya Halimatu ita dashi sai ido da gaisuwa, Kullum kafin ya futa zai shigo su gaisawa ya zauna suyi ta wasa da Naja'atu! yana kaunar yarinyar sosai kasancewar sa mutum mai son 'yaya gashi har yanzu Allah bai bashi ba! Itama Naja'atu d'an zamanta a gidan ta saba dashi sosai idan ya shigo zuwa take ta zauna a cinyarsa tayi tai masa labarin makaranta da kawayenta shi kuma ya dinga biye mata, dan wataran gurin tsayawa sauraran shirmenta har makara yake a kasuwa, Idan kuwa zai futa sai ya tambaye ta me take so ya siyo mata, sautu iri-iri take masa na kayan wasa dasu biscuit da chocolate, aikuwa duk abinda tace ya siyo mata baya mancewa sai ya tsaya a danja ya siya mata ya shiga ya kai mata, wannan abinda yake yana masifar 'batawa Halisa rai! ta tsani taga yana nuna kulawarsa kan yarinyar ko kadan tana so kamar yanda ya banzatar da Halimatun to ya kasance itama yarinyar itama ya daina kulawa da ita, Idan tana fushi kan abinda yake wa Naja'atun har mamaki take bashi, rabuwa yake da ita idan tayi ta gaji sai ta hakura.
Ita kuwa Halimatu ganin yanda yake kula da kanwarta yasa ta rage jin zafinsa a zuciyarta, addua takeyi kullum Allah ya karkato da hankalinsa kanta tabbas tasan abinda yake yi ba a hayyacinsa yake ba, tunda tasan irin kauna da son da yake mata, babu shakka Halisa ba'a haka ta barshi ba.
To Haka dai Halimatu ta cigaba da zaman hakuri a gidan, tana ji tana gani mijinta yafi karfinta dan sai yayi wata biyu uku bai kwanta da ita gabadaya an cire masa sha'awarta a cikin zuciyarsa.
*IDAN RABO YA RANTSE*
Ranar Juma'a bayan an sauko daga massalaci ya dawo gida a gajiya ga kuma sha'awar dake damunsa tun daran jiya dan kwana sukayi rigima da Halisa ta yanko masa uban kudi wai sai ya bata sannan zata amince ya biya bukatarsa, shi kuma yace ba zai bayar ba sai ta fada masa abinda za tayi dasu, nan ta shiga inda-inda! ya fahimci bata da hujja sai yace ba zai bayar ba, shine tayi fushi tace itama ba zata bashi kanta ba, da yake mutum ne mai zuciya kawai sai ya kyaleta ammafa daurewa kawai yake dan baida hakuri ta wannan 'bangaran......Washe garin ranar Halisa naganin ya futa itama ta shirya ta futa itama ta nufi gidan Yaya Ramla domin tafada mata abinda yake faruwa.......koda ya shigo gidan kai tsaye gurin Halisa ya nufa gabadaya idonsa a rufe yake bukatarsa kawai yake so ta biya yanzu ya amince zai bata kudin mutukar dai zata biya masa bukata.
Ya dubata ciki da waje bata gurin, rai a 'bace ya nufi gurin Halimatu, suna Tare! Da Naja'atu a palo tana koya mata karatu ya shigo bakinsa dauke da sallama!
Naja'atu ta mike a guje taje ta d'ane jikinsa tana fad'in "Oyoyo Abbana."! Dariya yasa ya mi'ka mata kumatunsa kamar yanda suka saba! aikuwa ta manna masa kiss a gurin! shima yayi mata sannan ya sauketa kasa, yana d'an ya mutsa fuska ya kalli Halimatu dake ta faman yi musu dariya! hannunsa ya mi'ka mata da fad'in " Ranki ya dad'e zo muje daki ina da magana." Halimatu ta tsira masa ido tana kallonsa da mamaki a tare da ita!
Gira ya daga mata yana yi mata wani irin kallo. Girgiza kanta tayi ta sunkuyar da kanta 'kasa, lallai wato sai yau take da amfani a gurinsa kenan! duk sanda yake cikin halin sha'awa tana ganewa.
Ji tayi ya kamo hannunta ya mikar da ita tsaye, gudun kada yayi abun kunya a gaban Yarinya yasa tayi saurin cire hannunta tace"Kaje ganin nan zan shigo." Babu kunya ya nufi bedroom dinta yana wata irin tafiya.
Zama tayi kan kujera tana kallon Naja'atu na rubutunta sai da ta tabbatar abinda take ya dauke mata hankali sannan ta mike a nutse ta bishi dakin.
Wannan had'uwar tasu ta firgita Halimatu gabad'aya mijin nata ya sanja mata hallitarsa ma kamar ta sauya, ya zage karfi a kanta yana bugunta babu tausayi da jin 'kai irin wanda yake mata, sosai yake sarrafata salo-salo duk ya fice daga hayyacinsa itama sai wuya yake bata, kukan wahala take masa tana bashi hakuri ya saurara mata haka, sam ba haka ya saba yin mu'amula da ita ba, da kyar ya saurara mata ya kwanta gefanta yana maida numfashi........To tun daga wannan had'uwar Ubangiji ya zartar da ikonsa ciki ya shiga ya zauna daram a mahaifar Halimatu, cikin kuma da bai bayyana kansa ba sai da yayi wata hudu tukkuna sannan Allah ya bayyana shi, saboda ita kanta Halimatu bata san da ciki a jikinta ba kasancewar ba ko wane wata take al'ada ba shiyasa duk ta rikirkice, ta dinga kokwanto a kan ciki.......Kai tsaye asibiti ya dauketa sukaje, likita ta dubata sosai dan har scanning akayi mata ciki wata hudu kuma yana cikin koshin lafiya. Abbas ya rasa inda zai saka kansa saboda farin ciki, tun a mota ya kira wayar mahaifiyarsa ya sheda mata abinda ke faruwa, Hajiya Abu tayi murna da farin ciki sosai ta kuma yi addua kan Allah ya sauke ta lafiya........Halisa kwanan kuka tayi da taji labari wai Halimatu nada ciki, ya akayi haka ta faru? wai dama mijin nata ashe yana lallabawa gurin Haliman yana biya bukatarsa bata sani ba, lallai zai shigo ya sameta.......Shi kuwa da farin ciki a tare dashi yake sake jaddada mata k'aruwar da ya samu! ta hasala! sosai ta dinga zazzaga masa rashin kunya kamar zata zage shi! aikuwa ta fuskanci 'bacin rai! dan lafiyayyun marika tasha wanda hakan bai ta'ba faruwa ba tsayin shekarun auransu, Yayi mata gargadi sosai kan tsaurin idon da take masa kana kuma ya dauke mata wuta gabadaya ya daina kulata, ya tare sashen Halimatu!!
Halisa ta zama tamkar mahaukaciya gashi *'Yar Sa'adu* bata gari ta tafi Nijar dama 'Yar can ce kullum ita kenan a tafe gurin zuwa gidan Yaya Ramlatu, suna tattauna yanda zasu 'bulluwa al'amarin, Ramlatu tsoron zuwa gidan takeyi saboda tasan halin 'Kanin nata zai iya kunyatata shiyasa ta zauna a gida, Halisan na zuwa inda take................Sau uku yana dawowa gida ya tarar bata nan a'lamarin da ya fusata shi sosai, ya tsaya harabar gidan nashi yana kai kawo kana ganinsa kasan ransa a 'bace yake, Tana shigowa ya buga mata tsawa da fad'in "Ta koma inda ta fito! gabanta ne ya fad'i baki na rawa tace''Wallahi naj.......Hannu ya daga mata yace." Bana bukatar naji komai daga bakinki sau uku ina dawowa gida bakya nan ina kike zuwa ba tare da na sani ba? saboda haka ki fuce min daga gida sai nazo gidanku inaso kafin nazo ki fada musu inda kike zuwa."
Halisa ganin yayi fushin mai tsanani yasa ta juya jiki a sanyaye ta futa daga gidan, kai tsaye gidansu ta nufa tana kuka.
A takaice dai sai da Halisa tayi sati biyu a gidansu sannan Yaje yayi bikon ta iyayenta ran su ya 'baci sosai jin irin abinda take aikatawa na fita yawo ba tare da izinin mijinta ba mahaifinta yace da Abbas duk sanda ta sake futa bata fada masa ba to ya sanar masa sai ranta ya 'baci sosai! Halisa ta tsorata sosai d'a zaman da tayi a gidansu har jikinta ya soma sanyi tsayin sati biyu da tayi a gidan nasu ji take tamkar shekara biyu tayi, ganin ya shere ta da ita al'amarinta yasa jikinta yayi sanyi tana addua kada Allah yasa yace zai saketa.....To tunda ta samu yanzu ya mayar da ita sai ta dauki aniyar gyara kuskuranta a gurinsa amma dai duk da haka ba zata fasa yiwa Halima zagon 'kasa ba.
Koda ta dawo gidan d kafin ya sakar mata fuska sai da ta dade tukkuna sannan ya warware gabadaya, tun daga sannan ta kiyaye abinda zai dugunzuma masa zuciya wanda zai haifar da sa'bani tsakaninsu har ta kaishi ga korata gidansu.
***
Cikin Halimatu nada wata bakwai Allah ya bawa Halisa nata, Halisa aka dinga murna da zumudi ana iyayi! shi kuwa maigidan ya dinga biye mata da duk abinda take so burinsa kawai yaga matayen nasa sun haihu lafiya shima ya shiga sahun mutanan da ake kira da Abbah, duk da sunan da Naja'atu ke kiransa dashi kenan Abbana, ko Abban Naja, a duk lokacin da zata kirashi da sunan yakan ji wani iri dan saboda yasan ba shine ya haifeta shi dai yafi bukatar 'yayansa na cikinsa su kirashi da wannan suna.
*****
Lafiya lau Halimatu ta haihu inda ta haifi 'yar ta mace ta d'an d'ebo kammanin mahaifinta gurin hasken fata gami da siririn hanci, Abbas mai kyau ne sosai irin namijin da mata keso yana da haske da cikin zati dogo ne amma ba sosai ba, yana da manya ido da dogon hanci wanda ya kyata masa fuskarsa, amma kuma bashi da fara'a da saurin sabo! Mutum daya ya amince dashi cikin abokansa shine Magaji Yayan matarsa kenan Abba magaji yasan sirrinsa kamar yanda shima yasan nasa...........Halisa ganin Halima ta haifi mace sai ta dinga addua Allah yasa ita ta haifi namiji dan tasan farin cikin da mijin nasu zaiyi sai yafi wanda yake yi a yanzu, hankalinta na masifar tashi a dik sanda taga ya shiga gurin Haliman ya jima bai fito takan shiga tashin hankali da damuwa saboda tasan yana can yana shiriritar da ya saba da shegiyar yarinyar nan Naja'atu da Babynsa wacce ya sanyawa suna Fatima amma sai suke kiranta da *Saddiqa* dalili kenan da ya sanya take Allah Allah itama ta haihu itama taga yana nuna kulawarsa a kan d'anta.
Haihuwar *Saddiqa* ta janyo masa bud'i da alkairai da yawa, harkokin kasuwancinsa suka bude sosai yake harkar gwangila na gina gidaje da ma'aikatu da sauransu........Wani 'katon gida yake ginawa a cikin unguwar *Danbare* sabuwar unguwa ce da masu kudi suka siyeta suke ta gasar gidana gida a gurin, gaskiya gidan da yake idan aka gama aikinsa babu shakka zai zama abun kallo a gurin jama'a.
Halisa ta haihu lafiya lau ta haifi namiji kamar yanda Scanning ya nuna mata, sai dai kuma cikin ikon Allah kwanan yaron d'aya a duniya ya koma.....Ihu! ta dinga zabgawa tana kuka dan rashin tawakkali cewa take wallahi Halima ce tayi mata asiri d'anta ya mutu saboda tana bakin cikin ita bata haifi d'a namiji ba.
Abba Abbas tun yana rarrashinta har ta si'ke shi haushinta ya rufeshi, ya shiga nuna mata illar abinda takeyi, Allah ne ya bata kuma ya kar'bi abinsa dan me zata d'orawa wani! sai da yayi mata kaca-kaca! sannan ta daina ikirarin cewar Halima ce tayi mata asiri.
***
Bayan shekaru uku Halimatu ta sake haihuwa inda ta haifi 'Da namiji! Wanda wannan haihuwar ta janyo tashin hankali sosai a gidan dan iskokai Halisa ta dinga tayarwa na 'karya dana gaskiya tana yun'kurin kashe maijego da jaririnta......Babu arziki ya tarkata ta ya kaita gidansu dan al'amarin yafi karfinsa haka kawai yana ji yana gani ta illata masa d'ansa.
Ashe iskanci ne Halisa na ganinta a gidansu, sai ta dawo hayyacinta mussaman da mahaifinta ya samo malamai, masu ru'kiya suka dinga jibgarta, babu arziki ta dai-dai ta nutsuwarta ta dinga kiransa a waya yazo ya dauketa taji sauki!
Shi kuwa dama tuntuni ya yanke shawara kan cewar zai raba musu gurin zama, dan gudun aikata mummanan aiki idan baya nan shima ya fahimci duk wani abu da Halinsan keyi sharri ne da ba'kin kishi da ganin kyashi!
Gidansa dake *'Dan bare* suka tare shida Halimatu da 'yayansa kana yasa aka gyarawa Halisan wanda suka bari ta zauna a ciki yana ganin hakan shine yafi alkairi a tare dasu baki daya...
Wannan al'amari ya sanya zuciyar Halisa kusan bugawa, gidan da take kulafucin zama a cikinsa shine zai ce ba zai je da itaba, kuka taci ta koshi tana tunanin mafita babu shakka ta ko'ina Halima tayi mata zarra! ta haihu har sau biyu kuma ta tare a sabon gida. tabbas dole ne ta nemawa kanta mafita yanzu ne ta sake gazgata maganar Yaya Ramlatu inda take cewa mugun sihiri iyayen Halimatu sukayi akan Mijin nata, itama idan hakane to tabbas zama bai kama ta ba.
To da yake yanzu bata da matsalar kudi yasa ta d'auki d'amarar shiga malamai domin bukatarta ta biya, duk ranar da ya kasance ba a gidanta yake ba to idan ta fita tun safe sai yamma zata dawo gida tare suke yawace yawacen malamansu da Yayar mijin nata.....Yaya Ramlatu bata da matsala saboda mijinta matafiyi ne shiyasa takeyin abinda take so a gidan, haka zata fuce ta watsar da 'yayanta a tsakar gida, kishiyarta Sakina mutuniyar kirki ita ke mata dawainiya da 'yayanta tayi da nata, tabbas albasa ba tayi halin ruwa ba, dan da Ramlatu ta gado halin iyayen nata to ba zata aikata abinda take ba.
*🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~~~
*PEGEN YAU NAKU NE*
*My Son Najib Sa'id*
*Abue Sale alqurami*
*Bashir Saleh*
*Umar Abbas Yusif*
*Muhammad Karim*
Ina mutukar godiya da kulawarku a kaina da 'kokarin yi min sharing ina rokon Allah ya sadaku da alkairin duniya dana lahira Allah ya za'ba muku abinda yafi alkairi a rayuwarku👏🏻
~~~~~~~~~~~~~~~
*6*
A takaice dai duk wannan fad'in tashin dasu Halisa sukeyi a kan Halimatu ba suyi tasiri a kanta ba, saboda halimatu ta kasance mace mai ibada kuma dukkaninsu bata nufe su da sharri ba shiyasa kullum Ubangiji ke kara kareta daga sharrin su da makircin su, duk wani asiri da sukeyi baya tasiri idan ma yayi baya dadewa yake karyewa, ta inda Halisa take samun galaba akan Abbas din shine ta gurin shaye-shayen magungunan mata to tana d'an janye hankalinsa watarana dan gaskiya irin magungunan da Halisa take sha suna da tsada har dana turawa sha take ita dai burinta ta janye hankalin Abbas din ya wulakanta matarsa uwar 'yayansa, abinda Halisa bata sani ba kuwa shine irinsu Abbas asiri baya saurin kama su idan ma ya kama su to baya wani tasiri a jikinsu zai karye! saboda Abbas mutum ne me yawan azkar da karatun al'akurani mai girma gashi sallahr asubah bata wuce shi, shiyasa duk wani asirin da suke masa baya zama a jikinsa.
Halisa tun haihuwarta ta farko take samun matsala daga zarar ta samu ciki baya yin kwari zai zube, ta shiga tsananin damuwa da tashin hankali! ganin 'Ya'yan Halimatu sunyi wayo har sun soma zuwa makaranta gashi mahaifinsu naji dasu yana yi musu hidima kamar hauka, ai babu shiri ta bazama yawon gidajen masu magani har gurin 'Yan bori zuwa take su bata magani tazo ta jika tasha, ta yini tana amai, da murkukusu, amma taki ta gane hanya madaidaiciya ta fawwalawa Allah domin shine mai bayarwa da hanawa, Kullum kokarinta ya za'ayi ta haihu ko ta halin 'kaka. Abbas ganin ta tashi hankalinta dan har ramewa tayi sai yayi musu viza domin zuwa 'kasa mai tsarki su roki ubangiji hakan be mata dadi ba taso ita ya kaita kasar waje likitoci su dubata idan ma dashe za'ayi mata zata amince ita gani take idan sukaje saudian ba zata sanja zani ba! Gabadayan su dashi da iyalinsa suka nufi kasa mai tsarki, Halisa ta dinga wani iyayi tana shige masa gani takeyi ai saboda ita aka zo kasar! Halima dai sai dai tayi mata dariya kawai dan ita wataran idan Halisa na wani abu har dariya take bata, tana kallonsu zasu shirya su fita ita da Abbas wai zasuje asibiti sai dai tayi musu fatan dawowa lafiya, ta lura shima mijin nasu na biyewa Halisan ne dan kawai a zauna lafiya.
Ita kuwa Naja'atu mugun haushin Halisan take ji dan ta soma hankali a lokacin, idan taga tanayi wa mamanta wani abu ranta 'baci yake sai tayi yun'kurin magana sai Halimatun ta hanata, sai dai tayi 'kwafa kawai! ita hakurin mamanta ta har mamaki yake bata, kuma a duk sanda za taga Abban nasu yana magana da Halisa sai taji haushinsa, tashi ma take ta bar gurin, wani lokacin kuma idan taga sun shiga daki da Halisan sun dade kuka take zuwa taci ta koshi! ta fito tana kumbura fuska, Halimatu ta gane yarinyar na kishinta shiyasa takejin ciwon abinda ake mata, ta kuma fahimci yarinyar za tayi kishi sosai dalilin da ya sanya take yi mata 'yar nasiha a fakaice! Naja'atu kam jinta kawai take yi tana ganin kamar wani abun ma itace take bada goyon bayan Halisan nayi mata, 'kiri-kiri sai suna zaune a guri daya Halisa zata tsiri wasu abubuwa wanda suke sawa ta janye hankalin Abban nasu! duk sanda haka ta faru taga ya tashi yabi bayan halinsa ji take kamar zuciyarta zata babbake! ko ya fito bata kulashi idan yazo yana musu magana banza take dashi sai dai yai ta tambayar Halimatu ko wani abun ne yake damunta Halimatu tasan abinda take fad'a masa maganar ta wuce! Naja'atu gabadaya daina walwala tayi ta daina sakin fuskarta, rashin kunya takeyi wa Halisa a duk sanda tasa mata baki a cikin maganarta dan Halisa akwai katsalandan daga zarar tazo taga suna hira da wasa da 'yan uwanta su Saddiqa da Mussadiq sai tazo ta dinga buga musu tsawa tana hantararsu, aikuwa dama a ciki take da ita, tace watarana suna wasa tazo tana yi musu tsawa! Tace"Mu dan Allah ki daina zuwa kina takura mana muna maganarmu ke waye ya takura miki eye? ina cewa abinda kike so shi kikeyi saboda haka ki daina zuwa kina mana tsawa mtwsss!." Takarasa maganar tana jan tsaki.
Halisa ta fusata sosai hannu ta fitar ta tsinka mata mari tana d'ura mata ashar! sai ambato sunanan Baba malam take tana zagi! Naja'atu ta dinga kuka tana fad'in "Allah ya isa ba kakana kike zagi ba naki kike zagi!
Halimatu tazo tana doke bakinta cikin 'bacin rai tace" Ashe baki da kunya Naja'atu." Tana kuka tace"Mamma kina ji fa tana zagin Baba Malam me yayi mata? wallahi sai na fad'awa Abbanmu." Kai tsaye ta nufi dakin da yake kwance yana bacci! Halisa da Halimat suka bita da kallo cike da mamaki! Halisa mamakin yarinyar take na mayar da uban wasu nata komai akayi sai tace Abbanta ko a gidan ubanwa ya zama Ubanta oho.
Yana tsaka da bacci yaji kukanta a kansa, ya bude idonsa da sauri! yana kallonta a tsaye a kansa tana goge fuska hawaye wani na sake zubowa, mikewa yayi zaune ya kamo hannunta ya zaunar kusa dashi.
Cikin tausasawa yace."Waye ya saki kuka." ? Cikin shashsheka tace"Gata can Anti Halisa muna wasa da dariyarmu tazo tana hantarar mu wai sai mun tashi mu bata guri zatayi kallo, shine dan nayi magana ta mareni har da zagin Baba Malam."
Ransa ya 'baci! Yace." Kan wane dalili zata tashe ku a guri kuna wasa? saboda za tayi kallo sai ta hantareku! hannunta ya ri'ke suka mike a tare suka fita palon
Halisa da Halima na tsaye sai musayar yawu suke Halisa na fad'in "Wannan iskancin da 'kanwar taki take yayi yawa haka kawai saboda samun guri ta mayar da uban wasu nata to tun wuri ki fada mata ba ubanta bane kada ma ta dauka tanada gadonsa."
Halimatu ta bude baki kenan za tayi magana ta hango fitowarsu yana rike da hannunta, Halisa ta kallesu ranta idan yayi dubu ya 'baci! Hura hanci ta shigayi tace"Au! zuwa tayi ta taso ka daga baccin."?
Ya 'bata fuska sosai yace."Koda bata tasheni ba dama dai-dai wannan lokacin nayi niyyar tashi, shin me yaran nan suke miki kullum kike matsa musu bakya barin su su huta."!
Halisa ta rik'e bakinta cikin mamaki take dubansa! Yace."Magana nake miki." Ganin yanda yasha kunu ne yasa ta sassauta murya saboda tasan halinsa sai tace"Kawai dan nace su tashi su bani guri zanyi kallo shine fa yarinyar nan ta hau yi min rashin kunya harda zagina."
Da sauri tace"Ni wallahi sharri tayi min ban zageta ba." Halisa tace"To nayi miki karya ko." Zumbura mata baki tayi ta murguda mata shi! Halisa ta shiga jijjiga kanta tana mamakin saken da yarinyar ta samu a gurin maigidan, kauna da son da yakewa yarinyar ta lura ko 'yayansa bayayi wa."
Yace."Kawai saboda zaki zauna kiyi kallo sai ki tashesu mai suka tsare miki! bana so ki sake hantarar min 'yaya duk wani abu da nake nema a duniya saboda su nake nemansa, kafin Allah ya bani sai da na cire tsammani dan haka dole ne na kyautata musu dan bana son abinda zai 'bata musu rai! duk abinda suke su zasuyi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali kamar yanda kema kikeyin abinda kike so."
Halisa takaici kamar ya kasheta, har ta bud'e bakinta zata ce "Ai ita wannan d'in da kake magana a kanta ba 'yar ka bace.......Sai kuma ta sanja shawara, tace" Shikkenan me 'yaya nima Allah ya bani." Tana 'kare maganarta sai ta fashe da kuka ta nufi daki....Jikinsa ne yayi sanyi kuma, Halimatu ta kalleshi murya na rawa tace"Haba Abban Naja'atu ba haka ya kamata ka yanke hukunci ba! kasan kowaye akayi wa haka dole yaji rashin dadi, yarinyar nan Naja'atu itace tayi mata rashin kunya kamata yayi ka fara hukuntata tukkuna."
'Dan ya mutsa fuskarsa yayi kamar zaiyi magana kuma sai ya fasa, hannun Naja'atu dake cikin nasa ya saki ya juya ya nufi dakin da Halisan ta nufa
Ita kuwa Naja'atu bata so hakan da yayi ba taso ya kyaleta taje tayi kuka taji ciwon a ranta kamar yanda take yini tana 'kuntatawa mamanta rai to itama yau ta d'and'ana taji.
Halima ta rufeta da fad'a kan abinda tayi tace"Wallahi duk sanda na sake ganin Kinyi mata tsaki sai ranki ya 'baci ko an fada miki sa'arki ce." ? Kuka tasa ta nemi guri ta zauna tana fad'in "Mama kina ji fa tana zagin mahaifinki Baba malam Kinyi shuru dan nayi magana sai kice nayi laifi ."
Jikinta a sanyaye tace"Dan ta zage shi sai me? ni nasan ba Ubana ta zaga ba nata take zagi saboda haka na fada miki babu ruwanki da ita har mu bar 'kasar nan." Shiru tayi kawai ba tace komai dan gaskiya ita ba zata dauki cin kashi da wulakancin da Halisan keyi mata ba
haka suka cigaba da zaman doya da manja tsakanin Halisa da Naja'atu babu sassauci kowa najin haushin dan uwansa, Naja'atu taci alwashi kan cewar duk sanda Halisa ta sake kuntatawa mamanta rai to itama sai ta 'kir'kiri abinda zai janyo musu fad'a a tsakaninta da Abbansu, Halisa tunda taga take-taken Naja'atu da irin iskancin da take mata sai ta shiga taitayinta ta rage yiwa Halima wasu abubuwan na rashin arziki badan komai ba sai dan sanin matsayin Naja'atu da tayi a zuciyar maigidan nasu, tasan idan ta tsananta ranta ne kawai zai 'baci a banza.
Sati biyu sukayi a kasa mai tsarki suka dawo gida, Likita ya d'orasu Akan magani, kan cewar in dai Allah ya nufa da akwai sauran rabo a junansu to zasu haihu.............Wata uku da dawowarsu Halisa ta samu ciki murna ta dinga yi tana adduar Allah ya zaunar mata dashi, to shima maigidan yayi farin cikin ganin cikin yayi wata hudu bai samu matsala ba, sai ya umarce data zauna ta daina aikace aikacen gida, mai aiki yace zai dauko mata, tace ya bari zata dauko 'yar yarta sai ta dinga taimaka mata, aikuwa hakane ya kasance Unguwar
Aisami
ya kaita da kansa taje ta dauko Shamsiyya 'Yar yarta budurwa ce 'yar kimanin shakara goma sha hida ta girmi Naja'atu da shekaru biyu, Shamsiyya irin masu shegen iyayi ne gata mummuna amma saboda tsabar shafa mai tayi fari da haske! murna sosai Shamsiyya tayi da zuwanta gidan Halisan tasan kafin ta dawo gidansu sai ta sauya tayi ki'ba dan gaskiya ko zuwa gidan sukayi da ziyara basa dawowa ranar da sukaje sai sun kwana dan har daukar kawayenta takeyi ta kaisu gidan tana musu iyayi kanwar mamanta na auran *Alhaji Abbas Dan kwagila*........To cikin ikon Allah Halisa ta haihu kalau ta samu 'ya mace sai dai ba haka taso ba taso ta haifi d'a namiji dan gaskiya Mussadiq ya tsone mata ido. Ita kuwa Yaya Ramlatu har akayi suna cikin yada habaici take mussaman idan taga Halimatu tazo gidan sai ta tsiri shige da fice tana sakin maganar da duk tazo bakinta........"Duk cikin da ya haifi mace watarana shi zai haifi namiji Halisa ki kwantar da hankali gabadaya dangi munfi bukatar mu samu zuria dake dan haka tunda kin fara dasa 'kwan ki a gidan Abbas to kiyi abinda kike so babu me ce miki don me.!! Ire-iren maganganun da Yaya Ramlatu keyi kenan Shamsiyya na taya ta, Halima bata ta'ba tanka musu ba abinda ya kawota takeyi ta tafi.
Ranar suna da kyar Abbah Abbas ya lalla'ba Naja'atu ta shirya ya kaisu, dan cewa tayi ita ba zataje ba bata da lafiya wanda shi da Halima duk sun san 'karya take yi kawai rashin jituwar dake tsakinta da Halisan yasa tace ba zataje ba.......kwalliya sukayi sosai gabadayan su harshi angon 'karni suna sanye cikin dakakkiyar shaddar galila mai kalar sararin samaniya(sky blue) sun yi iri daya da juna Halima da Naja'atu da Saddiqa! dinki iri daya ne a jikinsu doguwar riga ce wacce tasha uban stone work da aka kashe kudi gurin yin sa
Abbah Abbas shida Mussadiq sunyi iri daya cikin babbar riga da 'yar ciki hularsu iri daya hakanan takalman su iri daya, agogo iri d'aya, sunyi kyau sosai dan kafin su fita sai da sukayi hotona sannan ya kira Salim dan Yayarsa Ramlatu a waya ce yazo ya daukesu.......Salim dan kimanin shekaru ashirin da biyar a duniya matashin saurayi mai jini a jiki d'an kwalisa ne sosai kuma yana kan lokacinsa dan babu abinda Abbah Abbas baya yi masa na rayuwa ya dauki yaron tamkar d'an cikinsa, shine ya tsaya masa kan karatunsa har yayi degree kuma ya d'ora shi kan harkokin kasuwancinsa Salim yasan wasu daga cikin sirrinkan Abbah Abbas amma kuma bai san wasu ba, Salim tun kafin Naja'atu ta kai girman haka yake sonta yana so su kammala secondary tukkuna ya tunkari Kawunsa da maganar tabbas yasan shi zai shige masa gaba gurin ganin ya mallaketa, amma dai duk da hakan yana ta kokarin kafa gwamnatinsa a gurin Naja'atun, itace take nuna masa bata gane me yake nufi ba.
Koda Salim yayi tozali da Naja'atu kasa nutsuwa yayi ya dinga kallonta yana sosa kansa ga wani shegan mirmushi a fuskarsa, Naja'atu ta 'bata ranta tana kallon Abban nasu dake gyara babbar rigarsa domin shiga mota, murya na rawa tace"Abbah kace ya daina kallona." Abba Abbas na gyara zamansa a motar ya kalli Salim yana d'an 'bata fuska yace."Kai bana son shashanci ka shigo mota mutafi na lura da kai tun d'azu ka damu yarinyar nan da kallo sai wani sosa kai kakeyi na fad'a maka ba zan baka itaba sai da amincewarta." Salim yasa dariya yana kallonsa Yace."Haba Kawu dube ni fa kaga ni da kyau! ni ba irin mazan da mata zasu ce basa so bane, ni nasan nan gaba kadan Ita dakanta zata furta maka ni take so." Abbah Abbas na murmushi yace."Ni dai na fada maka malam ka nemi yardar ta dan cikin 'yayana babu wacce zanyiwa auran dole." Salim yace."Insha Allahu Naja'atu tawa ce." Mussadiq ya rike hannunsa da fadin"Nima ina so ka auri Yayarmu." Rank'washin sa Naja tayi ya shiga motar yana kuka, Halima ta d'auka Abban nasu zaiyi mata fada mai yasa ta dakeshi sai taji yana cewa"Kai Mussadiq bana son rashin kunya ka tsokane ta ta hukuntaka kuma sai ka kama kuka." Mamaki sosai ya rufe Halima! Girgiza kanta kawai tayi dan bata da bakin magana tana iya yiwa Naja'atu fad'a yace dan me shiyasa tayi shuru da bakinta, hakika kulawar da yake nunawa a kan 'kanwartata tana burgeta haka nan suma su Baba malam suna jin dadi yanda Abbas din ya r'ike musu 'yarsu tamkar shi ya haifeta, duk abinda zaiyi wa 'yayansa shi yake mata wani sa'in ma har yana bambamta ta dasu gurin wani abun.
Gabad'aya Naja'atu kasa sakewa tayi a gidan sunan ganin yanda jama'a ke musu wani irin kallo wasu ma sai nuna su sukeyi, dalilin da yasa kenan ta zauna guri guda tana kalle kalle.......Halima kam kasa zama tayi ta mike ta shiga cikin mutane ana hidima da ita duk da irin kallon banzan da suke mata hakan bai sa ta koma ta zauna ba, ta kau da kai tana ta shiga jama'a cikin fara'a ana gaisawa da ita.
Tana zaune a palo wasu 'yan uwan Halisa suka shigo suna she'ka dariya d'aya daga cikinsu tana fad'in "Ku tsaya kuga yanda kishiyar Anti Halisa take tafiya." duk sai su katsaya suna kallonta, sai ta shiga cangala 'kafarta d'aya tana cillata kamar yanda Halima keyi idan tana tafiya! Dariya suka kwashe da ita suna tafawa! Shamsiyya tace"Kuma wai a haka a nakashe take matar so a gurin miji." Duk sai suka ri'ke bakinsu suna kallonta 'karin bayani suke jira tayi musu! Shamsiyya ta bud'e bakinta za tayi magana taji saukar mari a fuskarta!
Naja'atu ce tsaye a tsakiyarsu tana zubar da hawaye itace kuma ta mari fuskar Shamsiyya! Wacce take gwada tafiyar Halimatu ta nuna murya na rawa tace."Yanzu hallitar Allah kike gwadawa? Ke baki ji kunyar abinda kika yi ba Allah yayi hallitarsa yanda yake so kina gwada kuna dariya kema fa baki wuce Allah ya mayar dake haka ba."!! Afusace Shamsiyya tace"Dan kutumar Ubanki ta gwada d'in! shegiya yar karoro! har ni zaki tsinkawa mari! lallai zan nuna miki nafi ki zafin kai!! kafin Naja ta ankara ta rufeta da duka! Sai sauran ma suka shiga taya ta suka rufar wa Naja'atu da duka har sai da ta durkushe a gurin!! Ihu! takeyi tana kokarin kwatar kanta....
Halisa ta fito daga daki a guje! jama'ar dake waje suka shigo palon suna tambayar abinda ke faruwa.
Shamsiyya tana hura huci! ta shiga fada musu karya da gaskiya. Yaya Ramlatu tazo ta tsaya a kan Naja'atu tana zaginta ta uwa ta uba! Naja'atu kasa motsi tayi dan ta daku sosai! Halima ce tazo ta kama hannunta ta mikar da ita, tana kuka itama tana kuka su Saddiqa da Mussadiq na kuka! abin gwanin ban tausayi! Ita kuwa Yaya Ramlatu kamar kara zugata akeyi ta tara mutane sosai sai aibata Halima da Naja'atu take da iyayensu kowa na tofin ala tsine a kansu! Halisa ganin abin ya kwa'be! yasa tazo tana bawa Ramlatu hakuri saboda tasan idan maigidan ya samu labarin abinda ya faru to babu shakka al'amura zasu 'baci! dan rayukan kowa sai ya 'baci! da kyar ta rarrashin Yaya Ramlatu tayi shuru taja tawagarta suka fita harabar gidan domin cigaba da rabon abinci.........Halisa ta dinga yiwa su Shamsiya fada kan abinda suke kokarin janyo mata, dukan Naja'atu da sukayi yana nufin abubuwa da yawa a gareta hakan na iya barazana ga auranta, shiyasa bayan ta shiga dakin tasa Mussadiq ya kira mata Naja'atun! K'in zuwa tayi sai da Halima ta rarrasheta sannan ta shiga dakin.
Halisa ta kwantar da kanta tana fadin "Naja'atu kiyi hakuri kinji ko abinda su Shamsiyya sukayi miki kinga dai a gabanki na hukunta su kuma nayi musu fada dan Allah kada ki fadawa Abbanku." Zum'bura bakinta tayi tace"To me yasa baki rama mun dukan da sukayi min ba! Ni wallahi bazan yarda ba sai na fada masa sun zageshi sun zagi Baba malam sun dake ni kuma sun kushe hallitar Allah."
tana k'are maganar ta ta fita daga dakin, Halisa rakata tayi da kallo baki a sake.
Tana fita daga dakin ta dauki wayar Mamanta wani guri ta 'buya ta kira numbarsa, ganin numbar Halimatu yasa ya dauka da sauri yace"Ranki ya dade yaya ina fatan komai lafiya."? ai kawai sai yaji fashewar kukan Naja'atu a kunnansa! Ya mike tsaye da sauri! Yace''Naja'atu lafiya kike kuka yi shuru ki fada mun abinda akayi miki?" cikin sar'kewa tana jawo numfashi irin na sharri ta shiga wassafa masa abinda ke faruwa a gidan sunan." Ranshi idan yayi dubu ya 'baci! Yace."Daina kuka kinji ko? zan dauki mataki wato Halisa ta tara mutane ne dan ta tozarta ni! babu laifi ki bawa maman taki wayar zamuyi magana." Tana shashsheka da goge fuska tace"To." Zuwa tayi ta kaiwa Halima wayar da fadin "Gashi Abbanmu zaiyi magana dake." Halima ta fita daga cikin mutane ta samu guri tana amsa wayar, Jinsa a fusace! yasa ta sassauta mirya tana so ta fahimtar dashi yaki sauraranta yace."Zai turo Salim yanzu yazo ya daukesu ya mayar dasu gida ita kuma Halisa zata gamu dashi." Kafin ma tace wani abu ya kashe wayarsa.....Kasa'ke tayi da waya a hannunta tana mamakin wannan al'amari! gabadaya idan Naja'atu zata fada masa magana baya tsayawa yayi nazari zai hau kai ya zauna, tabbas ba sune suke da laifi kan faruwar hatsaniyar ba, to amma yana da kyau yabi komai a sannu tasan halinsa da mugun zafin zuciya zai iya aikata abinda ba shikkenan ba.
Aikuwa dai bayan watsewar taron suna da ya shigo gidan Halisa sai da ta fuskanci 'bacin rai sosai dan cewa yayi ta ajiye masa 'yarsa ta fice masa a gida tunda dama abinda ta shirya yi kenan shiyasa ta damu sai tayi taron suna dan haka ta ajiye masa 'yarsa ta bar masa gida, kuka wurjan-wurjan ta dinga yi tana bashi hakuri tana kuma gaya masa yanda al'amarin ya kasance cewar ita sanda abun ya faru ma tana daki bata da laifi.
Jin tana ambatar sunan Shamsiyya a maganar yasa ya 'kwala mata kira tana zaune a palo tayi tsuru tsoronta Allah tsoronta annabi kada yace ta bar masa gida, Da sauri ta shiga dakin, yace"Kece mai gwada yanda matata Halima take tafiya ko."? Girgiza kanta ta shiga yi tana rantse-rantse! Yace."Duk abinda kukayi wa Ubangiji ku dashi ne dan haka bana bukatar ganin ki a gida nan ki dauki kayanki ki tafi." ai ta haihu babu wani sauran aiki yanzu." Hannu ya zira cikin aljihu ya dauko dubu daya ya mika mata da fadin"Ki shiga mota." Kar'ba tayi jiki a sanyaye ta fita daga dakin, zuwa tayi ta shiga hada kayanta tana kukan takaici taso ta zauna a gidan har sai ranar da Antin nata tayi ar'bain sai ta tafi amma mutsiyaciyar Yarinyar nan Naja'atu tasa an koreta......Abba Abbas bai bar gidan ba sai da ya tabbatar da cewar Shamsiyya ta bar gidan sannan hankalinsa ya kwanta ko sallama baiyi da Halisan ba yayi tafiyarsa.
Gidan Yaya Ramlatu ya nufa koda taga yanayin da yazo mata dashi sai tasha jin jikinta, ta shiga yi masa rawar jiki, ya dinga kallonta takaici kamar ya kashe shi, Ramlatu ta girma amma bata san ta girma kullum abubuwa take irin na marasa tunani, ganin yanda take rawar jiki a kansa ne yasa ya sassaura zuciyarsa ya shiga nuna mata illahr abinda takeyi take kuma tara mutane na wulakanta masa matarsa hakuri ta bashi kamar gaske tace insha Allahu ta daina........Yaji dadi sosai hakan yasa ya zauna sukayi hira irin ta 'yan uwantaka.
Fushi sosai ya shiga yi da Halisa duk domin ya nuna mata kuskuranta a ganinsa idan da bata bada goyan baya ba to babu wanda ya isa yaci zarafin matarsa da iyayanta, Halima ba tayi musu laifin komai ba amma sun dauki karan tsana da tsangwama sun dora mata.
*BAYAN SHEKARU UKU*
Lokacin Naja'atu nada shekara goma sha shida a duniya komai nata ya fito a zahiri macace doguwa mai fadin 'kugu da cikar kirji bata da haske sosai amma ba za'a sata a layin bakake ba fatar ta mai kyau ce mai kuma wahalar samu, tana da kyau a fuska da jikinta wannan dalilin yasa bata fiye yin kwalliyar fuska ba, kuma bata sanya mayafi sosai tafi amfani fa hijabai saboda ta tsani kallon da maza ke mata a duk sanda zata fita babu hijab a jikinta takan fuskanci 'bacin rai sosai! maza sun dinga kallonta kenan har da masu tsayr da ita, shima Abban nasu ya fahimci yarinyar nada wani irin jiki mai daukar hankali duk wani lafiyayyan namiji, wannan dalilin yasa kullum idan yana gida zasuje wani gurin idonsa a kai! idan sun saka hijabin da be rufe musu jiki sosai ba sai yace suje su sanja wani, sosai yake kula dasu da takatsantsan a kansu. mussaman ita Naja'atun da ya lura tana kan lokacin balagar ta....to a dai dai lokacin ne kuma suka gama secondary ita da Ilham 'Yar gidan Baba Magaji ita kuma Saddiqa na aji ss1 aji hudu kenan....... Lokacin kuma Halimatu nada tsohon ciki haihuwa ko ya yau ko gobe........ a wannan lokacin ne kuma sha'kuwa gami da soyayya mai kar'fin gaske ta shiga tsakanin Salim da Naja'atu, hatta da manya sun san da maganar! mahaifiyar Salim wato Yaya Ramlatu kwata kwata bata kaunar al'amarin ta zuba musu ido ne kawai tana kallonsu! Ita kuwa Naja'atu soyayyar da takewa Salim din tasa ta manta wacece mahaifiyarsa tana gani ita in dai Salim din zai aureta babu ruwanta da masifar Mahafiyarsa, Abbah Abbas kuwa ganin yanda suke kaunar junansu sai al'amarin yayi masa dadi sosai yana fatan Allah ya tabbatar da alkairi a tsakaninsu, kenan shi ya kasance waliyyin mutum biyu Salim din da ita Naja'atun.
A dai-dai lokacin da suke kokarin tafiya babbar makaranta, Allah ya saukar da ikonsa kan Halimatu gurin haihuwar cikin dake jikinta Ubangiji ya dauki ranta! bata tare data haife abinda ke cikin nata ba, mutuwar data girgixa zukatan al'umma da dama! mussaman Yaya Ramlatu da Halisa kwana sukayi suna sambatu da zabure zabure! Halima ta mutu da kalmar shahada a bakinta kuma ta mutu sanadiyar haihuwa babu shakka abun alfaharin ko wane musulmi kenan, duk wani mai kaunar Halimatu zai taya ta farin cikin samun rahamar Allah da tayi dalili kenan da ya sanya mijinta da iyayenta ke jin sassauci a cikin zuciyoyinsu idan suka tuna da cewar fa Halima tuntuni ta manta da rayuwar duniya domin ta riga ta gama dacewa, duk wanda zai budi baki alharin ta zai fad'a! Tabbas Annabi yayi gaskiya da yake cewa mutuwar mumini itace ke sawa mutane su girgiza kuma duk wanda ya mutu jama'a na fadar alherinsa babu shakka Allah yaso shi da rahamarsa.
*Ubangiji Allah kasa muyi kyakkyawan karshe ameen*
To Bayan kwana bakwai ne da rasuwar Halimatu al'amarin ya kasance.......
Inda su Baba Malam Alhaji Samaila Abba Magaji dashi kansa Uban gayyar suka zauna suka tattauna maganar yin *MADADI* da Naja'atu wato Naja'atu ta maye gurbin 'Yar uwarta Halimatu data dauka a matsayin mahaifiyarta.
*A Pege na gaba zamu dawo ainihin labarin da muka fara da farko*
*NAGODE 'KWARAI DA ADDUARKU A GARE NI NAGODE👏🏻*
*🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~~~
_*Na gaishe daku 'Yan 'Kungiyata ta Manazarta Writers Association, Hakika ina jin dad'i had'in kanku, kuma ina alfahari daku mutu'ka! gabad'ayan ku ina rokon Allah ya d'aukaka min ku d'aukaka mai amfani Ubangiji Allah ya baku ikon rubuta abinda al'umma zasu amfana dashi*_
*PEGEN YAU NAKI NE*
*UMMU HANIFA*
Marubuciyar littafin
*ANYA MUTUM CE?🤔*
Ina mutukar alfahari dake 'Yar d'akina Allah ya 'kara miki basira da haza'ka, ki cigaba da rubuta littafai masu dadi da ma'ana♥️
*7*
Kanta a tsakanin cinyoyinta ta d'ora duka hannuwanta saman kanta ta takure kanta guri guda sai kuka take tana girgiza kanta, Baba Talatu ta dafa bayanta a sanyaye tace"Naja'atu yanzu kinji komai daga bakin malam ko? Alhaji Abbas bashi ne ya haife ki ba kamar yanda kike tunani, A'a ba haka bane shi d'in ya kasance miji ga 'yar uwarki Halimatu Allah ya ji'kanta da rahama, wannan dalilin ne yasa su malam suka yanke wannan hukuncin a kanki babu laifi dan kin auri mijin 'yar uwarki kuma dukkanin mu bamu aikata haramci ba kamar yanda kike tunani da farko, idan kin auri Alhaji Abbas hankalin mu zai kwanta saboda mun san zai ri'ke mana ke da kyau da amana kuma su Saddiqa da d'an uwanta Mussadiq zasuji dad'in kasancewar ki a matsayin matar babansu zasu dinga kallonki tamkar mahaifiyar su." ............Fuskarta jage-jage da hawaye ta d'ago kanta tana kallon mahaifiyar tata, girgiza kanta ta shiga yi kana tace"Ni wallahi bazan iya zaman aure dashi ba, a Uba fa na daukeshi kuma ya za'ayi kuce zaku daura min aure dashi, bayan dukkanin ku kusan da maganar Salim wannan ai abun kunya ne a gurunsa ace ya aure ni bayan shine ya raine ni ya rike ni a matsayin 'yarsa, kawai kuma saboda mutuwa ta ratsa tsakaninsa da matarsa sai kuce zakuyi masa *MADADI* dani ni wallahi bana sonsa."
Ta'karashe maganar cikin gursheken kuka mai karfi.
Baba Malam yace."Ai dama ba cewa muka yi dole sai kin so shi ba, cancanta muka duba shiyasa muka yanke wannan hukuncin saboda haka ina so ki cire maganar ko wane namiji a cikin ranki domun kuwa mutukar ni ne na haifeki to baki da miji sama da Mijin 'yar uwarki wato Alhaji Abbas, zaki aure shi ko bakya sonsa nan gaba idan kinyi hankali zaki gane abinda muke nufi dayin hakan."
Da rarrafe ta isa inda yake ta ri'ke hannunsa jikinta sai kyarma yake tace"Wallahi Baba malam zaku jefa rayuwa ta cikin garari saboda na fada muku iya gaskiya shine ni ba zan iya zaman aure dashi ba, na farko yayi min tsufa kuma abun kunya ne ace ya aure ni alhalin Ni 'yarsa ce bayan haka kuma yasan shine waliyi na gurin daurin aurena da Sali.......Abba Magaji ya fusata! ya kai mata mari da bayan hannu! jikinsa na tsuma! yace."Dan ubanki har wata cancanta kike nema? dame kika fi Alhaji Abbas din ? da har kike kiransa tsoho! ana nuna miki abinda ya dace dake kina maganar abin kunya, kina nufin dukkaninmu bamu san abinda ya dace ba kenan? to wallahi tallahi na 'kara ji kin bud'e baki kinyi wata magana anan gurin sai na futar miki da jini shashashar banza da wofi."
Shuru tayi jikinta sai rawa yake hawaye kuwa kamar an bude famfo! sai famar girgiza kanta take tana toshe bakinta tamkar wata zautacciya.
Tausayi ta bawa Baba malam ya kalli Alhaji Magajin a nutse yace."Yarinyar nan taurin kaine da ita ina ganin zamu sake zama mu tattuna kan maganar, bana so ayi abu daga baya kuma azo ana dana sani.
Alhaji Magaji yace."Malam babu wani zama da za'a sakeyi idan wata magana ta fito daga 'bangaran mu ba zasuji dadi ba, tunda kaga sune suka zo mana da maganar yana da kyau mu basu goyon baya kan abinda suka zo mana dashi duk mutumin da ya nuna yana kaunar had'a zuria da kai to ka tabbata ba 'karamin so yake maka, hakika nasan abokina Abbas yaji dadin zama da Halimatu shiyasa ya bukaci a bashi Naja'atu ta zame masa *MADADIN TA* dan haka tunda mun riga mun gama magana babu dadi kuma aje ace musu wani abu daban."
Baba Malam yace."Yarinyar ce take bani tausayi bana son wannan kukan da take yi yana d'aga mun hankali amma tunda kace haka shikkenan Allah ya sanya alkairi cikin al'amarin ya kauda kowace irin fitina da zata biyo baya.
Baba Talatu dashi Magajin suka amsa da "ameen" Mikewa yayi yai musu sallama da niyar tafiya gida dan lokacin goma na dare ma ta wuce! Fatan sauka lafiya sukayi masa ya dauki hularsa da key dinsa ya fita daga gidan.
Cikin tausawa ya kalleta da fad'in"Ki tashi kije ki kwanta komai yayi tsanani maganinsa Allah kuma ina so ki zauna kiyi tunani kan wannan hukuncin da muka yanke a kanki, mune muka haife ki ba zamu cutar dake ba, da mutumin nan da ba nagartacce bane to da baza mu amince da bukatarsa ba to mun tabbatar da cewar idan muka dauke ki muka bashi muna da tabbacin zai kula dake kamar yanda ya kula dake a lokacin da baki san kanki ba."
Mikewa yayi ya shiga da'ki bayan ya gama maganarsa, Baba Talatu ta jima tana rarrashinta kafin ta mike itama tabi bayan Malam din suka barta ita kadai a tsakar gidan tana kukan zucci.
Mamaki take sosai! wai ashe dama Abban Abbas din ne ya bukaci auranta ita duk a tunaninta su Baba malam ne, girgiza kanta kurrum take tana mamakinsa, to ta aureshi tayi yaya dashi? ta yaya za ta iya rayuwar aure dashi? lallai ma! ita abun ma mamaki yake bata ko kunya bai ji ba yace zai aureta bayan yana amsa sunan Uba a gurinta, gashi kuma yasan da maganar Salim hummm! aikam ba zata yarda ba duk yanda za tayi sai ta rushe wannan auran, sam ba zata auri tsoho dan shekara hamsin ba haka kawai sun gina soyayyarsu da masoyinta yazo yayi musu kutse a rayuwarsu ko kunya baya ji zai zo da wannan maganar! 'Kwafa tayi ta mike ta shiga d'aki!
Tana shiga dakin taji shashshekar kukan Saddiqa suna kwance ita da Mussadiq a katifa ta rungume shi sai kuka take!
A gigice ta kunna haske wayarta, tana haske su! Saddiqa ta rufe idonta tana sake takure jikinta guri guda......"Ke Saddiqa menene? dama ba kiyi bacci ba."? Saddiqa ta mike zaune tana goge fuskarta, 'Karasawa tayi ta zauna gefan katifar tana kallonta, a sanyaye tace"Meye kika kuka? nafada miki ki dainawa Mamma kuka idan kina so ta dinga samun rahamar ubangiji."
Saddiqa ta goge fuskarta tana kallonta tace"Ni ba Mamma nakewa kuka ba, nasan abinda nake yi a halin yanzu Mamma babu abinda take da bukata a gurinmu sai addua ba kuka ba."
A d'an sanyaye tace"To me kikewa kuka."? Saddiqa ta kalleta wasu hawayen na sake zubo mata tace"Yaya Naja'atu me yasa kike nuna 'kiyayyar ki 'karara a kan Abbanmu."!? Gabanta ne ya fad'i! sai tasha kunu! tace"Wace irin magana ce wannan Saddiqa? kada kice min kema kina goyon bayan na aureshi."
Saddiqa taja majina tana goge hancinta tace"To menene aibu a ciki? dan kin auri Abbanmu ai ba wani abun bane kuma ba ke kad'ai ce kika ta'ba auran *MADADI* ba Yaya Naja'atu idan kika maye gurbin mahaifiyarmu zamu ji dad'i sosai dan Allah kiyi mana wannan alfarmar ki daina nuna 'kiyayyar ki a fili."
Shuru tayi tana nazarin maganar yarinyar! Wai shin da suke ta wannan maganar ta yaya zata fara ne? wane matsayi zata ajiye shi miji ko mahaifi? bafa zai yiwu ba.! Ta kalli Saddiqan data kura mata ido tana jiran amsarta tace"Saddiqa nayi wa Abbanku 'kan'kanta kuma shima yayi mun girma bayan nan kuma ni matsayin mahaifi yake a gurina bazan iya rayuwar aure dashi ba, kuma ki daina tunanin ina 'kinsa wallahi bana 'kinsa saboda Abba Abbas yayi min abinda ba zan ta'ba mancewa dashi ba, kawai dai bana tunanin zan iya rayuwar aure dashi."
Saddiqa tace"To idan baki aureshi ba kin san dole yayi aure kuma gabadayan mu bamu san matar da zai aura ba, kinga zamu shiga halin 'kaka na kayi tunda dai kin san ba 'kaunar mu Anti Halisa take ba, kinga rayuwarmu na cikin 'kalubale nida Mussadiq."
"Eh gaskiya ne duk maganar da kika fad'a to ai ba dole sai kun zauna tare da matansa ba, sai ku dawo gidan Alhaji da zama ko kuma ku dawo gidanan nan nasan Baba Talatu zata ri'ke ku to meye abun tashin hankali.
Saddiqa ta shiga girgiza kanta zuciyarta na wani irin d'aci! tace" Yaya Naja'atu kin manta maganar Abbanmu kenan kin san fa yasha fad'a cewar mutuwa ce kawai zata rabashi da 'yayansa bana tunanin zai amince ya kawo mu nan mu zauna ke ko gidan Alhajin da kike magana ba zai barmu muje ba duk da cewa gidansu ne."
Naja'atu shuru tayi tana tunanin al'amarin Babu shakka zaman Saddiqa da Mussadiq hannun Halisa gagarimun had'ari ne zata iya cutar dasu ta ko wace siga! Itace zata rike su tamkar uwarsu, to ita kuwa ko a mafarki bata tunanin zata koma gidansu a matsayin matar mahaifinsu, insha Allahu ta bar gidan har abada.
Ganin Saddiqan ta tsura mata ido yasa tace"To ki kwanta kiyi bacci zanyi tunani kan maganar ki." Saddiqa taji farin ciki ya rufe ta tace"To shikkenan Yaya Naja'atu nagode Yaushe zaki gama tunanin."? Kallonta tayi na minti biyu tace"Ke dai tunda nace zanyi to zanyi duk hukuncin dana yanke zan fada miki."
Saddiqa tace"To Ubangiji Allah yasa naji alkairi." Amin tace a takaice, Saddiqa ta juya ta kwanta tana adduar Allah yasa ta amince da maganar ta.........
Tsuru tayi ta tsirawa guri guda ido tana tunanin yanda za tayi ta rusa wannan gagarimin al'amarin daya tunkaro ta, kira ne ya shigo Wayarta dake gefanta, ta dauka hannu na rawa, a kunne tasa wayar, ta fashe da kuka 'kasa-'kasa tace"My prince kaji abunda Abbah Abbas ya 'bullo dashi ko.''
Salim dake kwance kan katifar sa yace." Menene ya faru ni banji komai ba." Juyawa tayi tana kallon bayanta, dan bata so tayi wata magana ya kasance Saddiqa taji, sai da ta tabbatar da bacci takeyi sannan ta sake sassauta murya ta shiga fada masa abinda ke faruwa.......Mi'kewa zaune yayi da sauri! lokaci guda gumi ya tsatstsafo masa, yace."Da gaske kike wannan maganar ko kuma dai tsokanata kikeyi."?
"Humm! wane irin tsokana wallahi tallahi da gaske nake wai Abba Abbas shine ya bude bakinsa yake fadawa su Baba malam yana so ayi masa *MADADI* dani!!!
Katifar da yake kai ya doka! da hannunsa da 'karfi! Yace." Kai kaji wata tatsuniya! shi yanzu dan girman Allah baiji kunyar fad'ar wannan maganar ba!!? To shin wai ko ya manta abinda yake tsakanina dake ne da har zai bijiro da wannan tatsuniyar."
Tace"Oho! ni gani nake kawai san zuciya ne yama za'ayi yace haka bayan shi da bakinsa ne yace."Mu daidaita kanmu zai daura mana aure kuma saboda mutuwa ta ratsa tsakaninsa da matarsa sai yace a mayar masa dani a *MADADINTA."*
Salim yayi wani murmushi na takaici yace."Ke nifa na daina mamaki! wallahi zai aikata dama yanda yake wani kula dake da wani takatsantsan a kanki akwai alamun tambaya dama so yake matarsa ta mutu ya aure ki! saboda haka ni kuma wallahi bazan bar masa ba, to in banda ma rigima ina ke ina shi! shekara hamsin har yake tunanin auran yarinya 'yar 'karama kamar ki 16years fa to idan ya aure ki yayi yaya dake? mtwwss."!!
"Humm! ni wallahi Salim mamaki ma ya hana ni nace komai ba kaga yanda su Baba malam suke murna ba, wannan ai tauyewa mutum hakki ne. Ni duk na rasa ma yanda zanyi."
Yace."Kece kuwa kike da yanda za kayi, tun kafin yafiya tayi nisa ki kokarin ganin kin rusa maganar ni kuma gobe idan Allah ya kaimu idan naje daukarshi domin zuwa kasuwa zanyi masa magana akan inaso yazo gurin Baba malam kan maganar auramu sai naji me zaice."
Tace"To yauwa kayi masa hakan nasan dole kunya tasa ya kasa magana ni wallahi duk mutuncin sa ma ya zube a idona mtssssw!!! Takarashe maganar tana jan tsaki!
Yace."Baby ki daina wani damuwa ki kwanta kiyi bacci bazan bari wannan al'amari ya tabbata ba, duk yanda zanyi to zanyi na rusa al'amarin.
A sanyaye tace"Tom shikkenan my Prince kayi bacci mai dad'i kaji ko." Yace."Ke ina wani maganar bacci mai dadi a gurina Wannan dattijon na nema yasa zuciyata ta buga."!!
"Hummm! kawai tace dan ta rasa ma abin cewa, kashe wayar tayi ta zurfafa cikin tunani da nazari! gabad'aya bata so tayi masa rashin kunya saboda shi mutum ne mai muhimanci a gurinta to amma tunda ya 'bullo da wannan maganar kashi hamsin na 'kima da mutuncinsa suka zube a gurinta.
Numbarsa ta laluba ta dinga kallon numbar kamar shi take kallo, shawara take da zuciyarta shin ta tura masa text ko kuwa, wata zuciyar tace" Idan kika tsaya lako-lako kan wannan al'amarin to za kiyi kuka da idonki.......Da sauri ta shiga rubuta masa text kamar haka.
_Assalamu alaikum Abba nmu barka da dare ina tafan kana nan lafiya? Abbah wata magana naji daga bakinsu Baba malam kuma sun ce kaine kazo musu da maganar shine nake so naji daga bakin ka._
Tana tura masa text din ta kashe wayar! kwanciya tayi tana takure jikinta hawaye ne ke kokarin 'kwace mata tana kokarin hana shi fita.
Sai bayan da ya dawo daga sallahr asubahi ne ya kunna wayar tasa, aikuwa text din ne ya shigo yayi saurin bud'ewa yana dubawa............Ya karanta ya kai sau biyar ya girgiza kanshi! lallai To bata yarda ba kenan tana so taji daga bakinsa, shi kam bai san abinda zaice mata ba, kawai sai ya share bai mayar mata da amsa ba, ya cire jallabiyar jikinsa, ya kwanta rigingine kan bed din yana tunanin rayuwa, Halisa ce ta shigo dakin jikinta sanye da hijab kamar wata mutuniyar arziki, tun bayan mutuwar Halimatu wata shiriya tazo mata takeyi komai cikin rashin kuzari.
*🗯️MADADI!!💍*